An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels : DUNIYA TA BISMILLAH INA MATUKAR GODIYA GA ALLAH DA YA BANI RAI DA LAFIYA DA KUMA IKON RUBUTA SABON NOVEL DIN NAN DUNIYATA. MAKARANTA NOVELS DINA DA BIBIYATA INA MUKU GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI,ALLAH YASA WANNAN NOVEL YA FADAKAR YA KUMA NISHADANTAR,KAMAR YANDA MUKA FARA LAFIYA ALLAH YASA MU GAMA LAFIYA AMEEN. KAMAR YANDA KUKA SANI NOVELS DINA NISHADI YAFI YAWA CIKI,INA KUMA GODIYA DA KUKE KARANTAWA HAR MUTUM YA SA KUDI YA SIYA WANNAN YAFI KOMAI DADI,INA GODIYA ALLAH YA BAR KAUNA. 1-5 FREE PAGE LITTAFAN DANA RUBUTA GASKIYA CE MARAICIN RAHMA MAAIKACIYAR GOMNATI CIRANIN AMANA DUK INDA TA FADI KAMARSU CE DAYA KASUWANCI NA JIN DADI SABO HADIN KAI ME MAGANI TUBABBIYA NA KUDI DANA RUBUTA RASHIN SA'A TA GYARU YAR KWANGILA ADDUAR KAWA GIDAN GWAURO/DAN NAZIA DANGIN RABI DUNIYA TA....... GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DIN DUNIYATA DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD, GTBANK. MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER TA 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page din farko naku ne Fans Dina duk wacce ke cikin groups Dina. Zaune suke a wani katafaren Palo na Alfarma,Palo Wanda yaji furniture Dan gaske,duk Wanda ya Shiga wannan Palo bazai so Fitowa ba,wani uban kamshi da sanyi ne ke tashi,Family Guda su Shida rakacal sai ta bakwan Yar karamar yarinya tana Wasa a kasa,Kidan Bob merly ne ka tashi a wata katuwar plasma tv kamar ka dakko mutum,gaba Daya sunyi Shuru duk Basu cikin nishadi,Ahmad Dake narke cikin luntsumemeyar kujera shine yake kada Kai cikin maye da kwaya da gani kasan Kansa ba kalau ba,sai bin wakar yakeyi da bakinsa,gashi babu Wanda ya Isa yace ya kashe ko ya daina,baya Jin Maganar kowa,Mummy dattijuya itace ta nisa fuskarta dauke da damuwa Tace Haba Ahmad Kaine fa babban Danmu Amma ka duba yanda ka maida kanka Completely Useless har mun gaji da Dake Hanya tun daga Lagos muna zuwa Nan Kaduna wajenka akan magana Daya kaki ji,tunda hakane yau da Yamma zamu koma,Wani farinciki ne ya bayyana a kyakyawar Fuskarsa,ya Mike tsaye yace wow Mama the Mama,Allah yau zaku tafi?yawwa Haka nake so sabo da na samu freedom,yau kwananku biyu Kun dameni dama,Shut up Daddy ya Furta banzan yaro marar tarbiyya,ai Kai dama Daddy nasan baka so na,Zama ya sake Yi Yana bin wakar Bob merly,sai Chanel din Suka cire wakar aka Sako tallan Wani body lotion. Wata Uwar Tsawa Ahmad ya saki tare da nuna Tv da yatsa cikin mayensa na giya da kwaya ya kalli dalleliyar Budurwar da aka Nuno tana tallan Body lotion a tv yace Kai...dalla ku matsa can Kar ku kawo Mana Harkar Daudu anan,mu ba Daudu Muka zo gani ba Ana Harkar arziki zaku zo Mana da Mata Yan Daudu,ke dalla ja can, Dan uwarki a Nan Nigeria muna da man shafawar mu Habiba yawwa,Muna da Habiba Muna shafawa Muna Kara Baki wuluk abin mu yafi Mana,Dariya ya Bawa duka Yan palon har Daddy ya kalle shi yace Ahmad Kai da kake fari Kal jinin Larabawa Kuma a gidan uban wa kake shafa wannan Man,sannan ce maka aka Yi Habiba karamin company ne? Mummy Tace Allah ya shirya min kai,Baki ya turo tare da gyara Ass down dinsa da yayi da wani Creazy jean. Wata Yar kyakyawar jar mota ce Honda tayi parking a bakin wani Restaurant,Yar kyakyawar Budurwar ta fito Hannunta dauke da Handkerchief tana goge zufa, Hannayenta ta Shiga tafawa tana Waka Sannu da Zuwa.....Sannu....da zuwa kekashashe na,Oyoyo Dan Kedararre na.....Oyoyo Karmashashe na,Barka da dawowa Dan tsomalalle na,My Karmash I miss you,Wani saurayi ne matashi mugun siriri wuyansa kamar murkin laima,Kugunsa Kamar zai tsinke,Baki ne wuluk Kamar Iska zata dauke shi Haka ya fito daga jar motarsa Yana wani basarwa a dole babban yaro,Bakinsa ya Bude da Niyyar magana Yan hakoransa manya na gaba Guda hudu Suka yo waje,Yana kallon Budurwar yace naga Alama Baki da tarbiyya,Kamar Ni saurayinki Ina sonki kina so na Amma kina ci min Fuska,glass dinsa ya zare a Fuskarsa ya kalle ta sama da kasa yace Yar talakawa Dake matsiyaciya ki kalle Ni kina wani ce min Oyoyo Karmashashenki? Baki da Manner? An fada Miki badan so ba Zan iya tsayawa da Yar matsiyata irinki? Ki kalle Ni nafi karfinki ta ko Ina,Yar budurwar kyakyawar gaske fara Tace Kayi Hakuri Wasa nake maka wallahi badan naci fuskarka na fada ba,Tsawa ya daka Mata yace dalla ja can dama iyayenki Basu Miki tarbiyya ba,Baki da hankali dai,Ran Budurwar ya baci tace kaga Malam na maka tauna na maka hadiya baka gani ba,to naji bani da tarbiyyar sai kace Iyayenka suzo su Yi min,daga na maka Wasa Kai baka San wasan masoya ba,wannan ne wasan a gidan uban wa ya Zama Wasa? Nan take Budurwar ta bashi amsa a gidan Ubanka Kamalu,Baki Bude ya kalle ta yace Aamna a gidan wa kika ce? Wacce aka Kira da Aamna ta sake cewa a gidan Ubanka nace Kamalu,Kamalu ransa ya dugunzuma yace it's over between me and you,bani ba ke,Aamna Tace ae naji Nima bani ba Kai tsotsatsen banza,me zanci da Kai dama idan anyi auren ma Banda kashinka ya dinga suka na me zanyi,Dana kwanta a jikinka gwara na hau katifar fasasun kwalaba,Kuma da na aureka ka min kiss da bakinka me hakora Kamar kacar Keke gwara na tsotsi Kusa me tsatsa,Yace irin na Ubanki ne ai hakoran,naji ta furta tare da koma cikin Restaurant taci gaba da aikinta. Wajen masu girkin taje ta faki idonsu ta saci yankan nama Uku ta watsa a Jakarta ta fito ta baya can ta cinye Naman sannan ta dawo ciki ta Iske Fried rice an Gama an kaiwa wani yaci ya bar Rabi kadan ma ya ci,Aamna da sauri tazo Wajensa Tace Alhaji ka Gama Zan gyara wajen 2pm yanzu resturant zai cika,kafin yayi magana ta sunkuce abincin ta dauke Masa lemon da ko budewa baiyi ba ta Sha kwana tayi ciki,Alhaji ya saki Baki Yana cewa ke ke ke ban Gama ba Amma Ina Aamna tuni Taki ma kula shi,tana zuwa Tace Alhaji ya koshi ta zauna ta lashe abincin ta Balle lemon ta shanye sannan ta fito fes da ita da mamakinta sai taga Alhajin Bai tafi ba,da sauri ta koma Wajensa Tace Alhaji wani abincin Za'a kawo maka ne? Alhaji ya kalleta yace ke Amma wacce iri ce bance na koshi ba kin dauke abinci lemon ma Dan wulakanci ko Bude shi banyi ba kin dauke Ina ta kiranka bakya ji? Aamna Tace eyya Allah sarki kayi Hakuri matsalar kunne gareni banji ba Kuma gashi na zuba komai cikin shara bare na dawo maka da shi,Harara ya balla Mata tare da zube wani kudin yace kawo min wani abincin,da murna ta dauka dama Bata koshi ba,taje ta hadowa Alhaji duk abinda ya bukata,wata white rice with salat ga kwai da kaza,ga lemo,Aamna tunda taga Haka take ta faman zaga wajen da mopper a Hannunta Wai a dole gyara takeyi,tana ta faman goge goge a saitin Alhaji,Alhaji yace ke kin dameni da goge goge ga customers can sunzo kije Mana Haba wannan wacce irin Maaikaciya aka dauka Haka idan bakya so sai na daina zuwa cin abinci a wajenku aikin banza,Aamna tayi murmushi tare da gyara pcap dinta Tace afwan Alhaji ta juya ta tafi Amma sai ta labe a bayan wani lungu daga ciki tana ta kallon Alhaji tana so yayi ya Gama ta samu rabonta,Siyama ce kawarta taje ta sallami wasu customers din Aamna tana labe tana zalama wajen Alhaji,Siyama tayi Dariya tare da kallon Aamna tana labe labe Tace Allah ya shirye ki,Alhaji kadan yaci ya bar komai ya tafi kafin ya Gama fita tuni Aamna ta kwashe komai tayi ciki,Nan ma ta zauna ta cinye ta koshi sannan Tace saura na dare kafin na tafi gida,dole na dinga kiba Ina yin kyau,Aiki a restaurant ai Dadi gare shi ko ba komai Zan cika tumbi na. Dattijo ne fari me gemu sosai Wanda shi kanshi gemun ka kalla kasan Dattijon ya tsufa domin yayi fari,da gudu gudu sauri sauri ya shigo gidansa inda yake wani mugun Rubabben gida,Gida ne na Haya Kuma gidan Talauci,da gani ba sai an fada maka ba Dattijon Talauci ya Gama da shi,cikin Gida ya Fado Yana masifa tare da furta me zangani Aishatu?me zangani yau,wacce ya Kira da Aishatu ta kalle shi shekeke tare da balla Masa Harara Tace mene? Gashi can kina karar min da kudi,kina min asarar Duniya da Almubanzanranta,yanzu ki duba sabo da Allah tunda na taho Ina kallon kwalabati kumfar Omo tana ta bin ruwa tana ficewa Ful...ful,Yanzu a zamanin Nan kumfa ka gani a kwata kasan kudinka ake kashewa,kina ta kashe min kudi kina abinda kika ga dama,Ga jarabar karar da Ashana kiyi ta kyastata sai ta Kare,Takaici na yanda kike wanki ko wanke wanke sai asarar Omon bala'i,to wallahi da sake baza ta yuwu ba,kullum Ina fama a hanyar sakateriya wajen Dan aiki na Wanda masinja ne ni nayi retired Ina nemowa Ana wulakantawa bazai yuwu ba,Daga yau ko mangyada ne za a zuba a abinci to kowa cokali Daya Daya babu kari aikin banza,Wata buta yasa kafa tare da yin fatali da ita Yana zare Ido yace Ina Aamna sakarai da Sweety Zuhra?Aishatu banza tayi Masa ta ci gaba da aikinta,yace Aamna har yau ba labarin Mijin Aure? Aishatu tayi Shuru,Dattijon yace na gaji da yahudanci wallahi da nasan Haka ne Aamna ko secondary baza tayi ba,Dan fa Kawai Ina tunawa Amana ce a wajen mu, Nima ban San ya akayi basirata ta toshe na biya Mata har tayi wani HND sabo da asara,ai karatun mace Bai da amfani,amfanin mace aure da girki tayi ta zazzago Haihuwa,yarinya ta Zama bayahudiya abinda taga Dama shi takeyi,Nima jarabata ce tasa Rana tsaka Ina Kauye tare daku cikin sutura na dawo damu Birni na Kama haya,da Muna Kauye da tuni hankalinmu kwance,da duk wannan karyar Bamu shige ta ba,Aishatu Tace ai sai Dana fada maka kaki ji Aamna tana secondary a Kauye Ss3 ka kwaso mu Muka dawo birni gashi yanzu ta waye Taki aure muna ta ciyar da ita a banza ,wallahi baza ta Sabu ba,gidana ya koma na yahudu bazai yuwu ba,ai Birni na dawo ne Kawai Dan na samu sana'a me kyau to gashi hakan Bata samu ba,Dan pension Nawa ma baya Isa Nawa yake Ina abin,kullum sai talauci ne ke karuwa,birni kwai masifa Ni tunda nazo banga wayewar ba,ban wani waye ba,Aishatu Tace yo shekarar mu Nawa a Birnin kwata kwata shekara hudu fa rak Ina wani wayewa Aamna da Zuhra ne Kawai Suka Dan waye Dake su Yara ne,Dattijon yace ke tafi can Aamna Ina ta waye ai gwara Zuhra,Amma Aamna kina gani magana ma Bata iya ba ta Kauye takeyi duk abinda yazo bakinta dankarawa mutum takeyi Dan tayi makaranta ne ma take Dan canjawa,ni dai na fada Miki a kiyaye asarar Omo yawwa ya furta tare da ficewa falau falau da rigarsa doguwa ta wani tsohon yadi dinkin wani falkeke komai ta Masa yawa Kuka Aamna ta saki Wiwi tana Hawaye tare da nuna Budurwar da Hannu tana masifa tare da Furta In Allah yayarda Shedan sai ya sumbace ki,Shedan sai yayi kissing dinki,muguwa,Azzaluma, maciya Amana,Baza kiga dai dai a rayuwarki ba Saratu,Saratu anyi asarar Duniya,An Sarai asarar duniya,Shegiya wacce Shedan yayi Mata fitsari a Kai, Wacce ake Kira da Saratu murmushi ta saki tare da karkada key din motarta Tace nafi karfinki Kina talaka kucaka me Deeni zaiyi dake duk kudinsu,ke wawiya ce Baki da hankali da har kina me siyar da Abinci a Restaurant kike tunanin Dangidan Dan Majalisar jaha Deeni zai so ki,ai ko kansila Aamna bazai tayaki ba,ganinki kyakyawa Fara Wai zai sa samari su soki? Kinyi kuskure Aamna,ai yanzu samari sai masu kudi suke Nema gidan da Suka gaji arziki,ai yanzu sai kana da kudi ake rayuwa da kai,ke Dan Dakikiya ce tunaninki kyau Yana sawa a so mutum? Dan kina da kyau har Shishigi kike Yi to ki sani samari sai dai su yaudare ki Amma yanzu duk munin masu kudi Haka ake aure su,Talaka ma Bai son Auren talaka bare irin su Deeni masu kudi,Ina Baki shawara ki fita Harkar Deeni ba ajinki bane. Aamna tana tsaye sanye da Jean skert Blue da rigarta T-shirt fara tas me Rubutu Red a Gaban Rigar An saka A&G Food Joint,ta Sanya pcap Red takalminta ma Red,ba karya Aamna karshe ce a kyau,haskenta me kyau ba fari Kal Kal ba Amma fara Ce dai ba Wanda ya Isa yace wankan tarwada ce,dole dai farar ce,Gashinta har gadon baya Baki wuluk,Ga Zararan gashin Ido tare da kwantaccen Gashinta dake goshinta,Girarta wuluk me yawa,Hancinta me kyau bai cika tsayi ba,Fuskarta ba doguwa ba baza Kuma ace Round face ba,Dan Bakinta gwanin Sha'awa Karami with pink lips,Gata doguwa Amma ba can ba,ga Uban Hips kamar ita tayi kanta komai nata me kyau,hakoranta kanana farare tas,Idonta dara dara, Mashaallah,Aamna baza ta wuce 24years ba,Haka kanwarta ma Zuhra kyakyawa ce Amma ita chocolate ce kamarsu Daya da Baba. Murmushin takaici Aamna tayi Tace ai gaki Nan da Muni yayi Miki yawa Deeni zai kwasa ki cinye Deeni please ta juya tare da komawa Kan bakin aikinta wurin masu siyen abinci,ita kuwa Saratu Tsaki ta ja tare da Bude dalelleliyar motarta baka ta Shiga sannan ta fisgeta a Tamanin. Sai 11pm ta tashi a Aiki ta saka After dress dinta me Dan kyau tare da rataya handbag dinta tayiwa abokan aikinta Sallama ta wuce gida,Napep ta Shiga zuwa gida,can cikin wata Unguwa ta masu rangwamen gata aka sauke ta a Kofar gidansu na Bulon siminti Amma ka rantse kango ne baiyi Kalar gida bane,da Sallama ta Shiga da kyar aka samu aka amsa mata,Mama Wato Aishatu ta Iske tana Daura Net a dakin babansu Tace Mama na dawo,Tsaki dattijuwar ta ja Tace to sai me,idan da sabo ta Riga da ta Saba,Baba ta kalla Yana daki Tace Sannu Baba,da kyar ya amsa,Kai Kawai ta girgiza ta wuce kitchen Nan ta Iske abincinta an zuba Mata Amma an barshi a Bude baza a iya rufe Mata ba,ta Saba Kawai ta dauka tare da Fitowa sai ga Daya matar gidan tunda dama gidan Haya ne,mutum Uku ne a ciki ko wacce mata da dakinta biyu da kitchen Amma toilet Guda Daya ce du,Gaisawa Suka Yi Tace Maman Zeenat ya gida,Tace lfy Alhmdllh da fara'a, dakinsu ta wuce ta Iske kanwarta Zuhra tana kwance a saman katifarsu tana chatting da saurayinta Wanda zata aura Nan da wata daya. Murmushi Aamna tayi Tace Zuhra Ana Shan love, Murmushi Zuhra tayi tana juyi Tace Aunty Aamna an barki a baya wallahi,Soyayya tayi a rayuwa,Adam ne ke kashe Ni da zafafan kalamansa masu sweet,Dariya Aamna tayi Tace na tayaki murna kanwata ke kin samu Miji Ni kuwa kin barni nice Kuma yayarki gashi Mama da Baba sun tsaneni akan ban kawo musu Wanda Zan Aura ba,Hawaye ne ya silalowa Aamna Tace why me naaa?why Me Zuhra? What have I done wrong? Tausayin Yayarta ya Kama Zuhra Tace kiyi hakuri Aunty Inshaallah kema Zaki samu miji very soon,Kuma Inshaallah su Mama zasu hakura su daina fushi da ke. Kai Aamna ta girgiza Tace Zuhra Ni bazan iya auren Wanda bana so ba,da Zan Iya Dana fitar da ko ma waye Dan na farantawa Iyayena Rai Amma idan nayi bazan iya yiwa Wanda bana so Biyayya ba,Illar Hausawa kenan Allah Bai kawo maka Miji ba a takura maka karshe har sai ka auri Wanda baka so,baza ka Dade ba za a sakeka,ko Kuma kullum ku Kare a fada da sasanci,bana fata inyi aure na fito Zuhra,Nafi so ko wa Zan Aura ace Ina sonsa sosai sabo da shine kadai Zan iya Masa Biyayya,kin San halina Ina da taurin Kai,Kuma Ni ba a iya tankwara ni,So shi kadai ne zai sa nayi Biyayya,Kin San idan bana son mutum wallahi zanci ubansa ne,Amma su Mama sun kasa fahimtata,Zuhra Tace ai ke matsalarki kenan Aunty akwai saurin fushi ga rashin barin ko ta kwana,aure Kuma sai Hakuri,Hakuri na Kawai na auri Wanda nake so ko jibga ta zai nayi kullum Zan zauna Kuma bazan ji Haushin kowa ba. Mama ce ta fado dakin Tace Ina Jin duk abinda kuke cewa,ke Zuhra ki daina saurarar marar hankali,ai yanzu ba auren kauna akeyi ba dubawa akeyi aikin mutum ake dubawa me yake samu,zai Iya rike ki, ci da Sha shi ake kallo ayi aure,ke soyayya Zaki aura Zaki ci ubanki kuwa a hannun maza,kika sake sai Namiji ya sa Miki ciwon zuciya,Aamna tace kinji ko Mama bakwa duba Iliminsa da Addininsa Kawai kudi kuke dubawa ayi aure,Baba Yana ji ya tsomo Baki daga dakinsa yace Ni ki tambaya Sanda na auri Uwarku ban taba ganinta ba Haka itama Bata taba ganina ba Kuma gashi Muna tare har mun haife ku,wallahi Aamna kika sake Watarana sai na koreki daga gidana,badan ma kece kike rage min nauyin gida ba da tuni nayi Miki auren Sadaka Kuma wallah Matukar Naga dama auren Sadaka Zan bada ke. To Baba kuyi Addua Allah ya kawo min na gari,Kuma da kuke cewa Baku ga juna ba aka muku aure ai ku a zamanin da ne Kuma asiri akeyi Ana kafe matar ta zauna dole,Salati Baba ya saki yace Ni Zaki hada da shirka Ina Dan Izala? Shuru Aamna tayi,Mama Tace mayaudariyar banza,kin Yaudari Affan kin Kore shi kince kin Kama shi da cin Amanarki Yana kula Mata,Hassan Kuma kince Dan karya ne,Deeni ma yaro me kudi yanzu kince ya yaudareki ya koma wajen Saratu kawarki Yar gidan Alhaji Sani Likita, yanzu ga Kamalu kin ci Masa mutunci ya gudu shima,Jollof din shinkafata wacce ta rigada tayi sanyi ta bushe ita Aamna ke ci su Mama suna ta mata fada har ta Gama,ta cire kayan jikinta gaba Daya ta wanke tare da shanya su a daren,Wanka tayi da ruwan zafi tare da Shirin bacci ta kwanta ta bar Zuhra tana chatting da masoyinta . Dalleliyar mota ce ta gaske wacce a kalla ta miliyoyi ce,ta danno cikin wani katafaren gida na Gagara,Gida ne Wanda ya amsa sunansa,Babu abinda babu a ciki,motoci ne zasu Kai takwas a gidan Wanda suka gaji da haduwa ga tsada,farare Guda hudu a jere bangare daban Haka ga wasu kaloli daban,Machine ne Guda Uku kala daban daban masu tsada harda Keke na masu kudi su biyu,Gidan Ya gaji da tsaruwa ga flowers ko ina,idan ka Shiga gidan baza ka so Fitowa ba,Kalar gate din ma na daban ne,ba ko Ina ake ganin Irinsa ba a kasar Haka furniture sai dai ko gidajen Gomnoni, Wani Matashi ne ya Bude motar baka Daya shigo da ita,Fitowa yayi da kyar Wow wani Fari ne tas kamar Balarabe har wani ja yake kamar ka taba shi jini ya fito,dogo ne Amma ba can ba,gashi shi ba Mai kiba ba baza ace Kuma siriri ba,Fuskarsa me dauke da hancinsa zarkadede ba irin me tsayi da yawa ba,Sumar Kansa baka wuluk dauke da wani mayen Aski irin na Yan duniya,an kwashe gefe da gefe an yanki wani waje siriri an Kona shi tare da maida shi Fari tas,Sajensa me kyau luf luf me dauke da Dan gemunsa cas,idanunsa Dara Dara farare tas suna wani lumshewa,kowa ya kalli wannan matashi yasan ya Gama gajiya da haduwa,Naira da Hutu sun zauna a jikinsa,Jikinsa na maza Wanda suka amsa sunansu maza,sanye yake cikin wani Crazy Jean me tsada gaba Daya wandon a farfashe yake ruwan toka,da wata T-shirt me Rabinta Fari Rabi Kuma Blue,Takalminsa da agogonsa masu tsada,Yatsansa sanye da zoben Azurfa,da kyar yake takawa ga takama ga aji Amma Kuma Yana tangadi da Alama yayi shaye shaye ya gaji,Yana dafa bango Yana tangadi AHMAD kenan a Haka har ya Isa katafaren palonsa tare da fadawa saman kujera ko Takalminsa Bai cire ba ya kwanta Haka Yana sambatun maye shi kadai har bacci ya kwashe shi. Tunda ya fara bacci gab da Magriba Bai tashi ba sai da gari ya waye sannan Rana da hasken gari yasa ya Bude lumsassun idanuwansa a hankali,Kara ya saki kadan Jin jikinsa a gajiye,da kyar ya iya tashi a hankali ya haura samansa Direct toilet ya shige ya Dade Yana wanka dake akwai tsafta,Bayan ya fito daure da Towel jikin mudubinsa ya nufa turaruka ne da mayuka na maza masu tsadar gaske,Lotion me kamshi ya shafa tare da fesa Body Spray a jikinsa sannan ya dakko sabuwar jallabiya me tsadar gaske fara sal Amma ta Dan tsangale Masa baya sa wacce zata Kai Masa har kafa sabo da Damunsa takeyi,Turaruka ya fesa sannan ya dauki wayarsa me tsada Yana latsawa,a hankali cikin tafiyarsa ta Isa da takama ya sakko kasa ya Bude kofa ya fito sanye da wani flat shoe fari sal shima Yana tafiya a hankali ya bi ta wani corido gaskiya gidan Nan ya Gama haduwa tiles din kasan gidan na tsakar gida fari da Baki ne ko Ina sheki yake Yi da walwali,Me Gadinsa ya hango Yana karasa gyara gidan Yana kida da bakinsa Yana rawa Yana aikinsa,Ya Dade a tsaye Yana kallonsa,Abin Dariya ya bashi mutum shi kadai Yana kida Yana Waka Kuma Yana rawa duk shi Daya, murmushi ya saki kadan tare da girgiza Kansa ya juya ya koma inda ya fito. Har yayi nisa sai ya dawo ya Kira me Gadi Musa,da sauri Musa ya dago yace Oga tare da takowa da gudu yazo gabansa yace Ina Peter banga ya gyara ciki ba Sannan ba Abinci,Oga ai Peter ya tafi kasuwa yace abincinka Yana kitchen yace sauri yake yi,Ni gaskiya Oga Ina tunanin yafi a dakko mace yar Aiki wacce zata na maka girki da gyara maka ciki tunda Ni Ina kula da Campun,Ogan yace ba Campun ake cewa ba Musa Compound,Kuma Ni bana bukatar mace yar aiki,Ni bana son mace ta rabe ni,duk abinda zai sa na hadu da mace bana kauna,Musa ya zaro Ido yace Oga Mata sune Jin dadin duniya duk wata nutsuwa da Namiji zai samu tana jikin mace,Baki Ogan ya tabe yace Allah ko? A wajen wawaye ba,gwara naci abincin Gardi akan naci na mace,Karka sake furta kalmar Nan mace a gaba na,idan ba Haka ba Kora ce tukucinka,Musa yace an Gama,Kayi Hakuri Ranka ya Dade Namiji gwara nace Namiji,macen banza Banda Mum dinka Oga,Baki ya tabe ya juya da Gadara ya wuce,Abincin Peter ya Bude yaga Bai Masa ba,da Kansa ya shirya Girkinsa da lafiyayyen tea dinsa ya karya sannan ya dauki key din mota yayi waje,Yau da wata mota Ruwan toka ya fita kirar Benz. Washe gari Aamna wanka tayi tare da Shiryawa tsaf cikin kayanta Riga da wando sunsha wanki da guga,After Dress ta Dora a Kai tare da yafa Mayafi,ba Wanda ya kalle ta a cikin Iyayenta Balle Tace Za'a Bata wani abinci dama yanzu basa kulata,ko ta gaishe su basa amsawa,Sallama ta musu ta tafi,Mama Tace yarinyar banza ace tasan Burin mu Bai wuce mu Aurar da su ba Amma Taki fitar da Miji abin kunya kanwa zata Riga Yaya aure duk ta tsufa a gida Allah wadaran Dan Riko,shekara ashirin da Hudu ai ba Wasa bane,mu duk da a cikin birni muke muna Nan da akidar mu ta Iyaye da kakanni na auren wuri Amma kash Yaran namu musamman Aamna ta Gama watsa Mana kasa a Ido,marikinta Bai da Buri sai na Aurar da su,ai mutuncin ya mace gidan Miji Amma ba komai Aamna wahala da azaba ma Sai ta sa kin fito Mana da Miji,kin daina Jin dadin gidan Nan kwata kwata,yanzu Zan canja Taku wajen gana Miki azaba duk da Kamar mahaifiyarki ce Ni dole wahala tasa ki fitar da Miji,Zuhra kuwa Shiryawa tayi tuni tayi Kari me kyau Ana ta nuna Mata gata da kauna ta tafi makarantar Boko Wato Secondary school sabo da sun kusa yin candy. Ahmad Bai tsaya ko Ina ba sai gidan Mashkoor inda Suka Fi Zama suna shaye shaye a gidan,can ya Iske abokansu su Biyar Mashkoor, Abdul Tawaga,Jibril Jibson,Bashir Bash, Mubarak Brown sai shi Oga Mai gayya me Aiki Ahmad King,Yana zuwa ya Iske su a zaune a Garden suna zaune a kujeru ga karamin Table an zube kayan maye na shaye shaye kwayoyi da giya iri iri ga Sigari taba da Wiwi,Kirari suke Masa Suna The King...Our King,shi Kuma Yana uban Gadara Abdul Tawaga ya Daga Masa kujerarsa ta tsakiya Kuma kujerarsa ta mulki ya zauna tare da Balle kwalabar Giya ya Shiga tiltila Kamar ya samu ruwa,Bash ya kunna Wiwi Yana zuka ga wasu kwayoyi Daya hada a cikin wani ruwan giya Yana korawa Yana tiltilo hayaki ta Hanci ta Baki cikin kwarewa,Tawaga Yana Aswaki Yana cijewa Yana karkace Baki yace Our King....Sweet Boy,The Handsome King,Fresh Boy, shi kuwa King ya kalli Kansa yace Na me....Na me My Guy,Look at my skin color.... Mubaraq Brown yace Handsome King,Mashkoor Yana wani tangadi a zaune yace Our King ka huta baka hura hayaki sai ruwa Kawai kake bulbula sai kwaya,King ya wani girgiza Kai alamar ya fara daukan chaji shima yace,Hayaki sai dai na shaki na Titi My Guy, Mashkoor yace Look King akwai wata yarinya tayi Fuck Up,the Girl done Mess up man, Wai Ni Ina sonta Tace Banda hankali wani yaro Rabiu Yana Nan malamin makarantar Islamiyya ya kwace min ita,King Yana lumshe Ido duk ya fita a hayyacinsa ya karkace bakinsa gefe Daya irin na Yan shaye shaye cikin kakkausar da mayen muryarsa yace She must Collect,Dole ta karbi Certificate na abinda ta aikata,Na yarje muku kuci mamanta,shi Kuma Yaron za a tare shi dole mu bashi Sample,Sumarsa me laushi ya yamutsa,yace guys gobe Mommy da Dad zasu shugo garin Nan Karku zo gida na sai bayan sun tafi,Abdul yace Confirm,No wahala,Jibril Jibson ya Mike Yana tangal tangal yace ya za ayi ace baza mu zo gidan King ba,The sweet Boy,Cikin zafi da daga Murya King Ahmad yace hey What's up man Ina magana kana magana kana hauka ne? I'm sorry cewar Jibson ya Fadi a kasa Yana mayensa,da ganinsu kasan talakawa ne Ahmad shine me kudin shike musu komai,Haka Mashkoor Yana da kudi shima Amma ba Wani da yawa ba,Sai Abinda Ahmad yace shine King dinsu,duk wani rashin mutunci da sukeyi a gari shine yake daure musu gindi sai da sa hannunsa akeyi,Ba Wanda ya Isa ya nuna su da yatsa,Dai Dai ne Basu San da zamansu ba musamman Ahmad King din Wanda ya fita daban sabo da Naira da hutu,suturarsa Kawai abin kallo ce,Dukkansu baza su wuce 30years ba zuwa 34years,Ahmad 34yrs yake cif. Washe gari da Yamma su Mashkoor da abokansa gaba dayansu har King din nasu Ahmad machine sababbi suka hau kowa da nasa Kuma duk King ne ya Siya musu kowa da nasa King shine a gaba suna binsa a baya sun kure Masa gudu sun biyo Hanya duk Wanda Bai matsa ba sai dai su bige shi ba ruwansu,sabo da an sansu Ana ganinsu ake kaucewa,Can layin da Islamiyayyar take suka tsaya Suka Parker machinansu,King shine kadai ya zauna a saman nasa suna ta Masa Kirari suna Our King,Fresh Boy,Sweet Boy,shi Kuma Yana ji da Kansa,Suna Haka sai ga malamin Islamiyya ya taho zai wuce matashi da shi Yana tafiya cikin nutsuwa Baki da shi,Tare shi Mashkoor yayi tare da cewa Yawwa ga dan Iska ya Furta tare da tallafe Masa keya,King ya Mike cikin maye yace kana gaba na kana tsaye,Robar Lemo Wanda ciki hadin kwaya ne a ciki Yana Sha ya daga ya tsiyaya wa malamin Islamiyya a kansa,Nan suka rufe shi da duka Wai yayiwa Sarkinsu magana a tsaye,Wata Mahaukaciyar mota ce me kyau da tsada ta taho a hankali,Mommy da Yar Autarta Humaira sai Daddy Mijinta a baya gaba Kuma Kanin Ahmad ne Saddiq da matarsa Mufida a Gaban mota suna tafiya, Saddeeq shi ke tuka motar,Daddy yace ai Kinga Ahmad din ma gashi Nan da Yan Iskan abokansa,na gaji da zuwa Kaduna akan Yaron Nan wallahi,Na rasa wannan masifa data sameni,Kinga Ni yanda suke dukan wani,Kanwar su Humaira Tace ga Yaya can da kayan maye a hannunsa, Saddiq ya tabe Baki tare da cewa kalli Askinsa Ana ganinsa anga Dan Iska,Mufida matar yayan Tace kuyi Masa Addua Kawai. A wajen Suka Yi parking sai tsawar Daddy dinsa yaji a Kansa Ahmad Mene Haka? Baka da hankali ne,duk suna mota ba Wanda ya fito sai Mummy da Daddy,Daddy ya tashi malamin makaranta Wanda ya ci duka da gudu ya arce Yaron,Su Mashkoor suka kame a Gaban Daddy tare da Sara Masa kamar suna Gaban wani Soja,Zaga Daddy da Mummy suka shiga Yi suna musu Sannu da zuwa Wai Nan murna ce da girmama Iyayen Ogansu,Bash kuzo mu Basu kariya Guys ba Wanda ya Isa ya daga Musu yatsa a Birnin Kaduna kaf. Tsaki Daddy ya ja Yana Jin yanda suke wa Ahmad Kirari,Wandonsa ya kalla wani shegen crazy an Masa daga daga,Askinsa ya kalla yace kalli yanda ka maida kanka Ahmad, Dariya ya Shiga Yi ta mahaukatan Yan maye,Mommy Tace Ahmad Dina meke damunka muje gidan da kake,Daddy yace shiga mota mu tafi,Wani fareti ya shiga Yi a Gaban Daddy Yana dariya cike da maye Yana karkace Baki yace No...no Ni a bike Dina zanzo kasan Ina Jin dadin bike Dina Kawai kuje zanzo daga baya,Tsawa Daddy ya daka Masa shiga muje,Amma ko a jikinsa sai ma Dariya da ya Shiga kyakyatawa irin ta basawa Yana kallon Daddy din da Mommy,Dole Haka Suka shiga mota Suka tafi shi Kuma shi da Abokansa suka take musu baya a machine suna tukin ganganci Dan Ahmad harda dage kafa Daya ya daura ta can sama Yana tuki da kafa Daya,Har katafaren gidansa Suka shiga sannan abokan daga bakin Gate Suka tafi gida abinsu shi Kuma yayi Horn me Gadi ya Bude Musu Gate,Bayan sun Shiga Suka firfito da akwatunansu,Wani handkerchief ya daura a wuyansa ya tsaya a Gaban Mommy Dinsa Yana zagata cike da maye Yana cewa Mummy...Mummy....Momma....You are looking Good ya furta tare da rungumeta yace Ina sonki Mummy,rokonsa ta fara Tace Dan Allah ka nutsu Ahmad,Da karaji Daddy yace Mene ne kike rokonsa, why are you Begging him,Dan ubansa tunda bashi da hankali sai yayi ai,Why...why...Daddy Ni dama fa ba tun yau ba nasan baka kaunata,musamman idan ka saka wannan farin Glass din naka sai ka dinga kwana idan anyi Nan sai kayi can,Ido Daddy ya zaro Yana kallon rashin kunyar Ahmad,Kaninsa Sadeeq ne yace ka canja wallahi Yaya,Cikin karaji ya tasowa Saddeeq Yana ce Masa Kai dalla gafara Ina yayanka zaka min fada,ko Dan kaga munyi Kai Daya Ina da gemu kana da gemu shine zaka rainani Kai wuyanka ya Isa yanka ko,Ka dai gyara halinka,Tafiya yayi zai Mari Saddeeq Mummy ta rike shi tana rokarsa yayi Hakuri, Humaira ya riko tare da Rungume ta yace kanwata kin girma,ya school? Tana Dariya Tace nayi Candy Yaya,Wow ya Furta tare da dagata sama ya ajiyeta suna Dariya,Matar Kaninsa ya kalla Mufida nutsatsiya kyakyawa yace matar mu ya gida fatan wannan shashashan yana kula Dake? Dariya Mufida tayi Tace sosai ma,yace Good muje ciki matar mu ke kadai ce tawa a gidan Nan,kishi ya Kama Saddeeq ganin Ahmad Yana shaye shaye tunaninsa har Mata yake bi sai kishi ya kamashi yace kaje kayi aure wannan matata ce Ni Daya ka daina cewa matarmu yawwa,Stupid Boy Kawai Ahmad ya furta Suka jera da Mufida suna Hira duk da a maye yake Amma Yama Saba Bai fiye buguwa da yawa ba, Sadeeq da Sauri yazo ya shiga tsakiyarsu ya rike Hannun matarsa ya janye ta da karfi,Baki Ahmad ya tabe ya Rungume Humaira Suka Yi ciki. Bayan sun huta sunci abinci Daddy yace da dare Yana neman kowa za ayi Meeting zasu fadawa Ahmad dalilin zuwansu yanzu ma again, Har dare yayi Ana jiran Ahmad Amma tuni ya bar gidan Yana can suna shaye shaye har 1am Bai dawo ba sai kowa ya hakura yayi bacci,Da safe ma Ana ta jiransa har sun karya Shuru Bai dawo ba,can sai gashi a bige ya Fado palon ya tafi taga taga zai Fadi sai ya cije ya Dage Yana bude Ido da kyar Yana Rufewa ya fada saman kujera shirim kusa da Daddy yace An tashi lfy? Ina....Ji...ji..jinku.....m....me.....yaaaaaa....ya...kawo ku Kuma yanzu Kun wani sake dawo min gida...na tuna ance jiya za ayi meeting yanzu gani Ina da abin Yi ku Fadi meke tafe daku har zuwa gidana? Daddy ya zaro Ido yace au gidan ka ne ma? Gidana kace gidanka? Yace gida nane Mana Kai ai Temporary Owner ne Nan gaba mutuwa zakayi naci gado,Ran Daddy ya baci yace gidan Nawa? ni da gidan gida ka gaje min gida?aikin uban me kake Yi? Kaki nutsuwa,Mummy Tace Ahmad Dan Allah ka tsaya ka nutsu kaji abinda ya kawo mu,Ina jinku Mana ku fada,Kaninsa Sadeeq ya tabe Baki,Humaira Tace Addua zaku Masa please,Ita Mufida ita tunda auro ta akayi Bata cikin wacce zata Shiga matsalar Family tana bedroom. Daddy yace kana ji na Ahmad? Yace Yeah,yace so nake ka bar Nan ka dawo Lagos kazo mu koma inda nake da Zama can Lagos Ina so Zan maka Visa mu tafi London gaba Dayan mu,akwai Company na Dake can kayi Handling dinsa kayi Aiki a can ka dogara da kanka,kullum sai dai na cika maka account da kudi kana kashewa a banza,ya kace?Ahmad yayi Dariya yace kasan amsata Mana Daddy Ni bazan je ba wata kasa da zanje Kuma Ni bana son Lagos a Nan gidana Zan zauna a Nan Zan mutu,Daddy yace to gidanka ne? Ni da gida na,Mummy Tace Dan Allah Ahmad ka bimu mu tafi kaga London ko Turkysh ko Kuma a Nan kasar Nigeria sai kayi Aiki an baka company kyauta ka dogara da kanka Kaine fa babban Danmu Kai ya kamata ace ka nutsu,kalli kaninka ya rike nasa a Lagos Yana aikinsa gashi da Degree da Masters Kai kuwa Degree daya ma da kyar muka samu ka karasa a Russia,Ahmad yace kunga fa Ni ba inda zanje Kawai ku daina Bata bakinku mutanen da basa son bakar fata ku Kun damu da su kuje kuyi harkarku,kuyi rayuwarku nima nayi tawa,yawwa kunji ba inda zanje ya tashi Yana tangadi ya haura sama,ya barsu a Nan cike da Alajabi yafi karfinsu.Daddy bakin ciki ya Kama shi ya juya kalli Mommy tare da galla Mata Harara yace Kinga danki ko kin ga abinda kika haifa ko? Mummy Tace au da nane ma Ni Daya? Daga Nan suka fara cacar Baki. Aamna ce ta fito tsakar gida sanye da wani gajeren wando ko gwiwa Bai ba Milk color,da Yar rigarta t-shirt dark Blue,Hannu biyu ta zuba a cikin aljihunta tana tafiya tana yan ga,Cinyoyi da kafafunta lukutaye,Mama ce ta Bude Baki Tace Yau me Zan gani? Aamna kece yau kika Yi wannan shigar ke da bakya so aga jikinki yau me Zan gani na Shiga Uku Kamar Namiji, Malam fito ka gani,Kuma wandon ma na Yan Ball ta saka wani katon buje,Aamna saman bakin rijiyar tsakar Gidan ta zauna daram tare da Harde kafafu,Baba ne ya fito da sauri shima ya Bude baki,yace kwaya kika Sha? Nan fa gidan haya ne ga maza Wanda da matansu,Aamna Fuska ta bata tare da Furta naga Alama a gidan Nan magauta sun min yawa,Magauta sun sani a gaba Ana so aga baya na,to Zan dauki mataki Mama kirji ta dafe Tace Aljanu ne da ke Aamna? Tace Ni yawwa da ace akwai Sigari a kusa ma yau Zan fara zukawa sai anayi ana feso da hayaki ta Hanci da baki sabo da Naga an tsaneni a gidan Nan so ake na lalace to wallahi Zan bi duniya kowa ya huta Matukar ba a daina uzura min ba. AsmaBaffa 10/26/21, 8:51 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK. MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 6-10 Official By AsmaBaffa. PAGE NAKU NE SAMEERAN GAYA FLOWER AUTA AIDA MAMAN TASNIM CHOICE Aamna ce a Resturant dinsu tana hadowa customers abinci tana bin wakar Dake tashi a ciki da manyan speakers sabo da Jin dadin masu cin abinci a wajen,idan kaji uban kida kamar kana club,ai Aamna Bata San Sanda take kada Kai ba tana bin wakar da Baki tana bi layi layi inda masu jiran order suke zaune tana ajiyewa kowa nasa,duk Wanda ya kalleta sai yayi Dariya yanda Bata ji bata gani bilhakki aikinta takeyi tana rawa da kanta,wani babban mutum Bai San Sanda ya saki Dariya ba Amma Aamna ko a jikinta sai ma data soke Wayarta a jikin aljihun skert dinta,wani kida ya dado ta tayi tafi tare da daura Hannayenta biyu a kanta tare da Furta wayyo Baba.... Ai kuwa wasu duk sunyi tunanin kwaya take Sha Kawai sai Dariya akeyi tana Basu nishadi gata kyakyawa ta karshe. Wata Budurwar da saurayinta Tace wannan Yarinyar ba karamar Yar Iska bace ko a jikinta duk mutanen Nan ko kunya babu,Matashin Yana zuba Dariya yace ai shi yasa nake zuwa resturant din Nan,sabo da ita nake zuwa wlh abin Dariya Zaki gani iri iri tana yi,Budurwar kishi ya turnuketa ta kalle shi ta watsa Masa Harara Tace Ni Kuma fa? Allah ya tona maka asiri ka Fadi gaskiya,shi yasa ko yaushe kace muzo Nan munafuki Ashe Dan ita kake zuwa,sai lokacin matashin ya tuna tabargazar da yayi a Gaban Babynsa. Aamna kuwa wani sufa tayi da takalminta a tiles din tana tafiya a Haka Kamar wacce ta hau takalmin Taya Wai duk cikin saurin Aiki ne,Siyama kawarta itama Haka ta shararo da sufarta Hannunta dauke da tire da kayan Abinci Washe gari da Ahmad ya fita Wata hanya Suka samu tare da tare hanyar mota kowa idan yazo sai dai ya juya Inda ya fito,sai da aka kawo Yan Sanda wajen suka dinga fada da Yan Sanda,Bincike Dpo yayi Dan waye? Ai Yana ji an Fadi waye Baban Ahmad a kasar sai ya tsorata yaje har gidan ya samu Babansa tunda ance yazo Yana Kd ma,Bayan sun gaisa Dpo ya Kai karar Ahmad yace mun kyale shi ne sabo da Kai da irin taimako da kake Yi a kasar nan sabo da Haka Dan Allah Ka Jawa danka kunne,Daddy ya Basu Hakuri tare da sanar musu duk irin kangarewar Dansa,Dpo yace sai dai ku dage da Addua Amma a tsawatar Masa Kar mu dauki mataki aga Bamu kyauta ba,Bayan sun tafi Shuru Ahmad Bai dawo ba sai cikin dare Daddy,Mummy da Saddeeq duk suna jiransa sai kuwa gashi ya dawo a make,Daddy ya lullube shi da fada ba ji ba gani,Kaninsa Sadeeq yasa Baki Nan take Ahmad ya shaki kwalar Sadeeq zai Duke shi,Mommy ta rirrike shi tana kuka tana cewa ka Bari Mana Ahmad wayyo na Shiga Uku Ni,Daddy kuwa Mari ya kwadawa Ahmad,Nan take ya dafe kuncinsa Daya da mamaki sai Kuma ya sheke da Mahaukaciyar Dariya Yana Nuna Daddy da yatsa Yana ka mareni akan wannan kanina shi zai ce zai min fada,Daddy yace banza shashasha sai na sake marinka wallahi,Juyawa Ahmad yayi ya haura samansa a fusace,Humaira kanwarsa da Mommy suka bi bayansa suna ta bashi Hakuri suna lallaba shi,Ahmad yace kina gani Mommy marina fa yayi Akan kanina,Ni dama nasan Daddy Baya kauna ta,Bai so aka haife Ni ba gaba daya,Ba Haka bane Ahmad Yana sonka Nima Ina sonka,Yace ai nasan ke kina so na Amma Daddy Baya kauna ta Ni ku tafi ku bani waje Kawai ya dakko kwalabar barasarsa ya shiga korawa,Mummy suka fita sun San halinsa idan yayi Fushi. Ranar da su Mymmy suka kwana Uku da Yamma Ahmad,Mufida matar Saddeeq da Humaira Autarsu suna Garden suna Hira Ahmad Yana ta musu magana irin ta Niggogi irin ta Yan kwaya suna ta dariya, Sadeeq ta sama ya hango su ta window kishin matarsa ya kamashi ya sakko tare da Fitowa Haka ya dinga zaga garden Yana kunci,ya Shiga ya fita ya dawo ya wuce ya sake dawowa,Mufida ta fuskanci wani Abu Tace lafiya dai Baby? Cike da bala'i yace ba lafiya ba ki taso ki kula da mijinki kin zauna kina wani dariyar banza da wofi,Ahmad yace ya zaka dauke ta muna Hira,Hira mukeyi Kai wanne irin yaro ne? Tsaki Saddeeq Yaja ya Fisgi matarsa Suka tafi,Juyawa yayi Suka ci gaba da Hira da Mufida kanwarsa suna ta dariya abinsu,Wayar Humaira ya karba ya juya yace irin wannan waya Haka sis idan kika hadu da irinmu Yan duniya ai sai mu tare Miki Hanya muyi Miki fashin ta,Dariya Suka sake yi Yana ta Dariya ba ji ba gani irin ta Yan kwaya,yace sis yanzu ma Dan na sanki ce ke kanwata ce da su Jibson Zan turo su kwace ta,Dariya Suka sake Yi a tare Humaira ta daki kafadarsa tare da furta Kai Yaya,Kallon Kanwar tasa yayi sosai yace sis you are cute wooo...see your Nose fine nose,kina sa Nikaf fa Kar ki hadu da irin su Brown abokina I swear Kamaki zasu Yi su Sha harka kina kula fa tam,hope Baki kula samari Kar wani yazo ya taba min kanwa Naga kin fara girma abubuwa sun fito Haka, zanzo har Lagos nayi yaki ne idan wani ya Bata min ke, Humaira harda rike ciki sabo da dariya ga kunyar abinda yace,shi kuwa ko a jikinsa Kwanan su Mummy biyar suka fito cikin Shirin tafiya Ahmad Yana binsu a baya Yana ta murna zasu tafi yanzu ma su barshi ya sakata ya Wala,Mummy ta Rungume shi Tace ka Zama mutumin kirki Dana tunda baza ka bimu ba ka kula da kanka,yace to Mummy na, Saddeeq yace wannan ba Wani shiryuwa da zaiyi Nan take Ahmad yayi Kansa da bala'i,Mufida tazo Tace Yi Hakuri kyale shi Yaya King,yace yawwa matar mu ki kula da kanki,Da sauri Saddeeq ya janye matarsa cike da kishi,Ahmad yace wannan wanne irin Dan Uwa ne Haka? Daddy ne ya Kira Driver su wurin Tara yace ya kwace Motocin Dake Hannun Ahmad kaf,Dama Bai damu ba yace tunda Yana da kudin machine ya ishe shi,Daddy kuwa yace tunda baza ka nutsu ba ai Motocin da kudi na ka siya na karbe,Ko a jikin Ahmad yace kuje da ita,Daddy yace dole ma ko baka fada ba,kudi dai Zan na tura maka na kula da kanka sabo da hakki na ne,gida ma kayi ta Zama Amma ka sani ba gidanka bane Nawa ne. Mummy Tace please Ahmad ka daure nasan kana Sallah Amma baka Yi sai Sanda kaga dama ka gyara Sallah ita ce komai awajen musulmi,Ahmad yace sured Mum Zan gyara ki yarda Dani,Nafa sanka Ahmad tun yaushe kake cewa zaka gyara Amma kaki,Ki yarda Mum Inshaallah,nine fa Ahmad dinki,Sunana fa aka kalla aka yo Guarantee trust Bank,Dariya sukayi har Daddy,Yawwa ehem Dad karka manta na tura maka new accnt number Dina Ina bukatar kudi kudina sunyi low,Daddy yace Zan tura ai Ina sane sakaran banza. Ahmad Yana ji suka shiga mota Gate man ya Bude Musu suka tafi Basu bar mota ko Daya a Hannun Ahmad ba aka su Suka kwashe su,Suna tafiya ya dauki waya tare da Kiran Abokansa su zo Iyayensa sun tafi sai murna sukeyi yau suna gidan King. Me Gadi ya kalle shi kawai ya jinjina Kai Amma Ogansa Yana da Hali me kyau Kawai matsalarsa shaye shaye da Rashin Ibada sosai. Aamna tana cikin Restaurant dinsu tana ta Kai abinci wajen masu ci,sannan Kuma suna Hira da Babbar kawarta Siyama wacce aikinsu Daya,tare suka Yi HND a Poly,Rashin samun Aiki yasa suka nemi Aiki a sabon Restaurant da Maman kawarsu Saratu ta bude sabo da Talaucin da suke fama da shi, Siyama Tace kawata Nima fa Allah ya kusa daga Ni,na manta ban fada Miki ba Nafa fada cikin kogin son Faisal,kwanan nan ma nake so na bashi dama ya turo magabata,Murmushi Aamna tayi Tace wow I'm Happy for you Kawa But Ina ganin Kamar kinyi gaggawa ya kamata ki Bari ku fahimci juna sosai Bai Yi ko 1month da fara zuwa wajenki ba,Karki je garin sauri da matsuwar Aure a samu matsala,Siyama ce ta dakatar da Aamna ta hanyar daga Mata Hannu tare da Bata rai,Tace Ni fa Aamna ban Gane Miki ba,ai sai kisa nayi zargin ko bakya kauna ta kina bakin ciki na samu Miji ke Baki samu, Subhannallahi Siyama Allah ya kiyaye ko wani da musulmi bazan Masa bakin ciki ba bare ke da kike kawata wacce muke kashewa mu rufe tare Allah ya kiyaye min,sabo da Haka Dan Allah gobe a daura aurenki da Faisal ma Bai Dame Ni ba Bai shafe Ni ba,babu abinda Zan tsinta ciki,idan wahala ce ma ke Zaki Sha abarki mu Yan jaje ne. Siyama Tace ai ke dama bakya kaunar Aure bakya so kiyi Kuma bakya kauna wani yayi,gaba kike da Sunnar ma'aiki sabo da ke Kinga Baki da samari idan ma kin samu guduwa suke yi,idan Zaki hakura ki auri kowa kika samu ki hakura yanzu an daina auren Soyayya wa zai Iya rike ka Kawai ake Nema ya zaka ci ka Sha ka rayu inda zaka huta da iyayenka,Faisal Doctor ne matarsa mutuwa tayi wajen haihuwar fari,yaro matashi ga kudi me nake jira ai yanzu ba a jira Yan Secondary ma idan suka samu Miji aure suke Yi,kiwa kanki fada,shekaru tafiya suke Yi mu matane,ko ba komai kar tsufa ba aure har mu zo lokacin Haihuwar mu ya wuce,Aamna Tace Allah Baki Hakuri ayi aure lafiya mu muna Nan daram za muci gaba da Addua Allah Bai manta damu ba Yana sane da mu,Siyama Tace ae aci gaba da Zama lafiya Ana gantali, wanne gantali mu da muka yo rako duniya,gamu an halicce mu a Nigeria babbar jarabawa,ga talauci,wannan duniyar Ina Dadi cikinta, aikinsu Suka ci gaba Yi suna Hira kamar ba sune Suka Yi fada ba,dama sun Saba fada da junansu. Washe gari Bayan ta tafi wajen Aiki Sai ta Iske Siyama Bata karaso ba sai Aamna da sauran ma'aikatan,Siyama kuwa Direct gidan Su Aamna ta wuce,Mama ta tarbe ta,Tayi sa'a Baba ma Yana gida,Bayan sun gaisa Tace Baba wata magana ce ke tafe Dani da Kuma shawara,Baba yace Muna jinki Siyama,Siyama ta Basu labarin yanda sukayi da Aamna Akan Maganar Aurenta da Faisal,Baba yace na rasa dalilin Yarinyar Nan da Bata kaunar Aure,Siyama Tace Ni abinda na fahimta Baba Aljani ne ya auri Aamna Kawai shawara ku kaita gidan malamai a Nema Mata magani shine Kawai,Mama Tace tabbas yarinya kinyi nisan hankali,shi yasa ake son kawa irinku ta gari,Haba biri yayi Kama da mutum cewar Baba,yace Inshaallah gobe zamu dauketa mu tafi da ita kauyenmu can Sokoto mu Nema Mata magani,dama jiya anyi Mana Albashi sai a fasa siyan komai mu tafi neman magani Allah yasa a Dace kafin ayi Auren Zuhra itama ta samu nata Mijin mu hada a Sha rikitiba sosai,Haka Siyama ta fito ta zo wajen Aiki a makare ranar Aamna Bata San dalili ba tana komawa gida taga Baba da fara'a ya amsa Sallamarta,ta Gaida shi Kuma ya amsa,Mama ma Haka,Aamna dai hankalinta Bai kwanta ba tayi mamaki,Zuhra kuwa tana ta karasa miyar Taushe,Mama Tace Aamna Sannu da Aiki zauna na kawo Miki abinci,Aamna mamaki ya kamata sai binsu take da kallo har taga an kawo Mata abincin a flask Wanda a baya ko rufe Mata ba ayi bare wani Flask,ta kalli abincin ta kalli Mama Tace Mama ko dai maganin bera kuka saka min zaku kashe Ni?Mama tana gyara daurin zaninta Tace haba Aamna kin taba ganin Iyaye sun kashe yarsu? Aamna Tace na nawa Kuma,bazan ci ba gaskiya wallahi,Ina so na Kara tsawon Rai,bana so na mutu yanzu sabo da Haka Ni bazan ci ba ko ruwan gidan Nan na daina Sha gaskiya. Babu irin lallabawa da lallashin Aamna da Iyayenta Basu Yi ba Amma Taki cin abinci ko ruwa Bata Sha ba,Baba ya kalle ta yace Ki shirya Aamna gobe zamu je Kauye gaishe da Yan Uwana da abokan arzuka,Aamna Tace Amma ba a fada min da wuri ba na shirya,shike Nan Allah ya kaimu goben Amma kafin mu tafi Zan sanarwa ogar mu sabo da gudun matsala,Ba damuwa Aamna cewar Mama. Aamna kwana tayi Bata ci komai ba duk da cewar taci a Restaurant dinsu,Washe gari da wuri ta nufi gidan su Saratu kawarta,Saratu tana bacci har Aamna ta Shiga aka Mata Sallama da Maman Saratu ta Mata bayani zasu Yi tafiya,Hajiya Tace Baki da matsala Aamna Amma kin San dai Baki da kudin fashin da zakiyi,a cikin Albashinki za a cire na Iya kwanakin da kika Yi bakya zuwa Aiki tunda kin San ba aikin Gomnati bane,Gomnati ce ake cin banza Ni Kuma ba Gomnati bace,Aamna Tace ba damuwa Amma,Hajiya Tace a dawo lfy ta Mike tare da haurawa sama,itama Aamna ta Mike ta tafi,dama sun Gama shiri Kaya Kawai ta canja wani lace ja me adon Golden, me Dan kyau Riga da skert,Ta sa takalminta na Sallah da jaka duka Golden,Zuhra Kawai aka Bari a gida sabo da makaranta suna Exam,Napep muka shiga zuwa Tasha daga can Muka hau Motar Sokoto tana ta Adduointa, sun Dade suna tafiya Amma sai kusan dare muka Isa can kauyen Su Baba da Maman su,Asalin gidan Iyayen Baba muka sauka a bangaren Baba,Dakuna biyu da toilet ne na Bulon Siminti Wanda Baba ne ya Gina ya sumulmule ko Ina da Siminti idan sunje can suke sharewa su zauna a gadon uban su,Ko wanne daki akwai Ledar tsakar daki da katifa katuwa da Bedsheet,sai kwanikan cin Abinci da Tukwane har da Reshio dinsu,komai na bukata akwai dai dai talaka,Mutanen gidan Suka tarbe su dake Babban gida ne a bangaren Kanin Baba wato Kawu Ismail muka sauka. Sai da suka ci abinci suka huta sannan suka gyara bangaren Baba ita da Mama, Bedsheet din Yana wanke a cikin kayansu suka shimfida abin su,a saman Katifun dakunan Guda biyu,wanka suka Yi tare da Yin Sallar Isha,Baba suna Kofar gida shi da Kaninsa da sauran dangi,suma dakinsu Mata ne Yan Uwa aka taru suna hira sai ga Baba da Kawu Ismail,ba tare da Bata lokaci ba Baba yace ke Aamna taso muje Ina Maman taku ta taso mu tafi muyi abinda ya kawo mu ba dadewa zamuyi ba,Hijab me Hannu Aamna ta Daura saman Riga da skert Dinta na jar Atamfa,Mama kuwa Mayafi ta yafa tare da Fitowa zasu tafi,Baba ya kalli Mama yace wannan tayani gantalin Wato baza ki daina yafawa ba ko? Har yanzu fa da sauranki Baki Gama Expire ba,Dariya Aamna tayi tare da sadda kanta kasa sabo da fadan Baba da Mama ya rigada yabi jininsu,Mama Tace Kai ka sani dai,Baba yace ya kamata ki daina Narka kibar Nan ke ba Wani abinci kike samu me Gina jiki ba Amma kullum Hawa kike kamar ana buga Miki Iska,Mama Tace sai ka fara rage taka kibar tukun,Haka suka tafi Suna ta cacar baki,Kawu Ismail kuwa fada yake ta yiwa Aamna lallai ta fitar da Mijin Aure,yace abokan haihuwarki daga me Yara hudu sai me Yara biyar a Nan kauyen,ita Aamna Bata taba sanin Mama da Baba Basu Suka haife ta ba,tasan dai suna Dan nuna Mata banbanci tsakaninta da Zuhra,Haka Dangin Baba tasan Suma sunfi son Zuhra,Haka ma Dangin Mama,Sai wani gida da ake kaita tun tana karama a cikin Sokoto city wani me kyau gidan mutanen Sudan ance Wai Yan uwane suma Gidan wani mutum suka je Malam me Almajirai,Bayan sun zauna Aamna sai ji tayi Baba suna ta Masa bayani akan bata samu Mijin Aure ba,Kuma ko zancen Aure akayi Aamna Bata kauna,Malamin Yana tauna goro yace Ashsha Aljan ne namijin dare ne wallahi take fama da shi,Mama Tace biri yayi Kama da mutum,Baki Aamna ta Bude tana kallon Iyayen Nata,Malamin yace yanzu Zan kwana Uku ba bacci Ina wani Aiki Amma dole aikin Nan kullum sai an yanka zakara Guda Uku har na kwana Uku,Baba duk talaucinsa sai yace dama na samu wasu kudi Nan take ya biya kudin zakaru tare da bawa malamin dubu goma kudin Aiki,yace Nan da kwana Uku ku dawo ku karbi wata laya wacce zata soke ta a cikin gashinta,Fuska Aamna ta Bata kamar zata saka kuka,Ace Allah Bai kawo lokacin Abu ba Amma Iyayen nata basa gani. Suna Fitowa Kawu Ismail yace saura wajen Malam Kare Aiki,Wannan malamin sanatoci layi suke Yi a Wajensa,Aamna ta girgiza Kai Tace Baba wallahi ba kyau,Wannan shirka ce baza a fadawa Allah bukata ba sai Malam,Baba ya kalleta cikin duhun dare yace ai ke Aljanu gareki sun aureki Bai ma dace a saurare ki ba sabo da ba a cikin hayyacinki kike ba,Yo ka biyewa sakarai cewar Mama,Kawu Ismail yaci gaba da cewa inshallah Kuna komawa zata samu Miji itama,Wannan malamin da suka je Wajensa Rubutu yayiwa Aamna a tafin Hannu yace lashe ai magauta ne Suka mata asiri kuma makwaftan ku ne,Takaici yasa Aamna Tace Allah ya tona muku asiri masu hada fada tsakanin Musulmai,Rankwashi Mama ta zubawa Aamna tayi Shuru,Lashe Kawu ya furta Yana zaro Mata Ido,Haka ba a sonta ba Tace Allah na tuba bana nufin kowa da sharri sannan ta lashe su Baba suna ganin Aljanu ne ke hanata Sha,Haka Suka je wajen wani malamin shima yayi nasa sannan suka jira Bayan Kwana Uku Suka karbo duk wasu Magungunan da aka hada Suka dawo ,Duk wani Rubutu da magani da Suka bawa Aamna Kan tayi amfani da su sai ta samu jikin katanga ta zubar babu Wanda ya sani,Laya Kuma Haka ta soketa da pin a gashinta sabo da kullum Mama sai ta duba gashin dole ta soke Laya a gashinta. Su Baba Basu Sani ba suna ta jira suga saurayi yazo neman Auren Aamna Amma Shuru,ga Kuma bikin Zuhra yana ta gabatowa,duk sunyi Anko da Dinku Nan su na biki duk wani shiri da za ayi mun Riga sunyi,Baba ya siyar da manyan shanayensa Guda hudu dake Kauye sabo da Haka ba Harkar Talauci sunyi komai cikin rufin asiri,Adam Ango ya hada musu Dinner zazzafa me kyau ranar Saturday,Sunday za a daura Aure a Kai Amarya,daga Aamna sai kawarta Siyama bata gayyaci kowa ba,Amarya dai taci Uban gayyar kawaye wurin Dinner,Biki saura kwana daya a fara Aamna tayi lalle da gyaran gashi,amarya kuwa ta Sha gyara sai sheki take zubawa,dangi na nesa sun zo sai tsiya ake yiwa Aamna kanwa zata Yi aure ta bar Yayarta,Haka suka Sha bikin Zuhra da Angonta Adam anyi an Gama lfy tare da Kai Amarya da gararta,gidan Adam madaidaici ne me kyau harda gate yayi kyau gidan,ga Yar motarsa me kyau Toyota,Itama Zuhra Baba ya Dage ya Mata Kaya masu kyawun gaske. Ahmad Yana kwance a makeken Gadonsa Yana zuba bacci,wayarsa ta dinga ruru gashi ya kasa tashi sai da kyar ya farka ba tare da ya Bude idonsa ba ya jawo wayarsa yaga number Mummynsa dama ta fada Masa zata zo ta ganshi a kaduna ita kadai kasancewar Daddy,Saddeeq da Humaira suna Saudiya Umrah,Cikin Muryar bacci ya Kara Wayar a kunnensa tare da Furta Hello Mummy......Muryar Namiji yaji yace da Allah me wannan Wayar sunyi Mummunan Hatsari Driver ya mutu ita Kuma tana asibiti da Allah ayi sauri azo,Firgigit ya farka Yace what....?cikin gigita yace please fada min Address din Asibitin,Nan take ya fada Masa,Da sauri Ahmad ya figi machine dinsa sanye da wando 3qutr da Riga t-shirt fara tas sai asibiti,a gurguje ya fada ciki Yana tambaya aka kaishi Emergency Nan ya Iske Mummy Rai a hannun Allah. Aamna Yau da matsanancin ciwon Mara ta tafi wurin aikinta gudun kar a hanata kudinta cas sabo da ba aikin Gomnati bane,a Haka take daurewa tun tana aikinta da karfin Hali har abin ya fara gagararta,Siyama ta kalla tana rumtse Ido Tace Siyama dole Zan hakura da aikin yau Hospital Zan wuce a duba min marata ya kamata ayi min scanning a gano min mene a wajen Nan,Siyama da tausayawa Tace Allah ya Baki lafiya kawata a dawo lfy sai munyi waya,Aamna ta daura After Dress a saman Uniform dinta Riga da wando ta fita tana tafiya a hankali ta Isa bakin Titi tare da Shiga Napep zuwa Asibitin da suke ganin Likita idan lalura ta taso,asibiti ne na Gomnati Amma ba laifi akwai kyau. Tana rike da mara hankalinta baya jikinta tana zuba Uban Sauri tabi wani Corridor,Gaf taji tayi Karo da mutum,wani kamshi me jarabar Dadi ya daki Hancinta,da sauri taja baya ko kallon Wanda ta buge Bata Yi ba,shima Bai ko kalleta ba hankalinsa baya jikinsa,Bayan tayi magana da wani Emergency ta nufa tana matse kwallar wahala gashi Bata fadawa kowa a gidansu ba,Karo suka sake Yi da juna kamshin mutumin dazu ta sake ji ya cika Mata Hanci Kamar Kar ta daina Shaka,Tsaki Yaja sosai yayi cikin Emergency Yana ta faman yiwa Doctors masifa,Yana cewa a bani Mummy na dole ne,Ni Nace bana son wannan Hospital din me Araha,a bani Uwata wannan so kuke ku kashe min Mummy a Asibitin Gomnati, Wallahi Mummy na ta mutum sai na daure ku,wani babban Likita ne yace Haba Malam Ahmad kake ko wa? Da masifa yace karka sake ce min Malam,Ni ba Malam bane,a masallaci ka ganni Ina Kiran Sallah ko Tafsiri kaga Ina Yi? Idan zaka iya Call me king,Doctor yayi Murmushi sabo da daga ganin Ahmad kasan inda tarbiyya take ma Bai nufa ba,Cikin tausasawa Doctor yace kayi Hakuri zamuyi Aiki iya yin mu a samu ta farfado wallahi Matukar ba a Bata agaji ba ka dauke ta to kafin kaje da ita wani Asibitin zaka iya rasa ta kayi Hakuri idan aka samo kanta sai ka dauke ta idan kaga dama ma ka tafi da abarka China. Aamna kwance take tana hawayen wahala Ana ta lallaba Ahmad Anki kulata,Cikin masifa Tace da Allah ku rabu dashi azo a duba marata Likita mayu sun kamani sun min Ajiya a marata watakil ma Tukunya ce a wajen ko wani karfen Kun zauna a wajen wannan muma ai ba daga sama muka Fado ba Kuma Nan gaba Aure zamuyi mu haihu,muma Iyayen wasu ne,Wani mugun kallo Ahmad ya aikawa Aamna sannan ya koma gefen Mummy ya zauna Yana cike da tashin hankali,Likita Yana zuwa kanta yace Rannan anyi Miki scanning nace ciwon sanyi ne dake sai kin dage da magani,Aamna Tace to ai har na gaji da maganin, wannan sanyi da naci yake jaraba Kawai,kankara nake Sha ko me?Ni ba Yar Madara ba Bamu da ko fridge ace wani sanyi,Ahmad sai lokacin ya kalli Aamna kadan tana kwance yace Doctor da Allah kazo wajen Mummy na ka rabu da wannan rubabbiyar Sanyi ya Gama kashe ta mijinta shike nan sai asosa Mata asosa,Aamna tunda ta kalli Ahmad Bata sake Kallonsa ba sabo da kyawunsa da wani mugun kwarjini da yake mata,cikin lokaci kadan Doctor ya yiwa Aamna Allurai tare da Bata magunguna,sai gata ta watsake ta warke yayin da Mummy itama ta farfado bayan likitoci sunyi aikinsu,Ahmad sai murna yake Yi,Mummy ta sa Hannunta tare da shafa sumarsa Tace karka fadawa Humaira da Daddy tunda naji sauki yanzu da ace akwai mace wacce zata kula Dani sai ta zauna har a sallame Ni,idan za a samo min Yar Aiki ma Zan biyata kudin jinya cewar Ahmad,Aamna ta dauki Handbag dinta ta wuce kenan taji Ana Neman me Aiki Sai gashi ta dawo baya da sauri tare da tambaya Nawa za a biya Ni? Mummy ta kalli Aamna sama da kasa Tace daga dubu Hamsim zuwa sama,Aamna ta Bude Baki Tace yanzu idan yau na fara jinya aka sallameki gobe dubu Hamsim Zaki bani? Ahmad yace kaji barauniya, Mummy ce ta kalli Aamna ta daga Kai Alamar ae,Aamna Tace Alhmdllh na karba zanyi Bari naje gida nayo Shirin jinya,Mummy Tace a dawo lfy tana rufe Ido sabo da da kyar take magana ba laifi Mummy ta Sha wahala. Agurguje Aamna ta koma gida ko abinci bata ci ba ta sanarwa Mama komai,Baki ta tabe Tace yo tunda kinki aure ai sai kici gaba da neman kudin tunda ke kudi ne a gabanki,Baba kuwa Baki ya tabe yace ba abinda kika sani sai neman kudi to a dawo lfy dama bikin Zuhra ya cinye Mana komai,ita dai Aamna kayanta ta bukata ta hada a karamar Akwati tayi wanka tare da yin Sallar Isha sannan ta wuce Asibitin abinta,tana tafiya kamar Namiji sabo da Tace ta daina Zama ta kirki. Tana Shiga ta Iske Ahmad ya jibgo kayan ci da Sha da duk wani abin bukata,Kallon Aamna yayi tare da galla Mata Harara cikin kallo na wulakanci,Aamna ta kalle shi itama tare da tabe Baki ta shiga rera Waka lalatacce....lalatacce ne ko a gidan su,da sauri ya kalle ta ransa a bace gashi ba damar fada Amma duk da Haka sai da Yaja Tsaki yace Talakar banza barauniya,Aamna tace ae naji da me kudi da talaka ai duk Allah yaga dama ya bawa kowa,You are very stupid....nayi magana dake? Ina wakata Zaki sa min ths your Smelling mouth,Mind your fucking Business ya Furta da karaji Wanda sai da Mummy ta farka tare da dafe kanta,duk abinda sukeyi tana jinsu, Nishi tayi Tace Son gobe a canja min Hospital wannan akwai sauro gashi ba Ac,Ahmad Yana maganarsa ta Yan duniya sai kace wani Me wakar Raps yace comfirm Mum,ki Dade kiyi karko and ki mutu AC Mum,Allah ya ja da nisan kwana,Mummy tayi Dan murmushi Tace Ameen a hankali,Aamna ta kalla tace dauki katin Nan ki Siyo maganin da ba a karasa siya ba,Ga kudi Nan a jaka ta,Aamna ta zuge jakar Mummy zata dauki katin da kudin,Ahmad ya fisge jakar ya dauko katin tare da zaro kudi a aljihunsa ya Watso a jikin Aamna yace Jeki,Aamna tayi murmushin bacin Rai Tace ba komai ta Eba ta fita,wurin siyen maganin taje ta Mika katin wani yaro matashi ne a ciki Yace dubu Uku da dari biyu,Me bada maganin da hantara yace ba canji malama,Dan Rainin hankali baza ki samo canji ba. Aamna ta Bude Baki tana kallon yanda yake masifa,Kai Malam kayi hankali da Ni Kanwar uwarka ce Ni da zaka dinga min magana Anyhow,Uban me kika Isa kiyi,Tas kake ji Aamna ta zuba Masa Mari Tace fito mu Buda wallahi Naga baka da tarbiyya,Wanda suke wajen ne Suka fito tare da raba fadan sannan Aamna ta wuce abinta ta siyo maganin a wani chemist dake wajen Hospital din,tana masifa an fada musu Ina tsoron fada da Namiji,In cakwumi Namiji,inci kwalarsa,muyi dambe ba komai ne a wajena ba,girman Kauye ce Ni,har yanzu da ragowar Tuwon dawa a jikina cewar Aamna har ta Shiga dakin da Mummy take tana fada cewar in Balla Namiji ba komai bane a wajena,In samu mutum in farke Masa makoshi Dan uban mazaje,Ahmad ya bita da kallo sororo Yana mamakin mace da tsaurin Ido Haka,Tsaki Yaja yaci gaba da latsa wayarsa. Amma ita Aamna ta manta ma da wata marar lafiya take jinya taci gaba da cewa ko wanne Namiji Dan iska,to Billahillazi girman Kauye ce Ni sai na soke mutum da kwalaba,Ahmad ya sake zaro Ido a ransa yace tab Wanda ya auri wannan yayi bye bye da duniya kawai,irinsu ne masu kashe mazaje,Aamna Ta fake da wayo tana zagin Ahmad Tace Dan Iskan mutum Dan Kawai Yana da kyau da kudi ai muma Muna da kyan,ae munji mu talakawa ne sai akayi kaka? Duk kudin mutum Dan ubansa malaikan mutuwa Yana Nan zuwa duk tsayin katanga da katon gate haka zai haura ya zare ruhin mutum,abi duniya a Sannu,Duk wani shiga katuwar mota Haka mala'ika zai zaro ran mutum,Wani mugun razana tayi sakamakon tsawar da Ahmad ya buga Mata,shut up kina min Ihu akan maralafiya Zan fa barar dake,Zan Baki certificate wlh watch your words,Mukus Aamna tayi a ranta Tace wannan shege ne shima. Babu yanda Mummy Bata yi ba Akan Ahmad ya tafi gida Amma yaki yarda ya tafi Yana Nan ya kafa ya tsare. AsmaBaffa 10/26/21, 8:51 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 11-15 DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER TA 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa. Page naki ne FANCY HONEY Yana Zaune a gefen Mummy ita Kuma Aamna tana zaune a wata kujera,Mararta ce ta sake murdawa da sauri ta rike mara tare da kwala Ihu Mummy sai da ta Bude Idonta,Da Sauri Aamna ta samu gadon da ba kowa ta kwanta tana Nishi tare da Kiran Doctor,Likita ya shigo yace to yanzu me jinya ce zata Yi Jinyar wata? Aamna tana cije lebe Tace zanyi Haka Kai Likita ba ruwanka yawwa kayi aikinka Kawai wannan kudi Ina Zan bar shi,Dariya Likita yayi yace Aamna kike ko? Tace no Amy karka sake ce min wani Aamna Aemy(Amy)Baki Ahmad ya tabe tare da Bude wata Leda ya fito da manyan kwalaban giya masu tsada Yana korawa Abinsa Yayin da Mummy take ta bacci,tana kwance ta juyo tana kallonsa bata Gane giya bace tayi tunanin wani lemo ne me Dadi na masu kudi,tana ta Kallonsa tana faman Hadiyar yawu,Aamna Tace Wanda yaci shi kadai shi kadai zai mutu,kafin ta rufe Baki yace da Ubanki za a sani a kabari da? Aamna Tace wakata nayi fa,Nima ai wakar nakeyi ko na kulaki? cewar Ahmad Yana cin magani kamar zaiyi Naushi. Aamna ita kanta Tsoronsa take Yi Amma karfin Hali Irin nata yasa take maida Masa martani,Mummy tana kwance tana numfarfashi tasan me yake Sha sabo da taji warinta,baya kunyar uban kowa,sai da ya Gama Shan wacce zai Sha ya Mike Yana saka wayarsa a cikin wani Crazy 3qurt Jean Kan Mummy ya shafa tare da furta Allah ya Baki lfy Bari naje gida nayi wanka Zan dawo,Mummy Tace baza ka canja ba ko son so kake bakin cikinka ya kashe Ni? Murmushi yayi Kawai sannan yace Zan dawo Mum yanzu 11pm Zan dawo a Nan Zan kwana,aci gaba da Mana Addua Ina so na shiryu Amma Ina,A gabanta ya tsuguna,Mummy ta daura Hannunta a saman sumarsa tare da furta Allah ya shirya min kai Ahmad,Allah ya maka Albarka Allah ya tsare min Kai,Ameen My sweet Mum ya Furta Yana Jin dadi sannan ya Mike ya fita Yana takunsa da wani takama da Isa kamar Dan sarki,Machine dinsa ya hau tare da Bude wuta kamar zai tashi sama,Direct gidansa ya nufa ko da ya Isa gidan Toilet dinsa ya wuce ta Sha gyara ya sakarwa Kansa Shower tare da wanka da wani liquid soap me tsada da kamshi,Bayan ya Gama a gurguje yayi Sallar Magriba da Isha sabo da akwai Wasa da Addini,Yana Idarwa ya daga Hannu sama Yana Adduoi tare da rokar Allah Allah ka Bawa Mummy na lafiya. Yace cikin adduar Allah duk da ba Adduar Nan nake Yi ba kullum Allah Ni me laifi ne a gareka ya Rabbissamawati Wal ard Allah ka yafe min laifuka na ka shirye Ni,Ina so na shiryu ya Allah Amma na kasa ya Allah ka dafa min na shiryu,Allah kasa mu mutu Muna Musulmai masu Imani,Allah karka Bari muyi maka shirka,Ka rabamu da Wutar Jahannama,Ka Bamu lfy da tsawon Rai,Allah kasa nayi tsawon Rai Allah bana so na mutu da wuri ka ja kwana na,Ka rabani da cuttuttukan zamani, ya Allah ka raba mu da talauci ka Bamu dukiya ta halak me amfani,Haka ma ya yiwa Daddy da Yan Uwa da Musulmai,karshe yace yace Allah duk da ba damuwa nayi da Mata ba Mummy ta tana so nayi aure Ya Rab ka bani mace ta gari me so na tsakani da Allah,me Ilmin Addini Dana zamani,wayayya,ba Yar Kauye ba,Ya Rab zukekiya ko ko fara ko light chocolate wacce idan na kalle ta kawai Zan washe Baki ba tare dana shirya ba,mace Yar dagwas wacce ta Dan dire ta Dan baje daga kasa. Har zai tashi sai ya koma ya sake daga Hannu sama yace Ya Hayyu ya Qayyum na kawo karar Daddy wajen ka Allah kasa ya daina min fada kasa ya dinga so na,Allah kana gani dai Tsoho Nan nawa ya tsane ni kamar ba a son ransa aka haifo Ni ba,to Allah Kaine ka halicce Ni ya zaiyi Dani Allah kasa ya daina tsanata Yana gamawa ya Mike tare da zare jallabiyar da ya saka domin yin Sallah,ya dakko gajeren wando wani me tsada iya gwiwa ya tsaya Masa me Dan Fadi Yana da Aljihuna kala kala a jiki gashi Kalar ruwan kasa yasa Riga Armless baka me rubuyu a jiki da zanen fari,Pcap ya saka Kalar wandonsa Takalminsa ma na Yan gayu Wanda suka San mene wanka ya saka Kalar wandon,wow ba karamin kyau yayi ba Kamar a sace shi a gudu,damatsan Nan gasu Nan na mazaje mul mul irin na Wanda ke Dan Gym,turare yabi jikinsa sannan ya dauki key din machine dinsa ya fita,time ya duba 12am wani 24hrs shawarma joint ya nufa,Ko da ya Shiga ga mutane Nan Kamar Rana,Ana ta shige da fice,wasu Kuma suna ta Shan Shisha shi baya Harkar Hayaki,Take Away yayi na Abubuwan ci sannan ya nufo Hospital wurin Mummy. Bayan Tafiyar Ahmad daga Asibitin Mummy ce ta Dan yiwa Aamna magana da kyar Tace 'ya ta kin iya cire kudi a bank? Nan take tace ae,Tace duba handbag Dina ki dauki Atm card Dina ki ciro min dubu dari,Mamaki tayi lallai masu kudi ne,Haka ta dauka tana mamaki da Bata Santa ba Amma har ta yarda Da ita, Code dinta ta fada mata ta fita da sauri taje ta ciro,Handbag dinta ta sa ta zuba kudin da Atm card din,lokacin Likita yazo yace Hajiya anyi komao dakin da kike bukata ya Zama ready aje a biya kudi sai ku koma ciki. Yana zuwa ya Iske an canja wa Mummy daki Already Kuma dakin na masu kudi ne Idan kana da kudi sai ka biya kudin daki Guda karami a baka Kai Daya,Gado ne daban na me jinya a dakin da Kuma me cutar nata daban,cikin abubuwan Daya siyo ya Bari masu yawa ciki ta Bude ledoji Aamna taga Naman kaza gasashiya ga tsire daban,ga wata Hanta me ruwa ruwa,sai pounded yam da Miyar Egusi shima a take away daban,Sai Lemuka kamar hauka da fruits ga kayan tea,ga plates da spoons,cups etc,komai an tanada,Ido Aamna ta zaro kenan,Mummy duk jikinta inda taji rauni yayi tsami ko Ina ciwo yake Mata Allah yasa Bata karye ba Sannan Bata Yi Mummunan rauni ba Wanda zai wahalar da ita,Dan Nishi tayi Tace Yar Nan zo ki taimaka min naje bayi,Aamna ta Mike da sauri tare da Rike Mummy ta taimaka Mata tana sannu...Sannu Baiwar Allah Sannu Hajiya me kudi Allah ya tashi kafada,Mummy sai da Aamna ta Bata Dariya yanda take Abu kamar tsohuwa,Mummy tace Yan Mata Kamar tsohuwa,Aamna Tace ai itace Hajiya shekarata ashirin da Hudu Babana yace na tsufa gashi naki aure,kin San Baba a Kauye ya taso shi yasa halinsa Bai canja ba,Mummy Tace Uhm,Bayan ta kaita har Toilet sai ta rufo Mata kofa ta fito,Mummy Tace Miko min brush da toothpaste Zaki gani Dana ya kawo,Aamna ta duba ta dakko ta kawo komai da Mummy ke bukata ta Kai Mata,duk Abinda Mummy zata Yi tayi ta fito,Aamna taje da sauri ta taimaka Mata ta kwanta saman bed,a Haka ta samu tayi sallolin da ake binta tayi Addua sosai,Aamna Tace Abinci fa Hajiya?Mummy Tace bani pounded yam din na Dan ci,Amma ta dakko ta zuba a plate tare da cokali ta Bude Hanta da kaza tare da tsire duk a Gaban Mummy,Fruits ma ta yanka sannan ta hada Mata tea me kauri ta zauna tare da sa Mummy a gaba kamar ta samu Yaron yaye,Tace yawwa mashaallah Bismillah ta yanko sakwara da Miya Tace to Hajiya ayi hankali gashi Naga gefen bakinki kin danji rauni tana ta Bata a Baki sunyi Shuru kamar ba kowa,Mummy tana ta ci Tace Baki magana ne? Me zance Mummy sai dai idan tatsuniya Zan miki,Mummy Tace sai kace wata yarinya bana so,Sai da Mummy taci da yawa sannan Tace na koshi,Aamna Tace to Naman fa? Ta Furta tare da ballo cinyar kaza ta mikawa Mummy. Mummy Tace Alhmdllh na koshi,Aamna ta zaro Ido Tace Kazar Hajiya?kaza ce fa,Mummy ta girgiza Kai Alamar Bata ci,Aamna Tace inda ake arziki ba a tsiya Ni Bari na aikata,Nan Aamna taci Kazar Nan ta gaji ta ajiye sauran,taci tsiren taci duk sauran,Mummy kuwa kankana ta Sha taci Banana da Red Apple,Aamna Kam yau harka ta samu sai da taji zata yiwa kanta Illa sannan ta hakura,ta Mike kenan Tace Bari na wanke Hannu da kwanikan tana juyowa gabanta ya yanke yayi muguwar Faduwa ganin Ahmad a tsaye a jikin Kofa da Alama ya Dade a wajen,Fuskarsa ba kwayar Rahma a ciki,Idonta ta dauke a Kansa ta rabe ta gefensa zata wuce wani kamshi Wanda ba irin na dazu ba ya daki Hancinta sai da ta lumshe ido ba tare da ta shirya ba Haka ta wuce da sauri tayi waje,sai da ta wanke komai sannan ta dawo da su ciki ta Adana a tsaftace ta Iske Mummy da Ahmad suna magana da,Mummy tana ta Masa fada ya Bata Rai yayi Shuru,Aamna tana dawowa Mummy ta bar zancen,ita kuwa Aamna saman gadon da ba kowa ta kwanta tare da dakko Wayarta wacce take Ringing tana bukatar a kawo Mata dauki. Ganin kanwarta Zuhra ta daga da sauri,Tace Amarya bakya laifi,Zuhra ta zuba murmushi tana kwance jikin Angonta Adam tace nayi missing naki sis yau naji ban Iya bacci sai naji muryarki,Wallahi Aunty Amy Aure Niima ne,sai yanzu nasan Ni mutum ce Ashe a baya gunki ce Kawai,da ace nasan Haka ne da bazan Dade Haka ba zanyi Aure,Aamna Tace to me yasa bakiyi ba Ana Haihuwar ki ba,ai sai kiyi tun kina jaririya,Ke Aunty Aamna ke fa adawa kike da Aure,ki daina min sharri wa zai ki Aure? Kawai Ni abinda nafi so a aure shine na ganni Ina fasa kwai a kitchen Zan soya Ina kwas kwas a kitchen,Dariya Zuhra take yiwa Yayarta Kamar me,Aamna Tace ban San Iskanci Dan na fada Miki Buri na a Aure shine kike wani dariya,To Ni ba abinda nake so a aure face in cakare da kwalliya Ina kitchen Ina fasa kwai,Mummy tana bacci Ahmad Yana jinsu Amma wayarsa Kawai yake dannawa,Zuhra Tace Aunty to babbar Harkar fa ta soyewa? Aamna Baki ta tabe tare da Furta Dan tani a yanke shege na kowa a duniya a jefar,Ahmad Yana jinsu wannan Maganar Bai Gane me suke nufi ba. Zuhra Tace Aunty Amy Allah ya Baki kema Kalar da kike so Wanda zai biya sadakinki da shegen tsada,Aamna Tace ke na rage tsada na zaftare farashi na yanda su Baba suka damu Ina Ni Ina zaben Yawan Sadaki,Adam ne ya kwace wayar dake Hannun Zuhra tare da Furta sai da safe Aunty kitt ya kashe wayar Baki daya sannan ya ja Amaryarsa Suka kwanta ita kuwa Aamna kwanciya tayi itama tana latsa Wayarta gashi ta kasa bacci sabo da Ahmad Yana ciki Ta kasa kwanciya bare tayi bacci,Bacci ne ya dameta Haka ta kwanta tare da rufe jikinta da katon Hijab Nan take bacci yayi gaba da ita sai Ahmad shi Daya baiyi bacci ba,sai wurin 2am sannan ya bar Asibitin ba tare da kowa ya sani ba. Washe gari da Asuba Mummy ta farka da karfi a jikinta sosai kamar ba ita ba,Kawai rauni ne da Bai warke ba Amma jikinta fes taji,Da kanta ta lallaba taje Bayi gaba Daya kyankyamin Asibitin take Yi shi yasa ta kasa wanka,Sallah tayi itama Aamna Haka Bayan sunyi Brush da komai suna Azhkar Sai da suka Gama sannan Mummy Tace Aamna kike ko? Aamna Tace ae Tace Yau Zan sa a sallame Ni naji sauki Zan iya karasawa a gida tunda Ina da masu Aiki masu kula da Ni,Aamna tana murmushi tace mashaallah Alhmdllh Haka ake so Allah Kara lfy,Ameen Mummy ta furta,Biro da takarda Mummy ta mikawa Aamna Tace rubuta min Address dinki full sai accnt number dinki,Aamna ta karba ta rubuta komai,Nan take Mummy ta kunna Wayarta tayiwa Aamna transfer na dubu Hamsim,Farin ciki ya lullube Amy Tace Hajiya naji kararrawa na gode Allah ya Kara budi,Ameen Mummy ta Furta tare da mikawa Aamna katinta gashi ko Watarana Zaki neme Ni,Aamna ta karbe jiki na rawa. suna Haka sai ga Ahmad ya shigo cikin jallabiya fara Kar ta kirki,yayi mugun kyau,Nan take Aamna ta bishi da kallo a ranta Tace wannan Dangin Larabawa ne gaskiya,ko kallon Inda Aamna take baiyi ba ya koma wajen Mummy dinsa suka gaisa Yana ta murna taji sauki,Itama Aamna Bata kula shi ba ko gaisuwa,Kayan breakfast lafiyayye ya musu take Away Suka ci tare da godiya ga Allah,Wasa Wasa Mummy ba a sallame ta ba sai 4pm,Aamna tana gani Wata galleliyar mota tazo tare da tafiya da Mummy,Suka Yi Sallama Aamna ta shiga Napep sai gida,ta samu yan kudinta Bata da matsala abinta. Bayan Aamna ta dawo gaba Daya kayan da taje asibiti da su har na jikinta ta cire ta wanke fes tayi wanka dama a koshe take,Zama tayi a gefen Mama,Lokacin Baba ya fito daga daki yace yanzu Zuhra tana can a dakin mijinta tana zamanta lfy Abinta,abin kunya Yaya Guda Bata da ko saurayi ko me Gadi babu Wanda ke zuwa zance,Mama Tace an Rubuta Hatimin Annabi Yusufa har an gaji Shuru kake ji sai Neman kudi,Iskanci ne Kawai da samun waje shi yasa Taki fitar da mijin,laifinta ne cewar Mama Kuma kudinki kwandala mun daina karba kije da abinki,Aamna tayi Shuru har Suka Gama ta Mike tayi waje zuwa Kofar gida a kasa ta samu ta zauna dirshan tare da kurma Ihu iya karfinta tana wayyooooo.....Allah.....na shiga Uku na lalace.....Ina samari suke ko Dattawa ku fito ku Aure Ni,Dan Allah gani sadaka ga me bukata,,Ko me tallan rake ko Shoe shiner ko me Gadi,me Mata uku ma yazo Zan Shiga a ta hudu. Wasu ma tunaninsu tabin kwakwalwa ne ya kamata,sai Dariya akeyi Amma Aamna ko a jikinta,sai da taji Rana ta ishe ta sannan ta koma gida,tana Shiga Baba ya rike ta ram tare da zaro katuwar Sanda ya samu Aamna Kamar Allah ya Aiko shi ya shiga jibgarta kamar zai kashe ta,Mama tana Kara Mata Yar Iska mu Zaki kunyata a Unguwa,Ihu Aamna takeyi ga Yan hayar gidan ba kowa,Karshe ta tashi da kyar ba Mayafi jikinta duk kulun Sanda ne ko Ina da gudu tayi waje tana ihu,Baba baya gudun Abin kunya Kawai ya bita a million Suka zuba tsere layinsu rigarsa tana tashi Kamar mahaukaci Ana ta kallon ikon Allah,har saman Titi suna falfala gudu Baba Yana na koreki a gidana karki dawo daga Nan kiyi gaba,Aamna tana gudun masifa tana cewa wallahi sai na dawo me yasa aka haife ni,Ni Nace ku haife Ni Ina ruwana,Suna Haka zugar machininan su Ahmad Suka taho gaba Daya Suma sun kure wuta,Ganin Baba da Aamna suna falla gudu,Dariya ta kwacewa su Mashkoor, a wajen Suka ci birki,Ahmad ne ya bi Aamna da machine tare da sa hannunsa me laushi ya cafko Hannunta da karfi ya daga ta Kamar ya dauki tsinke ya cilla ta a bayan machine ta zauna daram,tana Jin dadi har da godiya Amma sai taga Ahmad yayi reverse ya juya da ita wajen Baba,Ta saki Ihu shi kuwa Baba zuciyarsa Dake tafarfasa yace Alhmdllh ya tsaya cak,a gabansa Ahmad ya Zana wani shegen kwabo da machine yaci birki sannan Aamna ta dire zata gudu Ahmad da shishigi ya samu ya yarfawa Aamna Mari ji kake gauuuu.....Nan take fuskarta ta kumbura ta zube a wajen kuwa,Baba yace na gode Dan Albarka,Ahmad ya kalli Baba da tsageranci yace Gata Nan Yi Mata dukan tsiya Ina Nan ba inda zata je,ko Kuma Ni yanzu nayi maka maganinta,Baba ya saki Baki yace Kai Malam Taya zaka marar min yata, Mace Budurwa ka mareta kalli yanda ka kumbura Mata Fuska,baka da hankali ne? Wata Mahaukaciyar Tsawa Ahmad ya yiwa Ba ba,Hey....tsoho,da sauri Baba ya rufe Baki jikinsa na mazari. Da yatsa Ahmad ya nuna Baba yace Kai tsoho baka Sanni ba Zan sa yarana su babbalaka,Baba yayi Mukus,Su Mashkoor suka saki Ihu da sowa,Kallon Aamna Ahmad yayi tana kuka,Tsawa ya buga Mata Dan Uwarki Ina Mayafinki? Irinku ne kuke sawa Ana yiwa Yara fyade a kasar nan,Dan uban Babanki Ina Mayafinki eyeeee yayi kanta da hargowa,Aamna ta Mike tsaye tana kuka Tace baka Gane Ni bane nice fa wacce nayi jinyar mahaifiyarka,wani dariyar hauka yayi yace ke dalla Ware so what Dan kinyi jinya,kyauta kikayi? Bar Nan wajen ko yanzu na Tara Miki gajiya,Aamna Tace wallahi sai dai mu Tarawa juna gajiya,Kai Malam Nifa ba ruwana muyi kokawa ba komai bane,baka Isa kaci min mutunci da Mahaifi na ba,sai mu Buda Nima fa Yar Tasha ce,tashancin Nan na Iya shi ta Furta tana dukan kirjinta,Tace baka San har yankan Aljihu nayi ba a kasuwa,su Mashkoor suka hangame Baki,Suka ga Kuma Ahmad Bai sa sun Mata duka ba,Jibson da Maganar Yan kwaya yace King kana fa jinta kana kallonta ka bamu Dama mu sassarata. Mutane tunda suka ga su Ahmad babu Wanda yayi gigin zuwa kallo Dan sun San halinsu,Baba ne ya cire Rigarsa daga shi sai wando dogo da Singlet ya mikawa Aamna yace lulluba mu tafi gida,Aamna Tace Ni a Haka Zan koma ba Kaine ka kwance min zani a kasuwa ba,ka biyo Ni Muna ta tsere Ana kallo duk da dama ai mun Saba,Baba zuciyarka bata da control Wai? Baba yace ai kece Aamna Yar Iska ce,kiyi aure kinki Ni fa duk na washe ki ma wallahi,shekara ashirin da Hudu zuwa da biyar ba ko saurayi,25yrs shine girma tsoho? Mashkoor ya tambaya,Baba yace ae ,to Jibson Yana tangadi yace to ke kiyi auren Mana,Aamna sai da tayi Dariya yanda ya fada da muryar maye,Baba yace ai Bata iya magana ba,Bata waye ba,kwana Nan Muka dawo birni,shekarar mu hudu kenan a birni,sai cin mutuncin samari takeyi na rasa yanda zanyi da ita tafi karfi na,Ahmad yayi Murmushi tare da da shafa gemunsa Yana wani rangaji ya furta Tsoho Bari na kaji idan tayi laifi Kawai ka kirani ka fada min har gida zanzo na kera maka ita,Baba yace na gode Dama ta ishe ni,ta gagareni,Aamna mamaki ya kamata,Tsawar data razana ta taji ance yafa rigar tsoho,jiki na Bari ta karba tare da yin Mayafi da ita,Tace wallahi sai na Rama Nima na iya tashancin,Baba yace kuce Mata ta taho mu tafi gida,da yatsa Ahmad ya nuna Mata Hanya ta juya salin alin tabi Baba suka tafi. Su Aamna suna tafiya wata Budurwa ta taho da gudu wajen Ahmad Tace Dan Allah kaga wani can Haka Kawai ya dameni da naci sai Maganar Batsa yake min nace bana sonsa yaki hakura Wai sai na bashi kaina ko yayi min fyade Dan yaga Kawai Ina tallan gyada tunaninsa Yar Iska ce Ni ta karasa da kuka,Ahmad Fuska a Murtuke yace Yana Ina guy din? Da yatsa ta nuna musu,Ahmad yace Boys kuje ku min maganinsa,ai kuwa Suka tafi Kamar an Aiko su Suka hau jibgarsa,sai da suka Masa ligi ligi sannan Ahmad ya karasa wajen tare da yarinyar,yace Kai Dan uwarka wannan kake so?Kai Dan Iska ne?zaka lalata Yar wasu Tace Bata sonka dole ne? Matashi Yana Nishi jikinsa duk jini Ahmad yace daga yau idan kaga wannan yarinyar hanyar da take idan kabi wallahi sai na yankaka,Matashin yace bazan sake ba,Zan gyara halayena,ayi Hakuri Oga,Ahmad ya Shure shi da kafa yace bace a Nan,ya tashi ya fece da gudu,Yace wa Yarinyar ki dinga saka Hijab idan Zaki talla,Tace to na gode yanlabai,ki daina talla ki Shiga makaranta ko kiyi aure,Tace to ai an kusa biki na Kuma Ina Islamuyya yace Good Ware ke ban son surutu,da sauri ta tafi tana murna. Tafiya sukayi sunyi nisa Suka samu wani yaro ya fisge Wayar wani a Hanya,Ashe Ahmad yaga abinda Yaron yayi ya arce,Sai da ya Bari Yaron yasha kwana sannan yabi bayansa,ya sauka a machine ya cafke Yaron a nutse ya dinga kashe Yaron da Mari yafi a irga tun Yana gani sai da Yaron ya sume,Wayar da Yaron ya fisge Ahmad ya karba tare da kwarawa Yaron ruwa ya farfado yace Kai barawo ko Nan take ya Kira police Suka Yi gaba da Yaron shi Kuma ya maidawa Babban mutumin da aka satar Masa,mutumin ya dinga godiya,yace yaro daga an kirani na dakko waya Kawai naji ya fisge,Ahmad Bai kulashi ba ya wuce gidansa Kawai su Mashkoor suka rufa Masa baya. Tunda suke tafiya Aamna kuka takeyi jikinta duk rauni,Baba yace kece dai kika jawo Kuma kin San Halina wallahi Sai in Miki jina jina,Aamna taci gaba da kukanta tana tafiya,Baba yace Jeki ki Siyo kayan Miya da Salat ki Shiga da shi gida,Aamna Tace bani kudin tana kuka,yace a aljihunki Ni Ina da kudi ne an fada Miki,Nima yau bazan ciyar da kowa ba wallahi tunda aka Dake Ni ta furta tana shesheka,Zan tsine Miki wallahi Aamna Naga kin rainani,Aamna tayi banza da mahaifinta,kwafa Yaja ya juya ya tafiyarsa inda zai je yace yunwa ta kashe ku, Zaki sani Zan dawo gidan ne,Aamna tayi tafiyarta da rigarta a kanta har Gaban me kayan miyar kusa da gidansu tana goge Hawaye tana sheshekar kuka Tace Dan...tala....Dantala... ba....bani kayan Miya na dari hudu.....Salat na na ... Naira dariiiiiiiiiiiii......sai ta karasa da sakin Kuka me karfi a Gaban Dantala,Dantala ya saba da halin Aamna yasan Kuma yanda dama suke fada da Babanta,Yace kiyi Hakuri,ita rayuwa ko da wa zaka zauna sai kayi Hakuri Aamna,da girmanki da shekarunki haba Haba,Aamna ta sake fashewa da kuka Tace Wal....wallahi....wallahi tallahi yau bazan ci abinci ba da yunwa Zan kwana,Kuma na rantse bazan Taya Mama Aiki ba,Dantala Ina da zuciya,Kawai duk an bi an tsaneni akan ban samu Miji ba,a kauyen mu kowa sai ya fada min bakar magana bana Iya Shiga cikin dangi na sakata na Wala,Haka a gida ace Iyaye sun tsaneka,Dantala yayi Dariya yace sai hakuri Aamna,Tace wallahi Watarana za a ga na mutu a tsinci gawata Kawai,kiyi Hakuri cewar Dan tala ya zuba Mata kayan Miya ta bashi kudin ta tafi gida. Tana yin Sallama Mama ko kallonta Bata Yi ba,kayan miyar ta Ajiye zata juya Mama ta rike Hannunta caraf,Tace wa kike wa raini Wai? Waye sa'anki a gidan Nan Dan Kan uwarki,Aamna tayi Mukus Mama ta shiga zuba Mata Rankwashi ba adadi sannan ta saketa Tace tashi ko na nayi ball da ke, Aamna ta Mike ta fada daki tare da sake fashewa da kuka,Ita kuwa Mama girkinta ta shirya shinkafa da Miya da salat. Wato Islamiyyar Asabar da lahadin ma kin daina zuwa ko Aamna cewar Mama,Aamna Dake kwance a katifa ta fito Fuska a kumbure Tace na girmi Islamiyya Ni,Duk abinda ya kamata na sani na sani na addini sabo da Haka zanci gaba da saurarar wa'azi Kawai a gidan Radio ya isheni zaman duniya,a kyale Ni inji da matsalata,Ni yanzu ba karatu ne a gaba na ba,Alhadisissani,salisu duk na Iya ya ishe Ni,Sira da Ishmawi na haddace quarter,Zikiri na iya,Qurani saura Izu goma nayi sauka to me Kuma zanyi,gishirin zaman duniya na sani ya ishe Ni,Mama ta rike Baki Tace tab ke Baki ji kunya ba 25yrs Baki sauka ba,to ai da a sauke ba a Aiki da shi gwara ka samu Izu goma kayi Aiki da shi,Bulala Mama ta dakko Aamna ta jawo kujera ta zauna daram Tace a tafke Ni ai na Saba,kamata kullum a Duke Ni to a Dake Ni,Mama kuwa itama akwai zuciya Nan ta dinga tsulawa Aamna Bulala iya karfinta,har ta Gama Aamna ko motsi Bata Yi ba ta tashi a nutse ta shige dakinta,Haka Baba da dare bala'i yakeyi Kamar me,Ita kuwa Aamna washe gari sai da taje chemist aka Bata magunguna,tana dawowa ta Hado kayan sawarta a Akwati ta fito sanye da Hijab Tace Zan bar muku gidanku gwara na shiga duniya. Baba ko a jikinsa yace a gaisar da Yan bariki maza Kar dare yayi a dawo lafiya,Mama ta tabe Baki Tace sakarai,Aamna tana ta jira a lallashe ta ko ace Kar ta tafi Amma taji Shuru,Tace Zan tafi fa bazan dawo ba,Baba yace to,Duniya fa Zan shiga Mama,Mama Tace madalla,Juyawa Aamna tayi ta fara tafiya ba Wanda ya kulata har taje bakin kofa,Tace baza ku kirani ba Wai? Tsaki Baba ya ja,Aamna tayi waje kenan taga wata dalleliyar mota me tsada,Wata Dattijuwa ce ta fito a motar,da wani Dattijo shima fari ya fito,Aamna taji an kirata,Matar ta kalla sai taga Mummyn Ahmad ce cikin shiga ta Alfarma,Aamna fara'arta ta karu har kasa ta zube tare da Gaida su,Mummy Tace ga Baban Ahmad,Aamna ta sake Gaida shi tare da rike Hannun Mummy Suka Shiga gidan. Baba da Mama sunga masu kudi Nan Suka rude,Baba yace laaaaaa Alhaji Ja'afar Kaine a gidan Nawa? Wanda aka Kira da Alhaji Ja'afar yace ikon Allah Malam Hussaini Umar dama a Nan kake yanzu? Baba yace ae wallahi,me ya kawo ku?Aamna dai da Mummy suna mamaki aka shimfida musu Tabarma,Aamna ta kawo musu pure water da lemo,Nan ta ebo musu shinkafa da Miya da salat ta Ajiye,Tace Baba kasan su ne? Baba yace kwarai kuwa zauna kiji labari. Labari AsmaBaffa 10/26/21, 8:51 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 16-20 FREE PAGE DUNIYA TA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER TA 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne MAMAN SAMHA ZAINAB SABO BK UMMEEN SADEEQ BASMAM GLAM ALHUSNA(MRS IDRIS) Ni Hussaini Umar kamar yanda kika sani mu Uku Mahaifiyar Hajiya Maryam ta haifa,Kuma mu kadai ne a wajen Mahaifinmu Malam Umaru,Ni Yan biyu aka haife mu Ni Hussaini da Hassan,Hassan tun Muna jarirai Allah ya Masa Rasuwa sai Ni,daga Ni aka Haifo Kawunki Isma'il sai Kanwar mu Kursum wacce kika Sani a kauyenmu Sokoto take aure,Munyi karatun Muhammadiyya har muka girma Noma da kiwo muka gado, tun baya dama mu Bamu taso a cikin kudi ba sai rufin asiri,sai da muka girma lokacin aka hadani aure da Aishatu Yar Uwa ce itama auren zumunci ne,daga Nan Bamu samu Haihuwa ba har Ismail yayi Aure shima a can kauye,sai da ya haifi Yara uku sannan aka yiwa Kursum Aure a kauyenmu itama ta Haihu Daya,duk Ni Allah Bai bani Haihuwa ba har Iyayenmu Suka rasu sai Yan Uwa da dangi,wannan da kike gani Shine Alhaji Ja'afar Wanda shima a Sokoto na sanshi Amma Asalinsu Yan Yemen ne kasashen Larabawa,kasuwanci ya kawo su Nigeria Sokoto suna da company Wanda a lokacin suna da Company na Yogourt da Kuma kamfanin Dake sarrafa Fulawa,sabo da Haka suna bi kauyuka suna siyen madarar shanu da Alkama Wanda a lokacin sana'ar mu kenan a wajen mu suke siya,mun Saba sosai muna mutunci da Alhaji Ja'afar lokacin ya Dade da Auren Mummy har da yaronsu Ahmad Yana shekara bakwai lokacin,su dama masu kudi ne da danginsu duk suna zuwa,ita Mum Yar Sokoto ce,bafulatana ce ya ganta ya aure ta sabo da sonta da yake Yi,Tun Bai Jin hausa har ya koya ya Zama Kamar bahaushe shima ga matarsa bahausa,Tunda yayi Aure ya dawo Nigeria gaba Daya da Zama Amma yanayin Lagos ya fiye Masa Dadi shi yasa yayi gida a can komai nasu a can,Ni Kuma mun Saba mun Shaku,Ja'afar yana tausaya min rashin haihuwa,lokacin akwai wata Yar Uwarsa Hajiya Sumayya,Sumayya marainiya ce gaba da baya sai Dangi Su Ja'afar kenan, Danginsa ce Amma Iyayenta sun rasu,a cikin Dangin Summayya Ja'afar shi ya taho da ita Nigeria ta Dan zauna a Wajensa na Dan watanni, a Nan ta samu wani Wanda shi a Nan Nigeria yake shima Kuma a Sokoto Amma shima asalinsa Dan Sudan ne,ganin balarabiya fara sai ya zauce sabo shi Yana da duhu ma bakin Balarabe ne,aka hada su Aure da Sumayya,Dan Sudan dai yayi Aure Bayan shekara Uku Sumayya ta Haifi Yarta mace kyakyawar gaske aka sa mata suna Aamna,Idan baza ki manta ba Aamna Ina zuwa dake wani gidan Yan Sudan a Cikin garin Sokoto birni,duk Hutu Ina kaiki wajen wasu Dattijai,Aamna Tace ae,Baba yace to kakanninki ne na wajen Uba Aamna,Wannan Ja'afar da kike gani Shine Dangin mahaifiyarki Sumayya wacce ta Dade da rasuwa,Katsam Bayan ta haife ki da shekara Biyu Babanki Rahil menk ya gudu ya bar kasar,aka Neme shi aka rasa,sabo da taurin Kaine da shi,bashi da tausayi, Jaafar ya Shiga Bincike Ashe karya yayi ya auri Sumayya matansa Uku a Sudan da yaransa manya,Ashe Auren sha'awa yayi ya gudu ya barta,lokacin Jaafar ya bani Amana Kan na kula da Sumayya,Muna Haka ciwon Hawan jini ya kamata daga Nan sai ta kamu da ciwon sugar Bata Dade ba sai ta rasu,Ja'afar yayi kuka dangi suka zo suka tafi da gawar mamanki aka binne ta a can kasar su,ke Kuma kina Yar shekara Biyu Ja'afar yace tunda bani da Yara Allah Bai bani ba Kawai na dauke ki ya bani ke halak na kula da ke. Ni da Aishatu munyi murna muka dinga kula dake sosai sabo da Alkawarin Dana dauka shi yasa kika ga na barki kinyi har HND na dage na biya Miki sabo da bana so kiyi kukan Rashi,sannan takurar Aure da kika ga mun dage sai mun Aurar dake muna gudun kar wata masifar ta afka Miki ya Zama kin lalace a Hannun mu,shi yasa muke so mu rabu lafiya,Aamna Hawaye ya shararo Mata Tace Amma Baba ita Zuhra fa Kuma me yasa kuka fifita a kaina? Baba yace Zuhra Bayan kin shekara Hudu a Hannun mu Allah ya bawa matata ciki ta Haifo min Zuhra,kin San zuciya da Kuma son Kai da son da na daban ne,wallahi bazan boye Miki ba,muna haifar Zuhra gaba Daya Muka ji tafi shiga ranmu,a Haka ma kokari mukeyi muna danne zuciyarmu Dan kar ace kin lalace a Hannun mu Amma har ga Allah Aamna munfi son Zuhra da ke,shi yasa Baba Ni ka Bari nayi school Wato na lalace ita Zuhra iya secondary tayi aure,sannan har Sweety Zuhra kake ce Mata fa. Mama Tace ae ai munyi kokari ma duk abinda kike Mana ke rike kin ma ai munyi kokari bazan ji tsoron ki ba,Aamna Tace tunda na taso nasan Kuna duka na ku hantare Ni Ashe duk fakewa kukeyi da naki aure Ashe dama tsana ce?Mama Tace ke dalla fitsararriya lokacin da Danginki suka Yi watsi da ke shi Kansa Alhaji Ja'afar din gashi Nan ya sake zuwa ko duba ki,in Banda Dangin Babanki da muke kaiki kaf Dangin Uwarki ba Wanda ya sanki domin tunda Ja'afar ya Bamu ke ya tafi sai labari muka samu sun bar kasar ba a San Ina suke ba,sai dai Hana rantsuwa Muna Jin sunansa a Radio Yana tallafi iri iri a kasar nan. Alhaji Ja'afar dattijon kirki me Kamala yace Bari Nima nayi magana,lokacin Dana Baku Aamna yarda da aminci tare da tausayawa yasa na Baku ita Amana,ku kanku Kun San Ina da arzikin rike ta,Kuma Dana Baku ita sai Dana Baku makudan kudade Wanda Aamna zatayi karatu har matsayin Degree,Kuma Ni bazan ce ba kuyi kokari ba koma Mene kunyi kokari Kuma mun gode Allah ya saka,Amma Kun San dai Aamna na bada gudunmuwa na kudin daukan nauyinta,Baba yace kwarai muma min Sha wahala da ita,Bata da kunya Bata da tarbiyya gata Nan,Aamna Tace ai tarbiyyar kuce Ni Kuma wallahi Ina da tarbiyya, Haka tunda na taso nayi wayo nasan Kuna nuna banbanci tsakanin Ni da Zuhra,Ni za ayi ta dukana har girma na,Ja'afar ne yayi murmushi yace ya Isa Haka,ke Aamna Har abada Iyayenki ne ban son sakarci,Mummy Tace ikon Allah Ashe Aamna ce Yar Sumayya shi yasa na rasa Ina na santa mashaallah,Ja'afar yace lokacin da Muka Baku Aamna bayan mun koma lagos Arziki na ya bunkasa,daga Nan Kuma Mummy ta Haifo Kanin Ahmad Saddeeq,na tattara Muka koma Colombia da rayuwa,a Nan aka haifar min Auta Humaira Wanda Candy zata Yi kwana Nan,Haka Saddeeq shi nutsatse ne yayi aure da matarsa harda yarsa,Zaman da Muka Yi a Colombia shi ya jawo Babban Dana Ahmad ya lalace da shaye shaye,na rasa yanda zanyi da shi wallahi,mun rasa ya zamuyi ya shiryu,abin ya dame mu,Alhaji Ja'afar ya nisa tare da cewa yaki aure bare yayi wani Aiki Sai dai kashe kudi ya sani Kawai da shaye shaye. Baba yace tab Ahmad din?Aamna Tace Baba shine fa Wanda ya mare Ni ranar Nan da ka bini Titi zaka Duke Ni ka tuna,Wanda ka karbi number dinsa Wai zai koya min tarbiyya? Baba ya daura hannaye a Kai yace lailahaillallahu wannan kwallon shegen Yaron Dan giya? Ai yayi suna kaf gari an San da zamansu,sai dai Kuma Yana da Dan Hali me kyau ta wani bangaren,Daddy ya kwashe duk abinda Ahmad keyi ya fada musu yace wani abin ma Sai Kun gani da idonku wallahi na rasa yanda zanyi,Ashe Aamna ke kika Yi Jinyar Mummy? Dariya Aamna tayi Tace ae Daddy,Baba yace ja'ira Ashe ma Dan uwanki ne,Baba ya kalli Daddy yace game da matsalar Danka Ahmad Kawai a bashi Auren Yar Uwarsa Aamna a daura musu Aure ku Kai wa shege ita gidansa,Ni Kuma nasan Aamna itama irinsa ce Dan ba mutuncin gareta ba suje can suyi ta fadansu har a samu ko Allah zai shiriyarsu sabo da itama Aamna ba wata ta kirki bace Tace ta daina Zama ta gari,Nan take Daddy yace Kuma fa Haka ne Ahmad Yana bukatar jajirtacciyar mace marar tsoro,Mummy Tace hmm ai Ni Naga Drama a Hospital suka dinga fada da juna ba Wanda ke barin wani idan Haka ta faru zanfi kowa murna,Aamna kuwa Hankalinta ya tashi matuka sabo da tasan ma Ahmad kashe ta Kawai zai yi,Kuka ta saki Tace yanzu Dan shaye shaye za a bani? Sabo da anga Uwata ta mutu ubana ya gudu ya barni shine za a min Haka,Mama Baki Bude Tace Aamna mene Haka? Dan Uwanki ne fa,ai Hannunka baya rubewa ka yanke ya Yar, yo tun yaushe da azaba ta ishi mutum Nawa aka Yi Hannu da kafa mutum da Kansa zai kai Kansa Asibiti yace wayyo Allah Likita yanke min na huta cewar Aamna,Mummy Hannun Aamna ta riko tare da mikewa ta ja Aamna gefe tana Mata magana a kunne cikin Rada,Aamna ta washe Baki Tace to na yarda. Baba ya tabe Baki yace Alhmdllh Allah ya yanke Mana zaman Yahudanci,Daddy kuwa Dariya yayi kawai sannan yace akwai wani gidana Babba ne Dana Gina a Nan Kaduna ba nisa da Nan Unguwar Taku na mallaka maka shi halak malak,sannan Zan baka Million Uku ka ja jari,Baba Hanci ya rike kamar mace ya rangada Guda Ayyiriririri....,Dariya Aka dinga yi,Ranar dai sai da suka Gama shirya komai Har dangi an Kira a waya cewar Nan da sati Daya za a daurawa Aamna Aure, kowa yayi mamaki,ikon Allah Wato aure idan yazo wani shi kanshi a shekarar Bai San zaiyi auren ba,Aamna dai ko a jikinta sabo da sun Gama shirya sirrinsu da Mummy ba Wanda ya sani,Gidan da aka bawa Baba Suka tafi har furniture an zuba a gidan, flat madaidaici me dauke da part biyu,ko Ina yasha tiles ga flowers da komai,gidan a kalla zaici mota Hudu a ciki iya wurin parking,Aamna da Mama sai Murna,ranar Abba ya bada kudin auren Ahmad dubu dari biyu Suka tafi cike da murna,Zuhra Suka sanarwa komai murna Kamar me Ita kanta Zuhra dama ta Dade da sanin basu da Alaka da Aamna ko a kamanni Aamna da Larabawa take Kama,Ita kuwa Zuhra Ana ganinta anga Yar Mama da Baba,Yan Uwa da abokan azirki Suka dinga zuwa ganin sabon gidan su Baba,Aamna a waya ta Kira Kawarta Siyama ta fada Mata komai,ai Siyama Murna Kamar tayi hauka ga Kuma mamaki Aamna ba Yar su Baba bace Ashe Shuru akayi,Amma duk da Haka Aamna ta Sha Jin zancen a Kauye,idan ta tambayi Mama ko Baba sai suce karyar mutane ce,,Aamna zata ma riga siyama Auren ma Ashe,Washe gari tare da Siyama aka maida kayan su Aamna na bukata sabon gidansu,Faisal saurayinta shine ya dinga jigila da motarsa har Suka tare,Baba Kuwa Ya samu ya fara Harkar Sana'arsa ta siyar da kayan masarufi jari ya samu. Tunda an San Auren da za ayi ba Wani shiri aka Yi ba,Saura kwana biyu daurin Aure Mummy,Daddy,Mufida matar Saddeeq da Yarta,sai Humaira Auta da Sadeeq Suka taho Kaduna gaba Daya a gidan Ahmad Suka sauka,Yana ta Fushi shi fa an takura Masa da zuwa Masa gida,Bai San Aurensa za ayi ba. Ranar cikin dare Mummy ta haura sama Bedroom dinsa, Yana kwance Yana latsa wayarsa me tsada ga barasarsa a gefe Yana korawa,Mummy ta kalle shi tare da Zama saman Bed din,Yana ganinta cike da shagwaba ya dawo da Kansa saman cinyarta,Yana kallon Fuskarta Idonsa sai wani lumshewa sukeyi sunji kayan maye,Wata kwaya ya dakko a kasan Pillow ya watsa a cikin kwalabar giyar ya jijjiga,Nan take kwayar ta narke a ciki Yace Mummy Dan Sha kiji Zaki samu nutsuwa yanda na ganki nasan akwai damuwa,Murmushi Mummy tayi Tace please ban son hauka Ahmad,Ni zaka kalla ka Bawa kayan Maye?Dariya yayi yace to Mene ciki Dan kin Dan caake kema,Tsaki ta ja,Tace Magana nake so muyi,Ahmad yace Ina jinki Beautiful Mum,Harara ta watsa Masa Tace gobe ka shirya zamuje gidan Wasu Yan Uwan mu a gaisa,Nazo maka da manyan Kaya su zaka sa muje kaji?Baki ya turo yace kin San dai Ni bana gaisar da mutane,idan so kike kiji kunya Kuma to kije Dani Dan wallahi babu Wanda ya Isa nace Ina kwana ko Ina Yini bani da wannan lokacin,Mum Tace ae naji muje Haka,Yace sannan Kuma zanje da Giyata ne kin San bana Free karki ce ban fada Miki ba. Mummy ta jinjina Kai Tace Ahmad me yasa baka da tarbiyya da biyayya ne Haka? Ina mahaifiyarka duk abinda kaga dama fada min kakeyi,Baki ya tabe yace kin San dai bana karya gwara na fada Miki gaskiya,Kansa ta zame Dake kwance a cinyarta da sauri ya rike Mum yace please Mum zauna ki Sosa min Kai nayi bacci,sai kayi aure idan Haka kake so ai, Dariyar Yan giya ya shiga Yi ba ji ba gani yace Aure....Tab ai kuwa sai dai a dauki gawar matar,Mummy ta tsorata Tace Idan Muka daura maka fa Auren da ita sai me? Yace kisa ne hukuncinta,kasheta zanyi,Ni na tsani mata bare wani Aure Dan Allah Jeki Good Night ya furta, Tsaki taja Tace wannan Drugs din da kake Sha sune suke kashe maka sha'awar Mata fa,zaka yiwa kanka Illa,Murmushi yayi yace ai gwara Haka akan nayi Zina,Tsaki ta jasannan tayi ficewarta. Washe gari da Yamma Mummy ta kulle Ahmad a bedroom ta hanashi fita,Yana ta dukan kofa a bude shi Amma Mum Taki,yace aski zanyi fa yanzu I promise you wallahi Zan biki muje can,Sai lokacin Mummy ta Bude shi ya Sha ya bugu Yana tangadi ya fito ya fice,Machine ya Haye sai wurin Aski,Ai wani gashi Attach ya Siya Red and green yace ayi Masa calaba kitso me kyau,Gefe da gefe an kwashe gashin kadan,daga sama Kuma gashi Nan da yawa,Ai kuwa aka Masa calaba me Dan tsayi Suka zubo a kafada kadan,gemunsa ma Haka aka Masa Yar karamar calaba daga tsakiya da red attach,Kyawun da yayi ba a magana ka rantse daga England ya dawo,Kowa ya kalle shi zai rantse wani mugun arnen bature ne ba musulmi ba,Amma Fadin irin kyan da yayi Bata Baki ne sai dai ba tarbiyya idan an gani,duk inda ya gifta da machine sai Kallonsa akeyi,Mum suna Palo Suka ga ya dawo,Su kansu sunga kyan da yayi Amma Kuma bana Tarbiyya bane,Mummy tasan Halinsa Tace Kayi kyau,yace naga gidan da zamuje kin dauke shi da muhimmanci shi yasa nayi gyara na musamman. Sadeeq ya tabe Baki yace Amma ba tarbiyya ba,Zan ci Uwarka yayi Kansa Mummy ta rike shi,Mufida Tace Kayi kyau,yace yawwa matar mu,Humaira ma Tace Yaya Allah ya bani Miji me irin kyanka,Hannu ya Mika Mata Suka tafa yace Ameen,Ai Ni Handsome King ne,Daddy ya tabe Baki yace Kai dalla sakarai je ka shirya mu wuce, Ahmad Daddy yayiwa wani kallo ya Haura samansa Yana cewa azo gidan mutum a Dame shi,Gidanka ne Dan Ubanka gida na kace gidanka cewar Daddy shima,Mummy Tace Dan Allah karka jawo ya fasa zuwa ta bi bayan Ahmad tana lallashinsa Kar ya biyewa Daddy. Toilet ya Shiga tare da banko Kofar kamar zai ballata,Wanka ya sheka ya fito,Mummy tana gefen bed,ya shafa lotion ,Fuska ya Bata yace Mummy Zan cire Towel ki fita,Mummy tayi Dariya Tace to Babban mutum,Sai da ya Gama kalailaitarsa sannan ya kwalawa Mummy Kira,ta shigo da sauri da wata Arniyar farar Shadda me tsadar gaske Gezna,Harda Hula yace ohhhhh.....wannan Zan saka?....na shiga Uku wayyoooo ya Furta Yana zaga dakin kamar zai saka wuta a jikinsa. Ohhhh Mum....Mummy... Mummy....Mummy yake furtawa Yana zagata a dakin,Tace Ahmad Ni din ko? Fuska ya Bata yace na fasa zuwa akan na saka wannan kayan,Tace Dan Ni fa zaka saka,Ohhhhh.....ya sake furtawa Yana girgiza kafadunsa kamar Yaron yaye, Dariya Mummy tayi tare da fisgo Hannunsa ya zille Yana ta Bata wahala sai da kyar ya tsaya ya saka Boxers Kamar zaiyi Ihu Haka ya saka wandon Shaddar wani dai dai shi cif kamar an gwada dinkin zamani fitted na matasa,Singlet Mummy ta bashi ya saka sannan ya saka Rigar Shaddar me Hannu dogo links cif cif shi,ba karamin Arnen kyau yayi ba,Hula kuwa Mummy sai hakura tayi yace bazai saka ba,Haka ta barshi,tana kallo ya dakko farar sarkar Azurfa ta maza wata Yar siririya karama ya saka,Mummy Tace Kayi kyau kuwa Amma sai dai a hausawa ba tarbiyya bace,Yace Mum ku ai local ne Baku San wanka ba Sam,takalmi fari half shoe ya saka,wayarsa kuma Silver color,Glass Brown and white ya saka,Kowa ya kalli Ahmad yasan ba karya Allah yayi halitta a Nan,Mummy tana murna ta fesa Masa turaruka ya tsaya a gabanta yace ya kika gani,Babban yatsa ta daga Masa,Murmushi yayi Suka fito,Ai duka su Daddy sakin Baki Suka Yi suna kallon yanda yayi azabar kyau,Daddy farin ciki ya kamashi Allah sarki mahaifa,yace da ace Haka kake Yi duk da dai kitson da sarkar ba tarbiyyar hausawa bace ai da yafi sauki sauki, Sadeeq yace the Handsome King,Humaira Tace wow I'm proud of you Yaya King,Comfirm...Confirm ya Furta Yana wani basarwa yace Ina Mufida? Da sauri ta fito dauke da Yarta sun Sha gayu Suma,yace kinyi kyau matar mu, Sadeeq yace Kanin miji ne ke wannan wasan ba yayan Miji ba,Baki Ahmad ya tabe yace ku kuka San wani Kani da Yaya. Ko da aka zo shiga mota Ahmad yace Bayan anyi min gorin mota harda kwace motoci na a machine Dina zanzo,Daddy ne ya balbale shi da masifa Kai wanne irin banza ne Wai? Ana gabas kana Yamma dalla je ka shiga waccen motar,Ahmad yace wancan bakar Haba ai sai dai ku ku koma cikin bakar Ni da Mum mu Shiga fara ko na fasa tafiyar wallahi ku baku san wanka ba,Dole Haka Daddy ya kwashe sauran a Daya motar baka Sadeeq ya tuka su,Mummy kuwa suna fara ita da Ahmad sun hakimce a Bayan mota Driver Yaja Suka wuce sai sabon gidan su Aamna. Aamna kuwa dama Mummy ta sanar musu da zuwansu sabo da Haka ita da Siyama Suka shirya abinci iri iri sannan suka Yi wanka,Aamna ta shirya cikin wata sabuwar bakar Truskysh gown me adon Golden,tayi masifar kyau sai ta fito Kamar wata balarabiya,Baba ma Tasha shaddarsa,Mama tasa Atamfarta maroon,Siyama kuwa an zuba lace dark Green,Mama ce ta ja Aamna Bedroom ta zaro wata laya ta makale Mata a kanta cikin gashinta,Aamna Kamar tayi kuka Tace Mama har yau Kuna wannan shirkar ga ta Rannan a kaina kin hanani cirewa layu har biyu,Mama Tace ke dalla ta farin jini ce,Haka aka sawa Aamna dole ta yafa mayafinta Wanda ta Sha acuci,Wani guru Mama ta sake dakkowa tace lallai sai Aamna ta Daura a Hips dinta, Aamna zata Yi kuka Tace wallahi kin San naci kashinki da fitsari idan na tsine Miki sai ta Kamaki,Zan tsine Miki idan Baki daura ba,Aamna tana gani ta dage Riga har wandon ciki aka daura guru sannan ta maida kayan ta fito palonsu hadadde Kamar zata Yi kuka ta zauna tana Danna Yar Wayarta Vivo. Suna Haka Suka ji shigowar motoci,Aamna gabanta ya fadi,Siyama kuwa tuni ta leka ta window har Sanda Ahmad ya fito ta haukace gaba Daya tana lallai Aamna wallahi ku Larabawa ne da gaske gashi na gani,kalli danginki Kan uba kaga wani tantirin Dan Iska Amma duk yafi kowa kyau da iya wanka,Aamna ta Mike ta leka itama tace ai shine Angon,Siyama Tace Yau mun Shiga Uku kashinki ya bushe da gani Zaki ci Ubanki,Aamna Idonta ya kawo kwalla Tace wallah bazan taba sonsa ba,Dan giya ne,idan Kuma ya shiryu fa cewar Mama,Aamna Tace Idan ta dalili na ne sai na yarda Ina sonsa idan ya shiryu sai na gudu na barshi Kinga na taimaki Iyayensa,ko Dan Iyayensa Zanyi sabo da yanda suke mutanen kirki masu taimakon musulmai Bai ci ace suna da Dansu irin wannan ba,Siyama Tace bafa a Wasa da so,karki Bari ya kamu da sonki kice Zaki Wasa da zuciyarsa idan ya Gane ba sonsa Zaki ba kin Gama yawo,na Baki shawara idan Zaki so abinki ki soshi karki ce ban fada Miki ba Aamna ba a Wasa da zuciyar mutum a so,Aamna Baki ta tabe Tace wannan Zan so? Zan dai je da yanda Mukayi magana da Mum,ba ruwanku. Sallama sukayi aka amsa kowa ya shigo a nutse,Baba Yana musu Sannu da zuwa,Nan da Nan Su Siyama suka cika gabansu da Abinci sai lokacin Ahmad ya shigo ya tsaya Yana waya a waje,Ganin Aamna ya bashi mamaki yace Kai keeee......Aamna ma Tace kaiiiii......Ran Ahmad ya baci yace Wai Mum dama gidan wannan zamu wani zo? Daddy yace zauna Malam,Ahmad yace Ni bazan zauna ba Ku Gama mu tafi Ina da abin Yi,Siyama Tace tab a ranta,Zuhra ce ta shigo Amarya taci gayu Adam ya sauke ta,Itama gaisawa akayi ta zauna,Ahmad fafur kin Zama yayi ya zuba Hannu biyu a Aljihu ya tsaya kerere Kuma ba Wanda ya gaisar ko kallon arziki Bai musu ba,Baba shi Kam murna yakeyi Aamna ta samu Miji sai ya kalli Ahmad yace Sannu Sarkin matasa,na baka Sarautar Sarkin matasan Nigeria,Ahmad wani murmushi ya saki ba shiri,Aamna ta wani washe Baki itama ganin irin kyan da yayi,a Haka Daddy ya bada tarihin Aamna da dangantakarsu da Ita,Tsaki Ahmad ya ja tare da zaro Yar karamar kwalabar giyarsa a Aljihu ya kwararawa makoshinsa,Aamna ya kalla ya galla Mata Harara tare da cewa daina kallo na,Tace na kalleka din Kai da wanne idon ka kalleni,ransa ya sake tunzura ya kwada Mata Mari a saitin Idonta Nan take ta durkushe ta saki kuka,Da sauri taro ya watse aka dauki Aamna zuwa Asibiti,shi kuwa Ahmad a waya ya Kira Mashkoor ya dauke shi a machine suka Yi tafiyarsu. Daddy kamar bakin ciki ya kashe shi ransa ya baci ganin yanda aka mannewa Aamna Ido Daya da auduga da plasta Kuma akace Nan gaba sai an Mata aikin Ido,Tunda suka koma gida Basu ga Ahmad ba har kwana biyu ta cika Wanda itace Ranar daurin Aurensa Bai Sani ba. Mummy a waya ta Kira Ahmad ta sanar Masa da Aurensa,ya zaci Wasa ne ya dinga dariya yace Mummy kina da abin Dariya to idan hakane a daura Auren na Amince, Mummy tayi Dariya Tace ka yarda kace? Yace Yeah..Yana dariya Wai Wasa ne, Daddy kuwa ya tattara mutanensa Dana Baba a masallacin Unguwar har Mashkoor ya sa aka Nemo su duka sabo da Suma su Zama Shedu,Ahmad Yana can gidan Mashkoor Yana ta sheka bacci, Ranar Juma'a Ana Idar da Sallar Juma'a da Shedu walliyan Amarya da wakilin Ango suka karbi Aure Nan aka Daura Auren Aamna Rahil Menk da Ahmad Ja'afar Yabalash, Kan sadaki dubu dari,Su Mummy lefe suka yiwa Aamna na gaske Akwati goma Sha biyar,Ahmad ranar ya dawo gida sai gani yayi su Baba duk sun Hada kayansu zasu tafi ba Wanda ya kulashi,Mummy ce ta shigo Bayanta Aamna Amarya ce sanye cikin wani material Brown yasha kyau,idon Aamna Daya yasha plasta a manne da Daya take gani,Yana ganin Aamna ya Mike yace me wannan takeyi a Nan Mum?Mummy ta Bata Rai matuka Tace matarka ce Ahmad,Daddy ya shigo yace yau Shedu sun sheda an daura maka Aure da Aamna Yar uwarka Kuma marainiya sannan da Amincewar aka daura, ta Zama Amana a wajenka,ka sani Aure ba Wasa bane,idan kayi shirme Allah bazai Barka ba,Kuma wallahi ka koreta ko ka Mata Illa ban yafe maka ba Ahmad. Mummy Tace gata Nan wallahi kaji bazan rantse a banza ba babu Wasa yau aka Daura muku Aure shi yasa nace Rannan ka bimu muje na kaika ne Dan kaga surukanka,Nima kaji na rantse Idan ka koreta ko kayi gigin sakinta bani ba Kai ban yafe maka ba,Kuma Matukar ka saketa Allah ya Isa Nono na daka Sha,sabo da Haka gata Nan Amana da kayanta,Nan Ahmad yaga me Gadi Yana ta shigowa da kayan lefe Yana kaiwa sama Daya dakin da ba kowa Wanda Mummy ta zabawa Aamna a matsayin nata,duk abin bukatar Aamna an kawo Mata abinta,daga Nan Mummy Tace Mashkoor ku shigo,Suka shigo suna tangadi,Mummy ta kalle su Tace gwara da kuka zo yau nasan ku shaida ne a gabanku aka Daura Auren Ahmad sabo da Daddy da Kansa ya gayyace ku Kuma Kun gani,Mashkoor yace kwarai King a gabanmu aka Daura muna ta so mu fada maka Amma wayarka Taki Shiga gaskiya ba a kyauta Mana ba,anci Amanarka King a gabanmu muna gani aka Daura Sadaki dubu Dari Daddy ya bada cewar Jibson. Bash yace Kuma Daddy yace kayi aure yanzu mu rage zuwar maka gida wannan fa ba Adalci bane King,Ahmad da yayi mutuwar tsaye yace shima cikin kwaya me yasa Baku Hana an daura Auren ba,me yasa Baku rotsewa liman Kansa ba,Daddy ya kawo securities ko Ina King,Ahmad yace Good za aga abinda ba a so kuwa,Mummy Tace kaji dai gargadi Kai ka sani,ta kalli su Mashkoor tace lalatattun banza ku fita muje marasa tarbiyya,Haka Suka fito ransu a bace,Ahmad Yana kwalawa Mummy Kira kizo Mummy ki tafi da Yar mutane,Zan Mata Illa,Zan kashe ta ne,kizo ki tafi da ita,Mum....Mummyyy.....Ahmad ya dafe Kansa kwaya ta motsa Nan ya Shiga hauka da tangal tangal a palon,Aamna tana kallonsa a ranta Tace kaddara ta hau kaina na shiga Uku,me yasa na yarda aka Daura Auren,Wayar Hannunsa ya tarwatsa da kasa,Wandonsa Kamar zai Fado zabar Ass down na iya shege,Ya kalli Aamna yace ke bi Mummy ki tafi kafin na kashe ki yanzu,Aamna Tace wace zata bi Mummy? Ai wallahi Zama daram sai dai mu mutu tare,Zan Miki Illa fa,Illa ai ka rigada kayi min ita tunda ka nakasa Ni ka maida Ni me Ido Daya,waye zai aure Ni a Haka,ai Ina Nan a matarka Zama daram wallahi yaro baka Isa ba kayi kadan Aamna ta Furta da karaji tana dukan Table,yace ke Ni Zaki nunawa hauka,Kai din wa Kai din me,me ka Isa kayi,Ai ransa ya Gama baci ya bita da gudu Suka tafi tare,ta haura Sama da gudu zuwa dakinta tana shiga ya damko gashinta,Tace wallahi ai dambe ne Nima na Iya Suka rukuma kokawa. Kici kici suna Nishi Kamar zakaru,ya dauketa ya makata a saman Bed,ya bita zai jibgeta ta samu tare da makalkale shi ta cikwikwiye shi,Taki bashi damar dukanta,gata da karfi itama Suka dinga kokawa Baji ba gani,sai da suka gajiyar da kansu sannan ya saketa ya dawo Palo ya zauna a kujera Yana maida numfashi kamar Wanda yayi tsere Itama palon ta dawo gashinta ya watse ta zauna tana Nishi itama taji jiki. Yana Nishi yace kin gaji kenan?,Tace na gaji a Ina ai ban gaji ba sai dai mu mutu wallahi,yace to Bari na huta na samo power kiga yanda zanyi da ke,Aamna Tace Nima Bari tawa power din ta dawo ka gani idan Zan kyaleka. AsmaBaffa 10/26/21, 8:51 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 21-25 FREE PAGE DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER TA 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER 08033933642 Official By AsmaBaffa Page naku ne BESTYNBEELAT UMMU LATEEPHA M BELLO SA'ADATU TIJJANI UMMI DEEJAT NAFEESAT UMAR MUHAMMAD. Yana Nishi a ransa yace shegiya karfi ne da ita,Aamna kuwa mikewa tayi Tace Bari muje mu gaida Ubangiji wani kuwa sai dai su gaisa da barasa,a fusace ya Mike sai ta zura da gudu tare da fadawa dakinta ta saka key,Yana huci yace Zaki sani wallahi sai dai idan baza ki fito ba Useless kawai,Key din machine dinsa ya dauka tare da ficewa ya bar gidan gaba Daya,Ita kuwa Aamna wanka tayi tare da Gabatar da Sallar Magriba,tana zaune tana Azkhar har lokacin Sallar Isha yayi ta Gabatar sannan ta Mike tare Shiryawa cikin wasu kayan baccinta doguwar Riga ce red me sililin Hannu ta wuce gwiwa sosai ta Mata kyau,Kayanta ta Shiga Shiryawa sai da ta tsara komai fes sannan ta kwanta saman gadonta yunwa kamar zata mutu,Kitchen dole ta fito ta Nema Amma wayam babu ko Lipton a ciki bare wani Abu na dafawa,Kugu ta rike Tace Kan bala'i Bari ya shigo,Zama tayi tana jiransa Aamna Bata San shi sai safiya ko tsakar dare yake shigowa ba,Yana can Yana shaye shayensa. Bangaren Ahmad kuwa tunda ya fita wajen su Mashkoor ya je Suka zauna Yana cewa Mummy Wai kamata Ni za ayiwa auren dole, aure ban sani ba, Mashkoor da maye Yana karkace Baki yace Mum sunyi fuck up fa,Muguntar Daddy ce Kawai cewar Ahmad,Bash yace karka kyaleta kaci uban Yarinyar ai wallahi zata gani ko mu ka Bawa dama sai munyi maganinta,Ahmad yace Guys the things is Mummy tsinuwa tayi min akanta fa,Yar Iska Wai Dazu Dani zata Yi kokawa,Jibson Yana zuka hayaki yace Eyyyeeee.....hey this girl get heart woooo....but show her you are our king,Sweet Boy just Sample the Beb,Ahmad ya kalle su, su Biyar suna ta korawa ya daga zundumemiyar kwalaba ya kurba yace gata da karfi har Elbow fa tayi min a kirji,La'ilaaaaah....cewar Mashkoor Yana dafe Kai yace aci mamanta Guys,Ahmad cike da Takaici yace Hmmmm me....me...me....Mum tayiwa haka,a bani Auren wata Ina Zan Kai wannan nauyin Kai wallahi ma dole ta karba,she must Collect...am....wayarsa ya zaro ya Shiga Kiran Mummy dinsa,Mummy lokacin tuni suna Lagos ma,ta daga Wayar tace Ya akayi Ango,Kamar zaiyi kuka yace Mummy kizo ki dauke wannan Ajiyar Taki Zan fa Iya kashe ta,Zan kashe ta ne Mum,karfa ki sa nayi mummunan laifi tam,Tsaki Mummy tayi tare da kashe wayar Baki daya. Mikewa yayi Zumbur yace akan wannan trash din Mummy ta juya min baya,dole naci uban Yarinyar Nan,Zaga wajen ya Shiga yi,Ya dauki kwalabar Giya ya tarwatsa ta,kujerar da yake zaune ya dauka tare da yin jifa da ita,Su Kuma sauran sunyi tagumi kamar an musu mutuwa Wai Ana Taya Oga bacin Rai ne,Ahmad Bai koma gida ba sai 4pm ya shigo a make ya wuce palonsa tare da fadawa saman kujera ya kwanta Nan take bacci me nauyi ya kwashe shi,Ita kuwa Aamna da Yunwarta ta kwanta Haka da Asuba yunwa ce ta tasheta,Bayan tayi Sallah da Azkhar ta koma baccin Yunwa,sai 11am ta sake farkawa,Gidan ta hau gyarawa sai da ta Gama da room dinta da toilet sannan ta shiga dayan ta gyara,ta Shiga Dakinsa Nan taga Haduwar furniture gadon Kawai abin kallo ne, a Nan ta lalace tana kallo,sai da ta gaji ta gyara Masa ko Ina Neat Yana kyalli da sheki,Har Toilet duk ta Gama sannan ta dawo kasa a Nan ta ganshi Yana ta bacci hankali kwance,kitson calabarsa ta kalla ta leka Fuskarsa tana kallon Halittar Allah Iya Halitta,Tace tab Allah yayi Kira a Nan,waye zaiyi wannan in ba Allah ba,cikin Creazy Jean dinsa fatarsa duk a waje fara Kar da gashi kwantacce luf luf,Aamna Tace Uhmmmm.....sunanka Dan Zarra daga yau,kayi Zarra wallahi kafin a samu me Kama kafarka a kyau sai an tona,Habarta ta tallafe Tace kaga Dan baiwa....Fresh dashi...karya suke wani sweet Boy...ai wannan ya wuce Sweet Boy sai dai Honey Boy,Aamna tana nuna shi da yatsa Tace See Nose Alqur'an,Juyi yayi tare da Sosa Dan wuyansa,Aamna Tace ga Chest lafiyayye,Lips dinsa ta kalla ta Bude Dan bakinta tare da lumshe Ido Tace kiss mukeyi da shi ita kadai ta cuno Baki gaba tana feeling Wai suna kissing,Wani Iri taji a jikinta,Tace Kai da gaske na fara Jin dadin,Tunaninta ta kautar Tace kalli dalla ya wani kwanta da takalmi a kafarsa,a hankali ta tsuguna a kasa tare da zare Masa takalmin kafarsa a hankali ba tare da ya farka ba,Aikinta taci gaba da Yi sai da ko Ina ya dau kyalli da kamshi sannan ta leka waje taga me kula da Compound ya Gama gyara ko Ina na wajen,da Hijab a jikinta ta karasa wajen me Gadi,ya gaisar da ita Tace Musa ya kakeyi da cin Abinci a Nan gidan? Musa yace ai Hajiya duk wata Bayan Oga ya biyani kudin aikina Yana bani kudin Abinci na wata wata safe,Rana Dana dare,ai Hajiya Oga mutum ne me kyauta,Baki ga yanda yake taimakon na kasa ba,abinda nake so shi nake siya naci,ga kyautar kudi akai akai Yana bani,idan zanje ganin Iyali na Sha Tara ta arziki yake min,wayata ma Tekno dubu Arbain da biyar shi ya Siya min sabuwa dal,Aamna Tace yanzu dai kullum siyo abinci kakeyi? Yace me dadi ma kuwa Hajiya,tafiya Aamna tayi yunwa kamar zata kashe ta,Tace Bari ya tashi wallahi dole Nima ya dinga bani kudin Abinci na,Palo ta koma da Idonta Daya a manne ta Iske ya koma Bedroom Yana ta baccinsa,Bai tashi ba sai 2pm lokacin Yayi wanka ya hada Sallar Asuba da Azahar yayi ya shirya cikin jallabiyya ruwan toka,Yana zuba kamshi ya sakko kasa da Niyyar fita,Aamna wacce yunwa ta Gama cinyeta ta Mike da sauri ta kulle Kofar palon tare da sa key ta datse ta jefa key din cikin bra dinta tana kallonsa da masifa Tace wallahi ba inda zaka je sai ka bani kudin Abinci,matarka ce Ni a gidan Mijina nake sabo da Haka hakkinka ne nauyin ka ne ka sauke,Kai ya girgiza yace kina Neman rigima Dani,bana son Wasa da shirme,Ina da aikin Yi bani key Zan wuce Aamna Tace wallahi bazan baka ba sai ka bani kudin Abinci,Kai ya girgiza yace karki Bari kwakwalwata ta dau chaji Zan Miki Illa,Zan Miki Illa ki bude na fita ban son wasa,Aamna Tace wallahi yau baka Isa ba sai ka bani abinci,ka nakasa min Ido sannan zaka kashe Ni da yunwa,yace Mum ce ta kawoki kije wajenta ta Baki ko Ni Nace kizo gidana,bana sonki na tsaneki Akan me Zan Baki kudi na dalla Bude min kofa ya taso da masifa,Aamna ta rike Kugu sanye da Hijab Tace wallahi bazan bude ba,yace look ni bana taba Nonon Mata jikinsu ma bana tabawa ki dakko key ki Bude min kofa kin San Zan iya kwata a cikin Bra din Taki Kawai ban son tabawa ne ya Furta Yana yatsina Fuska,Tace Bazan Bude ba wallahiiii.. ta karasa da kukan wahalar Yunwa. Sauri yake yi zai fita sai ya koma Sama ya fito da kudi dubu Hamsim Bundle na Yan dari biyar biyar yace gashi Zan Baki badan Ina tsoronki ba badan Kuma tausayinki ba Dan Ina so na fita ne Ina da Abinyi,Kudin ta karba Tace da karka bayar Mana Idan ka Isa,kaji dai tsoro na Yaro woooooo......cikin tsawar data razana ta yace Open the door,Ba shiri jiki na rawa ta zaro key ta Bude Masa ya fice a fusace tare da banko Kofar kamar zai ballata. Ita kuwa murna da farin ciki ya kamata ta dauki dubu biyu ko wanka Bata Yi ba ta gyara Hijab dinta tayi waje,ko me Gadi Bata aika ba ta fice daga gidan,a Unguwar tana tafiya taga wani Resturant da sauri ta Shiga ciki tayi Order taje Away na Jullof rice with salat and chicken,ta siyo lemuka harda su Icecrewm Yogourt ta dawo gida ta baje abinta a Palo taci ta koshi tayi dam sannan taje tayi wanka tasa wani gajeren Wandonsa ta zabo fari ya Mata yawa Amma ta saka Haka,ta dauki t-shirt dinsa baka ta saka sun Mata yawa Amma abinka da me kyau sai tayi kyau,Haka ta gyara palon ta Karo karfin Ac tare da kunna kallo tana kallo ta wani can saman Hannun kujera baza ma ta zauna a kujerar ba ta tale kafafu tana Shan Iceream dinta tana ta Dariya a Haka ya shigo gidan ya sameta,Kallo ya bita da shi ganin kayansa a jikinta tana Shan Icecream,Wayar charger ya fisgo da sauri yace kayana are you Mad,Da gudu tayi cikin wani daki ya bita da kyar ta samu ta buya a toilet,yace Zaki fito ne,idan kin Isa kina ji ke kece ki fito,Tace kaima idan ka Isa ka shugo,baka kunya fada da mace,Namiji da Kai kaje kayi da maza Mana idan ka Isa a tumurmusa ka,Yace Zaki fito ne sai na Ballaki Kuma wannan kayan da kika sa wallahi sai dai a kone su ban Haka skin da ke Idiot ya juya tare da komawa palo. Tunda Aamna tasan tayi laifi Bata sake Fitowa ya ganta ba sai washe gari ta fito sanye cikin wani Lace fari Riga da skert daf da ita tayi kyau sosai Sanda ta shigayi tana tafiya a hankali,a main Palo ta Iske shi yayi Order Breakfast ya hada tea lafiyayyen gaske ga chips and Egg da farfensun kaji Yana ci hankali kwance,Aamna ta hadiyi Yawu ta fito a hankali yaji motsinta Amma ko kallonta baiyi ba yaci gaba da cin abinsa,a gabansa ta durkusa Tace Ina kwana Yaya Ahmad,sai lokacin ya kalle ta kadan Yaja uban Tsaki,tace Nima yunwa nake ji,wata Uwar Harara ya aika mata,Dan Allah San min ko na fita na siyo? Dama jiya na fita na siyo Abinci na manta ban nemi Izninka ba ka yafe min,Cikin tsawa yace Ina ruwana da rayuwarki Ni da Zaki tafi ma bangon duniya Ina ruwana,wallahi bazan je bangon duniya ba salon idan tashin kiyama yazo yajuju da majuju su fara ta kaina,Kinga ki daina Shiga harka ta,na fada Miki kiyi rayuwarki Mummy ce ta kawo ki to duk wahalarki sai ki fada Mata,Yar wahala Kawai,Yar walagigi Kawai,Ai kuwa Ni gaskiya Raina ya biya da wannan Abincin naka ka fada min Inda ka siyo naje na siyo ai Ina da kudi sannan ko ka bani naka na ci,Tana Gama fadin haka ta janyo plate din chips din gabanta ta fara ci Tace Dadi,sai ta dauke plate din ta gudu daki ta sa key,Ahmad ya dura wata Ashirya yace yau ba abinda zai Hana ban karyaki a gidan nan,Sa'anki ne ni? Aamna Tace ae daga bedroom,Sai da ta cinye tas ta fito lokacin ya bar gidan ma,ta kalli kwanikan Daya Bata duk abincin ya rage Bai cinye ba duka,ta zauna gaba Daya ta cinye sannan ta hau gyara gidan tana mita mutum sai yawon jaraba kullum Yana waje. Duk wani Aikinta sai da ta Gama sannan ta zaro Yar Wayarta Vivo ta Kira Mama suka gaisa da Baba,ta Kira Zuhra ma Suka Sha Hira,Siyama ta Kira karshe,Siyama Tace Amarya bakya laifi kin tafi kin barmu da Aiki a Resturant,Yaya Mutumin naki ko anyi abin ne? Aamna Tace Allah ya kiyaye na hada jiki da Dan giya,ke Siyama wallahi baya kaunar Mace,wannan ko tsirara Zaki zo gabansa baza ki birge shi ba,Dariya Siyama tayi,wallahi Aamna ga masifa kullum Fuskarsa ba Rahma Abu kadan Kuma sai masifa,wannan bazai shiryu ba,banga abinda za a Masa ya shiryu ba,to Ina ma yake Zama da har zai fahimci wani Abu mutumin da sai ya kwana a waje can ko sai cikin tsakiyar dare zai dawo,ga Dan Ido na Guda Daya a manne,Suna ta surutu har suka Gama ta fara karatun Qur'ani,Jin yanda aka banko kofa tasan Ahmad ne ko Sallama dama bayayi Yana shigowa yace ke koma dakinki kiyi karatunki ko ki koma masallaci ki tare,Ganin yanda ya shigo a buge sai ta tashi tsam tayi bedroom shi Kuma ya kwanta a saman kujera,Ya kunna tv ya kure volume karshe kida ya cika gidan a manyan speakers Yana sani yayi Kuma dole Aamna ta hakura da karatun Qur'anin sabo da yanda kida yake dauke Mata hankali,Fitowa ta sake yi,ai kuwa ya Mike a fusace yace ba nace ki daina matsowa inda nake ba ya dauki Remote ya jefe ta da shi da karfi ji kake kwas a goshinta,sosai taji zafi wajen ya kumbura yayi Mata kulu,Itama ta dauka ta jefa masa a bayansa,ta gudu ya bita cikin zafin nama Amma ta kulle Kofa Haka ya rabu da ita yace Zaki fito ne. Sai bayan Sallar Isha Aamna ta fito sanye cikin doguwar Riga Yar kasar masar,me shape sosai wata silver,ba karya tayi kyau,Mayafinta tayi Rolling ta dauki kudi ta fito,yau ma tayi sa'a sai ta ganshi a kwance Yana cin green Apple,Aamna cike da tsoro ta karaso inda yake wani kamshi yake na musamman,a gabansa ta tsuguna Tace Sannu da hutawa zanje siyo Abinci,Baki ya tabe sai da ya dauki mintuna yace Ina ruwana,mikewa tayi ganin masifa yake ji kadan yake jira sai tayi tafiyarta kuwa,taje tayi take Away sharp sharp ta dawo,Lokacin Yana Zaune Yana kallon wani American film, Sakwara da miyar kifi, ruwa Eva da fruits salat,tana ci tana kallon Film, . Wayarta ce ta hau Ringing tana dubawa taga Mama,da sauri ta daga,bayan sun gaisa Mama Tace Aamna ga fa kudin sadakinki Baki karba ba,Aamna Tace Ina sane da abina,suna Rai na,a ciki ki dauki dubu Goma kyauta,ki Bawa Baba dubu Talatin,Zuhra a Bata dubu bakwai,Siyama kawata a Bata dubu Uku Kinga dubu Hamsin ta Kare ko? Mama Tace Haka ne,to dubu Hamsin din a ciri dubu biyar a bayar Sadaka Allah ya Kai ladan kabarin mamata sumayya Allah ya Mata Rahma,a sake cire dubu biyar Abba na Daya gudu ya barni ayi Sadaka nayi tawasili da ita Allah ya shirye shi ya canja Hali,Mama tayi Dariya Tace ai duk kin rabar da kudin ba Haka akeyi ba,Zan dai cire na Bawa kowa abinda ya Dace sauran ai naki ne,Aamna Tace to koma dai mene abinda aka barmin a kaiwa Kawu Isma'il can kauye ya Siya wake da Alkama a ajiye idan sukayi tsada sai na siyar na samu riba,Nan fa Ahmad yace tab Riba kudin riba ai masifa ne, ka siyi Abu ka boye sai yayi tsada kazo ka siyarwa mutane,Wannan ba Business bane,Aamna Tace Kai baka ga laifinka ba barasa kwalaba Nawa kake dirkewa cikinka wlh kayi hankali Kar Hantarka ta tabu tam,Hannu yasa ya murde Mata kunne ta kwalla Kara,Mama ta waya taji Kara Tace lfy? Mama wani kwaro ne ya firgita Ni. Can Baba ya fisge Wayar yace ke Aamna Dan Ubanki kiwa fa mijinki biyayya,duk abinda yace kiyi bana son sakarci,Kuma ko me Zaki shuka ki shuka gaskiya kiyi gaskiya ato sabo da mu dangwali arziki da kyau,Aamna Tace yo Baba ai Gaskiya Ni a jinjina take da ita aka haife ni,dankwalin Aamna ne ya zame layar ta Guda biyu Dake soke a kanta suka bayyana,Ahmad Yana gani ya girgiza Kai a zuciyarsa yace mashirkiya,Ita dai Aamna abincinta take ci tana Dan juyowa ta kalle shi kadan sabo da faratansa na Hannu Dana kafa Daya Tara sunyi tsayi Kamar Arne Amma da gani suna Shan gyara wani fes da su sai dai ba a Yankewa,Allah yasa kayi bacci sai na yanke wannan uban faratan Aamna ta furta a ranta. Ganin tana ta Kallonsa Yaja Tsaki tare da mikewa ya dauki key din machine dinsa zai fita,Aamna Tace Ina zaka je da daren Nan Haka?Ni tsoro nake ji gaskiya,Kwafa Yaja a ransa ya furta Mummy ta Gama Dani,idan na Mata Illa tsinuwa ta hau kaina,juyowa yayi a fusace yace Allah ya taimakeki Ina son Nonon Mummy Dana yasha yabi lafiyar jikina Amma da kin Gane kurenki,Aamna ta kyalkyale da Dariya Tace au har yanzu Nonon Mummy Bai Gama bi maka jiki ba? Sanda aka haife Ni ko yaye Ni ba ayi ba aka samu cikin Saddeeq shi yasa ya cuce Ni na Sha gubar cikinsa,Aamna sake kecewa da dariya Tace ko shi yasa aka ce ka Dade a tsumbure baka girma ba Dan Mummy Tace har cutar koshokwo kayi Haka Kawai Aamna tayi karya Tace Mummy ce ta fada Mata,ai kuwa shi da saurin Fushi kwaya tana sashi saurin Fushi ai Kan Aamna ta rufe baki yace uwar Koshokwo nayi,Aamna ta Mike zata gudu Suka dinga zaga palon Nan sai ya kamata ya dake ta Itama ta guduwa,ta samu tayi waje Compound da gudu,fita yayi Yana huci ya hau lifan dinsa ya fice sannan Aamna ta dawo ciki abinta. Bayan Sati biyu da Auren Aamna kullum fada sukeyi da Ahmad ba Wani mutunci, Mummy ce ta Kira Aamna Tace,bayan sun gaisa Aamna ta saki kuka Tace Mummy wallahi kullum sai munyi fada ya Duke Ni saurin duka ne da shi Kuma yaki siyo kayan abinci kullum sai dai naje na siyo ko na aiki me Gadi shima Haka Mummy, Dariya Mummy tayi Tace Kuma wallahi Ahmad ya Iya girki sosai a haka,kin San nice na sallami Peter me dafa Masa abinci, Aamna ki Kara Hakuri,bazan turo Miki kudin Abinci ba Yana da kudi,kece Zaki San yanda zakiyi Masa dole ya Baki kudi ki zuba abinci a store kin Gane,ae naji to ta furtawa Mummy,Bayan sun Gama Wayar Aamna ta zauna tayi tagumi tana saka Taya zata sa ya siyo Mata kayan abinci ko ya bada kudin ta siyo tunda kudin hannunta sun kusa karewa. Bayan tayi Shirin bacci cikin wata Riga da wando farare masu laushi ta zuba kyau ciki,a Palo ta zauna tana jiransa ai kuwa taci sa'a yau Ana Sallar Isha ya shigo gidan Yana tafiya da kyar da yanda yake Gadara ya nuna yau baiyi shaye shaye da yawa ba,Sannu da zuwa Aamna ta Furta,ko kulata baiyi ba Direct sama ya haura ya fada toilet,wanka yayi ya fito tare da Gabatar da Sallar Isha ko Addua baiyi ba ya Mike ya saka wasu kayan bacci dark blue me digon fari Riga da wando,fresh milk ya sha sannan ya kwanta a Gadonsa Nan take bacci ya kwashe shi me nauyi,Aamna ta biyo shi dakinsa Wanda Bata shiga sai idan zata gyara,a hankali tayi knocking Shuru taji,tayi Sallama Shuru,sai ta bude Kofar a hankali saman bed ta hangoshi ya wani Yi dai dai Yana baccinsa,Aamna tayi murmushi Tace Allah sarki yayi bacci,a gefen bed din ta zauna a hankali gefen kafafunsa,Nan take ta tuna da taga faratansa ya Tara sun Sha gyara,Room dinta ta koma ta dauko razor blade sabuwa dal ta bare,a tsorace tayi shahada ta Dan rike Yatsansa kadan sannan ta fara yanke Masa farcensa daya Tara Yana gayu da abinsa,ta fara yanke su Daya bayan daya,gashi da nauyin bacci har ta Gama hannaye Bai ko motsa ba Kawai baccinsa yake Sha,ta dawo kafa ma ta yanke Masa tas ta gyara ta kwashe farcen data yanke ta zuba a trash da razo din duka,ganin Bai da Niyyar tashi ta hakura itama ta koma dakinta Bayan ta kashe Masa hasken wuta ta Dan rufa Masa blanket sabo da taji sanyin ac yayi yawa. Itama komawa tayi dakinta ta kwanta abinta,sai 2am Wayarta ta tashe ta sakamakon saita Alarm da tayi, Mikewa tayi tare da Gabatar da Sallah Nafeela raka'a hudu tayi Adduointa sannan ta koma ta kwanta,sai Asuba ta sake tashi tayi raka'atanil fijr tare da Sallar Asuba ta zauna ta Gabatar da Azkhar sannan ta koma bacci,10am ta tashi ta hau gyaran gidan,Compound kuwa me Gadi ya Gama gyara ko Ina har Garden,Dakinsa ta shiga karshe taji karar ruwa alamar ya tashi Yana toilet,bedroom din ta hau gyarawa komai ya koma neat dama shi Sam Bai da kazanta akwai tsafta,ko Ina kamshi ne ke tashi,toilet ya Bude ya fito daure da towel a Kugunsa karami Kuma a hannunsa Yana goge wuyansa ga kitson kalabarsa Nan sabo an canja Masa sabo sai wani sheki yake Yi Bai jika gashinsa ba sabo da Attachment aka saka yellow, red and green,Aamna jikinsa ta kalla lukwi lukwi sumulmul,Fuskarsa a daure ko kulata baiyi ba ya tsaya a jikin Mirror Yana karewa Kansa kallo,Muryarsa taji yace Sexy Guy,gemunsa da Sajensa ya shafa yace Fresh Guy,Aamna ta zaro Ido taga Yana ta yabon Kansa Yana kallon Kansa a mudubi Yana shafa kitson kalabarsa,Toilet din ta shige ta gyara masa a ranta tana jinjinawa tunda take gyara Masa gida Bai taba nuna yaji Dadi ba ko abin ya birge shi ba,harkarsa Kawai yake Yi,Tana wanke toilet taji Muryarsa Yana Kiranta Bush girl.....Bush girl....tsoro taji Kar Taki zuwa ya Mata duka a banza Fitowa tayi da sauri Tace gani,Wani murmushi ya saki me tsada yace Good girl Ashe kin Gane sunanki,da Hargowa yace Ina wani perfume a Nan sabo? Murmushi Aamna tayi tace ai na dauke shi Ni zanyi amfani da shi sabo da Naga na Mata ne Kai Kuma Namiji ne,wani Ashar ya dura yace kin San tsadarsa kuwa? Yo ba gidan mijina bane,Kuma ma kayan Mijina ai Nawa ne ta karasa da shagwaba,Tsaki Yaja yace why are you always looking for my trouble? Idan na balla ki hmmm common dakko min kafin Raina ya baci,Aamna Tace Idan kana son na baka ka bani kudin Abinci ko ka siyo kayan abinci a gidan Nan yanda Zan na girki da kaina. Wani Takaici ya kamashi ji yake kamar ya harbeta yace bana Baki kudin abincin ba uban me Zan Miki,Aamna Tace Ni ka bani Dan Allah yau naje kasuwa na shirya store da kitchen dina,kana min fuck up fa a gidana,kanta yayo Aamna ta fisge towel dinsa ya Fadi kasa ya dawo zigidir, da sauri ya dauki towel din ya daura kunya ta balain kamashi,Abu na farko a rayuwarsa da yake Jin kunya Bai so aga tsaraicinsa Amma wannan Yarinyar ta cuce shi,Aamna takawa tayi zata gudu ya cafko ta ya dakko belt din Wandonsa tana Ihu ya riketa Kam ya dinga tafkarta iya karfinsa,tana ta Ihu tana cewa banga komai naka ba,kayi Hakuri,bazan fadawa kowa,bazan cewa kowa ga Kalar abinka ba,ganin zai Mata Illa a banza Tace Tsinuwar Mummy a kanka,Yana huci Idonsa yayi jajir ya tsaya cak Yana haki,Ita kuwa Aamna da Dan Idonta Daya a manne ta Mike tana kuka Wiwi,ta koma toilet din ta karasa wanke Masa tana kuka ta fito zata fita kenan ya shirya cikin wasu kana Nan Kaya farare tas marasa nauyi wandon pencil irin na shakatawa a gida da Alama ba fita zaiyi ba yau,rafar kudi Yan dubu dubu ya jefo Mata yace gashi Nan ki Siyo Uwar kayan girki,last warning ba ruwana da ke,karki sake Shiga harkata,ke magana ma ban so ki min,Aamna Tace ai wallahi baka Isa ba Mijina Guda ai dole na maka magana,Kwafa Yaja yace to kuwa Zaki ci Ubanki wallahi. Key din machine taga ya dauka Ashe fita zaiyi Ba zato Aamna ta sa key din kofarsa ta kulle ta cire key din ta jefa a bra dinta Tace Yau ma baza ka fita Muna dakin Nan zamu yini sai dai yunwa ta kashe mu,lips dinsa ya tamke tare da rufe Idonsa kam tsabar bacin Rai,yace ban so Tsinuwar Iyaye ta shafe Ni,sannan gwara nayi komai Akan na taba Nonon mace Bude min kofa ko yanzu na karasa Miki idon Daya,Aamna ta tsaya sanye da Atamfa Riga da skert na lefe ne sun kamata sosai,Tace tunda aka auro Ni baka taba ko Dan Rungume Ni ba,Please yau kafin ka fita Ina bukatar warm Hug,just ordinary Hug,Nima yau Ina so na motsa jam'iyata,kina hauka ne? Meke damunki,Ni zanyi Hugging naki? wata Dariya yayi yace Ashe nine ma na ganki nace Ina so,kanki akwai motsi lallai,Aamna Tace to lallai zamu kwana a Nan,tsayawa Suka Yi a Gaban kofa har na tsawon minti biyar ba Wanda yayi magana,nisawa yayi tare da girgiza gashinsa yace open the door,Aamna tace Baby Hug me Mana ka fita abinka,tunani ya tafi idan ya duketa Mummy dinsa,idan yace zai kwace key sai dai ya zura hannunsa a Boobs dinta shi gaskiya Bai son taba Nonon Mata,Baya Yaja kadan yayi Dan tangadi sannan yace Okay ya runtse Idonsa sannan ya Bude hannayensa,Aamna tana murmushi taje ai kuwa ya cakumeta irin bai iya ba Kawai cakumarta yayi ita Kuma tana sani ta kankameshi ya fisge jikinsa da bala'i yace bazan tabaki ba din,kinyi kinji Dadi Bude min kofa,Tace yanzu kuwa ta dakko key ta Bude Masa ya fice a fusace,ya hau machine dinsa kenan sai ga Aamna ta fito da gudu tana wait wait...da masifa ya juyo sai yaga Ashe wayarsa ce ya manta,Tace ka manta wayarka Baby,fisge Wayar yayi tare da Mata wani kallon banza ya Bawa machine dinsa wuta ya fita,Aamna kuwa wanka tayi ta shirya tsaf ta Kira Siyama kawarta suka je kasuwa,duk kayan Abinci na more rayuwa sun siyo dai dai gwargwado,tare suka dawo a taxi Suka shirya kayan a Store tsaf,kitchen kuwa komai na amfani akwai dama,sabo da Haka Jullof rice sukayi da wake taji kayan lambu da nama,Zuhra ce itama tazo ganin Amarya suka zauna suka ci abinda suke so,sannan suka gyara wajen,Palo Suka dawo suna kallo,Zuhra Tace Kan bala'i gaskiya gidan Nan ya hadu ba karya,Siyama ta Mike a saman doguwar kujera Tace har wani bacci nake ji ga ac ta ko Ina,Suna kallon wani Indian Series suna Hira sai ji sukayi an banko kofa,Siyama da Zuhra sai da suka firgita,ita kuwa Aamna ta Saba ko a jikinta tasan shine,ya shigo dauke da Ledar take away a hannunsa,Yana ganin Baki ya sake daure Fuska Kuma ko Sallama baiyi ba Sannan kallo Basu ishe shi ba bare su sa ran zai musu magana,ba Wanda yayi magana yazo har inda Siyama ke kwance a doguwar kujera yace cikin tsawa keee....tashi Zan kwanta a Kan kujerata,ai da sauri ta hantsilo kasa ya haye tare da kwanciya ya wani Mike Yana wata Mika,su Zuhra sai kallon kallo,Suka Yi tsit a palon sannan Suka ce Ina Yini? Banza Iska yayi da su,da Tsawa yace bani remote ya dakawa Zuhra tsawa,ta Mika Masa abinsa Wai Gadara yake gidansa ne. remote ya dauka da Gadara ya canja Chanel suna kallo ya Shiga wata Chanel ta Yan Iska Wanda a tashar Watarana har Xxx suke saka wa,sannan sai tallan Magungunan maza Dana Mata na Kara karfin gaba,da tallan kayan sex,Shi Kansa Bai taba kallon Chanel din ba sabo da su Zuhra ya kunna,ai kuwa sai Suka ga Ana Nuno maza da Mata tsirara,sai aka koma tallan condom na maza,Yana kalla yayi wani murmushi yace mun gode Allah ya Kara basira turawa,ya kamata fa ku yo Mana wanda yafi Haka kauri wannan fashewa yakeyi Bama Jin dadin shiga da fita,Mata aka nuna daga pant sai Bra,Ahmad yace wow see Bebs wannan zata Yi min,Wata kanjamammiya aka nuna,yace ke dalla matsa Jibson ke son irinku, kunya ta lullube su Zuhra Suka Mike tsam tare da yiwa Aamna sallama,Tace tun yanzu zaku tafi Haba Dan Allah? Ai ko kulata basuyi ba suka hada karansu sukayi waje,tuni suka bar gidan. Yana ganin Haka yayi Dariya ya canja Chanel ya koma kallon kwallon kafa,Aamna ce ta dawo daga rakiyar su Zuhra,da kukan shagwaba ta shigo tana dire diren kafafu tana Haba Dan Allah....Haba...Dan... Allah Baby, wani Haushi ta bashi Takaici yasa Ahmad ya zaro Wayar charger ya kifa Aamna da ita ta gudu dakinta ta kulle Kofar ya dawo Palo Yana masifa Ni Zaki yiwa shagwaba,Baki San na tsani wannan haukan ba,aikin banza Kawai,wani Ihu ya saki Yana kallon yatsunsa na kafa Dana hannu,Jin Ihu sa yasa Aamna ta yo waje ba shiri tana cewa lafiya? a tsorace yake lokacin shi yasa yace fingers Dina,farce na Dana Tara Ina ji da su an yanke min,jikinsa ya kalla tsaf yace Aljani ne,Amma wannan ya cuce ni,Dariya Aamna ta dinga Yi Tace nice ta fece da gudu daki. Rasa abinda zai Mata yayi sabo da bacin Rai wuka ya dakko a kitchen ya ajiye a kusa da shi yace yau Zaki ga abinda Zan Miki ba ruwana da wata Tsinuwar Mummy. AsmaBaffa 10/26/21, 8:52 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 26-30 FREE PAGE DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne AGRA ANEESAH UMMIN HIBBAH ASMAU YUSUF RAHMA FARHAT MRS MJ PHAATIMAH Ranar Aamna Bata sake Fitowa ya ganta ba kullum sai ta tabbatar ya fita take Fitowa tayi abinda ya kamata har kwana Uku sannan yau Bayan tayi Sallar Isha taci abincin data dafa Tace Fitowa zata Yi ai ta San yanzu ya huce,a hankali ta fito sanye cikin wani Bum short sky da Riga t-shirt red ta zuba kyau ciki,tana Fitowa taga shima ya banko glass door din palon ma'ana yanzu ya shigo kenan,Yana ta uban tangadi ya fada saman kujera shirim Yana magana a hankali cikin maye shi kadai,Aamna ta kalleshi taga bacci zaiyi ta lallabo a hankali Tace ka koma bedroom ka kwanta,ya furta barrrr.......niiiii....aaaaa.....aaaa....Nan.....Aamna Tace no Nan bazai maka dadin bacci ba tashi ta Kama hannunsa kenan ya fisge hannunsa,sake rikewa tayi Tace taso ta janyo shi ya Mike da kyar Yana tangal tangal a Haka ta kaishi sama ya fada saman bed dinsa,tsugunawa tayi ta zare Masa takalmansa a hankali,ganin har ya fara bacci ta Karo Masa karfin Ac din ta kashe Masa light ta fita ta barshi tana tunani,Palo ta dawo ta zuba Uban tagumi tana mamakin Ahmad kullum cikin shaye shaye baya Free Sam,Tace wannan wacce kaddara ce Haka ta sameni,da wacce zuciyar Zan iya daukan wannan masifa,gashi na Bari an daura Aure ya zanyi,Sam bana birge shi duk shigar da nayi Bai taba kallona ya nuna na tafi da shi ba duk da Nima ba so nake ya Yana ba. Taya zai shiryu Haka,Ido ta lumshe ta kwanta a saman kujera tana ta sake sake a ranta. Dakinta ta Mike zata tafi Bayan ta Gama kashe kayan wuta ta sake leka shi ta gani ta hango shi kuwa Yana ta bacci Amma ya dunkule waje Daya Yana ta Rawar sanyi kamar zazzabi ne a jikinsa,dama taji jikinsa ya dauki zafi dazu,kamar ta wuce sai ta fasa ta shiga bedroom din,a gefen bed din ta zauna tana tunanin me zata Masa,Tsaki ta ja kadan ta shiga zare Masa Riga a hankali,jikinsa ta taba zafi zauuuuu,Toilet ta shiga ta ebo ruwa a Bowl da towel karami ta shiga goge masa jikinsa a hankali,kirar jikinsa ta shiga karewa kallo tana Dan goge Masa jikinsa da Towel,ita mamakinta Sam a face baiyi Kama da me Shan giya ko wani Drugs ba,idan baka sani ba baza ka taba ganewa ba,sai dai acting dinsa yanda yake abu ba tarbiyya kana gani,Ac din ta kashe gaba Daya sannan taji zafin jikinsa ya Dan ragu,a hankali take girgiza shi tana tashinsa Me Burkutu....me Burkutuuu.......Shuru,taceme giyaaaaa.....Shuru,ta girgiza shi shuru, Kuma Yana numfashi sai da ta Dade sannan taga ya dafe Kansa da Alama ciwo yake Masa Yana Nishi kadan yace Ohhh my God,a hankali ya Dan Bude idonsa,ba a wani hayyacinsa yake ba,ya fara Mika Hannu jikin Drower yace i need to take my drugs,Drower din ta Bude da sauri mamaki ya kashe ta ganin kwayoyi iri iri Kamar hauka duk na Maye,Salati Aamna ta saki Hawaye ya shararo Mata ta shanye da kyar,ta Dan duba Drugs din sai taga paracetamol,shi ta ballo ta dakko Masa ruwa da sauri ta Mika Masa Yana daga kwance ya karba ya Sha abinsa a kwance shi ba Wani ganeta yake Yi ba. Zama ta ci gaba da Yi gefen Bed din tana ta faman gyangyadi,so take Yi ta ga ya samu sauki,a ranta Tace ko Ina ruwana oho,Amma tunda dai lalura ce Bari na jira,tana Nan zaune taga ya fara Juyi ya hada uban zufa alamar zazzabin ya sauka,ac ta kunna Masa,cikin mayen baccinsa yace Mummy yunwa Zan Sha ruwa,Aamna ta kalle shi taga bacci ma yake Yi,da sauri tayi kasa ta hau dafa Indomie lokacin 11:30pm, sharp sharp ta Gama ta dakko da kankana wacce ta yanka Nan take,da sauri tayi sama,ta ganshi zaune a gadon ya jingina bayansa a fuskar bed din ya lumshe Ido,still ba Riga a jikinsa. Aamna ita ke shirmenta ba ganeta yakeyi ba ya bugu da yawa dishi dishi yake hango ta shi yasa ya kyaleta da lafiya yake da tuni taci duka,sabo da samun waje saman bed din ta haura ta zauna a gefensa Tace ga abincin,you have to eat something sabo da kafi Jin sauki,a hankali ya juyo ya kalleta ya turo lips dinsa gaba,Tace haba na Mummy ci Mana karka kwana da yunwa akwai Dadi wannan Indomie taji Hadi kaci sai kayi Santi,Kansa ya dauke can gefe,Aamna Bata hakura ba harda rera waka Wai Dan tuzuru....ya dawo mata,.....yanzu....da ba'ayi maka aure..... ba wa zai dafa maka....Oya Fadi kaima tana tafi,Dake a bige yake sai yace shima Nine Tuzuruuu......yawwa to Bude bakin ta furta tare da ebo Indomie a fork,.....ya Bude da kyar Yana kumbura,ta zuba Masa tana murmushi Tace Ehemm....mutumin kirki...maza Kara ci ta sake ebowa ya karba a bakinsa,Tace Good King...oya again....ya karba,yaji tayi Dadi sosai tana ta bashi Yana ci Yana ganinta dishi dishi. sai da ya cinye tas ta dakko kankana Itama Haka ta dinga bashi baya ko magana sai da ya Sha da yawa sannan yayi gefe can da Kansa Nan ta Gane ya koshi,ta Balle ruwa ta tsiyaya a glass cup ta bashi Nan ma a Baki ya shanye ta Kara Masa ya shanye,Tace Inye King din ba,Harara ya Aiko Mata tayi shuru,ta tattara kwanikan ta maida kitchen,shi kuwa Yana Jin karfi a jikinsa wanka yayi sai lokacin Yayi Sallar la'asar ,Magriba da Isha sannan ya kwanta bacci ya sake gaba da shi. Aamna shugowa tayi taga yayi bacci ga sallaya alamar Sallah yayi,baya kashe light sai ta kashe Masa tare da sake feshe room din da wani Room freshner me Arnen kamshi ta rufe Masa kofa taje itama ta kwanta. Washe gari da Ihu ya farka Daya tuna kamar jiya Aamna ce ta shigo,Nan ya tunano me tayi,wani ransa ne ya baci shi kadai ya dinga masifa har yayi wanka ya fito cikin wani gajeren wando ruwan toka da Riga brown t-shirt,Lokacin Aamna ta cakare cikin wani wando legins tight,pencil tayi kyau duk na lefe ne, Yar rigarta yellow me siririn Hannu cibiyarta a waje,a kitchen take tana shirya Breakfast kamshi ya cika gidan,ji tayi kamar ya fito da sauri ta fito ta sawa Kofar palon key Yana kallonta yasan cewa zata Yi bazai fita ba sai ya Bata kudi ko wani Abu,dama da fushinta ya tashi yau,yace tun kafin na Miki duka ki Bude kofa ko ki Fadi abinda kike so na Baki,bani da lokacin shirmenki yau,Aamna Tace Breakfast zaka ci sannan ka fita,kullum Ina matarka baza kaci Abinci na ba yau ba inda zaka fita a gidan Nan,sabo da ma baka da lafiya baka Gama murmurewa ba,Ahmad yace shine jiya kika shiga Zaki min fyade? to ta Allah ba Taki ba,nafi karfinki,Wai harda wani cire min Riga ke Uwata ce ko ubana,ke Wai matata ko?Dariya ya bawa Aamna Tace ae naji zauna ka jira Ni,idan naki fa?,kitchen ta shiga da sauri ta Hado komai a tire ta kawo gabansa a Palo ta Ajiye Tace Bismillah kayi ka ci na Bude maka ka tafi,sai da ya dauki lokaci sannan yace badan Ina tsoronki Zan ci ba,Dan Ina da abin Yi ne kawai yau,Aamna Tace a Haka zaka fita da gajeren wando? Ina ruwanki munafuka Uwar gulma ya Furta,Shuru tayi Tace Enjoy your meal,Bread ya dauka ya gutsira ya kurbi tea sau daya,sai ya dauki chips Guda hudu yaci yace to Bude min na fita,ba musu ta Bude masa,zai fita ya zuba Mata Rankwashi me zafi ya fita abinsa,Ihu ta saki kadan ta zauna ta cinye abincin nasa,shi Kam Machine dinsa ya hau ya fita da shegen kitson calabarsa,Wanda sai dai ayi ta binsa da kallo. Tunda ya fita Bai dawo ba sai cikin tsakiyar dare,yau anci sa'a Bai Sha komai ba,hannunsa dauke da Ledar take away na abinci,a gajiye ya shigo Amma yaga Aamna zaune tana kallon American film,Sannu da zuwa ta furta,Baki ya tabe ya haura sama abinsa ko kallo Bata Kai matsayinsa ba. Bayansa ta bi a hankali Yana jinta Bai kulata ba,Yana Shiga bedroom dinsa Wanda ya Sha gyara kamshi ne Kawai ke tashi,kafin ta Shiga ya kulle kofarsa tare da murda key Yana faman Jan Tsaki,Dariya Aamna tayi tana daga jikin Kofar Tace ya jikin naka? Kai ya girgiza yace Uwaki yake ciki,,ta rasu fa marainiya ce Ni,Yace to tayi ta mutuwa Mana Ina ruwana,Wai ke Baki da zuciya ne? Aamna Tace ae bani da ita My Husband,tana Jin tsakinsa ta juya ta koma dakinta ta kwanta abinta tare da Adduar bacci ta kwanta. Shi kuwa Abincinsa ya zauna yaci ya shiga toilet yayi wanka tare da brush,cikin kayan baccinsa dogon wando da Riga me dogon Hannu silver color wani yadi Silk sharara,Sallaya ya shimfida ya fara jero sallah ba nutsuwa ba komai da saurin masifa kamar zai tashi sama,idan yayi ruku'u ko Gama dagowa baya Yi zai sabe da sujjada, kafin kace me tuni ya idar tun daga Azahar har Isha,ko Addua babu Ya Mike Yana tunanin ma kamar Sallar Isha raka'a Uku yayi Amma ya fuske tare da furta Ina laifi ma na karasa raka'a dayar a raina Kawai ta cika hudu nayi ya fada saman bed yayi kwanciyar ruf da ciki sai bacci. Washe gari 9am ya tashi kasancewar baiyi shaye shaye ba,Room din dake cike da kayan Exercise ya shiga Yana ta motsa jikinsa sai da ya Dade sannan ya fito sanye cikin kayan gym dinsa bakake yayi kyau,Yana Fitowa ya Iske Aamna har ta Gama gyara ko Ina na ciki,kamshi yaji a kitchen lekawa yayi ya hangota tana ta soye soye, Shiga yayi fuskar Nan ba Rahma cikin Muryarsa ta Yan kwaya yace bani kasko zanyi girki,Aamna Tace ga wasu Nan ka dauka Mana Kuma ma ai gashi Ina girkin da Kai sai muci wannan,cike da bala'i yace da wannan nake so nayi,gidanki ne ko Ubanki ya Siya min kayan kitchen ne? ai kayan Mijina Kaya nane Kuma wallahi bazan baka ba,baka Isa ba kayi kadan kayi karami da yawa na baka kaskon nan, sabo da Nan gidan Mijina nane Kuma gida na yawwa eheee ....Mari ya dauke ta dashi garin Jin zafin Mari Aamna ta saki ludayi ya Fado saman kafarta gashi yasha Mai na suya me zafi Nan take ya kone Mata wani Dan bangare a kafarta,Ihu ta saki ta durkusa kasa Amma duk da Haka Bai kyaleta ba ya tallafe Mata keya ya dauke kaskon da man Baki Daya da dankalin ciki ya watsa a cikin Sink,har kankon ya Bari cikin Sink,sabon kasko ya dakko ya fara Girkinsa,Aamna ta Mike cikin bacin Rai da Hawaye a fuskarta ta tattaro karfinta ta durma Masa duka a gadon baya ta arce da gudu,shi ko jin zafin dukan ma baiyi ba,ita Tunaninta ta Rama,Zuma ta dakko tare da shafawa a kafarta iya inda ya kone,Palo ya dawo da kwansa soyayye da tea da wani snacks Kamar bread,Aamna Fitowa tayi dama tasan shi Bai zuwa Dining Sam,Yana Palo zaune saman kujera ya wani kishingida a Haka yake cin abinci,Aamna a ranta Tace duk abinda ya shafi Sunnah da dabi'a ta Musulmai baya Yi Sam,abinci a kwance za a ci,a kasan center carpet ta zauna tare da nannade kafafu kamar wacce zatayi karatun Qur'ani ta zuba Masa Ido,Hannu ta zura da sauri ta zari soyayyen kwai fefe Daya,ta fisge snacks ta balli Rabi ta Ajiye Masa,ta Buda tsakiya ta sa kwanta ciki ta rufe,Bai ko kulata ba,tana ta ci yasha tea da yawa saura Rabi ta dauke cup din ta gudu,dama ya koshi shi take uban gudu da tayi zamanta ma shi baida time dinta yanzu. Mama zaune take a Palo tana gyara wake Baba yayi wanka ya Sha Yar shaddarsa zai tafi kasuwa ya daga Hannu sama yayi wata Hamma tare da Mika yace Alhmdllh Aishatu sakayau nake jina,Kamar wani sabon musulunta,ji nake Kamar yau aka Yi min wankan tsarkii,sabo da mun Aurar da Yaran Nan mun huta Kuma Alhmdllh Bamu siyar da akuya ta dawo tana goge Mana danga ba,Mama Tace Bari Kai dai Baban Zuhra ai idan na tuna musamman Zuhra tana can tana zamanta lafiya sai naji Ni kamar Ina cikin watan Ramadana Naga Kuma Daren lailatul qadri,ita kuwa Aamna mun fita ko ba soso ba Sabulu,ta koma bangaren danginta suje can su karata,gashi Dake so suke su Aurawa Dansu Dan Giya har da bani jarin Million Uku cewar Baba shima,Mama Tace yo ai mun gano wayon badan Allah aka Bamu ba,harda wani gida ,Baba yace ai Ina sani na kwantar da Kai na nuna musu mutunci na hada dabara nace su bawa Aamna auren Ahmad zai shiryu. Hahaha Mama tayi Dariya Tace Dantijara wannan ai bazai taba shiryuwa ba,ita Kuma Aamna nasan kwadinyin tsiyarta shi zai zaunar da ita shi yasa kaji shuru,ko mun Mata waya sai Tace lafiya suke,Munafuka cewar Baba tana can tana Shan wahala,yanzu da zamu je sai Munga ta rame,Kaga yanzu har tayi kusan wata Guda da Aure, kudin Sadakinta data Bamu mun karbe ba ruwanmu sauran Kuma da Tace a siya Mata wake a ajiye a Kauye fa? Baba yac ae gobe fa zamu je gidan Aamna sabo da karta gano cewar Bamu damu da ita ba ko Bamu dauke a matsayin 'ya ba sai mu tafi Mata da kudinta mu Bata muce Kar tayi wannan sana'ar Kawai ta kashe kudinta,Mama Tace ita a dole me Neman kudi Ubanwa zai barta tayi Sana'a, Dan taga kudin sadakin Zuhra mun siya Mata Saniya a Kauye Ana kiwo shine itama tace a siya Mata wake,Mama Tace ai baza mu Bari ta Gane komai daga wajenmu ba,kamar yanda ta taso a Hannunmu ba yabo ba fallasa ita Bata Isa Tace Bamu sonta ba Kuma Bata Isa Tace muna sonta ba to yanzu ma hakane,musamman yanzu da ta auri jinin kudi,a hankali zamu dinga zararta kudi,so nake Nan gaba ta Bude min katafaren shago na siyar da kayan sawa na Mata cewar Mama,Baba Yana dariya yace ai Ni Kinga na samu jari. Amma naga Harkar tayi min kadan dole Nan gaba Nima ta Kara min jari,Mama Tace na karbo wasu layu da guru idan munje Zan sa ta Kara daura su so nake sai na mayar da ita Yar bori da wayo sabo da idan Mijin nata ya gani yace malamai take bi kaga bazai taba sonta ba bare ta zauna a daula,lokacin mun yagi rabon mu,idan ya sako ta sai ta dawo ta zauna a shago na Wanda Zan Bude Nan gaba da kudin surukanta ta dinga siyar min da kayan. Baba Yana dariya har da buga kafa yace kin iya planning,tunda Bata auri talaka ba Allah ya canja lamarinsa Kinga muma harka ta Bude sai mubi a Haka mu yagi rabon mu. Siyama kwance take saman tsohuwar katifarta sai faman Juyi takeyi tana murmushi ita kadai tare da matse pillow a hankali Tace Kai idan ban ganshi ba yau bazan samu nutsuwa ba,Wasa Wasa a hankali sonsa ya Shiga Rai na daga ganinsa sau biyu sau uku,wata zuciyar ce ta gargade ta tace to Faisal din naki fa,Kuma Wanda kika haukace akan sonsa Mijin babbar kawarki ne, wata zuciyar Tace so so ne Amma son Kai yafi,a fili Tace duk yanda naso kawata ta samu farin ciki ai Bai Kai ga kaina ba,Kuma ma mene tunda Allah Bai haramta ba,abinda ya Dace na San yanda zanyi ya Gane Ina sonsa,kafin kawata ta rigani gwara Ni na rigata,zumbur ta Mike Tace dole na Kori Faisal na daina sonsa,Sam baya birge Ni yanzu,Akan Ahmad Zan iya koyar Shan barasa Nima Indai zai so ni,ta yanda Zan bullo kenan Nima na nuna Masa Ina Sha nasan zanyi Nasara,Mikewa tayi tsaye tare da jawo Wayarta ta danno Number Aamna. Aamna kuwa daidai wannan lokacin 11am su Mashkoor su Biyar ne Suka zo tare da cike palon suna ta kurbar giya,Ahmad Yana kwance,Aamna ce ta fito sanye da Arabian gown black da Alama fita zata Yi,ta gansu a palo,kallo Suka bita da shi Banda Ahmad da ko kallo Bata ishe shi ba,Mashkoor ne ya galla Mata Harara ya furta anzo an aure Mana Sarkin mu,kina Bata Masa Rai a banza,Jibson ya ja tsaki,Aamna dai Bata ko kulasu ba,wurin Ahmad ta karasa ta Dan dukar da kanta saitin Fuskarsa Tace zanje kasuwa ba kayan Miya da kayan lambu ka bani kudi da Izni,Tsaki Yaja yace dalla Wai Ni na kawo ki ne,ki tafi ko Ina kika ga dama,Kudi ya jaro dubu Ashirin ya jefa Mata a Fuska yace dauki ki bani waje mayya,Su Jibson Suka kyakyace da dariya ba ji ba gani,Aamna ranta ya baci ta Harare su tayi waje abinta. Napep ta shiga har kasuwar kayan Miya,duk abinda take bukata sai da ta siya,ta zuba komai a Napep zasu tafi Kiran Siyama ya shigo Wayarta,Fuskarta dauke da murmushi Tace Yar halak ya kike? Siyama Tace Ina Kofar gidan mijinki kina gida na shigo? Aamna Tace Ina kasuwa wlh Amma bani 10mnt yanzu Zaki ganni,Kawai ki shiga gidan Ahmad Yana Nan da abokansa kije kafin na zo Amma ki kula karki kulasu zasu iya Miki wulakanci,Siyama Tace to tare da kashe wayar Tace dama ba Dan ke nazo ba ai ta shiga taci Uwar gayu cikin lace Riga da skert wani ruwan kunun kanwa,Sallama tayi tare da Bude Kofar ta shiga dauke da Sallama,wani kamshi da sanyi ya daki Siyama, Siyama a ranta Tace shegiya Aamna akwai iya gyara,babu Wanda ya amsa Sallamarta cikinsu,shiga tayi Kawai ta zauna a wata kujera da bakowa,Ahmad ta kalla Suka hada Ido ta bangale Baki da murmushi Tace Ina kwanan ku,Suka kece Mata da dariya banda Ahmad da ya sake hade girar sama data kasa,a ransa yace an kawo min yarinya gida danginta sun dameni da zuwa gidana,Siyama tayi Shuru tana ta kallon Ahmad Kamar zata cinye shi,gefen Bash ta zauna Tace lemo kuke Sha ne? Kallonta Suka Yi Suka sake kwashewa da dariya,Bata hakura ba Tace Kai dama na sanka ma Brown ake ce maka ko ta nuna Mubaraq Brown,Siyama a ranta Tace Kan uba Taya Zan samu ko number Daya daga cikinsu ne? Tana wannan tunanin sai kuwa Jibson Sarkin son Mata yace Yan Mata kin hadu fa,Siyama tayi murmushi hankalinta na Kan Ahmad,Jibson yace da Allah bani number dinki Mana,ai da sauri Siyama Tace to dama abinda take so kenan ta kulla alaka da wani a ciki ko zata samu hanyar Shiga jikin Ahmad ta Haka,ta Bawa Jibson number ya Kira ta Nan take tayi Saving tana cewa ya matar gidan Bata kawo muku girki bane? Abdul Tawaga yace ta fita fa,Cab Miji yayi Baki Amma matar baza ta kawowa abokan Miji abinci ba wannan wacce irin mace ce,Ahmad ne ya kalli Siyama kadan ya dauke kai,Tace Bari ta dawo ai dole ma na tayata ta shirya muku better,Jibson yace da kin kyauta Uwar Kinibabba,Siyama ta kalleshi da sauri Wato itace Kinababba,yace dama yunwa muke ji,suna Haka sai ga Aamna ta dawo da fara'a tayi Sallama. Siyama ce Kawai ta amsa itama da fara'a Tace kawata kin dawo kenan,Aamna ta mikawa Siyama Hannu Suka tafa tace kinsan Ni jinin Larabawa ce Zan koma na tuno da Dan larabcina na Islamiyya Marhababiki ya Siyama,Kyaifal Ummati? Siyama tana Dariya itama da kalkala Tace Alhamdulillah...Alhamdulillah,Shukran cewar Aamna,Kujera ta nunawa Siyama tare da Furta Ijlis kawata,Siyama ta koma ta zauna tana cewa jalasna ya kawata,duk sai da suka Bawa su Jibson Dariya,Ahmad Kam Kawai Dan Baki ya tabe sabo da shi Yana mugun Jin larabci Dan Basu Sani bane. Zama Aamna tayi itama,Siyama Tace Hauwa'u kuwa tace tana Gaida ki,Hauwa'u Yar class dinmu,na Gane ai kice Ina Amsawa na gode,Siyama da larabci tace Ma Fi mishkla,ya kamata mu shiga kitchen ayiwa abokan mijinki girki Bai kamata su zauna da yunwa ba,ya kike Abu kamar Baki San darajar mijinki da abokansa ba,Aamna Bata kawo komai a ranta ba Tace Kuma fa Haka ne muje to ki tayani. Kitchen Suka Shiga Siyama tana ta wani kwarkwasa Wanda take Yi Dan shi Bai gani ba su Jibson sune Suka bita da kallo suna Hadiyar yawu. Fried rice suka Yi hadaddiya taji hadi da soyayyar kaji,ga zobo sun hada me Dan Karan dadi,salat ma an hada daban,a Dining suka shirya komai tare da gyara ko Ina sannan Siyama da Shishigi tazo Tace mun Gama guys gashi can a Dining,Ahmad Bai ko motsa ba sai su Jibson ne Suka zagaye abinci suka far Masa,kafin kace me sun cinye komai suna Santi sun shanye komai,Siyama tana zaune a cikinsu Suka ci tare sai taga Aamna ta fito da katon tire da wasu miyagu food flasks na musamman komai ta jera a Gaban Ahmad kasancewar tasan Bai zuwa Dining side. Serving dinsa tayi komai ta zauna a gefen kafafunsa tace tashi kaci Abincin,Siyama ta Bata Rai tana daga can Dining ta tsura musu Ido ranta a bace tana Jin Ina ma itace a wajen Ahmad Haka ba Aamna ba,Abinda Aamna ta fuskanta Kamar Bai da lafiya kwana biyu tunda yayi zazzabin Nan,Bata San tsabar kwayace ba take sashi Yana slow. Ka tashi please tun safe baka ci komai ba,Ahmad yaki tashi,Siyama ta saki murmushin Jin dadi,a hankali Kuma da ya gaji ya Mike tare da Zama ya saki jiki sharaf yayi wani Slow ya tsaya a Haka yaki Kuma magana. Aamna tasa spoon ta ebo abincin Tace to Bismillah,kamar bazai karba ba sai Kuma Yaja Tsaki tare da bude bakin kadan Tace ka Bude Mana ya Dan Kara budewa ta zuba masa,Kamar Yana tauna madaci Haka yake ci,a hankali yace kice waccen Yar Uwar Taki ta bar min gida kallo na take Yi bana son kallo,Dan kar ya fasa cin abincin Aamna Tace to Bari ka Gama cin abincin tana ta bashi a Baki Yana ci sai uban Tsaki yake ja,ya ci da yawa yasha Zobon ya daure Fuska Kuma yace cikin tsawa ta bar gidan Nan,ba Aamna ba Siyama ita kanta sai da ta firgita ta Mike ba shiri,ya kalli su Jibson yace daAllah kuje Ina son Zama Ni Daya Yana magana ya girgiza kitsonsa,gaba Daya Suka ce an Gama sarki Suka kwashe kayan mayensu Suka Yi gaba,Siyama ta kalli Aamna tayi murmushin yaudara Tace kawata na wuce,Aamna ta Mike ta saka Hijab Tace muje na rakaki,har bakin Titi ta raka Siyama,ta Bawa Siyama dubu Uku tace gashi kawata kiyi kudin Napep. Siyama ta karbe Tace na gode kawas,Aamna Tace kiyi Hakuri da korar da ya Miki wallahi banji Dadi ba Amma Kinga ba yanda zanyi da shi idan kin dawo next time sai na Bude Miki kayan lefen Nawa ki zabi abinda kike so ciki,Siyama ta washe Baki Tace na gode kawata ai na matsu na fara daukan wanka zanzo jibi sai na zaba,Aamna Tace ba damuwa Amma me kike ganin Zan bawa Zuhra itama?Siyama ta daure Fuska Tace zuhran data auri me rufin asiri uban me za a bata,irin mu ai mune muke bukatar taimako,Aamna Tace haba Siyama ya Zaki canja Hali Allah ya Hana mutum zaiyi Alheri ka Hana hakan,ko mutum Yana tayar da Kai da million ai Alheri Dadi gareshi Kuma ma ai kamar Yar Uwata ce tare Muka taso itama abinda take so zata zaba,me Napep ja muje dalla cewar Siyama cikin Fushi,Dariya Aamna tayi ta juya gida,tana zuwa ta tura Kofar palon taji Gam an rufe,tasan Ahmad ne ya rufe Wato Bai so ma ta shiga Kar a takura Masa,Murmushi tayi Kawai ta Danna door bell har ta gaji Bai bude ba,a bakin Kofar ta zauna ta zuba tagumi Tace kaddara kenan,Allah ya jarabce ni,Kwalla ce ta cika Idonta taf. Wasa Wasa har Magriba tayi Bai Bude ba sai jikin tap taje Wanda ke Garden tayi Alwala tare da Gabatar da Sallah a Nan tayi har Sallar Isha sannan ta dawo tayi bugun duniya Ahmad Yana can Yana baccinsa yaki budewa Kawai Kuma Yana sani yayi haka.. A bakin Kofar Aamna ta zauna tare da jingina da jikin bango a Haka bacci ya kwashe ta,har 9am lokacin Kuma Mama da Baba sunzo kawo Mata Ziyara,a Nan Suka hango ta,Mama Tace cab ga Alama mun gani Aamna Bata cikin Jin dadi,Baba yace Yar jakar uba gwara duniya ta koya Mata hankali ko ta koyi darasi,gida har gida sai Takaici a ciki,Allah yasa ba Zuhra bace a wannan halin, Mama ce ta taba jikin Aamna da Kalar tausayi Tace tashi Aamna,firgit ta farka taga gari ya waye sai Rana ta gani kwall a kanta,Salati tayi ta Mike tsaye cike da kunya Bata so su Baba suka ganta a wannan halin ba sabo da tasan zasu shiga damuwa. Baba yace Ashe yau za ayi yaki a gidan Nan,yata Dana rike da Hannu na muka Raine ta in dauka in bada ita Amana Amma a wulakanta min ita Haka karya ne wallahi,ba a haifi mutum ba,Baba Yana bala'i ya kaiwa Kofar Naushi zai daki kofa Mama ta kifta Masa Ido tare da yin wuf ta damko hannunsa tana Haba Baban Aamna da Zuhra Haba,gidan suruki ne Bai kamata ba,Abi komai a Sannu,Aamna tana Jin tsoro Ta durkusa a kasa tana rokon Baba tana Dan Allah Baba kayi Hakuri ka rufamin asiri,Kayi min Rai Baba wallahi idan kuka tafi Ni zai duka,dukan tsiya zai min,a hakan ma ya muke karewa kusan kullum sai ya dakeni,Dan Allah Baba ku tafi gida Ni zanzo,Kamar gaske Baba yace Ina ai wallahi yau sai na Kira Uwarsa da ubansa Akan Haka baza mu lamunci wannan ba,Mama tace ai batun tafiya gida Bai taso ba akwai abubuwan da mukazo tattaunawa da yawa sannan Kuma yau a Nan zamu yini muci mu koshi muna Nan har sai ya Bude Kofar,Aamna ta dafe Kai Tace wayyo Allah na Shiga Uku,Baba Kar ya wulakantaku a gabana bazan jure ba sai dai ya kashe Ni a kanku Dan sai na Rama,Ashe akwai hargitsi da balbalin bala'i kuwa yau a gidan Nan cewar Baba ya nemi waje ya zauna daram,Mama ta gyara Mayafinta ta zauna itama,Aamna kuwa Tap ta nufa tayi Alwala tayi Sallah sannan ta dawo wajen,Suna zaune sai Suka ji baram an Bude kofa da karfin tsiya,kamshi ne na daban ya daki hancinsu,Yasha wata jallabiya Brown Yar tsangalalliya Takalminsa flat Brown yayi kyau kace baya Shan komai,Fuska ya sake daurewa ganin Dangin Aamna,Tsaki Yaja da karfi ya furta sai kace Uban tsohonki ne ya Gina min gida,Kun da dameni da wannan tsofaffin Banzan,Aamna Tace wallahi ba sune tsofaffin banza ba sai dai in naka ne na banza na wofi. A fusace ya juyo Yana huci yace Mummy na data auro min ke wacce ta nace tana sonki kika zageta yau? Jikin Aamna ne yayi sanyi Tace ai ba da ita nake ba Ni,ko kaji nace Mummy? Mummy ai na fika kaunarta Aamna ta wayance Kar yaci ubanta,Baba ne yayi karfin Hali yace ae da ita ake din sai me? Aamna Tace Ni bada ita nake ba Baba,Mama Tace Iyyee.....Juyawa Ahmad yayi yace Zan dawo gidan Nan zamu hadu ya Haye machine dinsa ya bashi wuta sannan ya dage kafa Daya sama yazo har Gaban su Baba ya kotse machine din tare da bashi wuta ya bulbulesu da hayaki ya fita a tsiyace. Aamna ce ta daka tsalle tare da nuna Bayan Ahmad da yatsa Tace sai nayi maganinka zaka dawo ne sai ka sani,sai na cije ka wallahi a gadon baya,Iyayen Nawa zaka yiwa haka,zaka San ni Yar halak ce. Mama Tace ke dalla rufe Mana Baki, banza matsoraciyar banza kin Gama cika Mana Baki gashi a gabanki ya ci Mana mutunci Baki ce komai ba sai da ya tafi,Baba Kuwa Takaicin Aamna yasa yace tir dake Aamna muje ciki mu kiyi Mana girki muci mu Sha. AsmaBaffa 10/26/21, 8:52 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 31-35 FREE PAGE DUNIYA TA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne MAMAN MURTALA HAFSATOU 'YAR BAIWA INNARO AISHA SALIHU UBAIDAT HARUNA Aamna da sauri ta fada kitchen sabo da so takeyi suyi sauri su tafi,babu Bata lokaci tayi musu farfesun kaji,ta musu jallof din taliya Tasha kifi da kayan lambu sai lemuka da ruwa ta kawo musu,Suka zauna Suka dinga kwasar girki, Baba Yana yin Loma Daya yace Allahu Akbar sai na tuna da Uwar dakina Dake Kano Hajiya Sahura lokacin da aka kaini almajiranta na Zama Yaron gidanta,Haka take dafa Taliya Malam Kamar daga Otel(Hotel),Mama Tace taji tarihu kaga inda tsiya tayi tafiyar dogon zango,ai a Nan gidan Tsiya Balaguro tayi ba tafiya ba cewar Baba,Aamna tana ta dariya Tace ai kudi yake bani da yawa,kwana na Daya na fara fita,ba ruwansa da wani Ni Amaryace inda Naga Dame nake zuwa,Baba ya tsurawa Aamna Ido yace indai akan irin wannan cefanen ne ki dinga ficiwarki daga Nan ki dinga biyowa ta gida kina yaga mana. Sai da suka koshi,Baba yace zuba min wani farfesun a flask na tafi dashi idan munje gida zamu ci da breadi,Aamna cikin sauri ta samo flask karami ta kwashe ta bar kadan ta hada musu harda lemuka,cikin lefenta ta dakko wata atamfa da turaruka ta bawa Mama atamfar turaren Kuma ta bawa Baba,Sai Jin dadi sukeyi,Mama ta zuge Jakarta ta sake zaro wata laya da guru na damtse ta mikawa Aamna Tace ungo Bude Damtsanki ki daura wannan,Aamna ta Bata Fuska kamar zatayi kuka Tace Mama Kinga fa wani a hips Dina kince idan na cire Baku yafe min ba Haka kaina layu ne fa har biyu idan zanyi wanka nake cirewa Ina Yi nake maidawa Kamar yanda kika ce shima Kar na cire,Mama ta Bata Rai Tace saka wannan layar a gashinki itama ki soketa ga pin Nan a jiki Kuma wallahi kika cire Bamu yafe ba,Aamna ta karba ta soke Laya ta Uku cikin gashinta,ta dauki guru ta bude farin damtsenta ta daura,Dake tana da haske sai ya Mata kyau. Mama Tace to Haka ake so,sai magana ta karshe zamu Kira surakanki a waya mu fada musu kina cikin wahala zamu dauke Yar mu idan suna so ki zauna sai sun turo Mana kudi sabo da Haka ko sun kiraki sun tambaya kice Haka magana take wallahi idan kika ce ba Haka ba kinji mun rantse sai kin bar gidan Nan ta karfi sannan sai Kinga matakin da zamu dauka a kanki. Aamna tace Haba Baba Wai me yasa kuke Haka ne,Ni fa ba sonsa nakeyi ba,Kuma ma Ni Nan gaba barin gidan zanyi Akan me zaku karbar Musu kudi,a gidan Ubanwa Zaki bar gida? Sai mun Gama kwasar rabon mu tukun yarinya,Shuru Aamna tayi Tace shike Nan to kuje Allah ya kiyaye Hanya na gode,sauri takeyi su tafi Kar ya dawo gidan,Mikewa sukayi ta rakasu Suka tafi,Suna tafiya ta dawo ta hau gyaran gidan sai da ko Ina ya fito fes sannan taci abinci ta sheka wanka tayi Sallar Azahar,Kwalliya tayi cikin wata English gown silk maroon,me Hannun vest tayi mugun Mata kyau ta fito da shape dinta matuka,Fitowa tayi ta koma kitchen ta duba farfesun data ragewa Ahmad,Sai tayi cabbage soup ta Sha kifi tayi sakwara,me Gadi ta bawa sauran ta Ajiye ta zauna a Palo tana kallo,Bayan tayi Sallar la'asar tana karatun novel a Wayarta taji ya shigo Yana waya yace Daddy Kuma me ya same shi? Yana asibiti? Bazan zo ba Allah ya bashi lafiya ya furta tare da Zama a saman kujera ya rufe Ido tare da dafe Kansa. Duk da baiyi Sallama ba sai tace me ya samu Daddy din? Wani kallon wulakanci ya Mata yace ina ruwanki ko son gulma,na fada Miki ki daina shiga safgata Zan Tara Miki gajiya wallahi tam,Shuru tayi Tace abincin fa? Baza'a ci ba ko dole ne sai naci girkinki? Wai me yasa kike son takura min ne? Sabo da Kai Mijina na ne shi yasa,Baki gaji da duka bane Naga Alama,Kai baka gajiya da fada da mace? Ko kunya baka ji fada da mace,idan kana Jin Kai Namiji ne kaje can waje kuyi da maza Mana kaga yanda zasu maka jina jina,ka zauna a Nan Ni sabo da mace ce sai dukana kake Yi wallahi sai Allah ya tambayeka,ranar lahira sai Allah ya Kamaka da hakki na,Murmushi yayi na rainin hankali yace sai na karasa wannan idon Daya shima a manne shi,Sai lokacin Aamna ta tuna ma Idonta a manne yake,Haka duk inda aka ganta sai dai taji Ana ta Mata Sannu da Allah ya sawwake,tana sani Tace zo na yanke maka farce gasu Nan sun fara taruwa,kwanciya yayi a kujerar tare da juya Mata Baya yace wannan karon wallahi kika kuskura ko da Wasa kika taba min farce saina ballaki a gidan Nan,ka godewa Allah ba sajenka da gemunka na yanke ba,Banza ya mata yana tunanin Daddy da akace Hawan jini ya kamashi saura kadan yayi paralyse. Damuwa ya Shiga a ransa sosai gashi shi bazai iya Addua ba baida time,juyowa yayi Aamna ta kalleshi da sauri,Je kiyi Alwala,tsoro ya Kama Aamna a ranta tace ko hakkinsa zai karba yau na Shiga Uku maybe nafeelar sunna zamuyi daga Nan sai Sex,Idonta ne ya kawo kwalla Tace Alwalar me Kuma? Fuska ya Bata yace Zan fa zaneki wallahi kije nace kiyi Alwala ki zo,Aamna Tace wayyo Uwata na shiga Uku,shi ya manta ma Daren farko Ana Alwala da Nafeela,Aamna tace ka Bari sai dare Dan Allah kayi min Rai,Yace Bari na tashi kiga tsayi na,da sauri ta tafi tayi Alwala ta fito da Hijab a Hannunta tana kuka Hawaye shabe Shabe a fuskarta,Alwalar kikewa kuka duk tsoron Allah naki da kurin Sallah da waye waye,Aamna tayi Shuru tana Hawaye Tace Dan Allah kayi hakuri ance da zafi,zafin me? Alwalar ce da zafi? Ya tambaya Yana zaro Mata Ido,Sallayar Dake Hannunta ta shimfida yace to kalli gabas ki fara Nafeela,Aamna Tace bangane ba,ba tare zamu Yi ba? Yace Kiyi Nafeela nace ki yiwa Daddy Addua Allah ya bashi lafiya a madadi na,Ni bazan iya Yi bane. Baki Aamna ta Bude sai lokacin taji kunyar kukanta na banza na tunanin banzan ta,Tace Bari ayi magrib,tana yin Sallar Magriba ta fara Nafeela. Haka tayi ta Nafeela tana yiwa Daddy Addua Allah ya bashi lafiya,sai da ta idar Tace nayi to,ko magana baiyi ba,Wayarta ta jawo ta Kira Mummy, bugu Daya ta daga Bayan sun gaisa Aamna Tace Mummy ya jikin Daddy din? Mummy tana murmushi tace waye ya fada Miki? Aamna ta saci Kallonsa yace in kika ce Ni na fada Miki sai na karya ki yau,Aamna Tace lokacin da kuke waya Ina wajen,Mummy Tace okay da sauki sosai gobe ma muke sa ran Sallama mu koma gida,yaya fatan dai rigimar Bata Yi yawa ba? Aamna Tace ae Mummy,Baba ya kirani jiya,Gaban Aamna ya fadi,Mummy Tace banji Dadin abinda suka Iske Ahmad ya Miki ba,naga Baba yaji Haushi da yawa yace zai dauke ki daga gidan,Kunya ta Kama Aamna Tace Mummy ki kyale Baba rikicin tsufa yake Yi. Dariya Mummy tayi tace Mama Kuma Ashe Business take so ta fara lokacin Muna cikin damuwa a asibiti abinda ta Nema Bai samu ba sai dubu dari hudu ta samu kacal Amma Inshaallah Zan Kara Mata wasu,Aamna tayi Shuru sabo da Matukar kunya da nauyi data ji, Tace kuyi Hakuri Mummy wallahi Ni ba sa Hannun na ciki,ban San zancen ba ma,Mummy ta fuskanci Aamna ta Kuma Gane su Baba Kawai kyalewa tayi,karki damu Aamna na fihimci lamarin,kici gaba da Hakuri Zama Dan Allah kinji,Aamna Tace Inshaallah ba matsala,kina bukatar kudi ko wani Abu? Aamna tayi murmushi Tace a'a Mummy ba abinda nake bukata komai Yana Yi min idan na tambaya,kin tabbatar? Aamna Tace ae Mummy kiyiwa Daddy Sannu da jiki a gaisar min da Humaira Kuma,Mummy ta dinga yiwa Aamna godiya sannan ta kashe wayar. Ahmad ransa ya tunzura Jin irin godiyar da Mummy ke Mata to uban me tayi ake gode mata,Cikin masifa yace ni baza a gode min ba Dana dauki kaddara nake zama dake cikin kunci sai ke Za'a godewa Ana wani sa Miki Albarka ke ga fitsararriya ko? Harda wani Jin dadi kina to Mummy...ya makale Murya tare da gwada muryar Aamna yanda take magana,Aamna Tace Wai Kai me yasa baka da kirki ne? Yace ke dalla rufe min Baki ke Wato an Baki lasisi ko harda wani Kara siyo waya Vivo sabuwa,wannan ba gata bane, ke ga tsigalalliya ko kina wani girgiza da kafada ya gwada girgizar Aamna Idan tana masifa,Aamna ta kyalkyale da Dariya gashinsa ya girgiza tare da gyara sabon kitson calabarsa,Aamna Tace shike Nan Zan Kai karar ka wajen Mummy,Yace idan kina yiwa bushashen tsohonki kije ki Kai karar tawa ki gani idan akwai Wanda ya Isa ya tankwara Ni ko yasa naji magana,an fada Miki wani Jin Magana nakeyi. Baki Aamna ta Bude Tace ai Ni tsoho na ka ganshi me kiba ne,Ashe Ahmad ba Baba yake nufi ba yasan Baban Aamna na asali Dan Sudan wani mugun bushashen tsoho ne,ramarsa ta baci tunda lokacin da wayonsa Bai manta shi ba,Sai yace kije ki binciki tarihinki yarinya kiji waye tsohonki Dan lukuti ne ko kuwa,Aamna ta Mike tsaye tace Allah ban yafe ba sai na cijeka ta fado Kansa Kamar wata Kura ta Bude Baki da gaske ta Kai Masa cizo a wuya,wuyanta ya cafka da hannunsa ya shaketa sosai ta fara kakari Idonta ya firfito kamar zata sheka lahira ya hankadata gefe ta Fadi a kasa dabar, mikewa yayi zai fita ta jawo rigarsa Iya karfinta,ya juyo ya dauketa gaba Daya ya jefata saman kujera Kamar Yana wrestling,Aamna ta cakumo kafafunsa ya Fado gefenta,Idonsa Wanda ya canja yayi ja sabo da kwaya ta motsa ya watsa Mata wani kallo ai sai ta Mike ta arce da gudu. Key din machine dinsa ya dauka ya fice abinsa ya hau machine kenan yaji an jefo Masa Robar ruwa a Kansa kwas,Kansa ya daga sama yaga Aamna ce ta baya balcony dinta ta sama tana cewa aje a Kai karata wajen human Right idan an isa,ko kazo ka dokeni,Yatsunsa ya wara ya Mata dakuwa Wato ambola Aamna ta Masa gwalo,yace zamu hadu ne da karfi yanda zata ji,mu hadu Mana gani ta matso jikin karfen wajen Dan Allah taho mu hadu tayi girgizarta da kafada,saura kadan yayi Dariya ya matse yace Fuck you....Aamna Tace Dadi ne da shi come and fuck me,Dariyarsa ya guntse yace Yar Iska ce ke ai,nafi karfin Iska sai dai Guguwa,Machine dinsa ya kotse yayi waje abinsa ya barta tana ta dariya. Tunda ya fita Bai dawo ba sai wurin 4am ya shigo a chake yasha da yawa,tunda ya Shiga Dakinsa Bai tashi ba har gari ya waye,12pm Aamna ta Gama komai tana ta duba shi Bai tashi ba,Haka taje ta wanke Masa toilet ta gyara dakin bed din ne Kawai bata gyara ba kasancewar Yana kwance,Fitowa tayi ta zauna sanye cikin doguwar rigar Shadda purple ta Sha kyau,sallamar Siyama ta ji,ta Mike Suka Rungume juna Siyama Tace ba Zama nazo Yi ba maza muje na zabi kayan,Bedroom Suka haura Aamna ta bude Mata akwatuna Tace zabi,da mamaki sai taga Siyama ba hankali duk kayan masu tsadar take zabewa har ta zabi kala biyar ta koma Kan Arabian dress,ta zabi English wear, ta zabi Inners,Aamna gashi ita Tace ta zabi abinda take so tana ji tana gani Siyama ta zuba a katuwar leda,Aamna Kamar ta kwace Amma ta danne zuciyarta Suka fito haka,suna Fitowa Ahmad Yana Fitowa ya Sha wanka cikin kana Nan kayansa kamar kullum 3qtr da t-shirt marasa nauyi ne da Alama ba fita zaiyi ba,Kallo Daya ya musu yace Mene a Nan? Ya dakawa Siyama Tsawa. Da sauri Aamna ta firgita Tace ka...Kaya...kaya ne na lefe kasan Ana Dan bawa kawa wasu abin,Ya Mika Hannu yace bani cikin tsawa....Siyama jiki na rawa ta Mika Masa ledojin ya fisge kuwa tare da budewa yaga Kaya da uban yawa,ya kalli Aamna yace waye ya Siya Miki kayan Answer me,Aamna Tace Mummy ce,yace ke ta siyawa ko wannan jakar ya nuna Siyama da yatsa,Aamna Tace Ni,yace to ba don Mummy tana sonki ba ta siya Miki shine Zaki bayar sabo da ba kudinki bane,Mummy ta me yasa bakya respecting din Mummy ne Wai duk son da take miki,Siyama ya kalla yace last warning duk abinda Zaki ki tsaya a Downstairs main Palo Kar na sake ganinki a sama Nan,sabo da idan na sake ganinki baza kiso abinda Zan Miki ba,baza kiji dadin abinda Zan Miki daga ke har kawar taki,bi hanya....ya furta da karaji,Siyama tayi kasa da gudu,Aamna zata bita yace wait...tafin hannunsa ya Buda kamar zai mareta yace karaso ki Mari kanki da kanki. Aamna da sauri tazo ta Kara kumatunta a hannunsa,yace Baki ji zafi ba da karfi Zaki taho ki taskawa kanki mari,Matsawa tayi baya ta taho da gudu tare da hannunsa da Hannunta ta Kara kumatunta a tafin hannunsa da karfi ta taskawa kanta Mari yace Good tare da murde Mata kunne yace daga yau idan kika sake ebar wa Mummy Kaya kika bayar sai na babbalaki nayi raga raga dake. sannan duk kayan Dana Baki kudi kika siya idan na samu kin bayar zaki ga abinda Zan Miki,Aamna Tace sabo da tsumulmula ko me? Yace yes...son kudi ne Dani...Ina son kudi...kayan ta kwashe ta maida daki sai murna takeyi gwara Daya kwace dama Bata Yi Niyyar bayarwa da yawa Haka ba,kafin ta fito tuni Siyama tana Napep ma sabo da tsoro gashi Kuma tana sonsa a Kansa take ta wulakanta saurayinta ya rasa me yayi mata ya kasa Gane Kan Siyama. Aamna cikin Fushi ta dawo Palo ta zauna kan kujera me kallon wacce Ahmad ke zaune sai harararsa takeyi,Tace abinda kake min Sam bana Jin dadi kawayena da Yan Uwana gaskiya gaskiya bana son abinda kake musu,bana wulakanta naka Nima karka wulakanta min nawa ehe,Nifa akan wannan bazan fa yarda ba,Nima kwayar Nan na Iyata,aikin Yan giya na iya shi nima,Haka Kawai in Banda kaddara ma Dana dorawa kaina,ga maza can suna kauna ta,ga masu kudi na gari masu Addini Wanda zasu kula Dani naki yarda dasu,banga laifinka ba laifi nane,Nan..nan Affan ya dawo daga malaysia ya dawo da kudi da mota Yana rokata naki yarda,Nan su Deeni Dan gidan Dan Majalisar jaha sakakina yasa kawata ta kwace min shi Ina ji Ina gani, ga bushashena Kamalu naci Masa mutunci a banza ya gudu. Dama ance kamatuddini tudan yanda nace Masa bushashe Haka tun ba ayi nisa ba gashi ka Rama Masa Ni Babana Mahaifi kacewa tsotsatse,tun anan duniya gashi Ina gani Allah na tuba Amma gaskiya Ina cin ubana a kasar nan,Ina karba a jikina wallahi,ta ko Ina duniya ta min daurin Alawa ko Ina ba sauki anyi min kika kaka,na Shiga tsaka me wuya,Baki Gama Shiga masifa ba yanzu kika fara tunda kika yarda kika aureni cewar Ahmad ,Aamna tana huci Tace Ina ma mu Mata aka bawa damar saki ko kishiya wallahi da tuni na maka saki dari da talatin da biyar, ko na auro maka kishiyoyi har Uku,kishiya na farko Mashkoor babban abokinka Zan kashe makudan kudade na auro shi sabo da na huce takaicinka,na biyu na Nemo tsohon saurayina Affan,na Uku nayi manage da Mubaraq Tawaga Kai Kuma Kaine Uwar gida,ai wlh da kaga wulakanci,duk ranar kwananka ba abinda Zan tsinana maka sai dai sha'awa ta kashe ka,Amma a sauran kwanan su Affan kullum asubar fari zaka ga mun fito yin wankar tsarki. Dariya ce ta Kama Ahmad yace ai ke dakikiya ce shi yasa kike wannan tunanin,Namiji Daya ma wallahi yafi karfinki Indai ya amsa sunansa Namiji Irina bare har maza hudu,,Dariya Aamna tayi Tace a Ina ka amsa sunanka namijin Kai dalla duk kwayoyi da giya sun Gama kashe ka,Kai da tsoron Boobs ma kakeyi,Ahmad yace ae naji ai tsoro halak ne,bana sonsu ne shi yasa,Ni ba birgeni sukeyi ba Mene abin sha'awa a Nan Abu cako cako Haka a kirji ba kyan gani,ka taba Abu kamar wani jikin mage ba dadi Haka yagwalgwal,Dariya Aamna take tayi Tace na fada maka kwayoyi sun kashe ka,ka daina Sha wallahi ka samawa kanka lafiya,wannan abubuwan ka tambaya kaji mu kanmu idan Muka je wanka dadin wanke su muke ji bare Kuma maza,Kama fara sonsu tun yanzu sabo da idan na gaji duk ranar dana je na kalli film jam'iyata ta motsa zanzo ne dole ka koyi sonsu. Fuska ya Bata yace ko da Wasa kika zo Zaki Sha duka ne, tunda ke Baki da kunya Ni Ina da kunya ni Fulani ne ni,Aamna yau tana mamaki Ashe Yana magana Haka,Tace Kaine me kunyar lallai,Shi yasa nace wa Mummy ta Bari na samo yarinya karama Yar secondary wacce Bata San komai ba me hankali da kunya Amma Mummy Taki yarda ta dakko min me Degree wacce ta Gama balaga a waje ta fitsare kafafunta. Aamna Tace kamar ka sani ai idan muka wuce 22yrs to Kar muke ganin kowa,Ahmad yayi Shuru Bai sake magana ba har ta Gama surutunta ta koma kallon Indian film,Yana ta kallon soyayya ya tabe Baki yace bani remote,Mika Masa tayi ya canja Chanel ya Kai Wrestling,yace ga inda ake abin arziki ba love ba,kasa ta lalace komai love,gidan radio love,Yan film love,writers love,matasa love,tsofaffi love,tsoho ya tsufa maimakon ya Bari aci gaba da dama Masa kunu Yana Sha har ya koma lahira a'a sai kaji ya Kara aure ko aji matarsa ta Haihu,tsohuwa sai aga tana Shan maganin Mata abin haushi ta Aiki mutum siyo min Zuma da gumbar Mata zaka ce,Aamna ta kyalkyale da Dariya harda rike ciki ya gwada yanda tsohuwar ke magana tana makyarkyata da Murya,Shi kuwa ko Dariya bayayi kamar ba shine yake Maganar ba. A Ina kaga tsohuwar ta fada,jajayen lips dinsa ya tsuke, Baki ya turo gaba Yana girgiza Kai kwaya ta motsa yace Maman Jibson ce take Aiken wani Dan yaronta Islamic chemist,Aamna tayi Dariya Tace Sallar Azahar lokaci yayi kaji ana Kira,ba yanzu zanyi ba sai ta nuna luguf,zata sake magana ya daka Mata Tsawa karki dameni Dan Kinga nayi magana dake Ina cikin Good mood ne Daddy ya warke karki kawo min raini ba Dan arziki bane ni yawwa kije kiyi sallarki ba ruwanki Dani,ko ke nake yiwa Sallar? An fada Miki zanyi Abu Dan wani Dan Adam ne eyeee? Aamna Tace a'a,yace to ki daina shiga hurumina,bana Shiga harkarki ko Kinga Ina Shiga rayuwarki? Ina ruwana da rayuwarki,Ina ruwanki da harkata,Tace babu yace to San Inda dare ya Miki ko na zubar Miki da hakora,Sum sum Aamna ta wuce taje tayi Sallah,ko da ta fito sai gani tayi har ya dafa Indomie da kwai ga coffee ya hada Yana sha abinsa,Yana gamawa yayi ficewarsa,Kitchen ta Shiga itama. Wasa Wasa Har Aamna ta kwashe wata Uku a gidan Ahmad kullum a haka suke ba Wani canji,halinsa ya ishe ta,ta Gama gajiya da zaman gidan gaba Daya,yanda ta sanshi tun farko Bai canja ba,ga Kuma Siyama da ta nacewa gidanta kullum shi Kuma Yana ci musu mutunci Wanda Haka Sam baiwa Aamna Dadi a gabanta Ana ciwa kawarta mutunci sabo da Bata San kudirin Siyama ba,Siyama tuni ta sallami Faisal ta sa an mayar Masa kudin auren da ya kawo,Faisal ya shiga damuwa Amma ba yanda ya iya Haka ya hakura bayan ya Sha fama da zuciyarsa,Siyama kuwa Bata fadawa Aamna ta Kori saurayinta ba sabo da kar a gano ta,gashi kullum Kara son Ahmad takeyi kamar hauka. Bangaren su Mama kuwa tuni kusa da gidansu ta bude katon shago tana siyar da Inner wears na maza da Mata,masu kyau take siya idan anyo order daga kasashen waje,ta gyara ciki komai glass da glass ne Dan karamin shago, Baba ne ya cika Mata kudin Suka Bude abinsu sannan a Kofar shagon daga gefe kayan kamshi take siyarwa citta,barkono,kanunfari da masoro da su Kimba da gyadar curry etc,tana Zama a shagon da kanta sannan ta sa wani yaro a ciki Dan makwaftansu da taga Yana da Dan hankali tana biyansa Dan abinda ba a rasa ba,Zuhra Bata San duk abinda ke faruwa ba sabo da ita Bata Bayan su Baba,duk abinda suke Yi Bata Jin dadi tana Kuma kokarin yi musu Nasiha,ganin Haka sai Suka daina fada Mata komai,gidan Aamna kuwa Bata zuwa sosai sabo da halin Ahmad taga baya son Baki a gidansa. Da Yamma Aamna tana share sharenta tana mopping ko Ina Ahmad Yana kallonta ta gama,sai kunci yakeyi Yana faman huci,duk abinda take Masa baya gani,tana gamawa da ciki ta fita compound kasancewar me Gadi Musa ya tafi Kauye wajen Iyalansa sai Nan da sati biyu ko Uku zai dawo,Duk girman Compound din Haka ta gyara shi,Ahmad ya fito yace sai ta wanke Masa machine Haka ta wanke Masa tas,ta Sha wahala da kyar take mikewa,Yana Fitowa ya kalli Tyre Kawai ya juyo ya kwashe ta da Mari a saman Idonta Wanda yake mata ciwo,Botikin ruwan data wanke Masa Machine ya dauka ya juye Mata ruwan a kanta gaba Daya,Aamna ta fashe da kuka yayo kanta ta matsa gefe sai ga Siyama ta shugo da sauri Tace lafiya Ahmad????....Kafin ta rufe Baki ya fyallawa Siyama nata rabon marin Yana cewa Yan Iska matsiyata,Aamna duk dukan da ya Mata Bata ji haushi ba sai Akan ya Mari Siyama,Machine dinsa ya buga ya fice,Siyama ta fara zuga Aamna Tace wallahi ki bar gidan Nan Aamna Idan ba so kike Watarana a tsinci gawarki ba,Wannan Bai da hankali kwaya da giya sun Gama da kwakwalwarsa,tun dare Bai Miki ba ki bar Masa gida,gwara ki rasa aurenki Akan wannan halin da kike ciki,auren me auren wahala,Iyayensa su na can sun barki idan an kashe ki Basu da asara,Dansu Yana raye suna da kudi abinsu kece a kasa Aamna ki Kama gabanki kinji na fada miki. Aamna Tace Mummy fa ba Haka Mukayi da ita ba,Mummy din banza,wallahi ki farka daga mafarki Aamna ko sonsa kikeyi? Da sauri Aamna Tace Allah ya kiyaye min tir na so wannan mutumin,Siyama taji Dadi a ranta Tace to ki hada kayanki ki tafi gidanku na tabbata Baba bazai Bari ki dawo ba ki fitar da kanki daga wannan masifa,Aamna Tace gaskiya kika fada na gode Siyama ke me kauna tace Inshaallah yau a gidanmu Zan kwana Bari na hada kayana idan ya dawo da wuri Zan tafi yau idan Bai dawo ba gobe da sassafe Zan taho,Siyama Tace yafiye Miki Ni na tafi ta fice abinta,Duk Hirar da sukeyi Ahmad Yana jinsu ashe Daya fita da machine ta Kofar me Gadi ya shigo Dake Kofar me Gadi biyu ce akwai ta ciki akwai ta waje,Dama shi ya gaji da su so yake ta bar Masa gida ya samu Freedom ya gaji da shishingi da take masa,yafi so ta Kori kanta da kanta sabo da Mummy Kar taga laifinsa,farin ciki ya kamashi,sabo da tayi sauri ma ta bar Masa gida sai da 5pm tayi sai gashi ya dawo gidan da fara'a Yana ta rera wakar Bob merly Yana girgiza Kansa Yana lumshe Ido har Palo. Sharhi Dan Allah AsmaBaffa 10/26/21, 8:52 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 36-40 FREE PAGE DUNIYA TA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne ZAHRAH RAMALURV JIDDAH ZEEY SOORAJ HAJIYA ABOU SERLMAH I LOVE MY SAIF Aamna Tana kitchen kamshi na tashi ta fito tare da furta Sannu da zuwa,Annurin fuskarsa ne ya gushe ransa ya dugunzuma ganin Bata da alamar tafiya,Tsaki Yaja yayi waje abinsa Bai dawo ba sai 9pm zazzabi ya dawo da shi gida,tana kallo a Palo taga ya shigo Yana kankame jiki Yana Rawar sanyi da sauri ya fada saman doguwar kujera ya dunkule,Aamna Tace lafiya? Harara ya watsa Mata tare da furta duk bake kika jawo ba,bakin cikinki ya zuba min zazzabi,Aamna Tace au nice? da wacece idan ba ke ba Kawai kinzo kin tare min fili da Fadin gida,ba dama na samu Freedom na Wala Ni da gida na,Dariya tayi Tace to Yi hakuri,bazan hakura ba sai kin bar gidan Nan cewar Ahmad,Ni kwata kwata ba kaunarki nakeyi ba,Sam Baki min ba tsarin zubinki gaba Daya Bai min ba,Aamna Tace duk kyan Nan nawa? Wani kyau ne Dake an fada Miki kyau nake Nema idan kyau ne naje na kalli kaina Mana har Zaki fada min kyau? Dariya ta Kama Aamna yace ke Baki da kunya ko tsagera ko fitsararriya ko? Idan ba tsaurin Ido ba ki kalle Ni kice me? Ki tafi gidanku na gaji Dake Ni,Ina Nan daram wallahi baka Isa na bar gidan Nan ba. Bargo ta Mike taje ta kawo tare da lulluba Masa Tace ko na shigo ciki na Dan jona maka heater? Wlh idan kika shigo bargon Nan yau Allah ne yasan irin dukan tsiyar da Zan miki,Dauko min magani a dakina paracetamol da ruwa,Aamna taje ta kawo Masa ya Mike ya karba ya Sha,Tace ko a Kira Likita ya maka Allura maybe Malaria ce,Ni ba a min Allura babu Wanda zai sokar min duwawu ko Hannu,Ina ma Likitanci na karanta ko Yar Hygiene din Nan da wallahi sai na tsira ma Allura cewar Aamna ta furta tare da daukan waya ta Kira likitan da Mummy ta hada ta da shi Wanda ke duba Ahmad,Bayan sun gaisa ta fada Masa,a daren yazo ya duba Ahmad ya rubuta magunguna yace malaria ce,Bayan ya tafi Aamna ta Aiki Musa ya siyo Magungunan. Lokacin jikinsa yayi sauki ta hado Masa cous cous da miyar kwai ta kawo ya karba yaci ba laifi ta bashi Magungunan Tace sha,yace sai ki dura min ta karfi bazan Sha ba,Aamna Tace okay sabo da ba kwayar maye bace ko? Yace ae ai Wanda baya shaye shaye ya bar Dadi ya furta da slow, Zan fadawa Mummy Allah gwara ka karba ka Sha, ki fada Mata Mana tsoro nake ji ke Baki ga ba Wanda yake fada min naji bane?na gani Dan Allah ka Sha zaka daina zazzabin,Da kyar ya karba ya Sha yace gobe bazan Sha ba,ya tashi ya koma bedroom dinsa, kwana Uku Aamna tana fama da shi da kyar ta samu ya Gama shanye maganin Kuma ya warke fes. Siyama ce ta kwada Sallama tare da shigowa,ta Iske su Mashkoor a palon lokacin Aamna tana bedroom tana bacci,ko nemanta Bata Yi ba ta zauna wajen Jibson ta kalle su Har Ahmad Wanda ke latsa waya,Ta kalli kayan mayen tace gaskiya Kuna birge Ni wallahi,Musamman idan na kalli giyar Nan Dake cikin dundumemiyar kwalaba,Ina so inga Ana daga Dunduma a duniya,Suka kwashe Dariya banda Ahmad,Jibson yace kaji fa sabo suna Wai Dunduma,Siyama taji Dadi Tace Ni ko Mijina naga Yana daga Dunduma bazan damu ba Zan koma Taya shi Sha ne, Mashkoor yace Baki da hankali mu kanmu so muke mu daina mun kasa Amma ke kina mace kina wani Eh yane Haba Yawa kike,Siyama taji haushi a ranta ganin Bata birge su ba sai ta tashi zata haura sama wajen Aamna Ahmad ya daga Mata Uwar Tsawa yace idan Baki bar gidan Nan ba wallahi na tashi ko ya Mike a zabure Yana cewa Upstairs din na Ubanki ne? Ko da kwandalar Ubanki aka gina gidan da har Zaki kallar min sirrin Dakuna,Shegiya da kanki Kamar butar Shayi, da gudu tayi hanya ta fice. Jin Hayaniya Aamna ta tashi ta fito itama tana murje Ido Tace lafiya naji Hayaniya?Takalminsa ya cire a zuciye ya Wulla mata yace ai duk ke kika jawo Ina Zama na lafiya Yan Iska Kun dameni a gida wallahi ranar lahira sai Allah ya Kamaki da hakki na,sai Mala'iku sun jibge ki da almudun bakin karfe,Su Mashkoor cikin kwaya Suka ce Kuma ta saman kwakwalwarki zasu dirka miki kinzo kin Sa abokinmu a bacin Rai,Dariya ma Suka Bawa Aamna Tace Dani da ku zamuga Wanda za a jibga a lahira kuci gaba da Shan kwaya ku gani,Kana jinta fa King cewar Jibson,Ku kyaleta Bata da hankali ai. Bayan wasu kwanaki Aamna Sam zaman gidan ya ishe ta shi yasa kullum sai ta fita siyo kayan Miya ko kifi ko nama etc Dan kawai ta Dan shakata,yau ma Shiryawa tayi ta tafi kasuwa zata siyo vegetables, Duk da Haka Siyama Bata hakura ba ta dawo gidan Aamna ta Iske Aamna ta tafi kasuwa,yau ba ma Jibson,Ahmad,Mashkoorsu Uku suna gidan suna kallon ball suna shaye shayensu,su Jibson sun turnuke palon da Hayakin Shisha da Wiwi,Ahmad kuwa Giya yake Sha a kwalabar Yana dagawa,Ganin Siyama ransa ya sake baci Amma baiyi magana ba,Jibson yace mayya an dawo ne? Mashkoor Yana tangadi yace Chaiii....Wai ko harda ke aka Daura Auren ne? Ko Mata biyu aka bashi Bamu Sani ba?to wallahi mu dai Iya Aamna muka ji ance an daura Aure mu ita Muka sheda an daura da ita cewar Mashkoor,Jibson ya kalli Siyama yace ke muna wajen fa har mandiri aka kada Ana Waka Ana Ahmad Angon Aamna Gam.. Gam... sannan kizo ki Raina Mana hankali. Siyama tayi banza da su sai ga Aamna ta dawo Siyama ta Mike Tace balarabiya kin dawo? Da murna Aamna ta wani tuno Dan guntun larabcinta Tace Marhababiki ya Siyama ta wani Rungume Siyama har da Yi mata kiss a kumatu Wai ita Balarabiya,Siyama da munafunci Tace Aina tazhab? Wai ina taje, Azhab Ilal suk cewar Aamna wai da larabci taje kasuwa Wanda da kyar suke tuna Dan abinda suka tsinta wani ma ba daidai suke fada ba,kiyi Hakuri na Dade ban San kinzo ba,Siyama Tace Ma Fi mishkla,Mashkoor yace cab da Kun taimakawa kanku Kun daina Sam Baku iya Larabcin ba,bakinku ya dafe da miyar Kuka zaku Raina mana wayo Baku Iya komai ba,Jibson ya nuna Ahmad yace da kun San irin Larabcin da King keyi ai da Sai Kun Mari kanku da kanki sabo da haushin kanku zaku ji. Aamna Tace Kai ku kiyayeni matar oganku ce Aunty ya kamata Kuna kirana bana Wasa da ku,Dariya sukayi Suka ce Aunty Balaraba daga yau,tun daga wannan Rana kaf abokan Ahmad sai dai sucewa Aamna Aunty Balaraba ita Kuma amsawa takeyi. Washe gari da dare Aamna ta kawowa Ahmad Abinci ganin baici komai ba tun Rana,Ashe hakan data Yi shi haushinta yaji ya tsaneta ya gaji da takura Masa da take yi Kawai ya dauki abincin ya watsa Mata a jikinta stew din Allah yasa ba zafi ta Bata Mata riga,Taji Matukar haushi har ta fusata Tace barin gidan zata Yi ,da sauri ta dakko mayafinta,Yana ganin Haka sai murna ta kamashi,Aamna sai ta ganshi har murmushi yakeyi sai ta fasa tafiyar ta dawo gabansa Tace ranka ya Dade zanje na siyo Abu a shago tayi waje,ransa yayi bakikirin sabo da bacin rai tashi yayi ya tafi wajen Me Gadi Musa,Musa Yana Zaune a Bench Yana waya da matarsa Ahmad ya zauna a Bench din. Musa cikin wayarsa yace da matarsa na Baki Ruhina gaba Daya,da sauri Ahmad ya kalli Musa yace baka da hankali idan ka Bata Ruhinka Kai Kuma ya zaka Yi da rayuwarka kenan ka bata Ruhin ka mutu kenan? Musa ya dagawa Ahmad Hannu Wai yayi shuru yaci gaba da cewa Ni gaba Daya na Baki duniyar Nan gaba daya ma Uwar gida na,Baki Ahmad ya bude da bala'i irin na Yan kwaya yace Kai...wai...to nufinka idan ka Bata Duniya mu da sauran mutane da muke ciki mu tafi Ina a Ina zamu zauna?ko sama ta Daya zamu koma,Musa ya kashe wayar yace a'a ikon Allah Oga Ni Matukar zata ji Dadi ku tafi sama ta goma Mana,Ahmad yace Kai Musa wallahi Indai zaka ci gaba da wannan furucin na soyayya wani ka Bata Duniya wallahi sai na koreka a aiki,akan me Dan wulakanci Muna zaman mu lafiya cikin duniya kace wani kayiwa wata banzar matarka kyautar ta,Baki Musa ya Bude sai Kuma ya tuna Ogan nasa Dan giya ne kwakwalwarsa da motsi Kuma Bai taba soyayya ba shi yasa. Musa yayi Dariya yace Allah huci zuciyarka Oga ai duk kalaman soyayya ne ai duk abin karya ce,Kenan duk karya kake mata? Ahmad ya tambaya Musa yace ai Dan aji Dadi ne,yace kenan soyayyar da ake fada duk karya ce? Musa yace duk ita ake zugawa juna,Nima fa Oga cewa tayi ta bani zuciyarta,Baki Ahmad ya bude yace to yau duk sai kunci ubanku wallahi maza tashi ka dakko Cooler dole ta Ciro zuciyarta ta baka ka saka a Cooler,Musa Dariya ta Gama Kama shi,Yace zaka Yi Dariya da kyau yau sai naga ta inda zaka Ciro Ruhinka Dan Ubanka,Kai ba mala'ikan daukan Rai ba komai ba kace wani ka Bata ranka Dan Ubanka gashi kana motsi kana numfashi yau sai ka Bata ka mutu yanzun Nan,Musa ya sake kecewa da dariya shi Ahmad Bai San soyayya ba,yace tsuguna yau sai ka kinkimi duniya a kanka Baki Daya ka Kai mata har kauyenku sannan bayan ka Kai Mata mu Kuma kazo kasan inda zaka Kai mu,Musa yace kayi Hakuri Oga na fasa Bata wallahi bazan Bata ba na Kuma fasa karbar zuciyar Tata,Ahmad yace Yan iskan banza da ka Bata mu gani mana,Kun zauna Kuna biyewa Mata ya Mike ya fice daga gidan. Aamna zaune take suna waya da Mummy,Mummy Tace Aamna me kike so a duniya ki fada min ko mene Zan Baki,Aamna Tace Mummy da gaske ko mene?Mummy Tace kwarai ai tunda kika iya jure Zama da Dana Ahmad a wannan halin ba abinda bazan Miki ba,Aamna Tace dama Ni burina idan na samu kudi naje Hotel na kama daki nayi kwana Uku Ina Shan ac,azo a gyara min room nayi order abinci naci nayi bacci,sannan Buri na na biyu idan samu kudi nayi wanka da ruwa Eva ko Swan,sannan naci abinci na wanke Hannu na da ruwan Roba,Dariya Mummy tayi Tace Anya kuwa Aamna kin Kai 25yrs ko kema kin fara Shan kwayar ne?Dariya Aamna tayi Tace Allah Mummy,to shike Nan ba yanzu ba ki Bari sai Nan gaba cewar Mummy sannan ta kashe wayar. Da dare Ahmad zaune yake a bedroom dinsa Yana Danna System Aamna ta shiga dauke da tiren Abinci ta Ajiye Masa,Tsaki Yaja da masifa yace ce Miki akayi yunwa nake ji? Bazan ci ba ki dauke abinki tun kafin nayi fatali da shi,Wayarsa ce ta shiga Kara yaja tsaki sannan ya dauka yaga Humaira ce kanwarsa dagawa yayi,yace sis ya akayi ne Mene ne Zaki dameni? Yaya dama gobe zanzo na kawo maka Ziyara,Fuska ya Bata yace ke karki zo min Ni Kun dameni kije gidan Saddeeq Mana sai Dole waje na Zaki zo wannan Candy da kika Yi ai ta zame min masifa tunda damuna zakiyi Dan Allah ki fadawa Daddy ya saka ki a University da wuri Haba,Dariya Humaira tayi ta Shiga rokonsa Dan Allah Yaya so nake fa nazo na ganka please.....Shuru yayi mata,Tace Yaya Dan Allah zanzo kaji....ke mayya karki lashe ni ki tsotse min bargo yau she Zaki zo? Kwana biyu ko Uku Kuma Zaki Yi,Tace to Gobe Yaya da wuri zan bi flight sai kazo ka daukeni a Airport,Alright sai kinzo murna Humaira ke Yi harda godiya,Aamna tana jinsu ta dauke Abincin tayi gaba,me Gadi ta kaiwa gaba Daya. Washe gari 2pm Humaira ta sauka,Aamna gani tayi ya Sha wanka cikin kananan Kaya wasu masu kyau ya fito ya hau wani machine dinsa Irin na Yan achaba Quilin ya tafi Airport,Humaira ta ganshi a machine ita Bata taba Hawa machine ba,ta Rungume shi tana murna ya janye jikinsa Yana dariya yace sis bana son wannan haukan kin girma ku Yan Lagos Baku da tarbiyya,Dariya tayi Tace Kai Yaya Kai fa yanzu muharramina nane fa,ku dai Kawai Kun dauki aladun turawa ya furta tare da rike Mata Hannu yace Oya hau mu tafi,ta kalli machine Tace Yaya kasan fa ban Iya hawa machine ba Kuma ai ya kamata ka aro mota ko ta abokai ce ka dauke Ni,Wanda Basu da motar kuma fa gasu Nan Ni ban Iya aro ba idan Zaki hau ki hau ko wallahi na tafi na barki iskancin banza Kawai ya fara bala'i,Humaira tayi Dariya Tace Kai Yaya ta ja kitson calabarsa tace da a Kano ne da tuni Yan Hisba sun Kamaka,Yace su ma Wanda suka Raina suke wa. Daukanta yayi tare da daura ta a saman machine din,Jakarta Kuma ya daura a gabansa ya figi machine Kamar zai tashi sama Haka yake fyalla uban gudu da Humaira tana ta dariya ita Dariya yake Bata. Aamna tana cin abinci a Dining suka shugo,Humaira ta taho da gudu zata tafi wajen Aamna Tace laaa Auntynmu...Auntynmu...da sauri Ahmad ya cafke ta yace ke wace Auntynki? Baza kije wajenta ba wajena kika zo ko wajenta? Humaira tayi Shuru yace muje sama,Murmushi Aamna tayi tace Barka da zuwa kanwata,Humaira ta dago Mata Hannu zanzo mu gaisa Aunty.....fisgar Hannunta Ahmad yayi Suka tafi sama Yana Hararar Aamna,Aamna Dariya tayi Kawai duk tayi laushi ta nutsu sabo da Duniya garata takeyi. Hana Humaira Fitowa yayi sai da ya tabbatar ta shiga wanka sannan ya fita ya Mata take Away na abinci Wai baza taci na Aamna ba,Yana dawowa ya Iske Aamna da Humaira suna ta Hira suna dariya,Muzurai ya fara Yi ya karaso tare da fisgo hannun Humaira yace wa yace ki kula min kanwata ko kanwarki ce? Aamna tayi Masa shuru kawai, a palon Suka zauna Humaira gudun masifarsa yasa taci abincin nasa ta koshi,Humaira Tace Yaya yanzu a machine kake yawo?gaskiya Daddy Bai kyauta ba,Ke share wannan zancen Ni nafi Jin dadin ma machine Dina,Aamna ya kalla yace Baban wasu kuwa ko Tyre Bai da ita bare mota,Aamna Dariya Kawai tayi,Humaira tana ta Mata magana da Ido,itama Aamna tana maida Mata da Hannu da ido,Ahmad idonsu Kawai yake gani Yana motsi, tashi yayi Kawai ya fice abinsa,Nan Humaira Suka zauna da Aamna suna ta Hira abinsu. Tunda Humaira tazo Aamna ta samu kawa har fita kasuwa sukeyi da yawo Ahmad ya kyalesu harkarsa yake yi,Haka shima Humaira ta takura Masa Wai sai ya kaita yawo a Machine,da ya fita da ita yawo yau suna ta zagawa duk Wanda ya kalli Humaira sai yayi Masa bala'i. Wani guy ya ga Humaira kyakyawa ta birgeshi suna tsaye da Ahmad a jikin machine Yana ce Mata Sis na fada Miki kina saka Nikaf tunda ku Kuna kula da Addini Kawai ku rungumi Islama hannu biyu kina saka Hijab da Nikaf kin fa girma tam,I'm warning you Sis,Humaira tana ta dariya shima ya kalleta ya dinga dariya a jere a jere irin ta Yan Kwaya ba kakkautawa,Humaira Tace Yaya kaima kana ganin kyanka Mata sai kallonka sukeyi,Ke dalla rabu da su sun kalle Ni a banza ai duk wacce ta Soni to Allah ya jarabce ta sabo da ban Dace da a so ni ba sis,Humaira taji tausayinsa kwalla ta cika Mata Ido Tace Yaya Wai waye ya koya maka shaye shaye ne Wai? Handkerchief din Dake hannunsa ya zabga Mata a Fuska yace muje gida Yana Juyawa yaga saurayin Nan ya kafe Humaira da kallo,a fusace ya nufi wajen saurayin yace zaka lalata min kanwa Dan uwarka me kake kallonta kana ayyanawa a ranka? Kana Nan kana ta kallonta kana ayyana wani Abu ko ya Kai Hannu zai chakumo shi Humaira ta rike shi tana bashi Hakuri Dan Allah Yaya ka barshi mu tafi,Fisgewa yayi ya dauki wani karfe da ya gani a kasa zai buga masa,Humaira tace ka gudu wlh,Matashin Nan ya arce a tamanin Dan yaga Ahmad ya birkice lokaci Daya ya haukace,Masifarsa ya maida Kan Humaira yace gobe Zaki tafi,Kuka ta saki Tace Allah Yaya Ni sai nayi sati Daya,Zan mareki gobe ki shirya ai kinyi 3days tafiya dole hau machine mu koma gida. Tunda suka tafi yake masifa Yar wa na lalata da Za'a lalata min kanwa,Bana kallon Yar kowa shine za a kalli kanwata,ko Wannan Yarinyar da akace matata bana kallonta shine wani zaizo ya fara ayyana wani Abu a ransa a Kan kanwata. Humaira da suka koma gida Bayan ya fita ta Bawa Aamna labari,Aamna Tace kwaya ce fa ke sashi wannan zafin zuciyar,Humaira Tace Aunty kina kokari Allah ya bada ladan Ibada,gashi gobe yace dole Zan koma ya zanyi, kiyi Hakuri ki tafi kawai,ai dole cewar Humaira,Haka kuwa washe gari 11pm ya Kai Humaira Airport ta koma lagos. Yau ma kamar ko yaushe Jibson da sauran abokan Ahmad suna Palo suna kallon ball sai ga Siyama ta shigo,Aamna Tana kitchen tana girki ita tana mamakin yanda Siyama ke sintiri a gidanta,Fitowa tayi suka gaisa ta samu wuri ta zauna Aamna ta koma kitchen abinta,Jibson ne ya Sosa gashinsa me uban yawa Wanda ya Gama kone shi ya dawo fari irin na Yan Ball,yace gashin Nan nawa ya kamata na Dan rage shi naji kaikayi yake min,Ahmad ya kalli Siyama Fuska ba Annuri yace ke Sosa Masa gashinsa Mene amfaninki,Siyama ta Bude Baki kamar zata Yi kuka Tace Ni wallahi ba Yar Iska bace,Tsawa ya daka Mata Sosa Masa karki Bari na tashi,Siyama ta Mike jiki na rawa ta tsaya a Bayan Jibson ta nutsa yatsunta a sumarsa tana Sosa Masa,Ido ya lumshe yace shi yasa nake sonka Sarkin mu,Kaji wani Dadi da taushin Hannu,Aamna ce ta fito mamaki ya kasheta,Siyama ta kalleta Tace mijikin ne yace sai nayi ta karasa da Hawaye,Aamna Tace ke Kuma ga banza ko dalla cire hannunki,Ahmad yace tana cirewa ke Zaki Sosa Masa,wallahi baka Isa ba Kai din banza ta janye Siyama Tace na tafi gida,Siyama ta fice da sauri ta tafi,Jibson yace Aunty Balaraba me yasa kike Mana bakin ciki ne? Respect your self Jibson Ogan naku ma Bai Isa ba bare ku ta ja tsaki ta haura sama. Washe gari Ahmad wani wankan Sugar ya dauka ya fito Yana wani tattala kafafu Yana Bouncing ga Uwar Gadara Mashkoor ne yazo da machine dinsa Quiln ya dauke shi tsabar basa jin Magana Ahmad baya ya juya ya hau machine ta baya sun hada baya da mashkoor Yana kallon baya shima me tukawa ya kalli gaba,Headphone ne a kunnensa Yana Jin wakar Shaggy da Sean Paul reggae music,Wani uban gudu Suka tsinkawa a Machine lokacin Aamna taje gidan Zuhra a Hanya suka hadu Mashkoor yace ai sai Aunty da karfi,Da kallo ta bi Ahmad irin zaman tijarar da yayi,Zaginta yayi da Hannu ganin tana kallonsa,Kanta ta dauke ta shiga Napep abin ma Dariya ya Bata. Su kuwa Basu tsaya ko Ina ba sai a Bank,ya Shiga ciki masu bin layi kowa Matsawa yayi ya Basu waje Ganin rigima suke Nema,Wani Dan matashi waya ya dauka Yana kusa da Ahmad Yana waya da budurwarsa kasa kasa yace Baby zuciyata kullum Dake take bugawa,da ace Ana bude zuciya Dana Bude Miki Kinga tawa yanda sonki yake dankare a ciki,Ahmad Yana ji ya juyo da masifa yace to Dan Uwarka sai kaje Likita ya yanka maka kirnjin a gabanta ta gani,Wai kowa sai karya a gidan Uwar wa zuciyarka take bugawa da ita a ciki mutum ne zai Shiga zuciyar mutum ta buga da shi,Ina zuciya Yar karama zata dauki nauyin mutum zaka wani ce da ita take bugawa a ciki,da karfi yake magana ai kowa hankalinsa ya dawo kansu sai Dariya akeyi wani tsoho yace yaro kayi gaskiya wallahi wannan karyar ce ta shigo yanzu ta kalaman soyayya. Tsaki Ahmad Yaja ya fitar da kudi masu yawa, wani yace bawan Allah ka Adana kudin Nan Kar ka hadu da Yan Iskan gari,Mashkoor Yana gefe yace ai mune da kanmu baka gani bane mune ai Yan iskan da kanmu a Nan,wa ya Isa ya zare Mana ido,aka Yi Shuru matar tana irgawa Ahmad kudi tana ajiyewa ya galla Mata Harara yace ke ni fa bana son Daudu Yar Daudu idan Baki iya aikinki ba wallahi na Kai kararki a koreki banza,Wai ke ma'aikaciyar Bank harda wani sa glass da Suit ke a dole kina samun salary,Yan Yara daku Kuna rainawa mutane wayo kuka sake kwanan bank Dinku tattalin arzikinsa zai durkushe mu daina Ajiyar kudi,Duk ma'aikatan sun San Ahmad Yana zuwa Yana musu tijara shi yasa Yana zuwa suke sallamarsa ya tafi,suna gamawa Mashkoor yayi wani Bouncing Suka juya Ahmad yace My man oya muje... muje....Yana wani Gadara,Wandonsa Daya sabulo ya danja kadan,Zasu fita kenan sai ga Aamna ta shigo itama zata ajiye kudi a bank,Ahmad ya kalleta Kamar ba matarsa zata wuce su ya riko Hannunta tare da sa damtsenta ya sakalo wuyanta yayi masifar kunyatata a mutane sai ayi Mata kallon karuwa,Fisgewa tayi ya dauke cak tare da Sabata a kafada yace Muje kudin cefanen kika taho ajiyewa bank Zaki tara? sabo da kar mutane suyi Mata kallon karuwa Tace Dan Allah ka ajiyeni Ina matarka Wai kullum sai kaci Zali na,kaje gida your food is ready, Ni ka ajiyeni wallahi,Ana kallo tana wutsil wutsil yayi waje da ita,Wasu suna cewa kanwarsa ce sabo da suna yanayin Kama sosai,wasu Kuma suce da gaske matarsa ce,wasu suce ko karuwarsu ce,Wani yace ai kuwa wannan zata Sha wahalar Zama da wannan bakin kadarar,wanne ubane Yana gani ya bawa wannan auren yarsa oho. Wajen Machine suka fito,Kamar Yana da hankali shi ya fara Hawa machine din sannan ya Mata Tsawa yace hau,Haka ta hau bayansa Mashkoor ya fige su kamar zai tashi sama,ya dinga kwanto a titi Yana ratsa motoci sai ihu sukeyi Aamna tsoro ya kamata ta kankame Ahmad yace wallahi idan Baki sake Ni ba sai na jefo ki a tsakiyar kwalta,kin sakinsa tayi har suka kaita bakin gate yace sauka,ta sauka yace kina Wasa da Mummy ta kawoki Nan kina wani yawo anyhow,Aamna tayi banza da shi ta shiga gida,Bai Dade ba ya dawo ya Iske ta baje saman Kujera tana bacci,ruwa ya ebo a kitchen ya sheka Mata a Fuska ta tashi a firgice,Harara ta balla Masa ta Mike ta wuce Bedroom dinta tana saka ranar da zata bar gidansa domin ta gaji. Garin Lagos Unguwar Masu hanu da shuni Mummy tana zaune Tare da Humaira a wani gida na ubansu Wanda idan ka kalli gidan ka kallo gidan Ahmad duk kyansa sai ka ganshi gidan talakawa,Humaira ce ta dauki waya Tace Mummy Bari na Kira Yaya naji,Ahmad ta shiga Kira Yana ganin Sis ya daga da sauri tare da furta sweety,Dariya Humaira tayi Tace Yayana ya kake yace Ina lafiya sis ya school,ai nayi Candy Wai ka manta na fada maka Yaya? congrat...Congrat Sis,Yaya Ina matarka? Zamuyi fada fa Ni nasan wata ne Kawai dai nasan Wacce Mummy ke so karki dameni Zan kashe wayata,Sorry Yaya ke ba Wani Yaya kauyanci ne karki Dora min tsufa da wuri wani Yaya,ki kirani Ahmad Dina sak ko King,Mene wani Yaya,ai girmamawa ne Yaya,bana son wani girmamawar mutane a wajena ke dalla Ware kiit ya kashe wayarsa Yana tsaki,Mummy ta kalli Humaira tace ai halin Ahmad sai shi na rasa inda ya gado halin Nan,Allah ya kyauta. Faratan Ahmad sun Kara tsayi sosai,Aamna tana zaune a Palo Yana kwance ta juyo ta kalle shi,Fuska ya Murtuke,Kallonsa ta sake Yi tana kasa a zaune ta jingina da kujerar da yake kwance,kanta ya dafe tare da Danna kanta kasa,Kara ta saki ya fisge dankwalin Atamfarta ya zabga Mata duka dashi,layun Dake kanta ya kalla ya saki Dariya yace nasan na fiki daraja a wajen Allah duk Iskanci na,ke shirka kikeyi yarinya duk Sallar da kike Yi ba a karba,munafukar banza kullum Sallah da karatun Qur'ani Ashe wurin bokaye kike zuwa,shi yasa Allah ya hadaki aure Dani ya daura Miki kaddarar Zama da me cin ubanki,Allah ne yasan irin Barnar da kike yi,Ni duk Iskanci na bana zuwa wajen boka,bana daura guru da Laya,Yan Iska irinku ne masu yiwa Miji Miya da jinjin Haila,fada min ke wanne kikeyi? Aamna Tace Ni wallahi bana zuwa wajen malam,karya kike munafuka,Ni nasan ba Banza Mummy ta auro min ke ba,kin shiga Uku kuwa ke da Jin dadi sai dai ki gani a makwafta,Aamna tayi Mukus ta Mike tare da cire layun gaba Daya ta yaye Hannunta ta Ware gurunta,ta daga rigarta ta zaro na Hips,Baki Ahmad ya bude yace kin Shiga uku,Uku ma sau dubu kika shiga,Ni ba ruwana da tsafinki ki maida abinki kece Zaki ga ba daidai ba a duniya,Zuciyarki ba Allah oh a Haka Shuru Shuru Dake sai daukan carbi da sallah,Ana karatun Qur'ani Ashe duk bana tsoron Allah bane,asubar fari za a jiyo muryarki har makwafta ya makale Murya tare da gwada Muryar Aamna yanda take karatu Wai Allazikhalakhal samawati wal'ard.....Ashe bana tsoron Allah bane wallahi sai Allah ya tambayeki. Aamna tayi Mukus yace ai dole kiyi Shuru ki kalleni kice me? Watarana sai Allah ya Toni asirinki. Dariya Aamna take Yi ta fara warware layun a gabansa da gurun,ya kalli takardar me Rubutu yace ga harafin A'lif da Hya'un can Wato Sunana kenan Ahmad gashi can na gani,Aamna ta tattara ta kone komai,yace a banza yarinya Yar bori mutuniyar banza,Harararsa tayi ya Mike ya bita zai daketa tayi daki da gudu Yace ki dake Ni ki hanani kuka ki min asiri in gani da Ido na ki dawo Kuma ki harareni Ni ban harareki ba sai ke,Zaki fito ne. Washe gari Aamna gajiya tayi ta fito lokacin zai fita tace Yau zaka nemeni ka rasa a gidanka yau Zan tafi gidan ubana,wani farin ciki ya Kama Ahmad yace Dan Allah da gaske kikeyi? Aamna Tace da gaske yau a gidan ubana Zan kwana,wani murmushi ya saki yace gaskiya ban taba sanin kina da kirki ba sai yau,Sabo da Haka yau dole Nima na gwangwaje ki,fada min me kike so? Aamna ta turo Baki ta samu waje,yace ai yau ko me kike so Zan miki,Aamna ta Kama shagwaba Tace koma mene ka bani kyautar Ina so,Ido ya zaro Mata wasu farare tas sai da ta tsorata Yace Gaskiya Zan fada Miki ke Yar Albarka ce babarki ta iya haihuwar Yar halak Haka nake so,yanda kika faranta min yau ace ban Miki kyauta ba nayi asara bani da amfani Kawai na mutu yanzu,Dariya ta Kama Aamna duk akan Tace zata bar Masa gida shine yake wannan murna Haka,wannan kiyayya wacce iri ce,Tunaninta ya katse Mata yace shirya kizo mu tafi na kaiki Shopping ki zabi abinda kike so na ban kwana,Dan Allah Kuma idan kin tafi karki dawo har abada kinji,Aamna Tace to,yace ko Mummy Tace kice a'a ke ba 'yarta bace ta juya Humaira Yarta data haifa Amma ba ke ba,Aamna Tace to,yace Ina jiranki,Da gudu taje sama ta canja wata Arabian gown Dark green me adon black ta Sha kyau ta fito. Machine dinsa ya gyara ta hau ya fisgeta Suka tafi sai wani katafaren Mall,tare suka shiga yace Ina jiranki zabi duk abinda ya miki,Aamna Bata zabi komai ba ta wuce Bangaren Gold ta zabi wata sarka me kyau da zobenta da Dankunne,yace shike Nan abinda kike so? Tace ae,Kai ya girgiza yace to dauka,Haka ta dauka yaje ya biya kudin Suka tafi,ya maidata gida zai fita Tace to saka min da Hannunka kaga anjima Zan tafi,yace ai yau ba abinda Zaki ce banyi ba tunda Zaki bar rayuwata na huta kawo,Mika Masa tayi ya saka Mata sarkar da kansa da dankunnen,Yatsanta ta Mika Masa ya sa Mata zoben,yace Nice one, karfe Nawa Zaki tafi? Aamna Tace 6pm yace Good,ya Mike zai fita Yana ta murna yau zai rabu da Kaya ya huta,Aamna Tace Idan ka dawo sai na tafi,yace to ai da wuri kuwa Zan dawo ya fita Yana ta murna Kamar an Masa albishir da Aljanna,Tun kafin 6pm ya dawo gidan ya shigo Yana wakar Bob merly Yana Bappalo Soldier........Ye...yiye....yiye.....Yee...Yee....yiye... Sharhi fans Dan Allah. AsmaBaffa 10/26/21, 8:52 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 41-45 FREE PAGE DUNIYA TA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne ZEE NANDU KALTUMA ZANNA SADEEY(QUEEN) TEEMA'S COLLECTION .Aamna daga kitchen ta fito tana amsa Masa wakar tasa tana girgiza Kai ta kwala da karfi Ohhhhh.....yeyi..yiye...your.....bappalo soldier....tsit Ahmad yayi murna ta koma ciki da Alama Bata da Niyyar tafiya,Girar sama data kasa ya hade kamar an Aiko Masa da Mummy ta rasu,Aamna kuwa Bayan ya fita zuciyarta ce tayi sanyi ta huce,kafin ya dawo Allah ya yayyafawa zuciyarta sanyi da Hakuri sai ta fasa,Siyama kuwa tunda ta tafi tana sa ran Aamna zata bar gida take ta murna tana uban Kiran Aamna akan taji ko ta bar gidan Amma karshe ma Sai Aamna data Kira Aamna tana dagawa sai taji tana dariya Tace ke Siyama na fasa tafiya na huce,na tuna ma fa Dan kwaya ne ba a ba'a hankalinsa yake ba nayi Masa Uzuru,ko ba komai ma ai Ibada nakeyi,aure Ibada ne zanci gaba da Masa Addua Allah ya shirye shi,Siyama ta danno Mata ashariya Tace wannan bazai taba shiryuwa ba,Ibadar me aure ne kadai Ibada a duniya,Aamna Tace Sanda Zaki auri Faisal ai masifa kika Kama Yi min akan nace kinyi gaggawa yanzu Kuma Ni da gidan mijina Zaki shigo kina min katsaladan a gidan aure na,kin fa Sanni Siyama ki daina uzura min Ina ta Miki Kara bakya gani,Ya kashe Ni ma Mana Ina ruwanki,Siyama Tace Iyyeee....Mrs Ahmad shike Nan kije ki zauna a wahalar,Tsaki Aamna tayi tare da kashe wayarta. Yana Zaune sai kunci yake faman yi,Aamna ta kamo Sunna tv taci sa'a kuwa an saka Wa'azin Malam Ahmad Tijjani,Yana magana akan hatsarin shaye shaye,Yace yanzu Duniya Malam ta lalace da shaye shaye,maza,Mata,Yara,manya,Dattijai,abin haushi ma Yara kanana matasa sun Gama kashe kansu da shaye shayen kayan Maye,abin Allah wadai matashi lafiyayye ya jefa Kansa a halaka,ya Zama marar amfani a rayuwar Musulmai,Musulunci bazai Yi alfahari da su ba,Shan Alkhabis,baza a Sha Aldayyib ba,Mene Alkhabis? Alkhabis shine abinda idan anci ko an Sha bashi da dandano me Dadi a Baki sannan a jiki Yana cutarwa,Aldayyib shine a Baki da Dadi a jiki Kuma Yana da amfani me kyau. Ko matasa jira kuke sai an lissafa muku a Alqurni ance Giya,taba,Wiwi,har Ana kawo ayar Allah Kuna cewa babu Aya,Ina Iyaye wallahi ku farka,Matasa maza da Mata Kuna da hankali,shaye shaye na kwaya,na hayaki na ruwan barasa da sauransu bashi da amfani ga rayuwarku sai cutarwa,Kun Zama marasa amfani a cikin Musulunci,shaye shaye shi kadai yana barna ba adadi a wajenka matashi,na farko shine Kai da lafiya kunyi bankwana,zai kassara maka lafiyar kayan ciki da dama,sannan babbar Illa zai rabaka da Allah,zai rabaka da addinin Allah,zai hanaka Sallah ko kayi ma kana cikin maye baza a karba ba,Azumi ma Sai ya hanaka domin zaka dauka ka kasa kaiwa sabo da dole sai ka Sha kayan Maye zaka zauna lafiya ya Gama bin jininka,sannan zaka sabawa Iyayenka babbar matsala sabo da dole sai ka kangare,ka bijire musu zaka cutar da su. Kasan kuwa wa ake cewa iyaye,ya ku matasa wallahi wallahi ku guji fushin iyaye,masifa ne Mahaifiyar ko Mahaifi su zubar da Hawaye a kanka,basai sun maka Addua ba Kai da ganin dai dai a rayuwarka sai in ka tuba sun yafe maka,wani abin haushin ma Iyalinsa zai dinga zalintar matarsa da yaransa,ya mazaje ku San hakkin matanku mataye Kuma wallahi wallahi kuji tsoron Allah duniyar Nawa take,bakwa ganin halin da ake ciki mafi yawan alamomin tashin kiyama sun bayyana,nuni ake mana mu Kara gyara Hali lokaci Yana matsowa,wallahi a Haka Ana da saura da saura Ana ganin kamar da saura a Haka za a wayi gari aga manyan alamomin tashin Alkiyama sun fara Bayyana..... Ahmad Yana ji ko a gefen rigarsa sabo da yaji Wa'azin Daya fi wannan zafi ma, Canja Chanel yayi yace idan Kinga dama ki gayyato malaman Nigeria kaf su zagayeni ki gani idan zanji na gyara,Aamna Tace ikon Allah a ranta Tace lallai wannan bazai canja ba gwara na nemi mafita,Giyarsa ma taga ya dakko ya Balle Yana korawa, Tsoronsa ya sake shigarta,jiki a sanyaye ta koma dakinta,a palon ya dinga zage zage tana ji,Haka tayi kwana Uku lokacin tuni taje ancire Mata plasta da aka manne Mata ido,sai ganin Idonta yayi tar da Alama ba abinda ya sameshi,Kallo daya ya Mata yace makaryaciyar banza,Shuru tayi sabo da ta gaji da kulashi Yana dukanta,da Yamma kwayarsa ta motsa Aamna taga yanayinsa ba mutunci,taja mutuncinta tana zaune a Palo Siyama ta kwada Sallama,tana shigowa Ahmad ya daka Mata Tsawa yace koma inda kika fito,da sauri ta juya ta fita,Ya zaka koreta?Aamna ta tambaya yace ke wallahi idan Baki daina min magana ba Zan sa wuka na Miki yankan rago,Aamna Jin irin kashen kashen rayuka da akeyi yanzu sai ta tsorata tayi sama da sauri kayan sawarta akwati biyu da duk wani abin bukata shi ta kwasa tayo kasa,Murna wajen Ahmad ba a magana,ko kulashi Bata Yi ba tayi waje,da kanta ta Bude gate sabo da me Gadi baya Nan,Tana fita Napep ta Shiga da kayanta sai gidansu. Su Mama suna ganinta sun San ma matsalar,Baba yace ya Koro ki ne? Aamna tana Hawaye Tace a'a nice Naga bazan Iya Zama ba Yana min barazana da rayuwata shi yasa na taho Kawai,Mama Kamar gaske Tace Allah sarki kiyi Hakuri komai zai dai daita,dama nasan wannan ba abin yarda bane,karki koma ko Iyayensa sun zo Kuma ko me za ayi karki koma,Aamna Tace dama bazan koma ba,kin San shagona yanzu sai kici gaba da kular min da shi kawai sai na sallami Yaron ciki,Aamna da murna Tace Kinga na huta da zaman Kawai,Mama Tace ae kina hada hadarki da customers me ya dameki da wani banza,Zauna ki huta sai gobe ki fara zuwa cewar Baba,Allah sarki Aamna sai murna takeyi. Washe gari kuskuren Aamna da su Baba sun Aamna matar aure da igoyoyi a kanta Bata nemi Izni ba ta shirya ta nufi kantin Mama,Yaron Dake ciki shi ya nunawa Aamna komai yanda abin ke tafiya sannan ya tafi gida shi dadi ma yaji sabo da Mama Bata biyansa Hakkinsa yanda ya kamata sai wahala a banza,Wayar Aamna ce tayi Kara ta duba sai taga Mummy ce,Sai lokacin ta tuna da Aurenta,dagawa tayi Suka gaisa sannan Aamna Bata boye ma Mummy ba ta fada mata komai,Mummy cike da damuwa Tace kinyi kokari Aamna bazan ce ki koma ba,na hakura kiyi zamanki Kawai Ina Jin Ahmad bashi da rabon shiryuwa,Zan ci gaba da Masa Addua,to Mummy Maganar fita fa?ko naje ya bani takardar saki,Mum Dariya tayi Tace karki nemi saki Ni na Baki Izni ki fita duk inda ya Dace Amma ki kula ki Kama kanki ki sani da Aure a kanki,to Inshaallah cewar Aamna sannan Suka Gama waya ,Siyama ta Kira ta Bata labari,Siyama sai murna Tace kinyi dai dai wannan shine magana karki sake ko da Wasa ki koma,ai dama bazan koma ba cewar Aamna kin ganni Ina kula da shagon Mama,Kinyi dai dai kawata Nan suka Sha Hira sannan suka kashe Wayar,Aamna Ana zaune a kujera ga table da kayan aikinta na calculation,Haka ta kwashe kwana Uku tana zuwa Kantin ta Gama Gane komai tana ta ciniki. Ahmad kuwa Bayan Aamna ta bar gidansa shi Bai ji wani damuwa ba ko a jikinsa,ci gaba yayi da shakatawarsa musamman da ya samu Mummy bai ji ta Masa fada ba,Su Mashkoor suka dawo gidan suka tare kullum sai shaye shaye sukeyi,Ranar da Aamna ta cika sati Daya cif da barin gidan Ahmad ya fito a machine a hankali Yana tafiya a nutse,Aamna ta fito kenan tana aunawa wani yaro barkono karaf suka hada Ido da shi zai wuce,Ido ya tsura Mata itama Haka ya Mata kyau da yawa,Machine dinsa ya karawa wuta ya bar wajen,fasa zuwa yayi inda yayi Niyya ya koma gida abinsa,tunda ya dawo Aamna ce ke Masa gizo a fuskarta,Kawai fuskarta yake tunanowa,Tsaki Yaja ya shige Bedroom dinsa ya kwanta Nan take bacci ya kwashe shi,Mafarkin Aamna ya Shiga Yi suna zuba soyayya tana jikinsa a kwance. A Matukar zabure ya farka Shuru yayi Yana tunani,yace ah....wannan wanne irin tsafi ne? Gashinsa ya girgiza Kamar Yana korar kuda Haka yake karkade Fuskarsa Yana masifa ki bar Fuska na daina ganinki,a'ahhh.....ki daina fito min a Fuska Ina kallonki,wannan wanne masifa ne Haka?.....Ni.....ya nuna Kansa da yatsa ni Zan zauna Ina tunanin mace,kamata Ni a'ahhhh....chaiiii......mikewa tsaye yayi ya kaiwa Iska Naushi yace Zan fasa Miki Baki fa......shi kadai yake ta abinsa a bedroom kamar sabon kamu,Zama ya sake Yi sai Kawai ya tafi tunanin Aamna...Tsaki Yaja yace again....Wai wannan wacce irin yarinya ce ki fitar min daga ido na daina ganinki....kasa ya sakko ya durkusa ya daga hannaye sama Yana Allah ka gani dai Yarinyar Nan sai Tunaninta nakeyi,Ina ta ganinta a Ido na,bazan Iya ba....nasan ni me laifi ne a gareka,nayiwa mutane da yawa laifi Allah karka Yi Fushi Dani ka jarabce Ni da yarinyar nan,Allah kasa na daina ganinta,Allah na tuba,ya Mike tsaye ya sake juyowa da karfi Yana tangadi yace Allah nayi Addua Kuma ban daina Tunaninta ba,kirjinsa ya dafe tare da furta wayyooo....my Heart woooo ....Ina ta ganinta fa ya Allah,Ya girgiza Kansa ya shiga zaga dakin Yana safa da marwa Yana Ohh....ohh.....Ni ta fita daga Ido na,ta fitaaaa.....a Haka ya yini Yana sambatu har dare yayi Bayan ya jero sallolinsa na yini Guda yace Bari na kwanta bacci da wuri ko Zan daina ganinta a idona,Yana kwanciya ya kasa bacci sai tunanin Aamna tana Masa gizo,Shi kadai yace kunga yau bazan iya bacci ba sai tunaninta yau an shiga Uku.....mikewa yayi zaune yace kaiii....yau bazan Iya bacci ba sai na ganta....naji idan ban ganta bazan samu nutsuwa ba,...Amma Bari naje na ganta nasan idan na ganta zan daina ganinta a idona...waiiii....ya akayi ne nake so sai na ganta,Kawai so nake Naga Yarinyar Nan yanzu yanzu,Kawai gidansu Zan tafi yafi sauki ai Zan Gane gidansu ko na Kira Mashkoor ya raka Ni gidan sabo da ai sunje daurin Aure zasu Gane gidan,a hankali yace Amma idan na Kira Mashkoor asiri na zai tonu Kuma na Gama kuri da cika Baki a gabansu abin kunya ne a ganni naje wajen mace,macen ma wannan yarinya,Amma fa gaskiya idan ban ganta ba bazan samu nutsuwa ba Dole na tafi,agogon Dake hannunsa ya duba yaga 9pm yace Bari naje ko ta katangar gidan ce na haura na ganta,gashi wani kunyarta nake ji da tsoronta bazan Bari ta ganni ba. Cikin dare ya dauki pcap ya saka sannan yasa face Mark a Fuskarsa Wai Dan kar a ganshi yaji kunya an ganshi a wajen mace,Musa Wanda jiya ya dawo shi ya bawa key din machine yace Musa zuciyata yau wani Bugawa takeyi bazan Iya tuki ba kaini wata Unguwa,Musa ya karbi key ya hau shima Ahmad ya hau sanye cikin kayan baccinsa wando gajeren da Riga me gajeren Hannu ko a jikinsa Haka Suka tafi,Yana ta nunawa Musa Hanya da kyar ya samu ya gano gidan tunda an taba zuwa dashi sau daya,can nesa da gidan yace Musa ya ajiyeshi,ya sauka yace ka jirani a nan bance ka biyo Ni ba,Musa yace to Oga,Face mark dinsa ya gyara ya bi ta can bayan gidan,Kamar Biri Haka ya Dane saman katanga Dake Bata da tsayi Haka ya haura gidan su Aamna lokacin Baba ya fito zai rufe gida. Ahmad ya labe Bai ganshi ba,Baba ya kulle ko Ina ta gidan,Bai San ya rufe kofa da barawo ba,Ahmad yace yanzu Ni ba abin na shigar musu gida ba,Kuma yanzu Taya zata fito na ganta? Ai wallahi idan Zan kwana bazan tafi ba sai na ganta,Yana tsaye har wurin minti goma sai yaga an Bude kofa an fito sai yaga Aamna ce sanye cikin kayan bacci ta fito da bucket,Ahmad ya Kara labewa ya gyara tsaiwa Yana kallonta Yana zuba murmushi yace kalli Hanci Dan Allah me kyau a Nan wajen.....Uhmmm .....Allah yayi baiwa, panties yaga ta Shanya Guda Uku da Bra Guda biyu,Aamna tafi so ta Shanya Rana ta dake su sabo da kashe kwayoyin cututtuka,Bata son Shanya su a inuwa tasan gobe Rana zata dake su. Ta Gama shanyawa Yana ta kallonta Mama ta fito tace Aamna ki shigo da kujera ciki Tace to,Ahmad yace kaji sunan ma Aam....nah.....my Aamna...no sunan gayu Ahmnaa....Yes...Ahmnna vs Ahmad...A&A kenan a'a wannan Dadi Haka.....kumatunsa ya Mara kadan yace to yanzu Zan Iya tafiya nayi bacci,Zabura yayi yace Kai Nafa haukace,wannan fa hauka ce,Ahmad Ni king Haka Kawai na zauce akan Yar Yarinyar nan,Tsaki Yaja yace Nafa haukace gaskiya....lallabawa yayi ya sake haurawa ya bar gidan,Musa ya hango shi ya taho Yana ta murna Yana murmushi Bai San dalili ba,Machine ya hau Suka koma gida,ranar wani irin bacci yayi me dadin gaske. Washe gari Yana farkawa da Aamna ya farka a ransa,Tsaki Yaja yace Wai na ganta ma bazan huta ba...Haba zuciyata me yasa Wai kike min Haka ne,jiya kinsa naje na ganta yanzu ma so kike ki Kara ganinta Baki koshi ba wannan wanne irin tsafi ne Yarinyar Nan tayi min ne,da safe sai na farka da ita Haba which kind juju be that? Ni ba sonta nake ba duk harkar love...love ba ruwana da shi Amma Kuma so nake na sake ganinta Haba nooooo.....ya Furta cikin karaji,Sannan cikin slow Yana yarfe Hannu yace idan na ganta anjima ai shike Nan Kuma sai na huta,ai abin kunya ne kamata Ina son ganin Yar yarinya,zuciyarsa ya dafe yace sai wani tsoronta nake ji zuciyata tana wani bugawa Haka Kawai idan na ganta to daga yau bazan sake zuwa ganinta ba aikin banza,tunani ya shiga Yi yace Naga kamar ma samari na zuwa wajen Baby dinsu da Kaya Decent,to Amma Ni ai ba Baby na bace,Kuma fa sai taji Dadi idan idan ta ganni da kayan hausawa? Murmushi yayi ya koma Gaban Mirror ya duka Yana karewa Kansa kallo ya shafa calabarsa yace gani kyakyawa ai dole ma na birge ta,hannayensa ya Buda a Gaban mirror ya saki murmushi yace chaii....see fine Boy.....oh..oh....baya Yaja sosai Yana kallonsa yace huuuu...Kalar birgewa kaga Kalar birgewa yesss.....Bari nayi wanka, Fuska ya Bata yace to Mene sai wani murna kakeyi zaka ganta aikin banza,Ni wallahi wani banza ne ma akan mace Subhannallahi ya Dan Mari kumatunsa kadan yace Bari na gwada Kalar murmushin da Zan Mata Nan fa ya shiga sakin murmushi kala kala Yana kallon kansa a karshe ya Dan yake kyawawan hakoransa yace ae tsaya dai dai Nan wannan yayi yawwa ae....sai ya wuce toilet. Tunda ya shiga ciki Yace yau wankan na musamman ne so nake na Kara haske Nan fa ya shiga dirzar fatarsa ba ji ba gani,yace bana wanka da soso yau Zan koma Yi da soso sabo da na fita fes,dubawa yayi bashi da soso,towel ya daura Bayan ya dauraye jikinsa ya fito a Haka daure da towel har wajen me gadi,kudi ya mikawa Musa yace ungo maza ka siyo min soson wanka,karka sake ka dakko min na jarirai me laushi me karfi zaka siyo Wanda Ina wanka Ina Jin radadi,Musa yayi Dariya yace irin namu na talakawa kenan? Karka Bata min time sauri nakeyi Ina da abin yi akan wannan soson wallahi Zan iya sallamarka daga Aiki Matukar baka siyo Wanda zai wanke min fatata sosai ba,Musa ya karba da sauri ya fice,Minti biyar ya dawo da soso me shegen karfi ya bashi. Wanka ya sake Shiga Yana dirje jikinsa Yana rumtse Ido sabo da zafin soson,Haka ya Gama tas ya fito Yana goge jikinsa yace yawwa Iska tafi shigata Ina Nan Ashe Ina ta cutar kaina da ace da irin wannan nake wanka tun farko ai da nafi Haka haske da Zama Fresh. Lotion dinsa ya shafa me kamshi ya shiga gyara kitsonsa yace ya kamata nayi sabo wannan kwanansa biyar ya fara tsufa Amma Bari dai naje,sai da ya Gama feshe feshensa sannan ya Bude ma'ajiyar kayansa Yana binsu da kallo yace Suit Zan saka ko me?can ya hango shaddoji da yadika masu tsada da kyau Wanda Mummy ta kawo Masa lokacin da za a daura aurensa kala bakwai,Wata Shadda ya dakko sea Blue Tasha dinki me kyau Hannun dogo me links,Nan ya sa Boxers ya fara kici kicin saka wando Wai Bai iya ba,da kyar da wahala Yana uban Nishi ya saka cif cif shi dinki ya zanu,Singlet ya saka yanda Mummy ta koya Masa sannan ya saka Rigar Shaddar wacce ta Sha guga ga kamshi Shaddar nayi sabo da me tsada ce,calabarsa ya gyara ya shafe Kansa da man gashi me kamshi Nan take ya dauki sheki,Fuska ya kalla ya matsa baya Yana kallon kansa a mudubi ya hau taje Sajensa da gemusa,fuskar ya goge sosai ya gyara sai gashi ya fito fes da shi,Sarkar azufarsa wata sabuwa ya dakko ya saka,Yana cewa duk da hausawa basa so Amma tana min kyau sai na saka sabo da wannan shine wankan sugar sai da ya Gama ya fesa turaruka masu kamshi,Ya tsaya jikin mirror ya kame a wajen yayi mutuwar tsaye yace ya Ilahi Ashe Haka nake? Dan Allah kalli kyau a wajen Nan ai Dole ma na birge,ya sake kallon kansa yace ah.. ah kalli kyau Dan Allah,irin wannan saurayi ai sai an wanke Hannu daka taba,wani Dan lipgloss na maza ya dauka ya Dan goga a lips dinsa yace yawwa.....Kar Kuma na Zama Dan Daudu Mana ya Isa haka....tsayawa yayi yace to me zance Mata idan naje Kantin nasu? Tunani yayi yace na tuna ma Bari naje,Illar idan na ganta sai naji tsoronta Kuma Haka Zan daure,Fitowa yayi Yana Taku dai dai Yana wani Gadara,yace me kyau sai da takama Nan ya Shiga wata tafiya Yana takama Yana basarwa,Musa Baki ya Bude tunda yake a duniya Bai taba ganin me kyau irin Ogansa ba,Bai taba ganin wankan da yayi ya zuba Uban kyau Haka ba sai yau,Musa yace Oga gaskiya kayi kyau,Murmushi yayi yace Allah Musa? Musa yace wallahi Oga Kar fa kasa Mata su haukace,Dariya Ahmad yayi ta Jin dadi yace Musa yanzu kana ganin duk wacce ta ganni zan birge ta? Bafa soyayya nake nufi ba Kai Musa Ni kasan ba ruwana da soyayya,Musa ya kalli sama ya nuna sama da yatsa yace Na rantse Oga duk wacce ta ganka sai ta kwana tana tunaninka yau ita da bacci haihata haihata,Machine Ahmad ya hau Wanda Musa ya wanke Masa Shar,a hankali yake tukin sai binsa ake da kallo da gani an San Yafi karfin yawo a Machine ko Ina ya gifta sai an koka. Aamna kuwa yau wanka tayi ta shirya cikin doguwar rigarta peach color ta lefe ce tayi rolling da mayafi ta dauki hand bag da takalminta me Dan tudu Kalar adon rigar Golden tayi kyau ta dauki bokitin chin chin da takeyi da kanta tana siyarwa a shagon wannan da kundinta takeyi tana samu Yar riba,da kanta ta gyara kantin fes ta shirya komai sannan ta zauna tare da dakko Wayarta tana karanta novel,idan masu siyan Abu sunzo ta Basu ta koma karatunta. Tana zaune ta dukufa taji machine yayi parking a bakin wajen,kanta ta dago da sauri Jin wani kamshi na daban me Dadi,Ahmad ta gani Wani tafiya yayi da Imaninta ita kanta sai taga kamar yau ta taba ganinsa,zuciyarta ta hau Bugawa da karfi,Kallonsa takeyi ba kyafta Ido tare da Mikewa tsaye,Babu alamun fara a Fuskarsa Yana wani Isa,a cikin ransa Kuma wani kwarjini ta Masa yaji wani tsoronta da shakkarta,duk kwarin gwiwarsa sai ya neme shi ya rasa,jikinsa yayi sanyi a hankali ya taka zuwa gabanta ya tsareta da idanunsa,Itama shi take kallo,can ganin Shirun yayi yawa sai Tace am...me kake so zaka siya Ahmad? Yayi Shuru ya kasa magana,ta kalle shi tayi murmushi Tace wow kayi kyau Wannan shigar tayi maka kyau,Wani sanyi yaji a ransa dama Dan ita yayi Kuma ta yaba,a hankali yana Ina Ina yace shi...shigar...ta...tayi Miki?da sauri ta daga kai Tace sosai wace zata ce ma baka Yi kyau ba,Yaji wani Dadi ya jinjina Kai kawai,sharewa tayi Tace me zaka siya? Kasa magana yayi sai da kyar yace Uhm....uhmm.....Yana ta kallon shagon Yana so yaga me zai iya siya....gumi ya hada Nan take tsabar abinda yake ji a ransa da kwarjinin da ta Masa gashi Bai Iya yiwa mace magana ba tunda ya taso a rayuwarsa wannan ne na farko,Tace Kayi magana Mana me zaka siya? Yace Uhmm....ahhh....ehmmm.....can ya hango chin chin yace Chin chin tare da nunawa da yatsansa,murmushi tayi Tace na nawa? Yace na....naira dari.....murmushi ta saki ta bude ta zuba Masa Guda uku dari cif a farar Leda ta Mika Masa,karba yayi Yana ta kallonta yace Zan....Zan...Iya Zama a Nan naci? Tace me zai Hana shigo ciki,kujera fara ta jawo Masa a ciki ya zauna Suka jere taci gaba da karatun Novel dinta. Kallonta Kawai yake ta faman Yi idan yaga zata dago sai yayi sauri ya dauke Kansa,Daya gaji sai ya fara cin Chin Chin din,harga Allah baya son chin chin Amma Haka yake ta ci Yana kallonta,ita Kuma tana ji a jikinta Yana kallonta duk sai ta kasa sakewa da kunya,juyowa tayi karaf suka hada ido,Tace ya kake kallo na? Yace kallo? Kallo Kuma? Ni na kalle ki ai kece ma naga kina ta kallo na tun dazu ya fada Yana dauke Kai,Tace Ni nake kallonka din? Yayi Murmushi yace ae Mana,Kai ta girgiza taci gaba da karatunta,cikin Wayar ya leka yace me kike karantawa? Novel ta bashi amsa, ko kana karanta Novel? Yace No...me zanci da Harkar love ai Ni sai dai dambe, murmushi tayi Kawai. Yace me yasa Mata kuke son Love ne? Wannan duk Bata lokaci ne,Dariya tayi Tace Kai baka so ta juyo tana murmushi wani kyau ta Masa ya gigice zuciyarsa taci gaba da bugawa,kasa magana yayi ya rike Hannunta wani mugun shock taji ko Ina a jikinta yace Ring din ya Miki kyau,Tace na gode Hannunta ya dauka ya maida Mata saman cinyarta yace kina boye Hannun Nan Kar wani yaga ya Masa kyau da yawa ya yanke Miki shi ya tafi dashi gida,Dariya ta dinga Yi shi kuwa ita Kawai yake kallo,komai nata Dariya a ransa ya furta,Yana sani ya dinga cin Chin Chin din kadan kadan sai da ya Dade lokacin Azahar tayi sannan ya Mike yace Zan tafi Tace ka Gaida gida yace to Zan fada Masa,Dariya ta sake Yi ta rako shi har bakin machine dinsa ya hau ya tafi da mugun gudu,Tun kafin ya karasa gidansa ya tsaya a Hanya ya cire rigar Shaddar tasa sabo da zafi yake ji ta dame shi Bai Saba ba,a kafada ya sakale ta har zuwa gidan. Da murna ya shiga Yana sauka a machine ya zaro dubu biyu ya damkawa Musa yace je kaci pizza Musa yau Ranar murna ce,Musa yace Allah Oga? Allah kuwa cewar Ahmad ya sake zaro dubu biyu yace kudin lemo ne wannan,Musa ya daka tsalle Yana murna da Ihu har Ahmad ya tafi ya sake dawowa ya zaro dubu Daya yace ungo Musa ka sawa matarka Kati a waya ku kwana kula hirar ku ta Yan karya Kuma karka sake ka Bata duniyar mu Dan Bamu San Inda zamu shiga ba idan ka bata.,,Musa yace Allah Kai sai kayi,Ahmad ya daga hannaye sama yace nine nan yayi ciki Yana wata tafiya ta musamman. Yana shiga ya cire duka kayan jikinsa ya watsa su a inda yake Tara wanki,saitin zuciyarsa ya dafe tare da furta shu'uma har ta dawo dai dai,Wato har wani bugu kike Yi a hankali da kika ga bana gabanta ai shike Nan kin kyauta,zuciya kin kyauta hakan ya Miki kyau kin Mai Dani wani Wawa Akan yarinya karama Ina ta zubar da aji na ai shike Nan Zaki sani ne. Washe gari ma wani sabon wankan yayi tare da saka wani yadi Milk color sharara da shi ya Masa kyau matuka an kashe shi da dinki na haduwa,wani takalmin ya zabo me tsada,waje ya fito ya mikawa Musa takalman yace sauri ka kaiwa Shoe maker ya wanke min yanzu Ina jira,Dan Allah Musa kayi sauri ka kawo min su Suna kyalli,Musa ya fita da gudu ya tafi Bai Dade ba ya dawo,Ahmad ya shirya tsaf kyau ba a magana yace yau barkono da citta Zan tayata siyarwa,yau ma Aamna tana zaune ta Gama sallamar wani ya siyo Singlet sai gashi ya Parker machine,Aamna tayi murmushi Tace Sannu da zuwa,Irin Dan gayun Nan harda wani basarwa Direct ya shige ciki ya zubawa Kansa chin chin yace na Naira Dari biyu yau Zan siya Aamna Tace to,Zama yayi Nan ma Yana kallonta duk kunya ta isheta,Wani magidanci ne yazo yasan Ahmad da irin iya shegensu mamaki ya kamashi ganinsa a Haka da wannan shiga ta Kaya,Bai taba ganinsa da shigar hausawa ba,Kuma Yana Zaune a shago kamarsa me kudi,Shuru yayi yace a bani barkono da citta,Aamna ta Mike zata zuba da sauri Ahmad yace No zauna Bari na tayaki Mana Haba,Tace Kai din? Bai kulata ba yace na nawa? Yace na Hamsim,Aamna tace ga kullin Hamsim can ka saka,ya dauki bakar Leda ya saka Masa ,Citta Kuma Tace gongoni Daya zaka zuba,ya fito ya auna gwangwani Daya ya zuba,mutumin yace babu gyara? Ahmad yace a gindinku kuke so mu kare ne Ina laifi ma duk arahar Nan Baku gani ba,Tsaki Yaja ya dauki citta Daya ya jefa masa a Leda yace gashi Nan anyi gyara,Mutumin ya karba ya tafi shi Kuma ya dawo ya zauna a ciki,Aamna tana ta mamakinsa. Wata Budurwa ce tazo Tace Aamna nazo siyayyar,Aamna Tace to shugo,Budurwar tayi layin bra da panties ai Ahmad Yana ganin Haka sai ya juya baya tare da rufe Idonsa ruf har sai da matar Nan ta Gama zaba ta biya kudin ta tafi sannan ya Bude Idonsa,Dariya ya bawa Aamna Yana jinta tana ta dariya,yau ya Dade sai Yamma lis ya koma gida,sai mamakin Kansa yakeyi Wai Kamar shi shine zai siyar da citta,Yana kwance a palonsa yace gaskiya na Gama fadowa nayi asara wallahi,Kansa ya dungure yace kayi asara kai Kam Ahmad. Wasa Wasa kullum Ahmad sai yaje ya Taya Aamna siyar da Abu har wurin sati Daya,gaba Daya su Mashkoor sun daina ganinsa,idan sun Masa waya ma zasu zo gidansa sai yace Kar suzo baya gida ya tafi Unguwa,yafi so ya zauna shi kadai yayi ta tunanin Aamna Yana Jin dadi,Kwaya da giyar da yake Sha duk ya rage ba sosai ba sabo da tunanin Aamna. Yau kin zuwa yayi gaba Daya Bata ganshi ba har duba Hanya takeyi ko zata hango shi Amma Shuru duk ta kasa sukuni ta shiga wani Hali,gashi Bata da number dinsa Kuma baza ta iya cewa ya Bata ba. Sai washe gari yau cikin wata maroon suit ya fito kamar a jikinsa aka dinka yayi kyau matuka 3pm yazo wajen,Aamna ta taso da sauri tana murna a ranta a fili Tace me ya hanaka zuwa jiya? Ya rasa me zaice zuciyarsa tsoro yake ji....yace...ahmm...karya yayi yace kaina ke ciwo jiya,Tace Eyya Sannu ya jikin? Da sauki ya furta tare da tsayawa a gabanta Yana so ya fada Mata me yake ji a ransa Amma ya kasa....yace dama Ina so muyi wata magana ne,akwai abinda nake so na fada Miki,Aamna tace Ina jinka tana ta faman kallonsa,kasa fada yayi ta Masa kwarjini sai ya waske yace kina cin kifi tarwada? Dariya ta kamata Tace sosai ma ai Ina sonsa ya,girgiza Kai yayi Murmushi Wanda ya tafi da Imanin Aamna,yace to gobe Zan kawo Miki da yawa ko yau kike son ci? Aamna Tace goben ma yayi,Yana so ya fada Mata shifa zuciyarsa ta kasa sukuni Amma ya kasa sai yace Zaki Zama kawa ta?Aamna ta kalle shi tace me zai hana,murmushi yayi yace to daga yau mun Zama kawaye ko? Tana Dariya ta Mika Masa Hannu sukayi musabiha Tace na Zama kawarka kaima ka Zama aboki na,yace ae dama Ina so na dinga shawarwari Amma Banda kawa,Aamna Tace Ina abokanka fa?Tsaki Yaja kadan yace ai Bama wani haduwa yanzu sosai,taji Dadi a ranta Tace to shugo ka zauna,no tafiya zanyi Ina da wajen zuwa yau,Aamna Bata so hakan ba Amma Tace to shike Nan sai goben,ya hau machine yayi tafiyarsa gidan Mashkoor. Yana zuwa ya samu Mashkoor shi kadai, Mashkoor yace Kai me Zan gani yau Kaine da wannan shigar lafiya king? Kafadarsa Ahmad ya buga yace ba lafiya ba yanzu ma taimakonka nazo Nema,ku kawo min agajin gaggawa, ka tashi mu tafi gidana akwai magana,Mashkoor yace to,Giyar da Mashkoor yake kurba ita Ahmad ya tiltila a cup ya Sha ya sake Sha yace muje,a machine suka tafi gidan Ahmad. Aamna tana so ta fada Masa anjima da yamma zata tafi Sokoto ganin Dangin Babanta Amma Bai zauna ba bare ta fada Masa Amma sunyi waya da Mummy ta San da tafiyar. Shi kuwa Mashkoor Yana palon Ahmad suna zaune Ahmad yace kasan Kai abokina na ne Zan fada maka ne Kawai sabo da yanda muke da Kai,Kai kadai Zan fadawa halin da nake ciki,Mashkoor da muryar Yan kwayarsa yace Ina jinka King,Ahmad ya kwashe kaf abinda yake ji a zuciyarsa game da Aamna ya fadawa Mashkoor,Mashkoor tsoro ya kamashi Yaja da baya Yana tangal tangal a zaune yace Sarkin namu Guda ah'ah,Ahmad cikin rada yace Ina fada maka idan na ganta zuciyata sai naji tana wani kida tana rawa tana wani foli..fafo..lifo...fil...fil....dardariya Mashkoor yake Kamar me,yace ah'ah duk Kai kadai? Ahmad yace Ina fada maka Dan uwarka Yana dukan kafadar Mashkoor kana ganin Wasa ne bafa Wasa nake ba kana wani Yi min Dariya Dan Iska Kawai wallahi zaka bar gidan Nan, Mashkoor yace na daina Ina jinka,Ahmad yace Ina fada maka ba sai naji Ina tsoronta ba,Ah'ah Mashkoor ya furta da karfi yace wannan Yarinyar da ko Nonon kirki babu? Duka Ahmad dirka Masa a baya yace be careful matata ce ba Budurwa ba, Mashkoor yace dalla ba so bane sha'awarta kakeyi Kawai kaje ka dakko ta ka lallabata kaci abinka ka barta,Wani dukan Ahmad ya kaiwa Mashkoor yace Kai dalla Ni ba wannan nake so ba,baka ganewa Ni Kawai nafi so mu zauna tare da ita idan Dan wannan ne zamu iya shekara Nawa da ita sai Sanda take so zanyi wannan fa ba Maganar Wasa bane,Mashkoor yace cab abin Babba ne asiri tayi maka,Haushinka taji daka koreta ta maka asiri. Ahmad yayi Shuru,Mashkoor yace Zan taimaka maka akwai wani malamin Baban mu zamuje da Kai Nan take zaiyi maka Rukiyya a cire maka tunaninta ka dawo normal asirin data maka ya karye,Ahmad sai ya tuno layoyin Daya taba gani a Kan Aamna,yace Mashkoor kaima kayi magana tashi mu tafi wajen malamin Nan Yarinyar Nan Yar bori ce muje a gwada, Mashkoor yace yawwa kasan yanzu duniya ta canja Wai Yan Mata Dan masifa da bin malamai suna shirka suna tsafi akan maza,Wai mace taje tayi shirka Dan wani ya aure ta ko taci kudin wani,wata ta mallake Miji etc,kawaye sai su cika Mota suyi Kauye Wai an tafi wajen Malam akan wani ya aure su ko taci kudi,ko ayiwa kishiya da yaranta,shi yasa aure yanzu baya Zama Ana ta Yi Ana Sako Mata barkatai,duk macen data auri Namiji da asiri ta sani wallahi idan ya karye sai saki,yanzu shirka Kawai akeyi an ma daina cewa malamai sai bokan Kan dutse,mutane suna ta maida kansu arna Basu Sani ba. Tafiya sukayi me uban nisa zuwa wani Dan Kauye,Wani dattijo kazami Ahmad ya gani,Mashkoor bayan sun gaisa ya Gabatar da Ahmad da abinda ya samu Ahmad,tsohon yace ku bada dubu biyar kafin alkalami,Ahmad ya zaro ya bawa Malam,Malam yace saura kudin Aiki dubu goma,Ahmad yace Aiki baiyi ba za a baka kudi? Dattijon yace Kai ka cika son kudin tsiya ka bada kudi a rabaka da masifa,ciwon so ai masifa ne,Ahmad yace Nifa ba soyayya nakeyi ba,nace maka tunaninta Kawai nakeyi,Ni nayi love Allah kiyaye, gashi nan yarinyar ta Gama kashe maka zuciya cewar malam,Ahmad ya bada dubu goma shi Sam da gani yasan karya ne wannan cin kudi Kawai zaiyi. Saman Tabarma yasa Ahmad ya zauna,Bayan ya zauna ya Bude Qur'ani ya dinga karatu a Kan Ahmad Yana zaga shi sai da ya Dade sannan yace an Gama Alhmdllh Aiki yayi kyau kuje gida daga yau ka Gama da shafinta, Mashkoor Yana murna ya dinga godiya,Ahmad Baki ya tabe shi baiji canji a ransa ba,Sai dare Suka koma gida,suna dawowa wanka sukayi Suka ci abincin da Suka siyo a hanya,Ahmad ya kalli Mashkoor yace Mashkoor Nifa so nake yanzu Naga Yarinyar Nan,Da mamaki Mashkoor yace ah'ah Kuma dai? Yanzu duk aikin da Malam yayi har kanajin ta a ranka? Ahmad yace tashi ka rakani gidansu Zan haura katanga idan ban ganta bazan iya bacci ba yau dole sai naji muryarta ko na ganta,Mashkoor yace dare fa yayi ka duba lokaci 11pm fa,idan zaka rakani to idan baza kaje zanje Ni Daya,Dan kaga Ina fada maka sirrina zaka wulakanta Ni,Mashkoor yace muje Amma idan munje me zaka ce da su a wannan Daren me zamu ce? Ahmad yace muje Kawai,machine suka hau a daren Suka tafi Kamar mayu. A bakin gate Suka tsaya tare da kwankwasa gidan,Baba ne ya fito Jin bugu yaki karewa Yana budewa tsoro ya kamashi ganin su Ahmad ya tabbatar giya suka Sha shi yasa Suka zo da wannan Daren yasan basa hayyacinsu,lafiya? Baba ya tambaya,soshe soshe Suka Kama Yi, Mashkoor yafi Baki shi yace dama...dama..munzo duba Aamna ne sabo da munji labarin Bata da lafiya,Baba yace sabo da kwaya ta gaya muku karya sai kuzo min gida a wannan daren? Kun firgita mu Ni da matata,to Aamna Bata Nan ta tafi Sokoto tun yamma dazu tace ta sauka tana can Dangin Babanta sai Nan da kwana hudu zata dawo,Kirjin Ahmad ya buga Kamar zaiyi kuka yau bazai iya bacci ba Matukar Bai ji muryarta ba,Baba zai juya yace sai da safe da Sauri Ahmad ya kalli Mashkoor ya Masa rada kace ya Bamu number dinta,Da sauri Mashkoor yace Dan Allah Dan Bamu number dinta Muna so muyi Mata ya jiki,Baba yace Wai uban waye yace muku Bata da lafiya fatan ba takura Mata zakuyi ba,da sauri Ahmad yace a'a Kawai Sannu zamuyi Mata,Baba ya Harare su sabo da Bai so Haka ba Amma sabo da kwarjinin Ahmad yace bani waya na sa maka,da sauri Mashkoor ya Mika wayarsa Baba ya sa Masa number a ciki Yace kuje garam ya rufe gidan,Ahmad ko a jikinsa sai murna Suka hau Machine suka koma gidan Ahmad. A Palo Ahmad yace Kira ta awaryarka muji, Mashkoor ya kalle shi da mamaki yace da wannan tsohon Daren? Ahmad yace Dan Allah ka kirata naji muryarta Ni bazan iya Mata magana ba zuciyata bugawa takeyi,kayi magana da ita kasa a handsfree idan naji muryarta shike Nan Zan samu nayi bacci yau,Amma Matukar banji muryarta ba yau bani ba zaman lafiya, Mashkoor yace abin har ya Kai Haka mun shiga uku?Tsaki Ahmad ya ja, lokacin Aamna ta kwanta ta fara bacci taji Wayarta tana ta Kara,dubawa tayi taga bakuwar Number AsmaBaffa 10/26/21, 8:53 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 46-50 FREE PAGE DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE MASU SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne RUKEY MUAZ LEEMAT ~- MINERH KHADIJA DANDAWAKI HUMAIRA MUHAMMAD AMINA ADAMU USMAN Tsaki taja tace waye wannan da wannan daren? Kin dagawa tayi har ta katse, Mashkoor ya kalli Ahmad yace King Bata daga ba a kyaleta tayi bacci,da masifa yace ka Kara kiranta Mana,to tana bukatar tayi bacci fa cewar Mashkoor,Bata bacci da wuri na sani ka sake Kira Wai me yasa kake min Haka Zan sa ma poison a lemo ka Sha ka mutu ka kirata again, Mashkoor yace Nifa baza ka Jani cikin haukarka ba,Kawai ka shigar Ni ciki mun haukace yau gaba Daya bansha ko kwalaba Daya ba mun Kare akan kwaila,wata Harara Ahmad ya aika Masa Nan take Mashkoor ya sake Kiranta lokacin wata Budurwa Yar Uwar Aamna Minal ta kwanta a gefen Aamna Tace Wai waye yake ta Kira ne Haka? Aamna Tace ban sani ba,Bari na daga naji cewar minal ta dauki Wayar tare da dagawa, Mashkoor yace an daga....an daga...Ahmad yace ehem Yi magana Mana. Mashkoor yace hello Aunty Balaraba Mashkoor ne? Minal tace ba ita bace Yar uwarta ce Minal ce,Aamna tana ji ance Mashkoor ta Mike zaune,Mashkoor yace ehem Dan Allah Bata kusa me Wayar? Minal Tace gata ma Bari na Bata, Wayar Aamna ta karba,Lokacin Ahmad ya gyara Zama tare da furta ehem a hankali, Mashkoor yace Aunty Balaraba Barka da dare,yawwa Mashkoor ya gida? Lfy Alhmdllh,dama...dama...Ni da King munje gidanku ance bakya Nan kinyi tafiya,Aamna Tace Yana Ina King din,Tsoro ya Kama Ahmad shi Taya zai iya magana me zai ce Mata, Mashkoor yace Bari na Baki shi ya mikowa Ahmad Wayar. Yana karba sai da yayi minti Daya Aamna tana ta faman hello hello sannan yace hello cikin Muryarsa da ya saita me Dadi ta nutsuwa....uhm...ahm...ahhh....munje gidanku dazu ance bakya Nan? Aamna Tace eyya sorry Friend Ina ta so na fada maka Bamu hadu ba Amma jibi Zan dawo Inshaallah,Ahmad yace okay...Allah ya kaimu, Mashkoor da rada yake cewa matarka ce fa ka daina wannan abin taya zaka barta tana tafiya inda taga dama Haka? Ahmad Bai kulashi ba yace Friend sai da safe Bai San me zai ce ba,Tace okay bye ta kashe Wayarta,Ahmad yace Nifa ba Maganar Mata nake maka ba ya za ayi Naga na birgeta shine magana Kawai,Dariya Mashkoor ya dinga yi yanda Ahmad duk yake ta murna akan yaji muryar Aamna,yace to yanzu Zan iya bacci,Mashkoor yace ka haukace Nima ka sani na Zama mahaukaci,Bari naje nayi bacci,Ahmad yace ungo wannan banzar akwakwar Wayar taka tunda nadauki number dinta,Ae ai dole ka zagi Wayar tunda ta Gama biya maka bukatarka. Washe gari da sassafe Ahmad ya farka ya dawo Palo inda Mashkoor yake bacci ya dinga dukan Mashkoor a gadon baya,da kyar Mashkoor ya farka Yana masifa Wai Dan Allah mene Haka jiya ka hanani nayi bacci yanzu ma Haka Mene ne? Baka tashi da wuri mene yanzu abin tashi again,Ahmad yace Yarinyar Nan nake so ka kirata ku gaisa sai ka sa min Wayar a Handsfree naji muryarta,Tsaki Mashkoor Yaja da muryar Yan kwaya yace wai a'ahhh....wannan wanne bala'i ne Haka? Okay kace min kawarka ce Kai ba sonta kakeyi ba wa yace maka Ana Kiran kawa Haka a waya,so kake Yarinyar Nan ta tsaneka sabo da yawan takura Haba su Mata basa son takura,kana nutsuwa fa King,Shuru Ahmad yayi yace okay Bari to bazan kirata ba sai ta neme ni Zan daure,Ehemmmm...Abeg jeka kitchen ka Mana girki King kasan ka iya girki cewar Mashkoor. Ba karamin dauriya Ahmad yayi ba yaki Neman Aamna a waya,Aamna taga Shuru Bai nemeta ba ranar da ta dawo Kaduna yau Ahmad Yana kitchen shi da Mashkoor suna magana Yana girki sai ga Kiran Aamna ya shigo wayarsa,Wata nutsuwa Ahmad yayi tare da cewa yeee...ta Kira ni...daga Wayar yayi yace Hello.....Kawata,Aamna Dariya takeyi Wai Dan rainin hankali ma ba matarsa bace kawarsa ce ma,a Wayar Tace dama fada maka zanyi na dawo dazu,Wata Uwar Zabura Ahmad yayi sai da Mashkoor ya firgita,Ahmad yace Kin dawo lafiya Kamar Yana gabanta har wani zufa yake Yi,Tace lfy Alhmdllh,yace Zan zo gobe,okay Aamna ta furta ta so ace yanzu zai zo Amma Wai wani gobe, Wayar ya kashe ya saki Dan Ihu yace she done come back Yana dukan kafadar Mashkoor, Mashkoor kallon mamaki yake Masa Kawai ganin king dinsu ya haukace. Wanka sukayi Mashkoor ya dauke shi Suka tafi Shopping Wai Ahmad shaddoji zai siyo da yadika masu tsada za Masa dinki sabo da ya birge Aamna. Ko da Suka shiga inda ake siyar da shaddoji da yadikan maza Ahmad ya kalli me kayan ya zaro Masa Ido yace Guy Kalar birgewa muke bukata masu tsada,Me Shadda yace gasu Nan ku zaba,Ahmad ya dinga zaba Mashkoor ya koma gefe Yana ta kallon ikon Allah har ya Gama sannan Suka wuce wurin tela,Ahmad yace Kai tela fa Wanda yasan me yakeyi yawwa idan kasan tela bana kirki bane karka kaini, Mashkoor Yana ta Dariya yace Wai Ni Kam ko Lilamin Masallaci za'a nada ka ne? Ko kula Mashkoor Ahmad baiyi ba,wani Shagon dinki Suka shiga,Ahmad yace Bari na gwada basirarsa Kai tela nawa zaka min Dinki na karshen tsada? Tela yace dubu bakwai, dubu biyar dubu goma sama da Haka,Ahmad yace wannan dinkin da gani bana arziki bane baka iya komai ba baka San me kakeyi ba Malam ja can dalla, mu bar Nan, Mashkoor ya sake daukansa Suka tafi Wani wajen na masu tsadar dinki Amma da kyau,Ahmad Yana ji an zuga Masa tsada yace yes.. .yanzu nasan Kai telan kirki ne Nan ya bashi kayan,yace auna Ni ko Ina dai dai Ni, wallahi ka min hauka sai na sa an kone shagon dinkinka da kayan ciki sabo da Haka don't Mess up,tela yace zaka ga Aiki ai bana Wasa,sai da suka Gama komai Suka je ya siyo takalma Designers da agoguna etc. Sai dare Suka Gama sannan Mashkoor yace Zan tafi gida,da masifa Ahmad yace akan me ai wallahi ba inda zaka je Sai an Gama tsare tsare da Kai, Mashkoor yace Nifa na gaji Haba ka rike Ni na kwana na yini Yar giyar ma ban Sha ba tun jiya Ni bazan iya ba, baza ka saka Ni a wannan haukar ba,Fuska Ahmad ya Bata tare da furta Kai meke damunka ina magana kana magana are you mad? Shuru Mashkoor yayi yace to kayi Hakuri na zauna Amma a kawo min ruwa da kayan aiki,Nan Ahmad ya koma bedroom dinsa ya kwaso kayan shaye shaye ya ajiye musu Suka dinga Kora abinsu,Ahmad Yana murmushi yace yawwa na tuno nasan dole tana yin Facebook babu Wanda baya Facebook a duniya,Nan take ya fara latsa wayarsa Yana duba Facebook Yana Searching sai dai Bai San sunan Baban Aamna ba,Amma sai ya gwada Aamna Hussain,Nan take sunan Aamna ya bayyana da hotonta,Yana murmushi yace Yes....see fine Beb,see Beb....naaa..wow...see her lips...oh.....My God...a'a...kaga kyau Haka,...fuskar Wayar ya shiga nunawa da yatsa Yana shafa gemunsa Yana murmushi yace abinda kike min baya dacewa,bakya kyauta min Sam,ki daina...ki daina Tam.....Mashkoor ya saki Baki Yana kallon ikon Allah, Pictures dinta ya shiga dubawa kala kala can ya hango Aamna da wani saurayinta a pic Wato Affan,Glass din wayarsa ya shiga Rankwashi da karfi a saitin Affan Yana ka...ga...shege...Dan... Iska,me yasa zaka tsaya kusa da ita....mugu....Tsaki Yaja ya fita daga Facebook din gaba daya Yana Fushi yace Taya zai tsaya a kusa da ita aikin banza,Cikin Maye Mashkoor yace Wai...Wai...ba kace kawarka bace?Yeah Ahmad ya furta,yace to Mene na damuwa Haka? Maganar gaskiya King ka fa haukace. Ahmad Yana Zaune yayi Shuru Mashkoor yace ya akayi ne? Yarinyar Nan nake so na gani yau da Daren Nan Amma bana son ta ganni kuma bana so ta San na ganta Kawai na ganta a boye ba tare da ta ganni ba,kaga yanzu 10pm muje ka kaini sai na tsallaka gidan, yau ko bacci takeyi har dakinta sai na ganta,Mashkoor tsoron Ahmad ya shige shi Kamar zaiyi kuka yace Wai Mene yake damunka kafa haukace King,Kaga Idan zaka kaini Malam ka kaini Zan zuba ma guba a abinci ka mutu Tam, Mashkoor yayi Dariya irin ta yan kwaya yace muje,a daren Suka hau machine suka tafi,a nesa da gidan Mashkoor ya sauke Ahmad,Ahmad yace karka tafi Ina ganinta Zan fito mu wuce,ta Kofar gidan Ahmad yabi ganin a bude Basu rufe ba,kamar barawo Haka yake Sanda yace bana so ta San Zan kalle ta,da sauri yabi ta bayan gidan wajen Flowers,Baba ne ya fito Yana masifa Dan Iskanci sai a bar gida a bude tun yaushe nacewa shedaniyar Yarinyar Nan ta rufe gidan Nan Amma dake Aamna ba Yar Albarka bace ta bar gidan Abude,Ahmad Yana ji Baba ya zagi Aamna sai ya kasa jurewa Yana bayan ginin gidan yace karya ne kaina Mara Albarka.....tsorata Baba yayi ya rasa a Ina yaji an ramawa Aamna ya shiga waige waige ko zai ga mutum baiga kowa ba,Tsoro ya kamashi ko aljanun Aamna ne suke tare Mata fada,da sauri ya rufe gidan ya kulle ko Ina ya koma ciki da saurin gaske. Ahmad ta Kofar kitchen yabi Dake kitchen akwai kofa ta waje ta ciki sai yabi ta Nan ya shiga Palo Yana shiga Baba ya shigo da sauri ya fada bayan kujera ya buya,Baba Yana masifa ya kulle Palo ma ya sa key, yace aikin banza kitchen dinma a Bude aka barshi Bari na rufe,kafin ya karaso Ahmad da rarrafe ya koma Bayan Daya kujerar,Baba ya kulle kitchen Yana cewa beraye sun fara addabata a Palo naji Kamar sun shiga cikin kujeru Bari gobe da wuri Zan samo mage tayi maganinsu. Ahmad Yana ji a hankali yanda Baba bazai ji ba yace Baba nine ba bera ba,Baba dai dakin matarsa ya shige,Sai ga Aamna ta fito sanye da wata guntuwar rigar bacci fara silk me siririn Hannu,Ahmad ya baza Ido Yana kallo Nan ma a hankali yanda baza taji ba yace Kai bakya kyautawa Baba fa idan Yana ganin irin wannan abin sai Shedan ya shiga zuciyarsa,wallahi sai ya Ayyana wani Abu gaskiya ki gyara,ba kishi nake ba Amma ki gyara,Aamna Bata San Yana yi ba taje kitchen ta fara dafa Indomie,cikin karfin halin Ahmad ya fito fili ya tsaya a Bayanta tare da Harde hannayensa a kirji Yana Shan kallo,a hankali ya Mika hannayensa biyu tare da wara su yace in Dan tallafooooo......hips Ido ya lumshe,Aamna Bata sani ba harda wakarta tana me so na....me so na....Ahmad Yana amsawa a hankali Yana Nuna Kansa Yana gani...gani....Aamna ji tayi kamar ana magana a Bayanta Matsawa tayi da Niyyar juyowa tuni Ahmad ya koma Bayan jikin bango daga Palo ya labe taga ba kowa,ci gaba tayi da aikinta ya dawo shima Yana ta kallonta har ta Gama ta dauka a plate sai ta tsaya dakko ruwa a fridge ta ebo pure water biyu tare da furta Allah sarki a gidan Mijina kuwa Ruwan Roba nake sha,kafin ta Gama gyara kitchen ta fito Ahmad yayi sauri ya shige Bedroom dinta Wanda yaga ta fito daga ciki. Bayan labule ya buya abinsa Aamna ta shigo tare da dannawa kofarta key tana Waka Tace yawwa Bari na kwashi harka ta zauna a gefen bed tana ci tana latsa waya tana Dariya,shiko Ahmad ta bayan labule yace kalli murmushi Malam Kamar wata flower Haba ai wallahi Babu Wanda ya Isa ya ja da Allah,wata baiwar Allah duk duniya kowa da kamarsa daban da Computer ce ke kera halitta ai da tuni tayi photocopy na Aamna ta yafi mutum dubu,Amma Kuwa Allah kowa hancinsa daban,bakinsa daban,Dariyarsa daban,kukansa daban,girarsa daban,kafa,Hannu,Kai,komai daban Allah kenan. Aamna Bata San da mutum ba Tace zafi Bari na sake wanka ba tunanin komai ta tube rigarta ta jefar,Ahmad ya zaro Ido yace tab gaskiya ban kyauta ba Zan kalle mata tsaraici ba Izni,Idonsa Daya ya leko ta labule yace tab Ni idan kika dawo gida na karya ne ki Haifi wani yaro,Ni da yarona zamu Yi takara kenan akan Abu daya Ni da shi ai karya ne,Yarana kuyi Hakuri Uwarku ta ja muku baza kuzo duniya ba akan wannan yaki zanyi da ku,Juyawa tayi yace lahaula fiii......see Ass uhmm....Ganin ta juya baya sai ya juro hannunsa Daya ta labile yace na taba suuu......da sauri ya janye hannunsa Kamar walkiya ganin zata juyo ta kamashi,Towel ta dauka ta shige toilet,sai da yaji karar ruwa sannan ya fito daga inda ya boye,Indomie ta rage yace Bari naci ragowar ta ko na samu karama da tabarakinta ya dauke ya cinye,ruwan data rage ya shanye tas harda tsotse bakin Ledar pure water Wai ya tsotse bakin Aamna,kafin ta fito ta Bude kofa Ahmad ya dauki Wayarta ya turata bakin kofa sannan ya Bude Kofar ya fice da sauri,ta kitchen yabi ya fita tare da haure katanga,ko Ina ya bar kofofin a bude sabo da dabara ya hada. Aamna da sauri ta fito daga toilet Jin karar key an Bude Mata kofa,mamaki ya kamata taga Wayarta a bakin kofa ita data barta a saman bed,abincinta data rage taga an cinye,da sauri ta fito tana duba gidan sai taga an Bude Kofar kitchen ko Ina,ga handkerchief an jefar,Ihu Aamna ta saki tana Baba barayi,barayin waya Baba,Baba ya fito da Aamna ta nuna musu kitchen,Baba yace abinda nake gudu kenan munafuka ai ke kika jawo kece ba Kya rufe gidan,Baba yace Bari na duba Naga me aka sace min,startime wacce ake Kamo tashar kallo Baba yaga wayam an sace,Hannu ya Dora a Kai ya kurma Ihu yace dubu goma Sha biyar dita,Radio dinsa da yake Jin labarai itama a Palo ya barta yaga an sace ta itama,Baba Takaici yace me yasa Dan Ubanki ba a sace wayarki ba Aamna? Aamna Tace ai Nima an cinye min ragowar abinci na da ruwa,wayata ma Allah ne ya kiyaye barayin suna bude kofa na fito daga Bayi da gudu shi yasa suka jefar da wayata garin gudu Basu sace ba,Baba yace ai tsafi sukeyi da tsafi suke Shiga gidan mutum ko ka kulle da key a banza,Mama Tace matsiyata Allah ya takaita Suka koma tare da kulle ko Ina. Mashkoor Yana Kan machine Yana ta jiran Ahmad har 12am ya fara gyangyadi ma Sai ga Ahmad ya fito ta baya da sauri Hannunsa dauke da Radion Baba da Startime din su Aamna wayo ya hada sabo da a tabbatar barayi ne. Mashkoor ya gano plan din abokinsa ya dinga sheka dariya yace sata har gidan surukai wannan wanne irin Dan Iskan suruki ne? Dariya Ahmad yayi yace yau nayi farin gani,tunda nake a duniya sai yau na kalli Abu mafi kyau a duniya,Duk kasar wajen da kaje? Cewar Mashkoor,Ahmad yace ai wannan duk ba kallo bane,Basu da komai me kyau,ai Country me kyau Yana jikin Aamna,Kansa ya dafe yace kaina Juyawa yake kaini gida Kar na Fadi na sume,Rawar sanyi nake ji da mun sani mun dakko Jibson ko banza ya dafe Ni juwa nake ji, Mashkoor yace me ka gani ne Haka? Cikin muryarsu ta Yan kwaya Yace New worldddd....my man,jiri nake ji....yau idona ya samu Karin karfi gani tarrr nake ganin komai,idona ya washe yau,Yau ko me Shan Carrot juice Bai Kai idona kwari da washewa ba,Fess nake gani,Mashkoor Yana ta Dariya yace barawon Suruki,yace ai dole idan ba Haka ba sai su fara Bincike suna sa Ido Watarana su kamani. Baba da safe cikin Fushi ya tashi an sace Masa startime da Radio yace wallahi kullum nayi Sallah sai na buga Tabbatyada duk Wanda yayi min satar Nan Allah ya bayyana shi,Dubu goma da motsi ai ba Nan take ba Kuma duk sakakinku ne ya nuna Mama yace Mene amfanin mace wacce Bata tattala kayan mijinta Bata kula da dukiyar mijinta komai naki Baki San adani da tattali ba ke Kam Baki Dace da matar aure ba da tsohuwar bazawara kika Yi Kama wacce mijinta ya Dade da rasuwa,Mama ta bude Baki Tace Wai ni na sace maka ne wannan wacce masifa ce akan Dan abinda Bai Kai ya kawo ba,Idan kinji haushi yau ki biyani cewar Baba,Mama Tace Zan biya ka Amma kaje Nima Allah ya isa,Baba yace ae ki biya naji Allah ya Isan. A ranar Mama ta aika aka siyo Mata sabuwar Radio da Startime,Baba yace kin taimakawa kanki. Aamna cikin wata doguwar rigar lace ta shirya sea green and milk ,takalminta,Mayafi da jaka duk milk tayiwa Mama sallama Mama Tace Yau ki dawo karfe biyu sabo da Zaki Mana wanki,to ta furta tare da ficewa zuwa Kantin,tunda taje take jiran Ahmad Amma Bai zo ba har 2pm lokacin ta rufe shagon ta wuce gida,20mnt da tafiyarta lokacin Ahmad ya Sha wanka cikin wata sabuwar Jallabiya me tsada ruwan zuma Kamar yanda ya Saba ta tsangale Masa,Takalminsa ma ruwan zuma yayi kyau tare da daura agogonsa me tsada,Sabuwar kitson calabarsa ya gyara tare da Kama ta yasa Black band ya daure ta a tsakiyar kansa,wani uban kyau ya sake tsulawa, Mashkoor Yana ta zugashi yace ai dole ma ta rude,Kaga Handsome,shi Kuma a Gaban mirror ya tsaya Yana kallon kansa sai da ya Gama yace yau ba sauki bazan kalleta ba karta ce Wani sonta nakeyi, Mashkoor yace Good ka ja ajinka ba yanzu ba kwaila Kar ta Raina mu,da Masifa Ahmad ya furta wace Kwailar dan Uwarka? Ya bi Mashkoor zai ci ubansa Mashkoor ya gudu daga room din Yana dariya. Kwafa ya ja ya fito tare da hayewa machine dinsa ya fita sai shagon Aamna Amma sai ya ganshi a rufe,Wanda ke siyar da takalma a kusa ya tambaya yace Ina me shagon Nan? Yace yanzu ta rufe tafi gida naji tana cewa zata Yi Aiki ne,Okay Kawai Ahmad ya Furta ya hau machine dinsa zuwa gidan su Aamna,har cikin gidan ya shigo da Machine dinsa,Aamna ya hango a jikin tap da tarin uban wanki a gabanta na Mama Dana Baba,Sanye take da Vest fara da Skert din atamfa wata maroon,gashinta har gadon baya Bata daura dankwali ba tana ta fama,Mama zaune take tana hutawa Kawai abinta tana ganin Ahmad ta Bata Fuska,ya manta ko Sallama baiyi ba ya karaso da Izzarsa yace Mama Barka da Rana,Baki Mama ta tabe Bata amsa ba Tace sai ka koyi Sallama sai na amsa maka gaisuwar taka,Baki ya tabe tare da yin Sallama ciki ciki ya kumbura Baki Kamar me shagwaba,Mama ta amsa tana hararsa sabo da bakin ciki,Juyowa Aamna tayi tana ta Kallonsa yanda yayi kyau,Murmushi tayi Tace Kawana Sannu da zuwa,Ahmad yace kawa ya Hanya,Lokacin Baba ya fito yace yau me Zan gani bayan auren da kuke da shi kun sake komawa sababbin kawaye Kuma? Mama Tace tayani jin sabon salon bariki, Ahmad Bai kulasu ba tunda wacce yazo wajenta tana Nan Ina ruwansa. Mikewa tayi tsaye suna facing juna juciyarsa sai bugawa takeyi duk sai ya nemi kwarin gwiwarsa ya rasa,a hankali yace wanki kike Yi me uban yawa duk ke kadai,Aamna Tace ae ya na Iya,Kallonta yayi da azababbun Idonsa masu narkar Mata da zuciya yace Bari na tayaki,Aamna tayi Dariya Tace Kaine ka Iya wani wanki kalle ka fa ko Sabulu ai baka iya wankewa ba,komai fa Yi maka akeyi,Nifa super Man ne Ina da karfi da kike gani na har noma Zan iya zuwa gona nayi,Zan Iya nome Miki gonar data fi girman gidana lokaci Daya,karfa ka Sha wahala,ya nuna Kansa yace Wasa kike Dani,Aamna ta Mika Masa kujera ya kalli kujerar yace ba Aiki kike so ba sai kace wata mace na zauna a kujera Allah kiyaye a tsaye Zan tayaki kawo bucket ki gani,Baba da Mama Suka saki Baki suna kallo suna Jin haushi su Kuma gashi Basu Isa su iya ko Masa Maganar banza ba. Bucket Aamna ta kawo Masa har biyu ya nannade Hannun jallabiyarsa dake me dogon Hannu ce,agogonsa ya cire ya ajiye gefe,Yace Ina kayanki a nan? Aamna ta Tace ka gansu a nan,yace Miko ta kansu Zan fara,ai kuwa ta kwaso ta bashi a gabansa kala hudu sai su Hijab da Vest yace idan an Gama sai kije ki cire na jikinki suma a wanke su yau baza ki kwana da Kaya masu dirty a gidan Nan ba,Baba Yana gefe yace Uhmmm.....Sun kasa magana suna tsoro Dan kwaya ne sai ya birkice musu yanzu. Ahmad wanki ya fara baya wanki Yana wanke kala Daya Hannunsa ya fara Dan fashewa Amma ya maze yaci gaba da abinsa,Kugunsa ne ya fara ciwo sabo da sunkuyo amma idan ya Kalli Aamna sai ya fasa mikewa ya huta sabo Kar ya Gaza,Haka ya wanke kayan Aamna fes ya kwashe kayan Baba da Mama Yana tayata suna wankewa ya kusa wanke na Baba,Mama ganin banza ta Fadi sai tace ke Aamna tashi ki barshi ya karasa wankin ki Shiga kitchen ki Mana girki,Ahmad yace ya Zaki ce ta tafi? Mama Tace Kai kace Super Man ne ai sai ka karasa ita ta Mana girki, to Aamna ta furta ta tafi ta bar Ahmad,tana tafiya ya Mike tare da dauraye hannunsa ya kwashe Takalminsa a Hannu da agogonsa da wayarsa,Mama Tace ya zaka daina aikin,dama yayi masifar gajiya,da masifa yace Ni na gaji bazan iya ba dama na gaji yayi tafiyarsa da sauri,Mama tana Kai...Kai....Amma ko juyowa baiyi ba ya hau machine dinsa ya bar gidan. Mama da masifa ta shiga wurin Aamna Tace to ya gudu sai ki Koma ki karasa yace ya gaji shi,Dariya abin ya ba Aamna dama tasan karfin Hali ne Kawai Haka ta fito ta karasa Mama tana ta masifa taje taci gaba da aikin girkinta. Ahmad kuwa a gajiye ya shiga gida Yana dafe Kugunsa ya Iske Mashkoor Yana kallo,Yana yatsina Fuska ya zare rigarsa daga shi sai Singlet da gajeren wando ya fada saman kujera Yana bawa Mashkoor labari yace yau wanki na tayata wash...bayana...taimaka ka siyo min pain killer a chemist kazo kayi min gashi da ruwan zafi wayyooo bayana My waist Yana magana da kyar yace yatsuna sun fashe ....Ni..Ni...nine nace Super man ne Ni, Mashkoor ya dinga dariya yaje ya siyo Masa ya dawo tare da hado ruwan zafi ya dinga gasa jikin Ahmad,shi Kama sai Kara da wayyo,Kwana Uku Ahmad Yana jinyar jikinsa kafin ya warke ya dawo normal lokacin Aamna Bata ganshi ba. Yau Juma'a cikin sababbin dinkunansa yasa wata farar Shadda kamar ka sace shi yanda ya zuba kyau,calabarsa ya daure ya shirya Yana kamshi, Mashkoor ya kalle shi yace ban taba tunanin zaka ja Ni cikin Harkar Nan taka ba,kwana Uku ko Kofar gida ban leka ba wannan wacce masifa ce Wai,Gemunsa yake tajewa Yana shafe shi da wani turare Mai kamshi yace Ni fa na fara gajiya da Harkar wani Kawa da Abokin Nan ya kamata ta San me nakeji a Raina,Mashkoor yace ka bani dama Ni naje na fada Mata kana sonta,Baka da hankali an ce maka sonta nakeyi Kuma ko sonta nakeyi wani ne zai fada Mata Ina sonta ba Ni ba,ai Ni abinda nakeji a Raina game da ita Zan fada Mata ba Wani love ba. Mashkoor yace to yanzu fada Mata zaka Yi? yace ae direct Zan sameta gaba da gaba na fada duk irin abinda zuciyata takeyi idan na ganta yau yau din nan,Allah ya bada sa'a cewar Mashkoor,Fita yayi abinsa Musa me Gadi Yana a dawo lafiya ranka ya Dade,Ameen ya Furta yiyiwa Machine dinsa key ya fita zuwa Shagon Aamna,tana tsaye tana sallamar wata ta siyi kayan kamshi ta hango shi yayi parking,Murmushi tayi Tace Sannu da zuwa,Kasa magana yayi sai kallonta yake Yi har ya karaso inda take ya tsaya a gabanta daf da ita Kamar zai shige cikinta Kuma ya Bata Rai zuciyarsa ce Kawai take bugawa,kasa fada Mata yayi yace ya gida fuskar Nan a daure,Lfy Alhamdulillah ta furta tare da cewa shigo ka zauna Rana,shiga yayi Yana ta Fushi,Tace fushin me kakeyi yau Haka? Kadan ya kalleta Bayan ya zauna a farar kujera yace da zuciyata nake Fushi ita nake nunawa bacin Raina,Dariya ce ta Kama Aamna Yana ta kallonta a ransa yace kin cuceni zuciyata bazan yafe Miki ba Kuma yau Bari na koma gida sai kinci ubanki,Me ta maka zuciyar Aamna ta tambaya yace Ni kadai na San irin wulakancin da take mini Amma ba komai Yaja kwafa,Aamna ta sake kecewa da dariya Tace kana da abun Dariya wlh,Kawai sai ran Ahmad ya baci shi ga abinda ya dame shi ya fada ya kasa fada duk akan Aamna Dan rainin hankali ta sashi a gaba tana ta dariya,a ransa yace na koma ma abin Dariya na koma Comedian ba komai yayi Shuru. Har ta Gama dariyar ta dakko Gyada soyayya Tace ga Gyada muci,ganin tasa hannnu a Ledar ta Eba tana ci sai shima zai Eba Aamna Tace tsaya na bare maka,bare Masa tayi Guda biyar ta zuba Masa a tafin Hannu Tace to ci,kallonta yayi sannan ya zuba a bakinsa Yana daga zaune Yaja baya yayi wani tangal tangal Kamar zai Fado Aamna ta rike kafadarsa da sauri tana tambaya lafiya???yace Dadi ne ya kwashe Ni sabo da hannunki da ya shafi jikin gyadar nan,Dariya Aamna tayi Tace Kai Ni nayi zaton ma wani Abu ne,wani English novel ta dakko na love tana karantawa Tace ka San littafin Nan? Na Mene ya tambaya? Love Novel ne Baki ya tabe yace sai ku wannan ai,Mayafinta ne ya Dan zame kadan gashin Gaban goshinta ya bayyana wani yala yala,Hannu ya sa tare da jawo mayafin ya gyara Mata Aamna dai mamaki yake Bata kamar ba shi ba,duk irin kiyayyar Daya nuna Mata tana ina ne? A ranta Tace Anya ba Yana da manufa a kaina ba kuwa? Gaskiya Zan nemi shawarar Siyama. Kiran Sallah aka kwala Sallar Juma'a,Aamna ta kalle shi tace yanzu za'a fara khuduba sai muje Sallah ko? Da sauri ya girgiza Kai yace a gida zanyi anjima,Jam'i Yana da Lada fa? Yace na fiki sani ai, kin San kuwa Islamiyya Nawa nayi a duniya? Kin San saukata Nawa? Aamna Tace Dan Allah muje tare,a ransa yace Yarinyar Nan fa zata fara juyani karka sake wannan Yar tatsitsiyar ta juyaka a banza,ai ba sonta kakeyi ba da har zata juyaka,wata zuciyar tace Amma idan kaje Sallar zata ji Dadi zata samu farin ciki,Kumatunsa ya Mara a hankali yace Kar ka Bari ta juyaka ka dawo hankalinka,mikewa yayi yace Zan tafi,Tace Nima tafiya zanyi zanje gidan Zuhra,yace kin fiye yawo to na fasa tafiyar Zama ya koma yayi Dole ta zauna,Lokacin Sallah yayi Yana kallo tayi Alwala tayi Sallah a Nan shagon,tana idarwa yace Sannu da kokari,Fuska ta Bata tace Dan Allah kayi Sallah Kar lokacinta ya wuce,Shuru yayi Kuma yaki tashi sai yaga tayi Fushi ta zauna,Fuskarta ya leka kadan a ransa yace akan Haka har tayi fushi,Bari to na Yi Amma badan fushinta ba,Mikewa yayi tana kallo yayi Alwala ya Tada Sallah murna tayi ta saki ranta ta juya tana kallonsa a nutse yayi sallarsa kasancewar Bai Sha komai ba,Yana idarwa ya Mike ya fice tare da tafiya ko Sallama bai Mata ba. Mashkoor kuwa Yana can a gidan Ahmad tare da su Jibson gaba Daya Yana ta Basu labari yanda Sarkinsu ya lalace,duk sukayi tagumi suna jimami,Jibson yace ai kuwa sai munje har inda yake tayata siyar da citta mun kure shi,yanzu King ne ya lalace Haka abin haushin Akan wannan Yar Yarinyar Aunty Balaraba cewar Bash,Mashkoor yace yanzu idan kaga shigarsa Daya canja kamar Limamin masallaci,Salati suka saki Tawaga yace duk akan Yarinyar nan lallai sai munci ubanta kuwa tunda ta mayar Mana da King Haka, Mashkoor yace Uhm Baku gani ba har wani sharemu yake Yi ba Amma muyi Masa Uzuri ai King ne sai abinda yace,Allah sarki masu shaye shaye da hankalinsu sun San Amana da abokantaka duk abinda dayansu ke so suna so,sannan basa mantawa da Alkhairi da zaman tare,shi yasa sun Shaku da juna sosai. Ko da Ahmad ya shigo ya Iske su tafawa sukayi ya haura sama,Yana shiga wayarsa ya dauka tare da Kiran Sis dinsa Humaira,Humaira Tace Yaya na? Ya kake? Ba lafiya sis Dan Uwanki ya fada cikin bala'i,Humaira ta tsorata sabo da Bata taba Jin yayanta Haka ba,Kamar zata Yi kuka Tace Yaya mene ya sameka? Sis wata ce Nan idan na Ganda zuciyata kamar zata fito ta fado,sai ta dinga Yi min kida me zaki,Humaira Tace Kamar ya? Yace idan fa ban ganta ba bana iya bacci,sai na ganta nake samun nutsuwa,Haka idan naji muryarta sai naji Kamar wani kidan goge sabo da Dadi,gashi tsoronta nakeyi sai naji na kasa fada Mata me nake ji,Yanzu ya zanyi? Humaira tayi zaton zaice Aamna ce Amma yace Mata wata,Amma duk da Haka tayi murna yayanta ya fada soyayya,Tace Yaya kaje ka sameta karka ji tsoro Kawai ka fada Mata me kake ji,ka daure Haba Yaya kamarka wace zata ce baka Mata,Sis Nifa ba sonta nake Yi ba Kawai dai Ni na fada Miki abinda nake ji,Humaira tayi Dariya tare da furta ka fada Mata karka ji wani shayinta kaji,yace to sis Zan gwada ya kashe wayar,lokacin da yayi wanka su Jibson sun tafi sai Mashkoor sai shi. Ahmad dakin Aamna ya Shiga Wanda ta bari,cikin kayanta data Bari ya zabo wani Mayafi Baki ya fito Palo wajen Mashkoor tare da jefa mayafin a jikin Mashkoor yace Man tashi ka yafa mayafin Nan za mu gwada practical akan yanda Zan furtawa Aamna me nake ji game da ita,yanzu ka yafa mayafin Nan Kaine a matsayin Aamna Ni Kuma Zan zo na gwada ya zan bullo Mata idan naje, Mashkoor ya dinga dariya harda buga kafa,ya Mike yayi Rolling da mayafin Aamna ya taho Yana yanga tare da wani shanye Hannu,a Gaban Ahmad ya tsaya tare da Yi Masa fari da Ido ya wani tsotsi lips yace Hey.....harda rike hips da Hannu Daya yanda Mata ke Yi,Ahmad Dariya ta kamashi shima ya kalli Mashkoor yace to ai Ni gemunka ne idan na kalla Taya Zan maka magana Ina ganin gemu dalla jiba Muscle dinka damatsa na maza,jiki Kamar katako, Mashkoor ya sake makale Murya Yana fari da Ido yace Dan Allah kayi mu gwada ai Kawai Kamar shooting Film ne Oya fara Mana nine Aamna gani. Ahmad Yana daga zaune ya fara magana Kamar zaiyi kuka,Baby Idan na ganki zuciyata wani Dancing take min,Idan kika min murmushi kuwa har wani Rawar galala zuciyata take min,Sannan Ni sai naji Ina shakkar Yi Miki magan....da sauri Mashkoor ya dakatar da shi yace dalla Haka zaka Yi lallai zata Raina ka Haka maza ke magana wani gadangatsai Taya zaka burgeta oya canja salo Action.....Ahmad yayi Gyaran Murya tare da gyarawa ya kalli Mashkoor zai fara magana sai ya sheke da dariya yace wallahi idan na kalli Damatsanka hankalina Bai kwanciya bana kallonka a Aamna ga gemu da saje haba,Kayi sauri Dan Allah wannan fa Kamar Film ne gwada Ina jiranka Mashkoor ya furta Yana wani Fari da Ido Yana karairaya Kamar Dan Daudu,Ahmad mikewa yayi tsaye yace Ni bazan iya ba kallonka nakeyi wani Gardin banza dalla bani ya fisge mayafin daga jikin Mashkoor tare da ajiyewa a gefensa, Mashkoor yace kaga matarka ce fa ka daina wannan abin ka fadawa Mummy ta fadawa Aamna ta dawo gidanka kaga shike Nan. Ahmad yace baka da hankali Nifa ba Wai wani mu zauna tare ko wani Sex ba,ya za ayi na birgeta,ya za ayi tasan me nakeji a Raina game da ita shine Kawai dawowarta gidana ba shine mafita ba,Ni ba wannan nake so ba,Dan dawowarta ai ba matsala bane Kawai Ni ka Gane nufi na,idan ta San halin da nake ciki Nan gaba Sanda taga tana so sai ta dawo gidana Ni wannan ba shine damuwa ta, Mashkoor yace Amma sai kayi ta wahalar da kanka kana tsallaka musu gida,Kai banza ne bana so ajina ya zube ta Gane Ina son na kalleta ko wani Abu,ai abin sai da dabara cewar Ahmad. Da dare 9pm Ahmad suka Isa gidan su Aamna Mashkoor Yana jiransa a can bayan gidan,Wai shi lallai Bai so Aamna ta Gane Yana son ganinta sai dai ya kalle ta a boye. Sharhi AsmaBaffa 10/26/21, 8:53 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 51-55 KARSHEN FREE PAGE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE MASU SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Kinfi karfin page NAFEE Allah ya bar kauna Page naku ne MAMU GALADIMA AYUSHEE MOM PAPI AND ALAMEEN OUM ABULKHAIR HAUWANCY COOL LIFE S.Y.SAGAGI RA'AYYS I HAFSAT UMMY MANGA MAMAN ARFAT MAMAN YASIR M DEWU HAUWA A CHINDO HALIMA GODIYA TA MUSAMMAN DIYAR KATIBI UMMIN HIBBAH UMMA KHURSUM ASMAU YUSUF UMMIN DEEJAT BESTYNBEELAT Yau Baba Bai dawo da wuri ba,Aamna Kuma dawowarta kenan daga gidan Zuhra Mama Tace tazo ta tayata dafawa Baba abinci,ko hutawa Bata Yi ba ta shiga wajen Mama a kitchen suna girki,ta Kofar gate Ahmad ya shigo gidan,ta windown kitchen ya leko dai dai lokacin Mama ta dago kanta sama Kawai Harshen Ahmad ta gani ya Mata gwalo ya bace. Amma Bata San shi bane Tace Kinga kamar Harshen mutum ta window ya min gwalo ya bace Aamna,Aamna ta sheke da dariya Tace wallahi Mama yanar Ido ta Kamaki sai munje asibiti an duba idonki,Mama ta dage ita fa sosai taga Harshen mutum,Aamna ce ta maida abin Dariya shi yasa Mama ta hakura Kawai, shi kuwa ya gansu a kitchen ai ta Kofar Palo ya shigo a hankali ya shige Dakin Aamna,bed din Aamna wani me kyau ne na karfe irin na kasar waje Dan madaidaici Amma kasan bed din Yana da tsayi mutum zai iya Shiga kasan Bed din ya buya gashi ta gyara bed din ta saki bedsheet har Yana taba kasa ma'ana ko mene a kasan Bed din baza a iya gani ba,lekawa Ahmad yayi ya kuwa shige ciki ya kwanta abinsa,Bai Dade ba Aamna ta shigo dakin tare da dannawa kofarta key,Abincinta ta Ajiye a plate da ruwa harda lemo mirinda,ganin ba kowa a dakin ta kulle ko Ina sai ta hau tube kaya,dama dabiarta ce idan ta kulle Kofa ta dinga tubewa daga ita sai pant ba komai a jikinta,Ahmad yace yau ma idona zai samu Karin karfin gani Ni da ciwon Ido haihata haihata ya Dan leko ta kasa,Baki ya bude ganin Aamna da pad a jikinta da Alama period takeyi,Yana kallo ta dakko wata pad din da bakar Leda ta shige toilet sabo da Gadarar ba kowa ga towel a Hannunta Amma Taki daurawa ta tafi da shi a hannu. Fitowa Ahmad yayi ya Bude plate din yaga rice and stew da Naman rago yanka Uku sai salat a gefe,yace da a gidana ne sai kinci nama kin koshi duk Loma Daya sai kin hada da yankan nama,Sorry My world ya rufe Mata tare da komawa kasan bed,ta Dade tana wanka kafin ta fito tana goge jikinta ta fara shafa lotion ta cire guntun Towel din tana ta shafe jikinta,Ahmad Idonsa Yana waje ya leko yace sunanki me Tinjim daga yau,sai data Gama sannan ta saka Riga da wando na bacci masu laushi ta zauna ta tare da fara cin abincinta da mamaki yaga ta cinye tas ta shanye lemo da ruwa,a hankali yace Allah yasa Ina da kudi Zan iya ci dake Amma da talaka kika aura ai ke Kam shikenan sai dai Gomnati ta kawo dauki, Popcorn yaga ta dakko a wani katon Bowl ta Ajiye a gefen bed ta kwanta tana latsa Wayarta tana ci a hankali,idan ta eba ta cire Hannunta tana can tana Danna waya sai ya zuro Hannu ya eba ya cinye a kasan Bed, suna Haka taga wayam Wai har ya Kare,Aamna ta dinga mamakin kanta Wai har ta cinye popcorn din,ta kashe Wayarta tare da kashe light ta kwanta tana adduoi kafin ta Gama Adduar bacci ya kwashe ta. Sai da ya tabbatar baccinta yayi nauyi sannan ya fito a hankali da Dan hasken wayarsa yayi amfani tare da Kare Mata kallo,Aamna ta baje a saman Bed,cinyoyinta Suka tafi da hankalinsa Hannu yasa tare da shafa su a hankali yanda baza ta tashi ba,motsi tayi kadan tare da sake wangale su,Ido ya Kura musu yasa Hannun ya janye rigarta sama sosai ya kallesu son ransa, ganin kamar zata farka sai ya daina, Kansa ya duka a saitin kirjinta tare da kwantar da Kansa a Kirjinta yaji wani laushi sai ya lumshe Ido Nan take yaji ya fara Jin bacci,da sauri ya tashi Jin ta hada zufa sosai sabo da Rashin wuta bare a kunna fanka,Mifici ya gani a can gefen bed din nata,Dauka yayi a hankali ya shiga yiwa Aamna fifita ba ji ba gani Kamar me jinya a gadon asibiti,Aamna cikin bacci taji Iska me Dadi tana Ratsata ta sake gyara kwanciya tare da Jan numfashi me Dadi,Murmushi yayi yaci gaba da Mata fifita sai da Hannunsa ya gaji sannan yaga Kamar zata farka sai ya ajiye mificin ya lallaba ya bude Kofar a hankali ya fita Allah yasa Bata farka ba Kuma Bai hadu da kowa ba har ya bar gidan, Mashkoor Yana ta uban jira ya hauro ya fito Suka tafi gida. Hannu Dayan Wanda ya shafa Cinyar Aamna sai Ahmad ya daga shi sama kada ya daina amfani da shi Kamar Wanda aka yiwa lallen Sallah,Mashkoor yace lafiya Wai me ya samu Hannun rauni kaji ne?yace ai wannan Hannu yau ya Zama special bazan na aiki da shi ba,Kai ko Gaisawa da maza bazai Yi ba sabo da jikin Aamna Yana makale a jikin hannun Nan, Mashkoor yace ka shiga Uku wallahi king. Bayan Kwana uku Siyama ce ta Kira Aamna lokacin Aamna tana shago Tace gani Nan zanzo Miki Ziyara,da murna Aamna Tace to sai kinzo,15mnt da yin wayarsu Ahmad yazo sanye cikin 3qutr da t-shirt hannunsa dauke da wata katuwar leda baka,Murmushi Aamna ta saki tare da Furta Sannu da zuwa,jajayen lips dinsa ya turo gaba da shagwaba,Ledar ya kawo gabanta tare da ajiyewa ta Bude yaga kifi tarwada da yawan gaske,murmushi ta saki tare da Kallonsa Tace yanzu baka manta ba Ashe Kuma ma ai Rannan ka Aiko Mashkoor ya kawo min kifin harda kaji da yawa fa,Ba kince kina sonsa ba? Ae ta furta yace to ai shine na kawo Miki,Kuma kaji ai Naga a gidan Baba bakya cin nama kina koshi shi yasa duk sai ramewa kike Yi,Dariya Aamna tayi Tace Ni bana son sharri duk kibar Dana yi,Kallonta ya tsaya Yana Yi har ta Gama dariyar,ke komai naki Dariya Wai Ina rashin kunyarki tayi ne da surutunki? a baya masifa kike min da Shishigi me yasa yanzu kika daina? Aamna kanta ta danga sama tayi fari da Ido Ahmad a ransa yace Mashaallah ko iya wannan aka barni da shi ya isheni farin ciki na sati Guda idan na tuna shi. Mikewa tayi tsaye tana Masa Murmushi Tace Kaine ka gyara min halaye na,kaci ubana da yawa sai lokacin na Gane Allah Daya,a hankali yanda baza taji ba yace ai Nima yanzu uban Nawa kike ci na Zama wani banza,Bakinsa taga Yana motsi Tace me kace? Cewa nayi Ni ba abinda na Miki kece kike min shishigi,Siyama ce tayi Sallama gabanta ya Fadi ganin Ahmad da Aamna a tsaye daf da juna kamar zasu Rungume juna,Fuska ta Bata tana Hararar Ahmad sabo da kishinsa,ita ba hassada takewa Aamna ba Kawai son Ahmad ne yayi tasiri a ranta taji dama ita ce. Laaa Siyama kinzo cewar Aamna,Ahmad juyowa yayi Amma ko kallo Bata samu daga gare shi ba ya maida hankalinsa cikin Shagon,Nan Siyama ta shige ciki ta zauna tana satar kallon Ahmad,Ledar dake gaban Aamna take ta faman kallo taga kamar Abu na motsi ciki,Ahmad ganin tana ta kallon Ledar ya tabbatar Aamna sai tabawa Siyama kifin Nan itama ko su raba tare sai ya leka Daya shagon ya Kira wani yaro Wanda Ahmad yasan Yaron kusa da gidan su Aamna yake ganinsa shima gidansu makwafta ne,Yaron Yana zuwa Ahmad harda shafa Kansa yace Dan magyatso kasan gidan su Aamna? Yaron da Ahmad ya Masa suna da Dan Magyatso yayi dariyar sunan sabo Yaron Kalar yunwa ne,jikinsa tsilili cikinsa Dan kato sabo da Almajirin gidan Wasu ne a kusa da gidan su Aamna,yace ae nasan gidan Ina shiga ma idan an aikeni,Ahmad yace ka iya machine? Yaron yace sosai ma ai Ni nake yo cefane a machine din gidan Uwar dakina,Good cewar Ahmad yace ungo key din machine Dina jeka gidan su Aamna ka kaiwa Mama sakon Nan kace gashi inji Aamna,Yaron yace to ya karba ya hau machine din Ahmad ya tafi,Siyama ta so ace ta karbi kifin ko Quarter ne itama taje gida sun Sha farfesu Amma tana kallo Ahmad ya dauke Dan mugunta. Tunda Siyama ta Shiga shi ya fito ya tsaya a waje,Aamna Tace ka shigo Mana yace a'a Machine Dina nake jira tafiya zanyi,Siyama ta kalla tace ina zuwa kawata ta fito Wajensa suka tsaya,tana ta Kallonsa a ranta tana ayyana irin kyansa,Shi kuwa ganin tana kallonsa harda Kara gyarawa Kamar za a dauke shi hoto,idan ta kalla ta kalla sai ya sake canja style din tsaiwarsa Haka yake ta Mata ya tafi da hankalinta sai daga baya ta lura da abinda Ahmad ke Yi Yana ta canja style din tsaiwa,Dariya ce ta Kama Aamna ta danne kadan tayi Murmushi Kansa ya shafa tare da mazewa kamar ba shine yayi ba,Hannunsa Aamna ta rike ya Janye hannunsa da sauri,Aamna tace lafiya? Kitsonsa ya Sosa yace ba komai Kawai Ni ba a taba min jiki kin sani ko kin manta ne? Baki Aamna ta tabe Tace daga an Dan rike maka Hannu sai kace Dan gwal? Yace ai nafi gwal Ni,Harararsa tayi a ranta tace Dan ma na Dan nuna Masa caring shi illarsa Bai San arziki ba,Ganin ta harareshi yace Jaraba tare da miko Hannun yace ungo cinye shi ki huta,Bige Hannun tayi tana Dariya Tace bana so,Suna Haka Yaron ya dawo da Machine din Ahmad ya karba tare da bawa Yaron dubu biyu,ya dinga Murna yana godiya,Ina Handbag dinki? Ahmad ya tambayi Aamna. Tana ciki yace dakko min ita,me zakayi da ita Fuska ya Bata yace ki dakko Mana Ni ba Mudubi ko powder dinki Zan gani ba nasan ku ba Uwar komai a jaka sai Kuna boyeta,Dakkowa tayi tare da Mika Masa yace Bude abarki ki rufe idonki Kuma,Aamna ta zuge jaka ta rufe ido,ganin Haka Siyama ta leko tana kallo Ahmad ya zaro kudi masu yawa Yan dubu dubu ya zubawa Aamna a jaka yace to Bude,Bude Idonta tayi taga kudi dama Bata da kudi tayi broke Bata da ko sisi gashi tana son siyen abinda ba a rasa ba na bukatar rayuwa,taji Dadi sabo da ya Bata lokacin da take bukata Tace Na gode Allah ya Kara budi Amma sunyi yawa kamar,Kansa ya dauke yace na tafi Mummyta ta aikeni tun dazu wani waje zanje na Mata Abu,Aamna Tace Kai dai kana son Mummy kullum Mummy,ai Mummy ta daban ce,Mummy na tafi Mummyn kowa cewar Ahmad,Aamna Tace Nima tawa tafi ta kowa,Murmushi yayi yace kin nemi Number Abbanki kuwa? Aamna Tace me Zan Masa tunda ya manta da ya auri Uwata ya Kuma haife Ni idan na karba me Zan Masa? You are not Serious Haka aka ce Miki Iyaye suna laifi?Shuru Aamna tayi Watarana tana mamakin Hankalin su Ahmad,gasu dai suna tafka abin tsiya sai Suna Abu Kuma na basira da hankali, a fili tace Suma Yan Uwan nasa Dana je Sokoto nace su bani number dinsa Suka ce wallahi wurin shekara Uku kenan duk sun kasa Samunsa sai dai suna Kiran Yan Uwa na can kasar sunce yana Nan lafiya Kawai dai yanzu yayi retire a aiki Bai da aikin Yi ga Yara da Mata sun Masa yawa wahala ta kamashi,Ahmad ya girgiza Kai yace tab nasan yanzu ya sake kanjamewa Allah Sarki Abbinki,Aamna Dariya ya Bata ta bigeshi a kafada kadan Tace Wai Mene Haka ka dameshi Akan ramarsa, Murmushi yayi yace Bai yuwa ya rasa waya sai kace a Nigeria ai can ba a wannan talaucin, Ni Zan nemo Miki number dinsa,Aamna Tace Okay thanks, Machine dinsa yayiwa key tare da tafiya abinsa. Siyama tana zaune ta kumbura tayi fam kamar ta fashe tace ke dai Aamna kinyi asara,wallahi Baki da hankali to wannan abinda yake nuna Miki ba so bane,Kar ma ki yaudari kanki Ahmad bazai taba shiryuwa ba ko jiya naje wajen Jibson a club Suka kwana suna shaye shaye suna rawa,Aamna Tace karya kikeyi Siyama wallahi Ahmad baya rawa,Yana Jin kida Yana bin Waka Amma in Banda ya Dan kada Kansa ba abinda ya taba Yi na rawa,Da kike cewa bazai shiryu ba kece Allah,Ina ruwana da Club dinsa,Siyama Tace Iyye to Bari kiji idan Baki sani ba Neman Mata suka koma Yi yanzu,kije ki tambaya Ahmad lallabaki yakeyi ki saki jiki da shi ya samu biyan bukata,Aamna Tace karfa ki manta Mijina ne,ko ma me yayi Hakkinsa ne ko ciki ya min akwai me zagina a duniya? Wai me yasa kika tsani Ahmad Haka ne Siyama? Siyama Tace sabo da Ina sonki kawata Ina kaunarki bana so ki fada wani Hali,Aamna tayi shuru....Tace to yanzu me kike so nayi? Karki bashi dama Kawai Kuma karki yarda da shi karki Bari Zuciyarki ta fada sonsa cutarki zaiyi,ki kiyaye Aamna bana so na ganki cikin wani Hali,plan suka hada Miki,Ahmad tun Yana yaro kangararre ne a Haka ya girma a tunaninki dare daya zai shiryu sabo da ke? Kiyi tunani fa,wanne duka da wulakanci ne Baki Sha ba a Wajensa? Ai Ni nake tsokanarsa Aamna ko a lokacin Ni ke shiga harkarsa da ban kulashi ba babu abinda zai min,Siyama tayi Dariya Tace kina Abu kamar yarinya 25yrs Sam Baki da wayo Baki da hankali Ni Naga wani Tsoronsa kike ji ma kina wani biye Masa,Dan giya irin wannan Dan kwaya abin kyama cikin Al'umma mutanen da Basu San darajar kansu ba bare ta wani Nan fa Siyama ta dage ta dinga zuga Aamna tana fada Mata karya,har ta Gama sannan Aamna Tace Ni fa bazan iya wulakanta shi ba,Kuma bazan iya masa komai da zai Bata Masa Rai ba,Kawai dai nasan bazan Bari na fada sonsa ba,ko cewa yayi Yana so na Zan Amince Amma badan so ba Zan Amince Dan nayi kokari na canja shi ya dawo mutum Kamar kowa ya daina wannan shaye shayen shine Kawai abinda Zan iya Dan na taimaki Iyayensa,Siyama tace ya dai fiye Miki Ina Baki shawara karki fada sonsa. Bayan wasu satikai Ahmad Haka yake ta wahala da zuciyarsa ya kasa fadawa Aamna idan yaje da Niyyar fada sai ya kasa babu irin plan din da Basu hada ba da su Mashkoor Amma idan Ahmad yaje Gaban Aamna sai ya kasa furtawa,Yau Suna zaune da Mashkoor suna shaye shayensu Mashkoor yace yau shine Plan na karshe King idan baka iya fada Mata ba wallahi gidan Nan Zan Bari kaje ka karata,Ahmad ya daki Center table yace yau Dole ne na fada ma Dole babu fashi mene plan na gaba?wayarsa ce tayi Kara Yana dubawa yaga Bash ne abokinsu dagawa yayi yace ya akayi ne guy? King ku fito Umman Jibson ce ta rasu a asibiti ciwon Sugar dinta ne ya tashi Ana kaita Hospital ta fece wallahi,Ba ko Salati Ahmad yace yanzu Ummati ta ware itama? Yace kwarai kuwa Kun manta yau Kuma ake Sadakar Arba'in din Baban Tawaga da ya Dier shima ya kamata ku fito fa Jibson Yana wani Hali, Mashkoor ya kashe waya tare da kallon Mashkoor tashi mu tafi Ummati ta arce itama shikenan mijinta yayi asarar matarsa Allah sarki Shan maganin Mata ya Kare Abbin Jibson Kuma karya ta Kare Dadi ya kare Masa ya Gama Shan rabonsa, Mashkoor yace Kai tsohuwar Nan ai ta godewa Allah ai su Kam sunci duniyarsu me zasu ce da Allah mu ware kawai. Machine suka figa Suka tafi Ahmad ya kalli Musa yace Kai Musa ka taho ta'aziyyar Ummatin Jibson kaga ku na kirki ne wala'allan adduarku tafi Shiga,Dariya abin ya Bawa Musa ya danne ya nuna jimaminsa yace gani Nan kuwa Bari na kulle gida,Ahmad yace biki ya same mu sabo da yanzu mutuwa ta koma biki Yan iskan mutane su taru ayi ta kwasar girki, Mashkoor yace Ana kaita kabari muje a agazawa su Jibson da tallafin kayan abinci kasan babansu ba harka Yana Shan wahala,Haka ne fa Guy cewar Ahmad,ai kafin kace me Yan shaye shaye ta ko Ina abokan su Jibson suna ta sauka wasu a mota wasu a machina, da su aka yiwa Ummatin Jibson Sallah aka kaita,Tabarmar su daban a Kofar gida sunyi jungum jungum Ana zaman makoki,Jibson ya dunkule waje daya a tsakiyarsu tare da sunkuyar da Kai kasa Yana Dan Hawaye motsi kadan sai Yace Uhmmmmm........Uhmmmm.....su Kuma abokan suna Sorry...sorry....Guy,Baban Jibson Yana kusa dasu Yana jinsu da mutanensa shima Ana karbar gaisuwa,duk Wanda yazo yiwa Jibson gaisuwa yace Ashe Ummati ta rasu? Jibson sai yace da Uwata ta mutu gwara Ubana ya mutu wallahi,Kowa yazo sai Jibson ya fada Masa da Uwata ta mutu gwara Ubana ya mutu Abbin Jibson Yana ji Yana ta Jan kwafa,wasu kuwa dariyarsu Kawai suke dannewa. Tawaga ne yazo ya kotse machine tare da bulbule mutanen wajen da hayaki ya sakko wajen su Ahmad ya Bude hannaye da sauri Yana takowa Yana an Kuma...an Kuma Yan Uwa an Kuma jama'a...suka ce cikin jimami an Kuma Guyu......ciki yazo ya zauna yace Yau akayi Sadakar Arba'in ta Abbana Ni fa yanzu gaba daya na koma Wani shege....shegeee ne Ni Kawai bani da uba...kaf mutanen wajen babu Wanda Bai Basu Dariya ba Amma wasu Haka suka danne sabo da wajen Mutuwa ne,wani Wanda ake cewa Gayu yace ai Nima Ina cikin Shegun mu mun Zama 'yayan shege to ba uba ai Kawai ka Zama Dan shege....wani Ana kiransa Jagu Dan wiwi a cikinsu yace wannan abin idan na tuna ba karamin kuka yake sani ba ya fashe da kuka shima Yana cewa Nima Ina cikin 'yayan Shegu,Wai su Kawai idan baka da uba ya mutu to ka koma Dan Shege,idan Kuma Uwa ce to ka Zama cikakken Maraya komai girmanka. Ahmad ya dafa Jibson yace ai gwara na Zama Shege akan na Zama Maraya Jibson,Mummy ta Mutu ai Kawai ku kaini kabari da Raina Nima ku binne,Mashkoor yace mu Kuma mu zauna da wa idan mun binneka shike Nan muma Bamu da kai? Ai bazai yuwu ayi biyu babu ko daya ba,Ana ta kallonsu Dariya ta cika mutane Amma an kasa Yi sabo da mutuwa kowa sai ya bar wajen yake Dariya,Wani Dan Majalisa yazo Ta'aziyya,Baban Jibson ya Kira shi yace ga babban Dana can,Jibson ya karaso wajen,Dan Majalisa yace Sannu da Hakuri Allah yaji kanta yaro kayi Rashi,Jibson yace Babban Rashi yau na tabbata Maraya Dan Allah ku bani mukami a Gomnati na shugaban Marayu na Nigeria da Uwata ta mutu wallahi gwara Ubana ya wuce sau dubu dubu,Danmajalisa shima abin Dariya ya bashi gashi da yanda suke Maganar abin Dariya ta Yan maye. Kudi ya zaro dubu Ashirin ya mikawa Jibson yace gashi ko ruwa a siyawa Mutane Jibson yace Allah kiyaye na karbi bakin kudi,wannan bakin kudi ne tunda baka bani ba sai da Uwata ta mutu zaka bani wanne amfani zasu min,Baban Jibson ya daka Masa Tsawa Amma Jibson yace wallahi bazan karba ba,da karfi ya daga Murya Dan wulakanci sai da aka ga Uwata ta mutu Za'a taimakeni duk an wani cika Mana Kofar gida Ana cinye Mana Dan abincin Daya rage Mana,Dame zamu ji da cinye abinci ko da jimamin,kowa Yana ci Yana wani jimami,Mata Yan Uwa suna kuka suna ta girki Ana Dora tunkunya Ana saukewa wallahi baza mu lamunci wannan ba,Ahmad ya mike shima yace a barmu da abinda ya dame mu na rashin Ummati mun gaji tun safe muke bi layi layi na mutane Muna rabon ruwan Sha da Abinci,Tawaga yace aikin banza Muma Haka Dan kudin Sadakar da aka Tara Mana da abincinmu cikin sati Daya aka cinye shi tas ga tarin Yara an mutu an bar min,Baba ya dinga aure aure ya Tara Yara Ashe duk Haihuwar da akeyi Ni ake haifawa ban sani ba, wallahi da nasan hakane da kaina Zan dauki matan Baba na kaisu asibiti Dan ubansu duk a daure bakin Haifarsu,yanzu ga Yara can sunfi ashirin Ni kadai ne Babba Kuma ba Wani Abu ya mutu ya Bari ba gona ce Kawai a Kauye Guda biyu. Ina Shiga gida Yara suna zare Ido Yan kanana turagutsa ba Wanda zai iya aikin karfi to wallahi a Nan ma tunda Ummati ta rasu Baba baza ka Kara aure ba wallahi ko wace zata aure ka sai mun farke Mata ciki,Ahmad yace bazai yuwu Iyaye ku dinga aure aure Kuna mutuwa Kuna bar Mana masifa ba,ga yanda kasa take ciki yanzu a mutu a bar maka Yara Kai kanka da kyar kake iya rike cikinka, daga yau mun Zama masu yaki da Aure auren Iyayenmu maza,duk tsohon Daya matsu zai Kara aure to ya Nemo juya wacce Bata Haihuwa ko Kuma aje a cire Mata mahaifa. Jibson yace Iya Ummati Abbi ya aura Amma Haihuwar ta Sha Uku Haba jama'a sai kace macen Zomo, Guda Daya ne ya rasu Sha biyu suna Nan cas da me zanji gasu duk mata,ko wacce na shiga Yaya kudin makaranta,Yaya kudin kitso,Ya..ya..ya...masu auren ma yau Fa'iza mijinta ya hanata abinci ta dawo gida an auno Mata shinkafa ta tafi da ita,gobe Safiya mijinta ya mareta ta kawo Kara,jibi Zakiyya mijinta ya korota to a gaskiya bazai yuwu ba,daga yau kunci abincin karshe gobe ko koko ba me Fitowa da shi wallahi. Mutane suna ji Ana ta kallo wasu suna zanzarewa Baba shima yasan Yaran sunyi gaskiya tsoro yake ji Kar a cinye Dan abincin nasu su fada wani Hali Amma sun tozarta shi ya zaiyi dole ya kyalesu tunda su suke siyo komai abokan,Ahmad kadai mota guda ya sauke musu ta kayan abinci da safe,Haka duk abokan kowa iya karfinsa sun kawo tallafi daban daban,Kuma ko ba mutuwa sune suke taimakonsu basa kukan rashi. Ranar da akayi Sadakar Uku suka Kori kowa Suka ce Sunna sak ba zaman makoki ya Kare,Ranar Bash ya tafi gida ya Iske Mamansa tana Aiki yace Mama Yaran naki Mu bakwai kika Haifa Dan Allah Mama karki sake Haihuwa Haka,Mama ta kalle shi tayi murmushi Tace baka da kunya Bashir Ni kake gayawa Haka? Wato ka Sha ta maka yawa zaka zo ka min hauka ko? Bash yace Mama Naga darasi Yaran Nan Ni fa kuke haifawa kina ganin Yayana ba lafiyayye bane yanzu nine kamar Babba gashi Mama da kuruciyarki,Dake ita Maman Bash sai ka rantse ba ita ta haife su ba,Allah ya Bata kyan jiki karamin jiki gareta sai ka rantse Yayarsu ko kanwarsu,Bash yace Mama gobe Monday ki shirya zamu je asibiti ki duba abokina,Mama Tace Allah ya kaimu Bashir. Washe gari da Sassafe Bash ya dauki Mama zuwa Asibiti,wajen Likita Mama taga sun shiga,Bash yace Likita gata na kawo maka ita akan Maganar da mukayi,yace matarka ce ko me? Kawai Bashir yace Matata ce, Maman Bash Dake akwai saukin Hali ba ruwanta yaranta Kamar abokanta tana kallo Bash yace a Mata Allurar Family planning Haihuwar ta Isa Haka,Likita yayiwa Mama tambayoyin da Suka Dace itama dama ta gaji da Haihuwar,Test aka Mata Bata da ciki Nan Likita yayiwa Maman Bash Allurar wata biyu,yace idan time ya cika ku dawo Karku tsallake,Bash yace an gama,ya figi Mamansa a Machine suka dawo gida,Kuma Mama Bata fadawa mijinta ba sabo da Bash yace karki fada Masa kin San Baba Dan gargajiya ne sai dai yaga Shuru kin daina Haihuwa,daga yau Haihuwa ta Kare a gidan Nan sun Isa Haka, Mama tana ta dariyar su Bash. Bayan Mutuwa ta lafa anyi Sadakar Bakwai Aamna yau kwana bakwai Bata ga Ahmad ba,duk ta Shiga damuwa ta Kira wayarsa Bata shiga,Bata San mutuwa aka musu ba,Shi kuwa Ahmad da dare Bayan sun Gama shaye shayensu da safe 7am ya koma gida, Mummy ya Kira a waya, yace Mummy Ina cikin wani Hali,danki ya fada soyayya jiya jiya na gano cewar Soyayya na fada,Farin ciki ya Kama Mummy Tace wannan wacce me sa'ar ce? Bata kawo Aamna bace tunda yace wata ce tasan da Aamna ce zai ce Aamna ce,ta so ace Aamna ce,Mummy Tace to itama tasan kana sonta ko me? Ahmad yace Mummy kwarjini take min na kasa fada Mata,zuciyata idan na ganta bugawa takeyi,Mummy Tace karka damu Son ka cire tsoro Kai fa Namiji ne ko wace kaje Ni na baka dama ka fada Mata duk irin son da kake mata,Ni Mummy Umarni na baka ka furta Mata karka ji tsoro,ta dinga zuga Ahmad tana dorashi a Kan hanya,suna Gama Wayar yaji wani kwarin gwiwar da Bai taba ji, yace Mummy ce ta bani Umarni,wannan Umarnin Mummy ne naje na fada Mata. Ai zumbur Ahmad ya mike sanye da 3qutr blue da Riga Armless wata white and sky,ba Wani shiri ko wani wanka da canja Kaya na Kamala,lokacin zuciyarsa ta Gama tunzura, Kansa Kuma ba Wani saiti tunda jiya an cake da yawa,7am da sassaffe ya tsaya a Kofar gidan su Aamna ya Shiga dukan gidan Baji ba gani kamar zai balla musu gate,gaba dayansu a tsorace Suka yo waje Baba,Mama , Aamna tare da Siyama sabo da ranar Siyama a gidan su Aamna ta kwana,Baba Ne ya bude kofa,ko kulashi Ahmad Baiyi ba ya fada gidan a fusace da Masifa hankali a tashe Yana Bala'i ya tsaya a Gaban Aamna Dake tsaye sanye da kayan bacci ya nunata da yatsa da karfi a gigice ba nutsuwa Yana haki yace Kin hanani sukuni...tun Sanda na ganki Bayan kin bar gidana kina shago...zu..zuciyata...ta kasa sukuni...Dora Hannu yayi aka ya sake nuna ta da yatsa da sauri da sauri yake magana ba kakkautawa Yana zaga compound din gidan Yana Wallahi na rantse.....ko idona na rufe bana bacci fuskarki nake gani kina min gizo....kullum idan na ganki zuciyata bugawa takeyi...Ina Jin tsoronki......ko yaushe bani da sukuni....burina kullum na ganki....ko naji muryarki.....bana...Bana Iya motsi sai da tunaninki......komai nakeyi kece a Raina....kece.... kike min gizo....sunanki idan aka ambata sai zuciyata ta buga.....Haka nake tsallakowa gidanku cikin dare in labe inyi ta kallonki.....Rannan ma Dan karku kamani nayi muku basaja na sace muku startime da Radio....Baba ya kurma Ihu tare da nuna Ahmad yace Kaine??......Ahmad Bai kulashi ba yaci gaba da bayani....yace kusan kullum da dare sai na shigo gidan Nan na ganki baki sani ba....har dakinki nake buya na Sha kallonki tsirara kin shiga wanka......da Ni kike rufe kofa a room Dinki duk abinda kike Yi Ina kallo....kunya ta lullube Aamna ta sunkuyar da Kai kasa. Ci gaba yayi da bayani yace duk abinda nake Miki Dan kiji Dadi nakeyi.... komai Danke nakeyi....har zuwa shago Dan na ganki naji Dadi ne.....Yan....yanzu ma....zuciyata bugawa takeyi wallahi Ina sonki....sonki nake Yi...da ban Gane sonki nakeyi ba sai yanzu.....Murya ya canja Kamar me kuka ya hada zufa Yana haki yace Yan....yanzu....ma tunda nazo gabanki zuciyata Bugawa takeyi.....idan Baki yarda ba taba kurjina kiji ya cafko Hannun Aamna ya daura a kirjinsa saitin zuciyarsa yace kinji?...kinji?....Aamna Tace ae naji ta zame Hannunta.....Siyama,Mama,da Baba suna ta tabe Masa Baki sabo da basa son abin,shi kuwa Bata su yake ba ci gaba yayi da cewa Wallahi Allah Sonki nakeyi......idan Baki yarda ba Kira number ta kiga sunan Dana saka Miki a Kan number dinki,Aamna ba musu ta latsa Wayarta ta Kira wayarsa sai ga Sunan Daya sa Mata ya Bayyana MY WORLD. Bai tsaya ba yaci gaba da bayani Yana tonawa Kansa asiri Wai duk cikin bayyana soyayyarsa a gareta ne. KARSHEN FREE PAGE ASMABAFFA. 10/26/21, 8:53 AM - A Maryam: P🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DAN ALLAH KARKI FITAR DA NOVEL DIN NAN BADAN NI BA DAN GIRMAN ALLAH, IDAN BAKI BIYA BA KARKI KARANTA DAN DARAJAR ALLAH. DUNIYA TA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 55-60 Official By AsmaBaffa Page naku ne mutanena Yan Albarka UMMI DEEJAT ALHUSNA Yace nine....Nine.....Ni ....ya rasa me zai ce ma karshe yace Ni...dai Dan Allah Ina sonki kinji....kinji....ya kafe ta da Ido Kamar zaiyi kuka,Mama ce tace ai taji ka kaje kawai....kallon Aamna yayi yace na tafi kawai? Ae jeka cewar Baba,yace Kawai? Suka ce ae jeka zata baka amsa daga baya,shi Kam tuni yaji zuciyarsa wasai tunda ya amayar da abinda ya dame shi sai Kawai ya juya ya tafi abinsa zuciyarsa Kuma na tsoron amsar Aamna da zata bashi Nan gaba,Haka ya koma hankalinsa ya kwanta ko Bata ce tana sonsa ba ya fada Mata sakon zuciyarsa. Gaba Daya ya samu su Mashkoor a gidan su Bash,yace to yau dai anyi ta Ta Kare yau na bayyana Mata,Ihu Suka saki na murna tare da tambayar me Tace? Yace Wai zata bani amsa daga baya,Tagumi Suka Yi Suka ce zaman makoki Bai Kare ba,Yarinyar Nan da raini take kamarka kace kana sonta Tace wani sai Nan gaba ma zata bada amsa,Gaskiya Aunty Balaraba Bata Yi ba sam,Nima Ina tsoron lamarin Nan cewar Mashkoor yarinya tsigigiya duk ta gigita Mana Kai,Ahmad yace wallahi Ni kaina zagin kaina da kaina nakeyi,kullum sai na shiga daki na tsinewa kaina sannan na fito,wannan abin tsinuwa ne Man cewar Tawaga. Aamna kuwa Bayan ya tafi Mama Tace masifa wannan wanne irin tsagera ne Haka ba ko kunya bare Kara,Baba yace Yaran karshen tashin alkiyama ne in Banda tambadewa kai mtswww Baba Yaja Tsaki,Siyama kuwa ranta yau idan yayi dubu ya baci,kallon Aamna tayi Tace Kar dai ki Kai kanki hallaka wallahi,Mama Tace Idan taje ya kasheta ai ita ta huta da Duniya Dan wannan zai iya yiwa mutum yankan rago,Aamna ce ta kalle su Tace ba Wanda zai fada min abinda ya kamata nayi,Ni matar aure ce Kuma matarsa,sannan Ni na San dai dai sabo da Haka ba sonsa zanyi ba taimakonsa zanyi na taimaki Iyayensa idan ya shiryu shike Nan sai na barshi,Zuhra ce tayi Sallama ta shigo ta Iske zancen, Siyama tana tabe Baki tana bada labari,Zuhra tayi murmushi Tace mashaallah Alhmdllh,Ke Aamna wallahi idan Zaki so abinki ki so shi tsakanin da Allah,ba'a Wasa da zuciyar mutum musamman Daya zurfafa Haka wallahi idan kika yarda bayan kin San ba sonsa kike Yi ba wallahi Kinga yanda yake zai iya komai,mijinki ne ki so abinki ki koma ki zauna lafiya,ke da Allah ya taimakeki ma iya shaye shaye ya tsaya baya Neman Mata da sauransu,karki Raina Masa hankali baza kiji da Dadi ba na Nan gaba,kiyi amfani da ilimin.....ke dalla rufe Mana Baki banza Shashasha cewar Baba,so kike ya kashe ta,ai Ni abinda nake so yanzu ta Amince Masa Kamar gaske sai mu samu mu dinga zarar kudi a jikinsa inda ya makance a kanki Haka nasan har aikin hajji sai ya kaimu,Zuhra Tace haba Baba haba Bai kamata ba,zuwa Makkah Dole ne?, Kuna cikin rufin asiri Iyayensa sun Gama muku komai a rayuwa,Baku da Muhalli Suka Baku Muhalli,Muna cikin talauci Suka fitar damu daga wannan gashi Kuna cikin rufin asiri,ci,Sha,sutura duk kunfi karfinsu Amma Baku godewa Allah ba. Dan Ubanki wanne rufin asiri ko motar Hawa bamu mallaka ba cewar Mama,Siyama Tace ai Kar ma ta wani koma gidansa,Aamna Tace Ni dai ba Wanda zai koya min komai,Kuma bazan taba karbar kudinsa ba ku daina sa rai,Nima ba gidansa Zan koma ba,Zan dai Amince Masa Dan na canja shi na taimaki Iyayensa badan komai ba sabo da Haka kowa ya Adana kalamansa,Zuhra tace to kuwa wallahi Baki tunani ba Kuma wallahi Ni na fada Miki sai kinyi da na sani Kuma sai kinyi kuka da idonki,Karki bada kofa aci kudinsa Kuma ki so shi ki kula da mijinki Aamna meke damunki haka? Allah ya gani na Baki shawara duk Sanda kwabarki tayi ruwa karki zo inda nake,Baba yace ai ke dabba ce Zuhra,Siyama Takaici yasa ta Mike ta tattara nata ya nata Tace Idan kin tsaya ya kashe ki ke kika jiyo Nan gaba Zaki ga amfanin shawarata karki biyewa Su Baba sabo da karki fada sonsa,sannan Kuma karki dauki shawarar Zuhra,Baba yace kaga Munafuka Dan Ubanki sai munci kudinsa Kuma baza ta bi shawararki ba tamu zata bi,Kuma karki sake zuwa Mana gida algunguma,Siyama tayi waje cike da kunci,Zuhra ta mike tace Aamna a buga game lafiya Allah yasan me gaskiya,Baba yace koma dakin mijinki Dan ubanki,Aamna ta Mike Tace Ni ra'ayina zanyi ba shawarar Wanda Zan dauka,Baba yace Zaki ci Uwarki Sumayya ta lahira,dama bakin halin Ubanki kika gado Wanda ya gudu ya barki,marar gata marar cikakken asali tunda Ubanki guduwa yayi ya barki,Tambadaddiya cewar Mama. Bayan Kwana biyu Ahmad shi kadai a katafaren palonsa Yana Zaune Yana kallon wani wrestling,tun ranar da ya furtawa Aamna Bata neme shi ba shima Bai nemeta ba har kwana biyu,Wayarta ta dauka ta fito tsakar Gidan can ta baya ta Kira Ahmad,Yana Zaune yaga Kiranta ya shigo,zuciyarsa ce ta Shiga lugude Haka dai ya daga,Yana dagawa ko gaisawa basuyi ba Tace Amsarka Yes na Amince Ina sonka Nima,tana Gama fada ta kashe Wayarta cike da kunya tana ta wani murmushi ita kadai,Shi kuwa tsalle ya buga tare da Kiran Mashkoor a waya,Yana dagawa yace Tace ta Amince tana so na,Yeeee....Mun lashe zabe Mashkoor ya furta Yana kuri yace ta Isa Tace Bata sonka ita din banza,haba Fesh King irinka ai karya ne,Ahmad Yana kashe waya ya Kira su Jibson Daya bayan Daya yana fada musu Suka ce Dole ayi kamarin party yau a gidan Mashkoor karfe 10pm na dare za a fara. Mummy ya Kira tana dagawa yace Mummy ki tayani murna ta Amince tana so na,Dariya Mummy tayi yanda taji Danta ya zauce Tace na tayaka murna Ahmad,yace thanks Mum,suna gamawa ya Kira Humaira Nan ma ya fada Mata,ya Kira Mufida matar Kaninsa Sadeeq ta dinga tsalle da Murna Saddeeq Yana kallonta yace kin haukace kema ai, Saddeeq da Daddy kuwa ko kulasu baiyi ba Basu San ma me ake ciki ba sai da Mummy ta fada musu,Daddy Baki ya tabe yace wannan mahaukacin Ina zaiyi wani hankali ai Ni na hakura, Saddeeq yace wlh kuwa Daddy,Harararsa Mummy tayi sannan yayi Shuru. 10pm su Ahmad aka Sha wanka gaba dayansu ba Wanda Bai kure wanka ba aka tafi party gidan Mashkoor anan suka taru harda wasu abokan daban an gayyato su tare da Yan Mata zuka zuka,ranar Giya da kwaya taci kwal ubanta,ansha kida Wanda zasu Iya rawa sunyi har kusan Asuba Ana Abu daya. Musa kuwa ya tafi ganin gida Kauye Bai San me ake ba,Bayan komai ya lafa Ahmad baya Kiran Aamna Sam,sannan Kuma tunda ta Amince Bai je wajenta ba,sannan ya dawo da sa kana Nan kayansa kamar da,Shaye shaye ne dai dama tunda tunaninta ya sashi a gaba ya Dan rage kadan. Aamna kwana biyu taji Shuru sai Kawai Tace Bari na bashi mamaki,5pm ta fito ta Sha uban wanka cikin wani Fari da bakin material cikin na lefenta me kyau da tsada yasha uban dinki Kamar Readymade,tayi kyau kamar a sace ta,Takalminta me tsini da jaka bakake,Mama Tace Ina zuwa Haka? Karya Aamna tayi Tace gidan wani bikin kawar mu zamu je da Siyama,Baki Mama ta tabe tare da Furta shine harda uban gayu Haka idan wani ya tareki a hanya yace Yana sonki fa? Shuru Aamna tayi Tace sai na dawo tayi waje,Already me Napep din data Kira Yana jiranta a kofar gida,Shiga tayi Suka tafi,a bakin gate din gidan Ahmad aka ajiyeta Aamna ta Shiga buga gidan,me Gadi baya Nan shi yasa Ahmad Bai fito da wuri ba,taci sa'a Yana gida,Sanye cikin black jean pencil da Riga t-shirt me gajeren Hannu wata ruwan toka ta Yan birni,Yana Gadara ya fito ya Bude kofa,ai mamaki yasa ya tsaya cak,Farin ciki ya lullubeshi,yace wow...My World.....oh....ya juya Tare da tafiya yayi Yar safa da Marwa yace ya akayi Baki ce min Zaki zo?Murmushi Aamna tayi Tace Surprise...kallo ya Kare Mata tare da furta Ohhh.....kinyi kyau Beb....duk wanka nane? Aamna Tace ae Mana,Hannaye ya Bude tare da Matsawa ya rungumeta kadan yace Sannu da zuwa,Yawwa Aamna ta furta tana Jin kunya tana murmushi. Yace Feel free gidanki ne fa shigo ciki,ta na shigowa yace Yi Hakuri Bari na rufe gate duk ya rasa inda zai sa Kansa,Yana Rufewa ya dawo da sauri ya Sha gabanta Yana tafiya da baya da baya Yana cewa kece a gidan Nan yau? Kika zo wajena Kai yau kin Gama min komai My world,Dariya tayi shima yayi Dariya,Tsayawa tayi cak shima ya tsaya suna facing juna,tana Dariya Tace Ka nutsu karka Fadi,yace idan na Fadi a kanki wani Abu ne? Idan na Fadi ma Sai na tashi ai kin cancanta a Fadi a kanki,Rigarsa ya cire daga shi sai dogon wando,surarsa ta bayyana,Aamna a ranta Tace gaskiya Namiji ne,wow kalli jikinsu sumulmul,Da rigarsa yayi amfani kafin Aamna ta taka waje Sai ya share Mata hanyar da rigarsa Haka suke ta tafiya Yana cewa My World yana ta murna, Aamna tana ta dariya har Palo Suka shiga da sauri yasa rigar ya sake goge Mata saman kujera sannan yace to zauna,Zama tayi ya tsuguna a gabanta tare da daura Hannayensa saman cinyarta yace me Zan kawo Miki My world? Aamna Tace koma Mene,Alright ya Mike tare da daukan hanyar kitchen,har ya tafii sai ya dawo yace karki damu kinji yanzu zanzo,to Tace ya fada kitchen,abincin Daya dafa dazu Jullof rice ta Sha Vegetables da nama ya kawo Mata a plate tare da ruwa da lemo. Plate dinma Kalar Design dinsa shape din zuciya akayi sosai ,Zata Bude abincin yayi saurin dakatar da ita ya Bude tare da nuna Mata plate din taga shape din love ne,Dariya tayi Tace wow....gefenta ya zauna tare da tsiyaya Mata lemon da ruwa a glass cup yace oya eat,Spoon ta dauka ta ebo abincin taci taji Dadi sosai Tace wow wannan Dadi Haka,Murmushin Jin dadi yayi Yana kallonta tana ta ci da sauri da sauri sabo da ya Mata Dadi,Santi ta fara Yi Tace Kuma Kai ka dafa? ae Mana ai kin San Ina girki na Iya, Aamna Tace gaskiya ne ta ebo a spoon ta Kai bakinsa Tace kaima ci mana,ganin ita zata bashi da kanta ya Bude bakin ta zuba masa,Bakinsa ya kulle Kam tare da fadawa saman kujerar ta baya ya kwanta flat Wai zata kashe shi da love,tana ta dariya yace Hannunki zai kasheni sai abincin ya Kara wani dandano,Mikewa yayi tsaye yace Dole nayi celebration Yana zaga palon Wai duk murna ce ta bashi abinci a Baki. Sai da ta Gama ci ya kwashe kwanikan ya maida kitchen ya dawo tare da Zama a gefenta,birgeta yayi sabo da yanda ba ruwansa da jikinta ya nuna ba jikinta yake so ba ita yake so, Gaskiya Zan dawo ka koya min irin girkinka,tagumi yayi tare da zuba Mata Ido Yana ta kallonta Yana murmushi,tafin Hannunta ta saka tare da rufe fuskarta tana Dariya tana cewa Wai Mene na wannan kallon haka? Hannunsa yasa cikin slow dinsa ya cire Hannun data rufe fuskar yaci gaba da kallonta, kafadar sa ta ture gefe cike da shagwaba yace Ni ki kyale Ni na kalli abuna...,Ci gaba yayi da kallonta kamar Yana Gaban tv ya sa yatsa ya taba Hancinta,ya taba girarta,Murmushi tayi tana Wasa da yatsunta,Mikewa taga yayi Zumbur kamar zaiyi duka ya daki Center table da hannunsa yace idanba sai na kwana Ina kallonki ba kafiri nake,ta sheke da dariya,Yana tsaye a gabanta ya Dan zaga kujerar da take zaune yace kutmar an Gama kure karshen kyau,ke Zan Iya mutuwa idan na rasaki,Aamna ta Bude Baki ya Buda hannaye Yana tsaye a gabanta yace da gaske Hmmm,da sauri ya koma ya zauna ya girgiza kitsonsa,Aamna tana kallonsa Yana ta Bata Dariya,tunani ta Lula da manufar data Amince sai taji tausayinsa,Hannunta ya rike tare da Tambaya My World me yake damar min ke? Murmushi ta kakalo Tace ba komai Kawai na tuna Abu ne,Okay Amma Bai Kamata Muna tare kina tuna wani Abu ba ko? Kai ta daga Masa tare da jingina da jikinsa ta kwanta tana lumshe ido,ita dai tana mamakin su Ahmad tsafta iya tsafta duk cikinsu kowa Dan gayu ne,a ranta Tace sai Hali yazo Daya ake Abota. Bacci zakiyi ne ya tambaya? Kai kawai ta daga Masa yace ai yakamata kiyi Balance Beb ya fada da Dan karfi sabo da su maganarsu kusan basa yinta a hankali sai sunga dama ko ansha me sa Slow,Saman doguwar kujerar ya zauna tare da Mike kafafunsa sosai ya Kuma ya Bude su sannan yace to kwanta,ta baya ta kwanta sosai a jikinsa kanta Yana saman kirjinsa,Hannayensa yasa ta cikinta ya rungumeta,tana ta baza Ido taga ko ta saman Kirjinta zai rungumo hannayensa Amma Ina sai taga cikinta ya Rungume,a kunne ya rada Mata yace My world me kike so? Ba komai ta furta gaba Daya jikinta ya mutu wani Iri take ji a jikinta gaba Daya sha'awarsa take ji,ta rasa me yasa ko ya zai taba ta ko ya matso daf da ita sai taji gaba Daya hankalinta Yana Neman guduwa daga jikinta sumamman kamshinsa,shi Kuma yaki ganewa ko romancing dinta yayi,a ranta wata zuciyar Tace to Ina ruwanki da Romance dinsa ke da ba sonsa zakiyi ba canja shi kawai zakiyi. Duk da Haka kasa sukuni tayi sai mutsu mutsu takeyi,tayi mikar ta sake yin Mika Amma ina,Kara tayar Mata hankali yayi yanda yake ta Mata rada a kunne Yana cewa mene ne ko Baki da lafiya ne? Kince zakiyi bacci Kuma sai mutsu mutsu kike yi ko bakya Jin dadin kwanciyar ne? Aamna Tace ae Ni canja kwanciya zanyi,yace to a ya kike so ki kwanta Kuma? Aamna Tace Ni irin kwancinyarka zanyi ta ruf da ciki,Dariya ma ta bashi yace a jikin nawa? Ae ta furta yace to ai ko me kike so,Juyawa Aamna tayi suna facing juna sai ta lalace a kallon kyawunsa kuma,Sajensa ta taba ya matsar da Fuskarsa gefe tare da rufe Ido yace kunyarki nake ji,Badan kece kika taba sajen Nan ba My world ai da wata ce yau idan na dinga dukanta a gidan Nan sai ta Gane Allah Daya ne,kin San ba karamin raini bane mace ta tabawa namiji gemu da Aljihu,Dariya ya bawa Aamna Tace akan gemun? Yace kin San Nawa yake ci kuwa a kullum? Aamna Tace a'a yace to a bar kaza cikin gashinta kawai, tsokanarsa Aamna ta sake Yi taci gaba da tabawa tana shafawa ta ja kadan,Yace Hmmm kiyi ta yi ai yanzu kin rainani wuyanki ya Iska yanka,Su Jibson ne suka banko kofa tare da shigowa gaba Daya. Wani Kara Suka saki, Mashkoor ya koma jikin kofa ya manne a jikin Kofar ya riketa Gam Yana me Zan gani,Jibson ya murza idanuwansa yace tare da dafe kirji ya Nuna ta da Yatsa yace daga Amsar soyayya shike Nan har anzo Nan wajen? Yanzu abin har yayi nisa yazo Nan kwana Uku kacal? Baki Aamna ta bude tace Ina ruwanku Wai ba mijina bane budurwarsa ce Ni da zaku ce Iskanci mukayi? Tawaga yayi mahaukaciyar Dariya yace ke Aunty Balaraba karki zo ki lalata Mana Oganmu baya kula Mata shi,dama kin jawo ya shiga wani Hali a Kan sonki wallahi kika ci amanarsa sai mun soke ki da mashi, ki kula ba'a Wasa da mu,mun San halinku mata, Mashkoor ya galla Mata Harara yace Bamu shirya Haihuwa yanzu ba,mu ba yanzu zamu Tara Yara ba sai mun Gama inganta rayuwarmu yawwa,Aamna dama ta Saba da iya shegensu Tace matsalarku ce ta maida hankalinta Kan Ahmad,Ya kalli su Tawaga yace ku koma Daya palon Kuma idan kuka sake Mata magana anyhow zaku sani,Baku da hankali She is My Woman fa,Yi Hakuri master an daina daga yau Dariya sukayi da murmushi Suka kalli Aamna Suka ce Sannu Aunty Balaraba Allah ya Kara girma ayi Mana afuwa,Ahmad ya koma kallon Aamna suna ganin ya daina kallonsu suka dinga gallawa Aamna Harara suna Jin haushi Dan su Basu yarda da Mata ba mayaudara ne zata yaudari abokinsu,daya palon suka koma. Wurin Magrib Aamna Tace tafiya zanyi dare ya fara,Fuska ya bata Yana Zaune ya saki wani jiki Yana ta shagwaba kamar Yaron yaye ya turo Baki gaba Yana wani motsa Kansa yace Ni ban gaji da kallonki ba idan kika barni Ni kadai Zan Zama......sai ya canja muryar Yara Kuma da Waka yace Lonely....... Lonely.....oh....lonely.....Dariya Aamna keyi kamar sabon kamu,Tace kasan Mama zasu min fada fa...lokacin Mashkoor ya fito zai dakko lemo yaji abinda Aamna Tace karaf yace wannan Yafi Mama power a kanki ko a wajen Allah Shi yake da iko a kanki ba wata Mama ko Baba ba,kin Gama Raina shi Yana aurenki ki dawo gidan Mana idan gaskiya kika kulla a ranki,Ahmad ne ya cire ta kalminsa da sauri ya wulwulawa Mashkoor zai kwada Masa, Mashkoor ya goce takalmin ya Fadi a kasa,Tafiya yayi da Niyyar cin uban Mashkoor Amma Mashkoor ya gudu wancan palon,Tsaki Yaja yace yi Hakuri muje na ajiyeki a gida to. Machine dinsa ya hau Aamna ta Haye itama ya fisgeta Suka tafi,a Kofar gida ya sauke ta sannan ya koma gida. Da masifa ya Shiga wajen su Mashkoor yace wallahi idan Naga Wanda ya sake Yiwa My woman magana sai naci ubanku,iskancin banza, Mashkoor yace kayi hankali baka San Mata ba,idan Aunty Balaraba gaskiya ta kulla a ranta ta dawo gidanka Mana kuyi rayuwar aure,Taya zata tafi Kuma Tace tana sonka Taki dawowa inda kake, wallahi kabi a hankali mata Basu da Imani Tam,Ahmad Tsaki ya ja yace Ni ance maka Zan Mata Dole ne idan tana so da kanta zata dawo ka daina damunta,Tawaga yace shike Nan mun kyale ku yanzu Abinda ya kawo mu Baban Mubaraq Brown ne ya kawo mu. Ahmad yace me ya faru Yana kallon Mubaraq,Mubaraq Brown da Muryarsa ta Yan kwaya yace Guys jiya Ina Shiga gida Wai na kure Hajiyanmu ta kulle kanta a daki tana ta Rusa kuka kaiii...abin fa ya caja min Kai,nace Hajiya me ya faru Tace ai tsohon Nan ne zai Mata kishiya,Tawaga ya daki Cinyar Ahmad yace abin haushin My Guy wata bazawara ce mijinta ya mutu ya barta da Yara biyar,Wai gaba Daya zai dakko ta ya aure ta da Yaran,Ahmad yace Uhm da ace ta daina Haihuwa to da sai muce yayi taimako ya tallafi marayu,ya kamata dama a dinga kula da marayu Ana samun masu Hali suna daukan nauyi kaga da an rage masifu,Jibson yace Kai Bari masu kudi sun daina taimako tunda Ummati ta rasu kwananta ashirin yau babu Wanda ya tallafamin da ko Sabulun wanki sai ku abokaina,Brown yace Dan Allah a duba matsalata,Sukayi Dariya Tawaga yace kaga a hasashe idan Ya auri me Yara biyar ta taho da su gidanku kaima Babanka idan da tsawon Rai a hannunsa zata haifi Kamar biyar ko shida kaga a lissafi Shida ga biyar Sha Daya kenan,Brown ya dura Ashar yace a Tara da mu Yaran Hajiya Guda tara,Ashirin cib cib cewar Jibson,Suka sheke da dariya. Ahmad yace kaga ko zaben Shugaban kasa kuka fito iya gidanku sai ku kayar da Jam'iya Guda ko kusa Jam'iya ta lashe zabe,Dariya Suka dinga yi, Mashkoor yace idan a Iya shida Amaryar ta tsaya kenan ai yanzu Mata sun daina wata Tara kafin su Haihu,Ahmad yace Musamman idan da Abinci kaga idan zaka bawa Mace abinci taci ta koshi ta samu nutsuwa ai wallahi duk buga kwallo sai cikin raga,Jibson yace sai dai kaji a goalll.....idan ka sake ma duk kwallo Daya a biyu ko Uku take Yan Uku Yan biyu za ayi ta zubo maka,Suka kyalkyale da Dariya, Mashkoor yace kutmar dosan Uwa idan aka sake kayiwa matarka family planning na shekara Hudu Dan karta Haihu idan Allah yaga dama sai ka Gama tsarinka sai tazo Karo maka Yara cikin farko ta Haifo maka Yan Uku ko Yan hudu ko Yan biyu ta maka Yan biyu sau uku a jere,kaga shekarun da Bata Haihu ba Ashe Tara maka yaranka akayi Hhhhhhh suka sake sakin Dariya.. Ahmad yace wallahi ta sake ta Haifo Yan hudu har abada ita da Haihuwa ko dai ta tsaya ayi planning na kirki ko tayi gidan ubanta,Tawaga yace gaba Daya tsoron aure nakeyi sabo da wannan,Ina son Mata Amma ko Dan wannan jarabar Haihuwar tasu Daya ta ishe Ni,sabo da kowacce sai ta zube nata,idan kana da kudi ma Mata ma har gasar Haihuwa sukeyi sabo da aci gado in ka mutu, Mashkoor yace Kai Sarki Kaine zaka iya korar Aunty Balaraba Dan Tace zata Haihu? Inda ka susuce me zaka iya ai sai abinda taga Dama,Ahmad yace to sai na dinga amfani da Condom ba shike Nan ba,fashewa wani yakeyi cewar Jibson,Ahmad yace to idan baza tayi planning dinba Ni sai naje ayi min a kashe kwayoyin Halittar yaran Dan Uwatasu kaga inta buga kwallo ba cin ball na dawo Dan Arsenal kawai kwallo ba ci gaba,Suka dinga dariya. Ahmad yace Amma yanzu a kiyayi Mata ba irin Iyayenmu bane na da,Indai mace zata samu shinkafa taci ta koshi,ga dankalin turawa,ga nama,doya...kaga doya ka guji bawa matarka doya naji ance tana sawa a dinga haifar 'Yan biyu 'yan Uku,Hhhhhh Suka sake sakin Dariya Ahmad yaci gaba da cewa ku daina Dariya gaskiya ne,yawan Shan Madara,da jarabar kwadayin mata su dinga girke girke to yanzu Mata sun daina wata Tara dauke da ciki ai wata shida shida suke Haihuwa yanzu,shekara Biyu Yara uku,Brown yace Ni yanzu a dawo wajen Baffa na,Ahmad yace ai Babansa Yana da Rai,Brown yace kwarai Ina da kaka a raye,gaskiya Kai Dan gata ne har wani Kaka ne da Kai Bai mutu ba? Bash ya tambaya,Ahmad yace wajen kakan zamuje lallai a dakatar da auren Nan yaran sun Isa,idan sunki yarda sai mu koma Kan bazawarar Baffa a cikinmu wani zai shigar Kamala mu dinga zuwa zance wajenta. Kaga zata ga yaro sabon jini me zatayi da tsoho shike Nan ta daina son Baffa,Dariya Suka Yi harda ihu, Mashkoor yace King Ni za a Bawa wannan fannin,Ahmad yace no Jibson ne zaiyi kaga Jibson shi a cikinmu dama Yana kula Yan Mata Sarkin yaudara ne, Jibson yace ai wallahi na yaudari Mata sunfi dari Kuma abin haushin duk Wanda na yaudara ban taba samu nayi ko Sex da su ba,a duniya sau Biyu nasan na taba Sex da wata guntuwar yarinya me Kama da kofin shayi Me Hannu,King yace ku kyale ma wani Kakan Brown baza su yarda da mu ba, Kawai mu fara Shirin zuwa wajen Bazawara,Kai Brown ka Nemo Address din gidansu da sunanta. Brown yace naji kanne na suna cewa sunanta Sameera,Tawaga yace kwanon cin abinci kenan Sameera fa tab,Bash yace daga yau sunanta kwano babu wani Sameera kwano kawai,suka tafa. Tunda Aamna ta koma gida ta kasa sukuni Kawai Ahmad take tunani da Kuma sha'awarsa Tace yanzu ko Dan Romance Haka akeyi,yanzu saurayi da Budurwa ma basa zance su tashi lafiya mazan yanzu sai Allah ya shirya,Amma Miji Guda na kwanta a jikinsa na tashi wani garau da shi Anya Ni mace ce kuwa,Wata zuciyar ce Tace to Mene yaje da jikinsa,tana wannan tunanin bacci ya kwashe ta,Washe gari da Sassafe Ahmad ya Kira Aamna tana dagawa ko gaisawa Bai Bari sunyi ba ya marairaice tare da furta Dan Allah nazo na ganki yanzu? Ba Zama zanyi ba Kawai bakin gate Zaki leko Dana ganki Zan wuce to sai kazo ta furta tare da mikewa da sauri ta fada wanka a gurguje ta shirya cikin wata silk Yellow and red doguwar rigar material,Powder ta shafa da lipgloss ta fesa turaruka duk Dan a birge shi,Mayafi red ta yafa sai gashi ya kirata a waya yace fito na zo,da sauri ta fito Mama da Baba sai gani sukayi tayi waje da sauri ko kulasu Bata Yi ba tana ta kamshi,da Murmushi ta fito,ya kalleta sosai ya sake leka fuskarta Yana zuba murmushi yace kwalliya kika Yi min? A'a dama nayi abata cewar Aamna da karya,Yace Ina Zaki je to? Tace dama Hospital nake so ka kaini,Me ya faru da ke ya furta a tsorace Tace wata takarda Zan karbo,Yace to kin shirya Tace ae yace hau mu tafi,kafadarsa ta dafa sannan ta hau suka tafi. Suna zuwa da Mamaki sai Aamna ta ja Ahmad Office din Doctor Tace Likita gamu a rubuta Mana Tests din da zamuyi na medical checkup,Ina so cikin Nan nasa ta nuna cikin Ahmad Tace a Bincike min shi sosai,koda,hanta,Huhu da sauransu duk a tabbatar min da lafiyarsu,Haka jininsa ma ko Ina a Masa test,Dan kar yaji Haushi Tace harda Ni Nima ayi Mana tare,Doctor yace to Nan take ya rubuta musu tests ya turasu Lab,Ahmad baiji komai ba tunda tana so Bai San manufarta ba sai ya bita Suka je aka ja jininsu sannan aka musu scanning ko Ina Kamar yanda Aamna ta bukata,Dake private ne Nan take Likita yace ku jira Kawai result ya fito ku tafi da abinku,Zama sukayi Ahmad yana rike da Hannunta,kudin ma shi ya biya komai,sai wurin Bayan 12pm aka ce suje su karbi Result ya fito,Suna karba Suka shiga Office din Likita Suka zauna,Likita ya fara Bude na Ahmad ya Gama duba kowanne yace Kaga Kai Alhmdllh Allah ya taimakeka lafiyarka kalau,komai naka Normal ne baka da wata matsala gaskiya,Yace gashi Genotype dinka AA ne shima,Ahmad yace na sani ai Ni Ina ganin Likita duk shekara Ana duba Ni,Aamna taji kunyar abinda tayi zarginta shaye shaye ya Gama illata Ahmad,Ahmad cikin kuri ya bigi table din likita yace Doctor duba Mana nata mu gani Kuma mutum idan ba lafiyayye bane yaci ubansa a Nan wajen, Doctor ya dinga dariya shi da Aamna Wato da Aamna yake kenan. Doctor ya bude na Aamna yana dubawa yace Alhmdllh kema lafiya kike Amma kina da matsalar Cold Bladder sanyin mafitsara Wanda Infection ne ya haddasa,Maganin ciwon Sanyi Za'a rubuta Miki Kuma sai kin dage kafin ya warke,sai Genotype dinki AS ce ke Wato carrier,Kinga Allah ya taimakeki mijinki AA ne baza ku haifi me Sickler ba Kun tsallake rijiya da baya, Doctor yace Kai kana mijinta ya akayi sanyin be Kamaka ba? Ahmad yace Amarya ce fa ai Bata tare ba,Gidan ne ba a karasa hadawa ba shi yasa nace tayi zamanta a gidansu sai an Gama,Kuma ka Iya Hakuri? Ahmad yace ae Mana Kuma kullum sai naje zance,yanzu ba gashi hakurina ya taimakeni ba da yanzu ta shafa min asosa,Dariya Aamna tayi Tace zaka ga Asosa wallahi. Likita dai maganunguna ya rubuta Mata masu zafi,Ahmad suka je aka siya, Allura za a Mata ta kwana biyar,yau za ayi Daya Kamar zatayi kuka,Ahmad ne ya riketa Kam aka Mata a Hannu,Aamna harda kukan shagwaba na ganin Miji na kusa, Suna Hanya a machine yace Wai ke Baki da kawayen kirki ne sai wannan banzar Siyaman? Aamna Tace ai Siyama bani da kamarta ita take dorani a hanya me kyau,Take doraki a keken bera dai wannan ce ta kirkin? Fushi Aamna ta fara Wai ya tsani kawarta. Lokacin suna zuwa kusa da wani masallaci anyi Kiran Sallah,Aamna Tace tsaya kayi Sallah a jam'i,tunda tana so sai ya tsaya a masallacin sai ya tsaya, tana waje ya Shiga ciki a Jam'i yayi Sallah yau,Yana Fitowa tana ta murna,Hararta ya Yi yace Sallah 12:30pm Bata Nuna ba,Kin jawo Nayi Sallah tun tana Danya sharaf,Aamna Dariya tayi Suka tafi ya ajiyeta a gida Yana ta Fushi. Zai tafi ta tsaya Tace ba ko Sallama? Kansa ya dauke ya kalli can gefe,zuwa tayi da sauri tana Dariya ta riko Hannunsa,Idonsa ya rumtse sabo da har kwakwalwarsa yaji wani yarrrrr, Kiss ta manna Masa a Bayan hannun Tace I love you,da sauri ya kalleta yace da gaske? Kai ta daga Masa tana murmushi,Sakkowa yayi daga machine tare da rungumeta yace I love you too,a kunne ta rada Masa idan anyi Kiran sallar la'asar kaje masallaci Kuma ka Dan zauna kaji Wa'azin liman Naga masallacin kusa da gidanka Ana wa'azi bayan Sallar la'asar,Ahmad Bai kulata ba ya hau Machine ya tafi gida. Zaune suke a gidan Ahmad,Tawaga,Jibson,Bash da Mashkoor,Kiran Sallah aka kwalla,Ahmad ya mike zumbur yace My world Tace naje sallah yau,Kirji Tawaga ya dafe Yana zuka Wiwi yace what....me zanji? Sallah ka manta mu Bama Sallah sai ta Nuna ligigif? Dariya Mashkoor yayi yace ai kwana Nan za a bashi limancin masallacin Unguwar, ku tashi muje muje ai muma ba arna bane Dan uwarka King cewar Bash. Tafiya suka Yi tare gaba dayansu,Gaf da za a Tada Sallah sukayi Alwala sai kallonsu akeyi sabo da kitson Ahmad da gyaran gashin su Jibson kadai abin kallo ne,Ahmad ne kadai da Yar tsangalalliyar jallabiya fara Amma duk cikinsu daga me 3qtr sai me Creazy jean,sai dai kana gani kasan ba kazamai bane Yan iskan Yan gayu ne Kawai jikinsu suna kashe Masa kudi,Limamin Unguwar yasan su musamman Ahmad Bai taba ganinsu a masallaci ba sai yau Kuma Suka hau sahun gaba shu'umai,. Bayan anyi Sallah an idar masu Zama Jin wa'azi Suka zauna har su Ahmad,Yau sai liman ya fara wa'azi akan Karin aure,ko wanne Namiji yayi kokari ya Kara aure,Ahmad ya kunna recording a wayarsa ya ajiyewa Aamna tunda itace Tace yaji wa'azi Kuma yayi Aiki da shi gashi ya fara da Jin falalar Kara aure mutum ya auri mace sama da Daya. Malam yace idan Namiji Yana talauci zai iya Kara aure Allah zai Iya Buda Masa sanadiyar wannan auren,Tawaga ne ya daga yatsa Sama yace Ina da tambaya Malam,Malam ganin irinsu Nan take yace Ina jinka samari,Tawaga yace cikin darajaka da kankan da Kai tare da mutuntuwa Malam karya kakeyi. Baki Malam ya bude ya kallesu Jibson yace kwarai kuwa katuwar karya ma,cikin Yaran Malam wasu Suka Mike da Niyyar tarewa Malam,Malam ya dakatar dasu tare da kallon Tawaga yace Kai bani hujjarka da kace ba Haka bane,ka daina gyarawa wani ba Haka bane Kawai karyace malam,ba hadisi ko Aya na karyata ba Kawai abinda ke faruwa,Babana kafin ya mutu talaka ne Haka Kawai karambani yasa ya Karo aure ai kuwa talaucinsa ya karu,Gomnati Watarana ta bada tallafin dubu dari ai sai Baba ya sake Karo ta Uku da kudin talauci ya sake dannowa gidanmu karshe wahala ce ta Kori matan biyu aka bar Mamata yanzu Yaran suna Nan rututu shi Kuma ya rasu an bar min nauyi sannan kace wani Ana samun Budi,ga mutane Nan yanzu da yawa ko mace Daya ya aura sai kaga duk ya fara lalacewa wahala ta isheshi yana dana sani. Jibson yace ance Wai Malam ko matashi Niyyar aure yayi Allah zai Buda Masa ya kawo Masa yanda zaiyi yayi auren? to Ni Malam Niyyar aure nayi shi yafi sau dubu sannan yanzu zancen da nake maka Zuciyata a kudurce take da Niyyar aure Amma kwandala bana samu abokaina su suke daukan nauyi na sannan kazo wani kace,Bash yace Kai Malam yanzu ba irin da bane rayuwar yanzu daban take ku San abinda Zaku dinga fada,wancan satin naji wani malamin yace idan matashi baida aikinyi Kar ya sake yayi Aure sabo da rayuwar yanzu,Haka Rannan wani yace Mata Kar su sake su auri mara sana'a,yanzu Kai Kuma kace ayi sama da biyu,Ahmad yace da Allah ku dinga duba littatafai sosai kafin ku fadawa jama'a wani abu,Ya za a dinga zuwa Ana Raina Mana hankali mun rasa inda kuka dosa wannan yace kaza wannan yazo ya karyata. Malam ya kalle su yayi Dariya yace Dana fara Wa'azin ai sai ku Bari na Kai Aya,da sai ku tsaya bayan na Gama fadar falala ai zanzo nayi bayani akan Kuma wannan matsalar da kuka ambata Amma sai kuka rigani,Dariya Tawaga yayi yace karka zo Mana da gyara Malam Kawai mun kureka ka zugo ta yawwa,Kai ku tashi mu tafi Sallah Kuma da Muka bika Allah ya baka ladan Jan Sallah Amma wa'azinka 0/0 baka ci ba,Suka Mike suka fice. Liman sallamar mutane yayi yace gobe zai Dora daga inda ya tsaya ya fita da sauri,Liman hamshakin me kudi ne Dan kasuwa ne na gaske,Su Ahmad ya dakatar a wajen masallaci suna tafiya,Tsayawa sukayi Liman yace cikinku duk ba me aure?Ahmad yace Ni ina da shi Amarya ce Bata tare ba Amma ta kusa,Yace mashaallah ai Kai na sanka a garin Nan har mahaifinka na sani,Ahmad ya tabe Baki,Jibson ya kalla yace Kaine kace kayi Niyyar yin aure baka ga Budi ba ko? Jibson yace kwarai kuwa,Liman yace to kaje ka Nemo yarinya Ni Kuma na tsaya maka har gidan Zama kyauta Zan baka aikinyi me tsoka Kuma Zan maka komai na auren,Jibson yace Malam karfa ka min Alkawarin Yan siyasa baza kaji da kyau ba,Malam yayi Murmushi sabo da yasan Basu San shi waye ba,Karfa ka bashi gida irin na talakawa talak idan irinsa ne ka rike abinka Bamu shirya aure ba sabo mu mun tsara Dole matanmu suji dadin duniya shi yasa Muka hakura da Aure muna talauci jira mukeyi sai munyi kudi cewar Mashkoor,Bash yace yawwa kaji dai Malam,Malam yace cikinku ma idan akwai Wanda yayi Niyya ya fada,Tawaga yace Marayu kannena sun ishe Ni ma Ina Ni Ina aure banyi Niyya ba, Mashkoor yace Ni kuwa Muna da Hali ra'ayi ne banyi ba,Banga wacce ta min ba,Malam yace Ina da Yara kaje ka gani idan da wacce ta maka a ciki, Mashkoor yace rabani da Yar malamai tazo tayi ta zunduma min Hijab a gida,idan nayi magana ta jawo Aya gwara wacce ta rike izu biyu na Sallah Yar jahila jahila Haka,Dariya suka bawa Malam yace duk Sanda ka shirya kazo ka gani dai, Mashkoor yace bafa zanzo zance gurin yarka ba ta malamai Dan Hannu bazan rike Mata bare Yar runguma a fara min wa'azi ai sai anyi aure etc bazan zo ba,Bash yace Ni ka ganni Malam a ministry of Environment nake Aiki Ina samu,Kuma Iyayensa ma duk ma'aikata ne Kawai Ni sai fara doguwa,idan ba fara ba taje,Malam yace idan Allah yasa kuma ka fada son bakar fa? Yace sai tayi bleaching Dole na siyo Mata mayamayai ta koma fara,Dariya Malam yayi yace Kai Dole sai fara? Bash yace ko bamagujiya ko arniya Matukar fara ce an Gama,ko a gidan karuwai take ba ruwana,Ni dama Malam ban damu da wata mace Virgin ba,Nafi son wacce ta San komai yawwa,Ni mace taje da Virginity nata ba ruwana,Kuma Ni ban taba Zina ba Kawai Ni Ba ruwana da wani virginity. Malam ya kallesu Kawai ya zaro check na kudi,ya rubuta dubu dari uku ya bawa Tawaga yace gashi kaje ka kula da marayu idan wani Abu ya taso na iliminsu ko auren wata ko wani Abu ka sanar Dani Zan tallafa,Tawaga ya karba da mamaki ya dafa Ahmad yace Malam sai kace wannan Abokin Nawa king shi yake mana irin wannan kyaututtuka,Malam ya kalli Ahmad da mamaki Ashe Yana da tausayi,Kudi ya zaro ya Basu dubu goma goma kyauta har Ahmad ya mikawa,Jibson ya kyaftawa Ahmad Ido Wai ya karba sai ya Basu su Kara,Ahmad ya karba,Tawaga Dake tura machine dinsa ai sai ya buga machine tare da zanawa Malam kwabo a gabansa,Jibson yace karya ne wani ya kawo ma raini a garin Nan,Maganar dazu daka fada a masallaci Muka karyata ka yanzu mun gano gaskiya ce,Wuhuhu Mashkoor ya daga hannaye sama Yana jinjinawa Malam,Bash yace sai kayi Malam mun baka Shugaban limamai na Nigeria wallahi,Malam dai Kai ya girgiza Kawai tare da komawa masallaci inda motocinsa suke na Alfarma. Ahmad kuwa Jibson ya bawa nasa 10k din yace ungo ka siyawa su Aymana littafan makaranta naji sun maka waya ance a siyo musu Books yace wallahi ga naji sunce gobe ma za a koresu daga school sabo kudin makaranta Abba Mutum biyu ya biyawa saura su takwas kowanne dubu goma Sha biyu,ga Jamila zasu Zana waec, Kuma Dan Iskanci baka fada ba? cewar Mashkoor, suna komawa gida Ahmad ya turawa Jibson dubu dari da Hamsim, Mashkoor ya bada dubu talatin,Shima Bash ya bawa Jibson 20k ,Tawaga yace kudin sun Isa da za abiya ko da Kari sai a ciri wani Abu a Nawa,Jibson yace ai sunyi yawa ma ciki har sai na siya musu taliya da macaroni dama sun Kare,tausayin Abba nakeji duk ya rame. Ahmad yace yayi rashin Ummati ba Dole ba,Jibson yace sai na ganshi a Dan dakinsa yayi malahooo....yayi tagumi bashi da kawar Hira sai dai idan mun shiga ko su Aymana suje su tayashi Hira,Amma lokacin da Ummati tana da Rai sai dai kaji dariyarsu kyalkyalkyal,Ahmad yace muje mu samo Masa Dattijuwa wacce ta daina Haihuwa mu aura Masa ita ya rage zafi. Mashkoor yace mu samo Masa me kyau mu siya Mata kayan gyara ta dinga birge shi irin Ummati suka Kama Dariya tare da cewa Haka za ayi,ga case din Brown gobe za a fara Suka fara shirya plan abinsu,Jibson yaje aka canja Masa salon Aski me kyau na Dan Kamala Amma fa Sumar akwai yawa ta matasan yanzu,Sajensa da gemunsa yasha gyara dama gashi wani chocolate kyakyawan matashi,Kaya kuwa Shadda sababbi aka dinka Kala biyar za a hurewa Bazawarar Baffan Brown kunne,Shi kuwa Bash Searching yake na inda za a samowa Baban Jibson Bazawara me Dan kwari. Tun safe Aamna ta fara amfani da Magungunan Infection dinta,ciwon yaji magani da Allura ya tabo shi sai ta fara Jin kaikayi a gabanta,dama Likita yace idan ta fara Sha zata ji sabo da an tabo ciwon,Sanye take cikin wata Riga karama me Hannun Vest fara da tight baki,Ahmad ya Mata waya zaizo da dare zai Bata labarin Wa'azin da Tace ya zauna ya ji,Bata Yi zaton cikin gidan zai shigo ba,sai Jin sallamarsa tayi a palonsu,Mama ya gaisar ta amsa sama sama Amma ganinsa dauke da ledojin take away sai ta washe Baki harda cewa shiga mutuniyar taka tana ciki, ai kuwa ya wuce bedroom din Aamna,Mama sai kallo sai Harara baza su iya komai ba dama,Aamna sai soshe soshe takeyi duk ta rasa sukuni. Yana shigowa ta janye Hannunta da sauri Amma ya rigada ya gani,Dariya ce ta kwace masa yace ai sai ki fada min nazo na tayaki,Kuka ta saki masa yace yanzu zanzo na tayaki kwantar da hankalinki. Ba kinyi zaton nine ba lafiyayye ba to gashi reshe ya juye da mujiya,Kuma yau Hira zamu Sha babu soshe soshe,Aamna ta goge Hawayenta tana Dariya Tace Allah baka Isa ba ka tafi gaskiya,Amma Kuma gaskiya yasha kyau cikin wani yadi brown me azabar kyau sai kamshi yake zubawa,Tana kwance Bata tashi ba,Saman bed din ya haura tare da kwanciya shima,Tace ka rufe Kofar da key kasan Mama Kar ta shigo,ai ba Wani Abu zanyi ba Dan Kawai na kwanta mene a ciki ya furta tare da gyara kwanciyarsa. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels