An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels Garkuwa📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 11:56 Am TUESDAY OCTOBER 20. *GARKUWA* PAGE 1 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *Littafi na ɗaya. Shafi na forko!* Free page *Gargaɗi! Gargaɗi!! Gargaɗi!!! Ban yardaba! ban Amince ba! ban lamunceba! A juya min labarin LITTAFINA tako wacce sigar bana so ban bada damaba in kana buƙata akwai number ta a jiki ki\ka nemi izinina a kiyaye domin zama lafiya yafi zama ɗan sarki! In kunne yaji gaggan jiki ya tsira. Kuma hanyar lafiya a bita da shera yafi, wannan littafin haƙin mallakarsa nawane Aysha Aliyu Garkuwa!.* Bismillahirahamanirahim Ina mai farawa da sunan Allah mai rahama mai jinƙai mai komi mai komai. Ina gode Allah daya bani aron rai da lafiya da nitsuwa da konciyar hankali ya bani damar fara wannan littafinawa mai suna GARKUWA. Ya Allah ina roƙonka ka tsare min tunanina da hannuna ka tsare min al'ƙalamina daga rubuta shari da duk wani abu da zai zamo guba ko masifa a rayuwar al'ummar Annabi, ya Allah ka bani ikon rubuta al'khairi da abinda zai zamewa al'ummar Annabi dan al'farma Annabi da Alqur'ani mai tsarki, ya Allah ka bani rai da lafiya dani da masu karatu ka nuna mana ƙarshen littafin nan lafiya kamar yadda ka nuna mana forkonsa lafiya, Amin ya rabbil izzati... *LITTAFINA NA KUƊI NE, BIYA ƊARINKI UKU KACAL DOMIN SAMUN DAMAR KARANTASHI BA TARE DA HAƘƘIN KOWA A KANKIBA, AKWAI SP GROUP SHI KUWA 1K PASTING NASU YAFI NA ƳAN 300 YAWA, TURO ƊARI UKU TA ASUSUNA 0005388578 JAIZ BANK AISHA ALIYU GARKUWA, SAI KI TURO SHAIDAR BIYANKI DA WANNAN NUMBER TAWA 09097853276, ƳAN SPECIAL GROUP BANA SON KATI, GA POS BURJIK A GARI, KUMA YAN 300 IN DAI KINADA DAMA DAN ALLAH YIMIN TRANSFER TA AC YAFI, AMMAN IN YA ZAMA DOLE BA MATSALA TURO KATIN MTN NA ƊARI UKUN, KANA BA HOTON KATIN ZAKIYI KI TURO MINBA, A A NUMBERS ƊIN ZAKI RUBUCE KU TURO MIN* Dan girman Allah da Manzonsa. masu tambayata tsoffin littatafaina ku daina bana so. Ku nema a cikin groups zaku samu, in dai ba Hukuncin Allah ko NAKASA BA KASAWA BACE, da GARKUWA kada ku tambayeni in kuna ƙaunar Allah, in kuwa bakya ƙaunar Allah to tambayeni. *YAHUNDE! Babban birnin ƙasar Cameroon.* Cikin wani kekyawan rugar FULANI mai tarin al'barkatun duniya. Kota wani sashi Allah yayiwa Rugar Arɗo Babayo, ni'imomi na musamman, makiyaye ne cikakkun Fulanin ƙasar Cameroon. Ranar wata jumma da yammaci la'asar sakaliya, makiyaya nata dawowa gida yayinda kota ina. Shanu tumaki raƙuma awaki zabbi keta kai komo ko wanne na nufar garken ma-mallakinshi domin ko dabba tasan uban gijiyinta, Garken Arɗo Babayo yana ɗaya daga cikin garken da babu kamarsa a nahiyar Afirka baki ɗaya, Yanada MAKIYAYA a ƙala mutun arba'in. Garin ya fara duhuwar sanire alamun yanayin sanyin damina da ake ciki ko ina yayi kore shar ga tarin tsirrai kana ga igiyar ruwa da yayiwa rugar Babayo ƙawanya, Wasu dattawane a zaune bisa ƙarƙashin bishiyar ceɗiya dake ƙofar gidan Arɗo babayo Farin dottijon ne mai cikar zarra da mutun taka ke zaune a tsakiyarsu, kana sai wasu manyan mutane dake zagaye dashi. A gefen damanshi kuwa wani Babban mutun ne mai cikar zarra da wadatar zuciya ga tarin alamomin mutuntaka da cikar imani da haiba, bisa dukkan alamu tattaunawa sukeyi kan abinda ya shafi rayuwarsu. Da sauri Arɗo Babayo ya ɗago kanshi ido ya zubawa sashin damanshi, inda ya hango wasu ƴan saffa-saffan samari guda huɗu suna biye da ƙatuwar suntsuwar Boleru babban cikinsu ne a gaba wanda zai kai shekaru 15 sa mai binsa wanda zai kai shekaru 13 sai mai bin masa da zai kai shekaru 11 kana sai ƙaramin cikinsu da bazai gaza shara 9 ba, gudu sukeyi sosai da iya ƙarfinsu sun tasa tsuntsuwar Boleru nan a gaba wacce ta kasa firewa sai gudu takeyi da sawunta biyu, bisa dukkan alamu tsuntsuwar tanada tsohon ciki mai girma. Gudun da takeyi gudune na ceton rai. Arɗon Babayo daya buɗe baki kenan da nufin zaiyi magana sai kuma ya juyo ya kalli kekyawar yarinya ƴar kimanin shekaru 8 a duniya wacce take kan cinyar mutumin nan dake gefen damanshi. Ta miƙe da sauri cikin tsananin azama da harshen fillanci da ƙarfi tace. ("Acce mo) Ku barta". Sai kuma ta juyo ta fuskanci mutumin da take zaune kan cinyarshi cikin kaɗuwa da firgici da alamun tsananin tausayawa tace. ("Appa a vi'a ɓe acca tokkugomo nɓe naunanmo) Appa kace su dena binta zasuji mata ciwofa". Murmushi Arɗo Babayo yayi tare da cewa. "Kai Gainako ku barta zaku kamata a hankali ai". Da sauri wanda aka kira da Gainako yace. "Baffa Giɗaɗo ne yace mu kama mishi ita mu yanka mishi". Da sauri suka juyo kan ƴarinyar jin wani irin ihu da tai tare da cewa. "Ku yankata kuma, Appa kajifa wai zasu yankata, wayyo Appa kace musu kar su yankata, gashifa tanata kuka gashi sun sa taji ciwo a hannunta yanata zunda jini". Da mamaki suke kallon ƴarinyar sabida furucinta na wai hannunta yaji ciwo yana zubda jini, ina tsunstsuwar Boleru ina hannu?. Wanda ta kira da Appa ne ya jawota gabanshi tare da cewa. "Parvina tsuntsu kuma tanada hannune?." Da sauri ta miƙe tare da ɗaga murya tace. "Ba tsuntsu bane Appa wlh mutunce gata nan da ciki gashi ma tana kuka tana-ta kare cikin jikinta". Cikin mamaki suka zubawa tsuntsuwar Boleru ido su dai Allah ya gani gaba ɗayansu tsuntsuwa suke gani tana guduwa da kyar wanda kuma kowa ya ganta yasan tanada tsohon cikine. Giɗaɗo ne wanda shine ƙarami yaron ɗan shakara 9 kuka yasa tare da cewa. "Wayyo ya Gainako kayi sauri ka kamo min ita karta gudu". jin haka yasa ƴarinyar nan da aka kira da Parvina ta miƙe da gudu tabi bayansu tana gudu tana kuka wanda har ga Allah daga cikin zuciyarta yake fitowa kuma ita ba tsunstsuwar Boleru take ganiba a zahiri a fili da kuma baɗinin Allah ya nuna mata mutum take gani kekyawar mace mai cikar sura da kamala kana ga ƙaton cikin dake jikinta wanda haihuwa yau ko gobe. Ihu takeyi tana binsu tana cewa. "Dan Allah ku barta zataji ciwo Wayyo Appa kazo mu ceceta zasu kasheta." Ihu tasa da dukkanin ƙarfinta tana yarfa hannu cikin gigita take kurma ihu lokacin da su Gainako suka isa kan tsuntsuwar Boleru suka danne fikafikinta suka kama suka medata baya. Ihun da tayine yasa gaba ɗaya dattawan nan suka miƙe tsaye suka biyosu a guje dan ihun nata ya cika illahirin rugar babu wanda zaice baiji ƙaranta ba dan saida tsaunuka da kogin da suke gaɓarsu ya amsa da sautinda da take cewa. "Wayyoooooooo! Appaaaaaa! zasu kasheta, sun karya mata hannu". A gigice suka ƙaraso wurin wanda ganin yadda take a gigice yasa Appa kamata da sauri, yayinda ita kuwa taketa son zillewa tana fiffizgewa daga hannunshi, Arɗo Babayo kuwa tsawa ya dannawa Gainako tare da cewa. "Kai! Kai!! Kai!!! Gainako sake tsunstsuwar nan saketa". cikin sanyi Gainako ya sake tsunstsuwar, daga tsaye ta faɗi ƙasa hakan yasa, Parvina sake saka ihu da ƙarfi ta fizge ta nufi kan tsuntsuwar da ita mace take gani kuma sanadin saketa da akayi daga sama ta faɗi ƙasa a kife yasa cikinta buguwa wanda yayi sanadin a take naƙuda ya fara murɗarta kana ga jini daya fara bin sawunta. Tana isa gaban tsuntsuwar tasa hannunta ta kamo hannun baiwar Allah nan da ita kadai Allah ya bawa damar ganin a mutun ba tsunstsuwar Boleru ba, hannunta data riƙo su kuma kab mutanen wurin gani suke fiffigen tsunstsuwar ta riƙo. Cikin kuka take shafa kan kurciya a ganinsu yayinda ita kuwa hawayen fuskar matar da take ganin take sharewa cikin muryar kuka tace. "Sannu sunji miki ciwoko, kice musu ke ba tsunstsuwa bace ki gaya musu ke mutunce kamarsu ki gaya musu kema bani adam ce karsu yankaki". Kuka ta kuma fashewa dashi ganin matar nan bata magana sai dai hannunta data riƙo ɗin ta ganshi tamkar robo wato alamun hannun a karye yake, cikin sauri ta sake hannun tare da cewa. "Appa mu tafi da ita mu kaita wurin masu gyaran ƙashi". To al'amarin parvina fa ya fara zarta zaton mai zato ya fara shallake tunanin mai tunani abin ya girmi shekarun Dattijannan. Shi kuwa Giɗaɗo kuka ya fashe dashi tare da nufarta yana mai cewa. "Ki bani tsunstsuwata ai tawace nine nayi ta renonta kullum tare muke cin abinci tare komai duk abinda naci sai na barmata dan tayi ƙatuwa, kuma yanzu kice baza a yanka min itaba". faɗawa tayi jikin matar wanda su a ganinsu ruggume tsuntsuwar tayi ita kuwa parvina cikin kuka ta juyo ta kalli Giɗaɗo tare da cewa. "Kai mayene ko? To Wlh bazan baku itaba in dai ina raye a duniya bazan bari a cutar da itaba, babu wanda zai kasheta a gabana sai dai in bana raye ku bar ce mata tsuntsuwa wallahi tallahi mutunce kamar kowa". Kiran sallan magriba da akayine yasa ɗaya daga cikin dottijon mai suna Yayari yace. "Arɗon Babayo lokacin salla yayi". Sai ya kuma kalli Giɗaɗo da Gainako da Seyoji da Ja'eh yace. "Maza kuje kuyi al'wala kuzo muyi salla, kai Giɗaɗo ka bar mata tsuntsuwar kurciyar kaji ko gobe da safe zabbi za'a yanka muku ku gasa kuci". Cikin kuka Giɗaɗo yace. "Wallahi Ni dai ta bani tsunstsuwata, bana son zabuwar ni ko ɗawisu zaku yanka min bana so kurciyata nake so a bani abuna". (Giɗaɗo sabo da kaza baya hana a yankata kenan) Cikin tsawa Arɗo Babayo yace. "Kai tafi daga nan ba kaine babba ba kaci girma ka bar mata tsuntsuwar kaji ko Giɗaɗona". Tura baki yayi yabi bayan yayun nashi yana cewa. "Ni a dena cemin Giɗaɗo ai dani Giɗaɗone da komai nakeso zaku bani". Basubi ta kanshi ba duk suka meda hankalinsu kan Parvina da tsuntsuwar dan ganin ƙasan tsuntsuwar Bolerun yana zubda jini, wannan abun ya sasu cikin nazari to, amman sai mgnar Parvina ta katse musu nazarin da cewa. "Allah sarki gashi sunji mata ciwo har sun fidda mata jini". Jin haka yasa suka sa a ransu yess jinin ne daya fita sanadin jin ciwo, cikin kula Arɗo Babayo ya matso parvina da taketa shafa kan tsuntsuwar da suke gani a idanunsu a hankali ya kamo hannunta cikin lallashi yace. "Parvina muje cikin gida ko, kinga dare yayi kiyi salla kici abinci, tsuntsuwar taki kuma ki saketa zata fire ta hau makwancinta". Da sauri ta fara jujjuya mishi kai hawaye na zuba tace. "Baffa Arɗo ta fire kuma? Bata da fiffigefa mutunce fa,tare zamu kwana da ita wallahi ba tsunstsuwar bace, mutunce ku daina ce mata tsuntsuwa, karmu barta ta kwana a woje". Sai ta kuma kama fiffigen tsunstsuwar tace. "Ga hannunta nan sun karya mata". Sai ta kuma kama ƙafafun tsuntsuwar tace. "Baffa Arɗo kaga ga sawunta ga idonta tanata zubda hawaye ga cikinta ga kunnenta ga bakinta ga gashin kanta har bayanta". Kallon-kallon suka tsaya sunayiwa junansu, domin kafiyar parvina kan cewa Wannan tsuntsuwar Boleru mutun ce bani Adam ce ya fara basu tsoro to ko dai ƴarinyar tayi gamone? Koko tsuntsuwar iskace?. cikin tsoron daya fara rufe Appa baki na rawa ya kamo hannun ɗiyar tashi da yake masifar so tamkar ƙoƙon ranshi cikin kaɗuwa da muryar fillanci kasan cewar sam fulanin ƙasar Cameroon basa jin hausa koda kawo min wuƙa in kashekane shiyasa cikin fillanci yace. "(Parvina tsonɗu on fa na ɗum innu adamajo, ko waɗi a vi'ata neɗɗo on) parvina tsuntsuwace fa ba mutun bace meyasa kicewa mutunce?". Kuka ta kuma fashewa dashi harda shessheƙan gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi ganin yadda jikin matar ke karkarwa. Ruggume tsuntsuwar kurciyar tayi a ganinsu yayinda ita kuwa cikekkiyar kamilar mace take gani hannunta matar ta kama ta juya ta nufi cikin gidansu dansu da Gainako suka shiga tana kukan shur-shur da hawayenta. Zurui sukayi suka rakata da ido har ta ɓacewa ganinsu. A mashigar gidan sukayi kiciɓis dasu Giɗaɗo da sauri ta koma gefe. Shi kuwa Giɗaɗo wani irin dundu ya kima mata a tsakiyar bayanta tare watsa mata harare cikin fillanci yace. "Hegiya muguwa wallahi sai na yanka tsuntsuwata muna fuka". da sauri tasa jikinta ta kare tsuntsuwar, tare dayin sauri tayi cikin gida. Seyoji ta samu tsaye gefen mamansu yana bata labarin tsuntsuwar da duk gidansu babu wanda bai san Giɗaɗo da itaba dan yanzu kimanin watanni takwas kenan kullum babu dare babu rana a nan gidan nasu tsuntsuwar take rayuwa kullum in Giɗaɗo yaci abinci ya rage inta kuma sai tazo tayi ta tsastsaga har sai tacinye duk abincin daya bari kana ya ajiye mata madarar shanu nanma tazo tasha, idan tasha ta ƙoshine sai ta juya da tafiya take barin cikin gidan ta koma bakin kogi. Da sauri Mamansu Giɗaɗo ta kalli Parvina tare da cewa. "Parvina na zo nan zo keda tsuntsuwar ki kada ki damu babu mai yankata". Da sauri ta iso gaban matar tare da cewa. "Inna ki hanasu yankata Allah kuwa ba tsunstsuwa bace mutunce". Cikin kula matar tace. "To parvina kada ki damu babu mai yankata daga yau ta zama taki, yanzu ajiyeta kije kiyi al'wala kizo kiyi sallah". Da sauri tace. "To". A jiye matar tayi bisa taburmar dake tsakiyar gidan, kana taje tayi al'wala tazo ta shimfiɗa sallaya a gefenta, itama Inna gefenta ta shimfiɗa suka sa baiwar Allah'n nan a tsakiya... Kamar da wasa da abin ya girmama domin koda sukayi salla isha'i fir parvina taƙi ta rabu da tsuntsuwar nan. Su kuwa su Arɗo Babayo sun mance batun tsuntsuwar ma, tunda sukayi sallan isha sukaci abinci. Suketa lissafin kan dabobbinsu kama daga kan Raƙuma, Dawakai, shanu, tumaki, raguna, awaki, ɗawisu, tolo-tolo, zabbi, tattabaru, saida suka waresu baki ɗaya dan sanin adadin zakkar da zasu fitar sannan suka gama fayace na zakkar kowanne daga ciki da shariya ta umarci a bada zakkanshi. Hira sukaci gaba dayi kan abinda ya shafi kiwon nasu. A can cikin gida kuwa, tunda Inna ta gama yiwa su Arɗo Babayo gashin zabbi ta haɗa da madarar shanu aka kai musu taketa fama da Parvina kan yadda ta tasa tsuntsuwar nan a gaba tana mata magiya kan tasa hannunta taci abinci, ganin bazata iya ci da hannun nata bane yasa iya tasa hannun tana bata abinci har baki tana amsa tanaci yayinda hawaye keta kwaranya a fuskarta babu ƙaƙƙautawa. Koda taci ya isheta sai ta mirgina alamun zata konta. Ganin hakan yasa parvina kallon inna cikin sanyinta da nitsuwarta tace. "Inna tare zamu kwana da ita". Kai inna ta jinjina mata kana ta miƙe tace muje cikin ɗakin kinga gari yayi sanyi Giɗaɗo da kike tsoron kada kiyi bacci yazo ya ɗauke tsuntsuwar ma yayi bacci". Kai ta gyaɗa kana ta miƙe suka shiga cikin ɗakin, bisa katifar gado huts ɗinnan ta zauna tare da tsuntsuwar a gefenta, yayinda ga hasken wutan da aka kunna janareta ya gauraye ko ina na gidan da kuma ɗakin. Inna kuwa kan gadonta take, suna ɗan hira, yayinda sam hankali parvina kan tsuntsuwar nan yake. Tashi zaune tayi lokacin da taga gaba ɗaya jikin matar nan yana ta karkarwan ga hannunta dasu Gainako suka karya ya kumbura simtin, hannunta mai lafiyan kuma ta ɗaurashi kan tirtsetsen cikinta, gaba ɗaya jikinta zufane keta tsastsafowa tako ina, cikin tausayawa parvina tace. "Sannu hannunkin ke ciwo ko? Kiyi haƙuri gobe da safe zamu kaiki gidan mai magani". Inna ce ta zubawa Parvina ido cikin yanayin tsoro tace. "(Parvina ɗun sonɗufa) Parvina tsuntsuwace fa. ki dena magana da ita ba jinki takeyi ba". Da sauri ta jujjuya kanta hawaye na zubo mata tace. "Inna Wallahi tallahi mutunce ku dena ce mata tsuntsuwa inna ki ganifa bata da lfy, jikinta duk rawa yakeyi". Kai Inna ta gyaɗa kana tace. "To na yarda yanzu dai ki kwanta kiyi bacci sai gobe da safe zamu kaita gidan mai gyaran karaya da targade". Jin hakane yasa ta konta tare da lumshe idonta. Sai bacci ya fara saceta sai kuma tayi firgigit ta farka, ta kuma tada Inna sabida, suntsuwar nan ta kasa nutsuwa, yayinda ita kuwa Parvina take ganin baiwar Allah'n cikin mawuyacin halinda ya rintane yasa bata gane cewa matarnan naƙuda takeyi ba. A haka suka kwana, har garin Allah ya waye basuyi bacciba, sabida ita kanta inna yanzu tsoron tsuntsuwar ta fara haka kuma take tsoron parvina, ita kuwa baiwar Allah'n nan zafin ciwon naƙudane ya hanata bacci ita kuwa parvina tausayin matar da mutanen garin da gidan ke cewa tsuntsuwar Boleru ne ya hanata bacci. Asuban fari suka tayi sukayi salla, daga nan suka fito tsakiyar gida, kai tsaye sashin Arɗo Babayo suka nufa ita da Inna, shiru sashin nashi alamun basu dawo masallaci ba, cikin alhini da tsoro Inna ta kalli Parvina cikin daburtacciyar murya tace. "Ajiye tsuntsuwar nan haka kina rike da ita kamar kin samu uwarki maza ajiyeta". Cikin zubda hawaye ta tsuguna ta ajiye tsuntsuwar kan buzun Arɗo Babayo, Wanda dai-dai lokacin ne kuma Arɗo Babayo da Appa, Gainako, Seyoji, Buba, Giɗaɗo, Ja'eh suka shigo kamar yadda suka saba. Cikin mamaki suka zubawa tsuntsuwar Kurciyar nan ido ganin yadda taketa birgima a kan buzun tana wasu irin cure-cure tamkar ranta zai bar jikinta. Ita kuwa Parvina kuka ta farayi bil haƙƙi da gskya tanayi tana yarfa hannu, Buba ne yayi maza ya nufi kan tsuntsuwar kurciyar tare da cewa. "Haukan banza a kan buzun salan Arɗo zaku ajiye tsuntsuwar. Ihu mai ƙarfi parvina tasa ganin Buba ya ɗaga kafarshi da ƙarfin bala'i zai kaiwa tsuntsuwar harbi da naushin ƙafarsa, Kamar a mafarki kamar gilmawar walƙiya tamkar daga sama. Sukaga tsuntsuwar Kurciyar nan tayi wani irin ɗagowa ta karkaɗa fikafikinta cikin ƙudurar Ubangiji da hikimarsa da buwayarsa sai gata-ta d...! Salon na dabanne labarine mai cike da sarƙaƙiya, biya 300 ko 1k ki karance badaƙalar cikin salama. By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 2 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *LITTAFINA na kuɗine, akwai na 300 wanda a wata ɗaya za'a gama Part 1, akwai kuma na 1k wanda a mako biyu kacal za'a gama Part 1 da izinin Allah. Yimin TRANSFER ɗin darinki uku ko 1ooo ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar BIYANKI ta number 09097853276 Ayyah ƴan SP Group banda kati, in baki da ac bada a POS. Kuna ƴan 300 in dai da hali turamin ta ac yafi, in babu kuma to turo katin mtn na ɗari uku ta layin 09097853276. Na roƙeki da Allah da Manzonsa da darajar iyayenki in dai kin san niyarki ki saya ki fiddamin littafina, dan daraja da girman Allah da tsarkin al'ƙur'ani kada ki saya Please kuwa darajar iyayenki kada ki saya, ba don niba sai ɗan Allah da manzonsa da iyayen da suka haifeki/ka* ~AKWAI KAYAN GYARA HAƊIN AMARE DA MASU JEGO, DA MASU SABUNTA AMARCI, IN KINASO KI TUNTUƁI WANNAN NUMBER 09097853276~ Ta juye ta dawo mutun *bani Adam* mace fara ƙal mai tsananin kyau da cikar sura da haiba. Wani irin zabura sukayi cikin tsananin tsoro da firgici da tashin hankali suka zaburi gaba ɗayansu, Giɗaɗo kuwa da azaban ƙarfi ya afka jikin Arɗo Babayo, Inna kuwa gaba ɗaya jikinta rawa da karkarwa yakeyi tamkar mazari wata iriyar fitinenneyar zufa mai azabar ƙarfice taketa tsastsafo mata tako wani sashi na jikinta. Seyoji, Gainako, da Ja'eh, gaba ɗaya jikinsu karkarwa yakeyi tamkar mazari. Giɗaɗo kuwa wani irin juyawa yayi a firgice ya yunƙura zai gudu, Arɗo Babayo ne yayi hamzarin kamo hannunshi ya rikeshi gam. Zabura sukayi. Gaba ɗayansu sabida wata iriyar fitinenneyar iska mai azabebben sanyi daya fara kaɗawa yana rausaya ganyayyaki da dukkan tsirran dake yakin surururururu haka iskar ke kaɗawa a hankali tana ratsa jikinsu. "Innalillahi wa innalillahi rajiun. Hasbunallahiwani'imanwakil". Shine abinda suketa maimaitawa gaba ɗayansu cikin tsananin kaɗuwa, ruɗani, firgici, tashin hankali da tarin tsoro, da nitsuwar ganin ikon Allah. Iskar dake karkaɗawa ce tasa gaba ɗaya suka hautsine. Parvina kuwa da sauri ta faɗa jikin baiwar Allah'n tare da ruggumeta. Baki na rawa ta fara addu'a. "Allahumma inni as'aluka khairaha wa'azubika min sharri ha". Da ƙarfi take fidda sautinta tana maimaita addu'ar. Wanda sanadin haka suma kab suka fara bin bakinta. Allah cikin ikonsa da ƙudurarsa sai ga iskar nan ta fara lafawa a hankali. Cikin al'ajibi da tsoron ƙudurar Allah suka ware idanunsu baki ɗaya a kan baiwar Allah'n nan, da shigar suturar dake jikinta ne yayi masifar sasu ruɗani. Cikin dakiya da ƙarfin zuciya Arɗo Babayo ya kalli Buba a hankali yace. "Buba ɗauki su Giɗaɗo ku tafi garke kuje kuyi tatsa". Kai ya gyaɗa mishi domin baki da jarumar Buba sun tafi, Dan a iya tsawon tarihin rayuwarsa ko a films ko a books story bai taba ji da katari da makamancin abinda ya yagini a zahiriyaba, tsuntsuwar Kurciyar ta zama mutun mace a gabanshi ba labari aka bashiba ra'anul ayni. Cikin yanayin tarin kaɗuwa da rawan jiki yasa hannu ya jawo hannun Giɗaɗo daya kifa kanshi jikin babanshi. Cikin fillanci yace. "Zo Giɗaɗo zomu tafi". Da sauri ya miƙa hannunshi ya kama na Buba kana suka juya suka fita. Appa kuwa kanshi ya kauda daga kallon wannan kekyawar halittar dake gabanshi a cikin ransa yace. "Anya kuwa, wannan mutunce ba iskaba". Inna kuwa gefe ta ɗan matsa cikin rawan murya na tsoro da hausar da sai ka dage zaka gane me take cewa tace. "Ra ga Allah bewar Allah mutun ko al'jan?". Ido suka tsurawa matar a zatonsu ko zata basu amsa. Sai dai ganin yanayin da take cikine ya sasu cire tsammanin samun amsarta. Domin gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi, tamkar mazari. Kana sai zufa dake tsastsafo mata tako wani hudan gashin jikinta, ta rumtse idanunta da azaban ƙarfi, tasa haƙoranta ta datse lip ɗinta na ƙasa, duk mace data taɓa haihuwa in ta ganta tasan naƙudace ke azazzabarta. Tausayin ta ne ya cika zuƙa tansu baki ɗaya. Arɗo Babayo ne yayi ɗan gyaran murya tare da kauda kanshi daga kallonta sabida kwarjininta yafi ƙarfin ƙwayar idanunsu cikin sanyi murya yace. "Allahu wahidun ƙahhar, Mutunce ba al'jana bace, Allah shi ya barwa kansa sanin dalilin kasan ce warta a cikin tsuffofin tsuntsaye, amman kam tabbas al'amarine mai tarin girma da sarƙaƙiya, Tine taimaka mata, da zuciya ɗaya ina ji a jikina ba mai cutarwa bace. Kuma akwai tabbaci da kekyawan zaton musulmace". Ido ta zubawa mijin nata da yake bata ƙarfin guiwa. Appa ne ya kalleta tare da gyaɗa mata kai, alamun eh ta taimaketa, Ita kuwa Parvina cikin tausayawa da zubda hawaye tace. "Appa kalli hannunta ya kumbura gashi jikinta zafi Appa a taimaka mata". Hannu ya miƙo ya kama Parvina cikin tausayawa yace. "Zo nan Parvina za'a taimaka mata kinga bata da lfy tashi a jikinta, kinga ki dena danne mata hannun da cikinta". kai ta gyaɗa kana ta kalli matar cikin sanyi tace. "Sannu!". Bata basu amsa bata kulasu bata kuma hafimtar komai daga garesu, haka yasa su Arɗo Babayo juyawa suka fita, ita kuwa Inna matsowa gareta tayi cikin tarin ƙarfin guiwa irin na fulani. Fulaninma irinsu na daji ba irin wasunku na birniba. cikin sanyi tace. "Taso muje daga ciki". ido ta zubawa Inna cikin yanayin wahalar da takeji, hannu Inna tasa ta kamo hannunta mai lafiyar, ta miƙar da ita tsaye. Allah da ikonshi, sai gata a tsaye cas. Haka yasa Inna ta jata suka koma cikin gida, cikin ɗakinta ta kaita, a bakin katifar da suka kwana ta ajiyeta, da sauri ta koma woje wuta ta hura ta ɗaura ruwan zafi. Kana ta dawo ciki. Cikin mamaki take kallonta ganin taja ta jingina da jikin gini kana, ta rumtse idanunta ga hawaye nata kwaranya daga idanunta. Gefenta ta zauna ta zuba mata ido. Jin an zauna gefen tanne yasa ta buɗe kekyawan idanunta, cikin kula Inna tace. "Sannu baiwar Allah, kamar naƙuda kikeji ko?". Kai ta gyaɗa mata alamar eh naƙudar takeji, murmushi inna tayi tare da cewa. "Alhamdulillah naji sanyi na ƙara gamsuwa ke mutunce, kuma kina gane me nake faɗa a yanzu, to amman kiyi magana mana". Kanta ta jujjuya mata alamun. "Bazan iyaba". Jin muryarsu Arɗo Babayo ne yasa inna tayi maza ta fito, Ganin Arɗo Babayo da Appa da kuma Malam Liman da sarkin bakansu wanda yake rugar makotansu ne yasata saurin fitowa tare da cewa. "Sannun ku da zuwa Malam Liman, Baka barka da zuwa". Taburma ta shimfaɗa musu, jin muryar Malam Liman ne na cewa. "A a bar taburmarnan ina baƙuwar tamu?". "Tana cikin ɗaki, da alamun tana fama da yanayin naƙuda ne". Inna ta faɗa cikin alhini. Sarkin bakanne yayi ɗan gyaran murya kana yace. "Ina son ganinta". Arɗo Babayo ne yace. "To bisimilla, shigo daga ciki". Ɗakin suka nufa Inna na gaba Arɗo Babayo na biye da ita a baya, kana Appa da Malam Liman da Sarkin Baka suka rufa musu baya. Suna shiga suka sameta zaune ta haɗe jikinta wuri ɗaya, jin motsin shigowar mutanene yasa ta ɗago kanta, da sauri ta kauda idanunta. Shi kuwa SARKIN Bakan, kanshi ya rinƙa jinjina wa cikin al'hini yake cewa. "Mutun ce ba al'janba, baiwar Allah an tozarta rayuwarki." Sai kuma ya kalli Arɗo Babayo cikin sauri yace. "Maza a bani madarar shanu mai ɗumi wanda aka tatsa yanzu". To Arɗo Babayo yace tare da juyawa ya fita, a harabar gida yayi arba da Gainako da yake shigowa da kwaryar nono, da sauri ya iso, kana yasa ƙaramar kwarya ya kamfati madarar shanun daketa tururi sannan ya juya ya koma cikin ɗakin. Yana zuwa ya miƙawa sarkin Bakan, yana amsar ƙoryar, ya ajiyeta a gabanshi jakar fatar ruƙimi da yakesa magungunanshi a cikine ya sauƙe daga kafaɗarshi, kana a hankali ya fara harhaɗa magunguna a cikin madarar, saida yasa komai sannan ya kalli Inna yace. "A bani zuma da zam-zam". Da sauri tace. "To". Kana ta miƙo ta ɗauko mishi, koda ta kawo da sauri yasa zumar da zam-zam ɗin ya gaureyasu,'. Kana ya bawa Malam Liman da Arɗo Babayo sukayi mata tofin ayatul shifa, a ciki, kana ya amshi kwaryar. Inna ya miƙawa kwaryar yace. "Gashi bata tasha". Amsa tayi kana ta matso kusa da matar a hankali tasa mata bakin kwaryar a bakinta. Tare da cewa. "Bismillah ki Sha". A hankali ta buɗe bakinta, ta fara shan madarar shanun nan da magungunan, masu haɗe da zam-zam da zuma da kuma rahamar ayatul shifa. Saida ta sha mai yawa sannan ta kauda kanta. Ae fa a take saiga naƙuda ta tashi gadan-gadan. Ganin haka yasa su Arɗo kab suka fito woje ya rage daga ita sai Inna. Ganin haka yasa Malam Liman tura Ori da yanzu ya shigo yaje ya kira matarsa ta taimakawa inna su amshi haihuwar. Ba jimawa kuwa Iya laure tazo, kai tsaye cikin ɗakin ta wuce. Cikin ikon Allah a take a sauƙaƙe Allah ya sauƙeta lfya, ta haifi yarta mace ƴar ƙanƙanuwa. Bayan sun yanke cibiya sun gyara, komai na wurin. Kana Inna ta taimaka mata tayi wonka, ita kuwa iya laure wonka tayiwa jaririyar ta haɗeta cikin zanin Inna ta bawa Parvina daketa tsalle. Koda suka fito daga wonka, konciya tayi a kan katifar, kana iya laure ta kontar mata da ƴar a gabanta. Ajiyan zuciya ta sauƙe mai ƙarfi kana a hankali ta lumshe idonta, tana son ta tuno wani abu na rayuwarta ta baya amman ina ta kasa tunowa, Abu ɗaya takeji bata manceba sunan Allah wanda tunda ta dawo mutun taketa maimaita kiranshi a zuciyarta dan taji bakinta bazata iya magana ba, amman a ranta tanaji tana bitar karatun al'ƙur'ani mai girma da tarin addu'o'in kamar yadda takeyi tun tana a tsunstsuwar ma. Ganin tayi shiru ne kamar maiyin bacci yasa inna da iya laure suka fito woje. Sashin Arɗo Babayo suka nufa, suna shiga sukayiwa juna barkar haihuwarta lfy. Shiru sukayi baki ɗayansu bayan duk sun zauna kamar yadda Sarkin Baka ya umarcesu, gyaran murya yayi kana a hankali ya fara magana. "To da forko dai sai dai muce. Alhamdulillah, mun godewa da yasa sanadinmu wata baiwar Allah zata samu waraka daga mugun cuta na magauta maƙiya azzalumai marasa tsoron Allah". Kai suka jinjina alamun gamsuwa, shi kuwa tonkoshe ƙafa yayi kana yaci gaba da cewa. "Kamar yadda kuka gani a yanzu mutunce bani adam ce ba tsunstsuwa bace kamar yadda kuka gani da zata a baya, aikin sihirine kawai ya maidata haka. Amman Alhamdulillah tunda gashi yanzu Allah yayi ikonshi ya karya abun da akayi mata ya kuma sauketa lfy dama shi asiri tasirinshi kaɗanne ga wanda yayi imani da Allah kuma dole gsky zatayi halinta watan-watarana". Arɗo Babayo ne yace. "Allah mai iko, mutun a maidashi tsuntsuwar Boleru kai abinnan da al'ajabi". Kai ya gyaɗa mishi tare da cewa. "Ɗan Adam kenan mai wuyar gane hali babu mai sanin halin mutum sai Allah, domin shi ɗan adam dare". Sai ya kuma kalli Inna tare da cewa. "Yanzu tayi magana ne?". Da sauri Inna tace. "A a batayi mgna ba sai dai in anyi magana tanaji kuma tana ganewa". Kai ya rausayar tare da cewa. "Zatayi magana in sha Allah, yanzu aci gaba da kula da ita yadda ya dace zan bata magunguna kuma, sannan kada kuji tsoronta ko kaɗan in sha Allah ba mai cutarwa bace". Malam Liman ne ya gyara babbar rigarshi tare da cewa. "To wannan baiwar Allah'n ko daga ina ta fito? Ko ta yaya zamu gano yan uwanta danginta ahlinta ko wani nata a duniya?". Sarkin bakanne yayi ɗan gyaran murya kana yace. "In sha Allah ita in ta dawo haiyacinta, zatayi mana bayanin komai zata faɗa mana sunanta sunan garinsu sunan iyayenta sunan mijinta da anguwarsu sai mu mikata garesu". Appa ne ya ɗanyi ajiyan zuciya tare da cewa. "Allah ya bata lfy ya kuma dawo da ita cikin haiyacinta, kuma in sha Allah duk wani abu daya kamata ayimata a duniya zan mata har sai munga ta samu' lafiya ta koma ga iyayenta". Da haka sukayi ta tattauna duk abinda ya dace ayi mata. Anan kuma sarkin baka yaje da kanshi ya ɗaure mata karayar hannunta yayinda Parvina kuwa ke like da ita...! Haka Inna da iya laure sukayi ta kula da ita a cikin wannan satin sunan...! ************ ...Bayan shekaru Goma sha biyu... Cikin Ƙasar Kautal A Jihar Ɓadamaya state. A wani yanki na Ɓadamaya state, cikin Shikan local Government area a wata rugar FULANI mai suna. *RUGAR BANI* Garin Shikan wani yankine daga yankunan Ɓadamaya yankine mai tarin ƙabilu ma banbanta addinai da al'adu wanda duk yankun Ɓadamaya shida Bimu sune sukafi tarin ƙabilun sai dai babbancin mafiya yawan kabilun Bimu musulmaine saɓanin mafiya yawan ƙabilun Shikan kafurine maƙiya Allah da Manzonsa. Shikan shine sashin da yafi tara ƙabilu mafiya yawa, masu baƙaƙen zuciya ƙabulun da hasken addini bai cimmusuba. Ƙabila mafi rinjaye a yankin Shikan itace ƙabilar ɓachama. Mafi akasari Ɓachamawa mutanene kafurai ne marasa ɗigon imani a zuƙatansu marasa son zaman lfya, mugunta da kisa shine abinda ke sasu farin ciki, abinda kawo ya sanine duk sanda akaji jihar Ɓadamaya cikin wani tashin hankali to daga ƙabilar ɓachama ne. Duda yawan ƙabilu na garin Shikan hakan baisa fulani sun sakar musu garinba, domin tushen garin na fulanine, sabida kowa yasan makiyayi basa nesa da wurin damshi da ruwa, domin rayar da ababen kiwonsu. Haka yasa akwai musulmai Hausawanmu da tarin yawa cikin garin Shikan, wanda duk rintsi da wahala sunƙi barin garin, koda yake hakan baya rasa nasaba da irin al'barkatu da ni'imomin da Allah yayiwa garin. Daga gefen. Garin Shikan akwai babban kogin da yakeda ruwa biyu wanda ko wucewa zakayi ta kan babban gadan da titin da zai kaika cikin Ɓadamaya zaka hangi ruwane kala biyu a kogi ɗaya basu kuma taɓa haɗewa wuri ɗaya ba da izinin ubangiji. Gefen kogin ta dama wata babbar *Rugar fulani mai suna Rugar Bani* ce mai tarin tarihi, rugace mai girma wacce Ubangiji ya ƙawatata da ababen buƙatar yau da kullum, wannan Ruga itace yanki mafi sanyi a yanki Ɓadamaya state rugace damu fulani muke ce musu *JOTTAN MA'EN* Bi ma'ana fuli mazauna wuri ɗaya, ba ire-iren fulani makiyaya masu tafiye-tafiye bin rugageba, fulanin Rugar Bani fulanine makiyaya masu tarin dabobi masu tarin yawa, Rugar Bani Rugace da aƙalla fulaninmu sunyi sama da shekaru dari da ashirin awannan Rugar, shiyasa harda gini zamani da kyawawan gidaje fulanin sukayi, yayinda kuma akwai bokkokinma a cikin Rugar tasu wanda kuma suka sayi filin da kuɗinsu zufansu a hannun sarkin Shikan na wancan zamanin ya sayar musu yankin wurin gaba ɗaya sun biya kuɗinsu ya kuma basu takardu su, suna zaune a nan suna noma suna kiwo. Rugar Bani na zagaye da ƙauyukan ƙabilun Ɓachamawa da tarin yawa, wanda nan gefensu ƙauyen Bonon yake wanda nanne dodon tsafin ƙabilar ɓachamawan take wanda sunan dodon tsafin nasune suka sawa suna ƙauyen suna Bonon. Kauyen Bonon shine zuciya da karfin kafuran nan, sunyi imani dashi, fiye da zaton mai zato, koda laifi wani yayi bonon ake kaiwa ƙara kuma muddin bonon ya tsinewa mai laifinsun to zai lalace ya ɗai-ɗaice dashi da zuriyarsa baki ɗaya, da yake sunyi imani da hakan kuma yana faruwa suna gani shiyasa bonon yake tamkar zuƙatansu, kamar dai yadda in jikin ɗan adam idan zuciya ta ɓaci gagganji na ɓaci to haka bonon take a wurinsu... Wannan kenan Rugar fulanin Bani yafi ko wani yanki na Ɓadamaya sanyi mai ɗan karen daɗi. Koda yake hakan ya samune sanadin ƙawanya da wani babban dutse mai fesar da numfashin sanyi yayi musu, wanda ya kasance musu tamkar rufar garin. Gefen hagun Rugar Bani kuwa wani babban fadama ne mai cike da lamɓu mai ɗauke da ababen more rayuwa wanda ya kasance mallakinmu Fulanin Rugar Bani, lambun yana da duk wasu kayan marmari kamarsu. Lemu, mangoro, gwaiba, ayaba, dabino,kwakwa, kashu, kankana, abarba, da jefi-jefin tuppa da inabi. Wanda wannan fili yake mallakin Fulanin Rugar Bini'nne, kana bayan filin kuma akwai wani rafin da ya kasance masarrafin noman shinkafawa ne wanda suke yinshi noman rani da damina, kuma shina mallakin Fulanin Rugar Bani ne, wanda komawa yasan iya filinshi, Daga gaban Rugar Bani kuwa kogin Shikan ne malale a gabansu iya ganin mai hange da ido biyu gefen hagunsu kuwa nan garken shanunsu ke shimfiɗe bila adadin. Rayuwar Fulanin wannan Rugar rayuwace mai cike da aminci da amana da hakuri da kauda kai duk da tarin zalunci da kafurai ƙabulun Ɓachamawa keyi musu. "Kamar yadda duk kowa ya sani duk duniya anyi ittifaƙin ba fulatani ko ba fulatana basa neman tsokana ko tada husuma bare tada zaune tsaye. Akan cutar da bafulatani yayi kamar bai san an cutar dashi ba ko bai ganeba, wannan dalilin yasa duk ƙabilun ƙasar Afirka sukeyiwa ƙabilarmu kallon wawaye ne ko basu san abinda sukeyiba ko sokayene, masu ƙarancin wayewa Gidadawa. Mu kuwa a namu sashin fulani mun kasance masu kauda ido kan cutarwar forko data biyu, sai dai a haƙiƙinin gsky bama lamunta ko jurar cutarwa ta uku! Domin rama cuta ga macuci ibadace. Kuma Ba'a sarar mumini a rami ɗaya sau uku". Wannan shine jawabin da wani farin dottijon bafulatanin dake zaune tsakiyar al'ummar wannan rugar bayan sun dawo daga jana'izar mutun ɗaya da ƙabilun ɓachama suka kashe musu cikin sunkuru, a daren jiya wanda ya kasance ɗane ga Arɗon Yabani shugaban Rugar tasu kenan. Hannu yasa ya share zafafan hawayenshi dake kwaranya daga ida nunshi cikin ɗaga sauti yaci gaba da cewa. "Fulani basa ɗaukar mataki domin yaƙi ko zalumci sai dai dan kare kawunansu. Kuma kun sani duniya duk ta sani FULANI BA ƳAN TA'ADDA BANE! Ba ƴan bindiga daɗi bane, makiyayene masu ƙare rayuwarsu dan samawa mazauna cikin birane jin daɗin rayuwa, muyi kiwo mu kai musu suci naman susha madarar shanu kana muyi noma mu ciyar dasu. Meyasa su mutanen birane basa ɗaukar matsalarmu tasu matsalar ana kashemu tamkar kiyashi kuma babu masu kulawa". Tsagaitawa ya ɗanyi tare da shashsheƙa cikin bada umarni a matsayinsa na shugaban Rugar uban wanda aka kashe kuma yace. "Na roƙeku da Allah kada wanda ya ɗauki makami domin ramuwa duk da munga yankan rago akayiwa Hashimu amman bamu san wayeba kuma bamu da hujja, dan haka kada wanda yace zai ɗauki makami. Muyi rubutu mu aikawa maimartaba sarkin Ɓadamaya, domin Al'ƙalami yafi tokobi, mu kai kukanmu gareshi, tunda shi sarkin wannan yanki na Shikan mun kai mishi kukanmu a karo na barka tai bai kulaba, kuyi hakuri mu miƙa lamarinmu ga sarakuna mu, inada yaƙinin zasuyi mana adalci". Shiru mutanen da aƙala sun kai ɗari da ashirin sukayi. Yayinda kowa ya keta zubda hawaye. Sai ɗaya daga cikine da ya kasance baƙin jakada Ɓachama ruwa biyu uwarshi ƙabilar ɓachama, wacce ubanshi bakura babarbaren borno wanda shike saida kanwa a rugartasu ya auro Uwar Ba'ana. yana naɗa komai a wayarshi, domin miƙawa shugaban mayaƙan ƙabilar ɓachama, komai ya gani, domin shi ɗin ya kasance, makashinsu ne kuma taburmarsu ne, domin dama bahaushe yace sai da ɗan gari akanci gari da yaƙi!... A cikin babban birnin Ɓadamaya kuwa. *Land of beauty* Garin Modibbo Joɗa, Mai tutar fulɓe garinda duk arawacin ƙasar Kautal mune kaɗai muka rage da tutar Shehu Usmanu Ɗan Fodiyo. Wanda ya dasashi ya kafashi da hannunshi masarautar fulbe mai ƙarfi Masarautar Joɗa... Cikin birnin matsarautar Joɗa. A cikin babban birnin Ɓadamaya. Wasu irin tsala-tsalan motocine wanda a ƙalla sun kai Goma suke jere suna fitowa daga harabar shaharerriyar makarantar Jami'a ta dake cikin babban birnin Ɓadamaya wato J.U.B Joɗa University Ɓadamaya Yayinda suke tafiya a jere a jere cikin tsananin gudu tamkar zasu tashi sama kana ga jiniya daya karaɗe illahirin sashin wurin wanda dole yaja hankali duk wanda ke wurin gudu sukeyi tamkar zasu tashi sama da titin. Motoci huɗune a gaba, wanda suka kasance masu kyau. Sai wata Rolls Royce, mai kuɗi kimanin naira million 4, 959,630. Motace mai tsananin sheƙi da azabar kyau motar sabuwace dal, sai sheƙi da ɗaukar ido takeyi komai na motar farine ƙal sai glass ɗinta daya kasance tin tek mai duhu. Wani kekyawan matashine mai cikar haiba da kamala da kima, uwa uba kwarjininsa mai cika idon mutane, farine ƙal wanda da ka ganshi kasan tabbas bafulatani ne, kuma zaka gane ya haɗa jini da larabawa. Wata iriyar shigace a jikinsa shiga mai ƙara daraja da kamala farin yadin Super Nour a jikinsa wanda a ƙalla zai kai tamanin ɗ kuɗinshi, ya ɗaura baƙar al'kebbarsa ta jinin larabawan saudia Al'kebbar baƙace mai faɗi, kana yasa farin hirami a kanshi da zagayen baƙin saman hiramin. Fuskarshi nan ta fito ras sajenshi mai tsananin kyau yayi lib a fuskarshi sai sheƙi yakeyi, kana gashin girarsa ya komta lib a saman siraran idanunshi masu kyau da ɗaukar ido, wani irin tsabtaceccen gemune da bazai wuce kamu ɗaya ba ne yayi lib a haɓarsa. Zaune yake cikin motar ya jingina bayanshi da sit ɗin, ya lumshe fararen idanunshi, A hankali yake motsa tattausan jajayen laɓɓansa yana tasbihi. "Subahanallahi wal'hamdulillah wa la'ilahaillah Allah Akbar, Astagafillaha wa'atubu ilaik". Yanaji a jikinshi kudun da akeyi yayi yawa, to amman dolene ayi irin wannan gudun domin lokaci na gab da ƙurewa, dan sosai sallan jumma'ar ya gabato, yasan yanzu masallacin ya fara cika, wannan dalilin yasa bai hana drevernshi gudunba, kuma bai hana fadawanshi sakin jiniyarba, dan ta hanyar jiniyarce zaisa a basu hanya su samu su isa kan lokacin daya dace. Bawai ya bari ayi jiniyar da gudun dan nuna isa da ɗagawa bane, sai dan son isa masallacin Masarautar Joɗa da yake limanci kuma yake gabatar da Hudubar jummar matuƙar yana ƙasar tiyatar da yayiwa watace ya sa lokaci yaso ƙure mishi. Motoci, biyar kuma na bayanshi wanda uku daga ciki na ɗaliban J U B da ya fitone, wanda yana aiki cikin Hospital ɗin makarantar, bayan kuma asibitinshi da kuma Genaral Hospital Ɓadawaya da yake zuwa sau ɗaya cikin ko wanne sati. motoci biyun bayanshin kuma, Jalal ne da abokanshi. Shiyasa motocin suka taho a jere-a jere dan shi bai fiye yarda ya fita da mota sama da biyarba, suma ba kullum ba, wani lokacinma yakan fita shi ɗaya. A haka dai har suka fara ratsowa cikin Ɓadamaya, a dai-dai mashigar laleko ne, Cunkoson ababen hawan ya yawaita, yayinda suka danno kai wurin yasa da yawa suka fara komawa gefen titi suna kauce musu dan basu hanya dan jiniyar dake musu nunin akwai uzurin gaggawa ga kuma fadawa a motocin. Wani mai keke Napep ne ya gangara gefen titi har kusa da wani mai saida su Oranges Banana da dai sauransu. Dogon tsaki mai Napep ɗin yaja tare da cewa. "Wannan ai mulkin mallaka ne da izza duk an tsaidamu sabida wani can zai wuce ai duk nan muma saurin mukeyi munada babban uzuri, saurin da duk mutanen wurin nan keyi duk an katse mana hamzarinmu na son isa masallaci kan lokaci muji huɗubar jumman wannan rana". Mazan dake cike a bayan napep ɗin ne suka haɗa baki wurin cewa. "Wallahi kuwa, gashi motocin nasu nada yawa. zasu sa mu rasa jin hudubar wannan fasihin Malamin". Wani mai motane dayake gefensu ya amshi zancen da cewa. "Kuma gaba ɗaya mutanen nan wurin masalacin zasu tafi, sabida duk mai son jin huɗuba mai ratsa jiki da zuciya baya ƙaunar ko furuci ɗaya na wannan malamin ya wuce shi domin Allah ya rigada ya mishi baiwar lafazi mai shiga zuciya". Wanda ke gefensu ne ya amshi zancen da cewa. "Gaskiya ne wannan sabida shi Allah yayi mushi baiwar lafazi da iya tabsiri mai nusar da gafalelle". Mai saida kayan yayan itatuwan dake gefen sunne yayi ɗan murmushi kana ya miƙawa ƴan matan daketa kallon motocin da ido, lemun da suka saya ya miƙa musu. Kana ya kalli dan-dan zo matasa daketa wuce da kafa, mutanen daketa maganar Malamin ya kalla tare da cewa. "Eh kam gsky duk malaman ƙasar nan babu yashi a lafazi, cikin second ɗaya zai yi maka lafazin da zai gamsar da kai tsawon shekaru Talatin, koda yake hakan baya rasa nasaba da tsatson mahaifiyarshi, da ta kasance balarabiya kuma alarabawanma a cikin ƙabilar da tafi dukkan ƙabilun duniya a baiwar lafazi da iya sarrafa harshe". Cikin mamaki suka kalleshi, Alhajin dake cikin zazzafar motar shin nanne yace. "Haba sai haka mana ashe Balarabe ne wani yanki na tsatsonshi Allah yayi mishi rahamomi masu tarin yawa. Gashi wannan zai hanamu muje muji Kuɗubar". Murmushi mai Appul ɗin yayi tare da kallon gefen baya yadda ya hango dandazon motoci da keke Napep dama masu tafiya da sawu ma. Wasu na meda motocinsu gefe sukayi suna fitowa da sallayoyinsu a hannu suna takowa da ƙafa, kanshi ya ɗan rausayar ya kalli mutanen dake gaban nashi tare da cewa. "Kasan su wayene a cikin motocin nan da kuketa zagin kuwa?". Da sauri suka jujjuya kai tare da cewa. "A a waye ne?". Tsala-tsalan motocin ya zubawa idanu zazzafar farar mota kirar Rolls Royce ɗince ya zubawa ido a hankali ya maida kallonshi garesu tare da cewa. "Shine Sheykh J....! Uhummmm wasa farin girgi. By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 3 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🍇🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *FREE PAGE* *LITTAFINA NA KUƊI NE. TURO 300 DOMIN samun damar KARANTASHI. Ko ki turo 1k domin shiga SP Group, inda zaku samu posting fiye da na 300. Ayyah Ƴan SPG bana son katin, turo dubu ɗayan ta asusuna na, 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta layina na 09097853276. Kuma masu 300 in dai kinada damar turawa ta ac tura,in kuma baki da dama to turo katin mtn na ɗari ukun ta layina na 09097853276, ba hoton katin zaki turoba, numbers ɗin zaki kofa ki turon* ```ALHAMDULILLAH MASU NEMAN TSOFFIN LITTATAFAINA, NA SAMESU GABA ƊAYA, SAI RIGAR KOWA NE BAN SAMUBA. IN KINASO KIZO DA KATIN MTN NA ƊARI UKU kacal IN BAKI DUK LITTAFIN ƊAYA DA KIKESO, A CINSU.ƳAR FULANI, MU'WASMITI, NAMIJI BAYA KAƊAN, A TAUSAYAWA JUNA, BANDIRAWO, RUBUTACCEN AL'AMARI, HUKUNCIN ALLAH, NAKASA BA KASAWA BACE, DA KUMA GARKUWA.``` "Sheykh Jabir Habibullah Nuruddeen Bubayero Joɗa ne. Doctor Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero kenan. Ina nufin GARKUWAN FULANI". Da mamaki a fuskokin su sukace. "Astagafirullaha. Bawan Allah ashe sauri yake ya rigamu kada muje muyi ta jira". Kai mutumin ya jinjina musu tare da nuna motoci biyu wanda Jalal da abokanshi ke ciki, wanda kiɗan dake tashi cikin motocin ya cika ko ina, a hankali yace. "Wannan kuma Jalaluddin kenan ƙanin Sheykh Jabir Habibullah Nuruddeen Bubayero". Dai-dai lokacin kuma motocin su Jalal keta gilmawa suna bin bayan nasu Sheykh da azaban gudu har kamar zasubi ta kan motocin gaban nasu, cikin mamaki mutanen sukace "Ikon Allah to wannan saurin duka na menene? shi kuma". Kai ya jinjina musu lokacin da yake rurrufe kayayyakin shi dan shima shirin tafiya masallacin yakeyi cikin yin ƙasa da murya yace. "Kuyi a hankali kada ya jimu domin takadirinin yarone, saurin da yakeyi kuma, yasan muddin Sheykh bai gansu a masallaci ba ranshi zai ɓaci". Cikin nisawa mai Napep ɗin yace. "Kai masu saida kaya a titi iyayen gulma, dasa ido to kai ina kasan su haka?". Da Murmushi mai lemun ya ɗanyi tare da cewa. "Wallahi sam ba gulma bace, akwai ƙaninshi Jamil abokin tagwaicin Jalal ɗin mutumi nane yakan tsaya a nan in zai shiga gari, kuma yanada ɗan karen surutu da fara'a shiyasa na sansu, akwai randa yana tsaye a nan yaga Jalal ɗin ya wuce a guje shine yayi dariya yace. "Hege mai komaɗeɗɗiyar fuska bosawa Sheykh ne ke nemanshi shine yake gudu kamar zai tashi sama". to nan ya ɗan bani labarinshi. Kuma Sheykh ɗin da kanshi akwai shekarar da yayi azumi a garin nan yakan sayi kaya wurina, wani lokacin Shiru sukayi tare da zubawa motocin idanu. ganin sunata gilmawa, saida suka wuce gaba ɗayansu. Sannan sauran al'ummar gari suka fara biyo bayansu. Mafi akasari ababen hawan dama mutanen dake tafiya a ƙafa kab masallacin Masarautar Joɗa ba fadan jihar suka nufa wanda tuni Sheykh ya isa har yanata gabatar da Hudubar jummar sa mai taken, mu tsaida salla a lokacin ta. A can cikin masallacin Masarautar Joɗa kuwa tuni al'ummar Annabi sun cika sunyi maƙil tako wacce kusurwa jama'a ne saffan-saffan suke shigowa, yayinda cikin masallaci yayi maƙil har harabar masallacin ma ya cika tab da muminai salihan bayin Allah. Kusan a guje wasu ke shigowa sabida lokaci na gab da ƙure musu domin bisa dukkan alamu an kusa ƙare Huɗubar. Duk da tarin mutane manya da yara, amman sabida ladabi irin na addinin musulunci addinin mafi karamci da tsari, shiyasa baka jin motsi ko sautin kowa. Sai wata iriyar zazzaƙar murya mai tsanani daɗin ji da sauraro da iya sarrafa harshe, cikin nitsuwa da iya laffazi muryar Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero ke tashi yayinda yake ratsa zuciya da jiki da Kunnuwan dukkan muminin dake sashin da sautin muryarsa ke kaiwa. A can cikin masallacin yake a fili na musamman wurin da aka ware domin Limami, Yana tsayene bisa sawunshi ya fuskanci tarin bani Adam dake cike maƙil a wurin. Kekyawan matashine mai tarin kwarjinin da haiba mai firgita magautanshi, Sanye yake cikin shiga ta al'farma shigar dake nuna nasabarsa ta wanne sashi, Wani datsetstsen yadin Getzner ne fari ƙal-ƙal wanda yasa riga da wondo, Kana sai wata hamshaƙiyar al'kebba dake nuni da nasabarsa mai tarin ilimin addini da kuma alaƙantuwa da jinin sarauta, Wani irin rawani ne ke murze a kanshi wanda jelanshi ke kwance a gadon bayanshi. Farar fuskarsa dake zagaye da tattausan saje baƙi ƙirin mai fitinenne sheƙi da ɗaukar ido, Ne yayi matuƙar kara mishi ƙwarjini sai tsabtataccen gemunshi da bazai gaza kamu ɗaya ba. Cikin rahama da nimar da ubangiji yayiwa laraba ta baiwar iya sarrafa harshe da tausasan laffuza, yake gabatar da Hudubar jummar da yakeyi. Wanda yana bayayi ne da jan hankali kan girma da darajar salla da tsaida ita a kan lokacin ta. Shiru mutane nen ya ƙara tsananta ne a lokacin daya fara tsorotarwa a kan illloli da masifun dake bibiyar mai wasa da salla. Shiru masallacin da farfajiyar sukayi baki ɗayanshi sai sautin A/C da kuma sauƙar numfarfashi mutane da shessheƙan kukan da wasu salihan bayin Allah sukeyi sabida yadda wa'azin ke ratsa jiki da zuciyar mai imani. A hankali yasa hannunshin ya gyara zaman al'kebbar jikinshi tare da gyara abin sautin maganar dake saƙale a wuyan al'kyabbar jikinshi. A hankali ya lumshe idanunshi kana yayi ƙasa da kanshi cikin yanayin nitsuwarsa ya buɗe jajayen laɓɓansa cikin zazzaƙan sautin muryarsa yaci gaba da cewa. "Ya ƴan uwana musulmai muji tsoron Allah mu tsaida salla, domin itace forkon, abin bincika a cikin aiyukanmu. Kada muyi wasa da salla a cikin dukkan halin da muke ciki. Domin hukuncin mai wasa da salla hukuncine mai girgiza zuciyar dukkan mai mutuwa". Kanshi ya ƙara rusunarwa sabida tarin manyan mutane daddatawa dake gabanshi waɗanda da yawa sunyi jika dashi wasu kuwa sun haifeshi, cikin tausasa lafazi yaci gaba da cewa. "Hukumcin mai wasa da salla lokuta biyar ɗin nan. Duk mai wasa da salla, za'a ɗebe al'barka a rayuwarsa. Ƴa yan uwana mene amfanin rayuwar da babu al'barkan Allah a cikinta, babu. Kana duk mai wasa da salla za'a ɗauke kamala ta mutanen kirki a fuskarsa, ya zamana baka da kamala da daraja a idanun al'ummar duniya. Sannan muddin baka tsaida sallaba dukkan wani aikin da zaka aikata Allah bazai baka ladaba. Kana dukkan addu'o'in da zakayi baza'a ɗaukakasu zuwa samaba. Kana bazaka kasance daga cikin addu'o'ina salihan bayiba matuƙar kana wasa da salla". Sassauta muryarsa yayi cikin yanayinshi na tarin kamala ya ɗan nago kanshi wanda dai-dai lokacin kuma ya hango ƙaninsa Jalal yana shigowa cikin harabar masallacin. Kanshi ya kauda kana yaci gaba da cewa. "Akwai uƙuba uku lokacin mutuwar dukkan mai wasa da salla. Na ɗaya duk mai wasa da sallah zai mutu a matsayin matsiyaci gafalelle. Na biyu Zai mutu yana jin yunwa. Kana na uku Dukkan mai wasa da salla zai mutu yana tsananin jin ƙishi. Ƙishinda koda za'a bashi ruwan ƙoraman duniyar nan baki ɗaya bazai gusar masa da wannan ƙishinba. Kana duk mai wasa da salla akwai uƙuba uku dake jiransa a ƙabarinsa. Za'a ƙuntata masa ƙabarinsa ya tsuƙe ya matse har sai ta kai matsayin da haƙarƙarinsa na dama ya haɗe dana hagu. sannan kuma. Za'a saka masa garwashin wuta a cikin ƙabarinsa yayi ta juyawa a cikinsa ba dare ba rana. Na uku. Za'a saka masa wata macijiya mai suna Shuja ul Qara,u wacce ta kasance ne ɗaya daga cikin macizan wuta. Ida nunta na wutane. Farshenta kuma na baƙin ƙarfene. Tsawon ko wani farcenta ɗaya tsawon tafiyar wuni ɗaya ne. Zatayiwa mamaci magana, da muryarta mai tsawa da amo mai firgitarwa, zatacewa mamaci mai wasa da salla yayin rayuwarsa cewa. (Ubangijina ya umarceni inyi ta saranka tun lokacin sallan asuba har zuwa azahar, daga azahar har suwa la'asar daga la'asar har zuwa magriba daga mangriba har zuwa isha'i daga sallan isha'i har zuwa wayen gari asuba. Duk sara ɗaya da zaiyima mai wasa da salla har ya mutu bai canzaba zai nitse cikin ƙasa anayi mishi azaba, bazai gusheba anai mishi azaba har tashin al'ƙiyama. Allah ya tsaremu. Uƙuba uku lokacin fitowarsa daga ƙabarinsa itace. Na ɗaya hisabi mai tsanani. Na biyu. Fushin Ubangiji. Na uku. Shiga wuta. Allah ya tsaremu ya bamu ikon kiyaye salla da tsaidashi a kan lokacinsa, yaku taron matasa kune shagala tafi auranku, mu dage mu tsare salla duk rintsi". Ya ƙarishe maganar cikin rauni da kushu'i. Gaba ɗaya kowa jikinsa yayi la'asar musamman matasa masu wasa da salla, Jin ya juya yayi gyaran murya ne. Yasa gaba ɗaya kowa ya mike ya fuskanci gabas masamar lada. Cikin nitsuwa da tattausan harshe yake rare karatun al'ƙur'ani mai girma. Lokacin da yake limancin sallan jumma'ar da a ƙalla yana samu halartan mutun sama da Dubu biyu. Bayan anyi salla raka'a biyu kamar yadda yazo a nafsi, akayi addu'a aka shafa kana, mutane suka fara firfita daki-daki. Bayan 30 minute shal cikin masallacin. Dan gaba ɗaya kowa ya nufi wurin lamuran yau da kullum ɗinshi sai mutanen da ba'a rasaba wanda su sai dare zasu bar cikin masallacin. Sarki Nuruddeen Bubayero Joɗa, ne tafe a hankali cikin irin takunsu na sarakai, Yayinda Jikinsa mafi soyuwa a garesa ke gefen damanshi, fadawane ke biye dasu a baya, sun zagayesu, Sai kuma bayansu can kuma Ayarin fadawan Jalal da Jamil ne wanda suke tagwaye ƙannen Sheykh Jabeer. shi kuwa Malam Jabeer taku yakeyi a hankali cikin rashin nuna ɗagawa a kan doron ƙasa, tafiyar yake tamkar yana tausayawa ƙasar yayinda mutane kuwa ke kallon hakan a matsayin ƙasaitace da jinin sarauta dake yawo a sasan jikinshi. Suna tafene a tare yayinda bakin Sheykh Jabeer ke motsawa a hankali hankali, wanda sai ka lura kake gane, tasbihi yakeyi a zuciyarshi wanda hakan ya zame mishi abin ci da sha a rayuwarshi. "Astagafirullaha wa'atubu ilaik, Astagafirullaha! Astagafirullaha!! Subahanallahi! Walhamdilillah wa lailaha'illalahu Allaahu akbar. Astagafirullaha". Waɗannan sune kalamen da basa rabuwa da bakinsa, dama wasu masu tarin yawa. Ta ƙofar dake shiga masarautar daga jikin masallacin sukabi. Masarautar Joɗa babbar masarautace mai tarin girma tarihi. Ginin Masarautar ginine mai masifar kyau da ɗaukan hankali. Kana shiga daga asalin babban gate ɗin fadar, zaka samu wata shimfiɗeɗɗiyar hanya mai girma irin mai guda biyun nan, gefe da gefen hanyar duk wasu irin dogin fulawowi na mijin kwanda ne masu tsawo da kyan gani, sai kuma tsakanin titunan, shima jerin dogayen bishiyoyin ne. Tafiya mai ɗan tsawo, zakayi kafin, ka isa wani babban Round about mai masifar kyau, wanda cikinsa ke ɗauke da babban kwarya a ƙasa, sai kuma ƙananan kware, guda uku, sai kuma ginin mutum-mutumi na kekyawar saniya fara mai ɗigo-ɗigon baƙi, wanda mace ke tsugune a gefe kamar tana tatsan nono sai kuma ɗan saurayi matashi na riƙe da sanda ya coge da ƙafa ɗaya. Sai kuma korayen ciyawi masu masifar kyau da sanyi wanda akayi alamun manomi na ciki. Daga nan ne hanyoyin cikin masarautar suka rabu huɗu, ɗaya yayi gefen dama ɗaya yayi gefen hagu ɗaya yayi gabas ɗaya yayi yamma wanda ta nanne ake shigowa. In ka miƙe ta yamma daret itace titin da zai sadaka da asalin sashin Sarki Nuruddeen Bubayero Joɗa wanda nan sashin matanshi da hadimanshi yake da sashinshi dama faɗar duk nan take. In kayi gefen dama kuwa wasu irin tsala-tsalan gine gine-gine masu tsananin kyau da ɗaukar hankalin wanda suna nan part-part ne masu girma da tsaruwa, an ƙawata tsakiyarsu da wani sassanyan Garden mai girman gaske. Inda part ɗin sun kai goma, mafi kusa da sashin mai martaba sarkin Nuruddeen Aliyu Bubayero, shine sashin GARKUWAN FULANI, wato Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero. Sai kuma na gefen daman Sheykh Jabeer shi kuma na Jafar Habibullah Nuruddeen Bubayero ne, da matarsa Juwairiyya. Sai na gefen hagunshi kuma na Jalal, ne na kusa da Jalal da kuma na Jamil ne sai dai Jamil yafi zama a sashin Jalal duk da korarshi da yakeyi wasu lokutan kuma lokacin kuma yana sashin Sheykh. Sai sashin baya kuma sashin Affan. Daga gefen hagun Masarautar kuwa wasu tamfatsa-tamfatsan plat ne masu girma har guda huɗu, sai kuma wani babban bene dake tsakiyarsu mai tarin girma wanda nanne sashin babban ɗan sarki Habibullah da matanshi. Sai ta gefenshi can kuma wasu manyan part- part ne kimanin guda biyar wanda duk ƙanne shi ne da iyalansu da ƙananan yaransu a ciki. Yayinda duk manyan yaransu kuwa kowa nada part ɗin shi a gefen da part ɗin Sheykh yake a ƙalla dai Part ɗin cikin masarautar Joɗa sun kai hamsin da biyar. Can wurin mashigar kuma wasu ƴan saffan-saffan part-part ne wanda bisa dukkan alamu duka na bayine da hadimai da matansu. Tsayuwa fasalta cikin ko wanne sashi na masarautar bazai yiwuba, sai a hankali. Sai dai ko wanne part yanada Garden mai ɗan girma, wannane yasa gaba ɗaya masarautar ke zagaye da korayen fulawowi da bishiyoyi masu kyau. Fentin masarautar gaba ɗaya iri ɗaya ne, Sky blue and white, mai ɗan karen kyau, a mahaɗar sashukan kuwa wani irin tamfatsetsen sweeminpool mai girma wanda ruwansa ke sky blue. Can bayan sashin Mai martaba da Sheykh kuwa wani ƙaton filine mai cike da dawakai, da sashin mai rainonsu, gefe ɗaya kuma raƙuma da shanaye ne da makiyaya su, kana ga tumaki, a gefen Sheykh Jabeer ne kuwa akayi wani ɗan madai-daicin gidan zu ta bayan ɗakunan shi wanda yake da tarin tsuntsaye kamarsu, Ɗawisu, jimina, mikiya, agwagin ruwa, tolo-tolo, tattabaru, kana sai Aku. Da sauran tsuntsaye carki, kurciya, hasbiya, caccagi da-dai sauransu, shiyasa sashinsa ya kasance namusamman, don Garden Park ɗin ciki yafi na sauran part ɗin duka girma da kyau, sabida shine asalin Garden ɗin tarihin masarautar Joɗa. Daga nan mashigar masarautar kuwa akwai wani babban filin sukuwa mai girma. Daga masallacin Masarautar kuwa akwai miƙeƙƙiyar hanya har cikin masarautar wanda za'a iso gab da fada sannan kowa zai samu hanyar sashinsa. A tsakiyar cikin masarautar ma kuwa akwai wani masallaci mai girma. Wannan kenan sai a hankali zaku san mutanen masarautar da sunayensu halayensu dama nasabarsa da danƙantarsu da manufarsu. A hankali Sarki Nuruddeen da Sheykh Jabeer suke takawa. Suna shiga cikin gidan waɗannan fadawan suka tsaya a bakin Gate ɗin. Kana wanda suka samu a wurin suka miƙe da azama wani dogon carpet mai azabar kyau da taushi, ɗaya daga cikin fadawan ya zo ya ajiye gabansu kana ya rinƙa yin baya-baya yana worwore musu carpet ɗin. A hankali Sarki Nuruddeen Bubayero Joɗa yasa hannunshi ya kamo hannun kekyawan matashin jikan nashi da kab cikin jikokinshi ya fita da ban, hannunshi yake murzawa cikin nasa hannun a hankali a hankali. kana suna tafiya a hankali, cikin takun sarauta, Gefen mai martaba Nuruddee bayine da dogarai a ƙallah sun kai Ashirin da biyar, gefen Sheyk Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero kuwa, Ƴan saffan-saffan fadawane da basu kaishi shekaruba, a ƙalla sun kai goma. Wanda wannan tsarinsa ne yace bazai iya ganin sa'an mahaifinshi ba ko sa'an Ya Jafar ɗinshi ba suna mishi bauta Babban Yayansu Jafar Habibullah Nuruddeen Bubayero suke kira Yah Jafar. Kanshi ya ɗan murza ya juya a hankali da gefen ido ya kalli Kakan nashi dake magana cikin yin ƙasa da murya dan ko sarkin dogaren dake gefenshi baiji me yake cewa ba. "Sheykh yaushe ne tafiyar taku?". Siraran kyawan Idonshi ya lumshi a hankali ya kuma buɗesu tare da rausayar da kanshi. Maimartaba bai damu da jiran amsar tasaba yaci gaba da cewa. "Munyi Magana da Aminina Sarki Jalaluddin yace min Kakarka UmmuKulsum tace tafiyar taku ta ƙara toko?". Shiru ya ɗanyi har saida sukayi taku uku zuwa biyar kana ya gyaɗa mishi kanshi kai a hankali irin gyaɗa kai na kamala". Dai-dai lokacin kuma suka iso dab ƙofar mashigar sashin Maimartaba, wanda dama duk ran jumma'a daga shabiyu yake tashi zaman fada, sanin hutawa yake a irin wannan lokacin ne ya sashi ɗan sake hannun Sheykh Jabeer tare da cewa. "Sirranta komai a rai yanada wuya, amman kai baya maka wuya, ya zama kamar jininki, akwai tauraro na musamman a goshinka, wanda nake fatan watan wata rana ya haska zuƙatan ahlinka dama talakawan da zaka mulka". Jin kakan nashi ya sake hannunshi da kalaman da yake jero mishine yasa ya ɗan kalleshi a hankali ya kuma sunkuyar da kanshi. Sai ya kuma ɗan kalli Sarkin tare dayin mgna. "Mulki yana da nauyi mai girmi Ni kuwa baya cikin tsarin jadawalin ababen buƙata ko sha'awa a rayuwata,". Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa. "Ba sai lallai abinda mutun keso ke samu ba, bakuma dole ka rasa abinda baka soba". Ganin kakan nashi yaci gaba da tafiya ne yasa shima ya yaci gaba da tafiya. Inda fadawanshi ke biye dashi a baya. Yayinda fadawan Maimartaba kuwa suka tsaya a bakin sashin sa. Sunyi tafiya mai nisa kaɗan kafin suka ratso ta gaban sashinsu mai azabar girma da kyau sashine mai ɗauke da part-part masu tarin yawa da girma wanda tsakanin ko wannensu da ƴar tazara sosaima. A hankali ya ɗago hannunshi daga cikin babbar rigarsa da zazzafar al'kebbarsa ta rufe, ɗan ɗaga musu hannunshi yayi alamun su tsaya daga nan. Cikin abinda bai gaza 18 second ba duk suka rusuna ba tare da sun ƙara koda taku ɗaɗɗaya ba, kusan a tare suke cewa. "Takarwarka lafiya ɗan Baban yaya Habibullah jikin Sarki Nuruddeen, jika ga sarki musulmai Jalaluddin". A hankali ya kuma ɗaga musu hannunshi alamun ya isa haka, dan shi dai Allah ya sani har ranshi baya jin daɗi da son wannan kirare-kiraren dan yayi imani da Allah zasu iya sawa ɗan adam ɗagawa da jin kanshi shi wani abune, zasu iya sa mutun yaji kansa a matsayin wani sarki mai iko bayan kuma babu wani Sarki sai Allah. Yana tsoron ɗagawa ta samu mazauni a zuciyarshi, sam baya son wannan kirare-kiraren na zamanin jahiliyya ina dalili kana mutum ɗan Adam mai daraja azo ana wani ce maka toron giwa ko tozon raƙumi ko dokin ƙarfe yaya Allah ya karramaka yayika ɗan Adam ka bari na ƙasa da kai suna suffantaka da dabbobi. A hankali yace. "Ya isa, duk kuje kowa yayi uzurin gabansa in inada buƙatar ku zan nemeku". Shiru sukayi tare da baje manyan rigunansu suka zauna a inda ya dakatar da suɗin. Kana sukace. "An gama". Shi kuwa a hankali yake taku cikin shigarsa da tafi kama data limamen harami. A hankali yake taku, har ya iso bakin ƙofar shiga side ɗinsa inda a nan dogari mai tsare mashigar sashinsa sarkin ƙofarsa ke tsaye. Tuni Sarkin ƙofa ya miƙe yasa hannu zai buɗe mishi ƙofar kenan sai ya kuma ɗan rusunar da kanshi, Ganin Jamil ya rigashi kai hannunshi ya buɗe ƙofar cikin salonsa na raha ya nunawa Hamman nashi ƙofar tare da cewa. "Sheykh Dr Malam Hamma Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero Joɗa GARKUWA barka da yamma". Kanshi ya kauda daga kallon ƙanni nashi, sannan ya kutsa kai ciki, da sauri shima Jamil ya mara mishi baya, Cikin wani haɗeɗɗen corridor mai fitinenne ƙamshi da azabebben sanyi suke tafiya a hankali. Tafiya kaɗan sukayi sai gasu cikin wani tamfatsen falo na al'farma da more rayuwa, ɗaya daga cikin lumtsuma-lumtsuman kujerun kilisai na manyan sarakunan dake falon ya zauna a hankali. Ido ya ɗago ya watsa ƙanin nashi su, cikin sauri Jamil yayi ƙasa da kanshi tare da cewa. "Na tuba Hamma kayi magana ina tsoron hukunci da idanunka gwara kamin duka kon ka haɗani da wannan saggamemen na bakin ƙofar kan nan ya dakani kawai in huta". Kanshi ya kawar Cikin harshen larabci yace. "Ban gankaba a masallaci". Da sauri ya durƙuso gaban Hamman nashi cikin yin wuƙi-wuƙi da idanu cikin sanyi yace. "Ana Aspet ya Akhi, a matsallacin ƙofar gidansu, Khadija nai sallan jumma'ar". Kanshi ya gyaɗa kana ya kauda kanshi ya fuskanci wani katon majigi dake liƙe a jikin ginin yana fuskarta kujerar da yake zaune a kai. Majigine dake ɗauke da full Qura'an, a hankali yake karatun cikin sassanyan murya. Ganin hakane yasa Jamil ɗan rusuna duk da yasan ba amsa zai samuba cikin sanyi yace. "Hajia Mama tana son ganinka". Kanshi kawai ya gyaɗa yaci gaba da karatun shi. Ganin hakan yasa Jamil ya juya ya fita. Shikuwa Sheykh yaci gaba da karatunshi, kusan awa ɗaya kana ya shiga Bedroom. Shine bai fitoba sai lokacin da sallan la'asar ta gabato, jin an kira sallane, yasa ya shiga ya sabunta al'wala kana ya fito ba kowa a wurin sun watse kemar yadda ya umsrcesu. Sai can bakin mafita ya samu mutun huɗu, yana tafe fadawanshi na biye dashi wanda suma sunyi al'walan. Jamil kuwa daga sashin Hajia Mama ya fito da nufin zaije side ɗinsu yayi al'wala. A harabar gidan yayi kiciɓis da abokin tagwaicinsa wato Jalal, cikin sanyi ya kalli yadda Jalal ke zagaye da fadawa yana tafiya da yanayinsa da muddin zaka yanke mishi hukunci da ganin zahiri zakace cikekken ɗan iskane, sai dai a baɗinin ba haka abin yakeba. Kekyawa ne shima dan shi yana ɗibin kamanni da Hamma Jabeer ɗin nasu sosai saɓanin Jamil da yafi kama da Babban yayansu, Barrister Jafar Habibullah Nuruddeen Bubayero. Tafiya yake cikin shigar tsamari zamani, wondon a saɓule har kana iya hango boxes ɗinshi, kana ga wani irin kafirin aski da yayi mai ɗaukar hankali. sam a rayuwarsa shi baya ta'ammali da manyan kaya, Baya tsoro ko shayin ko shakkar kowa a duniya sai Hammansun kaɗai. tafe yake bayinshi na biye dashi a baya, da wasu kolabe a hannunsu, cikin tsare fuska Jamil yace. "Kai ku tsaya, kolaben menene wannan a hannunku?". Juyowa yayi a zafafe cikin halin faɗa yace. "Kwalaben Giyane ko kanada maganne Akukkuturu?." Da azaban ƙarfi da tsoro Jamil ya zazzaro ido cikin ɗaga murya yace. "Kwala ben giya a gidannan Jalal kasan abinda kake cewa kuwa? Kwalaben giya a Masarautar Joɗa". Ya juyo da masifa kenan yayi arba da Hamman nasu, shiru yayi tare da yin ƙasa da kanshi, jiki a mace. Shi kuwa Sheykh Jabeer idanu ya zuba mishi na wasu yan daƙiƙu kana ya juya ya nufi hanyar da zata sadashi da ƙofar tafiya masallacin Masarautar tasu ba tare fitar nan bisa dressing mirror suka ajiyesu kana suka juya suka fita. Shi kuwa al'wala yayi ya nufi masallacin. Ƙarfe tara dai-dai na dare. Sheykh Jabeer, ne zaune a bisa wani tattausan carpet mai azabar taushi, Wata Hamshaƙiyar Gimbiyace mai cikan iko da muƙami, mulki, iko, cikin wani irin kallo mai cike da kulawa tasa hannu ta ɗauki ɗaya daga cikin nonon inabi dake cikin wani kekyawan tray dake gabanta miƙa mishi tayi tare da cewa "Jabeer Yaushene tafiyar taku?." Tankwashe kanshi yayi bisa kafaɗunshi kana a hankali ya ɗan kalleta tare da motsa laɓɓanshi a hankali yace. "jibi". ya faɗi mgnar a gajarce, gyara kishingiɗarta tayi bisa kilisan tum-tum dake gefenta, Cikin kulawa tace. "Da Umaymah zakuje ne?". Kanshi ya jujjuya mata alamun a a. Kanta ta rausayar cikin ƙasaita tace. "Naga kamar bacci kakeji Saida safe". Kanshi ya gyaɗa kana cikin girmamawa yace. "Allah ya bamu al'khairi". Amin tace, shi kuwa daga nan ya fita ya tafi. Koda ya koma sashinsa. A falo bakin ƙofar ya samu Jakadiya, tana ganinshi ta ɗan rusuna duk da tasan yana hanata hakan a hankali tace. "Akarmakallahu, Umaymah ce take biɗar mgna da kai, ta kirayi layinka ba'a ɗagawa, shine tace in kawo maka wayar". Kanshi ya ɗan sunkiyar a hankali yace. "Ummi kice mata tayi hakuri saida safe". Cikin mamaki jakadiya tace. "Lafiya dai ko Sheykh?". Kanshi ya gyaɗa mata alamar eh lfy. "To ba laifi zan gaya mata". Daga nan ta juya ta koma sashinta. Shi kuwa Sheykh Jabeer, daga bakin ƙofa ya dakatar da bayinshi. Kana cikin nitsuwa ya kallesu tare da cewa. "Sarkin ƙofar ka janye bayin dake bina da bin Jalal da Jamil, kaima ka koma can sashunku, ba'a buƙatar bibikon nan, in inada buƙatar ku Ummi zata sanar muku." Ciki girmamawa sukace. "To Sheykh". daga nan ya juya ya nufi ciki. Su kuma suka juya. Koda ya shiga ɗakinshi kai tsaye bathroom ya wuce wonka yayi tare da al'wala a cikin bathroom nashi da yafi makoncin wani kyau. Komai na bathroom ɗin glass ne mai ruwan garai-garai, bathroom ɗin katone, mai ɗauko da babban drower'n glass wanda yake cike da ƙananun kayan sirrin jikinshi kamarsu vets boxes and pants kana towels da rigunan wonka da jalabiyoyinshi masu masifar kyau da tsada da taushi da yawa, sai kuma 3 qtr da kuma turaruka dasu brosh da su makilin da dai sauran kayan buƙata na aske pravet part. Ko ina na kusurwan ban ɗakin da madubai. Bayan ya fitone, yayi shirin baccinsa cikin wani tattausan jallabiya mai masifar kyau da tsada, A bakin gadonshi na sarakuna ya zauna, idonshi ya zubawa woyoyinshi dake kan bedside drower' Woyoyin sun kai biyar, a hankali yasa hannunshin ya ɗauki ɗaya daga cikinsu data kawo haske, alamun ana kiranshi, Karawa yayi a kunnenshi tare da yin shiru. A can ɗaya sashin kuma kekyawar tsohuwar balarabiyace keta mishi faɗan ina ya shiga tana kiranshi bai amsawa. A hankali ya lumshe idanunshi tare da mirginawa ya konta tattausan gadonsa da shimfiɗar sa, wanda Jamil ke gyara mishi a koda yaushe, cikin harshen larabci yace. "Sitti raja'an!". shiru sukayi baki ɗayansu, can kuma sai yaci gaba da magana cikin larabcin, sawon 32 second yana maga kafin ya katse kiran, kana yayi laduban konciya bacci ya konta. Washe gari da safe da misalin karfe sha ɗaya na rana. Dawawonshi kenan daga fada, Yana shiga falonshi asalin falon dake gab da makoncinsa kiran Umaymah na shiga wayarsa. Ganin video call ne ya sashi, amsa kiran kana ya ajiye wayar kan Glass Stull dake gaban kujerar da yake zaune. Fuskar wata kekyawar Matace ya bayyana a fuskar wayar tashi, cikin sanyi ta zuba mishi idanu ganin yadda ya tonƙoshe wuyanshi bisa kafaɗunshi a hankali tace. "Jazlaan". Kanshi ya ɗan mirgina cikin wani yanayi ya jujjuya mata kai a hankali yace. "Jazlaan, Umaymah sai yaushe zan zama Jazlaan? Sai yaushe, Jazlaan zai wadaci rayuwarmu?". Murmushi mai ciwo a zuciya tayi tare da cewa. "In sha Allah nan kusa". A hankali ya lumshe idanunshi cikin sanyi yace. "Umaymah, kizo kafin mu tafi, ina so mu haɗu". Cikin tarin kulawa da tsananin ƙauna tace. "Menene matsalarka?". A hankali yace. "Ya Jafar...! Littafin na kuɗine. By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 4 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GAREKU MUTANEN NIGER, +22799460151 kuyi haƙuri an samu akasin number da nada bada, wayarta ta lalace. Yanzu ga number da zakuyiwa mgn +22799460151 300 ko 1k idan kun turata mata, saita turo min number ki/ka sai in saki/ka a group ɗin da kika biyawa🤝🏻. Gareku mutanen ƙasata ga number ta 09097853278, turo katin mtn na ɗari uku kacal, ko kimin TRANSFER ɗin darinki uku ko 1k ɗan samun SP Group. In kin biya sai kiyi screenshort ki turo min shaidar biyan kuɗin littafin GARKUWA ta wannan number dai 09097853276* Cikin nitsuwar da ya kasance halittarsa, ya ɗan ranƙwafar da kai yayinda fuskarshi ta ɗan sauya yanayi murya can ƙasa yace. "Ya Jafar! Yana buƙatar kulawata, baya son nayi nesa dashi, Umaymah Jalal da Jamil basu da hankali yaran basu da nitsuwa Umaymah basu san ciwon kansuba Affan kuma baya nan". A hankali wacce ya kira da Umaymah ta gyara zama cikin tarin kula da bege da tausayi da ƙaunar Jazlaan ɗin nata cikin tausasan laffazi tace. "Daɗewa zakuyi ne Jazlaan?". Hannunshin yasa yana ɗan shafa sumar kanshi cikin rumtse ido murya can ƙasa yace. "Sitti tace zamu daɗe a can, kuma Maimartaba ta gayawa kai tsaye, shi kuma ya faɗawa Abba kai tsaye umarni suka bani". Kai ta ɗan rausayar tare da cewa. "Ba komai Jazlaan in sha Allah babu abinda zai samu Jafar, in kaje kayi ta mishi addu'o'in kamar yadda ka saba, in sha Allah yana cikin kulawa da kariyar Allah". Kanshi ya ɗan gyaɗa mata, Domin bai fiye yawan maganaba in ba amɓaton Allah ba, dan ma ta kasance cikin mutun biyar ns duniya da yake iya yin doguwar magana dasu, musamman Maimartaba da mafi akasari faɗa ke haɗasu, sai ita sai kuma Umminshi Jakadiyarsu kenan wacce tun yana jariri itace uwar rainonshi sai Sitti da Jadda". shiru ta ɗanyi tana kallon yadda ya lumshe ido tamkar bazaiyi magana ba, bata dai katse kiranba har tsawon 3 minutes kafin ya ɗan motsa laɓɓansa ba tare daya buɗe kwayar kekyawan idanunshi yace. "Umaymahhhh". yadda ya kira sunanra ya tabbatar mata halin da zuciyarshi ke ciki, tafi kowa na duniya sanin matsalarki Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero. Cikin kulawa tace. "Na'am Jazlaan". tashi yayi zaune a hankali ya fuskanci wayar tasa da kyau, hannunshi ya haɗe wuri ɗaya tare da cewa. "Umaymahhhh Jalal". Cikin kulawar da ƙanwar uwa shaƙiƙiya kan iya bawa ƴaƴan ƴar uwarta, da tarin son da takeyiwa ƴaƴan ƴar uwarta Tata, musamman shi Sheykh, a hankali tace. "Me Jalal yayi". Kanshi ya ɗan ranƙofar tare da cewa. "Umaymahhhh Jalal bayaji, ya fiye gagara, da son jawowa Ahlinmu abin faɗa. Ɗazuma kwalaɓen giya fa ya shigo dasu cikin masarautar da ta kasance tsarkakkeya. Ga Jamil kuma babu nitsuwa tattaredashi, duk inda yaga mace, jikinshi na rawa yakebi ya zama kamar ɗan akuya, Umaymah in nayi nisa da gida, zasuyi abinda zai sasu a matsalar rayuwa". Wani dogon ajiyan zuciya Umaymah ta sauƙe a hankali tace. "Kada ka damu, in sha Allah babu abinda zasuyi da izinin Ubangiji rayuwarsu bazata lalaceba kodan addu'o'in da kakeyi musu, da irin tarbiyar da kake basu". Kanshi ya gyaɗa tare da taune lips ɗinshi na ƙasa yayinda lokacin ɗaya kwayar idanunshi sukayi wani irin kala su ba jaba sunba fariba. Cikin rauni miskilar muryarshi yace. "Na sanifa Umaymah babu abinda sukeyi, nasan Jalal ba mashayin giya bane baya shan komai, amman ya rigada duniya tanayi mishi kallon mashayi, tantiri kana taƙadirin yaro. Haka nan nasan Jamil ma ba mazinaci bane Umaymah amman a idanun mutanen duniya shi tamkar ɗan akuya suke ganinshi, Kamar yadda Ya Jafar yake ba majanuni bane amman mutanen duniya kallon majanun suke mishi". Kanshi ya sunkuyar cikin sakekkiyar murya yace. "Duk an liƙa musu munanan tabo, a cikin rayuwarsu, Umaymah, ni ma ɗin bazan tsiraba tabbas nasan nima akwai wani tabon da ake kallona dashi, nasan nima bazan tsiraba". Da sauri Umaymah ta sunkuyar da kanta ƙasa wasu zafafan hawaye masu azabar zafi da ƙuna a zuciya suka fara kwaranyowa a idanunta, wani zazzafan shessheƙan kuka ya kwabce mata. Jin shessheƙan kukan natane yasa Sheykh Jabeer ya ɗan ɗago kanshi cikin jarumta da ƙarfin hali yayi wani murmushi mai ciwo a rai. A hankali yace. "Kuka kuma Umaymah, inada yaƙinin ƙarfin zuciyarkine da yasani sanar dake matsalar ƴaƴan ƴar uwarki, tunda ita bazata iya yin komai a kaiba". Cikin shessheƙan kukan tace. "Ba komai Jazlaan in sha Allah babu komai face al'khairi a cikin rayuwarku, insha Allah babu wani tabon da mutane ke ganinka dashi. Yanzu yaushe zaka wuce Leddi julɓe?". Cikin miskilar murya mafi karamci yace. "Yau da dare zan wuce, gobe da asuba zamu wuce Saudiyya Sittin ta matsa tana so taje taga ahlinta". Kai ta ɗan gyaɗa kana tace. "Ibrahim ma yace ya kusa dawowa". Kanshi ya ɗan rausayar kana yace. "Eh munyi mgna dashi ɗazu". Kanshi ya ɗan juyo ya kalli sauran woyoyinsh dake bisa Stull ɗin dake gefenshi, Kiran shugan ɗaliban J.S.U Ɓadamaya ne ke shiga, bai kula kiranba yaci gaba da magana da Umaymahnshi, har saida yaga ta samu nitsuwa kafin ya barta. Tashi yayi a hankali yake taku cikin kamala da nitsuwa irinta manyan limamai a hankali yake manna farar tattausar fatar ƙafarshi da in ya taka sai kaga kamar jini zai tsallo. Yana shiga cikin ɗakin nashi, al'kyabbarsa ya cire tare da buɗe wani sashi na durowarsa ya sanƙala a masanƙalinta. Da tattausan farar jallabiyar dake ƙasanta ya shiga bedroom da ita, Wannan lokacin wonkansa ne, babu abin da zai katse mishi uzurin domin ya kasance mutun mai mutunta lokacin rayuwarsa ko wani lokacin da abinda yakeyi. Wonka yayi cikin tamfatsen bathroom ɗin nashi. Yana fitowa, ya wuce gaban dreesing mirror, kimtsawa yayi a gaggauce dan lokacin tafiya aikinshi ya karato. Koda ya gama kimtsawa cikin wasu tattausan manyan kaya riga da wondone da kuma babbar gariyarsa, kayan sun kasance farare ƙal-ƙal ne, sai zazzafan aikin kufta da akayi mishi mai blue color, kana sai hular zanna bukar daya murza bisa kanshi da yake wadace da tattausan suma baƙiƙƙirin mai sulɓi da sheƙi, hular itama farace sai ratsin blue, hakama takalman sawunshi da suka kasance irin na sarakuna ne, Agogon Daimond dake hannunshi shima yanada yanayin ɗigon blue mai garai-garai, Sai kuma ya sunkuyo ya ɗauƙi biyu daga cikin woyoyinshi yasasu a al'jihun babbar rigar tasa, jakar system ɗinshi ya ɗauka da hannunsa na dama, kana hannunshi na hagu kuma sajenshi yake shafawa a hankali har zuwa kan madai-madaicin tsabtaceccen gemunshi mai ɗan karen kyau da burgewa. A haka ya fito daga cikin ɗakin nashi. Yana fitowa cikin tamfatsen falon nashi da ya kasance yanada iyaka da bayi da hadimai duk iya karsu can bakin ƙofar babban falo bai yarda da wai bayi su shigo suyi mishi hidima har cikiba, Jamil shike kula da tsabtan sashin sirrin ɗan uwan nashi. Ido ya lumshe jin wani irin sassanyan ƙwamshi da sanyi mai ratsa zuciya daya ziyarci jiki da zuciyarshi. A hankali yake taku, har zuwa dinnin area, a hankali ya ɗan juyo, jin an jamishi kujerar. Jamil kenan. Zama yayi bisa kujerar, kana, ya miƙawa Jamil jakar system ɗin nashi. Amsa yayi ya rataya a kafaɗarshi, sannan ya matso gab kusa da ɗan uwan nashi, baƙin Tea ya haɗa mishi da zuma sai bredy wanda shima da zuma a jikinshi , wanda yasan iya abinda zai ci ya sha kenan duk da tarin. Abinci da hadiman Aunty Juwairiyya, suke kawowa dominshi ga kuma na Hadiman Hajia Mama, wanda duk Umminshi Jakadiyace ke kawosu, domin ita tana shiga har cikin falonshi ɗakin konciyarshi ne dai bata shiga, amman falo ukun nan duk tana shigarsu da kitchin da sauran ɗakunan sashin. Suna zama babu jimawa, wayar Jamil ta fara tsuwa, da sauri ya ɗauka tare da karawa a kunne, sai kuma yayi zuru-zuru da idanu ganin yadda Hammanshi ya tsareshi da fitinannun idanunshi masu sa hanjin cikinsu kaɗawa, cikin yin ƙasa da murya yace. "My love Sheykh yana kusa". Ya ƙarishe mgnar da murmushi a fuskarshi, shi kuwa Sheykh kauda idonshi yayi yaci gaba da zuƙan tea ɗin a hankali a hankali. Shi kuwa Jamil cin abinci yai haninƙan kana. Shi kuwa Sheykh ido kawai yake zubawa ƙanin nashi bai tashiba har saida yaga ɗan uwan nashi ya gama cin abincin. Sannan suka jero suka fito falo, A can bakin ƙofar shigowa babban falon suka samu sarkin ƙofa da kuma hadimai na jere a wurin suna hangosu duk suka rusuna har ƙasa har suna haɗa baki wurin cewa. "Takawarka lfy ɗan Babban Yaya jikan mai martaba sarkin Nuruddeen jika ga mai Alfarma Sarkin Musulmai Jalaluddin. Malam ɗan Malam Habibullah jinin Limamen Saudia malamai magada annabawa, jika ga ƙabilar da tafi ko wacce ƙabilar duniya d...". Hannun shi biyu ya ɗaga musu alamar amsawa gaisuwar da sukayi mishi, da kuma dakatar dasu da kirarin da sukeyin. Kana yaci gaba da taku Jamil na biye dashi a baya, Sarkin ƙofane yayi saurin rusunawa tare da cewa. "Hajia Mama ta turo jakadiya a sanar maka cewa tana buƙatar ganinka". Kanshi ya gyaɗa kana yaci gaba da tafiya, Gefen dama ya nufa, inda wani tamfatsetsen part mai tarin girma yake, a hankali hadiman dake tsaron wannan ƙofar suka fara rusunawa tare da bashi hanya da gaidashi. Tafe suke har cikin part ɗin, wani babban falo suka fara ratsawa kana suka wuce zuwa cikin wani corridor sai gasu a wani fitinenne falo mai wadatar tsabta da ƙamshi. Wasu ƴan yarane guda biyu duka mata, Suna ganinsu suka ruga a guje jikin Sheykh Jabeer suka faɗa tare da cewa. "Sabahul khair Uncle MJ". Sunkuyowa yayi ya ɗan shafa kansu tare da cewa. "Sabahul noor ya Habittey". murmushi sukayi kana suka sakeshi suka isa gaban Jamil sunkuyowa yayi ya ɗauki ƙaramar bayan sun gaidashi ne babbar ta juya da gudu tana cewa. "Ummi ga Uncle MJ". tsayawa tayi tare da kamo hannun wata kekyawar mace matashiya yar duma-duma, tayi shiga irin ta larabawa, kamo hanunta tayi suka fito falon. Murmushi ta ɗanyi tare da cewa. "Barka da safiya GARKUWAN FULANI, GARKUWAN ahlin Sitti". Fuska ya ɗan sake still bawai yayi murmushi bane, a hankali yace. "Barka da safiya". "Barka dai Sheykh Dr Garkuwa". Babbar rigarshi ya ɗan gyara tare da cewa. "Ya jikin Ya Jafar?". Kai ta ɗan ranƙwafar tare da yin rau-rau da idanunta murya na rawa tace. "Jiya kwana yayi baiyi bacciba, Sheykh, hankalina yana tashi, sabida duk randa baiyi bacciba, to kwana yake karatu yanayi yana kuka, kukan da yakeyi ɗin ne yake sashi zazzaɓi da ciwon kai, gashi ba cikin zuciyarsa yake karatunba ya wuni karatu a baiyane ya kwana karatu a baiyane babu bacci". Kanshi ya ɗan jujjuya tare da nufar kofar wani ɗaki. Jamil da Juwairiyya na biye dashi a baya. Suna shiga cikin ɗakin, da sauri Sheykh ya karisa gaban wani kekyawan mutun fari ƙal mai tarin tsabta wanda yake tsananin kama da Jamil duk da duk suna kama da juna amman Jalaluddin yafi kama da Jabeer, Jamil kuma yafi kama da Jafar. Zaune yake bisa sallaya, ya jingina kanshi da jikin gado, karatun al'ƙur'ani yakeyi cikin nitsuwa da da cikar tajwid, babu ɓata ko na ɗigo, yana karatun ne hawaye na kwaranya daga kwayar idanunshi, A hankali Sheykh Jabir yasa Hannu ya kamo hannun ɗan uwan nashi, A hankali Ya Jafar ya buɗe idanunshi ganin mutumin da shi kaɗai ke sashi yin abu yayi ko ya hanashi ya hanune ya sashi gyara zama still yana karatu. A tausashe Sheykh Jabir ya ɗan ranƙwafar da kanshi cikin salon tausayawa da muryar larabawa yace. "Sadakallahul Azeeeeeem". Jin hakane yasa wannan bawan Allah'n ya ɗago tafin hannunshi addu'o'in ya, fara karantawa kusan tsawon 3 minute sannan suka shafa a tare, Cikin wani zafi da ƙuna Sheykh Jabeer ya taune lips ɗin shi na ƙasa hannunshin yasa ya kamo na Ya Jafar ɗin, ba musu ya miƙar dashi, kan gadonshi ya zaunar dashi, A hankali ya juyo ya kalli Juwairiyya cikin sanyi yace. "Yaci abinci kuwa?". A hankali tace, "Tunda asuba daya dawo masallaci na bashi yaci abinci, kuma yanzuma na bashi ya ɗan ci". Kanshi ya rausayar kana yace. "Maganin shi fa kin bashi". Kai ta jinjina tare da cewa. "Eh na bashi maganin yasha". Jin hakane yasa Sheykh ya kamo hannun kekyawan Yayan nashi ya kontar dashi bisa gadon blanket yaja ya rufe mishi rabin jikinshi a hankali yace. "Ya Jafar kayi bacci, kaji jikinka zafi". Shiru bai kulashiba sai dai, ya lumshe idonshi. A hankali ya juyo ya kalli Matar ɗan uwan nashi kuma ƴar kawunsu yayan Mamansu yace. "Juwairiyya Nagode". Hawayen dake zubo mata ta sharce tare da kamo yaranta ta ruggumesu, Jamil kuwa tuni yaketa zubda hawaye. Cikin rawan murya Juwairiyya tace. "Sheykh ka dena gode min nimafa Ya Jafar ɗan uwanane kuma mijinane, uban ƴaƴana, to in ban kula dashiba da waye zan kula a duniya?." Kanshi ya kauda kana ya juya ya nufi hanyar fita a ranshi yanajin ko sai yaushe manyan burukan rayuwar da fatanshi da addu'o'in shi zasu ƙarɓu yana ganin daraja da girman Juwairiyya domin tayi musu tsantsar halacci ta zauna da ɗan uwanshi a matsayin majanuni, a haka suke tafiya yana zancen zuciya. Jamil na biye dashi a baya. A haka suka fito, suna tafe hadimansu na biye dasu a baya. A hankali ya ɗan juyo ya kalli Jamil da yasan yanada rauni dan Jamil yanada tausayin ɗan uwanshi duk da yanada shekiyanci amman yanada rauni a kansu abu kaɗan ke sashi kuka, Sashin dake tsakanin sashin su Jamil dana Ya Jafar suka wuce wanda nanne sashin Sheykh, sashin su Jamil ɗin suka shiga. Kai tsaye suka wuce har cikin bedroom. Tsaye suka sameshi yana taje suman kanshi mai yawa ga wondo iya ƙugu duk rabin boxes ɗinshi a woje ga wondon da rabin jiki duk woje waishi kirezi ko? da alamun fita zaiyi. "Meya hanaka zuwa masallacin jumma'a da wuri jiya? Waɗannan kolaben barasar na waye ne?". Sheykh ne ya jero mishi tambaya biyu a lokaci guda, A hankali Jalal ya juyo cikin shakku da shayi da kwarjin Hamma nasu ke sasu ji yace. "Mamace ta aikeni, jiya shiyasa na dawo a ƙurerren lokaci. Kolaben barasar kuma nasu Ashid ne, na kwace ne lokacin da suka saya, dan karsu sha". Kanshi ya gyaɗa dan ya gamsu ya kuma yarda dan yasan duk rintsi ƙanennshi basa mishi ƙarya. Cikin faɗa yace. "Ka kula da salla, ka tsaida ita kan lokacinta, kasan irin abokan da zakayi yawo dasu, ka tabbatar kaikeyi nasara akan juya halaiyarsu daga mummuna i zuwa kekkyawa. Shiyasa ban hanaka mu'amala da suba, domin manzon Allah yace. "Mutun ɗaya ya shiryu ta dalilinka, tarin ladan yafi a baka tarin jajayen raƙumi. Kada ka bari suyi nasarar juya rayuwarka daga kekkyawan i zuwa mummunan. Kanshi ya gyaɗa cikin ladabi yace. "In sha Allah". Daga nan suka juya baki ɗayansu, Kai tsaye sashin Hajia Mama suka wuce. Inda hadimanta sukayi musu iso, Har cikin bedroom ɗinta suka shiga, A bakin gado suka sameta, zaune, yayinda baiyawarta Mansura keyi mata tausa. Murmushi tayi tare da kallonsu yadda suke a jere, koda maƙiyinsu ne sai sun burgeshi sun bashi sha'awa yayi fatan inama da ƴaƴansa ne. Kan dantsatsetsen shimfiɗar kilisa mai kyau da zanen tsuntsuwar ɗawisu, suka zauna, Cikin kula tace. "GARKUWAN FULANI, Jamil, Jalal, Allah yayi muku al'barka". Amin Amin, Sheykh da Jamil suka amsa, Jalal kuwa shiru yayi, Ita kuwa Hajia Mama murmushi tayi tare da cewa. "Babanmu mai Al'farma Sarkin Musulmai Jalaluddin meya farune naga fuskarka a haɗe?". Kanshi ya girgiza alamar. "Babu". Shi kuwa Sheykh ido kawai ya zuba kan wayarshi, Jamil ne ya ɗan gyara zama, tare da cewa. "Mama Abba fa". Kai ta ɗan jinjina tare da cewa. "Abinda yasani nemanku kenan, Abbanku ya tafi Abuja jiya da dare, yanzu kuma Gimbiya Samira zatabi bayanshi". Shiru Sheykh yayi a ranshi yake jinjina al'amarin mahaifinsu. Babusu a cikin dukkan sabgogin rayuwarsa komai nashi saidai suji a bakin Hajia Mama ko kuma a jaridu ko gidajen Radio ceɗi meɗinshi da amaryarshi Gimbiya Samira ƴar sarkin Nokan ce ita kuwa mijinta shine rayuwarta babu ruwanta da sabgar kowa. Sam Abba bai shaƙu dasuba da wuya ka ganshi zaune dasu yana hira dasu kamar uba da ƴaƴan shi. Saɓanin Maimartaba ko meye zaiyi Sheykh zai sani shine mutumin da yake shawara dashi akan duk abinda ya shafi addini. Kanshi ya ɗan kauda tare da cewa. "Allah ya dawo dashi lfy". Amin Amin sukace baki ɗayansu, Cikin kula yace. "Hajia Mama Affan fa sai yaushe zai dawo?." "Next month?". Ta bashi amsa a gajarce. A gogon hannunshi ya ɗan kalla kana a hankali ya miƙe tare da cewa. "Zan wuce Hospital shugaban ɗaliban makarantar ya kirani cewa sunada mara lafiyar da take buƙatar kulawar gaggawa". Kai ta ɗan rausayar tare da cewa. "A dawo lfy". Amin Amin sukace kana suka fita suka tafi. Daga nan kai tsaye FADA suka nufa. Inda sarkin fada yayi musu iso zuwa ga Maimartaba kakansu. Suna shiga suka samu fada na cike da dattawa karsu Waziri, Matawalle, Galadima, Wambai, Ɗan isa, ɗanm' buram, sairkin Dogarai sarkin Gida, da kuma Duba gari, kana, sai kuma hadiman dake tsaye bayan sarki sunayi mishi fifitar sarauta da maficin fiffigen Ɗawisu. Farin dattijo bafulatani, mai cikar haiba. Yana cikin manyan kaya na sarakai, wanda al'kyabbarsa kaɗai ta kai kuɗin mallakar wani gidan, A gabanshi suka zauna gaba ɗayansu uku, A hankali Sheykh yasa tafin hannunshi kan rumfar sawun kakan nashi da suke kan wani tim-tim mai girma da masifar taushi. taɓa sawun kakan nashi yayi tare da cewa. "Barka da hantsi Maimartaba, ya sawun naka?". Duk maganar nan da yayita a hankali yake yinta ko Jamil da Jalal dake gefenshi basujiba. Shi kuwa Maimartaba hannunshi ya ɗaura kan tsakiyar kan Sheykh wanda tun kafin ya zauna ya tura hulanshi ya koma baya, dafa tsakiyar kanshi yayi tare da cewa. "Alhamdulillah". Sai kuma ya kalli Jamil da Jalal da suke gaidashi, dan su sai yanzu suka haɗu dashi tunda gari ya waye, Tsaɓanin Sheykh da kullum tare suke dawowa masallaci sallan asuba daga nan kuma ɗakin hutunshi suke shiga kakarsu mace ta kawo musu abin taɓawa. Bayan sun gaggaisa ne da mutanen fada, suka fita suka tafi. Sashin kakarsu Gimbiya Aminatu suka nufa. Basu da hijabi da sashin kakar tasu shiyasa kai tsaye suka shiga a falo, suka sameta, Da alamun yanzu ta fitito Dan ga al'kyebba a jikinta ga kuma hadimanta a zagaye da ita. Cikin tarin so da ƙaunar Jazlaan ɗin nata take kallon su, Murmushi tayi tare da cewa. "Miskili kafi mahaukaci ban haushi, kai dai kaji abinda malam zaice kada kace zaka binciki aikin malam". Shiru Jamil da Jalal sukayi, shi kuwa Sheykh ido ya zuba mata. Ita kuwa rausayar da kai tayi tare da cewa. "Eh mana kaji abin da malam yace kada ka duba aikinshi, dazu na gama jin wani wa'azin ka da kayi kan falala da ni'imomin dake cikin aure, kana bayani duk maluntar mutun darajarsa bata cikaba in bashi da aure. Sai najima wa'azin kamar da kanka kakeyi. Meyasa ne Jabeer kayi niyar yin aure mana ka cikata nasabarka da kamalarka da martaba da darajar ka data masarautar Joɗa". Jalal ne ya miƙe tare da cewa. "Ke in anzo gaisheki sai ƙaƙale-ƙaƙalen zance tsiya kika iya ni na tafi dan inada aikin yi". Haratanshi tayi tare da cewa. "Tafi daga nan mai ƙugu kamar buzuzu hegiyar masifa". Hararanta yayi kana ya juya ya fita. Ita kuwa Gimbiya Aminatu. Jamil ta kalla wanda shima ya miƙe yabi bayan Jalal. Shi kuwa Sheykh numfashin ya fesar tare da cewa. "Maganinki ya kare koda saura?." Da sauri tace. "Yauwa magani ya ƙare a kawo min wani". To yace kana ya mike ya fita. Daga bakin harabar sashin kakar tasu, Fadawanshi ke biye dashi a baya har parking lot ɗinsu mai ɗan karen girma da kyau, duk zagaye suke da fulawowi masu kyau. Wasu tsala-tsalan motocine da a ƙalla sun kai su takwas sai sheƙi sukeyi. Da sauri Ado drevernshi ya buɗe mushi ƙofar wata mota mai ɗan karen kyau wacce bada ita ya fita jiyaba, dan ita sai ranakun jumma'a-jumma'a yake hawanta, wannan ta yau mai kalar ruwan tokace sai sheƙi takeyi, yana shiga sauran fadawanshi suka yi yunƙurin shiga motocin dake jere a wurin a gefen wurin wanda dasu akeyi mishi rakiya. Da sauri ya ɗaga musu hannu, cikin in in narsa da in yana saurin mgna yake fitowa yace. "Kkku ba bari ba'a bukatar rakiya". Da sauri suka ɗan rusuna tare da haɗa baki wurin cewa. "Aje lafiya a dawo lfy Allah ya kiyaye gabanka da bayanka Sheykh". Amin Amin yace a taƙaice kana ya shiga motar, sarkin ƙofa ya rufe mishi marfin sannan Ado yaja suka tafi. Suna fita kai tsaye Babbar jami'ar dake cikin babban birnin Ɓadamaya suka nufa. A can cikin makarantar kuwa, Kasan cewar duk ɗaliban jami'ar sun san babban Doctor zai shigo yasa gaba ɗaya harabar asibitin dake cikin jama'ar cika da taron tsala-tsalan ƴan mata ƴaƴan manya, duk mai matsalar lfy tana fatan ya dubata sabida ƙwarewarsa. A hankali wasu ƴan mata biyu suke taku a farfajiyar shiga asibitin, bisa alamu duka ɗayar bata da lfy dan ɗayar na rike da hannunta, kuma a hankali suke tafiya. Cikin tausayawa ɗayar ta kalli wacce ta riƙewa hannun a hankali tace. "Garkuwa ki daure kiyi sauri mu isa, wallahi zamu samu layi da yawa, kuma wannan Sheykh ɗin kasaitarsa nada tarin yawa, yanada doka da ƙa'idoji da tsari, yanada tsauri kan tsare kima da darajar addininshi, daga shigar jikinki in kinyi kuskure kaɗan na shigar kima wallahi bazai dubaki ba. Shiyasa ahlul kitabi dake cikin makarantar nan suke masifar shakkarsa, kinga gashi azahar ta kusa, kuma wallahi ko sarkin garin nanne yazo ya dubashi in dai lokacin salla yayi to tashi zaiyi ya fita ya barshi, gashi shiru-shiru da ido yake hukunta mutun". A hankali wacce aka kira da GARKUWA tasa hannu ta gyara niƙab ɗin dake fuskantar, wacce ta dace da wata kekyawar arabian gawn dake jikinta wanda dama shigartace haka kullum sabida gudun kada wani ya ganta ya tsaida ita dan tasan duk namiji daya nuna yana sonta har lahira ake kasheshi wanda kuma duk Rugarsu akeda yaƙinin Ba'ana ne dan mutunne mai masifar baƙin kishi, yasha sanar mata a kanta zai kashe kowa ba damuwarsa bane da fari duk wanda ya nuna yana sonta da bulalin shaɗi yake korarshi, to yanzu duk wanda yace yana sonta sai dai a wayi gari ya rasu. Cikin sanyin muryar dake nuna azabar da takeji, murya na rawa tace. "Rafi'a, bazan iyaba marata ciwo kamar zata ɓalle, ki sakeni kije ki amsar mana foldana kafin in ƙaraso". Jin haka yasa Rafi'a cewa. "Zaki iya tahowa ke ɗaya?". Kanta ta gyaɗa mata a hankali. Hakan yasa cikin sanyi ta saketa kana ta wuce cikin Hospital ɗin da sauri. Dai-dai lokacin kuma motar Dr Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero ta kutso kanta cikin farfajiyar. Bayan Ado ya dai-dai ta parking ne a cikin rumfar adana motor da aka rubuta Dr Jabeer a samanta. Ado ne ya fito da sauri ya buɗewa, Sheykh marfin motar, a hankali ya zuro ƙafafunshi ya fito. Cikin nitsuwa ya fara taku yana ratsowa cikin farfajiyar Hospital ɗin. Kasan cewar ta gabas ya fito Aysha kuwa ta yamma ta fito sai ya zama suna fuskantar juna. Yayinda sai sun haɗu wuri ɗaya zasuyi kwana sun fuskanci kudu inda nanne mashigar cikin asibitin. A hankali suke takowa suna fuskantar juna. Sosai ya zuba mata ido sabida ya lura gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi alamun tsananin ciwo takeji gashi a hankali take taku. Ita kuwa Aysha, tafiya takeyi da kyer sabida azaban ciwo da mararta keyi. Kanta a sunkuye take tafiya, hakan yasa bata san da mutunba a gabanta. Da sauri Sheykh ya tsaya sabida wani irin bugawa da ƙirjinsa ya fara. Ganin ta tunkaroshi gadan-gadan, kuma daga yanayin tafiyarta tamkar zata faɗi ƙasa. Ganin tayi wani irin sunkuyawa tasa hannunta duka biyu ta damƙe mararta da takeji tamkar caccakarsa akeyi da allura. Gefe ya ɗan tsaya yana kallon ikon Allah, ita kuwa GARKUWA rumtse idanunta tayi da karfi, wata fitinenniyar zuface ke tsastsafowa tako ina, a hankali ta fara buɗe idanunta jin kartan da mararta keyi ɗin yana ɗan lafawa, a hankali ta zubawa kyawawan sawunshi idanu, cikin sauri ta ɗago kanta, ganinta tsaye gab kusa da namijin da bata saniba ne yasata ja da baya da sauri tare da miƙe tsawonta cikin firgici murya na ɗan rawa tace. "I'm very sorry". Bai kulata ba, sai kauda kanshi da yayi gefe. Ita kuwa Garkuwa cikin sanyi tace. "Dan Allah kayi haƙuri". Kai ya ɗan gyaɗa mata alamar Uhumm. Ita kuwa cikin sanyi tace. "Uhumm kaima Doctor Sheykh ɗin kazo ganin ne?". Da mamaki ya ɗan kalleta da gefen idonshi, sai kuma ya ɗan juyo kanshi kaɗan jin muryarta a sanyaye taci gaba da cewa. "Muyi sauri mu shiga ance yanada shegiyar ƙasaita da isa, wai ko sarkine yake dubawa in dai lokacin salla yayi tashi yakeyi ya fita". Cikin tarin mmki ya ɗan waro kyawan idanunshi tare da cewa. "Umh". Ita kuwa Garkuwa, hannu tasa ta matse mararta tare da cewa. "Muyi sauri mu shiga, kaga kuwa kayi sa'a kayi shigar mutunci dan ance shi baya son ganin musulmi da lalatacciyar shiga, ancema in mace tayi shigar banza baya dubata, kaji shishshigin mutunfa ko meye ruwansa da rayuwar wasu ai kowa yayi mai kyau dan kansa ko?". Rolling Ball eyes nashi yayi tare da gyaɗa mata kanshi. Kana ya tsuke fuska yaci gaba da tafiya. Ita kuwa Garkuwa cikin yin ƙasa da murya tace. "Uhum shidama akace shine shugaban tuzuran ƙasar nan, yana zaune baiyi aureba, ai zama ba aurema ba kyau tunda dai yanada damar yi ko?". Ɗan tsagaita takunshi yayi tare da cewa. "Hummh". A hankali ta bishi a baya cikin yanayin muryar mara lfy tace. "Dan Allah ka tsaya in rigaka shiga kar yace sai ya dubaka kafin ya dubani". Dai-dai lokacin kuma suka kutsa kansu cikin asibitin. Da sauri Garkuwa ta zazzaro idanunta baki ɗaya, tare da dafe ƙirjinta ganin gaba ɗaya Nurses ɗin dake ƙoƙarin fitowa sunyi maza suka koma baya, tare da rusunawa suka haɗa baki wurin cewa. "Barka da hantsi Sheykh". Kai kawai ya gyaɗa musu yaci gaba da tafiya, har ya shiga cikin wani ɗan corridor ya shiga wanda zai sadashi da tamfatsetsen Office dinshi ba tare daya ratsa ta cikin Reception ɗin su ba. Ita kuwa Garkuwa gaba ɗaya tsorone ya rufeta, Gefen Rafi'a taje ta zauna wanda a take kuma mararta taci gaba da murɗawa da kartawa. Da ƙarfi ta damƙi hannun Rafi'a. Cikin tausayawa Rafi'a tace. "Sannu, in sha Allah bazamu jimaba za'a kiraki, dan na nemi al'farman sauran sun yarda Khadija Nasir Shugaba ce aka shigar, ƴar gwamnan, ba lfy". Kai kawai ta iya gyaɗa mata, sai taune lips ɗinta da takeyi. Shi kuwa Sheykh yana shiga Office dinshi, ya fara aikin daya kawoshi cikin ikon Allah kuwa Khadija ta samu sauƙi tunda ya dubata aka bata magunguna. Mutun biyar ya duba, na shida kuwa, Aysha ce. Koda aka kira sunanta jiki a mace ta miƙe ta nufi inda take ganin ana shiga. Nurse namiji na gabanta. A haka suka shiga, Ajiyan zuciya taja a hankali sabida tsaruwa da kyau da tsabta da ɗan karen ƙamshin da ya ziyarci hancinta, su sukasa ta son bin Office ɗin da kallo amman ina ciwo bazai bartaba. A hankali ta iso gaban table ɗin baƙin Glass dake gabanshi. Ɗaya daga cikin kujerun biyu dake gaban table ɗin ta zauna. Ƙasa tayi da kanta cikin tarin ciwo da fargaba. Shiru tayi zaune bisa kujerar tayi ƙasa da kanta. Shikuwa Sheykh ko kanshi bai ɗago ya kalli inda takeba wanda wannan al'adarsace da wuya ya kalli mutun, mafiya yawan lokuta yafi kallon mutun ta cikin gilashi table ɗinshi, shiru Office ɗin sai sautin A/C da yake busawa, shima kanshi Nos ɗin sai ya gaza abin cewa, Ita kuwa Aysha pat-pat haka zuciyarta ke duka, gashi tana jiyo mararta na fara kartawa. Kusan tsawon 1 minute suna a haka, cikin dakiya da rauni ta ɗan nago kanta ta kalleshi, Ga mamakinta sai taga asalima hankalinshi baya kanta, yana dai murza yatsunshi da alamun tasbihi yakeyi. Shi kuwa Sheykh duk abinda takeyi yana ganinta ta kan glass ɗin, Cikin sanyin murya tace. "(Jam ɓanɗuna). Ina kwana". Shiru bai kulataba har sawon wasu daƙiƙun har ta fara zaton ko bai jita bane. Da sauri ta ɗago kanta jin yayi mata magana, cikin wata sahihiyar murya a takaice yace. "Suna?". Cikin fargaba ta tace. "AYSHA ALIYU GARKUWA....! *Uhummm wani kayan sai amale, wani littafin yafi ƙarfin a baka lbri ka iya haƙura baka karantaba. GARKUWA YA WUCE ZATON MAI ZATO* By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 5 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *LITTAFIN GARKUWA na kuɗine ga masu buƙatar biyan kuɗin samun damar karantawa al'ummar Niger da kewaye ga number da zakuyiwa mgn +22799460151 biya ɗari uku, ko dubunki ɗaya kacal un saki a group. Gareku mutanena mutanen ƙasata in kina buƙatar GARKUWA ga hankaɗo min ɗari uku kacal! ko dubu ɗaya rak! Ta asusuna na Jaiz bank, 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyan ki ta number ta 09097853276. Mutanen Ayyah SP Group bana son KATI. Kuma al'ummar 300 in ba dole ba yaseen bana son KATI, to amman in babu yadda zakiyi, nasan akwai irina ƴan ƙauye, ba POS. Kuma kuna son karantawa, to hankaɗo katin mtn ɗinki na darinki uku kisha karatu. Allah ya nuna mana ƙarshensa lfy kamar yadda ya nuna mana forkonsa lfy. ALLAH ya bamu haƙurin zama da juna* ```Fans 1&2 sarakan surutu, Ina gaidaku ina ji daku har cikin ƙoƙon raina. SP Group, inai muku jinjina dubu-dubu.Fans 3 Allah ya rayamu ku cika maƙil. Group ɗin kurame kuma ina sane duku ina kuma jin daɗin nitsuwarku ba surutu. i love all my fan's irin lodi-lodin nan mafa``` ```Gyaran amare uwar gidaye masu jego da masu tada komaɗa da sabunta dararen satin forko na amarci. Ku garzayo gani gareku da tsaraba kamarsu, tsumin Tsartai, sa buzu kuwa, garin babambaɗe, garin maɗi mai maɗemaɗin ni'imomi, bunbar ke ɗaya, gumbar Mali mai taken kolli mai sheƙi sai dai gsky ita tanada tsada, gumbar Uku csrmazaƙoi, gumbar haɗin inabi dabino kwakwa riɗi. Akwai haɗin ilan waddi, duk ba fula tani in yaji ilan waddi uhumm, akwai garin Belɗam yel, akwai tsumin ta baje, akwai kwanon ƙasaitacciyar mace, akwai kirɓeɓɓen tsumin domin mutanen nesa, akwai mgnin sanyi Infection, akwai butar sirri mai. abubuwan dai da yawa, gani ya kori ji, in kina buƙata kiyi min mgn ta wannan number 09097853276 kada ki kira dan ban fiye daga kiraba, gwara kimin mgn ta whatsapp in kinga bana kusa Turo min text message ta in-box``` A hankali ya ɗan ɗago ƙwayan idanunshi ya kalleta. Kanta a sunkuye hannunta biyu duka na kan mararta cikin wani, irin yanayi take wanda yake nuni da tana cikin wahala. A hankali ya maimaita sunan cikin zuciyarshi. "AYSHA ALIYU GARKUWA! To GARKUWAN ina? GARKUWAN meye?." A fili kuma kauda idonshi yayi daga kanta ya maida idanunshi kan tarin foldan dake gabanshi, wanda sunanta ke rubuce akan na samanshi yaja da yatsu biyu. Shafin forko ya buɗe a folder kana, yasa hannu cikin wani ɗan abu mai kama da kofi wanda yake cike da biro masu kyau da tsadar gaske. Tsiraran idanunshi ya lumshe sabida wani irin bugu da yakeji zuciyarshi nayi tun sanda ya hango yarinyar har zuwa yanzun nan da take gabanshi a zaune. Rubuce-rubuce yayi a ciki irin nasu na Doctors masu kama da tafiyar wahainiya. Kanshi ya kuma ɗagowa ya kalleta a fizge da gefen idonshi, sunkuyar da kanshi yayi tare da cewa. "Meke damunki?". Cikin shessheƙan wahala da son danne kukan da ke son kabce mata tace. "Marata, da bayana". Kai ya ɗan jujjuya tare da kallon shekarunta dake rubuce a cikin folder din, Yar shekara ashirin kuma da ƙorafin ciwon baya, cikin dakekken sauti yace. "Yaushe ya fara miki ciwo?". Hannu tasa ta cikin niƙabin da yayiwa fuskarta ƙawanya ta share hwayenta a hankali tace. "Shekara uku da suka wuce". "Meyasa bakije asibitiba tun lokacin?". Ya tambayeta a daƙile. "Ina zuwa asibiti duk sanda ya tashi". "Kamar yaushe da yaushe yake tashi?". Ya jefo mata tambayar kamar yadda zuciyarshi ke harbawa da ƙarfin tsiya da kuma sauri-sauri, Kai ta sunkuyar tare da cewa. "Duk ƙarshen wata daga 21 zuwa 25". Shiru yayi kamar bai jitaba sai wasu rubuce-rubucen ya kumayi. Saida ya gama sannan ya tura mata folder ɗin gabanta. Jikinta na rawa tasa hannu ta ɗauki folder ɗin, ta yunƙura zata tashine, ya basu damar samun kusanci da juna, da sauri ya rumtse idanunshi sabida wani irin azabebben bugu da zuciyarshi keyi tamkar zaiyi tsalle ya faɗo woje, cikin zuciyarshi yake maimaita. "Innalillahi wa innailaihi rajiun." A hankali ya buɗe kyawar kyawan idanunshi jin bugun zuciyarshin ya fara yin ƙasa-ƙasa, ido ya zubawa mata ganin ta juya tana tafiya, wani abin al'ajabin a gareshi shine duk taku ɗaya da zatayi tana nesanta dashi sai yaji zuciyarshi na tsinkewa yana bada wani mugun bugun ras-ras, yayinda bugun tsinkewanta kuwa yaketa dai-dai-ta, Cikin mamaki ya sunkiyar da kanshi yana kallon yadda takeyin taku, tana riƙe da mararta, taje gab bakin fofar fitane, Taji wani irin murɗa da kartan da mararta ya farane yasa ta sakin wani sauti mai cike da wuya. "Wayyoooooooo Allah na, Wayyo Ummeyna cikina". Da sauri nurse ɗin nan yayi kanta tare da cewa. "Isah Allah rena joɗu". Ya ƙarishe mgnar da nuna mata kujerun farin ƙarfe dake gab da bakin ƙofar. Bata da zaɓin daya wuce ta zauna ɗin, domin gaba ɗaya ƙafafuwan ta rawa sukeyi alamun bazasu iya ɗaukar nauyinta ba ga duhun daya rufe mata ido. Sunkuyowa Nos ɗin yayi ya amshi folder kana yace. "Zauna bari inje Pharmacy in amso miki magungunan da alluran sai ayi miki". Kai kawai ta iya gyaɗa mishi tare da bashi. Har ya fita sai kuma ya dawo yace. "Ok sir". Jin Sheykh Jabeer yace mishi ya turo ta gaba Da sauri ya fita. Shi kuwa Sheykh Jabeer, tasbihinshi yaketayi da yankan yatsunshi yake ƙidayar, sabida, suma yatsun su kasance cikin bautar Allah shiyasa yake ƙidayar amman ba don wai yasan adadin salati da hailala da istigifarin da yakeyiba, wannan ubangijine kawai masanin adadinsu. Bayan fitar Nos ɗin da kamar 1 minute wata, Kekyawar budurwa ta shigo, cikin yauƙi da ƙasaita, sai wani irin masifeffen ƙamshin da take zubawa. Ƙarasowa tayi gaban table ɗin nashi ta zauna, cikin yauƙi da korkosa tace. "Barka da rana Al' Sheykh". Ko inda take bai ɗaga ido ya kallaba, ya lura ya gane akwai wani abu tattere da yarinyar, dan mafi akasarin ranaku sai tazo, wai bata da lfy, kuma takan zo da ciwuka mabanbanta ne. Sanin ba musulma bace yasashi ƙara tsuke fuskarsa tamkar zatayi aman wuta, a zafafe yace. "Name". Cikin yauƙi da son isar da aikin da aka bata tasa hannu ta jawo foldan ta dake sama tura mishi gabanshi tayi, Cikin harshen hausa da tasan bai fiye son English language ba a rayuwarshi a hankali tace. "Breast ɗina kemin ciwo, har bana iya sa bra." Sai kuma tayi ƙasa da mayafinta dake jikinta, hannu tasa kan zip ɗin gaban rigarta tana ƙoƙarin zugeshi ƙasa tare da cewa. "Kalli Nipples ɗin sun.... Cikin tsananin firgita da tsoro, ta miƙe da azaban ƙarfi, jin yadda yasa hannunshi ya bugi table ɗin da azaban ƙarfi wani irin gigitaccen tsawa mai firgitarwa ya daka mata tare da cewa. "Tashi, daga gabana". Karkar jikinta ke tsuma sabida kwarjinshi da tsoronshi sun daki zuciyarta da take cike da fajirci dama dan bata kallon fuskarshi ne ta iya faɗin waɗannan kalaman ma. Dai-dai lokacin kuma, Nos ɗin nan ya shigo, ganin yadda AYSHA ta gigice taketa karkarwa, alamun tana son ta miƙe kuma ta kasa tashi. Shi kuwa Sheykh foldan ɗin Rabeca ya jawo wani rubutu yayi saman foldan ɗin kana ya tura matashi gabanta cikin zafi da tsauri ya nunata mata hanyar fita tare da cewa. "Fice min daga Office daga yau in kina buƙatar ganin Dr kije gun Dr Ute, shi zakiyiwa duk sakarcinku na al'jihun baya. Ba niba, sannan daga nan ki wuce Zaria kije asibitin Shika domin ina zaton breast cancer kike dashi". Da sauri tasa hannu ta ɗauki foldan ɗin, gaba ɗaya jikinta na rawa, juyawa tayi ta fice tare da yin magana can ƙasa yadda bazai jitaba tace. "Allah ya sauwaƙa Ni bani da breast cancer, mugun bakin kawai." Shi kuwa Sheykh Jabeer komawa yayi ya jingina da jikin kujerar lumshe idonshi yayi a ranshi yake haɗa kalaman da yaci karo dasu a safiyar yau. Kakarshi tace mishi, aji mgnar Malam kada a duba aikinshi, ta jaddada mishi, wai yayi aure, kana wannan mayyar yarinyar da in tana kusa dashi zuciyarshi ke barazar fashewa, kuma tace mishi wai shine shugaban tuzuran ƙasar nan baki ɗaya. Tabbas wannan shaidace na abinda ake faɗa a cikin gari a kansa kenan, yaji ya sani Sitti ma da take son suje saudia wai so take ya zaɓi matar aure a can, ga wannan kafurar da ya san turota akeyi ta tallata mishi kanta, don a samu cinikin jarida ya hauhawa ta hanyar buga kanun labarai cewa, Sheykh mazinacine ko kuma mata yakebi shine ya hanasa aure. Jingina kanshi yayi da kujerar tare da mgn a zuciyarsa. "Ya ilahi ya mujibadda'awati". Ta yayane ta inane wa zai gayawa cewa, shifa yanada banbanci da sauran maza, ba kamar kowa yake ba, taya zai gaya musu ko zai samu a daina binshi da kalmar yayi aure, me zaiyi da mace ta yaya zai fahimtar dasu su barshi ya huta. Wannan shine nazarin da yakeyi cikin zuciyarshi, Ita kuwa Aysha ido ta tsurawa, ƙasan kujerar da yake zaune a kai tana kallon wani al'amari mai cike da ruɗarwa. Ido ta rumtse sabida bazata iya jurar ganin wannan abun ba. A hankali Nos ɗin nan ya matso gabanshi, magungunan da alluran daya amso ya miƙa mishi su. Cikin sanyi yace. "Sir ga magungunan". Kanshi ya ɗan tankwarar tare da cewa. "Kira Dr Ruƙayya tazo ta mata alluran". A hankali yace. "Sir na duba duk sun tashi, sabida babu kowa. A Reception ɗin, mune kadai muka rage". Kanshi ya jinjina, don shima yanzu zai tafi, sabida akwai gidajen likitocin a nan kusa koda shi ya tafi Dr Ruƙayya da Dr Ute suna nan cikin makarantar. Ta gefen idonshi ya ɗan kalli Aysha daketa fama da ciwo, Ganin Nos ɗin na haɗa allurar ne yasashi, fara tattara woyoyinsh dake bisa table ɗin. Shi kuwa nos ɗin. Yana gama haɗa alluran ya nufi inda take, tare da cewa. "Gyara in miki alluran". Cikin sanyi tace. "To". Yana isowa gabanta yace. "Dole ai sai kin tashi tsaye, kinga doguwar rigace a jikinki kuma sai kin naɗeta". Ido ta ɗan zuba mishi ta cikin niƙabin tare da jujjuya kai a hankali tace. "Um ummm". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "Tashi mana sauri mukeyi lokacin sallah ya ƙara to". Shi dai Sheykh ido ya zubawa bayan Nos ɗin yayinda ita kuwa yake kallon gefenta, cikin bada umarni yace. "Kuzo". Da sauri Nos ɗin ya juyo ya nufoshi, hannu yasa ya amshi allurar, kana ya ɗan kalleta a fakaice yace. "Zo nan". A hankali ta taso cikin sanyi takeyin taku tana matsoshi. A take kuma bugun zuciyarshin ya fara hauhawa yana komawa matakin sama. Taku biyu tayi ana uku yaji ƙirjinshi ya bar tsinkewar da yaketa yi ɗin, sai kuma bugun da yakeyi da sauri-saurin ne yaketa tsananta. Taku takwas tayi ta iso tsakiyar Office ɗin, ido ya fara jujjuyawa kan table nashi yana mai jin wani masifeffen bugun zuciyarshin dayasashi hatsala cikin ɗan ɗaga murya yace. "Ke da Allah kiyi sauri". Jin hakane yasa ta kara saurinta, ai kuwa da sauri ya dafe ƙirjinshi lokacin da ta iso gab dashi, cikin ranshi ya kuma cewa. "Hasbunallahiwani'imanwakil". A zahiri kuwa, da kai ya nuna mata ta kuma matsowa, ba musu ta matso, yatsarshi ya jujjuya mata alamun ta juya mishi baya, still babu musu ta juya, a hankali ya murza kujerar da yake kanta, ya juyo ya fuskanci bayanta, dai-dai saman mazaunanta ta sama ta ɗan gefe kaɗan, ya saita, tsinin bakin allurar, cikin iyawa da gwarewa dan salonshi ne baya taɓa yarda ya kalli fatar jikin wanda zaiyiwa alluran ta saman tufafinka yake zira allurar, shiru tayi tana jin yadda, allurar ya ratsa dogon rigar jikinta ya bada sautin tub alamun ya huda rugar, a hankali ta kuma jin ya huda, dogon wondon jikinta tub, sai kuma taji ya sauƙa kan pantien jikinta, daga nan taji ya ɗisa bakin allurar kan fatarta, rumtse idanunta tayi da azaban ƙarfi sabida, wani zafi da taji yana ratsata, bawai tana tsoron Allurar bane, sai dai hannunshi yanada masifar zafine, kana shina ruwan alluran irin mai, mai-mai ɗinanne kuma duk cikin allurai yafi zafi. Da ƙarfi tace. "Wach Allah na zafi-zaffi." Wani irin azaba taji lokacin daya fara cusa mata ruwan allurar a jikinta, babu zato babu sammani yaji tasa hannu damanta ta cabki hannunshi dake mata alluran hannunta na hagu kuwa yarfashi take tare dasa kuka da sauti tace. "Wayyo Allah na, ka bari bana so zare Allurar nan zafi nakeji". Ta ƙarishe magar da zurma sakalin ihu". Bugawa da zuciyarshi keyi yana bada sautin dib dab dib dab dib dan shine ya kusan hallakashi lokacin data riko hannunshi, da sauri ya tura mata ruwan kana ya zare Allurar da ƙarfi. Sannan ya miƙe tsaye, sabida muddin yana kusa da ita babu makawa wata ƙil zuciyarshi zata faso ƙirjinshi ta fito woje. Wani dogon tsaki yaja tare da juyawa ya bi gefen Nos ɗin ya fice. Itama da sauri tabi bayanshi bayan tasa hannu ta amshi ledan magungunan. Shi kuwa da sauri yake tafiya sabid iya yedda yake nesanta da ita iya yadda kirjinshi ke dai-dai ta bugawa, sai kuma tsinƙewa da zuciyarshi keyi babu ƙaƙƙautawa. Ita kuwa AYSHA da sauri ta nufi sashin makwancin ɗaliban Hostel dake cikin makarantar sabida ta fara jiyo alamun bakonta ya iso. Baba Ado kuwa drevernshi yana hangoshi ya tashi ya buɗe mishi marfin motar, yana zuwa, ya shiga, maida kofar Baba Ado yayi ya rufe sannan ya shiga yaja motar suka fice daga harabar asibitin. Ita kuwa Aysha tana shiga Side ɗinsu ita da Rafi'a, ta samu Rafi'a bata falo da alamun tana kitchen nasu, dan tajiyo ƙamshi alamun tana ɗan dafa musu abinda zasuci ne. Kai tsaye bathroom ta wuce, tabbas kuwa baƙon ya iso, dan haka ta nitsu ta gyara jikinta, bayan ta gama ne ta miƙe a hankali ta kwance niƙabin tare da fara zare dukkan kayan jikinta dan yin wonka, Aysha farar ba fullatanace irin farare ƙal-ƙal ɗin nance, gashin kanta kuwa mai tarin yawa da tsawone baƙine sit mai sheƙi, yanada cika, jikinta ɗan fiyau, sai dai tanada welcome and bey bey masu girma da cika, cikinta kamar babu hanji a ciki ɗan fiyau dashi, breast ɗinta tirtsa-tirtsane masu cika tab-tab kuma irin mai gindin tasa ɗinnan wanda da alamun ba masu zubewa bane, domin suna nan cas dasu, kamar zasu tsone idon mai gani, tanada tsukekken ƙugu da kyawawan mazaunai, sawonta dai-dai musali baza'ace mata doguwa ba sam, kuma baza'a ce mata gajera sosaiba in tana kusa da dogo dai za'a iya kiranta da gajera. Fuskarta kekyawa ce irin kyan da babu namijin da zai gani ya cire ido, hancinta dogo har kan ɗan ƙaramin bakinta mai jajayen tausasan laɓɓa idonta manyane sai dai ba ƙattiba, zirin idonta wurinda akesa kolli jane mai kyau, shiyasa yake ƙara baiyana farin idonta bakin ciki kuwa bakine sitik sai dai ɗan ƙaramin ɗigon cikin bakin shi kuma ruwan ƙasane wanda yakeda sirri namu samman. Gashin idonta zara-zarane, gashin girarta kuwa irin mai W ɗin nanne kamar na Kajol, bi ma'ana yana haɗe bisa karan hancinta, Tanada fararen haƙora masu kyau suna jere reras dasu tanada dimple ɗinta mai ɗan karen kyau. Idanunta kuma ko yaushe kamar maijin bacci suke. Wonka tayi kana tayi al'wala dan ko bata salla bata zama babu al'wala. Tana fitowa ta kimtsa jikinta kana ta zura tattausan doguwar riga. Tana kokarin fitowa falo Rafi'a na ƙoƙarin shigowa da sauri Rafi'a ta zaro ido tare da cewa. "Yaushe kika dawo?". Hararanta ta ɗanyi tare da cewa. "Ba dai kin gudo kin dawo kin barni ni ɗaya ba". Cikin tausayawa Rafi'a tace. "La wlh yanzu nake ƙoƙarin komawa, na dawone in ɗan dafa mana abinda zamuci in mun dawo, sabida naga rabonki da abinci tun jiya, shiyasa kina shiga Office ɗin Dr na dawo". Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa kana tace. "Na dawo a guje fa, wannan Sheykh ɗin hannunsa zafi kamar allurar mashi yakewa mutun". Zaro ido na mamaki Rafi'a tayi tare da cewa. "Shida kanshi ya miki?". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Eh". Cikin taɓe baki tace. "Lallai yau kin tashi da ƙafar dama, gashi kuwa naga har kin worke". Wucewa sukayi zuwa tsakiyar falon, cikin sauƙe numfashin Aysha tace. "Ba doleba yadda yake tura ruwan alluranshi nan kamar mai tura mai a mota, kuma ina dawowa nasha mgni, sannan abin ya iso, kinsan dama wuyar kafin ya isone". Dariya Rafi'a tayi tare da cewa. "Kinji allurar manyan likitocin da duniya keji dasu dai". Uhum kawai tace sannan suka fara cin abinci, sunaci suna hira. Cikin hirar tasu ne Rafi'a tace. "Anjima da yammafa jirginmu zai tashi". Da sauri Aysha tace. "Haba dai Rafi'a dan Allah ki bar zuwa hutunnan mana ki bari mu zauna, wallahi in kin tafi nima dole in tafi kuma ke kin san matsalar da nake da ita a gida ko Mamey ma da mukayi waya dazu cemin tayi kar in koma hutu Rugarmu, in zauna a makaranta". Cikin sanyi Rafi'a tace, "Wallahi nayi kewar gidane Aysha, shekara guda kenan banje gidaba fa". Cikin sanyi Aysha tace. "Haka ne kam ba, matsala, ai hutun sati ukune, kina tafiya yau nima gobe zan shirya zan koma Rugarmu". a haka sukaci gaba da hira suna cin abinci. Ƙarfe huɗu dai-dai na yamma jirginsu Rafi'a ya tashi daga Ɓadamaya international airport, zuwa Farazan state. Ita kuwa Aysha taci gaba da shirinta ba tare da ta gaya mutanen gida cewa zata dawo ba. Kaya kaɗan ta ɗiba dan tanada kaya a gida, system ɗinta da wayarta da kuma kaya kala biyu kawai ta ɗauka, sai yan ƙananun abubuwan, ta da tayi nufin sai gobe zata koma. Amman ina tafiyar Rafi'a yasa taji bazata iya zaman kaɗaicinba, dan haka huɗu da rabi, ɗaya daga cikin motocin dake maida ɗalibanda in gidajensu na kusane ya ɗauke ta. Kai tsaye garin Shikan suka nufa. Tafiyar ba wata mai nisa bace daga cikin birnin Joɗa zuwa Shikan, cikin mitina kaɗan suka isa, Ƙarfe biyara da miti biyar suka isa. Cikin Shikan a nan tasa drever ya tsaya ta sayi Junainah sweet. Biyar da mintuna goma dai-dai suka isa kwanar mashigar Rukarsu Rugar Bani. Cikin tsoron kada Ba'ana yaga wani yazo ya sauketa ya masa rashin mutunci, tace. Ya sauketa a nan ba musu ya sauketa dan ai inda sabo ya saba. Tana fita taja jakarta, ta rataya kana ta gyara tarhan da tayiwa kanta. Shi kuma ya juya ya tafi. A hankali ta zubawa yankin garin nasu ido, ko ina yayi kore shar, yabanya da ni'imar damina ta wadaci ko ina, wata iriyar sassanyar iska mai daɗin ke ratsa mata jiki da zuciya. Ajiyan zuciya ta sauƙe a hankali tare da lumshe idanunta kana ta buɗe hannayenta cikin begen gida tace. "Rayuwar ƙauye mu akwai daɗeeee". Ido ta buɗe tana kallon tako ina makiyayen rugarsune suketa dawowa daga kiwo, Dabbobi saffan-saffan sunata dawowa, garin yayi lum ga wani hadari mai ƙarfi daya keto, daga ƙasan dutsen da yayiwa Kyauyen ko ince Rugar Bani ƙawanya, a hankali take taku tana bin kan faffaɗan hanyan da makiyayan sukayishi bi ma'ana burtali kenan. Taku take yayinda gefen hagunta wutsiyar kogin Shikan ne konce iya ganinta, gefen dama kuwa Garden ɗinsune mai girma wanda yasa sanyin wurin yake yawaita, sauri ta ɗan farayi sabida akwai ƴar tazara kana kuma gashi magriba ta karato. Tana cikin tafiya tana rataye da jakarta, kamar daga sama taga wulgawar inuwan mutun, cikin sauri ta zaro idonta ta kalli gefen hagu da damanta, Ba kowa ganin hakane yasa taci gaba da tafiyarta cikin dakiya, taku uku tayi ana huɗu taji ansa hannu an amshi jakarta, da sauri ta juyo ta kalli gefen da aka amshi jakar. Babu kowa a wurin kuma ga jakarta a rataye ita ɗaya tana binta suna tafiya a jere. Cikin wani irin fargaba tsaro kaɗuwa da tsananin firgita ta....! By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 6 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *FREE PAGE* *Kada dai ku manta har yanzu Free page kuke samu, wanda zamu datseshi cikin ko wanne lokacin, hamzarta ku biya darinki uku kacal ko 1k ga mai dama da niya, domin samun cikekken labarin daki-daki cikin salama. Turo kuɗin ta asusuna na Jaiz. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidan biyanki ta layina 09097853276. In ya zama larura ba halin turawa ta ac turo katin mtn na ɗari uku, ko na 1k ɗin domin ci gaban lbrin GARKUWA. Sayan na gari maida kuɗi gida. Ina mai yi muku fatan al'khairi masoyana makaranta, ina sonku domin Allah ina fatan kyautata alaƙa ta da kowa sabida nasan ko ina raye watarana zan zama tarihi a duniyar marubuta, sabida yauda gobe ta wuce watsa, in ba mutuwa akwai tsufa. Kana dole watan wata rana gwanayen zasu zama tsoffin hannu kana yan koyo na yanzu su zama gwanayen, domin da babu yan koyo tabbas da gwanayen sun ƙare, inada fata da burin ganin al'ƙaluman Adabi sun inƙanta baki ɗayansu ba nawa kaɗaiba, tsarkake rubutu ki/ka domin kece madubin wata marubuciya da zata iya tasowa nan gaba.Ina mai muku fatan al'khairi🙏🏻🤝🏻🥰😘makaranta da marubuta* Cikin firgita da tsoron tace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun, Hasbunallahiwani'imanwakil, lailaha'illalahu Muhammadurasulillahi sallahu'alaihi wasallam Auzubikalimatillahi ta'ammati min sharrin ma khalaƙa Allahum...". Da sauri ta koma da baya ba tare da karisa addu'ar ƙarshen data faro ɗinba. Ganin Ba'ana ne tsaye a gabanta cikin wata iriyar dariya yace. "Ke ki nitsu masoyinki ne ke gadinki, gsky *Mata* dole in rage miki wannan tsoron, domin matar Ba'ana bazata kasance matsoraciya ba, dole in ƙara tsumaki in dafaki da kyau, ta yadda idanunki zasu buɗe da kyau". Cikin karkarwar da bai bar jikintaba tace. "Bana so. Ni ka barnin da tsorona, nifa macece ba namiji irinka ba, kaine ke shiga daji da tsaunuka kake buƙatar wani abu ya kare ka". Da sauri Ba'ana farin kekyawan babarbare ya matso gareta cikin shigar fulanin da ya zame mushi sutura yace. "Mata ke bakya buƙatar kariyar ne?." Da sauri ta gyaɗa mishi kai tare da cewa. "Ni na yarda cewa addu'a'u saiful muminin ne, kuma shi na riƙe, so bana buƙatar waɗannan asirce asircen". Murmushi yayi tare da murza ƙafarshi ta hagu sai gashi ya zama kamar inuwa ba mutun ya ɓacewa ganinta ɓat. Da sauri ta rufe idanunta tare da cewa. "Bana so ina tsoro ka dena caccanza kamanni a gabana". Da sauri tayi baya ganinshi gab da ita, Dariyar ƙeta yayi tare da cewa. "Baga irinta nanba, idonki baya iya ganin komai, dole zan ƙara haɗaki irin haɗin da zaki ke banbance mai layar ɓata data zana da jingina bongo da dama duk mutun mai juyewa i zuwa wata halittar". Ya karishe mgnar yana nuna mata hanya alamun su tafi. A hankali suka jera suna tafiya a tare. Allah ya sani Ba'ana yana masifar son Shatu tun tana ƴar ƙaramar yarinya, yana sonto irin sonda ko ƙudane in ya sauƙa kanta in dai namiji ne to zai kasheshi, ganinta kusa dashi kawai yana sashi jin daɗi, duk muguntarsa baya yi mata, duk duniya babu wanda Ba'ana ya yarda da shi bare yasan sirrin makarin sihirurrukan dake jikinshi. Ba'ana mutunne da yake tamkar al'janu sabida yawan ta'ammali da sihiri kai harma da tsafi, Ba'ana riƙeƙƙen tantirin ɓarawone wanda ya buwayi Fulani al'ummar Afirka gaba ɗayanta, da sace-sacen dabbobinshi, muddin ya ƙella ido yaga garken shanunka yayi mishi, to tazarar kilo mita talatin da biyar yake tsayuwa da garken, yayi FITO ɗaya tak, wallahi duk sihirin kafiyar garkenka zai kunce kuma duk inda yayi shanayenka zasu bishi a baya da kuma wannan tazarar, da zaran kasa Hukuma cikin zancen kuma yana burza layar ɓatanshi dashi da dabbobin duk zasu ɓace. Duk garken da yaga yayi mishi to sai ya kwashesu tsan da wannan ya tara dukiyar dabbobin da shi kanshi baisan adadinshiba babu ƙasar da bashi da makiyayanshi kamar su. Chadi, Nijer, Cameroon, Ghana, Gabon, Maroco, Senigal, da dai sauran kasashen makusantanmu kuma masu dabbobi, hikimar da yakeyi, muddin ya saci shanayen ƙasar Niger to sai ya cillasu ƙasar Senegal, in kuma makiyayanshi na ƙasar Sanigal sukayi sata to sai ya turo shanayen ƙasar Gabon, haka dai yake banbance mazauninsu. Sai dai garin zamansa ɗaya ne Rugar Bani, inda nan aka haifeshi mahaifinshi Bukar wanda babarbaren Norba ne saye da sayar da kanwane ya ajiyeshi cikin rugar FULANI shiyasa ya zama dilan saida kanwa, sabida dole duk bafulatani makiyayi yana ta'ammali da kanwa dan ana zubawa dabobbi susha a ruwa ko asa musu a dusa ko harawa yana musu mgni. Ba'ana ya shiga cikin Fulani ya saje dasu. Yayinda hakan ya bashi damar da duk duniya ake ɗaukarshi matsayin bafulatani, koda yake hakan baya rasa nasaba, da kallon da mutanen duniya sukewa duk mutumin da akaga shanu, tumaki a gabanshi tofa ko wacce gabilace shi, ya zama bafulatani, wanda kuma sam ba haka abin yakeba. Mahaifiyar Ba'ana ɗaya daga cikin ƙabilar ɓachama ce, wacce Bukar ya aura tana a matsayinta na anniya, koda kuwa suka haihu ɗan su. Bukar ya rinjaye ta Ba'ana ya kasance musulmi, sai daifa a baɗini baƙar zuciyarsa da aiyikansa na kafuraine, sata kuwa a wurin babarsa ya gada. Ba'ana kekyawan mutun ne ajin forko wanda ya gaji wannan kyan ne a kakarshi mahaifiyar babanshi wacce take shuwa Arabce, koda maƙiyinshi yasan tabbas Ba'ana kekyawane. A duniya kab Shatu ce tasan sirrinshi ciki da woje, sai daifa bata san yana sataba, amman duk wani abu na asiri da yadda za'a karya asirin da kuma yadda yake juyewa duk ta sani. To hakanne yasa sam bata fatan ya zama miji a gareta bare uban ƴaƴanta, sai dai babu yadda ta iya. Domin ya mata babbar rana a rayuwarta ya mata taimakon da yasa aka ɗaukar mishi al'ƙawarin aurenta. Gashi kuma duk wanda yace yana sonta karshenshi mutuwa, kuma yana gaya mata cewa duk wanda yace zai rabashi da ita zai kasheshi Wannan yasa kullum addu'ar shirya take mishi da fatan Allah ya rabata dashi lfy innshi ba mai shiryuwa bane. Tafiya sukeyi cikin nitsuwa a hankali, murmushi yaketayi cikin so da ƙaunarta yace. "Mata ya akayi na ganki da ƙaramar jaka?". Kai ta ɗan gyaɗa mishi tana kallon kekyawar fuskarshi, cikin murmushi yace. "Kece kika ajiyeni a kasar Kautal a Rugar Bani, kina ƙare karatunki zamuyi aurenmu in ɗaukeki mubar ƙasar, kawai dolece tasa na hakura da batun aurenmu kiyi karatu, dan naga kina son karatun kuma nasan zaki karantar mana da yaranmu, kuma ina son ki zama babbar lawyer mai zaman kanta, sai ki zama lawyer na koda watan-wata rana, rana zata ɓacin min". Murmushi tayi tare da cewa. "Kamar yaune zan kare karatun, Ya Ba'ana". Kanshi ya rausayar tare da gyara riƙon igiyar jakar da yayi, kana yace. "Allah ya nuna min wannan lokacin, in sha Allah sadakin aurenki Garken shanu ɗari zan bada". Cikin mmki ta zaro ido tare da cewa. "Kai Ya Ba'ana garke ɗari bama shanu ɗariba, ya bana ina zaka samu wannan shanun kaida garken naku ko shanu hamsin bai cikaba". Murmushi yayi tare da cewa. "Allah zai kawosu kafin lokacin auren namu". A hankali tace. "Allah ya kawosu". Amin Amin yace tare da ɗan juyowa ya kalleta, murmushi yayi mata, kana ya miƙo mata jakar tata cikin so yace. "Mun iso bakin Gari ki shiga. Ni zan koma baya dama rakoki nazo nayi kar shaiɗanun bakin kogi su cutarmin dake". Kai ta ɗan jinjina tare da cewa. "Ya Ba'ana lokacin sallah ya kusa fa ai gwara ka shigo sai kayi salla ka koma". Bakinshi ya ɗan tabe tare da cewa. "No bar sallan nan sai bayan mako biyu ina ƙara dafa jikinane kuma in nayi al'walan duk aikin zai karye". Dafa kanta tayi da sauri tare da cewa. "Wa'iyazubillah Wayyo Allah na Ya Ba'ana ka gane mana wannan abin da kakeyi shirka ne,". Kanshi ya jujjuya tare da cewa. "Shiga cikin gari zanzo musha hira da daren". To kawai tace mishi ta juya ta nufi cikin garin. Tana shiga ta kama hanyar gidansu, tana gab da shiga gidane ta haɗu da ɗan makotansu Iro cikin girmamawa tace. "Ina wuni Ya iro". Fuska cike da fara'a yace, "A a lale marhabin da ƙanwarmu yar al'barka anyi hutukenan?". Kai ta gyaɗa mishi sannu da hanya ya mata sannan ta wuce ya wuce. A gindin bishiyar mangoro dake kofar gidansu gab da zaure ta hango Bappanta yana zaune bisa dakalin dake wurin yana al'wala, da sauri ta nufi in da yake fuska cike da jin daɗi. Shima Bappa da sauri ya miƙe yana murmushi yake cewa. "Maraba lale da ƴar al'barka." Da sauri ta iso inda yake tana murmushi mai nuna tsantsar jin daɗinta tace. "Oyoyo Bappa na, Alhamdulillah na sameka lfy, ya Ummey na da Innata?". Dariya yayi tare da matsota yace. "Duk muna lfy". da sauri suka juyo ta cikin gida jin muryar yayunta suna cewa. "Oh wato mu kam bakiyi kewarmu bama ko?". Da sauri tayi gabansu cikin jin daɗi tace. "Oyoyo ƴan uwana Ya Gaini, nayi kewarku mana, musamman Ya Giɗi sarkin son girma". Murmushi sukayi dukansu, Seyo ne ya kalleta tare da cewa. "Wallahi yanzuma mgnarki mukeyi da Ummey, har Junainah na cewa wai ai duk munfi sonki". Dariyar jin daɗi tayi tare da cewa. "Ayyah ƴar ƙanwaliya tawa mai kishidani". Murmushi sukayi baki ɗaya kana Lado ya kalleta tare da cewa. "Shiga gida mu zamu wuce masallaci ne". To tace kana ta nufi cikin gida tana cewa. "Yauwa yaya Giɗi dan Allah a kawomin rake". Kai ya gyaɗa mata kana suka wuce ita tayi cikin gida. Tana shiga da fara'ar jin daɗi da ɗan karfi ta buɗe murya tare da cewa. "Assalamu alaikum, gani na dawo, ina Inna ina Ummey, Junainah ina kike?". Ai kusan a tare suka fito gaba ɗayansu, wani irin tsalle Junainah ta buga tare da rugawa ta nufi kan yayar tata cikin ihu da ɗaga sauti take cewa. "Oyoyo Addana oyoyo". Da sauri Ummey ta harateta tare da cewa. "Ke Junainah magriba cefa, kike irin wannan ihu ke sam baki da nitsuwa". Ita dai batama jitaba. Da gudu ta faɗa jikin Aysha, itama Aysha wurgar da jakarta tayi ta ruggume yar uwarta. Inna da Ummey kam ido suka zuba musu, suna masu jin daɗi irin soyayya da shaƙuwar dake tsakanin yaran nasu. Dariya sukayi baki ɗayansu, cikin jin daɗi inna tace. "To yanzu dai lokacin salla yayi ku shigo kuyi salla tukun sai ayita murna dan yau dai kam nasan kwanan zaune za'ayi". Murmushi Shatu tayi tare da karasowa gabansu cikin ladabi ba biyayya tace. "Inna ina wuni". Fuska a sake tace. "Lfy lau Alhamdulillah ya karatu". "Alhamdulillah karatu dai mun samu ɗan hutu." "Masha ALLAH yayi kyau". cewar Ummey hannun Ummeyn ta kamo tare da cewa. "Ummey ina wuni". Murmushi tayi tare da shafa kekyawar fuskarta tace. "Lfy lau Shatu muje muyi salla ko?". Kanta ta ɗan sosa tare da cewa. "Ummey ni nayi sallana a mota". Dariya Ummey tayi domin ta gano cewa Shatu na fashin salla, Ita kuwa Junainah baki ta tura tare da cewa. "To ba gashi ba, ba yanzu muka gama musuba ya Giɗi ba nace mishi nafi Addana son salla, tunda ni kullum sai nayi ita kuma wata rana sai tace a a ita tayi a makka ko kuma tace wai ai tayi kuma babu wanda zai ganta tanayin sallan". Ummey ce ta. Buge bakinta tare da cewa. "To Aku uwar mgna maza wuce kiyi salla, babu wanda ke son jawabin ki". Tura baki tayi kana ta wuce cikin ɗakin nasu, tana cewa. "Ai dama nasan kunfi sonta". Ita kuwa Ummey harara ta watsawa Shatu tare da cewa. "Ke kuma kada dai ki rinƙa kiyaye bakin wannan magananniyar". Murmushi tayi ta bita kana ta ɗauki buta ta shiga bayan gida dan gyara jikinta, sannan ta dawo. Tana shiga ta samu Junainah ta idar da sallan, Gefenta ta zauna, tare da jawo jakarta, sweet ɗinta data seyo mata, ta kwaso ta fitar mata. Ai kuwa tuni fushi ya ƙare, tazo ta raɓa jikin yayartata. Ummey kuwa da Inna saida sukayi sallan isha, kafin suka, fito tsakar gida dan tuni hadarin nan ya watse sai iska mai sanyi daketa kaɗawa. Bappa da su Ya Ladoma saida aka idar da sallan isha kafin suka dawo gida. Gaba ɗayansu a tsakiyar gidan suka zauna bisa manyan taburmaii guda biyu mazan na kan ɗaya matan na kan ɗaya. Abinci sukeci mai rai da lfy, tuwon faran ɗanyar shinkafa, da miyar ɗanyar kuɓewa data sha man shanu da tantakwashi, sai kifin banda sabi kifi na araha a wurinsu. Sai kuma zazzafan kunun nono da yaji nono da zuma. Sunaci suna ira ga hasken farin wata daya fito yayi ral ya haska ko ina na gidan. Cikin jin daɗi, Giɗi yace. "Shatu hutun mai tsawone ko gajere?". Kunun nonon data kurɓa ta haɗiye kafin tace. "Eh to Yaya Giɗi hutun sati uku ne muka samu". Seyo ne ya amshi zancen da cewa. "A hutun da ɗan yawa". Shi kuwa Giɗi dariyar mugunta yayi tare da cewa. "Ai kuwa naji daɗi wlh sai kinyi kiwo kema kiji hazar da muke ji". Bappa ne ya amshi zancen da cewa. "Giɗi mugunta ba kyaufa, Wato kai wuya kakeso tasha". dariyar ƙeta ya kumayi tare da cewa. "Ai naga duk anfi kashe mata kuɗi kuma muke wahalar kiwo, makarantar da takeyi kawai duk shekara kusan million 1 takeci muko sai wuyar tsiya da muke ci". Gaini ne yace. "To ai kuma ita bata da shanu ko ɗaya kaikuma garke biyu kakeda naka na kanka haka kuma muma". Ladone ya ɗanyi murmushi bayan ya haɗiye lomar da yasa a baki yace. "Ato gaya mishi kam". Ummey ce ta ɗan kalli Shatu tare da cewa. "Kici abinci ki dena shan ruwan kunu ba rike miki ciki zaiyiba". Da sauri Junainah tace.. "A a Ummey ai Inna tana tasa an yanka zabbi zata gasa mana Adda karkici tuwo". Dariya sukayi baki ɗayansu dan duk kowa yasan Junainah tsakaninta da. Nama akwai ƙauna. Haka dai sukaci gaba da hira da dariya, Hatta makiyayan gidan nasu wanda ba yan gidan bane saida suka shigo akayi ta hira da dariya dasu. Suna cikin hirar ne yaro yayi sallama cewa Ba'ana yana kiran Aysha, cikin sauri Aysha ta konta tare da lumshe idonta, ganin hakane yasa Ummey cewa yaron. "Ayyah kaje kace mishi yayi hakuri AYSHA har tayi bacci, in ba matsala yaje sai gobe, in kuma da matsala a tada ita". To yaron yace ya juya ya tafi. Fitarshi bada daɗewa ba ya dawo, Yace,. "Yace a barta tayi baccinta gobe da safe zaizo". To sukace kana yaron ya fita ya tafi. Sukuwa sukaci gaba da hira. Gashin zabbi mai kyau Inna tayi musu gashin da yaji haɗi, nan ta ware na maza ta basu kana ta ware nata da Ummey sannan ta bawa Aysha da Junainah, nan fa sukaci gaba da ci, suna hirarsu ta zumunci wanda ko yaushe haka suke duk daren kuma anan Bappa ke karantar dasu. Bayan duk sun fara miƙewa da dare ya fara nisa, a hankali Bappa yace. "Aysha kinyi baccine?". Cikin sauri ta miƙe zaune daga konciyar da tayi kanta na bisa cinyar Ummey, a hankali tace. "A a Bappa idona biyu". Tashi zaune yayi tare da fuskantar ta, ganin haka yasa ta rarrafa a hankali ta iso gabanshi, cikin kulawa yace. "Ya karatun naki?". Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah Bappa karatu na tafiya yadda ya kamata". Kanshi ya jinjina tare da cewa. "Baki da matsalar komai dai ko?". Da sauri tace. "Babu matsalar komai Bappa na". "Masha ALLAH haka nake son ji, Allah ya miki al'barka dake da sauran ƴan uwanki baki ɗaya. Allah ya miki zaɓi da miji na gari". A hankali suka amsa da Amin Amin gaba ɗayansu. Daga nan kuma yayi ta mata nasihar ta kama kanta, Jin sanyi ya fara yawane yasa sukayi saida safe kowa ya nufi makoncinsa. Yayinda a can cikin garima masu hira a dandali duk sun watse. Al'walan konciya bacci sukayi kana suka shiga, ɗakin Ummey da yake mai girma da faɗi an laileyeshi da siminti da leda carpet, kana ga jere da gadajenta biyu masu kyau, Ita da Junainah suna kan babban gadon ita kuwa Ummey tana kan ƙaramin gadon. Hira sukaci gaba da yi irin hira ta tsakanin uwa da ƴarta, cikin sanyi tace. "Aysha, kinji Hashimu ɗan Arɗo ya rasu ko?". Da sauri cikin razana AYSHA ta tashi zaune tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun Ummey banjiba yaushe ya rasu meya sameshi?". Ta jero tambayoyin a tare kana ga hawaye na kwaranya cikin sanyi Ummey tace. "Kwanan ya rasu, yankan rago akayi mishi sai tsintar gawanshi akayi a burtali ana zaton Ɓachamawa ne suka kasheshi". Cikin shessheƙan kuka tace. "Allah sarki Ya Hashimu Allah ya jiƙanka da rahama yasa ka huta, Allah ya saka maka duk wanda ya kasheka Allah ya toni asirinshi." Sai kuma ta konta tana kuka sosai saida tayi kamar 3 minute tana kuka kafin tace. "Yanzu shike nan Ummey duk wanda zai soni ƙarshensa yankan rago?". Cikin yin ƙasa da murya Ummey tace. "Ba dukaba in sha Allah akwai wanda zai soki ya kuma rayu dake bisa lfy". A hankali tace. "Ummey wa zai soni a irin yadda kullum ya Ba'ana yake kara zama masafi mugu, wa zai tsira da tarkonshi?". Da sauri Ummey tace. "Wanda yake mai ƙare rayuwarsa a amɓaton Allah da kekyawar zuciya." Kai kawai ta kife tana mai kukan rasuwar Yaya Hashimun ta, a haka dai sukayi ta hira har bacci ya sacesu. A can cikin masarautar Joɗa kuwa. Bayan anyi sallan ishane, Sheykh ya fito cikin shirinsa na tafiya, riga da wondon yaɗin wagambarine a jikinsa sai bakar alkyebbarsa dayasa kana sai hiraminshi fari da kuma bakin tarden dake saman kanshi. Sai takalman sarautar da ya saka, suma farare kalar hiraminshi. Jamil ne ke biye dashi a baya yana riƙe da ƴar madai-daiciyar jakar Hamman nasu, kana hannunshi ɗaya na riƙe da jakar System ɗinshi, shi kuwa Sheykh woyoyinsh ya zura a al'jihunshi. Tare suka fito, a mashigar ƙofarshi nan sukayi kiciɓis da Jalal, da Jakadiyarsu, cikin muryar da bata cika fara'aba Jalal yace. "Please Hamma Jabeer, dan Allah karka daɗe". Kafaɗanshi ya dafa tare da cewa. "In sha Allah bazan daɗeba Jalaluddin, ka kula da kanka da Yah Jafar". Kanshi ya gyaɗa alamar to, Jakadiya kuwa, ido ta zuma musu tana jin so da ƙaunar yaran kamar itace ta haifesu a cikinta. Cikin girmamawa Sheykh yace. "Ummi bari inje in sallami Yaya Jafar". To tace kana ta juya ta nufi sashin, Hajia Fatima, tsakar gidan Maigirma Habibullah. Su kuwa suna shiga a falo suka samu Yayan nasu da iyalanshi, a hankali Sheykh ya ƙaraso gaban ɗan uwan nashi, cikin sanyi yace. "Ya Jafar zan tafi Leddi julɓe Sitti ta nemi muje gidansu, can ƙasar saudia, Abba ne da kanshi yace inje badon hakaba babu inda zanje in barka a haka, zanje ƙasa mai tsarki tushen mahaifiyarmu da kakarmu da take jininsu, in sha Allah zan nemi al'farman a buɗe min ka'aba zan shiga har ciki inyi maka addu'o'in samun lfy, kuma bazan daɗe ba zan dawo kajiko Ya Jafar?". Bai kulashiba kana kuma bai bar karatun da yakeyiba, sai dai hawaye daya fara zubdawa a jere-a jere. Jamil kam juyawa yayi ya fita da jakar ɗan uwan nashi dan yasan zaiyi kuka. Ita kuwa Juwairiyya cikin sanyi tace. "Babu komai Sheykh Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy in sha Allah zanyi ta kula dashi yadda ya kamata". Jalal kuwa tattauna laɓɓa shi kawai yake tamkar zai hudasu, tabbas sunada ciwo a cikin zuƙatansu musamman Sheykh da yasan shike ɗaukan damuwarsu kab harda ta mahaifiyarsu". Shi kuwa Sheykh hannu yasa yana sharewa Yayan nashi hawayen, a hankali suka juyo suka kalli ƙofar ɗakin Hajia Mama ce, ta shigo hadimanta na biye da ita a baya. Gefen Juwairiyya ta zauna ta zubawa su Sheykh ido, lokacin ɗaya hawaye ya fara kwaranyowa da idanunta, cikin rawan murya tace. "Sheykh lokacin na tafiya, Maimartaba ya aika a kirawo ka a zatonsa kana sashina, tashi kaje, Allah ya kiyaye hanya karka damu yayanku na ƙarƙashin kulawata musamman". A hankali ya miƙe ga mamakinsu sai gashi shima Jafar ya mike hannunshi yasa ya kamo ƙanin nashi, cikin rauni Sheykh yace, "Hajia Mama kodai in tafi dashine, kingafa baya son in tafi in barshine". Hannu tasa ta share hawayenta kana a hankali tace. "Bazai yiwu ka tafi da shiba, karka damu Jabeer komai zai wuce". Kai ya gyaɗa mata, sannan ya juya, ya nufi hanyar fita yana riƙe da hannun yayan nashi, Jalal na biye dasu a baya, Hajia Mama da Juwairiyya da yaranta na biye dasu. Koda suka zo tsakiyar farfajiyar gidan cikin bada umarni Hajia Mama ta kalli Sheykh tare da cewa. "Jabeer kuje sashin Hajia Fatima ka sallamarta". Ɗan jim yayi, a hankali ya kalleta, ita kuwa da sauri tace. "Umarnine ba shawaraba". Kanshi ya gyaɗa alamun to. Daga nan suka shiga sashin nata, bayan Jakadiya tayi musu iso. A folon forko suka Sameta, tana hakimce hadimanta na zagaye da ita. Tana ganinsu ta tashi ta zauna, cikin sanyi tace. "A a Sheykh da kanka". Ɗan rusunawa yayi tare da cewa. "Zanyi tafiya Hajia mamace tace inzo in sallameki". Da sauri tace. "Ayyah, to Allah ya kiyaye hanya ya kaika lfy ya dawo da kai lfy". Amin yace a takaice kana ya kama hannun Ya Jafar ɗinshi suka fito. Nan suka raka'a zuwa sashin Gimbiya Aminatu nan suka sameta a falon, sukayi sallama da ita. Daga nan ya wuce fada, Hajia Mama kuwa ta koma sashinta da hadimanta bayan ta mishi addu'o'in insa lfy. Juwairiyya kuwa parking lot ɗin su inda ta hango an jera motoci. Ta nufa inda Jamil ke tsaye da alamun waya yakeyi da Malika sahibarsa sabuwar budurwar da yayi. Shi kuwa Sheykh yana shiga fada ya samu Waziri ne kaɗai da Maimartaba da alamun zaman jiransa sukeyi. A gaban Maimartaba ya rusuna, tare dasa hannu ya tura hularshi ya maidashi baya, Cikin kulawa Sarki Nuruddeen yasa hannu kan tsakiyar kanshi ya dafa tare da cewa. "Allah ya kaika lfy, ya dawo da kai lfy, ya baka sa'an tafiya, ya kareka a duk inda kake". Amin Amin suka amsa baki dayansu, kana Waziri ma ya mishi addu'o'in sannan suka miƙe gaba ɗayansu sukayi woje dan mishi rakiya, Sarki Nuruddeen da bayinshi wazirinsa da bayinshi, shina Sheykh da bayinshi, sai ya zama rakiyar ta samu taron mutane, kana ga bayin Ya Jafar, nan suka shishshiga tsala-tsalan motoci a ƙalla motoci goma sha biyar ne sukayi mishi rakiya zuwa Airport. A wurin rabuwarsa da Ya Jafar ne yasa zuciyar kowa raunata domin Jafar kuka sosai yayi tayi da kyar dai suka dawo gida bayan jirgin su Sheykh ya tashi zuwa birnin Jalaluddin. Cikin abinda bai gaza awa ɗaya ba sai gasu a birnin Jalaluddin. Kafin jirginsu ya sauƙama a ƙalla motoci goma ne suka zo tarbansa, a ciki kuwa harda mai Alfarma Sarkin Musulmai Jalaluddin. Koda yaga jikan nasa mota ɗaya suka shiga, suna isa fadar musulunci, suka fito daga cikin motocin da sauri Sarki Jalaluddin ya zagayo ya kamo hannun jikan nashi, suka nufi sashin Amaryarshi Gimbiya Kulsum, jikanshi Kabir na biye dasu a baya, suna isa falonta gaba ɗaya ma'aikatanta suka fita ganin mai alfarma da kanshi, shi kuwa Jalaluddin cikin ɗan ɗaga murya yake cewa. "UmmuKulsum! UmmuKulsum!! Ga Jazlaan ya iso, gashi na kawo mikishi har ɗauki". Wata kekyawar tsohuwar balarabiyace ta fito da sauri, cikin tsananin soyayyanshi ta ruggumeshi, shima ruggumeta yayi cikin harshen larabci Sheykh yace . "Ana uhubbiki hubban axeeman ya Sitti". Kanshi ta shafa cikin tsananin son jikan nata tace. "Laisa li misluka abadan ya habibee". Murmushi mai faɗi yayi tare da bin bayanta, kai tsaye dinning area ta nufa dashi Kabir da Sarki Jalaluddin na biye dasu, da kallon sha'awa. Kujera taja ta ajiyeshi, kana ta jawa Jalaluddin tasa kujerar nan kabirma ya zauna, Suna zama sai ga wasu dattijan mata su uku sun shigo a jere a jere, suna zuwa duk kanshi suke shafawa shi kuwa sai murmushi yayi tare da kallon Mai alfarma Sarki Jalaluddin yace. "Malam kace su dena shafa min kai haka na gaji". Murmushi sukayi baki ɗayansu kana suka zauna, cikin kulawa babbar cikinsu tace. "Kazo lfy, ya jikin Jafar?". A hankali ya ɗan kalleta tare da cewa. "To Alhamdulillah jiki da sauƙi zance". Allah ya ƙara sauƙi cewar Jalaluddin Amin Amin suka amsa baki ɗayan su, ƙaramar cikinsun ce ta ɗan kalleshi cikin tsokana tace. "Ina mai gidanmu Sarki muminai". Taɓe baki Sheykh yayi tare da cewa . "Uhumm Jalal ne Sarkin Musulmai ko? Baki sanshi bane". Dariya sukayi duka kana suk gaggaisa sannan suka fita gaba ɗayansu, ita kuwa Sitti abinci tayi ta bashi har saida ya kwaɓe fuska tare da cewa. "Na tuba ki barni haka na ƙoshi". Kai ta gyaɗa kana suka dawo falo zata fara hira, yace shi dai ya gaji bacci yakeji hakanne yasa, Jalaluddin da kanshi ya kaishi makwancinsa. Asuba ta gari al'ummar Sokotawa A nan Ɓadamaya kuma cikin Rugar Bani Washe gari da hantsi, bayan duk sun karya, kowa makiyaya duk sun tafiya kiwo, manoma kuma duk sun tafi noma, kana mata masu shiga tallan nono cikin gari sun tafi, garin yayi tsit kamar yadda aka saba Ba'ana kuwa da Shatu suna zaune a ginɗin bishiyar mangoro dake bakin zauren su, ita tanata. Ciki shi kuma yanata woje, cikin sakin fuska ya kalli Junainah dake gefensu yace. "Junainah je cikin gida kice a baki ɗanyen kwai ki kawo mana in dafa mana". Da mmki Shatu tace. "Ka dafa mana kuma?". Kai ya gyaɗa mata, ita kuwa Junainah uwar kwaɗayi tuni ta tafi cikin gida Inna na tambayarta me zatayima Bata kulataba, sai ɗan kwano data ɗauko a konɗonsu kwan zabbi ta ɗebo a kalla sun kai goma, kana da gudu ta dawo wurinsu. Da sauri yasa hannunshin ya amshi robar, ita dai Shatu Ido ta zuba mishi taga ta ina zai dafa kwan, shi kuwa Ba'ana hannunshi yasa ya fara tona ɗan ma dai-dai cin rami, da mmki Shatu tace. "Ya Ba'ana me zakayi da tona rami kuma?". Cikin murmushi yace. "A ciki zan dafa mana kwan". Junainah kam gabanshi tazo ta zauna, tana kallonshi har ya gama tona ramin. Kana ya zuba kwayayen a ciki ya maida ƙasar ya binnesu. Sannan ya juyo ya kalli Shatu yace. "To musha hirarmu kafin kwan ya nuna". Junainah ce tace. "Ya Ba'ana ta yaya zai nuna kuma babu wuta?". Kamo hannunta yayi tare da cewa. "Ke dai zauna ki jira ki gani ƙaƙara". Kai ta gyaɗa tare da gyara zama, shi kuwa Ba'ana murmushi yake a baiyane a ranshi kuma cewa yakeyi. "Uhummm shi Bappa dan ina son yarsa bazai hanani yashe Garkensa ba, kuma da koyayen gidanshi kawai zan iya karya kafin da yayiwa garkenshi". A zahiri kuwa kallon Shatu a yayi tare da cewa. "Zakiji girkina mai daɗi". Kai ta jinjina tare da cewa. "Uhumm girki ko al'mara." Kanshi kawai ya gyaɗa alamun zaki gani daga nan sukaci gaba da hira. Bayan kamar 42 minutes ya fara tono wannan ramin daya tona a gabansu babu wuta ko ɗigo ya binne ɗanyen koyaye, sai gashi ramin yana tururi tamkar an bude tukunyar dake tafasa, da sauri Aysha ta waro idonta. Junainah kuwa sai tsalle take, shiko Ba'ana saida ya kwatso ƙoyayen kab kana ya sasu a robar da aka kawosu a ciki, Ɗaya daga ciki yasa a gefen dutsen da yake zaune ya konkotsashi kaɗan kana ya ɗagoshi, yatsunshi biyu yasa yafara ɓarewa. Cikin mamaki Shatu ta zazzaro idanunta woje tare da cewa. "Hehhhhh...! Ga masu buƙatar biyan kudi littafin mutanen Niger ga number da zakuyiwa mgn +22799460151 in kun biya ta wurinta ita zata turo min number ku in saku cikin group. By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 7 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *Littafina na kuɗine, turo 1k domin karanta part 1 cikin mako biyu, ko ki turo 300 domin karanta part 1 a kwanaki talatin, da izinin ubangiji. Turosu ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank, Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo min shaidar biyanki ta number da nake whatsapp dashi. 09097853276, in da hali bana son kati, amman in babu dama turo katin ba matsala, domin wani baida damar turowa ta bank ac.* *Ayyah masuyi mun voice note Dan Allah ku rinƙa ɗaga murya, baku saniba ko inada matsalar kunne bayan na idon. In kinga kinyi min mgn ban amsaba wata ƙl fahimceki bane, ko kuma mgnarki bata da amsa a wurina, kana abubuwa suna min yawa, irin asha hira a chart ɗin nan bazai yiwuba, kuyi haƙuri masoya, yawan maimata min slm ince wslm ayi sama da sau goma yana sa in share mutun tsakani da Allah sabida kamar bashi da abin faɗane so Please na tuba,🙏🏻 a ɓari kada kice ina muku wulaƙanci.* Ido ta zazzaro tare da cewa. "Hihhhhhhh, ya dahu?". Kanshi ya rausayar tare daci gaba da ɓare kwan saida ya ɓaresh tas ya fito subul gwannin ban sha'awa, sai turiri yaketayi, Junainah ya miƙa. "Karɓi kici kiji mana, kwan ya nuna ne Ƙanwaliya". Da sauri tasa hannu, zata amsa, cikin sanyi Aysha tace. "Ke uwar kwaɗayi bazaki ciba". Rau-rau tayi da idanu alamun zatayi kuka, shi kuwa Ba'ana fuskarshi ya haɗa tare da kafeta da ido, da sauri tayi ƙasa da kanta, tana mai wasa da ƴan yatsun hannunta, dubanshi ya maida kan Junainah tare da cewa. "Kici abinki Junainah". Fuskarshi ya ƙara haɗawa jin Aysha ta kuma cewa. "Dan Allah Ya Ba'ana kada taci". Ba tare daya kalleta ba, tace. "Kema zakici ai bare ita". Da sauri ta ɗago kanta tare da girgiza kan tace. "A a ni kam ngd bazanci abinda ban san da me aka dafashi ba". juyowa yayi ya kalli Junainah da tuni ta fara cin kwanta, tana lumshe ido baki cike da kwan tace. "Ya Ba'ana bari inje cikin gida in kawo mana yaji mai daɗi Addana bata cin kwai saida yaji". To yace mata, tuni ta juya tayi cikin gida. Kallonshi ya maida kan Shatu cikin haɗe fuska yace. "Mata kina tunanin zan cutar da kene?". A hankali ta jujjuya mishi kai alamun a'a, gyara zamanshi, yayi tare da cewa. "To baki yarda dani bane?". A hankali ta buɗi bakinta tace. "A'a ni dai tsoron abun naji, ka toni rami mai danshi da sanyin yashin damina, ka binne ɗanyen kwai mai sanyi ka fito dashi da zafi a dafe ni kam ina tsoro ban san da wutan me ka dafashiba". Fuskarta-ta yayi da kyau kana, ya fara magana. "Ki yarda dani Mata, bazan taɓa cutar dakeba a rayuwa, duk abinda zakiga inayi, zanyine dan kare lfyarki da kuma baki kariyar. Jikin ki, kici kwannan, babu abinda zai miki". A hankali tace, "Ni bana cin kwai dama, kuma ai shi kariya Allah ke hadashi ga dukkan bayinsa". hannu yasa ya amshi robar dakekken yaji da Junainah ta miƙo mishi, wacce yanzu ta dawo wurin. Wani kwan ya kuma ɓare mata, ya miƙa mata, tanaci tana lumshe ido saida taci biyar, sannan tace. "Ya Ba'ana na ƙoshi". Shatu ya ɗan kalla tare da cewa. "Saura biyar kuma nakine, in kin shiga gida kicishi, sannan kuma akwai wani haɗin maganin da zan kawo miki kiyi amfani dashi. Ni yanzu zan tafi". Kai ta gyaɗa mishi alamar to, kana kuma tace. "Ina zakaje yanzu? Tunda naga lokacin tafiya kiwo dai ya wuce". Miƙewa tsaye yayi tare da cewa. "Zan shiga ƙauyen Bonon ne". Da mmki a fuskarta tace. "Ya Ba'ana me zakayi kuma a ƙauye Bonon garin masafa kafurai ƙabulun Ɓachama". Ido ya zuba mata har saida taji tsoronshi a hankali yace. "Kema watan watarana zakije, ki tuna da kyau Mamata ƙabilar ɓachama ce, ƴar garin Bonon kinga kuwa dole inje can tunda kawuneina ƙannen Mama da yayunta da iyayenta duk suna can". Ya ƙarishe mgnar kamsr yaji zafin zancen ta, ganin hakane yasa a hankali tace. "Kayi haƙuri". Kai ya juya mata alamar babu damuwa. Daga nan ya juya ya tafi, ita kuwa tacewa Junainah su shiga gida. Suna shiga cikin gidan ta harari Junainah tare da kai mata bugu cikin faɗa tace. "Hegiya kwaɗayayya maza ki zubar da sauran kwanan jakar yarinya ai sai ya ciyar dake guba tunda kince ke kwaɗayayya ce". Ihu Junainah ta kurma tare da cewa. "Wayyoooooooo Inna kin ganta ko tana cin zalina". a guje tayi gaba, ita kuwa Shatu tabi bayanta da sassarfa tana cewa. "Wallahi sai kin zubda ƙoyayen nan". A haka suka isa har gaban Ummey da inna da suketa tafasa nonon da aka tatsa a sanyin safiyar yau, wanda a ƙalla ya kai jarka goms sha uku, so masu gidajen fura da nono na cikin Shikan ɗin nema suke saya, dan matan gidan Bappa kab bai lamunce da zuwansu tallan nono ba. Inna ce tayi saurin kare Junainah dan saura ƙiris ta abka cikin tafasasshen nono da yanzu aka sauƙeshi, cikin tsoro tace. "Kai ya ilahi ku dai bazaku zauna lfy ba". Cikin nitsuwa Shatu ta zauna gefen Ummey nan ta labarta musu abinda ya faru da yadda ya dafa kwan ta ƙara da cewa. "Amman da yake Junainah uwar kwaɗayi ce, a take a gabanshi taci kwai biyar cas tanaci tana lumshe ido". Cikin tarin mamaki Inna da Ummey sukayi ta salati tare da tafa hannu, a tare sukace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun, oh wannan yaron anya kuwa mutun ne ba shaiɗan ba?". Cikin rau-rau da ido, Shatu tace. "Ni ina jin tsoronshi, bana sonshi bazan aureshiba, mutumin da komai nashi na tsafine Inna ki cewa Bappa ya rabani dashi mana". Cikin alhini, Inna tace. "Rashin sani yasa Bappanki dama ke kanki kukayi mishi al'ƙawarin shine mijinki duk rintsi, gashi yanzu ya zame mana masifa. Juyowa sukayi suka kalli Ummey da idonta ya ciki da hawaye a hankali tace. "Dana sani wlh da ban bar haka ta faru ba". Shiru sukayi cirko-cirko a wurin, saida suka jiyo ƙaurin nono na zuba cikin murhune suka dawo haiyacinsu. Kana suka juya suka ci gaba da aikin su. A birnin Jalaluddin kuwa ƙarfe tara na safiyar ranar, dai-dai jirginsu Sitti da jikanta Sheykh ya tashi zuwa ƙasa mai tsarki da sauran taro al'ummar Annabi masu zuwa Umrah. Soyayyar da Sitti keyiwa Sheykh soyayyace mai tarin yawa, wanda ko uwa iya son da zatayiwa ɗanta kenan, tana ji dashi tamkar ranta, wata ƙil hakan baya rasa nasaba da tsananin kamanni da yakeyi da mahaifinta wanda shine baida lfy yanzu kuma shine tsohon Limamin Harami yanada zuriya mai tarin yawa yayansa na cikinsa zalla su arba'in da bakwai. Bar jikoki da ƙanne da yaran yan uwa, sai dai ya tsufa sosai tun shekaru ashirin da suka gabata ya ɗaura babban ɗanshi wanda yake ƙanin Sitti ne uwa ɗaya uba ɗaya a matsayin shi. Zuwa yanzu tsotsai tsufa ya kama Sarki Abdulkarim, Hairan wanda yake da shekaru ɗari da biyar a duniya, sai dai sufarsa suface mai tsabta tsuface da ka gani kasan an rainin ƙuruciyarta da tsoron Allah da ibada. Shiyasa babu gigita ko fita haiyaci, yana son diyarsa Sitti kakarsu Sheykh kenan so mai tarin yawa ko dan tayi nesa da shine, wacce ita kuma tun tanada shekaru ashirin da uku, Sarkin Musulmai na ƙasar Kautal na wancan ƙarnin yazo da babban ɗansa, Jalaluddin wanda a nan yaga UmmuKulsum Sitti kenan, ya sota, kuma Allah cikin ikonsa suka dai-dai ta, haka yasa kafin ya koma ma da amaryarshi ya koma dan sitti ta kafe ita dai tana son Bahaushen ga, duk da tasan yanada mata biyu, tace ai a gidansuma bata tashi ta samu mahaifiyarsu ita ɗaya ba. Tuni ita kam Allah ya mata rasuwa mahaifiyar Sittin kenan, yanzu mahaifinta ne kadai a raye, sai kuma ƙanninta da yake matsayin ɗaya daga cikin manyan limaman harami a yanzu sai sauran zuriyarta da yayu da kannenta. Kowa na ahlinsu yasan Sheykh domin Sitti tana yawan zuwa dashi tun yana ƙarami, kana tana zuwa da sauran ma baki ɗaya, to shi Jabeer anan ƙasar saudia ya haɗa digiri ɗinshi na forko dana biyu. Shiyasa ya zama duk zuriyar an sanshi farin sani, ga kuma tarin kama da yakeyi da mutanen zuriyar wanda da zaran ka ganshi kasan jininsu ne. Tafiya mai tsowo sukeyi cikin sararin samaniya suna keta gajumare, a ƙalla tsawon aha huɗu kenan suna tafiya. Kafin suka sauƙa cikin babban Airport ɗin jidda, wanda yake tamkar zai fashe da jirage, ko wacce ƙasa ta duniya tanada jirginta cikin wannan babban Airport ɗin, tashin jirage da hawa da sauƙansu tamkar babu wani abun hawa a duniya sai jirgi. Koda suka fito daga jirgin, wani jirgine na musamman suka shiga wanda yake daga fadar Mai Alfarma masarautar garin. Wanda ya turo a tarɓi ƴar uwar abokinshi da mahaifinsu keta begen gani. A take suka shiga jirgin ya wuce dasu, asalin cikin garin makka, wanda pilot ɗin kuma ɗane ga Umaymah ƙanwar Mamansu Sheykh wato shima jikan Sitti ne ɗan Umaymah sai kuma Jannart wacce ta biyo Haroon Dan tarban kakar tasu wacce ita kuma ƴace ga babban ɗan Sitti wato ƙanwar Juwairiyya ce kuma anan take karatu. Suna sauƙa a Airport ɗin, suka fito, a jere, yana gaba yana rike da hannun Sitti tana biye dashi a hankali tana taka step ɗin Jannart kuwa tuni itace a gaba. Haroon ne wanda yake biye dasu a baya yana kallon yadda kakar tasu ke taka step da kuma yadda ɗan uwan nashi ke rike da hannun ta, murmushi yayi tare da jingina a ƙofar bakin jirgin cikin harshen larabci yace. "Ko dai zaka goyeta ne ka sauƙar da ita". Sheykh bai kulashi ba, har saida suka sauƙo ya gyarawa Sitti tsayuwarta, kana ya miƙawa Jannart hannun Sitti alamun ta rike musu ita. Cikin jin daɗi Jannart ta riko hannunta tare da cewa. "Ana Uhubbiki ya Sitti". Cikin jin daɗi da son jikokin nata tace. "Ana". Sai kuma suka juyo suna kallon Sheykh dake tsaye cikin shiga ta al'farma shigar salihan bayi, wata dandatsetsiyar al'kyabbace mai masifar kyau ruwan ƙasace al'kyabbar sai surfani da aka sarrafa a jikinshi wanda yake da kalan gold, haka takalmanshi da hiraminshi duk masu ratsin Golding color ne, cikin tsananin jin daɗi Haroon ya fara sauƙowa daga step ɗin, yana kallon ɗan uwan nashi manda suke sa'anni, ruggume juna sukayi, cikin jin daɗi Haroon yace. "Marhabin da zuwa Al'Sheykh, ya gida?, ina ƙannena? Yaya jikin Ya Jafar? Ya Hajja Mama da kowa da kowa." Kwaɓe fuska ya ɗanyi tare da janye jikinshi daga na Haroon cikin sanyinshi yace. "Duk in kana son ganinsu kaje Nigeria zaka gansu, kana nan kullum sai yawo a jirgi kamar turuwa a daji, duk ƙasashen duniya ka gama zagayesu". Murmushi Haroon yayi tare da cewa. "To ai dama na sani bakinka ɗaya da Umaymah'nka, zan koma ne in sha Allah, zan koma inyiwa ƙasarmu aiki, suma ai suna buƙata na". Fuskarshi ya ɗan kauda tare da cewa. "Da yafi kam". Juyowa sukayi jin Sitti na cewa. "Kai Haroon ku taho mu tafi, ka tsareshi da surunka tun daga nan ko?". murmushi Haroon yayi kana ya nufi inda take tare da cewa. "Oyoyo My Sitti". Kai ta juya tare da cewa. "Rabu dani ba kaga ɗan uwanka ka shareni ba". Ruggumeta yayi ta baya tare da cewa. "Na isa in share uwar gida ran gida a gidan Sarki Jalaluddin". Jannart ce tai dariya tare da cewa. "Sitti karki yadda da daɗin bakinshi". Hannunshin yasa ya ɗan dungure kan Jannart tare da cewa. "Kishi ko dan kinga gani ga uwar gida". murmushi Jannart tayi tare da jan hannun Sitti sukayi gaba, shi kuwa Haroon baya ya dawo ya saita da Sheykh suka fara tafiya a jere, duk wanda yaga salo da tsarin tafiyar Sheykh zai gane cewa jini na sarauta na gudana a jikinshi, zai kuma gane nitsuwa ta addinin musulunci da kamala da haiba na hasken imanin ya game jiki da zuciyarshi. A haka suka jera suna tafe, suna hira wacce ƙarfinta duk Haroon ke yinta. Suna tafiya kaɗan. Nan suka samu wasu irin zafafan tsala-tsalan motoci masu masifar kyau da tsada, suna jere a ƙalla sun kai goma sha biyu, motocine masu azabar kyau da sabunta da sheƙi da kyelli suna jere. Kana ga kekkyawa fararen larabawa yan uwa da abokai Da sauri suka rinka ɗan rusunawa suna, gaidasu Sitti da jikokinta, wani cikinsu ne da yake jikin wata dan datsetsiyar mota ƙirar Mercedes Benz maybach Exelero wacce kuɗinta zai kai kimanin $8 million dollars. Motace mai masifar kyau da tsada, tana da inƙancin da ko bilet baya shigarta. Bisa dukkan alamu kuma sabuwa ce dal. Direban dake jingine da ita ne yayi maza ya budewa Sitti bayan ta, a hankali suka ƙaraso gaban motar gaba ɗaya ma'akatan sunyi musu ƙawanya, cikin so da ƙaunar jikokin nata, ta yiwa Sheykh nuni daya fara shiga, ba musu kuwa ya shiga, motar, kana itama ta shiga sannan Haroon ya shiga, ya zamana sun sata a tsakiya, Jannart kuma gaba ta shiga gefen drivern, suna gama shiga aka maida ƙofofin motar aka rufe. Kana duk sauran hadiman suka shishiga motocin. Kana suka fara tafiya a jere-a jere, tafiya sukeyi cikin salama da nitsuwa da bin doka da ƙa'idar tuƙi, kai tsaye suka wuce tushen ahlin nasu. Wanda kafin su zoma, duk labarin zuwansu ya riski al'ummar family, kamar yadda aka saba, haka aka shirya musu tarba ta musamman an gyara sashin na musamman wanda nanne masaukin Sitti asali kuma sashin mahaifiyartace, anan cikin sashin kuma duk ahlinta da zaizo daga ƙasar Kautal nanne masauƙinshi, kuma kullum hadimai da bayin dake kula da wannan wurin suna nan suna tsabtace wurin. Suna isa fadar mai darar Sheikh Aliyu da kanshi ya fito tarbar babbar yayarshi wacce take a madadin uwa a gareshi a yanzu. A wani falo da yafi dacewa da a kirashi al'jannar duniya, suka haɗu, a hankali Sheykh Aliyu ya ɗaga hannunshi alamun dakatar da ko wanne hadimi, a tare suka rusuna tare da komawa baya gaba ɗaya su. Da sauri ya karaso gaban Sitti Ruggumeta yayi irin ruggumarsu ta jinin larabawa, murmushi mai cike da jin daɗi ƙauna haɗida bege Sitti tayi tare dasa hannunta tsakiyar kanshi tace. "Masha Allah, ɗan uwana na sameku lfy?". Saketa yayi tare da ruggume Sheykh yana murmushi tare da cewa. "Alhamdulillah yar uwata, Barka da zuwa lfy". Cikin kula da zaƙuwa tace. "Yaya jikin Baba". Murmushi ya kumayi still yana ruggume da Sheykh yana shafa bayanshi, yace. "Alhamdulillah jikin baba da sauƙi kewarkice tafi damunshi". Sai kuma ya kalli Sheykh bayan ya sakeshi yace. "Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero, barka da zuwa Doctor, ya gida ina Jafar da ƙannenka". Cikin son dottijon Sheykh ya ɗanyi wani ɗan guntun murmushi wanda shima sai yayi tsawon lokaci bai yishiba, cikin sassanyan murya yace. "Suna lfy, sun gaidaka". Haroon ya tura baki tare da cewa. "Wato mu ko ƴar ruggumar ma ta zumunci baza'ayi manaba, dan mu mun dade, nima zamu koma ƙasarmu mu rinƙa kawo muku ziyara jifa-jifa dan naga baƙi farinjini garesu a ahlinmu". Dariya sukayi baki ɗayansu,. Yayinda duk mgnar da sukeyi da harshen larabci sukeyi. Wani faffaɗan corridor mai girma suka ratsa, wanda suka riski wani babbanshi na musamman, inda gaba ɗaya yayan family suke nan zaune dan mahaifin nasu a tsakiyarsu. Wanda yake tsakiyar gatan duniya, farin dattijone wanda tsabar tsufa har ya juye ya koma tamkar ƙaramin yaro, ya ƙanƙance, yana hango Sitti, ya rinƙa sakin murmushi tare da miƙa mata hannunshi alamun tazo. Da sauri ta nufi inda yake su Sheykh na biye da ita a baya, yayinda duk sauran mutanen ketayi musu barka da zuwa. A gaban tsohon ta rusuna, tare da sunkuyowa, hannunshi ya saka bisa kanta yana jero mata addu'o'in da sanya mata al'barka, ita kam sitti da sauran ƙannenenta wanda a ƙalla sun kai arba'in sai Amin Amin suke amsawa, Koda ya gama da Sitti jawo Sheykh yayi ya manna kanshi da cinyarshi, Shikuwa Sheykh. Motsoshi yayi da kyau Cikin wani irin mashahurin daɗin da sai in yana gaban tsohon nan yakejin daɗi yasa hannunshi biyu ya kamo hannun dattijon ya ɗaura tsakiyar kanshi kana ya ƙara manna kanshi da cinyar tsohon tasbihi yakeyiwa Allah mai rayawa mai kashewa. Ya sani shi kanshi da macece shi da yanzu yanada ya budurwa amman gashi wai a gaban kakan mamanshi, ga kuma kakar tashi da sukewa kallon tsohuwa itama gata gaban mahaifinta wannan abu shine abu ɗaya da yake sashi kuka muddin yana gaban tsohonda kullum in yazo irin gaisuwar da sukeyi kenan. Shi kuwa Sarki Abdulkareem cikin rawan jiki irin na tsoffi yake shafa kan Sheykh tare da kallon taron ahlin naahi cikin muryarsa da bata fita sosai yasa suke sanƙala mishi na'urar ɗaga sauti a jikin alkyabbarsa, shiru sukayi gaba ɗayansu suka dakata da ruggume-ruggumen da sukewa Sitti, Cikin rawan muryan da alamu tsohon kuka yakeyi a hankali yace. "Ku bashi dukkan kulawarku, domin yana cikin Magauta, yanada tarin ƙunci da ƙuna a rayuwarshi, matsalolin rayuwar duniya sun mishi ƙawanya, saukinshi ɗaya Allah yayi mushi dafa'i da hasken imani da riƙo da ibada, damuwar tana daƙushe duk wani farin cikin rayuwarsa rashin fara'a ba izza bace damuwace, yana cike da al'hinin kula da ahlinshi,". Shiru ya ɗanyi tare da zubawa gaba ɗaya ahlin nashi idanu, sawon wasu daƙiƙu shiru falon babu sautin komai sai sassanyan sautin shessheƙan kuka da Sheykh a hankali, sai kuma sautin ƙaran A/C. A hankali Dottijon yaci gaba da cewa. "Kanshi akwai wani abu mai girma a tare dashi, yanada manyan baiwowi a jikinshi, sai dai kuma akwai tarin ƙalubale, zai ɗauki nauyi da yawa a kanshi". Ya ƙarishe mgnar yana shafa tattausan suman Sheykh. Shiru sukayi baki ɗayansu Sitti kuwa Hannu tasa bisa haɓar Sheykh tana share masa hawaye, Haroon kuwa Umaymah ya kira tun shigarsu tana jin duk kalaman kakan nasu haka yasa taketa kuka. Sosai yayi jawabai masu ratsa zuciya kafin daga bisani, ma'aikatan gidan suka shigo suka rinƙa gabatar musu da abubuwan ci da sha a nan suka zauna ana ɗan ciye-ciye da taɓa hira, Ganin lokacin salla yayine kab kowa ya miƙe dan yin al'wala su tafi harami. Kamar koda yaushe Sashin Sitti suka wuce wanda yake a gyare, Jannart da Sitti side ɗaya suka shiga. Haroon da Sheykh kuwa Side ɗaya suka shiga. Ruwa suka ɗan watsa sannan duk sukayi al'wala suka fito suka kimtsa cikin manyan alkyebbars masu taushi da masifar kyau wanda sabbine dal akazo aka shirya musu a drower'n. Koda suka gama a tare duk mazan suku tafi Harami. Haka dai rayuwa tai ta gudana a cikin kwanakin nan. Randa suka cika kwana uku da zuwa a ranar ne Sitti ta samu mahaifinta da ƙaninta a kan batun tana son kafin tabar ƙasar nan ayiwa Sheykh aure, ta kuma bada zaɓin yaran yan uwa wanda suke larabawa, nan take kuma Sheykh Aliyu da kanshi yace ya bawa Sheykh Jabeer auren diyarsa Jazrah... Rugar Bani Ɓadamaya state. Yau kusan kwanan Shatu biyar da dawowa hutu, kuma kullum da salon da Ba'ana yake zuwar mata dashi, wannan abu shine abinda yafi tada hankalin Malam Liman Bappa kenan, wanda yana yawan tattauna matsalar da Ardo Bani kamar yadda yanzuma haka suke tare su daddatawa biyar, Cikin kamala da harshen fillanci Arɗo Bani yayi gyaran murya tare da cewa. "Koda Hashimu ya rasu, in sha Allahu bazamu zuba ido a aurawa Shatu wannan fasiƙi fajiri mushirkin yaron nanba, Salmanu zai fito zai nemi aurenta,in Allah ya yarda kuma zamu cire batun shaɗi tunda, mun sani cewa, bulalin da Ba'ana yake amfanin dasu wurin shaɗi da manema auren Shatu bulalin sihirine wanda duk wanda ya daka dasu ƙarshe mutuwa yakeyi ko ya haukace, to a karon nan zamuce babu shaɗi domin ai shi shaɗi al'adace ba shariya ba. Zamu kuma bawa salmanu dakarun tsaro masu bibiyar lamuranshi a sirri dan gudun kada ayi mishi yankan rago kamar yadda akayiwa Hashimu duk da dai bamu da sanin shin Ba'ana ne koko kafuran Ɓachamawa ne". Da sauri ɗaya daga cikin dottawan yace. "Yo ai shima Ba'ana kusan kafurin ne, tunda baya salla kuma matsafine". Bappa ne ya nisa tare da jan dogon numfashi mai tsawo sannan yace. "Bazai yardaba duk yadda za'ayi sai yace dole ayi bulalin Shaɗi, kana kuma muddin akace baza'ayi Shaɗi ba to haƙƙun zai kashe Salmanu kisan da bazamu samu huja ko madafaba". Shiru sukayi baki ɗayansu cikin kamala da nitsuwa da rauni Bappa yace. "Kaɗan kenan daga illar riƙo da Al'adar daba addini ne ya tanadar dashi ba". Ardonne yayi gyaran murya cikin sanyi yace. "Ya Allah ka kawo mana mafita kan wannan bawa naka Ba'ana daya zame mana masifa a rayuwarmu". Ɗaya daga cikinsu wanda tunda suka zauna baiyi mgna bane ya gyara zama tare da cewa. "Gashi shi kamar ibilis yake, ya rigada ya gama dafa kanshi wuƙa ko bindiga basa shigarsa bare banzan abu shi bulalan Shaɗi shiyasa kullum shine da nasara a rayuwarsa". Shiru sukayi suna kallon ɗaya daga cikinsu wanda ya kasance malamin da suke sawa yana bincikar musu jikin Ba'ana wato Chubaɗo yana cewa. "Akwai bulalin da zasu shigeshi su kuma karya duk wasu manyan sirrukan dake jikinshi, ta kuma sashi yayi kuka,cur-cur da hawayenshi, to amman bazasu taɓa samuwaba bamu da hanya ko damar samunsu, domin bulaline da a ƙalla sun shekara ɗari biyu a murde kuma suna cikin tsumin ma'jiya mai cikar tarihi da girma bulaline da tsawon shekara ɗari da ashirin da biyar kenan rabon da ayi amfani dasu, kuma an killacesu, killacewa mai tsauri, shi kanshi Ba'ana yana neman bulalin ruwa a jillo domin babban dodon tsafin Bonon ya sanar mishi saida bulalin zai samu nasarar da yake so, to amman bai san bulalin ina bane baisan a ina sukeba bai kuma san ta ina yake nemansuba an dai bashi yaƙini a hannun Fulani yake wannan dalilin ne yasa ya baza jakadunshi duk ƙasar da takeda Fulani." Da sauri Suka zuba mushi idanu baki ɗayansu cikin zaƙuwa sukace. "To Chuɓaɗo kai kasan inda bulalin suke e?". Kanshi ya jinjina musu tare dayin ƙasa da murya yace. "Eh na sani". Cikin sauri sukace. "Bulalin inane a wacce ƙasar suke?". Cikin tsoro yace. "Bazan fadaba bazaiyiwu in faɗaba". Magiya suka fara yi mishi amman fir yaƙi yace mutanen jikinshi sun hanashi faɗa, dole haka suka haƙura suka tashi daga taron ganin dare ya raba tsakiya kowa ya koma gidanshi. Washe gari da Asuban fari Rasuwar Chubaɗo ya zagaya garin Rugar Bani wanda akayi hira dashi lfy lau kawai washe gari aka riski ya rasu da alamun kuma ɗaure mishi wuya akayi ya rasu har lahira. Wannan rasuwa ya jijjiga zuƙatan dottawan nan huɗu da suka rage Arɗo Yabani da Bappa, da kuma Alhaji Ja'eh da kuma Malam Umaru. Sun shiga jimami mai yawa. A haka dai akayi mishi sutura aka binneshi akayi zaman makoki na tsawon kwana uku, randa akayi sadan uku duk hankali mutane huɗun nan ya ɗan konta ganin ba'a sake kashe wani ba a cikinsu. Yau tun da yamma Ba'ana ya matsa aka kira mishi Shatu wacce dolece tasa taje, inda yake har rugar shanunsu bata damuba sanin bai taɓa koda yunƙurin cewa zai taɓa koda ƴar yatsartace, Cikin sanyin jiki ta sallami aminiyarta Bintu ƴar gidan malam Umaru, sannan ta tafi bakin rugagen. Zaune ta sameshi cikin ƴar bukkarshi da yayi a cikin tsakiyar turken garken nasu, A hankali ta ƙaraso wurin ta sunkuya zata zauna ne a saman farin yashin dake wurin yayi maza yace. "Mata a ƙasa kuma? A a gskiya kada ki zauna a ƙasa. Ga buzuna zauna a kai". Kanta kawai ta jinjina shi kuwa shimfiɗa mata buzun yayi, a hankali ta zauna tana fuskantar cikin ƴar bukkar da yake zaune a cikinta ɗin. Shima gyara zama yayi tare da fuskantarta, Kwaryar dake gabanshi ta zubawa ido, shi kuwa. Cikin yin murmushi ya sa hannunshi yana gauraye magungunan dake ciki tare da cewa. "Matar dafaki nakeso inyi, irin dafar da muddin mutun ya tuna zai miki sihiri, misali ya miƙa hannu zai amshi mgnanin da zai samiki to zai kuturce in kuma baki ya buɗe zaiyi mgna kan a miki sihiri to zai kuramce". Cikin sanyi ta kwaɓe fuska tare da cewa. "To ni kuma wa zaimin sihiri a duniya wayama damu dani?". Murmushi mai kama da dariya yayi kana yace. "In an nemi mijinki ba'a sameshiba dole kanki za'a dawo shiyasa nake shiryaki sabida kar Ni in an jefeni bai sameniba ya sauƙa kanki". Ya ƙarishe mgnar da miƙo mata ɗan ƙaramin korya yace. "Ingo ki fara shan wannan". Kai ta gyaɗa ganin madarar shanuce da aka tatsa da ɗuminta. Cikin takaicin halinsa tace. "Me wannan kuma?". dariya yayi tare da cewa. "Baki da yarda ki yarda dani wata rana zaki tuna nayi miki gata, wlh bazan taɓa cutar da keba mata, kisha madarace da zuma nasan kinaso". Cikin sanyi tace. "Sai dai in na koma gida zansha". Murmushi yayi tare da zuba mata ido kana a hankali yace. "Fulaku ko? Nasanku fulanin da kunya wato irin bazakici abu a gabana ba, to ai kafin ki koma gida zaiyi sanyi, bari in tafi can bayan bishiya in barki ke ɗaya kisha abunki da ɗuminshi". Ido kawai ta zuba mishi domin tabbas badon halin banza da Ya Ba'ana yake dashiba ya cancanci ta soshi tabbas tasan ko ba yayi mata alherin da bazata taɓa mancewa ba a rayuwarta. Ko komai nashi na duniya mara kyau ne to soyayyarta kekkyawace a zuciyarshi ya sota tun tana yar mitsitsiyarta kuma bai taɓa yunƙurin cutar da itaba ya kuma yi mata halacci. Murmushi yayi tare da cewa. "Mata nayi miki kyau ne?". Kanta ta gyaɗa mishi alamar eh, cikin jin daɗi ya juya ya tafi, can nesa ya ɓuya, ita kuwa a hankali ta fara shan madarar nonon da yaji zuma mai daɗi, kasan cewar nonon ɗan kaɗanne a take ta shanye. Saida ta goge bakinta tace mishi. "Na shanye kazo". Da sauri ya fito ya dawo gareta cikin bukkar ya koma ya zauna wani nonon ya ɗibo ya miƙa mata amsa tayi cikin sanyi yace. "Me kika gani a ciki?". Murmushi ta ɗanyi tare da cewa. "Nono fari ƙal mana". Amsar ƙoryar yayi ya koma cikin bukkar dashi, jin kaɗan ya kuma fitowa ya miƙa mata tare da cewa. "Me kika gani?". Tura baki tayi tace. "Farin nono mana". Kanshi ya jinjina tare da cewa. "Da kyau, yanzu kiyi kamar zakisha ki gani". Ido ta zuba mishi tare da cewa. "Sha kuma?". Kai ya jijina mata kana yace. "Eh amman ba shan zakiyiba kiyi dai kamar zaki kaishi bakinki da niyar sha zakiga wani abu". Jim kaɗan tayi jin yana ce mata sha mana, yasa ta ɗan ɗago kwaryar ta nufi bakinda kamar zata sha. Wani irin wawan zabura tayi jiki na tsuma da karkarwa cikin tsananin firgita da tarin tsoro ta sake kwaryar....! By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 8 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 Kada dai ku mance Free page ne, yana kuma gab da karewa. *Ga mai buƙatar saya ga number ta, 09097853276 turo ɗari uku ko dubunki ɗaya kacal domin samun damar karantawa cikin salama, Ga Ac ɗina 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, in kin biya sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276 in ba halin turawa ta ac bisa dole turo katin mtn.* Ta saki kwaryar, a sorace, da sauri yasa tafin hannunshi, biyu ya tare kwaryar. Cikin tsoro jiki na rawa ta zazzaro idanunta woje kana murya a hargitse tace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun, Ya Ba'ana mekabani? Me ka shayar dani? Na shiga uku me kasa nasha?". Gaba ɗaya ta gigice tana rawan jiki da murya, ga hawaye kuma tuni suke shatata. Ganin yadda ta firgitane ya sashi matsowa gabanta cikin ɗaga murya yace. "Ba komai ba abinda na shayar dake Mata, wallahi Allah ki yarda dani wancan da kikasha babu komai a ciki". Da sauri taja da baya tare da cewa. "Ban yardaba me ka shayar dani?". Sai kuma ta fara kakarin amai da ƙarfi, ganin kamar aman bazai zo bane yasa ta tura yatsunta biyu a baki, amman ina aman yaƙi zuwa sam. Kawai sai tasa mishi kuka. Cikin tashin hankali yace. "Kiyi haƙuri Mata wlhi bazan taɓa shayar dake wani abu na guba, ko na ƙiba, duk abinda nasan bazaki shashi da sanenki ba bazan taɓa bakishi a ɓoyeba. Ki yarda dani wlh ban shayar dake komaiba". Ina taƙi ta saurareshi sabida tayi matuƙar firgita da tsananin razana da ganin abinda ke cikin kwaryar, cikin sauri yasha gabanta tare da cewa. "Ki gani mana ki duba babu komai a ciki fa madarar shanunce". Tsayuwa tayi tare da zubawa cikin kwaryar ido tas farin nonone kamar ko wanne nono da bashi da gamin komai". Hannutasa ta mutstsuke idanunta tare da kuma sake kallon, cikin tuhuma ta maida idanunta kanshi tana mishi kallo mai cike da tuhuma. A hankali ya sunkuya ya ajiye akwaryar kana ya taso ya fuskanceta da kyau fuska ya haɗe tare da cewa. "Sam bakya min adalci Mata, na lura dake, wani mugun zato da zargina kikeyi. A zatonki wai zan iya cutar da kene? Shin kin mance tun kina ƴar tatsitsiyarki nake sonki ne? Da inada mummunar niya a kanki da na cutar dake tun kina ƙarama. Kullum idanunki na nuna min baki yarda dani ba. Me kike nufi? ko dai wani kikeso ba niba?". Ya ƙarshe tambayar da taune bakinshi kana ya tsareta da idanunshi, da sauri ta sunkuyar da kanta tare da cewa. "A a ni kam babu wanda nakeso." Kanshi ya ɗan rausayar kana ya dawo ya zauna a bakin bukkar tashi, cikin kakkausar murya yace. "Dawo ki zauna". A hankali ta dawo gefen gaban bukkar ta zauna, shi kuwa wani ɗan randar ƙasan dake gefenshi ya buɗe, cikin haɗe fuska ya ɗan kalleta tare da cewa. "To zakiyi sabon Saurayi. Salmanun Arɗo Yabani, zai fara nemanki, kamar yadda munafukan tsoffin rugar nan suke tsarawa, dan ana son rabani dake". Da sauri taketa jujjuya kai tare da cewa. "A a Wallahi ni Yaya Salmanu, ba sona yakeba, ka sani tun ina ƙarama duk abinda ya shafi karatuna shike koya min har dai yasa aka sani. Makaranta kai kuma baka hanaba". Cikin haɗe fuska yace. "Ehh ai nasan ke baki san yana sonkiba, amman na lura shi yana sonki, kuma zanci ubanshi da bulalin shaɗi bashi babu sake kallon duk wani abu da nakeso". Cikin tarin tsoron kada a cutar da Yaya Salmanun tace. "Wallahi ƙarya ake mishi, baice yana sona ba, shi yama tsaneni ne yanzu, dan Allah Ya Ba'ana kada ka yarda da ƙaryar mutane". Kai ya rausayar tare da cewa. "Uhum kinga nan cikin ranɗar nan, to bulaline wanda nake shaɗi dasu, yanzu tsawon shekaru biyu kenan da aka hana shaɗi basu samu wanda suka dakaba, na tsumasu da tarin tsumi mai zafi, wanda muddin na zana jikin mutun dashi sai ya fashe, Kuma gasu a ƙalla sun kai tamanin a cikin randar nan kuma a ƙa'ida da guda goma sha bibbiyu kawai zakayi shaɗi to kinga kenan zan iya shadi da mutun sama da shida dasu basu ƙareba". Kanta taketa jujjuya mishi tare da cewa. "Ya Ba'ana kada ka yarda da sharrin mutane kasanfa Yaya Salmanu shike karantar dani, tun ina ƙarama kuma ko yanzu dana girma tunda shi ya rigada ya gama digiri ɗinshi shike fahimtar dani duk abinda ya shige min duhu, kuma tunda nazo hutun nanma ban haɗu dashiba". A hankali yace. "Eh ai yau kam zaki haɗu dashi". Yunƙura tayi ta tashi tare da cewa. "Uhumm, shike nan ni bari in tafi gida an fara kiran salla." Da sauri ya miƙe ya fito yabi bayanta tare da cemata. "To Mata jirani inzo in rakaki Mana". To kawai tace mishi, a haka suka jero suna tafiya yana gaya mata irin tsumin da yayiwa bulalin nashi. Suna isa dai-dai garken su Shatu, ta ɗan tsaya hango yayunta sun dawo daga kiwo, cikin jin daɗi ta ɗan juyo ta kalleshi tare da cewa. "Bari inje wurinsu Ya Giɗi, in tayasu ɗaure shanun". Murmushi yayi kana yace. "To Mata ki kulan min da kanki kada shanu ya taɓa min ke, dan akan ɗan mai shanun zan rama miki ba kan shanu ba". To tace tare da juyawa ta nufi cikin tsakiyar taron dabobbi su da aƙalla zasu kai guda dubu da yan ɗaruruwa tsakanin shanu, tumaki, awaki, rakuma. Da sassarfa take kutsa tsakiyar dabobbin tana cewa. "Yaya sannunku da dawowa". Da sauri Giɗi da Seyo suka juyo murmushi sukayi tare da cewa. "Yauwa ƴar ƙanwarmu, daga ina kike?". Da ido ta nuna musu Ba'ana dake tsaye can gefe ya zubawa dabbobin nasu idanu tamkar mai ƙidanya su. Gaini ne da Lado suka zuba mishi ido domin gaba ɗaya ya shagala da kallon da yakeyi, har wani ƙan-ƙance idanu yakeyi. Sam bayaji kiran da Babanshi Bukar ke auna mishi. Har saida Giɗi yace. "Heyy Ya ba'ana Ubanka na kiranka". Ya ƙirishe mgnar da bagwariyar hausarsa. Shi kuwa Ba'ana da sauri ya juya ya nufi wurin babanshin da yanzu ya dawo kiwo. Cikin sakalci da gajiya Giɗi ya kalli yayunshi mazan tare da tura baki gaba yace. "Wayyoooooooo Allah bayana zai karye, Ni dai na gaji bazan iya sunkuyon ɗaure shanu ba, ga Shatu zata tayaku". Sai ya kuma kalli yadda duk suka sunkuya sunata ɗaure dabobbin suna ɗan dariyar yadda itama Shatu ta dage tana tayasu. Junainah ce wace dama duk lokacin dawowarsu zata kawo musu sassanyan kindirmo susha tun a nan kafin su koma gida. Da saurinta take ratso cikin shanayen tana cewa. "Ya Giɗi tareni, na gaji ga damunku". Da sauri ya nufi inda take kwaryar ya amsa kana suka dawo gaban bukkokin da nanne ma kwancin masu gadin dabobbin suke. Zama sukayi ludeyayen dumar dake kan fefeyin daya rufe kwaryar ya ɗauke kana ya buɗe kwaryar, ludeyi ɗaya ya sa musu a ciki. Aysha dake kusa da sune ta zauna tare da cewa. "Ya Giɗi kama ka bani". Kai ya gyaɗa mata kana ya cika ludeyin yasha sannan itama ta ɗebo rabin ludeyin tasha, kana ta bawa Junainah itama ta kamfato ta cika ludeyin ko rabinshi bata zuƙaba. Ta miƙawa Ya Seyo dake tsaye gefensu, da murmushi a fuskarshi ya amsa ya sha, sauran nata, Shatu ce ta gyara zamanta ta matso kusa da ɗan uwanta tsokonta Giɗi abokin tsamarta, gyara zamanta tayi kana tace. "Ya Seyo zauna ga fili." To yace kana ya zauna suka fara sha, Lado ne ya kallesu cikin gajiya yace. "To wai mu aka kawowa ko kune?". Shiru babu mai magana sai kamun ludeyin da sukeyi, Gaini ne ya matso gefe shima ya zauna kusa da Junainah yasa hannu ya ɗauki wani ludeyin, nan suka zauna suna sha, ganin hakane, Ya Lado yace. "To ni naci girma". Da sauri Shatu ta mike wurinda ta tashi ta nuna mishi tare da cewa. "A a ya Lado zauna kusha ni na ƙoshi". Murmushi Bappa dake gefensu yayi, wanda yanzu ya iso da jarkan ruwa a hannunshi, Cikin kallon so da tausayin yaran nashi yakeyi, Cikin kula yace. "Sannunku- sannunku da rana, Allah yayi muku al'barka". Amin Amin suka amsa baki ɗayansu, Sai kuma ya kalli Aysha da Junainah yace. "Ayshatu maza kama hannun Junainah ku koma gida, kinji an fara kiran salla". To tace tare da kamo hannun ƙanwar tata suka nufi gida. Su kuwa Bappa da yaranshi da makiyayanshi anan sukayi al'wala, kana suka juya suka nufi cikin Rugar tasu dan zuwa masallaci. Yayinda ko wanne garke an bar mutun ɗaya sabida tsaro... Bayan sallan isha sunci abinci sun ɗan taɓa hira, kaɗan kana Bappa ya tarasu yana karantar dasu kamar yadda ya saba duk dare, da kuma safiya kafin a tafi kiwo shiyasa sam ahlin wannan Rugar Bani ba jahilai bane. Suna zaune, yaro yayi sallama, yace. "Wai ana kiran Shatu a woje". Ummey ce ta ɗan juyo ta kalli yaron tare da cewa. "Wake kiranta?". "Wai yace ince mata inji Ya Salmanu ne". Yaron ya faɗi. Da sauri Ummey tace. "A a Salmanu ne ya zobe? To maza kace ya iso mana ya zai tsaya a waje kamar baƙo". To yaron yace kana ya juya ya fita. Jim kaɗan sai gashi ya dawo gefen Ummey ya rusuna tare da cewa. "Yace wai ince mata, ta fito woje". "Da mamaki Ummey tace to gata nan zuwa". Sai kuma Inna ta ɗan kalli Shatu tace. "Tashi kije ai mun gama aikin ma". Ita kuwa Aysha dake zaune gaban Inna suna gasa tattabarun da aka yanka tunda yamma, kwano ta ɗauko a konɗonsu kana tasa gasassun tattabarun guda biyu. Tasa yaji a gefe, ta rufe, kana ta gyara wuyan hijabinta sannan ta miƙowa Junainah kwanon. A hankali ta ratsa gefen su Ya Giɗi ta wuce. Ummey kuwa da ido ta rakasu tana fatan Allah yasa fata da shirin Bappa da Arɗo Yabani ya tabbata. Suna fita suka sameshi zaune bisa dakalin ƙofar gidan nasu. Da sauri Junainah ta isa gareshi tare da cewa. "Oyoyo yaya Salmanu". Ajiye kwanon tayi a gefenshi. Da sauri yasa hannunshin suka tafa da hannunta data miƙa mishi, cikin sakin fuska da nitsuwa yace. "I miss you ƙanwali". Dariya mai ɗan sauti tayi tare da cewa. "Miss you too my dear". Dariya mai sauti sukayi a tare cikin jin daɗi wanda aka kira da Salmanu ya lakace hancin Junainah tare da cewa. "Alhamdulillah alama ta nuna ƙanwaliya tana zuwa makaranta babu wasa". Cikin jin daɗi tace. "Sosai ma ya Salmanu yanzu ajiyana huɗu fa, yanzuma dan hutu mukeyi, kuma gashi ko a gidama Ina karatu". Jinjina mata yayi da hannunshi kana, ya jawo kwanan data ajiye tare da cewa. "Ƙanwaliya me kika kawo mim ne?". Cikin murmushi tace. "Gasheshen naman tattabarune Ya Salmanu barima in koma ciki inci rabona inci na Addana". Kafin ya ankarama tuni ta juya da sauri tayi cikin gida. Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da kallon Aysha dake jingini da bakin kofar zauren, Cikin sanyi yace. "Kamar bakiyi farin ciki da zuwana ba? Ko dai in komane?". A hankali tace. "A a Ya Salmanu nadai ga kamar kafi farin cikin ganin Junainah ne akai na". Murmushi yayi tare da cewa. "Kin rama kena". Murmushi sukayi dukansu, cikin sanyi yace. "Ga wuri kizo ki zauna mana". A hankali tace, "A a Ya Salmanu mu shiga cikin gida mana". "Kina tsoron kada saurayinki yazo ya ganmune?". Salmanu ya faɗa a hankali. Da sauri tace. "Eh". Kanshi ya ɗan rausayar tare da cewa. "Babu abinda zai faru sai al'khairi zoki zauna, ki gayamin me kike tsoron?". A hankali ta zauna gefenshi ɗan nesa dashi. Shi kuwa juyowa yayi ya fuskanceta a hankali yace. "Gaya min me kike tsoro?". Kallonshi tayi cikin yin ƙasa da murya tace. "Ina tsoron kada Ya Ba'ana ya cutar da kai, ina gudun kada sakaiyar alaƙarmu ya zama cutarwa, sabida Ni kamin rana a rayuwata, rana kuma ta al'khairi shiyasa bana son abinda zai cutar da kai". Murmushi mai yelwa yayi kana a hankali yace. "Ina sonki zan kuma aureki da izinin Ubangiji zan rabaki da wannan taƙadirin, domin baki cancanci zama matar mushurkiba". Da sauri tace. "Kada kace haka Ya Salmanu Wallahi zai cutar da kai, kada ka bari wani yaji, bare mgnar ta koma kunnenshi". Murmushi yayi tare da jawo kwanon ya buɗe. Numfashin yaja jin ƙamshin naman a hankali ya fara ci, saida yaci ɗaya kab sannan ya rufe kwanon yace. "Ga rabonki dan nasan Junainah ta cinye naki rabon". Cikin yanayin nitsuwarta tace. "A a kaci kawai Ya Salmanu". Da sauri yace. "No kada kimin musu". Shiru tayi jin yaci gaba da cewa. "Muddin dai ina raye in sha Allah. wallahi Allah bazan bari Ba'ana ya aureki ya lalata miki rayuwaba, zan jure duk azabar da zai shayar dani na shaɗi in Sha Allah zan aureki". Ido ta zuba mushi tana kallon shi cikin kamalarsa, ganin sam hankalinta ba'a kwance yakeba, yasashi ce mata ta shiga gida zasuyi mgna a waya, haka kuwa akayi, ta juya ta shiga gida shi kuma ya nufi hanyar gidansu. A dandalin wurin da yake kamar kasuwar garin nasu ya samu abokanshi, kowa da budurwarshi suna ɗan hirarsu Can gefe kuma ga yara nata wasansu, ga farin wata ya fito yayi ras, kana iya ganin komai. Ita kuwa Shatu, bayan sun gama shirin baccinsu, ta kalli Ummey tare da cewa. "Ummey". "Na'am". Ta amsa mata cikin kula, sai kuma tayi shiru, ita kuwa Ummey ido ta zuba mata, ganin hakane yasa a hankali tace. "Ummey Ya Salmanu". Still kuma tayi shiru, Cikin kulawa da shaƙuwa wanda ke tsakanin uwa da yarta Ummey tace. "Gaya min mana, me Ya Salmanun yayi?". Konciya tayi gefen Ummi dake bisa sallaya, kana a hankali tace. "Wai yana sona, Ummey ina tsoro Ya Ba'ana zai illata mishi rayuwa, gashi kwanan nan Ya Hashimu ya rasu, kuma shima ance kasheshi akayi, Ummey ki cewa Bappa na, yacewa Baba Arɗo ya hana Ya Salmanu cewa yana sona, kinji ko Ummey?". Kai Ummey ta jinjina mata tare da cewa. "To zaki aureshi kenan duk da kinsan baya salla kuma yana tsafi". Kai ta juya tare da cewa. "Bazan aureshiba Ummey, amman ya Salmanu yayi shiru, bari in gama karatuna, in sha Allah akwai mafita in na gama karatuna, Ummey kin gane ai ko? Kin tuna ko". Murmushi Ummey tayi kana tace. "Eh na gane, yanzu konta kiyi baccinki". da haka suka konta bacci. Bayan kwanaki, sosai lamarin Ba'ana yake bawa mutane tsoro, mutun kamar ifiritu, dan yanzu yanayin sihirinshi ƙaruwa yakeyi sosai, Wasu lokutan ba hawa ba sauƙa sai dai kawai ka ganshi a gabanka sabida yanzu layan ɓatarshi tama fi ta baya ƙarfi, ya dage wai zai bawa Shatu taƙi fir daya matsama kuka tasa mishi hakanne yasa ya hakura ya barta. Ya Salmanu kuwa yanzu ya dage kan batun soyayyarsa da Aysha, ita kuwa tsoron abinda zai faru ya hana yarda da kowa, gaba ɗaya kuma yanzu Ƙabilar ɓachamawan nan masifa tuƙuru suke neman fulanin Bani dashi sabida baƙin ciki da hasadar ganin yadda shuke-shuken wurin fulanin yayi kyau, shinkafa, masara, dawa, gero, maiwa, wake, gyaɗa, gujjiya, riɗi, da dai sauransu. Ga tarin bishiyoyi dorowa da suke zagaye da garin wanda kan ko wacce bishi akwai jingogin zuma, shiyasa garin suke da tarin zuma. To waɗannan abubuwan sune suke ƙara tunzura kafuran, sabida gani suke aifa da filin nasune, sun mance kafin a saida wa fulani filin kufayine, fulaninne suke tafe da al'barkasu a jikinsu. Zuwa yanzu kowa na Rugar Banin da kewaye yasan masoyan Shatu biyune, kuma za'ayi shaɗi, wanda tsawon shekaru biyu kenan ba'ayin ba. Kowa in yaji da Salmanu za'ayi ana tausaya mishi domin shi mutunne mai laushin jiki shiyasa tun yana ƙaraminshi aka meda hankali kan karatun da yakeso, hakane yasa yayi karatun shi yanzu haka yana zama cikin Shikan ne inda yakeda shagunan kayan tireda sabida bazai iya noma da kiwo ba, kuma Alhamdulillah kasuwar ta amsheshi. Shiyasa shi zuwa yakeyi Rugar Bani ɗin. A can ƙasa mai tsarki kuwa, Yau kwanansu Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da Sittinshi goma da zuwa, to kasan cewar zasu gudanar da aikin Umarne yasa tun randa suka cika kwana uku da zuwa suka tafi, Madina, Kuma sun bar mgnar batun Jazrah cewa sai sun gama gudanar da aikin Umararsu kafin su shaida mishi, kana in sun dai-dai ta da Jazrah sai su shaidawa Mai alfarma Sarki Jalaluddin, shi kuma yaje har Ɓadamaya ya shaidawa mai daraja sarki Nuruddeen Bubayero, da kuma Habeebullah, batun auren in yaso su shirya suzo ayi ɗaurin auren. To yau kwanansu takwas a Madinah kuma yaune suke shirin dawowa makka. Kullum sai sun gaisa dasu Hajia Mama dasu Jalal. Kullum yakan kira Juwairiyya. Da maraicin suka isa cikin Makka kai tsaye masarautar suka wuce. Bayan sun gaggaisa, Sheikh Aliyu yace suje su huta, kafin su gaisa da Sheykh Abdulkareem domin yana tare da manyan baƙi. Haka kuwa akayi, bayan duk sunyi wonka suka dawo falon Sitti. Suna zaune cikin shiga ta al'farma a wuri na al'farma, an zagayesu da dukkan kayan jin daɗin rayuwar duniya, Sitti na zaune bisa tsakiyar falon akan wani tattausan carpet, Jannart da Jazrah suna gefenta, cikin shiga ta al'farma, Sheykh kuwa zaune yake bisa wata lumtsimemiyar kujera kana sawunshi na kan wasu tim-tim masu masifar kyau da taushi, wasu kyawawan larabawane guda biyu suke zaune a gaban Sitti sawunta dake bisa tim-tim ɗin sukeyiwa tausa. Yayinda wasu hadiman kuma ke shirya musu ababen ci dasha dangin yayan itatuwa kamarsu, Inabi, tupa, ayaba, dabino, gabaruwa, sai zam-zam kana, saisu shawarma and pizza da kuma wasu irin manyan Foodflaks da aka cikasu da danƙawa-ɗanƙwal dajaja sai sauran abincinsu na larabawa. Haroon kuwa gefe yake kusa da Jannart suna ɗan taɓa hira. Wayarshi ce ta fara ringgin a hankali, idonshi ya ɗan juya ya kalli wayar ba tare daya juya kanshiba, Da idonshi ya nunawa hadimin dake gefenshi wayar, da sauri ya ɗauko wayar ya miƙa mishi, ganin Hajia Mamace ya sashi amsa kiran. Kara wayar yayi a kunne cikin girmamawa yace. "Barka da dare Hajia Mama". A can gida kuwa cikin wani irin salo na musamman Hajia Mama ta rufe idanunta tare da cewa. "Uhum ka manta Jabeer mu nan yammane". Idonshi ya ɗan ɗago ya kalli agogon dake jikin ginin, a hankali yace. "Haka nefa Hajia Mama. Ya gida yasu Jalal". Murmushin jin daɗi tayi tare da cewa. "Suna lfy gasuma nan kusa dani, Jamil ne ya tsokano Jalal shine suka shigo sunata muzurai". Kanshi ya jingina da jikin kujerar, a hankali yace. "Hajia Mama kiyi musu faɗa kice su barifa sun girma". Murmushi mai sanyi tayi tare da cewa. "Na gaya musu sunma daina gasu nan sunata hira kuma". Gyara zamanta tayi kana taci gaba da cewa. "Ina Sitti na?". A taƙaice yace. "Gata nan kusa dani". Cikin yanayin jin daɗi tace. "Bata waya". To yace kana ya miƙa Sitti daketa kallonshi wayar, da sauri ta amsa tare da karawa a kunne, murmushi tayi jin muryar Hajia Mama na cewa. "(Allah beddu sabbugo Sitti), Allah ya ƙara nisan kwana Sitti". Amin Amin tace, kana suka gaisa cikin tsananin jin daɗi. Bayan sun gama wayarne kuma Juwairiyya ta kira Jannart nan suka gaisa ta bawa Sitti wayar hirar tasu kab kan ya Jafar ne. Saida suka gama wayarne ta kalli Sheykh dake kishinƙiɗe ya lumshe ido a hankali tace. "Juwairiyya tace , yau tun safe Jafar ya shiga sashinka yayi ta nemanka ɗaki ɗaki, da bai gankaba yaƙi fitowa sai kuka yake tayi, har saida yammane da Jalal ya dawo gida shine ya lallasheshi ya maidashi sashinsu. Hannu tasa ta share hawayenta da ke kwaranyowa, Haroon ma hawayen ne ke zubo mishi, Haka Jazrah da Jannart, Shi kuwa Sheykh cikin sanyi yace. "Lamiɗo ya gaya min ɗazu da mukayi waya". Shiru sukayi baki ɗayansu, a hankali Haroon ya miƙe kwance tare da faɗawa nazari mai zurfi. Nan kuma kiran Umaymah ya shigo wayar Sitti still hira sukayi sosai wanda ta kontar musu hankali kafin, sukayi sallama da juna. Yau jumma'a ne gajeren lokacine basa kai yamma a wurin kiwo, kafin azahar suke dawowa, shiyasa yau Shatu tace da ita za'aje kiwo. Dariya kawai sukayi mata dan sun san ba iya jurewa zatayiba amman tunda ta kafa ta tsare cewa dole zataje, sai aka barta. Kasan cewar basu kai yamman bane yasa kuma suna tafiya da wuri. Bayan duk an kunce dabobbin gaba ɗaya, hakama sauran makiyayan baki ɗaya, sahu- sahu shanayen keta wucewa. Sun tafi tun shida da rabi na safe, Kafin zuwa tara na safe sunyi nisa cikin wurin kiwonsu, inda nan kuma Aysha ta samu su Hindema sunzo kiwo, wanda su kullum dama suna zuwa. Wani irin hadarine mai ƙarfi ya taso daga ƙasa, ganin hakane yasa, Gaini kwallawa Shatu kira wacce take can cikin ƴan uwanta mata makiyaya, jin shiru bata amsa bane ya nufi wurin da suke zaune, Cikin kula yace. "Aysha tashi keda Hinde dasu Mero duk ku tafi gida, kunga hadarine mai ƙarfi ke tasowa daga ƙasa da alamun za'ayi ruwa mai ƙarfi". Cikin ƙarfin hali da son wasa cikin ruwan da taketa hari murya a sanyaye tace. "Ba komai ya Gaini zamu jiraku ai lokacin tashi kuma ya kusa ko?". Su Giɗi dasu Aro da sauran makiyayan ne sukace. "Ya Gaini barsu mana ba kiwo zasuyi ba ai makiyayin shanu da tumaki baya gudun ruwa duk yawa shi". Cikin jin daɗi sukace, eh mana, Shi kuwa Ya Gaini murmushi kawai yayi tare da cewa. "Shike nan yau zakusha dukan ruwa". Murmushi sukayi sukace "Babu matsala". daga nan mazan duk suka koma wurin kula da dabobbin nasu da suka duƙufa cin koren ciyawa. Su kuwa Shatu da Hinde a hankali sukaci gaba da tafiya, sosai tsarin wurin da yanayin shigar suturar dake jikinta yayi tsananin dacewa da ita. Doguwar rigace irin tamu ta fulani, yadin farine, sai daga samanshi akayi mishi kolliya da zaron huɗu, mai color red white, blue, yellow, and green, wanda aka ƙawata saman rigar da kolliyar zanen ɗawisu, inda daga kafaɗunta har zuwa saman ƙirjinta, duk an shimfiɗa zaren, bisa wuyan rigar mai V. sai kuma hannun rigar shima duk an zagayeshi da kolliyar, Kana sai tsakiyar rigar dai-dai kan ƙugunta shima an ƙawatashi da wannan kolliyar ulu irin namu na fulanin daji, Kana sai ƙasar rigar can itama an ƙawata da wannan zaren. Sai dogon gashin kanta da yake zube a kafaɗunta, yayinda daga saman goshinta kuma tasa, bandana amman irin namu na fulani mai kalolin ƴaƴan tsakiya, ta zagaye kanta dashi, sai kolliyar da tayi a fuskarta irin ta asalin fulani, a goshinta zanen kan shanu tayi, shaidar cikekkiyar bafulatanace, sai kuma ƙasan lip ɗinta na ƙasa zuwa kan ɗan gemunta shi kuma taja zane da kuma yin ɗigo-ɗigo a gefenshi. Sai wata kekkewar jakar sakan ulun mai kalolin kolliyar jikin rigarta data rataya a hannun damanta, wanda cikin jakar kuma ruwan shantane a ciki sai sassanyan kinɗirmo da goran zuma, sai ɗan sandar mu ta gado, takalman sawunta irin sau cikin nanne daku mutanen cikin birane kuke masa laƙabi da tashi kabi shanu. Tayi masifar kyau a cikin wannan shigar tamu ta gado, kyau iya kyau farar fatarta ta baiyana tamkar balarabiya gashin girarta ya konta lib lib. A hankali suke ɗan tattaki a cikin dogayen saunukan, da koriyar ciyawa da tayiwa ƙasanshi ƙawanya. suna ɗan tafe Suna ɗan tsinkar ya'yan kanya da gwandar daji da suke cike da wurin Chaɓɓulle wato tsada. Hadari kuwa sai gamgami yakeyi gabas da yamma kudu da arewa, ko ina yayi dib babu motsin komai sai nasu dana dabobbin su, Iska ta tsaya cak koda ganye ɗaya baya kaɗawa duhu ya kareɗe illahirin yankin. A hankali Hinde ta kalli sararin samaniya cikin tsoron ganin gaba ɗaya duniyar tayi baƙiƙƙirin ko ina yayi dib, hakanne yasata ɗan zaro ido tare da cewa. "Kai Shatu, kalli sama, fa hadarin nan yayi duhu da yawa gsky mu tafi gida". Da sauri ta ɗago kanta kana tasa hannunta na hagu ta ɗan kare saman goshinta kaɗan, ware idanunta tayi ta kalli sararin samaniya, wani irin azabebben firgita da tsorone ya rufeta wanda yasa ta juya da azaban ƙarfi ta ruggume Hinde dai-dai lokacin, sukaga wani irin tartsatsin azabebben igiyar...! Dan Allah da Manzonsa in dai kin san zaki sayi littafinane ɗan ki fiddashi na roƙeki da Allah da Manzonsa da darajar su. Kada ki saya bana so, ki riƙe kudinki. By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 9 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *FREE PAGE* *TURO KATIN MTN NA ƊARI UKU KACAL ta wannan number 09097853276 DOMIN SAMUN DAMAR KARANTA littafin GARKUWA, ba tare da haƙƙin kowa a kankiba. Akwai Special Group shi kuma na 1k rak, ki turoshi ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai ta WhatsApp 09097853276* ~Ga masu buƙatar kayan gyara na amare, akwai set-set masu kyau, a ƙananan robobi masu sauƙin kuɗi, akwai kuma na manyan robobi masu zafi, akwiasu dai-dai da tsarin al'jihun mai ƙarfi da mai rauni, ina araha ina hana bashi. Koda kuɗinka saida rabonka, kayan Kamfani daban dana shago.~ *Al'ummar Hausawa mazauna Saudiya wannan shafin nakune kyauta gareku, domin jiya da yau saida mai zaton babu wasu masu karanta littafi sama daku. Nasha mamaki da sanyin safiya naita cin karo da numbers ɗin ƙasa mai tsarki suna ta antayo min manyan kuɗi na ƙasa mai tsarki tun ina ƙidaya numbers ɗin +966 har dai abun yaci tura sabida yawansu, ashe daga zauren Umar Maisanyi sukayi ta antayowa gareni. Godiya mai tarin Yawa Umar maisanyi mai Tsakar gida You tube limamin tsakar gida* Walƙiya mai tsananin haske da tartsatsi wanda saida ya haska gaba ɗaya, dajin ya zamana, har kana iya ganin inuwar dogayen bishiyoyin wurin da sukayi musu ƙawanys. Wani irin tsoro da firgici da karkarwan ne ya bijirowa Aysha. Cikin dauriya da sabo da ganin ire-iren irin waɗannan ababen a wurin kiwo, Hinde ta kamo hannun Shatu tare da cewa. "Kai Aysha babu komai fa walƙiyace kawai fa kai". Sai kuma tayi dariya tare da cewa, "Uhum a hakan kike tunanin jurar taraddadin da muke gani cikin tsaunuka in muna kiwo". Janye jikinta tayi daga jikin Hinde, hannun tasa ta tattare gashin kanta dake baje a kafaɗunta, tubkeshi tayi cikin, fidda numafashin tsoro take karisa addu'o'in datake tayi a bakinta, a hankali taja da baya ta jingina da jikin ƙatuwar bishiyar Gamji dake gefensu, jingina kanta tayi jikin bishiyar gamjin tana jin yadda zuciyarta ke harbawa, pat-pat da azaban ƙarfi domin tasan Hinde bata san me idonta ke shirin hango mataba, ita kuwa Hinde, a gabanta take tsaye ya zamana sun fuskantar juna. Su Ya Gaini kuwa sun duƙufa kiwonsu kamar dai yadda suka saba, ruwa ko iska ko zafin rana da ƙishi baya kora makiyaye daga kiwo a daji ya dawo gida. So duk kowa yana yankin da yake bawa dabobbin tsaro, sam basuma hango su Aysha sosai. Ita kuwa Shatu idonta dake lumshe ta fara ƙoƙarin buɗewa sabida wani irin tashi da taji tsikar jikinta nayi. Hinde kuwa ido ta zuba mata tana ganin yadda ƙirjinta yake sama da ƙasa alamun tsananin firgita. A hankali ta ware manyan kyawawan idanunta. Wani ƙaton curi, dake can bayan Hinde ta zubawa ido sabida wani abu da take gani kamar hayaƙi yana fitowa ta ƙananan ƙofofin curin. Ita kuwa Hinde bata san meke wakana ba sabida, ita baya ta bawa curin, asalima yanzu kanta ta ɗaga sama tana shan ruwan dake cikin goranta. Ita kuwa Shatu so take ta janye idanunta daga kan wannan CURIN amman sai taji ta kasa, bugun da zuciyarta keyine ya tsananta, lokaci ɗaya jikinta ya fara tsuma da karkarwa zufa mai azabar zafi ta fara tsastsafo mata tako wani hudan gashin jikinta. Yayin da zuciyarta. Ke harba jini one litter. A Cikin ko wanne one second. Bakinta ta buɗe da nufun furta addu'o'in dake jere a zuciyarta amman sai taji ta kasa, zuru-zuru tayi da idanunta lokacin da taga wani dogon abu yana fitowa daga cikin babban ramin dake tsakiyar CURIN nan, a hankali ta ɗaga kwayar idanunta sama tana bin abin da kallo, wani irin dogon numfashi taja, ganin abun nan yana miƙewa yana yin sama, abun dogo kamar igiya sai dai kuma yanada zane kala-kala red, yellow, green, blue. Kuma abun biyune ɗaya a sama ɗaya a ƙasa, cikin ranta take iya ammabaton sunan Allah ganin zahiri fitowar bakan Gizo daga cikin curi Allah ya nuna mata, ras zanen bakan Gizon nan yayi kama da kalolin kolliyar jikin rigarta, Kanta ta ɗaga sama, tana bin Bakan Gizon da kwayar idanunta, tana gani har ya haura sama can ya konta a gicciye gabas da yamma kudu da arewa, kana kuma mai hasken ras yana sama mai ɗan dishi-dishin yana ƙasa. Wanda a falsafar al'ummar Duniya ake cewa suma mata da mijine, muddin kaga mai hasken in ka zuba ido zakaga mai dishi-dishin wanda akecewa, mijin shine dishi-dishin kuma shike goyo matarsa shiyasa sai ake ganin mai hasken shine a sama. Wasu irin numfarfashi take ja da azaban ƙarfi da razana, kar-kar haka jikinta ke rawa. Cikin tsoron halin da take ciki Hinde ta wurgar da goran dake hannunta, tare da cewa. "Hande en boni, yau munga ta kanmu Shatu me haka meya sameki?". Ina babu mgna sai zamewa da ta farayi tanayin ƙasa alamun zata faɗi, ganin hakane yasa, Hinde juyowa da ƙarfi ta fara rabƙawa su Ya Gaini kira. "Ya Gaini! Ya Seyo! Ya Lado, Wayyo Ya Giɗi kuzo kuga abinda Shatu keyi". Maganarta ta karshece ta sasu, tasowa a guje gaba ɗayansu suka nufosu da gudu, kafin su isoma Aysha ta faɗi ƙasa zaune, sai karkarwa da rawan sanyi takeyi. Suna isa Ya Gaini yasa hannu ya tallabota ganin yadda taketa karkarwa, idanunta na rufewa, Seyo ne ya kalli Hinde cikin kiɗima yace. "Subahanallahi Hinde me ya sameta?". Cikin kuka Hinde tace. "Ban saniba wallahi haka kawai naga tana karkarwa". Giɗi ne ya zauna kusa da yayan nashi kanshi ya sunkuyo kanta yana kiran sunanta a jere a jere. "Aysha! Shatu. Ayshatu tashi buɗe idonki ki gaya min meya sameki meke miki ciwo". Ina babu magana saima kara rumtse idanunta da tayi tare ƙara ƙaƙƙame jikin Ya Gainin nata. Ya Lado ne da Seyo suka sunkuyo kanta addu'o'in suka rinka tofa mata, duk addu'ar da tazo bakinsu tofa mata sukeyi, Giɗi kuwa ruwa yasa a tafin hannunshi yana shafa mata a fuskarta. Cikin al'hini sauran makiyayan duk suka iso kansu, ganin yadda suke birkice ne ɗaya daga cikin ƴaƴan Alhaji Haro da kuma Alhaji Umaru sukace. "Gaini mu tafi gida da ita, tunda dama lokacin tashinmu yayi, an kusa fara tafiya masallacin juma'a." Cikin damuwa Giɗi yace, "To ai bazata iya tafiya ba". Seyo ne ya miƙe cikin sauri yace. "Bari inje in kawo doki sai mu ɗaurata a kai". Da sauri Manu ɗan Alhaji Haro yace. "Yauwa yi maza, kunga ku kuma Gidi kuje duk ku haɗo mana kan dabbobi ku fuskantar dasu hanyan gida". Ai kuwa haka akayi sauran yaran duk suka kaɗa shanun. Koda Seyo ya kawo dokin, shida kanshi ya hau baya sannan aka ɗaura mishi ita a gabanshi, a haka suka nufi gida. Koda suka isa gida, da kanta ta taka har zuwa cikin gida, suna biye da ita a baya. Kai tsaye ɗakin Ummey ta shige, bisa gado ta konta ta duƙunƙune tana rawan sanyi. Da sauri Ummey da Inna da Junainah suka biyota a baya. Cikin tsoro Inna tace. "Subahanallahi Shatu meya faru". Ummey kuwa gefenta ta zauna, tare da jawo borgo tana rufe mata jikinta. Giɗi ne da yanzu ya shigo, shine ya basu lbrin iya abinda suka sani. Seyo kuma cewa yayi a mata hayaƙi. Haka kuwa akayi sukayi mata hayaƙin kana Ya Gaini ya zauna yayi mata rubutu nanma aka wonke aka bata. Jin jikinta yayi zafi jau ne, alamun zazzaɓi ne ya rufeta yasa, Ya Lado yaje ya ɗauko mata mgnin a ɗakin Bappa, nan Ummey ta bata tasha, a take bacci ya ɗauketa. Ummey kuwa da Inna woje suka fito sunata dariya dan su a zatonsu ko gajiyane yasata hakan tunda ita dai bata saba zuwa kiwoba tunda tanada yayu maza da yawa. Koda akayi sallam Juma'a aka idar, su Bappa da yaranshi kab basu dawoba saida akayi sallan la'asar kafin suka dawo gida. Ummey kuwa da Inna aikin abincin dare sukeyi wanda girkin ranar jumma'a na dabanne, zabbi biyar suke yankawa kullum jumma'a wata rana kuma tattabaru wani lokacin kuma jan nama Bappa ke saya to yauma hakanne. Inna ce zaune tanayi musu wonke-wonke yayinda Junainah kuwa keyin shara, dama wonke-wonke aikintane to duk randa takeji tsiya sai tayi ta ƙorafi, shiyasa yau tana farawa Inna ta fara aikin. Ummey kuwa tana cikin kitchin ɗinsu, wanda dama da Shatu lfyarta lau muddin tana gida ita keyi musu, girki domin Ummey ta horeta da iya girke-girken na ban mamaki. A hankali Shatu ta bude idanunta daga baccin da takeyi, Cin karfin jikinta ya ɗan dawo, a hankali ta tashi zaune, da sauri ta fito woje, sabida ganin ita ɗaya ne a ɗakin. Da sauri ta fito, Inna ce ta ganta cikin kula tace. "Shatu kin taso?". Kai ta gyaɗa mata alamar eh. Cikin kula tace. "To ya jikin naki?". A hankali tace. "Da sauƙi, Inna zanyi wonka". Mikewa tayi dan dama ta gama wonke-wonken. Botiki ta ɗauka kitchin ta shiga, ruwan zafi ta ɗebo nan take cewa Ummey. "Shatu ta farka". Murmushi Ummey tai tare da cewa. "Na jita ai wai zatayi wonka, ke kuma harda biye mata kamar ta shekara ba lfy, Shatu ba dai rakiba". Dariya suka ɗanyi, ita kuwa a tsakiya gidan ta zauna kan dakalin da ke gindin bishiyar ceɗiya dake wurin. Bayan inna ta kai mata ruwan ne ta kalli Junainah cikin sanyi tace "Junnu zoki rakani inyi wonka Mana." Ido Inna ta zaro tare da cewa. "Hahhh Shatu yau kuma ta rakaki wonkafa kikace". Kanta ta gyaɗa cikin raunin fuska tace. "Eh Inna tsoro nakeji shiyasa". Ummey dake kitchin ne ta fito rike da aikoshn data zuba zabbin data soya a ciki, tace. "Shatu ki rage tsorofa". Kai ta gyaɗa kana taja hannun Junainah tare da ɗaukan kondon kayan wonkanta, A bakin ƙofar mashiga bayan gidan tace. "Yauwa Ƙanwaliya jirani a nan". To Junainah tace, haka ta tsaya tana jiranta, Ita kuwa wonkanta tayi, a nitse kana, tana fitowa. Tayi al'wala, ɗakin Ummey ta shiga, sallan azahar da la'asar ɗin tayi, sannan ta zira wata tattausar doguwar riga. Turare ta ɗan fesa kana, ta fito, Gefen katangar kitchin ɗinsu ta samu Ummey tana haɗa wuta a murhun dake wurin. Inna kuwa zaune take a gefe, da turmi a gabanta, kana tana jajjaga tattasai da tumatur da kuma tarugu da al'basa. Taburman data fito dashine ta shimfiɗa gefensu. Inna ce ta kalli Junainah da itama yanzu ta fito wonka tace. "Yauwa Junainah zoki kawowa Addanki abinci." To tace kana tazo ta shiga ɗakin Inna. Ta fito da tire a hannunta da wasu ƴan kananun robobi guda huɗu a kai masu marfi, sai kuma kula a tsakiyarsu. A gaban Shatu ta ajiye kular. Kana ta wuce ta nufi ɗakin Ummey. Ita kuwa Aysha kular ta buɗe, dambun zogalenen a cikin wanda yaji, ganyen zogalen da kuma al'basa, sai tururi yakeyi. Ƙananan robobin kuwa, ɗaya dakekken yajin ƙaragone wanda yaji magi da borkino da kuma tafarnuwa. Kana ɗaya robar kuma, soyayyan man shanune a ciki. Ɗaya kuma yankekken al'basane da kuma tumatur, sai dafeffe kwai duk a yayyanka, Kana ɗayan kuma dambun namane mai laushi, a ciki, ɗan karamin aikoshin dake gaban Ummey taja, ta zuba dambun, kana ta zuba sauran kayan hadin. A hankali ta fara ci. Junainah da ta fito yanzune ta kalla tare da cewa. "Junainah bani ruwa". To tace kana ta juya ta nufi gindin randunarsu inda suke jere a ƙalla sun kai shida ko dan ba manya bane dukansu na taɓone masu ɗan karen sanyi, ga kuma inuwar bishiyoyin ayaba da sukayiwa randunar ƙawanya, Shiyasa ko yaushe ruwan zakajishi kamar na firiji, A kofin silver ta ɗebo mata kana tazo ta zauna gefenta, sunaci a tare. Ummey kuwa tukunyar ƙasa ta ɗaura a wuta tare da tsulala man shanu, a ciki. Kayan miyan da inna ta kirɓa ta amsa ta zuba a cikin manda yayi zafin ta fara soya miyar, zabbin da zatayi musu. Kana ɗaya murhun kuma ruwan tuwo ta aza a tukunyan ƙarfe. Inna kuwa data gama kirɓa kayan miyar, shinkafar tuwon ta ɗebo tazo tana wonkewa. Suna cikin haka su Bappa da yayunta maza suka dawo. Nan suka shimfiɗa katuwar taburma a tsakar gidan. kana Giɗi ya ajiyewa inna ledodin tsarabar jumma'a da Bappa kanyi duk ranar sati. Tirirruka Ummey ta miko mata ta baza, juye kayayyakin a cikin. Reke,Lemu, kwakwa, da Giginya, da kuma dafaffiyar gyaɗa, da ƙosai mai zafi da biredi da soyayyen doya da fulawa mai jawa. kayan cimarmu kenan fulani Zubawa maza nasu akayi, aka basu a tsakiyarsu suka ajiye sunaci da mahaifin nasu. Shatu kuwa da Junainah aka basu nasu. Ummi da Inna kuwa sun ajiye nasu dan aiki sukeyi. Ya Gaini ne ya ɗan danki ƙosai da bredy yasa a bakinshi, tauwana yayi kana idanunshi na kan Aysha saida ya haɗiye kana yace. "Shatu, ya jikin naki?". Murmushi ta ɗanyi sai kuma ta ɗan harari Junainah dake cewa. "Uhum ta worke ai dama kawai hegen tsorone da raki". Dariya sukayi baki ɗayansu. Seyo ne wanda yakeda tarin jinƙai da nitsuwa, ya ɗan afa geɗan daya ɓare a bakinshi tare da cewa. "To Amman Shatu meya samekine lokaci ɗaya kika firgita?". Giɗi ne da shi kuma doya yakeci yace. "Kamar mai cutar al'janufa ta zama". Bappa ne ya ɗan kalleta cikin kulawa yace. "Shatu meya sameki ne?". Murmushi ta ɗanyi tare da kallon Ummey dake cewa. "Uhum tsorone da gajiya fa". Kai ta jujjuya a hankali tace. "Allah ko Ummey ba tsoro bane". Sai ta kuma meda hankalinta kan Bappa cikin sanyinta tace. "Bappa naga abinda ya firgitanine. Shin Bappa dama bakan Gizon cikin curi yake fitowa ne?." Cikin mamaki suka zuba mata ido baki ɗayansu. Bappa ne da kanshi yace. "Ban fahimceki ba Shatu". Bredy dake gefenta ta gutsura kana ta dandola da zuman data sa Junainah ta kawo musu, a baki ta ɗansa ta tauna kana a nitse ta basu labarin abinda ta gani da kuma yadda taji, ta ƙara da cewa. "Bappa dama bakan Gizo a curi suke fitowa ne?". Cikin mamaki da al'hini yace. "Allahu al'alamu. Sai dai koma menene, lallai tabbas akwai abinda ke tunkarar rayuwarmu, fatana mu dage da addu'a koma menene Allah ya kawo mana shi kan al'khairi ya kuma sauƙaƙa manashi, zan kuma bincika in sha Allah. Sannan kada ku gayawa kowa mgnar nan". Ya karishe mgnar da kallon Junainah. Wannan labari ya sasu cikin dogon nazari. haka dai sukaci gaba hira kamar yadda suka saba. A can cikin yola kuwa, yau tunda Ya Jafar yaje sallan juma'a ya dawo baiga Ƙaninshi Sheykh ba, gaba ɗaya ya tashi hankalin ƙanenneshi da iyayenshi. Domin kama hannun Jalal yayi yana kuka, yana jan Jalal zuwa sashin Sheykh koda suka shiga, Jamil kuwa sashin mahaifinsu ya nufa. Ba tare da ya saurari Hadiman ba ya wuce. A babban falon ya samu , Abba Haurawa sama yayi yana shiga kuwa ya sameshi a falo shida jarabebboyar amaryar tasa cingom dinshi. Sai dai tana konce bisa kujera, Shi kuma yana zaune bisa sallayane ya fuskanci al'ƙibla, da ƙur'ani a gabanshi yana karatu cikin suratul Khafi. cikin rauni Jamil ya ƙaraso gabansa. Bai kulashiba har saida ya kai ƙarshen surar kana ya shafa addu'a. Cikin haɗe fuska da alamun faɗa yace. "Jamil lfy kuwa mehakan?". ido na zubda hawaye yace. "Abba Ya Jafa". Rai a hade yace. "To me zan mishi?". Cikin zubda hawaye yace. "Abba tunda aka dawo aka sauƙo sallan jumma'a fa yaketa kuka yana bin Jalal yana kuka alamun a kaishi wurin Hamma Jabeer, yau ko abinci baiciba, Aunty Juwairiyya ma sai kuka takeyi hakama su, Jiddah." Tsaki ya ɗan ja tare da cewa. "To ni zaka gayawa? Kaje ka gayawa Mamanku mana". Wasu sabbin hawayene suka zubowa Jamil a hankali ya juya ya fita". A can sashin Sheykh ya samesu, Juwairiyya da Jalal ɗin da Affan sun tasashi a gaba, Affan yanata kuma, shi kuwa Jalal sai tattaune laɓɓansa yakeyi, da sauri Jamil ya iso cikin sanyi yace. "Affan je ka gayawa Mama". Da sauri Affan ya juya har zai fita kuma ya dawo jin Juwairiyya na cewa. "No Affan kada kaje, ka gaya mata, nasan yanzu tana bacci ne". Shi kuwa Ya Jafar sai ya shiga ɗakin nan ya fito ya shiga wancan ya fito yana kuka kuma. Shigowar Abbane ya sasu su Jalal duka fita. A hankali Abba ya kamo hannunshi suma suka fito, da mamaki a fuskar Jamil ya bisu da ido. Shi kuwa Abba yana riƙe da hannun babban ɗan nashi suka wuce har makoncinsa, Gefen gado ya kontar da dashi, kana a hankali yake shafa kanshi cikin taushi da tausayawa yace. "Jafar kayi haƙuri kayi baccinka kabar kuka, Sheykh yana lfy lau, ya tafi ƙasar Saudia ne shida kakarku Sitti." Shiru yayi yana kallon mahaifin nashi. Shi kuwa Abba, kanshi yake shafawa yana kontar mishi hankali a take yayi baccinsa. Bayan sallan ishane Jamil yaje wurin Kakansun ya sanar mishi halin da ake ciki ya ƙafarsa cewa. "Allah rene, magar gsky kace Hamma Jabeer ya dawo, sabida abin ya Jafar yana tsananta in bayanan". Murmushi kakan nasu yayi tare da cewa. "Uhum ai Allah ya sauƙaƙa abinda zai taso Sheykh ya dawo ba tare da an gama dai-dai-ta abinda ya kaishi ba Dole shi wannan mai saɓulellen mondon Jalaluddin shi zai dena yawon iskanci ya zauna ya kula dashi tunda yafi kallonshi a madadin Sheykh". Cikin takaici Jamil yace. "To ni zan kai Ya Jafar saudia wurin Sheykh ɗin suci gaba da zama a can in sun so, tunda dai kun san Sheykh shine GARKUWAnmu". Cikin kontar da murya kakan nashi ya ɗan tausasashi kana yace in yaje ya turo mishi Jalal. A can Saudia kuma, sosai aketa shirya yadda ɗaurin Auren Sheykh da Jazrah zai kasance, duk da basu sanar mishiba, sabida kashedin da Sarki Jalaluddin da Nuruddeen sukayi musu dan ko yaushe in dai ana shirya batun aurenshi muddin yaji sai yaƙi fir yayi ta kaucewa dole a ƙarshe aure ya fasu, to wannan abunne yasa ba'a sanar mishiba. Sai dai yasan batun zuwan da Jazrah take sashinsu wai nune da ita suke zaɓa mishi in tayi mishi. To shi kuwa bayan gaisuwa ko sannu bai taɓa haɗasu da itaba. Haroon kuwa da Jannart sunata shirye-shiryen dawowa gida Nigeria. A garin Bani kuwa, Yau tun bayan sallan isha'i yaro ya shigo yace, Ya Salmanu yana sallama da Aysha, haka kuwa ta fita taje, Suka zauna a dakalin ƙofar gidan nasu suna hango yadda, Yara keta wasa a dandali domin ranar jumma'a tafi ko wacce rana a garesu wurin shanawa. Ya Gaini ne ya fito riƙe da hannun Junainah, a bakin ƙofar suka wuce Su Shatu Bayan sun gaisane ya wuce riƙe da hannun ƙanwar tasa, Murmushi Salmanu yayi tare da cewa. "Shatu, inaga dai aurenmu dana babban yaya rana ɗaya za'ayi shi". Murmushi itama tayi, tare da cewa. "Tab shifa har an kai kayan aure". Ido ya ɗan lumshe tare da cewa. "To ai in kin bani dama nima gobe-goben nan sai a kawo kayan aurenmu ko?". Da sauri tasa tafin hannunta ta rufe fuskarta, alamun jin kunya. Su Ya Gaini kuwa kai tsaye ƙofar gidan Ahaji Haro sukaje, A bakin ƙofar suka tsaya, sunkuyowa ya ɗanyi a hankali yace. "Yauwa ƙanwaliya maza shiga cikin gidan kicewa Addanki Bintu tazo". Cikin happy tace. To kana ta shiga cikin gidan da sallama. Kamar yadda gidansu yake hakama gidan Ahaji Haro duk suna zaune a tsakiyar gida da yaranshi da matanshi sunata hira, bayan ta gaidasune taje gefen Binto cikin raɗa ta gaya mata saƙon ƴaƴansu. Wani ɗan kekyawan matashi ɗan kimanin shekaru sha takwas mai sunan Junaidu ne ya kalli Junainah cikin tsananin so da ƙaunar yarinyar yayi murmushi tare da taɓa mamanshi cikin raɗa yace. "Inno ga surkarki in Allah ya yarda". dariya suka ɗan yi dan kowa yasan Junaidu yasan son da yakewa Junainah tun tana ƙaramar ta. Ita kuwa Junainah hannun Binto ta riƙo suka fito tare, Junaidu na biye dasu a baya, Koda suka fita, Gaini ne ya kalle Junaidu tare da cewa. "Yauwa Junaidu raka min Junainah gida ko". To yace kana yabi bayanta suna tafe suna hira, sunzo dai-dai ƙofar gidansu Ahaji Umaru ne suka samu Ya Seyo da Hinde suna hirarsu. Koda suka wuce, murmushi Junaidu yayi tare da cewa. "Junainah sai yaushe zan fara zuwa muma muyi hira ne?". Cikin yin ƙasa da murya tace. "Sai na ƙara girma kafin nan Addana tayi aure". Murmushi yayi tare da cewa. "Ko dai bakya so nane". Da sauri cikin yarinta tace. "A a ina sonka mana". Dariyar jin daɗi sukayi baki ɗayansu, sun zo kusa da ƙofar gidansu. Ya Ba'ana ne sukayi kiciɓis dashi, murmushi yayi tare da cewa. "Yauwa Ƙanwaliya kuzo mu shiga in baki aike ki kaiwa Shatu". To sukace kana sukabi bayanshi, a tsakar gida suka samu, Iya Bultu majaifiyar Ya Ba'ana kena ƙatuwar mace baƙa ƙarin da ita, ga jajayen idanu, fuskarnan a haɗe ta kalli Junainah dake gaidata da fullanci cikin tsananin tsawa tace. "Ke tafi daga nan ƴan iskan fulani masu jajayen kunnuwa, dan uwarki Ni ba fillatace da zaki gaidani da fullanci, hegu kwarkwasa fidda mai gida a gidanshi yan iska masu kama da al'janu, in sha Allah ƙarshen zamanku a wannan yanki yana nan tafe". Da sauri Junainah ta koma bayan Junaidu, shi kuwa Junaidu wani irin tafasa zuciyarshi keyi akanme zata zagesu dan kawai sun gaidata da fullanci. Bukar ne mijinta wanda yake babarbaree ya kalleta tare da cewa. "Kuma dai al'barkacin fulanin kikeci". Ba'ana ne ya ɗan harari mahaifin nashi tare da waskewa yace. "Fulani kecin al'barkacin ta dai, tunda kowa ya sani wannan yankidai na Ɓachamawa ne, ba fulaninba". Cikin ƙarfin hali Junaidu yace. "Ato ai dai ba kyau aka bamuba da kuɗin mu aka bamu, kai kamma ya Ba'ana kaifa bawanmu ne tunda kai babarbarene". Wani irin suka kalawan yaron suka mishi a ƙahon zuciyarshi amman sai ya dake, ledan su ayaba da inabin ya bawa Junainah tare da cewa. "Uhu Junaidu kenan aini ba bakanuri bane ni ba Bachamene, Dan da in zama bawan fulani gwara in zama bawan karnuka". Haka nan kalamansu ke tafasa zuciyar Junainah da Junaidu, haka yasa fuska a hade suka juya suka tafi, har sunje bakin ƙofar fita Ba'ana yace musu. "Yauwa kuce mata ina zuwa yanzu bari inyi wonka". To sukace kawai suka fita suka tafi. A ƙofar gidansu suka tsaya gaban Ya Salmanu da Aysha, ledan Junainah ta ajiye a tsakiyarsu cikin jin haushi tace. "Addana gashi inji ya Ba'ana wai in kawo miki, yace kuma yanzu zaizo wai wonka kawai zaiyi". Tana kaiwa nan tayi cikin gida shi ma Junaidu Binta yayi a baya, har gabansu Ummey ya tsuguna suka gaisa kana yace. "To Ummey ga Ƙanwaliya na rakota Ya Ganin ne yace in rokata har cikin gida". Murmushi Ummey tayi tare da cewa. "Mun kuwa gode, ka gaida min Innonka kace mata, in Allah ya kaimu gobe ta turo min Hari tazo tamin kitso". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "To saida Safe Bappa". Allah ya bamu al'khairi sukace baki ɗayansu. Daga nan ya fito, har ya wuce Ya Salmanu yace. "A a Junaidu zoka amshi tsarabar mana". Cikin girmamawa yace. "A a Ya Salmanu ya isheni". Cikin kula Salmanu yace. "Ni kam yaushenene zaku koma school?". Da sauri yace. "Saura kwana biyar hutunmu zai ƙare". "To Allah ya taimaka yanzu aji nawa kane". Murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "Ina SS 3 ne fa, Ya Salmanu na kusa gamawa ai". "Masha Allah, Allah ya taimaka". Amin Amin yace kana ya juya ya tafi. Ita kuwa Shatu cikin tsoro ta kalli Ya Salmanu a hankali tace. "Ya Salmanu tashi ka tafi kada yazo ya sameka". Cikin harshen fillanci yace. "To shi mala'ikan ɗaukan raine? Ko dai so kike in guje masane Shatu, kina son ragon mijine?". A hankali tace. "A a Ya Salmanu zai cutar da kaine nake tsoro". Da sauri ya katseta da cewa. "Babu mai rayawa da kashewa sai Allah, ko yaya zaiyi bashi da ikon kasheni sai in kwana-nane ya ƙare. Ko ciwon kai bai isa ya samin ba". Shiru tayi tana kallonshi. Sai kuma tai maza ta miƙe tsaye ganin kamar daga sama aka jefo Ba'ana gabansu. Kallon kallon sukeyiwa juna shida Ya Salmanu, cikin wani irin mugun kallo mai cike da mugunta yayi kwaffa tare da cewa. "Uhummm Salmanu manyan gari, wato har an samu wani mai yar guntuwar jarumtar da zai iya haɗa so dani a kan Shatu, to bazan ce maka komaiba, amman ka shirya ranar litinin zamuyi shaɗi muddin ka cini na bar maka ita duniya da lahira, zan kuma bar garin Bani, da ƙasar nan gaba ɗaya zan koma ƙasar Cameroon, in kuwa na cika zaka bar duniya baki ɗayanta!". Cikin tsananin tsoro da kaɗuwa Shatu tace. "A a fa Ya Ba'ana wlh ba sona yakeyiba, karatu yake koya min". Da sauri Salmanu ya katseta da cewa. "Sonta nakeyi Ba'ana so kuma na aure, na kuma yarda zan shiga gasar Shaɗi da kai a ranar Litinin na amince". Wata irin muguwar dariya yayi wacce har tasa Aysha kowa cikin gida da gudu, shi kuwa saida yayi dariyar mai isarshi kana yace. "Lallai gidan Arɗo Yabani na gab da rasa motsin ɗana miji". Yana faɗin haka ya murza layar zananshi, sai gashi ya ɓaci. Cikin ƙarfin hali Salmanu ya nufi gida. Shi kuwa Ba'ana yana ɓacewa a tsakiyar dottawan Fadan Arɗo Yabani ya baiyana,. Wanda badon tsoffin makiyayene sun saba ganin abinda yafi haka ba tabbas watsawa zasuyi. So amman suka dake, cikin kamala Bappa ya kalleshi tare da cewa. "A a Ba'ana lfy kuwa?". Sunkuyar da kanshi yayi kamar mutumin kirki, cikin danne fushinsa yace. "Ku gafarceni Bappa nazone da batun neman al'farma fagen shaɗi, nida Salmanu ɗan Arɗo zamuyi gasa kan Shatu, na kuma yarda, muddin yayi nasara akaina na bar mishi Shatu zan kuma bar Rugar Bani baki ɗaya". Da sauri Bappa yace. "A a". Da sauri Arɗo Yabani yace. "A a Malam Liman ba komai, na amince na basu damar yin gasar Shaɗi mai nasara yaci gasar". Jin haka yasa dattawan nan duk sukayi shiru. Shi kuwa Ba'ana cikin tarin ƙeta jikinshi har tsuma yakeyi yana maganar zuci. "Uhumm zan kashe Salmanu kuwa kisa mafi muni zaku gane kurenku hegun fulani kunzo garin daba nakuba kun fisu dukiya zan kashe Salmanu irin kisar da ban taɓa yiwa waniba kisan da zaisa har abadan babu wanda zai sake cewa yana son Shatu". A zahiri kuwa, godiya yayi musu kana ya juya ya tafi. Nan dattawan kuma sukaci gaba da tattaunawa yadda Shaɗin zai kasance. Washe gari ranar asabar da sanyin safiya akayi shelar sanar da gasar Shaɗi da za'ayi jibi litinin, da kuma, waɗanda zasuyi gasar da sunan wacce za'ayi dan ita. Gaba ɗaya magarna ta cika Rugar Banin da kewayenta, duk wanda yaji yana firgici, Maman Salmanu kuwa tuni taketa kuka tana cewa ita kam so ake a ƙarar mata da yaranta an kashe mata Hashimu yanzu kuma ace da Salmanu za'ayi gasar Shaɗi da mutun da sun san ba'a taɓa nasara a kansa a., Mutanen sauran rugogin Fulani dake mutunci da Arɗo Yabani kab sai gudumowar magunguna suke kawo na dauri dan a tsuma jikin Salmanu. Sosai kuwa babanshi da yayunshi mata da maza da abokanshi keta tsumashi. Shi kuwa Ba'ana tun ranar ya ɗauki tunƙur ƙasar da yake tsuma bulalinshi, ya kaishi Ƙauyen Bonon, gaban dodon tsafinsu, Anan tukunyar ta kwana bulali tamanin dake cikin tunkuyar nan aketa tsumawa da tsafi. Kana an jikasu da ruwan gishiri sannan an juye kunamai sama da ɗari a ciki, irin baƙaƙen kunamun nanne masu mugun dafi, an sasu ciki sunata harbin bulalin nan suna sa dafinsu a jiki. ranar lahadi da yamma ya amso tukunyar, Har zauren gidansu Shatu yaje yasa aka kira mishi ita bayan ta fitone yace ta leƙa cikin tukunyar, a hankali tace. "Me zan gani a ciki?". Kanshi ya jinjina mata tare da cewa. "Nazo in nuna miki bulalin shaɗi nane, ki gansu da kyau, dan ki cewa wancan koɗeɗden ya shirya shan zabga". Kai ta jujjuya tare da cewa. "Ni ba sai na ganiba". Murmushi yayi tare da buɗe tukunyar kana ya karkatar mata shi gabanta. Da sauri taja da baya tare da cewa. "In...... Littafina na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ko karanta a nitse. By *GARKUWAR FULANI*📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 10 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘 LITTAFIN GARKUWA NA KUƊINE, TURO KATIN MTN NA ƊARI UKU KACAL ta number 09097853276 domin samun cikekken labarin, ko kiyi min transfer ɗin 1k ɗan samun SP GROUP ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276 FREE PAGE Cikin tashin hankali tace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun. Ya Ba'ana me wannan, abu kamar macizai". Da sauri ya meda ya rufe kana ya miƙe cikin yin ƙasa da murya yace. "Kinga ni kada ki tayarmin da hankali kinsan bana son ganinki cikin tashin hankali, in sha Allah nine da nasara ko dai bakya so nane". Da sauri ta girgiza kanta tare dasa tafin hannunta ta rufe bakinta. Ganin haka ya kwashi abinshi ya tafi. Ita kuwa koda ta shiga gida, gefen Inna ta zauna tare da cewa. "Inna ku cewa Bappa ya cewa Arɗo ya hana gasar nan, kada a cutar da Ya Salmanu". Cikin sanyin jikin da duk kwanan haka inna ta zama, a hankali tace. "Uhumm ba komai Shatu in sha Allah duk abinda zai faru da sanin Allah. Yanzu ke yaushe nema zaki koma hutunmu?". Kanta ta gyaɗa a hankali tace. "Rana ita yau zan koma kimga saura mako ɗaya kenan". Ummey ce dake gefe ta ɗanyi ajiyan zuciya gami da cewa. "Alhamdulillah ni in kin komama hankalinmu zaifi konci, domin muddin kinanen sai Ba'ana yayi ta kalato fitina". Shiru sukayi baki ɗayansu, jin an fara kiran sallane tasa, duk kowa yayi al'wala haraman salla. A daren ranar kuwa Ya Salmanu da abokinshi Sale suka zo, wurinta, nan take ce musu ita kam bata son wannan gasar da za'ayi kuma tunda an kafe sai anyi sam ita bazata jeba. Haka dai sukayi ta hira daga bisani suka tafi. Washe gari ranar Monday kuwa, tun da sanyin asuba aketa gangamin. Haɗuwa a filin da za'ayi shaɗi. Mutanen sun cika maƙil dan anfi yawan yin gasar da safe, sabida da rana duk makiyaya sun tafi kiwo manoma sun tafi daji. Tuni matasan Fulani na rugogin nesa da Bani ma sun zo. Bukar kuwa tunda aka fito sallan asuba yaje. Gidan Arɗo Yabani, yaso ace an janye gasar tun randa aka shelanta amman Arɗo yaki, still yanzuma da yazo, bayan sun gaisane ya ɗanyi gyaran murya tare da cewa. "Haƙiƙa naso a janye wannan shaɗi, domin nasan abun bazaiyi daɗin ganiba ace Ba'ana na zane Salmanu ɗan Arɗo ga wannan rugar, amman kaƙi ka saurari zancena, Dan haka ni ba kada wani abu ya faru ku kuskura kuyi kuka dani, duk abinda ɗana yayiwa ɗanku kune kuka saya mishi da yawun bakinku kun rigada kun san bazaku taɓa samun wanda zaifi ƙarfin ɗanaba". Shiru Arɗo Yabani yayi yana nazartan kalaman Bukar, ganin yayi shirune alamun ya gama magarsa cikin sanyi Arɗo Yabani yace. "Duniya da faɗi take, Bukar Mai kanwa a kwana a tashi watan-wata-rana zakaji zaka gani da idanunka za'a samu wanda zaifi ƙarfin ɗan ka, Allah zai bijiro da wanda zai iya jure bulalin ɗan ka". Cikin wani irin yanayi Bukar yace. "Babu mamakin a samu mai iya, jure bulalin, tabbas babu mamaki. Sai daifa abun da bazai taɓa yiwuwa bane har illa masha ALLAH ace an samu wanda zai iya nasara a kanshi babushi babu namijin da zai iya sashi jin zafin bulala bare ya zubda hawayen da zaisa ya rasa Shatu". Wani dogon numfashi Arɗo Yabani yaja tare da cewa. "Uhummmmmm". Daga nan bai kuma cewa komaiba, Shi kuwa Bukar tashi yayi ya kakkaɓe rigarsa ya juya ya tafi yana faɗin. "In dai kunne yaji gangan jiki ya tsira". Da ido Arɗo Yabani ya rakashi, yana maiji a cikin ransa inma ace yanada dama, inama ace zai samo wannan bulalin da Malam Chuɓaɗo ya gaya musu, da tabbas ya samu hanyar da zai cire mugun iri a garinshi. A haka Salmanu da abokinshi, sukazo suka sameshi zaune. Bayan sun gaisane Sule ya ɗan matso kusa da Arɗo a hankali yace. "Allah rene, duk wuri an taru mu ake jira, shi Ba'ana tun da asuba yana can, yanzu Iro yazo yake ce mana gacan fili ya cika, mu kaɗai ake jira, har wasu nata maganganun wai Salmanu ya ji tsoron Ba'ana ya gudu". Murmushin da yafi kuka ciwo Arɗo Bani yayi dafa tsakiyar kan Salmanun yayi kana yace. "Kuje Salmanu, Allah ya bada sa'a Ubangiji yaga niyarmu na son tseretar da wannan yarinyar daga fadawa auren wannan mushurkin, taƙadiri in Shatu matarkace Allah ya baka sa'a in kuwa ba matarka bace, Allah ya baiyono mata wanda zai zame mata GARKUWA daga faɗawa auren wannan azzalumin". Amin Amin sukace baki ɗayansu kana su sukayi gaba. Shi kuwa Arɗo, saida ya jira su Malam Liman Bappa kenan dasu Ahaji Horu, da Ahaji Umaru da Garbati. Koda sukazo ba ɓata lokaci suka nufi, farfajiyar wurin da aka tanada dan shaɗi. Filin ya cika ya batse tako ina mutane zuwa sukeyi arna da musulmai fulani da hausawa da ƙabulun, Ɓachamawa, domin duk yankin nahiyarsu an san babu taƙadiri sama da Ba'ana sabida tunda ake gasar Shaɗi da kuma gasar kokuwa yayin nunan sabon gero ba'a taɓa cin nasara kanshiba, muddin ya shiga gasa tofa shine da nasara. Har ta kai da in dai ya ɗaga hannun to babu mai ɗagawa. To sanadinshi aka hana Shaɗi a Rugar Bani, tsawon shekaru biyu sai gashi yau an dawo dashi. Wannan dalilin ne yasa gaba ɗaya Rugar Bani ta cika maƙil da mutane maza da mata manya da yara, Ga mai busar sarewa kuma yana tsakiyar taro inda akabar filin da za'a gobza yanata rere kirari wa Ba'ana. Isowar su Arɗo yasa aka basu hanya har suka iso gaba inda aka tanada musu, kujerun zama. Na bencin katako. Daga nan manyan Dattawan duk suka Zazzauna. Bisa ƙa'idar gasar Shaɗi wanda ya fara cewa yana son yarinya shi zai fara duka, in wanda yace yana sonta daga baya ya ƙetare bai zubda hawayeba baiyi kukaba, to sai asa kwanaki sai yaje yayi jinya ya worke daga zabgar da yasha, sai ya dawo ya ɗauki fansa, to in ya zana wannan yayi kuka shike nan yayi nasara in kuma wannan ma baiyi kukaba za'a sakeyi har sau uku to nan in babu wanda yayi kuka cikinsu sai yarinya ta zaɓi wanda takeso, don anada yaƙinin duk wanda ta zaɓa, zai iya kare kanshi tunda ƙarfinsu yazo ɗaya. Bayan an gama dai-dai-ta komai, Salmanu ya cire rigarsa kamar yadda ƙa'idar gasar take, ya rage dagashi sai gajeren wondon. Shi ma Ba'ana ya cire rigarshi ya zama dagashi sai gajeren modo, irin masu zuwa har guiwa ɗinnne. To dole a ƙa'ida Ba'ana ne zai fara duka, amman da yake ya shiryawa abun sai yace, shi ya amince a fara dashi, kuma shima yau zai rama Ba sai an ware kwanakin zuwa jinya ba. Nan kuwa take al'kalin gasa Barmuji yace an amince. Daga nan aka zaro bulalin shaɗi na cikin tanɗun masarautar Arɗo Yabani wanda an ƙara tsumasu suma. A hankali Barmuji ya miƙa wa Salmanu, bulalin, kana ya ɗaga hannunshi ya dawo dashi ta bayan Ba'ana. Shi kuwa Ba'ana tsayuwa yayi ƙam tare da ɗan ware sawunshi, Busar sarewar da mai busan yayine alamun a fara, Ai kuwa cikin kuzari da jaruma Salmanu ya ɗan ja da baya, kana ya tattaro ƙarfin shi ga ba daya, ya ɗaga kitsetsten bulalan nan, ya taƙarƙara ya zabgawa Ba'ana shi a tsikar bayanshi, Wanda a take taron matasan dake wurin suka kurma ihu mai karaji, Yayinda shi kuwa Ba'ana, ƙim ya tsaya kamar ba shiba, domin ko idonshi bai ƙebtaba. Sake taƙarƙarewa Salmanun yayi ya kuma zabga mishi bulalar a inda ya kima mishi na farin. Still ihu, taron matasa sukasa, tarin ƙabilar ɓachama kuma dake wurin sai rurrufe idanunsu sukayi da ƙarfi sabida wai bazasu iya jurar ganin ana zabgar jakadan suba. Mai irge kuwa da iya ƙarfinshi yake kware baki yana cewa. "Ɗaya! Biyu! Uku! Huɗu! Biyar! Shida! Bakwai!!!". Haka yaketa irga duk bulalar da aka kaiwa Ba'ana amman wannan tagadirin mutumin ko a jikinshi kamar dutse ake zanawa ba shiba. Ƙa'idar bulalin shaɗi Hamtsine akeyi. Haka Salmanu yake ware iya ƙarfinsa yana zabgar Ba'ana, yana tsaye ƙiƙama. In wannan bulalan ya lauye, sai a bashi wani bulalan. Har akaje arba'in da takwas ko gezau. Gaba ɗaya hankalin mutanen kirki ya gama tashi, domin sun sadakar da nasara ta kubcewa, Salmanu. Shi kuwa Salmanu tattaro sauran ƙarfinshi kab yayi, ya narka mishi bulala ta 49-50". Amman shirunshi. Ihun da kafuran ƙabilar ɓachama suka sakine ya tabbar an gama, nan take suka shigo filin da gudu ruggumeshi suketayi suna shafa bayanshi, da yayi shati-shati. Shi kuwa Salmanu gaban Arɗo yaje ya zauna, nan aka basu ruwa sukasha gaba ɗayansu. Hutun 30 minutes sukayi aka koma fagen fama. Da ƙarfi mai busan sarewa ya busa alamun a fara, wani irin kafurin murmushi Ba'ana yayi tare da gyara riƙon da yayiwa bulalar tashi. Cikin tsananin mugunta ya ɗan koma da baya, kana ya ɗago bubalar da masifan karfi ya zabgawa Salmanu ita a tsakiyar fatan bayanshi. Wani irin gan tsarewa Salmanu yayi, sabida wani irin masifeffen azaba mai girgiza zuciya da yaki yana ratsa dukkan sasasan jikinshi. Bai gama dawowa daga gigi da azabar bulalar forkoba, yaji ta biyu, Rumtse idanunshi yayi da azaban ƙarfi, gaba ɗaya inda bulalar ya taɓashe, harbin kunama yakeji yana ratsashi. Wani irin numfarfashi yaka lokacin da aka zabga mishi bulala ta goma. Gaba ɗaya hankalin mutane ya tashi domin kowa yaganshi yasan yana jin azaba. Bulala ta ashirin da biyar da akayi mishine ya sashi buɗe idanunshi da suka koma jajazir dan azaban da yakeji. Su kuwa kafuran nan sai ihun farin ciki sukeyi. Shi kuwa Barmuji zagayawa yayi gaban Salmanu wai yaga ko idonshi ya kawo ruwa, babu ruwa kam sai azabar da yakeyi tamkar idanun zasu faɗo ƙasa, ci gaba da irgens yayi. "Ashirin da uku! Ashirin da huɗu!!". Wani irin tsalle Ba'ana ya buga da iya ƙarfinshi ya tsulawa Salmanu bulala ta ashirin da biyar. Wani irin duhune ya rufe ganin Salmanu, saiga wasu zafafan hawayen azaba sun kwaranyo masa, ihu ya kuma zurma jin zafin bulalar ta isa kan mazantakanshi. Gaba ɗaya su Bappa dama matasan kowa rufe ido yayi sabisa dukan da akewa Salmanu dukane na son ɗaukan rai. Aysha kuwa tana gidansu kamar kullum tajiyo ihun Ya Salmanu kamar yadda kullum ihun wanda ake gasar dasu ke shaida mata sun faɗi. Cikin kuka konta bisa cinyar Ummey tare da cewa. "Shike nan Ummey zai kashe ya Salmanu". Tuni itama Ummey da Inna hawayen suke zubdawa. A can gidan Arɗo Yabani kuwa inna laure Maman Salmanu, kuka takeyi tamkar zata shiɗe domin yaranta mata sun zo sun gaya mata halin da yake ciki. A can wurin gasar Shaɗi kuwa, ganin tuƙuru Ba'ana so yake ya kashe Salmanu ne yasa, matasan Fulani sukayi kanshi dan dukanshi yake harda tattakashi kuma tuni ya wuce balali hamsin ɗin ƙa'idar gasar. Koda matasan Fulani suka shiga dan crton ran Salmanu kawai sai ga ƙabilar ɓachamawan nan, sun fara zaro makamai sun rufa duk wani ba fulatani da duka da saran wuƙa. Lokaci ɗaya wurin ya hargitse gaba ɗaya. Aka kaure da faɗa saida. Ganin wurin ya hargitse ne yasa, Gaini yayi saurin kiran hukuma mafi kusa ya sanar musu. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa suka iso. Hakane yasa duk ƙabilun Ɓachamawa suka gudu. Allah ya takaita faɗan baiyi nisa ba, a take ɗaya daga cikin police ɗin wanda yake abokin Salmanu ne ya kwashesu suka tafi asibi. Bayan garin ya lafa, kowa ya dawo haiyacinsa ne. Isa ƙanin Salmanu ya tafi asibiti dan jinyar ɗan uwanshi kuma Alhamdulillah da yake ya samu taimakon gaggawa komai yazo da sauƙi. Shi kuwa Ba'ana daga nan izayarsa ta ƙaru manufarsa shida ƙabilar ɓachamawa shine. Su tarwatsa al'ummar fulanin Rugar Bani baki ɗayansu. Zuwa yanzu kuma ko ƙudane in dai na mijine to bazai sauƙa kan jikin Aysha ba, sabida asirce, asircen da yakeyi da kuma tsoronshi da akeji. Aysha kuwa ko zuwa dubo Salmanu ya hanata domin yace muddin taje a bakin ransa. Yau kwana huɗu da faruwar abun, ya da faruwar abun kuma yau ta kasance jumma'a ne. Kasan cewar jummace yasa gaba ɗaya makiyayan suka taso kiwo da wuri, sabida son samun jam'in sallan jumma'a. Iro ɗaya daga cikin yaran Ahaji Horo, wanda yake yayan Binto da kuma Junaidu. Kusan shine karshen dawowa kiwo. ya taso ya taso tarin dabobbin sa a gaba kenan ya haɗu da gungun matasan Ɓachamawa, har sun wuceshi, sai kuma suka bishi a baya, cikin izaya babban cikinsu yace. "Kai ɗan fullo nan garin ubankane ko garin ubanmu?". Cikin jarumtar jinin fulani yace. "Gari dai da daji namune tunda iyaye da kakannimu sun saya, in kuma kuna maganar tushen nasabane, to Adanawa Yola dama kewayenta duk namune fulani". Cikin mugunta ɗaya daga cikinsu ya kai mishi mari da addan dake hannunshi". Murmushi Isa yayi cikin hausar fulani yace. "Kada ka sake dukana". Kusan a tare suka haɗa bakin wajen cewa. "In mun dakeka sai me?". A kufule yace. "Wallahi sai in rama, yawanku ba shine abin tsoro ba". Ai kafinma ya rufe baki suka haushi da duka, da sauri ya fara kare kanshi tare da kai musu duka,. Kamar da wasa su rai shida sun gaza ji da ɗan lenge-lengen saurayi matashi ɗan Fulani. Ganin kamar zaici galaba a kansune, yasa, ɗaya daga cikinsu ya dawo baya-baya ya zaro wukar dake ƙugunshi, da ƙarfi ya dawo kan Isa, ya luma mishi wuƙan a cikinsa wani irin ƙara isa ya sake, sai dai babu mai jinsa bare ya kawo masa agaji domin. Dai-dai wannan lokacin duk wani musulmin wannan yankin yana masallacin jumma'a, Da wannan damar suka samu suka kashe isa, wanda suka daddatseshi da wuƙa. Daga nan suka kira Ba'ana a waya, nan take ya kaɗa shanayen yace. "Yauwa aikinku yayi kyau, yanzu kuyi maza kuyi gaba da shanayen kasar Cameroon, zaku nufa birnin Yahunde kuna isa bakin boda yarana na kasar zasu amshi shanayen ku kuma sai ku dawo, kafin nan ma komai ya lafa baza'a zargekuba". Haka kuwa sukayi, suka kaɗa kan shanu suka fasa daji, suka nufi hanya, shi kuma ya dawo cikin gari ya wuce ɗakinsa bayan ya bawa uwarsa lbri. Koda aka taso sallan jumma'a, anyi mmkin ganin isa bai dawoba, shiru-shiru dai har akayi sallan la'asar babushi, tofa daga nanne hankali ya ƙara tashi. Cikin kiɗima suka fara shiga daji a duba ko lfy bai dawoba. Ai kuwa nan maza matasan Fulani suka watse cikin daji, Bayan sun gama bulayin nemane babushi babu shanunshi, suna cikin zagayawan ne Sale yayi arba da gawar Isa dake malale cikin jini. Nan suka ɗauki gawa suka koma cikin gari dashin. Wannan rana hankali Fulanin Rugar Bani yayi masifar tashi, gaba ɗaya ma sai ba'amaida hankali kam ɓatan shanunba, Hankali ya tashi, ɗauki ɗai-ɗai da akeyi musu ya fara hautsuna musu tunanin, Gashi kisane da babu wanda za'a iya kamawa, koda aka sanarwa hukar cikin Numan sai suka korasu da case ɗin, sabida a lokacin da suka zo shigar da report babu musulmi a police cikin officers ɗin shiyasa suka korasu da batun. Salmanu wanda shine ɗan bokon da kan iya jagorantan lamarinsu, yana gadon asibiti, bisa ƙarƙashin kulawar abokinshi badon hakaba da tuni Ba'ana ya kasheshi. Koda fulani suka hatsala kamar kullum haka Arɗo Yabani ya tarasu ya taushi zuciyarsu, da kuma shawarar, su kai kukanmu ga sarkin Numan ɗin, tunda ya hanasu samun damar ganin sarkin Nuruddeen Bubayero. Koda sukaje masarautar Numan ɗinma abin da akayi musu a police station, fiye dashi akayi musu. Dole suka dawo suka nade hannun suka kai kukansu ga, Allah, sai dai sun ɗauki mataken kare kai da kai, bisa shawarar daddatawa cewa kada makiyayan ko manoma su yarda su rinƙa rabuwa a daji ya zama suje tare su dawo tare da hakane zasu gane mai ke musu ɗauki ɗai-ɗai ɗin. Yau la'hadi tunda safe, Aysha keta shirin komawa makaranta. Sabida hutunsu ya ƙare. Tafiyan safe takeso tayi shiyasa ta gama shirinta da wuri. gaba ɗaya suna tsakiyar gida Yayunta maza sune zasu rakata bakin hanya. Haka nan taji bata son tafiya ta barsu, tsoro mai yawa ya rufeta Especially in tayi tunani da yadda ake kashe makiyayan. Durƙushe take gaban Bappa yana yi mata masiha mai ratsa jiki da zuciya ya kare nasihar tashi da cewa. "Allah ya miki al'barka Shatu, Allah ya kaiki lfy." cikin sanyin murya tace. "Amin Amin Bappa ngd matuƙa". Sai kuma ta kalli Ya Giɗinta da ya zuba mata ido tamkar bai taɓa ganintaba, cikin sanyin murya yace. "Yanzu shike nan zaki tafi ki barmu, ki tafi can ke ɗaya ki zama baki da kowa naki a kusa". Haka nan kalamanshi ya karyar mata zuciya, sai kuma taji hawaye nason zubo mata. A hankali tace. "Ya Giɗi bazan daɗe ba zanzo". Cikin sanyi Seyo yace. "Allah yasa ki samemu in kinzo ɗin". Da karfi ƙrjinta ya bada wani sauti mai karfi, ta buɗi baki zatayi mgna kenan Ya Lado ya ɗanyi murmushi cikin sanyi yace. "To Shatu Ni zan tafi inje in kunce dabobbin, bazan samu daman rakakiba, Allah ya kaiki lfy, ya ƙaddara saduwarmu kan al'khairi, ki yafe". Kawai sai taji hawaye na zubo mata, cikin dariya ya Gaini yace. "To kunga kun sata kuka, Shatu ko dai bakya son komawane?". Cikin rawan murya tace. "Inaji bana son rabuwa daku". Murmushi inna tayi tare da cewa. "Ai kuwa dole ki rabu damu, domin lokaci yazo". Ummey dai ido ta zuba musu. Shi kuwa Ya Lado da murmushi a fuskarshi ya fita yana ɗaga mata hannu. Bappa ne ya ɗanyi murmushi cikin sanyi jiki yace. "Maza tashi ki tafi, ki gaida Aminiyarki Rafi'a, Seyo Giɗi Gaini ku rakata har bakin titi". Da sauri suka miƙa. Ita kuwa Aysha kamo hannun Junainah tayi wacce tayi kasake tana kallonta cikin sanyi tace. "Ƙanwaliya, sai na dawo". Kai ta gyaɗa mata cikin sanyin da sam ba ɗabi'arta bane a hankali tace. "Addana, bana son ki tafi". Shafa kan Junainah tayi, kana ta faɗa jikin Inna, tana zubda hawaye, sake Inna tayi sannan ta faɗa jikin Ummey, murya can ƙasa Ummey tace. "Tashi ku tafi, Allah ya sadamu da al'khairi, Shatu". Da kuka ta fita, ta barsu jiki a mace. A hankali suke tafiya tafiya, suna hira, kayan lambu da suka cika mata bakko dashi na hannun Giɗi, jarkan nonon kuma na hannun Seyo, ya Gaini kuma, jakar kayantane a hannunshi, da kwaryan kwan zabbi, kamar dai yadda suka saba, suna tafe suna, hira suna gab da bakin hanya. Ba'ana ya isosu aka ci gaba da tafiyar, suna isa motar da zata wuce cikin Yola (Ɓadamaya) na isa, saida suka samata kayanta, kafin, tazo har zata shiga taji Giɗi na riƙe da hannunta juyowa tayi ta kalleshi cikin murmushi yace. "Kinsan abinda zamu iya aikatawa a duniya da abinda bazamu iya aikatawaba". Kai ta gyaɗa mishi alamar eh, murmushi yayi kana yace. "To ki ƙara yarda zamu zamu zama GARKUWA'nki muddin muna raye." Murmushi tayi cikin ɗan jin daɗi tasan akan mgmar auren Ba'ana yake nufi. Ido ta zubawa Ya Seyo shi kuma sai murmushin shi nan yake mata, Ya Gaini kuwa hawayene ya cika masa ido shiyasa ya juya ya bata baya. Cikin sanyi Seyo ya matsota kana a hankali yace. "Ki sanarwa duniya halinda muka ciki in kin samu dama Aysha, ki sanarwa duniya Fulani ba ƴan ta'adda bane ba ƴan bindiga daɗi bane ba kuma ƴan Garkuwa da mutane bane, wasu kesa rigar Fulani ke wanzar da ɓarna da wasu ƙalilan na mugayen daji." Cikin rauni ta zuba mishi ido tana kallon kekyawar fuskarsa, da gyaɗa mishi kai. Ba'ana ne ya ɗan kalleta tare da miƙo mata damin kuɗi yace. "Mata zanyi kewarki, amman ba matsala duk ƙarshen mako zan ke zuwa." Drivern ne ya katse su da cewa ta shigo su tafi, haka yasa ta juya da sauri ta shiga, yaja suka tafi tana ɗaga musu hannu, suma basu tafiba saida sukaga motar ta ɓace musu. Juyawa sukayi suka nufi cikin gari. Shi kuwa Ba'ana da ido ya rakasu a a baiyane yace. "Zanga ta yaya zaku zama GARKUWA'nnata, dan na fahimci duk bakwa son aurena da ita, toko zanyi mgninku." Su kuwa basuma juyo sun kalleshi ba. Ita kuwa Aysha tana komawa ta samu, Rafi'a ta dawo ta gyara musu komai na ɗakinsu, to samun Rafi'a da tayine yasa ta ɗan samu nitsuwa, ranar kam wuni sukayi suna hira, darema haka sukayi ta hirar yaushe gamo. A Rugar Bani ( Rugar kikan) kenan nake nufi. kuwa, su Ya Gaini suna komawa suka tafi kiwo, kamar dai yadda suka saba, sukaje kiwo lfy suka dawo lfy. Washe gari ranar Litinin! Saudia. Sheykh ne konce, bisa wani fitinenne gado yayi lib cikin tattausan blanket, bacci yakeji yasa gaba ɗaya jikinsa yayi lakwas sabida jiya a harami ya kwana ɗawafi, shiyasa yana dawowa ya konta. Yanayin wayarrshi na bada ɗan sassanyan sautin, wani irin ɗan gajeren tsaki yaja, ba tare daya buɗe idanunshiba ya miƙa hannun kan bedside drower'n glass dake kusa dashi, lalubo wayar, yayi tare da ɗan liƙa yatsarsa kan gilashin wayar ya amsa kiran, kana ya ɗauwara wayar bisa kunnenshi a hankali cikin muryar bacci yace. "Assalamu alaikum, Umaymah". Murmushi Umaymah tayi cikin son ɗan yar uwartata tace. "Na'am Jazlaan ya akayi". Cikin murya baccin ya kuma gyara konciya tare da cewa. "Umaymah baki amsa sallamar ba". Da sauri tace. "Afwan Jazlaan, Wa alaikassalam". shiru yayi. ita kuwa murmushi tayi tare da cewa. "Naji kamar bacci kakeyi ko?". Murya can ƙasa yace. "Uhummmm". Da sauri tace. "To yi baccin sai ka tashi muyi mgna nasan a harami ka kwana". Da sauri yace. "No Umaymah gaya min menene?". Dan shi a zatonshi ko akan Ya Jafar ɗinshi ne. Ita kuwa Umaymah cikin hikima tace. "Uhum dama batun Jazrah ne". Fuska ya kwaɓe kamar yana gabanta cikin nuna ko in kula yace. "Menene kuma hakan? Umaymah". Kai ta jinjina dan tasan a rina, cikin tsare gida tace. "Ina nufin Jazrah ƴar Ƴayan Sitti Uncle ɗinmu Aliyu". Numfashin ya ɗan fidda cikin ƙosawa da zancen yace. "Ni ban santaba. Umaymah zanyi bacci, kaina ciwo. Kin yarda in katse kiran Please Umaymah kada kicemin a a dan Allah". Murmushi tayi wato duk yadda mutun ke zaton Sheykh ya wuce tunanin mai tunani a hankali tace. "Kashe, Allah ya muku al'barka". Da sauri yace Amin Amin kana ya katse kiran, hannu yasa ya cusa wayan ƙasan pillow'nshi. Kana ya gyara konciyarshi afili yace. "Ni ina zan kai mace? Toma me zanyi da mace a rayuwata. Zakuna damuna da wata Jazrah mai koɗeɗden fuska". Daga nan ya lumshe ido yaci gaba da baccinsa. Haroo dake bakin kofar shigowane yayi dariya kana yace. "Uhum zaka san me zakayi da ita ai Ustadz ai ba'a gane maci tuwo sai miya ta ƙare, dama kirarinku ustazu ƙalilan iya shege kasiran, wai me zanyi da mace, hmmm miskilanciba ba". Daga nan ya koma da baya dan dama Sitti ce ta aikoshi ya kira mata Sheykh ɗin, akan yazo yaci abinci kafin yayi baccin wai. Koda ya koma sanarwa Sitti cewa yama rigada yayi baccin sai suka zauna na nan sukaci gaba da hiransu... A nan gida Nigeria kuwa cikin Rugar Kikan. Tunda safe duk makiyayan garin suka tafi kiwonsu. Sosai suka shiga irin tsakiyar tsaunuka, wasu na nan wasu na can suna dai hango juna da, sabida abu na kiwo bazai yiwu su zauna wuri ɗaya ba, dama sai in zasu komane suke haɗuwa baki ɗayansu. Misalin karfe uku da rabi na yamma, duk kowa ya fara ɗan zagawa cikin kwazozzobon dake gefensu da. Yin ɗaharan yin al'wala. Ya Gaini ne ya fara gangarawa cikin korin babu sanda bare wuƙa a jikinshi. Ko buta babu a hannunshi Don akwai ruwa a cikin kwarin dashi suke al'wala, a hankali ya tsuguna yayi buƙatarsa kana. Ya dawo wurinda suke al'wala ya tsugana yayi al'wala. A hankali ya yunƙura ya tashi. Ɗago kanshi da zaiyi yayi dai-dai da.....! By *GARKUWAR FULANI* Wasa farin girki, yanzu ake nutsawa ciki. Da yawa naga basu fahimci banbancin. Garinsu Parvina da kuma Rugar Bani ba. To ku saurara, Rugar Arɗo Babayo, itace Rugarsu Parvina, kuma a can ƙasar Cameroon yanki Yahunde Rugar take. Sai kuma ɗaya rugar wacce a nan ƙasarmu Nigeria take yankin Adamawa state, wani dalili yasa na sakaya sunayen garuruwa da ƙasar tamu da masarautun. Amman nasan duk mazauna Nigeria Adamawa zasu gane Rugar Kikan nake nufi nasa Rugar Bani Numan nake nufi nasa Shikan, dama duk sauran jihohinmu na sakaya sunayensu sabida wani dalili Amman nasan duk munsan inda tushen ƙabilar ɓachama suke. Amman ba mmki in medasu yadda zakufi ganewa. Ba wata ƙasa bace Kautal Nigeria nake nufi🤝🏻🥰 By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 11 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘 Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta layin nan 09097853276 domin KARANTASHI daki-daki, ko kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, kana sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta WhatsApp number ta 09097853276. Special Group ne 1k cikin mako biyu za'a gaba wani sashi na littafin. Ido ya zubawa mutanen da yayi arba dasu, dai-dai lokacin daya. Ɗago kanshi, yayi arba, da wasu mutanen, da shigar hukuma (police), da sauri ya miƙe tsaye yana ware hannun rigarshi da ya naɗe dan yin al'wala, tare da cewa. "Lfy? Ku su wayene?." Basu kulashiba, sukayi kanshi gadan-gadan, cikin dakiya yace. "Me hakan?". Still no respond. Sai matsoshi da suƙa ƙarayi, cikin dakiya da jarumtar jinin fulani ya gyara tsayuwarshi, yana binsu da ido ganin zagayashi da suka farayi, da ido yake binsu a zatonsa faɗane shiyasa bai guduba, domin, duk da yawansu bai Karaye ba, dan zuciyar gskya ce dashi kana jinin fulani ke yawo a jikinshi. Su kuwa mutanen, na gabanshi ne ya ɗan fesa mishi wani abu mai kamar turare a fuskarshi. Da sauri yasa hannunshin wai zai kare fuskarshi, cikin dakiya da haɗe fuska ya buɗe baki yace. "Me kuka fesa meeeen." Sai kuma kawai yayi lu ya lumshe idonshi ya faɗi nan kamar gawa. Da sauri biyu daga cikinsu suka ɗaukeshi tsallaka korin sukayi sukaje suka ajiyesu cikin motorsu dake can bayan lampon dake bayan korin. So biyun kuma komawa mafakarsu sukayi. A can wurin kiwon kuwa, Seyo ne ya ɗan kalli Giɗi tare da cewa, "Bari in shiga muyi al'walan,in mun fito, sai kai da ya Lado ku shiga mu kuma mu tsare dabobbin namu gudun kada su shiga gonakin manoma." Kai Giɗi ya gyaɗa mishi daga, nan ya gangara ya shiga cikin korin. Yadda sukayi Ya Gaini haka sukayi mishi, shima. Giɗi da Ya Lado sunata jira, shiru-shiru ba motsinsu, ganin hakane yasa, Giɗi ya fara kiransu. "Ya Seyo!, ku fito mana, Lokacin sallafa na tafiya". Lado ne ya kalleshi cikin sanyi jiki yace. "Shiga ka kirawosu". To yace kana ya juya ya nufi cikin korin, har yaje inda zai gangara ya shiga sai kuma ya juyo ya kalli Ya Lado cikin sanyi yace. "Ya Lado ka kula da dabobbin nan fa kada su cutar da manoma kaga kai ɗaya ka rage mai kula dasu, kada ka bari suyi nesa dakai". Lumshe ido Ya Lado yayi cikin wata sassanyan murya mai cike da rauni yace. "Zaku dawo ai, kuɗin sai ku kula dasu da kyau in yaso ni sai in tafi". Kai ya gyaɗa tare da yiwa yayan nashi murmushi ya shige cikin korin. Yana shiga ya fara dube-dube babusu babu dalilinsu, cikin ciyawa da kozozzaban ya fara leƙawa yana cewa. "Ya Gaini! Ya Seyo!! Ya Gaini!!!". Jin shiru babu amsarsu bare motsinsune ya sashi ci gaba da waige-waige tare da cewa. "Ya Gaini ina kukene? Yaya Seyo, ina kuke ban gankuba, kuyi mgna mana". Cikin fargaba yake lelleƙa wuraren, da yake ganin mutun zai iya fakewa a wurin. Yana sunkuyowa cikin wani sunkurun kawai sai ya koma luuu ya faɗa ta baya sabida abinda suka fesa mishin yasashi bacci. Daga nan suka ɗaukeshi sukaje suka sashi cikin motar da suka saka sauran yayunshi. Da suke konce kamar gawarwaki. Tsaye suke jikin motar, yayinda biyu daga ciki dakeda uniform ɗin police officers, kuma suna cikin motar da itama ta police ɗinne. Ɗaya daga cikin mutun huɗu dake gaban motarne, yasa hannu ya rufe ƙofar, sannn ɗaya kuma ya kira waya, cikin yaren Ɓachamanci yace. "Mun sace mutun biyar, uku yaran gidan Malam Liman ne, biyu daga ciki yaran gidan Ahaji Horo ne". Ɗan jim yayi alamun karɓar umarni. Tsawon daƙiƙu biyar sannan ya ƙatse kiran kana ya juyo ya kalli, sauran tare da cewa. "Yace ku, ku tafi dasu a cikin motar, ku wuce dasu,inda kuka shirya, mu kuma yace mu ɗan tsaya nan, yanzu zaiyiwa shanun Rugar Malam Liman kiranye da dogon fito. To in shanun suka nufi inda yake ba mamaki wasu su biyo shanun daga cikin makiyayan, to yace idan sun biyosu mu kashesu!". Kusan a tare suka sara mishi tare da busa sigarin dake hannunsu. Nan mutanen cikin motar sukaja, suka tafi. Su kuma saura mutun huɗun, komawa mafakarsu sukayi. Can cikin tsunƙurun dajin kuwa. Ba'ana ne zaune cikin taron matasan ƙabilar ɓachama da a ƙalla sun kai goma, cikin kausasa murya da bada umarni yace. "Zanyi fito ɗaya zuwa uku, cikin daƙiƙu 10 shanayen Malam Liman da Alhaji Haro da wasu. Zasu baiyana, a nan. Suna zuwa ku jasu ku fuskanci gabas, ta ƙasar Jihar Gombe zaku ratsa, kana ku nufi ƙasar chadi daga can." Shiru ya ɗanyi tare da zuba musu idanu, wani irin azzalumi murmushi yayi cikin barbarci ya kalli biyu dake kusa dashi wanda ƴan ƙanwar Bukar ne su barebari ne, cikin izaya yace. "Kada ku kauda ido akan ko wacce gonar makiyayin da zaku wuce ta gabanshi, ku shiga gonakin manoma, kuyi kiwo a ciki. Idan manoman suna cikin gonakin in sun muku mgna ku kashesu, sannan ku gudu da dabbobin yankin wurin". Cikin barbarci ɗaya daga cikin su yace. "Ba'ana, tsayuwa kiwon bazai ja mana tsaikoba, har cekiyar ya riskemu ba tare da munyi nisa ba". Murmushi yayi mai cike da fajirci sumar kanshi ya shafa tare da cewa. "Ba'akana Ku kiwaci duk gonakin manoma, hakanne zai jawo faɗa tsakanin MAKIYAYA da manoman, daga haka saiku gudu, kaga mun jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, domin su mutanen duniya sun ɗauka duk wanda suka gani da dabobbi yana kiwo, BAFULATANI NE, sam mutane sun kasa ganewa cewa ba sai Fulani kaɗai ke kiwoba, kaga mun tada faɗa mun kwashi dabobbinsu, mun kashesu mun gudu, kuma in sunje kai korafinsu ga hukuma a kamasu ko a korasu ko azagesu, ace suke haddasa faɗa tsakaninsu da manoma, sun zama ƴan ta'adda a idon duniya. Mun kwashe dukiyoyinsu". Dariya sukayi baki ɗayansu, kana suka sara mishi, juyawa yayi, ya fuskanci gabas kana ya durƙusa, ya zuba guiwowinsa duka biyu a ƙasa, yatsarsa manuniya ta hannun hagu ya kafa a ƙasa, kana yatsarsa ta hannun dama kuma, ya toshe kunnenshi na dama, da ƙarfi ya rufe idanunshi kana, ya tsuke bakinsa ya rinƙa zuro iskar wata zazzafar fito mai bala'in sauti. Su kuwa sauran duk rufe ido sukayi dan jin fiton sukeyi tamkar zai fasa musu dodon kunne. Shi kuwa Ya Lado yana cikin kiwonshi kawai yaga gaba ɗaya, shanun sun juya sun fuskanci gabas, kana sun ɗaɗɗaga kunnuwansu sama, daga baya kuwa sunata karkaɗa binɗinsu. Cikin mamaki yake ratso tsakiyarsu. Dan in makiyayi yaga dabbobi suna haka yasan akwai abun da suka gani, ko mutun ko iska, ko maciji ko dai wani abu na daban to sukanyi wannan alamar dan sanar da makiyayinsu. So ganin hakane yasa Lado ya ƙara kutso kai cikinsu. Su kuwa dabbobin gaba ɗaya fiton da Ba'ana yake hurawane ya cika musu kunne, ai fa a take suka nausa a guje suka fuskanci gabas, da wani irin masifeffen gudu. Shanu da dawakai na gaba tumaki da awaki na baya hatta belbelun dake cikinsu, suna kiwo binsu sukayi. Cikin ƙarfi Ya Lado yayi wani irin ihun wanda dashi suke kiran dabbobinsu, amman ina basu juyoba. Da gudu ya fara binsu kana yana ihun neman taimako a wurin sauran makiyayan su. Amman da yake gudun dabba dana mutun ba ɗaya ba, Sun mishi nisa mai tarin yawa, hakanan shi kuma yayiwa sauran makiyayan dake biyoshi a guje su kawomishi agaji ya musu nisa. A haka suka rinƙa gudu, waɗannan mutun huɗun dake laɓene suka fito suka, tareshi ba zato ba tsammani kawai yaji an burma mishi wuƙa juyowan da zaiyi kuma yaji an kuma burma mishi wuƙaƙe a tako ina na jikinsa. A nan take ya faɗi babu rai. Su kuwa nan sukabi shanun da gudu. Koda sauran makiyayan suka iso inda gawar Ya Lado take. Hankalinsu yayi masifar tashi. Tabbas sun san babu masuyi musu wannan aikin sai ɓachama. Ko hanƙo kurar dabbobin basayi. Hankalinsu yayi mummunan tashi ganin gawar Lado, ga kuma tashin hankali da firgici rashin ganin su Gaini da Giɗi da Seyo Manunu da Sale. Junaidu ne yayi sauri ya kira mahaifinsu Ahaji Horo a waya ya sanar mishi halin da ake ciki. Wannan mummunan labari yayi matukar firgita al'ummar Rugar Bani hankalin kowa ya tashi. Hankali Bappa kuwa in yayi dubu to ya tashi, kuka cur-cur yakeyi da idanunshi. Junainah kam kuka da ihu harda burbuwa takeyi tana cewa. "Wayyo Ya Lado, Bappa ku nemo min Ya Gaini na da ya Seyo". Sai ta kuma faɗa jikin Ummey daketa kuka tamkar ranta zai fita, cikin kukan take cewa. "Ummey kicewa Bappa suje su nemo min Ya Giɗi na, kada su bari a kasheshi kamar yadda aka kashe Ya Hashimu da Ya Isa, da kuma Yaya Lado". Babu mai iya bata amsa a cikin wannan gida. Duk da tarin maƙota da suka cika gidan. suna zagaye da Inna wacce, take sume tunda taji yaranta Rai uku babusu babu dalilinsu su ko gawarsu ba'a ganiba ga kuma mutuwar Lado wanda shine yasata, sumewa. Faɗin tashin hankali da mutanen Rugar Kikan ke ciki bazai taɓa misaltuwa ba. Saidai ƙunane wanda duk mai imani zai iya ƙiyastashi a ranshi. A cikin garin kuwa tuni Arɗo Yabani yasa anyi shela anyi taron gaggawa, kowa ya shirya za'a shiga daji neman su Gaini, ko Allah zaisa a samosu. Haka matasa kusufa-kusufa suka rinƙa kusa kai cikin daji suna ratsa tsaununka da kozozzabai. Bappa kuwa da Arɗo Yabani da Ahaji Haro, da Ahaji Umaru ne da sauran dattawan rugarsu dana kewaye, gawar Lado suka ɗauko suka dawo gida da ita da sauran shanayensu gaba ɗaya matasa kuma suka bazama nemansu Gaini. Su kuwa sauran matasa majiya karfi daji suka rinƙa ratsawa. Amman babu koda kurar dabbobin nan, bare alamun su Gaini illa iyaka dai takalmansu da suka tsinto. A Rugar Bani kuwa, hankali na matukar tashe, Bappa ya tasa gawar Lado a gaba wacce sunyi mata wonka sun kimtsata cikin sutura kamar yadda shariya ta tanadar. Kuka mai tsananin cin raine ya kwabcewa Bappa, yana ruggume da gawar. Inna ma da yanzu ta farfaɗo da kukan ta farfaɗo, kuka takeyi tamkar ranta zai bar gangan jikinta. Hakama sauran matan maƙota. Hiden da Binto ma kuka sukeyi sosai a gidajensu sabida ɓacewar samarin su. Dattawan ne sukayi ta bawa Bappa haƙuri da tausan zuciyarshi. Ganin dare yayine yasa akace dole a bar gawar tayi kwanan keso. Su Sule, Iro, Ado, Junaidu, Madu, Ari, Sani, Ibi, ja'eh, Ori, Binbi, dama sauran samari majiya karfi kuma kab sun cikin daji. Haka suka kwana a can. Suna tafiya suna nema, kafin gari ya waye, wasu sun isa har jihar taraba, wasu Gombe, wasu har bauchi, wasu har cikin iware da mutun biyu na taraba, Wasu sun nausa da nisa, sabida in dai tafiyace bata taɓa bawa bafulatani tsoroba domin anyi ittifaƙin duk ƙabilun duniya babu ƙabilar da takai ƙabilar fulani saurin tafiya da jumurin doguwar tafiyar ƙafaba, bayan laraban da. Washe gari Litinin. ɗin, sauran dattawan garin suka sallaci Ya Lado, kana suka zauna amsar gaisuwa. Suna kuma jin labarin inda yaransuke. Ganin sunata wahalar tafiya ba lbrine yasa. Bappa yace su dowo. Domin wanna abu addu'ace mgninshi. Sannan kuma wannan karon bazasu saurari masarautar Numan ba , gangami zasuyi su kai kukansu, ga masarautar Joɗa, wanda a cikinta ne GARKUWAN FULANIN ƙasar Nigeria gaba ɗaya yake. Da fari Arɗo Yabani bai gamsu da hakanba saida Bappa yayi mishi bayanin. Dolefa suna da buƙatar hukama mai tsarki ta shiga tsakaninsu da ƙabilun Ɓachamawa nan, kana dole mgnar ta isa ga babbar masarautarsu, wacce za'a miƙa mgnar ga Ƙungiyar *TABITAL POOLAKU, DA KUMA ƘUNGIYAR.* *MIYETTI ALLAHA* Wannan dalilin ne yasa Ardo Yabani ya umarci gaba ɗaya matasan da suka bazama neman su Gaini su juyo su dawo gida. Haka kuwa akayi kafin yamma sai gasu duk sun daddawo domin. Wasu da yawa motoci suka shigo. Bayan sallan ishane suka zauna zaman mitin domin sun gama shirya komai gobe dai kai tsaye masarautar Joɗa zasu wuce. Bayan sun gama tattauna yadda abun yake suka tsaida zance kan cewa dattawansune zasuje. Daga nan Duk suka tashi taron kowa ya koma gidanshi da tarin al'hini a zuƙatansu. A can cikin birnin Ɓadamaya kuwa cikin makarantar su Aysha. Zaune take bisa salla hannunta riƙe da carbi tana ja. Kana hannunta ɗaya kuma rike da wayarta, wacce taketa kiran yayunta kab baya shiga tun jiya da yamma. Cikin kula Rafi'a ta kalleta a hankali tace. "Aysha ba komaifa, kinsan garin naku kunada matsalar Network, wasu lokutan kuma kinsan basu da cajine". Kanta ta jingina da jikin gini, murya can ƙasa tace. "Gaba ɗaya fa, woyoyinsu basa, shiga, na maƙotanmu kuma ko sun shiga basa ɗagawa, Rafi'a hankalina ya tashi." Da sauri Rafi'a tace. "No kada ki damu tunda kikaga basa ɗagawa alamun kenan woyoyinsu na wurin cajine ko?". Idonta ta lumshe tare da cewa. "Zuciyata na yawan sinkewa Rafi'a, fargaba nakeji". Cikin sanyi Rafi'a tace. "Yauwa to ki kira Ba'ana mana". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Eh hakane fa". Ta karishe mgnar tana dannawa wayarshi kira. Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga, Da sauri tace mishi. "Ina wuni ya Ba'ana". Ba'ana dake zaune tsakiyar ƙabilun Ɓachamawa suna mitin yadda zasu farma garin Rugar Bani da yaƙin sunƙuru gobe, murmushi yayi cikin sonta yace. "Lfy lau Mata, ya karatu?". Alhamdulillah tace tare da cewa. "Ya Ba'ana ya garinmu ya lbrin gidanmu duk suna lfy?". Murmushi yayi tare da cewa. "Duk suna lfy garinmu duk anata kewarki ɗazuma na wuce ya Ladonkin a kwance yanata shan baccinsa babu ruwanshi da damuwar duniya". sam bata kawo komai a rantaba kan mgnarshi ta ƙarshe, saima sanyi da ta ɗanji daya bata tabbacin, suna lfy, sabida iya tsawon zamanta da Ba'ana bai taɓa yi mata ƙaryaba, koda zaiyiwa duk mutanen duniya ƙarya to ita baya mata ƙarya, kuma duk zafin gskyar mugun abunda yakeyi zai gaya mata. Abu biyu ya ɓoye mata a rayuwarshi sata da kisan da yakeyi, sai dai yana gaya mata in dai a kantane zai iya kashe kowa ma. So cikin sanyi tace. "To yasu Ya Gaini kuma". Murmushin mugunta yayi tare da cewa. "Shima na wuceshi wurin Binto sunata hirarsu har tanata raira masa waƙoƙin soyayya". Murmushi ta ɗanyi tare da cewa. "To ka gaida min su bari in ɗanyi wonka". Murmushi yayi tare da cewa. "To Mata kiyi wonkanki anjima zan kiraki muyi hira". To tace mishi kana ta katse kira, tare da cewa Rafi'a. "Alhamdulillah duk lfyarsu lau ashe". Itama Rafi'a murmushi tayi kana sukaci gaba da hirarsu sai dai still fa tsoro da fargaba da bugawar da zuciyar Aysha keyi bai bariba, ganin hakane yasa Rafi'a, kallonta kasancewar Rafi'a ƙwararriyar mai koyar da girgirkene, a zahiri cikin makarantar tasu, da kuma social media. Cikin kula da son samawa aminiyar tata nitsuwa tace. "Yauwa GARKUWA, zomu shiga kitchin, muyi ɗan alalan kwai, naga kin kawo mana koyaye da yawa." Murmushi Aysha tayi wace, akefi kiranta da ƙarshen sunanta. hannun ta miƙa Rafi'a, cikin sanyi tace. "Help me my friend, jikina yayi sanyi da yawa, ji nake kamar bazan iya tashiba". haka nan itama Rafi'a jikinta ya fara sanyi, sai dai sanin in ta baiyana kasalarta tashin hankali Aysha zaifi tsananta ne yasa ta dake, cikin sauri ta kamo hannunta ta jata-ta miƙa kana suka shiga kitchin ɗin. Nan suka fara aikin sunayi tana ɗan janta da hira. a haka dai har suka gama, kana, ta shiga wonka. Shi kuwa Ba'ana maida woyarshi yayi cikin al'jihunsa, kana ya kalli Sarkin mayaƙan ƙabilar ɓachama da yake ce mishi. "Shege Ba'ana wato, yana bacci cikin kabarinsa babu ruwansa da damuwar duniya". Dariyar mugunta sukayi dukansu, wanda yake gefenshi ne ya kece da wata dariyar tare da cewa. "Wai ita kuma Binto kukan natane waƙen SOYAYYA ko?". Kanshi ya gyaɗa musu cikin muguwar fuskarshi. Wannan matashin ɗaya fara sokawa Ya Lado wuƙane lokacin da suka kasheshi. yace. "Ita kuma da yake sokuwace har ta yarda k...". Wani irin tashi sukayi gaba ɗayansu sabida wani irin shaƙa da naushi da Ba'ana ya kai mishi, wanda a take ya fara kakarin mutuwa. cikin zafin rai ya hankaɗa tarin mutanen dake son cotan yaron daya shaƙe ɗin amman ina sun kasa, wata zabgegiyar wuƙa ya lumtsumamishi a ciki wanda yasa sauran duk suka watse tura gawarshi yayi gaban su cikin ɗaga murya yace. "Ina kashe wanda ya yabi Shatuma yace yana son Shatuma bare wanda ya zageta, duk wanda baya son ransa ya aibata min Shatu a gabana ya gani". Cit kake jinsu sabida masifar tsoronshi sukeji. Dan ya fisu taƙadiranci dan Ba'ana mugun babarbarene mai baƙar zuciya. Haka dai aka tashi wannan taron da yake dama sun gama tattauna yadda zasuyi farmakin. Washe gari ranar wata Tuesday 21 November 2017 itace ranar da har abada al'ummar Rugar Bani bazasu mance da itaba a tarihin rayuwarsu, itace ranar da duk motsin da numfarfashi Shatu zatayi sai ta tunashi ranace data girgiza, zukatan al'ummar musulmai, ranace da tasa duk wani bafulatani makiyayi jin ƙuna da tafasar zuciya. Ranace da tada hankalin al'ummar ƙasarmu nan dama maƙotanmu. Tunda safiyar ranar, dattawan garin suka gama shirinsu cikin shigarsu ta al'farma, Malam Liman (Bappa) Arɗo bani Jauronsu, Ahaji Horo da Ahaji Umaru, kana Malam Yero, da kuma Alhaji Sa'idu. su rai takwas dai suka shirya cikin kamala da mutunci. Junaidu ne yake cikin Shikan ya samo musu mota kirar siyana wacce suka ɗauki shatarta, domin zai kaisu har cikin fadar masarautar Joɗa kuma zai jirasu. Su dawo tare. Nan suka shiga Mota gaba ɗayansu, suka tafi. Kai tsaye har bakin masarautar suka tsaya dan an hanasu shiga, sai da ɗaya daga cikin hadiman dake tsaron ƙofar, yaga duk manyan daddatawa ne yasa yaje ya samesu bayan sun gaisane sukayi mishi bayanin abinda ke tafe dasu. Jin abin babbane yasa yaje yayiwa sarkin ƙofa bayanin. Nan shima yaje suka gaisa suka ƙara jaddada mishi, zancen abinda ke tafe dasu, sannan sukayi musu izini suka shigo cikin asalin farfajiyar mashigar masarautar. Kan kujerun dake jere a wurin suka nuna musu su zauna. Bayan sun zaunane sarkin kofa yaje, wurin sarkin fada ya sanar mishi, to nan sarkin fada ke cewa. "To ai babu abinda zamu iya musu, tunda shi GARKUWAN FULANI, baya ƙasar waye zai saurari kukansu, suje sai ya dawo su sake zuwa". Cikin rauni sarkin ƙofa yace. "Ranka ya daɗe sarkin fada, da dai an nema musu izinin ganin mai martaba, domin bazaiji daɗi ba in yaji sunzo kuma an medasu". Cikin isa da izaya sarkin fada yace. "A kul sarkin ƙofa ka tsaya iya matsayinka, kaje kace suyi maza su bar nan domin GARKUWANSU baya nan". Cikin sanyi da mutuwar jiki sarkin ƙofa ya juya ya fita, koda yaje ya sanar musu, abinda sarkin fada ya faɗa hankalinsu yayi masifar tashi. Cikin tashin hankali Arɗo Yabani yace. "Shikenan danmu fulanine makiyaya mazauna daji, sai ya zama matsalarmu ba abar dubawa bace, wa al'ummar birane, duk inda muka kai kukanmu sai a koramu". Cikin sanyi sarkin ƙofa yace. "Kuyi haƙuri ba korarku akayiba, in sha Allah za'abi kadunku, wlh shi kanshi mai martaba in zaiji abinda sarkin fada yayi to zai barranta dashi, kuma haka nan shima GARKUWAN FULANI in da zaiji abinda sarkin fada yayi wallahi zai haɗu da fushinsa mai tsauri, domin shi zuciyar Sheykh zuciyace mai cike da imani da tausayi". Cikin rauni Alhaji Haron yace. "Ana binmu ana kashemu, ana sace yaranmu ana kora dabbobinmu. Munje Police station an koramu, da mukaƙi tafiya suka watsa mata tiyagas, muje masarautar Numan akaci mana zarafi, sannan yanzu mun gudo gareku da yaƙinin zakubi kadunmu sannan kuma zaku koramu, so kuke mu ɗauki makami domin ramuwa ne?". Da sauri suka juyo gaba ɗayansu jin muryar Jamil da yanzu ya iso wurin da hadimanshi, cikin sanyi yace. "A a Baba kada ku ɗauki makami domin ramuwa zuwanku nan shine babban abinda ya dace". Cikin jin daɗi suke kallonsa, murmushi sarkin ƙofa da sauran hadiman sukayi dan sun san yanzu dai sarkin fada bai isa ya hanasu ganin Maimartaba. Domin yanzu bai fito fada bama tukun so zasu ganshi a kebantaccen wuri na musamman. Cikin kulawa da sakin fuska Jamil yace. "Baba ku biyoni". Cikin jin daɗi sukace mishi to, kana suka bishi a baya. Ta gaban shashin Sarkin fada suka shiga, kai tsaye har cikin fada ya shiga dasu, shida kanshi yasa hadimai suka kawo musu ruwa. Sannan a nitse yace. "Baba ku zauna a nan zanje in sanarwa mai martaba, duk sanda ya fito daku zai fara, tattaunawa In da masu buƙatan zagawa gacan wancan kusurwar in kumbi cikinta zata sadaku da bayi". Cikin jin daɗi sukace. "Mun gode yaro Allah yayi maka al'barka". Amin Amin yace kana ya sallamesu ya fita. su kuma sukaci gaba da zaman jiran fitowan sarki. A can kasa mai tsarki kuma, Sheykh ne zaune a gaban Sitti, kana Haroon da Jannart na gefenshi Sheykh Aliyu Abdulkareem, kuma da Sheykh Jabeer Aliyu da wasu manyan malamai na zuriyar tasu duk suna zaune a cikin falon. Jazrah kuma na gabanshi da wani tray mai masifar kyau da tsada. Madara da zuma take zuba mishi a cikin wasu ƴan kananun kofuna masu masifar kyau da ɗaukan hankali. Wannan ya kasance al'adarsuce ta baiyana nuna yarda da soyayya ko akasinshi, indan ana son a haɗa yara aure, to za'a tattauna tsakanin manya, bayan sun gama dai-dai-ta magana tsakaninsu kamar yadda yanzu su Mai alfarma Jalaluddin da Sarki Nuruddeen, da kuma su Sheykh Jabeer Aliyu da babban babansu Sheykh Aliyu Abdulkareem da kuma Sitti suka gama haɗa zancen auren Jazrah da Sheykh Jabeer, to yanzu ta zuba mishi madara da zuma a gaban kowa, ta ajiye mishi, idan ya ɗauki kofin madara to yana nufin yana sonta ya kuma amince da ita da aurenta. In kuma ya ɗauki kofin zuma, to yana nufin ya tsaneta baya kuma sonta bazai kuma auretaba bare ya zauna da ita. Za'ayi komai a gaban manya ne, don suga zahiri kuma a tsarin ko ɗan uwanka zai iya yi maka zaɓin da kuma in dai am zaɓa maka sai ka aura. Shiru sukayi baki ɗayansu falon, kowa da tunanin da yakeyi. Sheykh Jabeer dake zaune a tsakiyarsu cikin shiga ta al'farma sai sheƙi al'kyabbar sa keyi, ga tattausan hirami a kanshi, ido ya lumshe daya gane manufarsu. "Domin shi basu gaya mishi cewa, zasuyi wannan abun bane daya sani wallahi da yasan duk yadda zaiyi ya gudu, ya tafi harami, har sai sun gaji sun watse. A hankali ya kalli Sitti dake kallonshi cikin rauni da alamun. "Dan Allah kada kace, a a yar ɗan uwanane, kada ka bamu kunya nida kakanninka maza yar uwarkace kasan tarbiyarta". Kauda idonshi yayi daga kallon Sitti, wani irin kallo yayiwa Haroon daketa yi mishi, murmushin muguntan yau dai an titseka baka da hanyar tsira. Cikin ranshi yake mgnar zuciya. "Ta yaya zan amince ince zan aureta? Dame zan zauna da ita?". Sai kuma ya ɗan fidda nannauyan numfashi. "To idan ban amince da aurentaba me zamcewa, waɗanannan bayin Allah'n da sukayi min dukkan gatan duniya, na zauna a gidansu tsawon shekaru masu yawa nayi karatuna har na gama, sukemin komai na rayuwa, suna nuna min soyayyar da mahaifinama baya nuna min, da wanne idon zan kallesu inna ɗauki zuma alamar na tsani yarsu?". A hankali ya buɗe idonsa, jin muryar. Sheykh Aliyu Abdulkareem kakan Mamanshi kenan, baban kakarshi Sitti dottijon daya yake sonshi tamkar ranshi yana cewa. "Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa, kayi zaɓin da ranka keso, bamu da nufin yi maka dole, sai dai ina da burin aurar maka jikata Jazrah ɗiyar mai sunanka. Ina so da fatan ganin nasabarka ta cika, cikar nasabarka kuwa, shene aure." Wani irin sassanyan numfashi ya shaƙa a hankali, wasu irin zafafan tunanuka ne ke zirya a zuciyarshi". Cikin harshen hausar katsinawa, Haroon yayi mgna can ƙasa yadda ko Sitti bazata jisuba. "Sheykh kafa, shanyamu, nifa zan ɗaukar maka Madara". Ido ya lumshe tare da ɗan jingina da jikin kujerar da yake zaune, wanda yake kusa da Sheykh Abdulkareem. Sitti ce ta ɗan kalli Haroon tare da mishi alamun ya taɓo Sheykh. cikin harshen larabci Haroon ya kalli kakar tasu, tare da cewa. "Sitti ai nasan zaɓinsa, bari ki gani in nuna miki". Ya ƙarishe mgnar yana kai hannunshi kan kofunan. da sauri Sheykh Jabeer ya buɗe kekkyawar ƙwayar idanunshi da wasu ke kiransu da zaiba, wato kamar idon mage, idon ya ɗan zaro ganin Haroon yasa hannunshi kan kofin M...! 😂😂😂😂😂 Masu cewa na kulle musu kai kada ku damu zan kuce kawunanne, lokaci ne😂🙏🏻🤝🏻 By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 12 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘 Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku ta wannan number 09097853276. KO kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz domin samun shiga Special Group, wanda cikin kwanaki ƙalilan za'a gama littafin da izinin ubangiji. Ga asusun kamar haka 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, 1k ne SPG sai ki turo min shaidar biyan ki ta wannan number 09097853276. Gareku iyayen ƴan mata da za'a aurar, akwai sittin amare mai kyau na gyaran jiki, bisa farashi mai sauƙin, akwai na manyan robobi akwai na ƙananan robobi, akwai haɗin masu jego, da na maida tsohuwa yarinya, sayan na gari meda kuɗi gida, in kayan gyaran kikeso ki fara min text message ta inbox ta wannan number 09097853276 sai ki gaya min kaya kikeso, kana sai ki kirani to nan zan ɗaga kirankin sai muyi mgn zaki turo kuɗi ta ACCOUNT number ni kuma zan tura miki kaya ta mota, duk garin da kike a Nigeria ina aikawa, in dai ba lungu yayi sosaiba. Kana mutanenmu mazauna ƙasashen ƙetare kamarsu Saudia, India, Gabon, Ghana, Niger, Cameroon, da dai sauransu in kinada dalili kayana na zuwa can cikin salama. Ina saida kaɗan-kaɗan ina kuma bada sari. A dai-dai kan kofin madarar ya sa hannunsa, alamum zai mishi zaɓi kenan, murmushi yayi dan ya samu damar, da zai tserewa tsarinsu. Cikin ihima da sanin makaman kariyar kai daga jin kunya ko yin abinda zai ɓata ran wani, ƙafarshi ta dama dake kusa da hannun Haroon yasa cikin hikima ya bugi hannun Haroon da ke gab da ɗaukar kofin. ture hannun yayi da babbar yatsarsa, wanda, hakan yasa hannun Haroon ya bugi kofunan da ɗan karfi, sai gashi duk sun tuntsure a tsakiyar tiren madarar da zumar kab suka malale cikin tray ɗin. A tare suka zubawa tray idanu gaba ɗayansu. Sitti kuwa wani irin kallo tabi Madarar dashi. Shi kuwa Sheykh Jabeer, cikin iya taku da kamalarsa murya a mutunce ya kalli Haroon daya kafeshi da idon tuhuma, cikin harshen larabci da kamala yace. "Harooon meyasa baka da nitsuwa?". Cikin tarin mamaki Haroon ya gwalo ido tare da cewa. "Haaahh". sai kuma ya kalli Sitti da ta kwaɓe fuska tamkar zata kurma ihun takaici. Shi kuwa Sheykh Jazrah ya zubawa ido, ganin yadda ta zuba mishi kekkyawan idanunta, wanda suke sheƙin hawayen dake nuni da zazzafan son da takeyi mishi. Kauda kwayar idanunshi yayi, da sauri. Jannart kuwa hannun Sitti ta kamo ganin zata jawo tray. A hankali Sheykh Khalillullah wanda yake ƙanin Sitti ya gyara zama cikin sakin fuska da murmushi ya kalli jikan nasu, nitse yace. "Laaba'as". Dib-dib haka ƙirjin Sheykh Jabeer Habeebullah ya fara bada sauti, fahimtar kakanun nashi zasu ɗaura zabin kan, fahimtar lafazin Haroon. Shi kuwa Haroon, wani irin murmushi jin daɗi yayi. Shi kuwa dottijon nan, ido ya zubawa ƴaƴanshi da jikokin ƴaƴan nashi, da wasu jikokinshi. Kallonsu yake yana nazartansu. A hankali wayar Sheykh Jabeer ta fara bada wani sauti mai masifar sanyi da daɗin sauraro, sautin gwauraye yake da kukan sassanyan tsuntsaye. da sauri ya zaro wayar a al'jihun tattausan al'kyabbar tasa. Ganin sunan Maimartaba Nuruddeen ne, ya sashi sakin wata sassanyan ajiyan, cikin ladab ya kalli Sitti, kana a hankali ya kalli Sheykh Abdulkareem, cikin sanyi da nitsuwa yace. "Mai martaba Nuruddee ke kirana, bisa alamu da babbar mgna domin baya kirana haka banza". Murmushi dottijon yayi, domin ya fahimci hanyar fecewa, Sheykh yake nema, hakan yasa ya mishi izinin tafiya. Cikin sauri Sitti ta yunƙuro da niyar yin mgna, sai kuma tayi shiru, sabida nuni da tayi shirun da mahaifinta yayi mata. Shi kuwa Sheykh Jabeer, a hankali ya yunƙara, ya miƙe ya nufi hanyar fita bayan yayi musu, su huta gajiya. Kai tsaye Side ɗinsu ya wuce. Yana shiga kai tsaye bedroom ya wuce, gyara al'kyabbar jikinshi yayi kana, ya zauna bisa wata tattausar doguwar kujera. A nan ƙasar kuma, cikin faɗar masarautar maiartaba Sarki Nuruddeen. Bayan Jamil ya fita, wurin da yayiwa su Bappa Masauki, kai tsaye, sashin kakanin nashi ya nufa. Bayan an mishi isone, ya shiga, ya gaisa da kakan nashi kana ya ƙara da cewa. "Mai martaba, akwai baƙi ma buƙatar kulawarka, suna tsumayinka". Murmushi mai cike da kamala farin dottijon bafulatanin yayi, cikin ratsin sarauta yace. "Yau ka zama, sarkin fada kenan, kaine mai yiwa baƙi iso ko?, ko dai matane baƙin dan nasan ta nan kafi ƙarfi". Ya ƙarishe mgnar da yanayin tuhuma. Kanshi ya ɗan shafa, kana a hankali ya girgiza kansa tare da cewa. "A,a mazane dattawan Fulanin dajine,". Ido ya ɗan zuba mishi kana yace. "Kaje kace a kula dasu, gani nan zuwa yanzu". Kanshi ya ɗan rusunar tare da cewa. "Nasa an basu dukkan kulawar da zasu, buƙata, zuwa yanzu sunfi buƙatar ganinka fiye da komai". Kai ya ɗan jinjina alamar to. Yunƙurawa yayi tare da cewa. "A fito lfy". "Allah yasa". "Amin Amin". Yace kana ya fita. Shi kuwa Sarkin ya fara shirin, fitowa fada. A can sashin Sheykh Jalal ne, zaune da Ya Jafar, Aunty Juwairiyya na gefenshi. karatu yakeyi kamar koda yaushe, tun jiya yaƙi barin sashin Sheykh, koda aka kira Sheykh Jabeer video call, ya ganshi sai yayi ta kuka. Wannan abun shiya ƙara tada hankali Sheykh Jabeer. Yana yawan, bin Jalal, wanda mutane ke zaton ko dan tsananin kamannin da Jalaluddin keyi da Sheykh Jabeer ɗinne yasa, yake ganin kamar shine, to sai dai sam Jalal baya iya mu'amalantar Babban yayan nasu, kamar yadda Sheykh keyi har yake sama mishi nitsuwa, sai dai shima yana iya yinshi. Shigowan Hajia Mama da hadimanta ne, yasa Juwairiyya, jin rauni, a take hawaye ya cika mata idanu. A duniya bata da babbar matsala sama da larurar mijinta. Ita kuwa Mama, gefenshi ta zauna, cikin sanyi ta kalli, Jalal da fuskarshi ke murtuƙe kamar ko yaushe, cikin baiyanar damuwa tace. "Ya za'ayi ya samu gamsuwa da kulawarka, a yadda kake haɗe fuskarnan tamkar wanda aka sanarwar labarin mutuwar uwarshi, ba haka Sheykh ke mushiba, yana kula dashi, da tausayawa da sakin fuska tunda yasan larurar haukace dashi, amman kai ko yaushe kana nan kamar boss". Sai ta kuma kalli Jakadiyarsu Kana, ta kalli Jamil dake waya da alamun da budurwarshi yake mgna, hararanshi tayi tare da cewa. "A haka kuke samawa kanku tabon nunawa a rayuwarku, shi wannan ya zama, mahaukaci, shi Jalal ya zama tantiri ɗan shaye-shaye, kai baka da aiki sai bin matan banza. Kuna samin ciwo a raina, shima kanshi Sheykh duniya ta zata fara zargin cewa mazinacine shiyasa yaƙi yin aure ya zauna, sinƙitin fakitin. Shi kuwa Affan in banda shashanci da tarin ƙuruciya babu abinda yasa a gaba. Ya kukeso inyi, ya kuke son mahaifinku yayi? Yana da yaya maza har ku shida, amman ku biyar manyan duk kun zama, ababe masu taɓo a idon duniya, ya za'ayi yayi mararin gadar mulki a hannun mahaifinshi, tunda yasan shi bashi da masu gadarsa, a kusa,ku duba, Imran da yake uwarsa ta tambaɗaku, ta nesan taku da mahaifinku, sai ta kusanta ɗanta da mahaifin naku. Shiyasa mahaifinku keta ƙin amsar sarautar har sai randa Imran ya mallaki hankalinshi, ku kuwa kun zama ababen kyarata. Yaya zanyi da raina. Shiru sukayi gaba ɗayansu, Shi kuwa Ya Jafar sai ƙara sautin karatun yayi. Yanayi yana zubda hawaye. Shi kuwa Jalal, shiru yayi yana riƙe da hannun Jafar ɗin. Jamil kuwa katse kiran yayi. Affan kuma wanda dama tare suka shigo, fuska ya ɗan kele, cikin irin matsayin da ƴan auta kedashi a wurin iyayensu yace. "Mama, shifa zato zunubine koda ya kasance gsky. Ki dena jifar Mommy da batun wai ita ta tambaɗamu, ya za'ayi keda kanki ki rinƙa suffantamu da marasa nagarta mu dai gsky ba a tamɓaɗe mukeba, Menene a cikin mulki da sarauta, Mama akwai wani mulkine matabbaci a duniya banda mulkin mahaliccin mu, in ma Imran ya gaji sarauta menene a ciki ɗan uwanmu nefa". Cikin sanyi ta girgiza kanta a hankali tace. "Ɗan uba dai ba ɗan uwaba". A tare suka zuba mata ido baki ɗayansu. Aunty Juwairiyya kuwa, ruggume yarta kawai tayi, tana jin ranta na suya. A cikin fada kuwa, tun tuni Maimartaba ya fito, yana shigowa suka gaisa dasu Bappa ya amshesu a mutunce, cikin kulawa, da mutuntaka, bayan sun gaisa ɗinne suka koro mishi jawabin abinda ke tafe dasu. Shiru mutanen fadar sukayi baki ɗayansu, sai muryar Ardo Bani, da yake ƙare zancensa da cewa. "Babban tashin hankalinmu, kullum ɗauki ɗaɗɗayan da akeyima yaranmu da tsoffinmu. Kana a sace dabobbin mu, in mun kai kukanmu ga hukuma ko masarauta sai ayi burus damu, koma a ƙara mana da cin zarafi ko ƙazafi. To gashi yanzu ankai matakin ana sace mana yara, ko gawarwakinsu ba'a bar mana, shiyasa mukayi tattakin isowa gareka adalin shugaba, ka duba lamarinmu." Wani irin zafi da ƙuna ne ya cika zuciyar, Maimartaba Lamido, zalumci yayi yawa. Gyara zaman babbar Al'kebbar sarautar dake jikinsa ya ɗan yi, yana maijin ƙuna da tafasa a zuciyarshi, fargaba da tsoron, haƙin bayin Allah'n da aketa kashewa ya cika mishi zuciya, sabida sanin shine sarki kuma shugaba, ga duk wani mutun dake yankin. Wani nannauyan numfashi yaja mai ƙarfi. Juyawa yayi ya fuskanci maga takardar fadar tashi, cikin bada umarni yace. "A rubuta takarda a aikawa Haman-Ɓachama cewar ina bukatar ganinshi, da gaggawa. Kana ya tabbatar kafin ya isoni yankin da yake mulka babu sauran zalumci, ko ƙabilanci!". Cikin cika umarnin da maga takardar ya ɗan rusuna, tare da cewa. "An gama ya Mai alfarma Sarki Adalin Sarki." Waziri, Galadima, Wambai, Sarkin fada, kana da sarkin dogarai, duk, shiru sukayi sabida a zahiri ake iya hanƙo tsantsar tashin hankali da ɓacin rai a fuskar adalin shugaban nasu. Su kuwa su Bappa sosai sukaji sanyi, a zuƙatansu, sabida nuna kulawarshi garesu, cikin iya sarrafa harshe da tausasan laffuza mai martaba sarkin Nuruddeen Bubayero Joɗa yace. "Kuyi haƙuri, ku gafarceni, bani da labarin dukkan abinda ke faruwa daku, sai yanzu, naji daɗi da kuka nemeni, da matsalarku, In sha Allah ni kuwa zan ɗauki mataki, da izinin ubangiji koda belbelun dake cikin shanunku baza'a sake kashesuba, bare dabobbin ku, bare a kai ga rayukanku. Zan kirayi GARKUWAN FULANI, yanzu, zan sashi maza ya taho ya dawo ƙasar sa, Domin shiga lamuranku nauyin a kanshi yake." Sai kuma ya ɗan numfasa kana ya kalli wani bafadensa dake tsaye bayanshi yanayi mishi fifita da maficin da akayishi da gashin kekkyawan ɗawisu. Cikin bada umarni ya umarceshi daya koma gefe, Da sauri ya rusana ya koma gefen. Shi kuwa Sarki Nuruddeen, wani ɗan kekyawan matashi dake gefen damanshi ya kalla tare da cewa. "Imrana, kiramin Sheykh Jabeer." Kai ya ɗan rusunar kana yasa hannu ya amshi wayar da Kakan nashi ke miƙa mishi. Amsa yayi, kana ya kira Sheykh Jabeer, wanda shi kuma a dai-dai lokacin yana gaban Sheykh Aliyu, Abdulkareem, Jabeer, Sitti, Jazrah, Haroon. Da dai sauran ahlin nasu. Wanda kiran ne yasa ya samu ya fece daga tarkon da ake naɗa mishi. Jin wayar tayi ringing har ta katse ba'a ɗaga bane, yasa Imran ɗan rusunar da kanshi tare da cewa. "Wata ƙil baya kusa da wayar." Kai ya jinjina mishi tare da cewa. "A a zai kira, bayan amsa kirana yanzu zai kira". Kai ya gyaɗa alamar gamsuwa. Suko su Bappa duk suna zaune cikin kamala. Shi kuwa Sheykh kamar yadda ya saba, hakane baya amsa kiran kakan nashi, sai dai ya bari in tayi ta katse sai ya kira, shiyasa, yanzuma ya bari saida ta katsen sannan ya kira. Gyara zamansa yayi tare da kara wayar a kunnensa na dama. Imran kuwa yana ganin kiranshi yayi maza ya amsa, cikin tarin girmamawa yace. "Barka da hantsi, Hamma Jabeer". A can gefen Sheykh Jabeer ɗin kuwa, ido ya lumshe cikin yanayinshi da sun rigaya sun saba yayi shiru. Da sauri Imran ya kuma ɗan rusunar da kanshi yace. "Afwan Sheykh Assalamu alaikum ". Murya can ƙasa yace. "Wa alaikassalam". Cikin ɗan tura baki Imran ya kuma maimaita mgnarsa ta forko. "Barka da safiya, Hamma Jabeer ya, Sitti?". A taƙaice yace. "Alhamdulillah". Da sauri Imrana yace. "Masha Allah, ga Lamiɗo". "Na'am". Yace a takaice. Shi kuwa Imran miƙawa kakansu wayar yayi. A hankali Sheykh ya ɗan buɗa laɓɓansa cikin zazzaƙan sautin muryarsa yace. "Assalamu alaikum". Murmushi mai cike da so da ƙaunar jikan, nasa yayi tare da amsa sallamar tasa. Gaisawa sukayi, bayan sun gaisa ya tambayi labarin su Sitti da ƙanennenta da kuma mahaifinta, sai kuma ya kora mishi jawabin abinda ke faruwa a jihar tasu. Kana, ya ɗoro da cewa. "Ka dawo, kayiwa lamarin tubkar hanci". Cikin sanyi yace. "In sha Allah. Ina nan tafe, nanda kwanaki uku. Ina jajanta musu, abinda ya faru, kuma in sha Allah. hakan bazai kuma faruwa ba. Da haka sukayi sallama. A can garin Numan kuwa cikin Rugar Kikan. Gaba ɗaya garin shiru yayi, dan wannan abunda ya faru yayi masifar shiga jikinsu. Da dama maza matasanmu sun tafi kiwo, kamar yadda suka saba, rayuwar yau da kullum. Saura sai irin dattawan da aka bari, da mata da yara maza da mata. Cikin garin Bonon kuwa, gaba ɗaya, matasan garin dama ƙauyuka gefensu na ƙabulun Ɓachamawa, duk sun hallara wuri ɗaya, suna cike gaban dodon tsafinsu, wato Bonon ɗin, giyar burkutu mai ɗan karen tsami da wari, suketa sha, tamkar zasu fasa cikkunansu. Yayinda gefe guda kuma, maƙerar dake gefe wasu matasa su ne maƙera keta wasa ababen faɗansu, kamarsu wuƙaƙe, Adda, sitaka, barandami, mashi, kibau, da dai sauran mugayen makamai, sai sheƙi sukeyi. Suna cike a wurin, Ba'ana ya iso, cikin wata shigar rigar saƙi. Hanya suka rinƙa buɗa mishi, hardai ya isa ga sarkinsu, dake zaune gefen dodo sun. Zama yayi kusa da sarkin nasu ya sasu a gaba, Cikin harshen ɓacamancin yace. "Ku hanzarta, ku shiga, duk matasansu majiya ƙarfi, sun tafi kiwo. Dottijan su kuma sun tafi, kai gulmarku, ga Sarkin su wannan karon basu tsaya ga sarkinku na nanba, ina da yaƙinin kuma za'a sauraresu a can. Yanzu matansu da ƴaƴansu, ƙanana mata da mazane suka rage a garin. Sai wasu dattawansu dake, dakon dawowar magulmatan can. Kuyi maza, kushiha kafin su dawo, ku share garin kab. Ku kashesu gaba ɗaya babba da yaro mace dana miji." Da sauri wani daga cikin su yace. "Harda gidansu Shatu?". Cikin izaya yace. "Harda su, domin Mata, bata nan, ku kashe kowa nata, ta hakane zata dogara dani kaɗai tunda bata da kowa nata a duniya, dole Ni zan zama mijinta ubanta yayunta ƙannenta uwarta, in zama Garkuwarta in zame mata duniyarta ta hakane zata yarda nine ɗaya gatanta kuma duniyarta, ba tare da ta zargeniba, a hankali wata rana in sata tayi ridda, musha giya, muyi tsafi tare da ita, bazatayi min musuba, mu haifi ɗanmu na forko mu bawa dodonmu yasha jininshi yasa mana al'barka a aurenmu". Wani irin ihu da sowa na tsantsar jin daɗin bayaninshi sukayi baki ɗayansu. Hakama dodonsun, saida ihunshi ya firgitasu baki ɗayansu. Dariya mai amo mara daɗin ji. Sarkin nasu yayi, kana ya busa ƙahon dodonsun, alamun ya basu izinin tafiya. Nan fa duk suka rinƙa shiga, cikin maƙerarnan suna ɗaukan makamai, suna nufar garin Rugar Kikan (Rugar Bani) kenan a guje... Cikin garin Shikan kuwa, Bani rana ta fara tasawa, mata masu zuwa tallan nono cikin garin Numan, suka fara ɗaukar ƙorarensu, suna fita garin. Yara maza da mata kuwa, wasu na wasa wasu na ɗebo ruwa, wasu na ɗebo kayan lamɓu. Yayinda wasu kuma suka dawo break dan tara tayi. Cikinsu kuwa harda Junainah. Tafe take da saurinta da ɗan tsalle-tsallenta tana rataye da yar jakarta, da sauri ta tsaya ganin Junaidu a gabanta rike da kwanɗon zabari wanda yake cike da ƴaƴan itatuwa. Murmushi ta ɗanyi tare da sunkuyar da kanta cikin surutunta tace. "Har naji tsoro!". ta ƙarishe mgnar tana kallonshi, Murmushi yayi mata shima cikin son ƴarinyar yace. "Haba dai, tsoron me kuma zakiji, tunda gani, babu abinda zai sameki muddin ina raye, zan zame miki Garkuwa". Da sauri tasa hannu ta rufe bakinta tare da cewa. "Kai! Kai! Ya Junaidu, sunan Babanmufa ka kira". Murmushi mai kama da dariya yayi kana yace. "Au na manta ashe sunan surki nane". Kai ta gyaɗa mishi kana tasa hannu ta amshi, nonon inabin da yake miƙa mata, baki ta buɗe da nufin sawa a baki, sai kuma ta tsaya tare da tura baki jin yana ce mata. "No kada kici ba'a wonke bafa." Sai kuma ya ajiye kondon, ya amshi inabin ya ɗan gangara, gefe kaɗan ya wonkeshi a bakin ruwan wutsiyar Kogin da yayiwa Rugar tasu ƙawanya. Ya tahowa tana kallonshi. Koda ya iso miƙa mata yayi, kana ya ɗauki kondon, ganin still tanata kallonshi ne ya sashi cewa. "Ya dai?". Kai ta kauda tare da fara tsinkar ƴaƴan inabin tana afawa a baki tana taunawa, Murmushi ya kumayi ganin yadda ta lumshe idonta. A hankali tace. "Ya Junaidu kayi kyau sosai yau, har kamar ka fini kyau". Dariya ya ɗanyi kana yace. "Yo dama ai na fiki kyau". Maƙe kafaɗa tayi tare da cewa. "Uhum a a kam". A haka dai suna tafe suna hira. Can cikin gida kuwa, Ummiy ce zaune bisa kujera ƴar tsuguno da buta a gabanta, alamun al'walan sallan walaha, zatayi. Inna kuwa, da wasu maƙotansu uku Biba, Hari, da Innawuro. suna zaune bisa taburma a tsakar gidan. Suna amsar gaisuwa. Can cikin garin kuwa su Alhamdulillah Manu dasu Siddine da dai sauran dattawan garin ne zaune a fada. Sai yara daketa kai komo. Da sauri su Siddi suka miƙe tsaye ganin, matasan mayaƙan ƙabilar ɓachama, sunata shigowa garin tako ina gabas da yamma kudu da Arewa, bisa dukkan alamu zobe sukayiwa garin Kana ga zurma-zurman makamai masu tsawo tamkar raƙumai. Sai sheƙi sukeyi. Cikin ɗaga murya, Alhaji Manu yace. "Kai lfy? me haka?". Ganin sun nufosu gadan-gadan ne yasa, suka miƙe gaba ɗayansu, kowa ya fara, neman makari, to amman ina, basu da zato ko sanin za'a far musu, shiyasa basu da shirin komai na kare kai. Ɗaya daga cikin sune, yace. "Mu gudu kashemu sukeda shirin yi ba tare da laifin komaiba". Siddine ya kuma ɗaga murya tare da cewa. "To in mun gudu matanmu da yaranmu fa". Ihun da sukajiyo tako wani sashi na garinne ya tambatar musu, ana karkashe su. Gudu suka farayi kowa ya nufi hanyar gidanshi dan ɗaukar matakan kare kai. Sai dai ina basu da hanya duk inda suka ɓullo sai sunci karo da, mayaƙan. Lokaci ɗaya garin ya ruɗe ya birkice kota ina sai ife-ife da gudun ceton rai da makiyayan Rugar Kikan keyi. Wani irin sauti mai baiyana azabar fitan rai Alhaji Manu yayi, lokacin da wani kafurin ya caka mushi sitaka a ƙahon zuciyarshi. Siddine ne ya juyo da azaban razani, amman sai shima ya saki wani sauti mai gigitarwa jin azaban sara da sukan da akeyi mishi. Garifa ya kacame, Hadi ne babban ɗa ga Alhaji Haro mahaifinsu Junaidun Junainah, ya nufi cikin gidansu da azama, Yana cike da fargaba, da tashin hankali domin wasu irin ihu da yake jiyowa a cikin gidan nasu. Yana kusa kai ya samu, makasan suna cike a gidan. Suna ta'addanci, sun kashe kowa na gidan. Ganin haka ya juyo yana juyowa. Yayi kiciɓis da abokinshi Sale, yana tafe jini na zuba an farka mishi ciki. Cikin magagin mutuwa yake cewa. "Hadi sun kashe kowa na garin nan sai wanda baya nan. Hadi na kira Hukumar yan sanda ta nan cikin Numan na shaida musu, amman kafuran nan maƙiya Allah da Manzonsa sai cewa sukayi, A kashe mu mana, ai an rage musu aikine. Na kira su Arɗo Bani, suna ɗagawa katin wayata ya ƙare. Hadi sun kashe kowa na gidanmu. Taroshi Hadi yayi suka faɗa nan suna kuka mai cike da taraddadin rabuwa. Cikin ƙarfin hali Sale ya ture Hadi tare da cewa. "Ka gudu Hadi ku gudu, Ni nasan bazan rayuba. Ka gudu. Sun kashe min Kowa har jariren tagwayen da aka haifa min shekaran jiya, sun kashesu. Cikin kuka Hadi yace. "Bazan iya guduba Sale su kasheni kawai, ina zanje bayan sunyiwa garin zobe. Da ƙarfi Hadi ya abka jikin Sale Jin ansa gatari an sari kafaɗarsa ta dama, Juyowar da zaiyi kuma aka tsira mishi mashi a ƙirji. Nan take ya cika, hakama Sale. Cikin gidansu Shatu kuwa. Ummiy ta sallame sallan kenan, taji. Inna dasu Innawuro suna kurma ihu da salati. Yunƙurawa tayi da azama jiki na rawa ta nufo woje. Fitowanta yayi dai-dai da lokacin da aka sare kan Innawuro, wanda kan yayi tsalle ya faɗo kanta, kana ya gangara ya faɗa gabanta. Wani irin ihu mai cike da karaji gauraye da salati ta kurma lokacin da taga an burmawa Inna mashi a ciki. Ihunta da salatinta ya jawo hankalin su, sukayo kanta. Sai dai kafin su isoma ta yanki jiki ta faɗi babu numfarfashi tamkar matacciya. Koda suka iso, dariya suka kece da ita cikin rashin imani ɗayansu yasa ƙafa, ya taka ruwan cikinta, tare da cewa. "Shegun FULANI ku mutu, mu huta, da ganinku a garinmu, gonakinku da dabobbin ku duk sun zama namu. Mu ɗauke yaranku mata mu maidasu karuwanmu, muyi musu ciki su haihu mu bawa dodo. Muji daɗi dasu. Ganin kamar ta mutune yasa suka tattakata suka wuce suka fita daga gidan. Junainah kuwa da Junaidun, suna gab da shigowa garin suka fara jiyo ihun mutanen garin. Cikin azaban firgici Junaidu ya wurgar da kondon ƴaƴan itatuwan dake hannunshi, da gudu yabi bayan Junainah data ruga a guje sabida hango, anata kashe mutane a gabansu. Cikin kuka da tarin kiɗima da fita haiyacinta take cewa. "Wayyo Ummiy Wayyo Inna Wayyo Bappa, zasu kashemu. Wayyoooooooo Adda Shatu zasu kashemu". Riƙo hannunta yayi da ƙarfi cikin rawan jiki da murya yace. "Junainah bazasu kashekiba, zan kareki da izinin ubangiji, zaki rayu, Shatu bazata rasa kowa duniya ba. Junainah zan zame miki Garkuwa zan fanshi ranki da nawa ran. Ki zama tamkar yar tsira, Shatu ta zama tamkar yar jarida, ta rubutawa mutanen duniya su karanta, kisan gillan da akeyiwa Fulani mazauna daji. Da ƙarfi yasa hannu ya zaro wukar dake ƙugunshi wanda da ita ya yayyanki nonunan ayaba dasu inabi. Wayarshi ya kuma zarowa Ya Salmanu ya kira, Salmanu kuma dake, kwance a gadon asibitin nan Genaral Hospital Numan. Wanda bai workeba tun dukan shaɗi da ba'ana ya mishi. A hankali yasa hannunshin ya amsa kiran wayarshi ganin Junaidu ke kiranshi. Cikin kiɗima da firgici Junaidu yace. "Ya Salmanu, mayaƙan ƙabilar ɓachama sun shigo Rugar mu, sunata kashemu, mazanmu da matanmu. Ya Salmanu Junainah ina son ta tsira, ko dan ran Junainah ka kira mana hukumar yan sandan cikin Adamawa, ina son su iso su ceci Junainah kada Shatu ta rasa kowa a duniya. Ban saniba ko zan gazawa bawa Junainah tsaro". Gaba ɗaya jikin Salmanu rawa da tsuma yakeyi, katse kiran yayi da sauri ya kira. "A.S.P Kabiru Nasir. Wanda yake, Hetkotan Adamawa. Koda ya mishi jawabin abinda ke faruwa, a take. A.S.P ya kira. S.P Daniyel dake Numan ya bashi doka da oda maza-maza su bawa fulanin Rugar Kikan tsaro gaggawa, shima yana nan tafe da rundunar sa. Ya bashi umarni mai ƙarfi ya ƙara da cewa, muddin yazo ya samu ba dai-dai ba ta ɓanƙaren tsaro, to akan aikinshi. Wannan abun na umarni daga samane, yasa mugun kafurin nan. Firgita gudun rasa aikinsa, da tonuwar asirinsu da gudun kada a cireshi asa musulmi a kujerarsa, yasa cikin gaggawa ya haɗa kan rundunar sa ya nufi. Cikin Rugar Kikan. Junainah kuwa wani irin karkarwa takeyi wanda, tuni fitsari ke tsiyaya yana bin sawunta. Wani irin ihu tayi, ganin wani kafurin ya kaiwa Junaidun sara a bayanshi. Wani irin juyi Junaidun yayi ya farma kafurin da da wuƙarsa dan kare kansa da Junainah. Duk da su biyar suka zagayesu, basuyi nasara a kanshiba, yana kare kanshi da Junainah, har saida suka tsira daga waɗannan. Sai kuma wasu, mutun takwas suka cimmusu. Da ƙarfi suka banƙaren Junaidun, suka fara kiciniyar zare Junainah da ya ruggumeta da azaban ƙarfi da yayi. Wani irin ihu yasa jin an caka mishi. Wuka a gadon baya. Still bai saketaba, sai yaƙin kareta da ya farayi, da iya ƙarfinshi. Ita kuwa Junainah ganin an caka mishi wuƙane yasa ta sume. Dai-dai lokacin kuma rundunar yan sandan suka iso. Kamar bazasu guduba, dan sun san da bakin hukumar sukeyin aikin, to sai dai ganin musulman cikin yan sandan suna sakin harbine yasa. Suka ari ta kare. Daga nan suka rinƙa gudu sunayiwa yan uwansu fito alamun su gudu. Cikin ƙanƙanin lokaci duk suka gudu. Su kuwa yan sandan, suka shiga cikin Rugar Kikan ɗin. Hankalin musulman cikinsu yayi masifar tashi ganin irin kisan gillar da akayiwa bayin Allah'n nan, kisa na rashin imani. Nan take suka kira motocin asibiti. Suka rinƙa jidon masu sauran rai suna sawa a motar ambulance suna kai cikin Genaral Hospital Numan. Kana suna harhaɗa gawakin kuma a tsakiyar garin. Cikin mintuna talatin rundunar A.S.P ta iso. Tare da yan jaridu. Su Bappa kuwa. Koda suka gama tattaunawa da Maimartaba, sai ya umarci Waziri daya hanasu tafiya a bisa adalcinsa. Yace su tsaya suci abincin rana, kana suyi sallan azahar kafin su tafi. To haka yasa suka zauna. Waziri yasa akayi musu duk ihsanin da Maimartaba ya bada umarnin ayi musu. Sukaci abinci sukasha, Sannan sukayi sallan azahar. Daga nan aka sallesu suka tafi. Tuni cikin gari kuwa gidajen rediyo sun ɗauka, batun faɗan FULANI makiyaya da Ɓachamawa manoma, wanda akaso a juya rahoton da cewa makiyayan ne sukayiwa manomanne ɓarna. Bayan. Tafiyan su Bappa da kamar 30 minutes ne. Labari abinda ya faru ya riski Maimartaba. Nan take yasa Waziri da Galadima da hadimai mutun ashirin suka nufi cikin Numan dan suje su tabbar da abinda akace ɗin. Su Bappa kuwa, sam basuji lbrinba saida suka isa cikin Numan. Ganin garin a hargitse ne yasa Arɗo Bani ya kalli Bappa da Alhaji Haro da suke gefenshi cikin mmki yace. "Lafiya kuwa? Meke faruwane a garin nan?". Cikin kaɗuwa suka haɗa baki wurin cewa. "Allahu alamu". Drivern nasune, ya kallesu a tsorace yace. "Anya kuwa yau ba faɗa akeyiba a garin nan ba". "Kai ba lfy ba kam!". Cewar Alhaji Umaru Shi kuwa Drivern, bakin titi ya ɗan gangara ya tsaya, ya tambayi wasu yan agaji daketa. Shiga cikin wani babban Pharmacy da alamun magunguna suke saya, koda suka mishi bayanin abinda ya faru. Jiki na rawa yazo ya sanarwa su Arɗo Bani. Lokaci ɗaya hankalinsu. Yayi masifar tashi. Nan sukace ya wuce dasu. Asibitin. Koda sukaje hanasu shiga akayi. Hakane yasa, sukace to ya wuce dasu Rugarsu. Suga ko canma akwai uban da zai hanasu zuwa. Nan ya nufi cikin Rugar tasu dasu. Su Wazirima tuni, sun iso. A can cikin masarautar kuwa, Sosai hankalin Maimartaba ya tashi. A can ƙasa mai tsarki kuwa. Sitti ce tsaye gefen Sheykh lokacin da yake mgna da kakanshi. Zama tayi gefenshi, tare da tsareshi da ido. Baibi ta kantaba, ya ci gaba da sarrafa wayarshi. Wata number, ya dannawa kira kana ya kara wayar a kunne, jim kaɗan aka amsa kiran. Bayan sun gaisane, ya ɗan gyara zamanshi tare da ɗan kallon Sitti ta gefen ido Cikin harshen fillanci yace. "A haɗa min zama da Ƙungiyar TABITAL POOLAKU". Sai kuma ya ɗan shaƙi sanyi da ƙamshin ɗauki ido ya lumshe cikin kamala da nitsuwa yaci gaba da cewa. "A kira min Ƙungiyar MIYETTI ALLAH, da gaggawa, ina da zama dasu. Ranar Jumma'a in sha Allah". Hannun damanshi yasa yana shafa sajenshi, tare da sauraron mgmar da. Arɗon Arɗaɓe keyi. "Ranar jumma'a kuma? Ka dawone?". A takaice yace. "Zan dawo!". Cikin gamsuwa da mgnarshi sanin in yace eh, eh ɗince in kuma yace a a, tofa a ance. Muddin kuma yace zaiyi abu to da izinin ubangiji sai yayi shi. Cikin jin daɗi adalci da kulawarshi ga shugabanci da aka bashi yace. "To Allah ya dawo da kai lfy". Yatsun ƙafarshi ya sunkuyar saida suka ɗan bada sautin ƙaras, kana yace. "Amin ya rabbil izzati". Daga nan ya katse kiran. Kamar bata wurin haka ya jawo System ɗinshi ya fara daddannata. Kamar babu kowa kusa dashi haka yaci gaba da aikinshi. A system, ita kuwa Sitti ido ta zuba mishi. Tana kallon yatsun hannunshi da yaketa sassarfa, tamkar shiya haaliccin na'ura. Yanajin idanunta na yawo a sasan jikinshi, hakan yasa, ya ɗan juya kwayar idanunshi, ya ɗan kalleta ta wutsiyar idonshi, murya can ƙasa yace. "Sitti wannan kallonfa, kin san bana son kallo kam ko?". Ajiyar zuciya ta ajiye, kana ta ɗan janye Hiramin kanshi, da sauri yasa hannunshin ya kame hiramin cikin kwaɓe fuska yace. "Sitti ya haka, kinsan Haroon ba kan gadone dashiba, yanzu zai iya shigowa da yaran nan". Ido ta ɗan rufe kana tace. "To su yaran mayune, ko yaushe kana rufe da Al'kyebba da hirami, kasha iska mana, ko nauyi basa makane?". Kanshi ya ɗan juya kana a hankali yaci gaba da aikinshi tare da cewa. "Suturce jiki shine, zaiyiwa ɗan adam nauyi, Sitti, sannan ya za'ayi in bari ko wani Tom and Jerry su kallarmin suman kai, ai shi hula da hirami kamar ɗan kwaline wa mace". Sai ya kuma ɗan juyowa ya kalleta tare da cewa. "Yauwa Sitti, bana son ana sawa Jazrah tana samin abinci, bana so, sai a turrota tazo taita kare min kallo". Fuskarta ta haɗe kana tace. "To yayi kyau, kawai in baka sonta, ka fito fili ka faɗa mana". Kauda mgnar yayi tare da cewa. Ki shirya in sha Allah zuwa ran jumma'a ina son in kasance cikin ƙasata ta haihuwa a jiharmu a kuma masarautarmu". Haroon da yanzu ya shigone ya ɗan kalli ɗan uwan nashi, cikin mmki yace. "Sheykh kawai dan ana mgnar baka matar aure shine kake shirin guduwa zaka bar ƙasar ba?". Bai kalli Haroon ba kuma baice, komai ba, sai rufe system ɗinshi yayi kana ya miƙe a hankali, gaban drower'n gadon ya nufa, buɗewa yayi, wasu E Passport guda biyu ya ɗauko, Kana ya dawo gaban Haroon. Hannun shi ya kamo ya danƙa mishi su, kana yace. "Gasu, ina son zamu bar ƙasar nan ranar al'hamis." Da sauri Sitti tace. "Kaida waye zaku tafi". Ba tare daya kalletaba yace. "Da ke". Kai ta kuma juyawa tace. "A a kam ka koma kai ɗaya, ni ban gaji da ganin ahlinaba". aKanshi ya kaɗa tare da cewa. "Zafa ki koma, don bazan barki a kasar nanba, kiyi ta haɗa min tarko, dole tare zamu tafi, inada zama mai mahimmanci, dole inje inji da matsalar al'ummar da aka naɗani GARKUWANSU, tunda ke kika sa na amince da wannan naɗin, ina zamana lfya, wani mulki ko sarauta basa jadawalin rayuwata, keda waɗancan tsofoffin sarakunan kuka likamin wai GARKUWAN FULANI, To sun samu matsala kuma dole inje in bincika". Shiru kawai Sitti tayi ganin karfin hali ziraran miraran. Zuwa yanzu ta dena mmkin, cewa akan abu biyu Sheykh ke iya doguwar mgna, akan Alqur'ani, wanda shine zaka samu zai iya wuni a zaune yana tabsiri ba gajiya ba yunwa bare ƙishi ko bacci. Sai kuma akan wannan sarautar GARKUWAN FULANI da aka bashi shekarun biyar baya, wanda harga Allah baison wannan Sarautar ko kaɗan sai dai dole da akayi mishi, da fushin da Abbunsu ya nuna a kan haka. Shiyasa duk sanda zaiyi ƙorafi yakan iya jera mgna biyar zuwa bakwai, wanda sam shi tsarin rayuwarsu ba mai doguwar mgna bace. Kai takaɗa jin yana cewa. "Ku ɗan bani wuri". Basuyi mgna ba suka fita, a tare, domin sun san Sheykh Jabeer mutunne mai tarin tsananin al'kuyya da killace jikinsa, shi kanshi yana kunyar kanshi a rayuwarshi ta duniya shi bai taɓa yin tsirara a kan kanshi wai yaga surar jikinshi ba, Allah yasani yana masifar jin kunyan kanshi. Haka yasa koda wonka zaiyi, baya yin tsirara, yanada wasu tausasan gajerun towel wanda duk rintsi dasu yakeyin wonka a jikinshi. Suna fita falo, Haroon ya tsaya yana kallon Jazrah, dake konce bisa kujera ta kife kanta a cinyar Jannart tana kuka mai sanyin sauti. Kai Sitti ta juya ta nufi ɗakinta, Allah ya sani Jazrah na son Sheykh, shi kuwa bai nuna ya tsaneta ba, amman dai ya nuna zahirin bazaiyi aureba. Haroon da Jannart ne suka zauna suna bata baki. Saida ta nitsune suka fita tare. Shi kuwa Sheykh suna fita, ya maida ƙofar ɗakin ya rufe. Kana ya dawo bakin gado. A hankali ya zare tattausan al'kyabbar jikinshi, fararen kayan dake jikinsa suka baiyana. A hankali ya zare rigar ya ajiyeta gefe. Zariyan wonɗon ya kunce, tare da zama, ya saɓule tare da matsawa gefe. Ya rage dagashi sai fararen boxes da vest. Juyawa yayi yana taku mai cike da nitsuwa, ya shiga bathroom ɗin. Yana shiga ya maida ƙofar ya rufe, kana ya rage hasken ciki. Sannan ya cire ƙananan suturun dake jikinshi tare da ɗaura towel ɗin, a ƙuginshi zuwa kan cinyoyinshi masu yelwar gargasa mai taushi da tsulɓi da sheƙi tana,konce lib-lib a farar fatar jikinshi. A haka ya fara, wonkan, bayan yayi Brosh a hankali yake bin jikinshi da sabulun mai ɗan karen ƙamshi, yanayi ya cuccuɗa jikinshin. a hankali ya iso kan ƙugunshin, cikin sabo da iya ɗabi'ar tasa, ya cusa hannunshi ta cikin ɗaurin towel ɗin, ya rinƙa cuccuɗa jikinshin da murza mishi daddaɗan sabulun ya murje ko wani lungu da saƙo na sasan jikinshi ba tare da idanunshi ma, sunga tsiraicinsaba. A ƙalla yayi sawon daƙiƙu ashirin a bathroom ɗin kafin, ya fito, yana ɗaure da wani babban towel mai ɗan karen kyau da taushi bayan ya matse wancan ya shanya. Yana saƙo ƙafarshi cikin bedroom ɗin ya...! Solo-salo-salon GARKUWA na dabanne! By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 13 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘 FREE PAGE Littafin GARKUWA na kuɗine, Special Group 1k Normal 300, in kina buƙatar karanta lbrin GARKUWA turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan layin 09097853276. Gareku mutanen Special Group turo dubu ɗaya ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276. *Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki, in kin san zaki sayi littafinane dan ki fitar dashi, na roƙeki da Allah da Manzonsa da darajar iyayenki kada ki saya bana son kuɗinki, ki riƙe kudinki ki barni in riƙe littafina. Dan Allah nace badon niba.* Yaji anata bubbuga mishi ƙofar ɗakin, bai kulaba, yazo a zauna bisa kujerar dreesing mirror, a hankali yake tsane ruwan jikinshi, bayan ya gama ɗan tsane ruwanne ya busar da tattausan sumar kanshi, ta hanyar na'urar busar da gashi. Mai ya ɗan shafa, kana ya gyara gashin da kyau, sannan ya miƙe yaje gaban. Drower'n, a nitse ya buɗe, wasu datsatstsun kaya riga da wondo na yadin Lamud, yadin Sky blue ne mai masifar kyau. Sai kuma ya zaro wata farar al'kyabbar fara ƙal. Da farin hirami. Rufe wannan gefen yayi, kana ya buɗe ɗaya gefen. Ƙananan kayan ne a ciki kamarsu Jallabiya da boxes vest dasu zagayen baƙin abin da yake ɗaurawa kam hiraminshi. Suma duk mafi akasari su fararene. A bakin gadon ya ajiyesu. Kana ya fara kimtsawa. Bayan ya gama shirinsa ya fito ras cikin kalar sky blue and white sai Black half cover da kuma baƙin zagayen saman hiramin. Ya fito ras tamkar dai yadda zuriyar mahaifiyarshi da suke tsatson limamen Harami suke fita. Ko yaya ka ganshi dole kace shi balarabene, sabida komai nashi irin nasune. Kyau, fari, gashi, ilimin addini, nitsuwa, imani, da kuma irin shigarsu, da shima ya rainu da hakan tunda a cikinsu ya girma. Wani turaren Oud Kareem ya feshe jikinshi dashi. Lumshe ido yayi sabida shida kanshi ya shaida ƙamshin wannan turaren nashi iyakane. A hankali ya nufi ƙofar fita yana tafe yana tasbihi. "Astagafirullaha wa'atubu ilaik. Astagafirullaha zunuba jami'an. Subahanallahi Wal'hamdulillah wa la'ilahaillahu Allahu Akbar." Da wuya ka iya jin abinda yake faɗin, sai dai ina ka lura da motsawan jajayen laɓɓansa, masu kama da jajayen kunnen fire masu taushi zaka fahimci tasbihi yakeyi. Ba kowa a wurin sabida haka ya nufi falo a nitse, A falon ya samu Sitti bisa dukkan alamu, shirin tafiya harami tayi. Tana ganinshi ta miƙe tare da cewa. "Muje ko". Kai ya gyaɗa mata, kana ya ɗan kalleta bayan ya ɗan tsagaita tasbihin bakinshi yace. "Zan shiga wurin Sheykh Abdulkareem". Cikin kula tace. "Muje sai mun dawo mana". Kanshi ya jujjuya mata kana yace. "Zan sanar dashi batun komawarmu". Gyara matafinta tayi tare da cewa. "Na sani ai, muje sai mun dawo". Fuskarshi ya ɗan haɗe tare da cewa. "Ni a harami zan kwana". Ganin ya kafe tasan fa duk yadda tayi, hakan zaiyi, binshi kawai tayi, suna shiga suka samu kamilin dottijon nan, bisa tsakiyar yaranshi, da alamun suma ɗin anjima zasu taho masallacin. Yana hanƙoshi ya miƙa mishi, hannunshi na dama, da sauri ya isa gareshi, ya kama hannunshi tare da rusunawa, ɗaura hannun yayi bisa tsakiyar kanshi, sannan yayi shiru yanajin yadda dottijon ke zuba mishi addu'o'in. Yayinda kamilan yaranshi ke amsawa da. "Ahmeehn! Ahmeehnn!! Ahmeehnn!!!." Bayan ya gama mishi addu'o'in ne, ya juyo ya gaida kakanun nashi, baki ɗayansu. Kana ya shaida musu tafiyarsu data taso cikin gaggawa ya kuma sanar musu dalilin tafiyan. Sun gamsu da hakan, kasan cewar sun ɗan ɓata lokaci a nanne yasa. Tare suka tafi masallacin baki ɗayansu. Haroon kuwa cikin kwana biyu ya gama musu komai na tafiyarsu, gida dan shima dama yana son tafiya gida shida Jannart ɗinshi duka. A cikin makarantar su Aysha kuwa. Sam bata samu lbrin abinda ya faru a rugarsuba. Sai da yamma, nanma Rafi'a ce, dake riƙe da wayarta tana chatting. A nan ne ta gani a kafafen yaɗa labarai cewa. Anyi faɗa a tsakanin MAKIYAYA da manoman, a garin Kikan dake gaɓar kokin Namun. Koda ta sanarwar Aysha. Taga tashin hankali ya wuce zatonta, hakane yasa ta bita suka tafi tare. Su Bappa kuwa bayan sun nufi, rugar tasune, sukaci karo da motar police officers, da kuma Ambulance ɗin, daya ɗebo su Ummiy dasu Junaidun da Junainah, kana. Da wasu wadanda ake ganin kamar sunada ɗan sauran numfarfashi. Da sauri C.P Daniyel yasa, drevernsu Arɗo Bani, ya juya dasu, dan suka nufi cikin Genaral Hospital Numan ɗin, sabida yasan in sukaje suka, ga irin kisan gillar da ƙabilun nan sukayiwa yan uwansu, tashin hankali zaiyi yawa ya kuma san A.S.P Kabir da rundunarsa na, can, to zasuyi mishi bayanin da zaisa ya iya korarshi a aikinshi. Shiyasa ya jasu suka koma, cikin asibitin. A cewarsa su kula da mutanen su, saura kuma, kuma, akwai hukuma na, kula dasu a can. To wannan dalilin ne, yasa suka koma cikin asibitin, Hakane yayi sanadin da koda Waziri da Matawalle da rundunar Hadiman da Sarki ya aiko, Suka zo, basu ga su Arɗo ba a cikin Rugar, kana kusan wuni sukayi a nan dan sai yamma, suka juya suka koma masarautarsu. Ita kuwa Aysha, suna zuwa, kai tsaye cikin asibitin suka nufa, dan tayi waya da Bappa. Koda suka iso, sosai hankalin ta ya tsananta gaba hankalinta ya tashi, ganin gaba ɗaya asibitin a cike yake da mutane su, sai dai ta ɗan samu nitsuwa kaɗan ganin Ummiy da Junainah sun farfaɗo, sai dai duk basa mgna sunyi zurui dasu hakama sauran waɗanda suka samu suka farfaɗo ɗin. Koda ta tambayi Bappa inasu ya Giɗi sai cemata yayi suna gida, ya ɗaura da cemata. "Yauwa Shatu ku zauna nan, ku kula da marasa lfyan, bari mu kuma mu ƙarasa can Rugar tamu, mu duba meke faruwa a gidan". Hannu tasa ta share hawayenta dake shatata daga cikin kumburarrun idanunta cikin disashewar muryar da kuka yasa ta dishe tace. "To Bappa kuje, zamu kuladasu, ga can Ya Salmanu ma, ya turo mana abokanshi, ga kuma ƴan agaji, zamu zauna dasu". Cikin tarin ƙuna da tafasar zuciya, Alhaji Haro, ya gyara gariyarsa tare da cewa. "Mu tafi". Arɗo Bani ne ya miƙe tsaye tare da yin gaba kana duk suka bishi a baya suka fita suka tafi. A hankali Rafi'a tasa hannu ta tallabi Aysha daketa kuka mai sosa zuciya, kuka mai cike da rauni da taraddadi. Zama sukayi cikin tausayawa Rafi'a tace. "Ki dena kuka Aysha, in sha Allah babu komai." Murya na rawa hawaye na kwaranya ta buɗe manyan idanunta da suka rine sukayi jazir da kuka da tashin hankali, cikin rauni tace. "Rafi'a babu komai kuma?, ko dai komai ya faru, kalli fa halin da yan uwana da maƙotanmu suke ciki, kinjifa ance an kashe mutun kusan 40, kuma kin san gidajen rediyo suna ragewa nema wasu lokutan sabida kada, hankali mutanen duniya ya tashi. Rafi'a banga Yayuna ba, ko ɗaya ban ganiba, banga Inna ba, kalli Junaidu, kalli can Ya Mati yayansu Ya Salmanu. Kowa baya cikin haiyacinsa, Ummiy ta zama kamar kurma meta gani ya gigitata haka, kalli yadda Junainah keta fizge-fizge alamun taga mugun abun daya firgitane ya ɗimautata. Rafi'a ga tozarci da cin fuskar da akeyi mana, kallifa babu likitan da yazo ya kula mutanenmu, an barsu ciwukansu nata tsami, sai Nurses keta, hararanmu. Rafi'a ya zanyi in banyi kukaba, ina zansa raina, Ina Yah Giɗi, ina Yah Gaini, Ina Yah Seyo? Rafi'a sun kasarani sun rabani da yan uwana." Kife kanta tayi jikin gadon da Ummiy ke kwance a kai, cikin murya mai cike da rauni tace. "Ummiy kiyi min mgna mana, Ummiy na inasu Ya Giɗi na ina Ya Gaini, ina Ya Lado, ina ya Seyo, meya hanasu zuwa wurinki na tabbar in suna raye cikin ƙishin lfy, dole zan samu ɗaya daga cikinsu a wurinki". Mari matar Arɗo Bani ce wacce ta ɗan dawo haiyacinta ne, ta rumtse idanunta wasu zafafan hawaye ne suka silalo mata, cikin sanyi tace. "Shatu sun tafi kiwo ne, zaki gansu". Jajayen idanunta ta zura mata, Alamun tana son tabbatar da abinda tace matan. Fahimtar hakane yasa ta gyaɗa mata kai alamar eh hakane. Cikin son kontar mata hanlali ne, Rafi'a, tace. "Kinjiko Aysha, to kiyi haƙuri ki nitsu in sha Allah dukkan tsanani yana tare da sauƙi". Kife kanta ta kumayi tana mai sake kuka mai ciwo a zuciya, gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi. Haka dai sukaci gaba da bata baki, wai dan ta samu nitsuwa amman ina, fargabanta sai tsananta yakeyi. Su Bappa kuwa, isarsu Rugar Kikan ya ƙara tada hankali matasansu da suka dawo kiwo da matansu da suka dawo tallan nono wanda sanadin basa nanne yasa suka tsira. Gaba ɗaya Rugar ta birkice ta kiɗime. Hankali dattawan nan yayi masifar tashi, ganin duk an karkashe musu, mafiya yawan matansu yaransu da jikokinsu. Especially Alhaji Haro, da iya cikin gidansa kawai saida aka samu gawar mutun goma sha uku. Koda aka jera masa gawakin suma yayi. Sai ga Tsoffin nan suna kuka cur-cur da hawayensu, gwanin ban tausayi. Ganin yamma na rufawane yasa, Dattawan maƙotansu, mazansu suka fara wonke gawakin maza kamar yadda addininmu ya koyar da mu. Mata kuma sukayiwa mata wonka, Kana suka sallaci Gawarwakin da a ƙalla sun kai mutun Settin da uku 63. Kana suka rinƙa binnesu da taimakon Hausawa musulman cikin Numan da maƙotansu fulani. Gaba ɗaya garin yayi tsit ya koma tamkar kufayi. Sauran rayayyun sunyi Kuka har muryoyinsu. Sun disashe. A cikin Genaral Hospital Numan kuwa. Musulmai Hausawa da Fulani, sune suka rinƙa kawai Fulanin Rugar Kikan taimakon abinci. Hankalin Aysha ya ƙara tashi ganin, har dare babu wanda yazo. Hakama da gari ya waye. Su Bappa kuwa da Arɗo Bani, Alhaji Haro. Malam Manu, Alhaji Umaru, tashin hankali da kiɗima da firgici da ɓacin ransu ya tsananta, sabida ganin. Duk Hukumar ma sun tafi, Gashi babu wani babba da yazo ya duba halin da suke ciki, sabida ai su basu san da cewar su Waziri sun zo tun jiyan ba. Ransu yayi matuƙar ɓaci, ganin Gwamnatin jihar, da Masarautar jihar, babu wanda ya tako ƙafarsa, yazo ya dubasu ko ya turo wakilinshi. Wato matsalarsu bata shafi kowaba. Wannan abun shine mafarin Fara da baƙar Kaddarar Shatu a tarihin rayuwar ta, domin iyaye da yayun wannan Rugar sun tunzura sun hasala, iya hasala, sun cika fam da tarin baƙin cikin rayuwa, an rigada an taɓo zuciyar Fulani haka yasa zasu iya gayawa kowa mgna dai-dai da abinda yayi musu. A can Saudia kuma, komai na dawowarsu Sheykh ya kammala, cikin kwana uku, domin hankalinshi yayi matuƙar tashi, jin irin kisan gillar da akeyiwa makiyaya, wanda Maimartaba ne, ya gaya mishi komai, ya ƙara da cewa. Yayi maza ya dawofa, don yana jiranshi suje tare yaje ya danni fulanin ya basu hakuri ya kuma taushesu kada su ɗauki mataki da sunan ramuwa ko ɗaukar fansa. Hakane yasa, Sheykh ya uzzurawa Haroon dole ya gama musu komai. A kwanaki ukun. Ranar Jumma'a da azahar jirginsu ya sauƙa, a birnin Shehu Sokoto. Mai Alfarma Sarkin Musulmi yaso. Jikan nashi ya kwana, sai dai ina ya tike dole a lokacin Haroon ya kuma saɓan mota suka fara kita hanyan kawoshi Adamawa. Wanda sai ƙarfe uku da rabi suka isa. Kasamcewar dama basu taso da wuriba. Kasancewar isar dare sukayi babu wanda yasan Sheykh ya dawo. Ƙasar sai Lamiɗo da kuma hadimanshi, uku kacal da sune suka tarbesu. Sai washe gari da. Asuba, sautin muryarsa yana karatun limancin Sallah asuba ne ya shaidawa mutanen masarautar Joɗa dawowanshi. Gaba ɗaya kowa ya cika da mamakin, kana da farin cikin dawowanshi. Duk da kasancewar sa, mai larurar da wasu ke mishi kollo ko kiranshi majanuni, yasan kiyaye lokacin salla dama yinta cikin kushu'i. Wannan shine ya hanashi sallame sallar, da akeyi yana cikin sahu na tara, wanda jin muryar ɗan uwanshi ƙaninshi, ya sashi zubda hawaye masu ɗumi. Ya Jafar kenan. Jalal kuwa dake gefenshi wata irin sassanyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da lumshe kekyawan ƙwayar idanunsa da suke iri ɗaya dana Sheykh, ga kuma bacci daya cikasu, domin daren jiya, Ya Jafar ɗinsu ya hanashi bacci. Jin muryar ɗan uwansu da shi kaɗai ke iya sarrafa babban yayan nasune ya sashi sauƙe, numfashin. Jamil da Affan kuwa, wani irin yalwataccen murmushi ya sake jin muryar ɗan uwansun. Abbansu kuwa, shi dai har yau yana rasa me yakeji a kan ƴaƴan nashi, Especially Sheykh, yana jin zuciyarshi na mishi nauyi duk sanda yaron baya kusa dashi, sai dai kuma in yana kusa dashi sai yaji tamkar bai taɓa wani farin cikiba a rayuwarsa. Ya sani tabbas su abun tausayawa ne, suna buƙatar kulawarshi fiye data kowa a duniya, to amman ya rasa meyasa yake jin kamar baya son kusancisa dasu. Maimartaba kuwa, suna cikin sahun na forko bayan liman, Sai da sauran malaman fada. A cikin gida kuwa, jin sautin zazzaƙar miryarshi yana rere karatun al'ƙur'ani, ya ida fatiha, kana ya ɗaura, Arrahama, daga bisani ya rufe da lakadja'akum, kafin ya tafi zuwa ruku'uh. Haka nan Juwairiyya ta tsinci kanta da zubda wasu zafafan hawaye, masu ƙuna a rai, tabbas ta sani. Kasan cewar Sheykh a masarautar nanne kaɗai yasa, suke a ciki. Ta sani in badon daraja da al'farmarsa ba, da tun tuni, an tabbatar da sunan mijinta mahaukaci. Hannu tasa ta share hawayenta cikin sanyi ta miƙe dan gabatar da sallan asuba, a zahiri tace. "Allah ne gatanmu, kaine GARKUWAR mu, Sheykh in baka nan gidan kanyi mana duhu, ƙasar tanayi mana zafi." Daga nan ta tada kabbara. Ummi Jakadiyarsu kuwa, Tana bayan gida, tana al'wala ta jiyo muryarshi, wani irin murmushi tayi tare da yin mgna a baiyane. "Dan Halak kaƙi ambato, ɗa ɗaya tamkar dubu, maƙiyanka fadawanka, sunyi sake ɗan zaki ya girma, in sha Allah zaka dawo da farin cikin masarautarnan, sunyi sake, sun bar kari tun ran tubani, Muhammad Jabeer bawan Allah". Haka ta fito tana wasu irin kalamai masu wuyar fahimta. A can sashin Hajia Mama kuwa, Wata kekyawar budurwa, ce. Konce kan gado gefen Mama, datake zaune bisa sallaya. jiyo muryashine ya sasu saurin juyowa, suka kalli juna, Cikin tsananin farin ciki da tarin shauƙi budurwar ta diro daga kan gadon gaban Mama ta zauna cikin zaƙuwa tace. "Lah Mama, yaushe ya dawo! Muryar Sheykh Jabeer nake jifa! Mama ko dai dama yana nanne?". Wani irin kallo Mama tayi mata cikin sanyi da murmushi a fuskarta tace. "Batul shine, ya dawo!." Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe cikin tarin shauƙi tace. "Yes Mama, farin cikina ya dawo, kamar yasan, nazo. Alhamdulillah, Mama Allah yana sona, ki gani ina zuwa, na samu baya nan, naji baƙin ciki kamar in mutu jiya kafin inyi bacci, sai gashi Allah ya turo minshi cikin dare ɗaya." Murmushi Mama tayi, tana mai jin mmkin yadda Batul ke masifar son Sheykh har take gaza ɓoyewa. cikin haɗe fuska tace. "To yanzu dai, sai ki tashi kiyi salla, tunda kinji muryar da kikafi so a duniya, kin sauƙo kan gadon, sau nawa ina tadake, sai kiyi miƙa ki kuma konciya". Cikin jin dadi tace, "Wayyo Mama baccinne bai isheniba Allah ko jiya kwana nai ina zulumi, sai 3:44 na asuba na samu bacci." Murmushi Mama tayi kana ta miƙe ta kabbarta sallan. Ita kuwa Batul, miƙewa tayi da sauri ta shige, bathroom tana cewa. "Bari inyi wonka inyi salla, in shiga kitchin yau nida kaina zan mishi breakfast." Tana faɗin haka ta shige ciki. A masallaci kuwa, ana idar da salla kamar koda yaushe, da yawa basu fitaba saida sunata lazumi. Yayinda Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da kuma Sarki Nuruddeen Bubayero, da Habibullah Nuruddeen Bubayero, suka jero, suka fito a jere, domin su kullum ana idar da sallan asuba, suke fitowa su koma cikin masarautar, inda kowa zai wuce Side ɗinsa, Yayi karatun qur'ani da kuma, Dua Azkar, inda har sai rana ta fito, kana suke ɗan maida bacci, to kuma sudayin breakfast sai 11. Suna isowa tsakiyar masallaci, Sheykh yaji an ruggumeshi ta baya, yasan mutun ɗaya ne rak zai mishi haka a cikin masallacin, Ya Jafar ɗinsu. Yana juyowa kuwa yaga shiɗin ne. Ruggumeshi yayi gam-gam Jalal, kuwa ido ya zuba musu, shi kuwa Sheykh hannu yasa shima ya ruggume ɗan uwan nashi. Yayinda ya zubawa Jalal kwayar idanunshi, ya rame sosai, hancinsa ya ƙara fitowa, sai sajenshi daya ƙara yin lib, da uban gashin daya tara, yayi wani kafurin aski. Ramar da Jalal yayi ta daki zuciyarsa sosai baya son ganin ƙannen nashi cikin halin matsala, a hankali ya janye kwayar idanunshi ya maidasu kan Jamil da Affan dake gefen damanshi, Calikan ƙanenneshi kenan ba, sheƙiyancinsu ɗaya, baki suka haɗa wurin cewa. "Sabahul Noor Al'Sheykh". A hankali ya ɗan motsa laɓɓansa, yana mai kallonsu yace. "Sabahul khair ya Uktih". murmushi sukayi, suna mai jin son ɗan uwan nasu, Abbs da Maimartaba kuwa, kai suka ɗan jinjina kana sukayi gaba, Ganin hakane suma suka bisu, a baya, shi kuwa Sheykh hannu yasa ya shafa kan Imran da yanzu ya iso gabanshi cikin sanyi yace. "Hamma Jabeer barka da safiya". jin yana shafa kanshine ya sashi lumshe ido, inama ace yadda Hammanshi ke nuna mishi so haka zai shirya da Mom ɗin shi, yana masifar son ɗan uwanshi baya jin daɗin yadda yake ganin wata iriyar mu'amala tsakanin Mom da yayunshi. Ganin Sheykh yaja hannun Ya Jafar sun tafine yasashi bin bayansu. Ƙofar dake cikin masallacin wacce zata ɓulla cikin masarautarsu sukabi. Suna shiga, kowa yayi sashinsa sabida sun sani ko sunbi Sheykh yanzu ba lokacin mgna bane, karatu zaije yayi. Shi kuwa Sheykh yana riƙe da hannun Ya Jafar ɗinsa suka shiga side ɗinsa, inda ya samu hadimai masu tsaron ƙofar, suna tsaye. Suna shiga, tamtsetsen falon nashi kai tsaye ya nufi wannan babbar kusurwar da zata sadashi da. Big part ɗin shi, Suna shiga suka ɓulla cikin wani mashahurin, falo, wanda yaketa tashin ƙamshi mai masifar sanyi da daɗin shaƙa, a hankali ya zauna bisa kujerar 3 str kana yaja hannun Ya Jafar ɗin suka zauna, tare. A hankali ya juyo kanshi ya zuwa ɗan uwanshi idonu, Karatu yakeyi kamar koda yaushe, yanayi cikin tsantsar lugga da tajwid, kana ga kushu'i, Suratul yaseen yake karanta, bisa alamu kenan ya kusa yayi sauƙa, domin step by step yake bin surorin, in yayi sauƙa sai ya sako daga sama, baya mancewa, kuma baya birkitashi, Wannan rahamar da Allah yayi mishi, duk da anso a maidashi majanuni, sai Allah yayi mishi muwafaƙa da littafinsa maisarki, yazama sihirin yayi mishi tasiri tako ina, amman banda gefen addininshi. Wasu irin hawa masu ƙunu yaji suna tsatstsafo mishi, cikin jijiyoyin kekyawan idanunshi, sabida ganin yadda Ya Jafar ɗinshi ke karatu yana, kuka ya za'ayi ya sama mushi farin ciki a rayuwarsa ta ina, zai san me ke cin zuciyar ɗan uwan nashi. Jin yadda ransa ke ƙuna da tafasa ne, yasashi. Komawa ya jingina bayanshi da jikin kujer, kamar yadda Jafar yake mahaddacin haka shima settin kab tana kanshi, Ido ya lumshe tare da yin bisimilla kana ya fara karu inda ya ɗauko daga forkon suratul. Noor ya farayin ƙasa. Saida sukayi awa ɗaya cur kana, Suka fara Azkar, wanda sai da sukayi 23 minutes suna, jero addu'o'in cikin harshen dake nuni da cikekkiyar jimla ta larabci da lugga. Koda suka shafa, sai ya ɗan kalli ɗan uwanshi dake riƙe da hannunshi gam. Ya lura Ya Jafar na tsoron kada ya kuma tafiya ya barshine, yasan duk sanda yayi doguwar tafiya ya dawo, haka yake liƙe mishi. Hannunshi yasa, ya share mishi hawayenshi kana, ya miƙa tare da jawo hannunshi, yasani yanzu lokacin yin baccinsa ne, Side ɗinsu, ya nufa dashi, ta wata ƴar siririyar hanyar dake tsakanin sashukansu. A babban falon suka samu Juwairiyya. Tana ganinsu, ta miƙe da sauri, fuska ɗauke da murmushi kana ido na tsatsafo da hawaye tace. "Barka da dawowa, Sheykh, Alhamdulillah zamu samu nitsuwar Ya Jafar". Kanshi ya sunkuyar sabida bai son ganin hawayenta, Hannunshi ɗaya yasa yana shafa, kam Mimi data ruggumeshi ta ƙafafunshi, cikin murmushi ta nitsuwa yace. "Mimina anyi sallako?". Cikin sauri ta gyaɗa kanta alamar eh, Shi kuwa kanta ya kuma shafawa tare da cewa. "Kinyiwa Ya Jafar ɗina Addu'o'in Allah ya bashi lfy ko?". Kanta ta kuma gyaɗawa tare da cewa. "Eh nayi mishi". A fakaice ya ɗan kalli Juwairiyya dake rugume da yarsu karamar, cikin sanyi yace. "Kukan bashi da wani amfani, muyi ta mishi addu'a, in sha Allah dukkan tsanani yana tare da sauƙi. Ina roƙon Ubangijina mahaliccina a cikin dukkan Ayyukana, daya aramin rai da lfy, kada ya ɗauki raina ko na ɗaya daga, cikinmu, har sai ya nuna mana lfyar ya Jafar, ya faɗa mana abinda ya maidashi haka a dare ɗaya, nasani shine ɗaya rak yasan meya faru, a dare mai duhu da muni na rayuwarmu". Cikin sanyi tasa tafin hannunta ta share hawayenta. Shi kuwa Sheykh, wucewa yayi da Ya Jafar ɗin har cikin ɗakinshi, bisa gado ya zaunar dashi, kana yacewa Juwairiyya dake biye dasu a baya. "Yasha mgninshi ne?". Miƙo mishi gorar ruwa da magungunan tayi tare da cewa. "Yaƙi sha, dan daren jiya kwana yayi, baiyi bacciba, Jalal nan abin tausayi, ko nanda can bai isa ya fitaba, sai ya bishi, Kullum sai Jalal yayi kuka". Wasu tafasassun hawaye ne suka cika masa ido, A duniya shi baya son yaga ko yaji na miji na kuka, domin shi ya sani, duk abinda kaga yasa na miji kuka to abun ya tsananta musamman maza irin Jalal yasan ba ƙaramin raunine zaisa Jalal zubda hawayeba. Shiyasa, shi kukan mace bai taɓa damunshi ba a zuciyarshi, domin mutane sunce in kaga mace na kuka to kayi dariya kafin ka tambayi meya sata kukan. In kuma kaga namiji na kuka to kaima ka fara kukan kafin ka tambayeshi meya sashi kuka. Shiyasa shi kukan mace, bai shiga ranshi, sabida yanaga mata sun iya kukan munafurci da kukan gulma dana ha'inci da yaudara, shiyasa in yaga mace na kuka haushinta yakeji a ransa. Maganin ya bashi sannan ya kontar dashi kafin ya wuce, ya koma sashinsa. Yana shiga, falon, ya samu, Haroon ma zaune, shida Jakadiyarsu, tana ganinshi ta faɗaɗa fara'arta cikin kula da so mai zurfi tace. "Farin gani, Garkuwa, Sheykh, Limamin Masallacin Moddibo Joɗa Jikan sarki mai hatimin sarauta." Gefen Haroon ya zauna tare da rumtse idonshi cikin nitsuwarshi yace. "Ummi ki bari mana, babu wani sarkifa sai Allah, Ummi nace ki dena min irin waɗannan zantukan masu sa kan ɗan adam girma". Murmushi mai cike da tarin so, sabida ita dai jinshi take tamkar ɗan da raina a cikinta ta kuma haifeshi, Koda yake hakan baya rasa nasaba, da cewar itace jakadiya gareshi tun randa aka haishi bacci kawai ke haɗashi da Mamanshi. Sai dai takanzo inda suke su sashi a tsakiya sunai mishi wasa da kallo mai cike daso." Ganin tayi kasake tana kallonshi ne ya sashi ɗan gyara zama, cikin girmamawa yace. "Ina kwana Ummi, ya su Jalal?". Murmushi ta kumayi tare da cewa. "Lfy lau Alhamdulillah, Jalal ya zama mazaunin gida, tunda ka tafi sabida, duk inda yaje , Jafar zai bishi, sai dai kuma abokanshi masu shigar banza har gida suke biyoshi, wani sa'in kwana kiɗe-kiɗe da rawa sukeyi a sashinsu, suna shan sigari. Wasu lokutan dole, Jamil yake gudowa ya bar musu can yazo wurina yake kwana, ko ya shigo nan wurinka". Kanshi ya ɗan maida baya, a hankali yace. "Ummi Jamil da mata?". Kai ta ɗan kauda kana a hankali tace. "Tafiyar bata sauya zaniba, kwanaki uku da suka wuce wata tazo daga, Kano wai ita ƙawarshi ce, kwananta biyu, a sashin Juwairiyya, da Abbanku ya samu lbrine ya korata". Cikin sanyi yace. "Ummi waya gayawa Abba?". Kai ta jujjuya tare da cewa. "Allahu alamu, yadai ji har yace zai kori Jamil ya bar mishi gidanshi, to da yake Jafar yana wojen ne, sai ya riƙe hannun Jamil yayi ta kuka, hakane yasa ya barshi, Mamanku kuwa kuka tayi- tayi". Wani irin zazzafan numfashi ya fesar kana, ya juyo ya kalli Haroon a hankali ya kuma kalli, Jakadiyarsu, cikin sanyi yace. "Basaji Ummi suna samin tunani a raina, ga wannan kuma shima ƙato dashi, sai ya ruggumi waya yayi ta chatting ko waya Da waccar yar mitsitsiyar yarinya Jannart ɗin. Da asuba nayi ta tadashi yafi sau uku baya tashi, sabida bai bacci da wuriba, gashi ko cikekken jam'i bai samuba". Ido Haroon ya lumshe tare da cewa. "Jiya dai ba chatting ko waya da Jannart bane, ya hanani baccin da yasani makara, Ummi ƙarshen darefa muka iso sabida ya sani dole sai mun taho nan." Murmushi Ummi tayi kana tace. "To Haroona ka kiyaye batun tsaida salla kan lokacin ta, kaji ko?." Hararan Sheykh yayi tare da cewa. "To Ummi". Ita kuwa Jakadiyarsu cikin muryar kula tace. "Haroona yaushene bikin naku kam?". Kanshi ya ɗan shafa kana yace. "Uhum Ummi saura watanni bakwai in Allah ya yarda, Ni dai zanyi aure in bar babban tuzurun". Bai kulashiba saima tashi yayi ya nufi bedroom. Ita kuwa Jakadiyarsu cikin yin ƙasa da murya tace. "Yauwa ya dai-dai ta da Jazrah ko?". Baki ya ɗan turo tare da cewa. "Uhum Ummi gudowafa yayi, kuma wlh in ba dagewa kukayiba, wannan bauɗeɗɗen ɗan naku, ustazu bazaiyi aureba, mutun duk yadda akayi dashi sai ya kauce". Kai ta ɗan juya ta kalli ƙofar ɗakin daya shigan, cikin yin ƙasa da murya tace. "Uhum ga zahiri ko mgnar aure akayi sai ya bar wurin." Haka sukayi ta hira da yake akwai sabo tsakaninta dashi. A sashin Hajia Mama kuwa, ita da kanta da kuma, Batul suka shiga kitchin sai kuma yardaddun hadimanta mutun biyu. Breakfast mai kyau suka, haɗawa Sheykh. Yayinda Aunty Juwairiyya ma ta shiga kitchin da kanta, ta haɗa mishi breakfast. Jakadiyarsu kuwa da Jamil da Jalal da Affan Haroon suna falon sunata hirarsu. A tare hadiman Mama dana Juwairiyya suka kawo, abin kari. Suna fita ba da ɗewa, hadiman Gimbiya Aminatu kakarsu kenan. Suka shigo suma da abun kari. Suka jera komai kan babban dinning table dake dinning area'n dake falon. Bayan sun fitane. Suna cikin hira, sarƙin ƙofa, ya shigo, ya shaida musu, ga saƙo an kuma kawowa. Jamil ne ya bada daman a shigo. Nan ya juya ya fita, jim kaɗan, aka turo ƙofar. Cikin mamaki suka zuwa ƙofar ido. Ganin M....! *Wannan shafin nakine ke ɗaya MRS SARDAUNA, Sheykh yana godiya da soyayyarki gareshi. Domin duk masoyanshi bayanki sunka biyo* By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 14 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘 *Daga gobe ne, FREE PAGE zai ƙare, in da zan saki page 15-16 daga su kuma in kin sake ganin littafin GARKUWA a woje ba cikin groups ɗin da na buɗe nasa wanda suka biya ba, To na satane, na waɗanda basu san darajar iyayenka da girman Allah da Manzonsa suka fitar ne, to ke kuwa in kin san darajan iyayenki da girman Allah da Manzonsa, kada ki karanta na sata, akwai group ɗin ɗari uku kacal ban tsauwala ba dan nasan halin TLC da muke ciki a ƙasar nan ga mai wadata wacce take da dama taga zata iya biyan na Special Group 1k ne rak. Zaki turo ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276, kuma ƴan 300 zaku iya turowa ta ac na ɗin, in kuma baki da dama to turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number dai 09097853276. Dan Allah da Manzonsa in kin san zaki fitarmin da littafi biyoni PC ki gaya min wlh zan baki kuɗinki in fiddaki group salum-alum, ina kuma jin san saya zakiyi ki fidda na roƙeki da Allah da Manzonsa wanda bayansu babu wani kada ki saya ki riƙe kudinki ki barni in riƙe littafina🤗* FREE PAGE, daga gobe dai zasu ƙare ki biya kuɗin ki in kinada niyan saya. Ganin Mom ce, yasa fuskokinsu ya baiyana abinda ke cikin zuƙatansu. Cikin ƙasaita, Mom ke tafiya, hadimanta biyu na biye da ita da manyan kuloli na al'farma. Jakadiyarsu ce tayi murmushi mai kama da yaƙe, tare da rusunar da kai, cikin girmamawa tace. "Barka da shigowa, Gimbiyar ahlin masarautar Joɗa. Cikin isa da ƙasaita ta gyaɗa mata kai bayan ta zauna, gefen Jamil dake ruggume da waya kamar, abin masifa, Kanta ta ɗan juyo ta kalli Jalal daya haɗe fuska, Juwairiyya yace ta ɗan gyara zamanta tare da cewa. "Barka da safiya Mom". Murmushi mai wuyar fassarawa tayi, tare da taɓe baki, a gyatsine tace. "Barka dai". Sai ta kuma juya ta kalli inda Jakadiyarsu ke zaune, cikin isa tace. "GARKUWAN YA FITANE?". A daƙile Jalal yace. "Yana ciki kuma hutawa yakeyi". Ko inda yake bata kallaba tace. "Jakadiya ina buƙatar ganinshi, yanzu". Cikin biyeyyarta tace. "Ranki ya daɗe, in zaton bacci yakeyi". A taƙaice tace. "A tadoshi". Haroon dai ido ya zuba musu yana ganin ikon Allah, kowa ji da kai da ƙasaita. Juwairiyya ce ta ɗan kalli Haroon ɗin cikin sanyi tace. "Ukhti, shiga ka sanar mishi". To kawai yace, kana ya miƙe ya shiga bedroom ɗin, da Sheykh ya shiga mituna ashirin baya, kasake yayi a bakin kofar ganin babu kowa a cikin bedroom ɗin. A hankali ya tako ya shiga ciki, bakin ƙofar bathroom ya ɗan matso, kunnenshi ya kasa wai a lissafinshi ko zaiji mitsin ruwa. Shiru babu kowa a ɗakin da kuma bathroom ɗin. Ko ina yayi tsit sai wani fitinenne sanyi daya cika ɗakin, wanda sai sautin A/C dake busawa shuuuuu a hankali. Waige-waige yayi ganin babushi babu, motsinshi ne, ya sashi ɗan ɗaga murya yace. "Jabeer! Jabeer!! Jabeer!!!". Jin shirune yasashi sa hannunshin ya ɗan ƙonƙosa ƙofar bathroom, still shiru. Hakane yasa ya ɗan tura ƙofar, wayam baya ciki. Ganin hakane ya sashi juyawa, shima ɗin cikin takun ƙasaitar ya fito gefen Jalal ya zauna tare da kallon Juwairiyya,kana yace. "Baya cikifa". Wani irin kallo Mom tayi mishi, wanda yake nuna abinda ke bakinta, cikin ɗan sakin fuska yace. "Allah kuwa Mom baya ciki". Kanta ta gyaɗa tare da yunƙura ta tashi tsaye. Kana a hankali tace. "Uhummm". Sai kuma ta juya ta kama hanyar fita, hadimanta na biye da ita a baya. Har yaje bakin ƙofa ta juyo tare da cewa, Ga breakfast ɗin Garkuwa". Haroon ne yayi godiya kana ta juya ta fita. Cikin mmki Haroon ya kalli Jamil tare da cewa. "Jamil baya cikifa". Murmushi Juwairiyya tayi tare da cewa. "Kun dai haɗa baki, kunƙi ya fito, ya gaisa da Mamanshi". Jalal ne ya ƙara tsuke fuskarsa tare da cewa. "Mamarshi ko makirarshi". Jakadiyarsu ta ɗan gyara zama tare da cewa. "Uhummm, sanin halin mutum sai Allah". Sai kuma ta kalli Haroon tace. "Haroona kace mishi yazo yayi karin kumallo, kace mishi daga sashin Gimbiya Aminatu ce, ga kuma na Juwairiyya". Cikin jaddawa yace. "Allah kuwa Ummi baya cikifa". Da mamaki a fuskokinsu suka ɗan kalleshi, Jamil ne yace. "Bai fita bafa". Juwairiyya ce, ta amshi zancen da cewa. "To kuma dai bai biyo nanba, tunda ya shiga bai fitoba". Shi dai Haroon Ido ya zuba musu, ganin kamar basu yarda Jabeer baya cikiba. Kuwa hakanne, saida Jamil yaje ya duba babu shi a ciki babu alamarsa. Cikin tarin mamaki ya sanar musu, baya nan ɗinfa. Jalal ne ya ɗan kauda tunaninsu da cewa. "To kunata surutu, ta ina zakuga sanda ya fita, kai Jamil hankalinka duk na kan waya ina zaka ganshi." Cikin kula Jakadiyarsu tace. "Kaga fitarsane?". Baki ya ɗan taɓe tare da cewa. "Ni ban ganiba, na dai san shi ba kuɗi bane bare ya ɓata, ku jira zaku ganshi". Da haka sukayi amanna dan a zatonsu yaga fitarshi kawai bauɗewarshi ne yasa bazai sanar musuba. A can cikin fadar Masarautar Joɗa kuwa, falon sashin mai martaba Lamiɗo, cike yake da ƴaƴanshi maza, ziryan, wanda kullum iwar hakan suke haɗuwa domin gaidashi kana su gaisa da juna, ya tambayi lfyar ko wanne ɗanshi da ahlinshin. To yau ta kasance jumma'atu babbar rana, wanda kuma, duk safiyar jumma'a. Cikin wani ɗakin gadon sarautarsu, yakan shiga shida kanshi, yake tsabtace wannan ɗakin duk ran jumma'ar duniya, a tarihi da tsarin masarautarsun babu wanda zai shiga ɗakin sai wanda yake, matsayin Sarki. Babu wani wanda ya taɓa shiga wannan ɗakin, sai wanda yake sarki. Suna cike a falon a ƙalla sun kai su bakwai dukansu. Manyan mutanene masu tarin wadatar duniya, jinin sarauta na yawo a jikinsu. Suna zaune kamar yadda kullum suke zama, suna ɗan hira a tsakaninsu. Habibullah ne, zaune a can tsakiyarsu a matsayinsa na shine babban ɗa ga Lamiɗo, hannunsa riƙe da. Carɓi, sai gefen damansa, Alhaji Sani, sai kuma Barrister Kamal, kana sai. Dr Aliyu, kana sai, Badamasi, Nasiru, basiru. Dr Aliyu ne, ke gefen daman Habibullah, bisa alamu duk mgna yakeyi mishi a kan lfyarsa. Bappa Nasiru, wanda shine, yake bin Habibullah a girma sai dai uwarsu ba ɗaya ba, gyara zama yayi tare da jan dogon tsakin da yasa duk suka meda idonsu kanshi. Cikin kula Habibullah yace. "Lfy dai Nasiru?." Wani irin kallo mara daɗin gani ya watsa mishi tare da cewa. "Yes lfy lau, sai dai mu nan duk muna da aiki, ba zauna gari banza, irinka bane, kowa yanada hidimar yi gashi har yanzu, Lamiɗo bai fitoba". Murmushi yayi ba tare da yaji ciwon abinda ya gaya mishibs, a hankali yace. "To Nasiru, ai duk saurinka kayi haƙuri dai ya fito, kaga lfyarsa yaga taka, tunda shi bai gajiya da bincikar lfyarmuba, ai muku wa bazamu gazaba. Domin abune mai wucewa". Wani irin kallo mai cike da tsana da tsoggoma ya mishi tare da kauda kanshi. Basiru ne yayi dariya alamar jin daɗin kallon da ɗan uwanshi yayiwa Babban yayansu da suke ƴan uba. shi kuwa Habibullah Abbansu Sheykh, kauda kai yayi kar bai ganiba. Kusan a tare suka miƙe gaba ɗayansu, tare da haɗa baki wurin cewa. "Barka da fitowa, Mai alfarma Lamiɗon Joɗa." Murmushi yayi tare da kallon ƴaƴan nashi ɗaya bayan ɗaya, a hankali ya ƙarasa fitowa, hannunshi sarƙafe da hannun Jabeer. Wanda baiyanarsa yasa, gaba ɗaya suka zazzaro ido. Cikin tarin mamaki, al'ajabi, firgici, kaɗuwa, gamida tsayawar idanunsu kan ɗan babban yayan nasu, cikin wani irin daskarewa, suka juyo suka fuskaci, junansu wannan ya kalli Wannan wannan ya kalli wancan. Murya a daburce, Nasiru ya nuna Jabeer dake tsaye, cikin wani masifeffen al'kyabbar mai masifar kyau da zadan gaske, cikin ƙafewan yawun baki yace. "Ka gafarceni Lamiɗo, me idonuna ke gani, daga ina ka fito da Jabeer? Me kayi dashi? Meye ma'anar hakan? Mu duk ƴaƴan ka bamu kai ka shiga damu ba sai shi?". Cikin tsare fuska irin ta manyan sarakai dattawan, ya zubawa, Nasiru idanu, wanda dole tasa ya hadiye rahowar maganar tasa. Habibullah kuwa, wani irin rawa da karkarwa jikinsa ya fara. Wani masifeffen tsoro da fargabane ya rufeshi akan ɗan nashi, koda dai baya jinsu a ranshi kamar sauran ƴaƴanshi, hakan bai hanashi tsoro da fargabar abinda zai cutar dasuba. Barrister Kamal kuwa. Wata irinyar madifeffiyar zuface ta keto mishi daga saman kanshi har tsakiyar tafin sawunshi. Lokaci ɗaya yaji wani irin abu ya saki ƙahon zuciyarshi, Maƙoƙoronshi ya bushe ƙamas, duhun daya rufe mishi idone yasashi komawa zaune. Dr Aliyu kuwa, wani irin murmushi yakeyi yana kallon ɗan babban wansun. Shi kuwa Lamiɗo hannun Jabeer ya kuma ja, wanda yake motsa laɓɓansa a hankali yana tasbihi kamar yadda ya saba. Zama yayi kujerarsa ta musamman, kana Jabeer kuwa ya zauna gabanshi. Cikin tattaro yawun baki Barrister Kamal yace. "Barka da safiya. Sarkin Joɗo. Sai ya kuma danne tarin baƙin cikinsa yayi mishi rumfa da fuskarsa ta zahiri kana ya kalli Jabeer da ya ɗan sunkuyar da kanshi tare da gaidashi. Cikin dakiya yace. "Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Joɗa. Yaushe a gari". Kanshi ya ɗan kauda tare da cewa. "Daren jiya". Nasiru ne ya katsesu da cewa. "Lamiɗo, ɗakin sarautar sarakunan Joɗa kuma ya zama kowa zai iya shigane?". Bai kulashi ba, har saida suka gaisa gaba ɗayansu, kana, ya fuskancesu, duka cikin hikima da, kaifin basira yace. "Rigar sarautarsu ta GARKUWAN FULANI, na bashi. Sabida akwai tafiyar gaggawa da zamuyi zuwa, Rugar Bani, da ƙaɓilun wurin suka far musu da kisa." Kai suka gyaɗa alamun gamsuwa, kana duk, ya sallamesu. Duk suka fita kowa da abinda ke cikin ransa, da zuciyarsa. Bayan fitansu ne ya kalli Jabeer cikin, tarin kula yace. "Kaje ka shirya kazo mu tafi". Kanshi ya kuma rusunarwa cikin ladab yace. "Allah saine, mu bari sai bayan sallan, jumma'a ina munyi jam'i anan, mu tafi gudun kada muje bamu dawoba kafin lokacin sallan." Gyara zamanshi yayi tare da gyaɗa kai kana yace. "Haƙƙun kayi, gsky to mu bari sai an sauƙo mutafi, in yaso muyi sallan la'asar a can." Da Wannan shawarar suka bari sai bayan sallan, azahar ɗin su tafi. Sun daɗe suna tattaunawa kafin, ya sallameshi ya tafi, shi kuma ya nufi fada. A falonshi kuwa, yana shigowa duk suka zuba mishi ido, da mamaki cikin zaƙuwa Jamil yace. "Hamma Jabeer wai ta ina kabi ka fitane? Duk bamuga fitankaba". Kanshi ya mirgina, alamun gajiya, kana a fakaice ya kallesu baki ɗayansu, tare da cewa. "Sama". Murmushi sukayi baki ɗayansu, sabida fahimtar amsar daya basu, na nuni basuga sanda ya fita bane. Bisa wata tattausar doguwar kujera ya zauna. Kana ya fuskanci ƙannen nashi da kyau. Jalal ne ya ɗan sunkuyar da kanshi, ganin yadda Hammanshi ya zuba mishi ido, Jamil kuwa, kanshi ya ɗan rausayar tare da katse wayar da yakeyi, ya fuskanci ɗan uwan nasu, Cikin yin fiki-fiki da idanu yace. "Barka da safiya Hamma Jabeer, ya hanya?". Alhamdulillah, yace mushi a taƙaice, kana ya ɗan gyara, hiramin dake bisa kafaɗunshi. Jalal ne ya ɗanyi baya tare da lumshe idonshi cikin saisaita muryar da indai da Hammanshi zaiyi mgna to sai ya nitsu ya gyarata, Domin yakanji yanada rauni duk sanda yake gaban Hammanshi, yana ji tamkar a gaban mahaifinshi yake. Cikin sanyi yace. "Ina kwana? Hamma Jabeer, ka dawo lfy t yasu Sitti?". Ido ya ɗan kauda kana yace . "Alhamdulillah, Jalal ya jikin Ya Jafar?". Kanshi ya ɗan jujjuya kana a hankali yace. "Kalmace dai ta musulmi, koda cuta babu sauƙi ya zame mana ɗa'a muce, da sauƙin, amman a zahirin gsky ciwon Ya Jafar babu sauƙin, komai yaci tura, abubuwan sun yawaita". Ya ƙarishe mgnar tamkar zaiyi kuka, ganin hakane yasa Jabeer ɗan kauda kanshi, Allah yasani, baya son ganin ƙunci ko baƙinci ko wata damu a fuskarsu, sabida ya ɗauka cewa Allah ya barshi da rai da lfy ne a tsakiyarsu, su da akewa kallon marasa lfy ya zame musu Garkuwa. A hankali ya miƙe cikin kula ya kallesu, murya a ɗan macce yace. "Kuzu kuci abinci". To sukace baki ɗayansu, kana duk suka nufi, dinning table ɗin. Wanda yake cike da abinci kala-kala. Juwairiyya ce ta sakawa kowa abinda yake buƙatar ci, Shi kuwa Sheykh sai jujjuya mata kai yayi alamar babu abinda zaici. Ya dai zauna yana kallonsu, Ummi kuwa, tana gefenshi. Kanshi ya ɗan juya ya kalli Haroon dake shan tea kuma still wayarshi na kunne yana, mgna da Jannart, ɗan gajeren tsaki Jabeer ya ja, jin Haroon na cewa. "Ina yin breakfast ne, ke me kikeyi? Bacci? Ko kwaliya? Ko kallo?". hannunshi yasa ya zare wayar kana ya katse kiran tare da mishi nuni yaci abinci kafin ya tsaya yin waya. Cikin haɗe fuska Haroon yace. "Ka ganka ko? Ni shiyasa har tsoron zama kusa da kai nakeyi, sabida tsarabe-tsarabenka nada yawa, yanzu zaka fara jawowa mutum aya da hadisai, kana wani, abu kaza ba laduban kaza bane, in an jika kayi doguwar mgn to an sosa maka wuri biyu, ko ayar Allah, ko wannan mulkin da kake cewa an liƙa maka jaraba". Jamil ne yayi ƴar dariya tare da cewa. "Mulkin nema jaraba a wurin shi ko? Gacan wasu na neman, zaunece sabida Garkuwan da aka bashi". Jalal ne ya ɗan tsuke fuskarsa tare da cewa. "Ni kaina Wannan GARKUWAN bai wani burgeniba, sabida baya cikin, masu iya gadar mulki, sabida shi ai ba jikan sarki ta wurin ƴa mace bane, jikanshi nefa ta wurin ɗa namiji ta yaya zai bashi Garkuwa?". Ummi ce taja wani dogon ajiyan zuciya tare da cewa. "Uhummm ta yaro kyau take bata ƙarko, to kai Jalaluddin, yanzu Jafar da aka bashi Galadima, wani hali yake ciki? Tun randa aka naɗa masa sarautar me mutane suke kallon ya zama? Dukfa duniya kallon majanun akeyiwa Jafar". Juwairiyya ce ta ɗan rumtse idonta tare da cewa. "Ni banyi fataba, banso a sake bawa Kowa wani mulkin da nasan baza'a barku lfy ba, shi Lamiɗo, meyasa ko ƴaƴan nashi babu wanda ya bawa mulkin komai?". Da sauri Ummi tace. "Sabida muddin yace zai basu sarautu, to wasu zasu hallaka wasu". Cikin daƙilewa Jalal yace. "Ok shine sai ya zaɓi ƴan ɗakinmu a matakan zakarorin gwajin dafi? Ya bawa Ya Jafar Galadima, yaga yadda aka medashi dare ɗaya, da rashi da bazamu samu madadinshiba a duniya, an cire hankalin mahaifinmu a kanmu, sannan ya kuma bawa Hamma Jabeer wani mulkin, salon a sabautashi kenan, nest target nasu kuna, wato a kanshi ne?". Shiru sukayi jin Jabeer na cewa. "Azzannu zambu walau kana haƙƙun, na haneku da irin waɗanan zantukan, babu wanda ya isa, ya cutar da wani sai Allah, domin shine mai rayawa, kuma mai kashewa, mai badawa, mai hanawa, mai cuta mai waraka. Ummi har kema, ya zakiyi ki zauna kina gaya musu hakan, to waye zai cutar damu, acikin ahlinmu, daga ƙannen mahaifinmu fa, sai ƙannen kakanmu, sai matasansu da jikokinsu, sai kuma ƴan uwanmu, dan Allah ku bar munanawa mutane zato." Juwairiyya ce ta ɗan girgiza kai. Shi kuwa Jabeer, cikin bada umarni yace. "Juwairiyya jeki duba Ya Jafar, nasan zuwa yanzu ya tashi daga baccin." To tace, kana ta miƙe ta nufi tsakiyar falon. da sauri ta tsaya tare da ɗan raɓawa gefe, sabida ganin Gimbiya Saudatu, na tsakiyar falon. Da sauri ta ɗan rusuna tare da cewa, "Barka da fitowa Gimbiya Saudatu". Zama tayi bisa kujerar da Jabeer ke zama, ɗaura kafarta tayi ɗaya kan ɗaya. Hadimanta, biyu ne suka zauna gefe da gefenta. Fuskarta babu wata alamar annuri, sai tsantsar tijara, cikin isa da ƙasaita tace. "Kai Jabeer!." Ido Jakadiyarsu ta zazzaro cikin firgici da tsoro ta kalli Jabeer da a take fuskarshi ta sauya launi, cikin rawan jiki da tsoro tayi ƙasa da murya tare da cewa. "Jabeer ka amsa, Gimbiya Saudatu ce, da kanta." Jalal ne da Jamil suka kalli juna, kana suka maida idonsu, kan Hamman nasu, da ya lumshe idonshi ya koma ya jingina tamkar badashi akeyi ba, kamar daga sama suka jiyo muryar Gimbiya Saudatu tana ratsa kunnuwansu. "Kai Jabeer, ka fito kazo nan, ina nemanka". Still bai buɗe idanunshi bama, bare ya amsa ko yunƙurin tashi, sai dai laɓɓan bakinshi da suke motsawa yana maimaita sunan Allah a zuciyarshi da harshenshi. Zuwa yanzu Gimbiya Saudatu tayi masifar kufula, cikin wani irin mugun kallo ta kalli Juwairiyya da jikinta ke baiyana tashin hankali ta, cikin isa da ƙasaita tace. "Ke maza wuce, kije tun wancan karen larabawan da suka turo ahlin masarautun Fulɓe, dan samun damar maida masarautun a hannunsu, kice mishi yazo dan kan uwarshi". Da ƙarfi Jabeer ya rumtse idanunshi, wani irin bugawa zuciyarshi ta farayi a saba'in. Ita kuwa Juwairiyya kasa motsawa tayi daga inda take tsayen. Ummi kuwa cikin firgici, ta kalli Jalal daya miƙe tsaye tamkar wanda aka tsabura. Jiki na rawa ya ture kujerarshi, zaiyi baya ya fita ya nufi inda taken. da sauri ya juyo cikin tarin zafin rai jin an riƙe mishi, hannunshi. ganin Hamma Jabeer ɗinsune ya damƙi hannunshi ne ya sashi, taune lips ɗinshi da masifan karfi. Jamil kuwa ido ya zubawa Hamman nasu yana ganin yadda jikinshi ke karkarwa, kowa ya sani duk duniya babu abinda yake saurin harzuƙa Sheykh sama da a zagar mishi iyaye Especially uwa! Haroon kuwa zuru yayi da idanu yana kallon ikon Allah. Ummi kuwa cikin rawan murya da tsoro da firgici ta kallesu murya na rawa, tace. "Dan Allah Jabeer, kaje, tashi muje ka amsa kiranta dan Allah badon niba, dan darajar Manzon Allah". Ta ƙarishe mgnar tana ƙoƙarin zubewa kan guiwowinta, Jin kalaman da tayi mishi da gane nufinta na rusuna mushine ya sashi saurin miƙewa tsaye. da sauri suma duk suka miƙe tsaye. Gyara kekyawar al'kyabbar jikinshi yayi wacce take ta limamaice bawai ta sarautaba, jam hiraminshi yayi ya rufe sajenshi da kyau ya rage iya shatin fuskarshi dan yasan dole tazo da hadimanta mata. Jalal ne ya tsaya gefen damanshi, kana Jamil a gefen hagunshi, Haroon kuwa na bayanshi, Jakadiyarsu kuwa tana gaba tanayi musu jagora. A haka suka fara taki kan stpes ɗin sauƙowa daga kan dinning area ɗin, wani irin taku sukeyi mai cike da ƙasaita da kwarjini. Yana tsakiyarsu tamkar sarki da fadawanshi. A haka suka nufo tsakiyar babban falon da ya kai wasu faluka huɗu. Ita kuwa Gimbiya Saudatu, wani irin hushi da numfarfashi takeyi tamkar wacce tayi gudun fanfalaƙi, cikin izaya da isa, take zaune bisa mazauninshi. Tare da cewa. "Ina karen Larabawan yakene, Dan kan uwark?". Bata ƙarishe mgnar tataba, sabida ganinsu sun nufota gadan-gadan, wani irin kwarjini yayi mata, wanda yasa ta haɗiye ragowar mgnar tata, shi kuwa Sheykh Jabeer, cikin wani irin taku naƙasaita suka karaso tsakiyar falon. Ido ta zuba musu kana cikin tijara tace. "Me zaka zo ka tsaya min a ka, ka zauna inada mgna da kai". Cikin wata iriyar dakekkiyar murya mai cike da ƙasaita yace. "Ai ba sai kince na zaunaba, dama dole in zauna, tunda ni ba bawanki bane, bazan tsaya a kankiba, sabida Ni ba dogari bane". Ido ta zazzaro woje alamun tarin mamaki, ajiyan zuciya ta sauke a ranta tace. "Ehe mai jajayen kunnuwa, uwarka zanci". Shi kuwa Jabeer, wani irin taku yayi mai cike da izza, bisa kujerar dake fuskantar wacce take zaune a kai ya zauna, da sauri ta tsareshi da ido tare da cewa. "Kai ina sama kana sama, haka aka koya maka irin tasu tarbiyar ta larabawan kenan". Ƙafarshi ɗaya ya ɗaura ya ɗaurs kan ɗaya, kana ya gyara zamanshi da kyau, cikin muryar ƙasaita yace. "Ki dena yimin ihu a kai, nan ba fadar masarautar waɗancan surutattun bane, nan fadace mai daraja masarautar Joɗa ce, kiyi hattara da lafuzanki, na baki mituna biyar daga cikin wunin yau gaya min damuwarki in baki mgninta". Jakadiya dai gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi. Haroon kuwa, bayan kujerar da Jabeer ke zaune ya tsaya, Jalal kuma yana gefenshi hakama Jamil. Juwairiyya kuwa, tana inda take tun ɗazu. Wani irin mugun kallo ta watsa musu, kana cikin zafi da azalzalar zuciya da jin tarin tsanarsu ta gyara zama tare da cewa. "Naji yau an ganka ka fito ɗakin sirri na masarautar Joɗa kaida mai martaba Lamiɗo, me hakan yake nufi?". Ba tare da ta gama rufe bakintaba yace mata. "Ina ɗakin sirrin masarautar Joɗa akace miki na fito, ba ɗakin sirrin masarautar kuba na fito?". Cikin kufula tace. "Itama ɗin wannan masarautar ai tamuce, tunda ƴaƴanane manyan jikokin sarkin Nuruddeen, kuma babansune Galadima, shine kuka kasheshi, aka bawa wancan majanunin yayan naki mulkin Galadiman, to yanzuma kuma ɗan tsurfa da tsiri uwar me kukayi a cikin ɗakin sirrin? Me ya gaya maka? Me kuke shiryawa?". Still harshenta ma bai gama komawa zaune ba ya jefa mata amsa. "Ɗakin sirri mgnar sirri, tunda shi jakin daya kai miki rahoton, bai sanar miki me muka tattaunaba, Ni sai in miki jagora zuwa wurin Lamiɗo ki samu ki ganshi yanzu sai ki tambayeshi me yace min me mukayi, tunda kinsan in bani nai miki isoba sai ki kai sati nan gaba baki samu damar ganinshi ba". Ya ƙarishe mgnar yana tsareta da fitinennun idanunshi wanda babu tsoro a cikinsu. Cikin kufula tace. "Ba girin-girin ba tayi mai, ta yaro kyau take bata ƙarko". Amsa ya kuma bata. "Surkin nakine yaron? Mutumin daya haifa miki miji, kika aura har kika haifi yayan da kike son su gajeshi, shine yaron? To asheko masarautar duk yarace, ke mulkarta, tunda nasan ko tsohonki bai kai, Lamiɗo ba". Ohoho ina wuta ta faɗa ciki, cikin kausasa murya tace. "Ina mai umurtarka da kada ka kuskura ka amshi wani mulkin daya wuce Garkuwa". Cikin taɓe fuska yace. "Anƙi bin umarnin naki". Wani irin Murmushi mai baiyana jin daɗi da tarin Mamaki Haroon da Jamil sukayi. Jalal da kanshi yau Hamma Jabeer ɗinsu ya shayar dashi tarin mamaki, ashe shi nashi ƙarfin halin da ake gani wasane, ga Jarumin da jarumtarsa ta girgiza, zuciyar Jalal. Dan harga Allah shi dai ya sani bazai taɓa iya yiwa Gimbiya Saudatu abinda Haammanshi keyi mata yanzuba, ashe dama haka yake, da kafiya da bada amsa tun kafin ta huta. Muryar Gimbiya Saudatu ce ta kuma katse mishi tunani. "Yanzu bakinka ke iya furta ka haka,, yaro zakaci kan uwark".. da sauri ta zaro mishi ido jin yace mata. "Kul kada ki ƙarasa, in kuwa kikayi gangancin ƙarasawa, zan". Katseshi tayi da cewa. "Zakayi me? Gaya min isshe ɗan fitsara me zakayi". Jalal ne ya amshi zancen da cewa. "Zan datse miki harshe, kika kuma zagar mana uwa". Cikin tsananin tsana ta watsawa Jalal harara tare da cewa. "Zaka aikata! Babu musu! Menene ɗan giya bazai iya yiba, menene, ɗan iska ɗan daba bazaiyiba, banza ɗan sara suka, gwada datse min harshen ka gani, in akwai wanda zai rage da harshe a zuriyar uwarku". Jabeer ne ya ɗan taune leɓenshi tare da kaɗa mata yatsa kana yace. "Kulfa, ki raba kanki da zagin mace mai daraja". Cikin isa da ƙasaita tayi wani irin dariya, kana ta miƙe tsaye, gabansu ta ɗan matso kana cikin izaya tace. "Eh daraja ko? Uhummm lallai kam, aifa sai dai mace mai daraja." Sai kuma ta ɗan ja da baya kana tace. "Mace mai daraja ko mai zunubi, ai dai kun fara ganin sakayyar Allah tun a duniya, waya san metayiwa ubangiji, y...." Juwairiyya ce, tasaki wani irin ƙara da yasa duk sukayi shiru. Ita kuwa ta faɗi kasa a sume alamun makaranta sun dawo. Ganin haka yasa Jakadiyarsu tayi kanta da gudu. Ita kuwa Gimbiya Saudatu murmushin jin daɗi tayi tare da cewa. "Haka dai. Duk a haka zaku ƙare, mulki kuwa sai dai ku ga anayi, GARKUWAN da aka bakanma, zakaga me zai sameka dashi". Tana faɗin haka ta juya ta nufi hanyar fita Hadimanta na biye da ita a baya. Shi kuwa Sheykh Jabeer murya ya ɗan ɗaga a hankali yadda zata iya jinshi yace. "Babu abinda zai sameni face dama Allah ya ƙaddara zai sameni, domin baki isa ki cutar daniba". Cikin harshen fillanci tace. "A laran ai, zaka gani ai". Bai kulataba. Ita kuma fita tayi. Jalal da Jamil kuwa, zama sukayi gefenshi, suna mai bin kofar fita da ido. Haroon kuwa cikin rudu da ɗaure war kai yake mgnar zuci. shin wai wannan wacce iriyar fitinenneyar masarautace, mai cike da tsarƙaƙiya, yanzuma dama a irin wannan yanayin Jabeer ke rayuwa da ƙannenshi da yayanshi da mahaifanshi. To meyasa, bazasu bar musu masarautarba, tunda shi Jabeer bama son wannan mulke-mulken yakeba. Sassanyan zazzaƙar Muryar Sheykh Jabeer ne ta katse mushi nazari, jin yana rere karatun Alqur'ani cikin nitsuwa yake, karanta fatiha. Bayan ya kai ƙarshenta ya kuma yi bisimilla, ya fara Suratul Baqra, wanda yakeyi da ɗan ƙarfi, tare da fuskantar inda Juwairiyya ke kwance, Yanayin karatun cike da taƙawa da kekyawan tajwid, shiyasa in ya fidda wani harafin kamarsu Khah sai kaji har ƙasan wurin yana amsa amon sautin." A hankali Juwairiyya ta fara buɗe idanunta, tana mai bin karatun da takejin, Cikin sauƙe ajiyan zuciya Jakadiyarsu tace. "Alhamdulillah Jabeer ta farfaɗo". Ta faɗi hakane sabida tasan duk sansa Juwairiyya ta faɗin in dai zai mata Rugyag rufe idonshi yakeyi. Jin Jakadiyarsu tace ta farfaɗo ne, tasashi, yin hamandala tare da cewa, Jakadiyarsu ta meda Juwairiyya Side ɗin ta, kana ya kalli Jalal tare da cewa. "Jalaluddin kaje, ka kula da Ya Jafar, ka bashi abinci kana ka shirya shi, shirin zuwa sallan jumma'a kaima kaje ka shirya." To sukace kana duk suka fita. har sunje bakin ƙofar fira yace. "Jalaluddin kasa kayan mutunci". Cikin sanyi yace. "To". Sannan suka fita. Kanshi ya ɗan juya ya kalli, Jamil, tare da cewa. "Ka gyara mana bedroom." Yana jin haka ya miƙe ya nufi bedroom ɗin. Shi kuwa Haroon ido ya zuwa Jabeer, sabida gaba ɗaya muryarshi ta tabbatar musu, yana cikin tsananin ɓacin rai, kai Haroon ya jinjina ganin Jabeer yasa hannu ya janye hiramin dake kanshi, ya taune lips ɗinshi, kana ya rufe idanunshi, cikin ƙarfi yasa hannunshi ya fara jan bakin hiramin , da yake sabo fil janshi yakeyi alamun zai yagashi. Shiru Haroon yayi baiyi yunƙurin hanashi ba, domin dama yasan za'a rina, sabida shi Jabeer wannan itace babbar alamar tsananin ɓacin ransa, muddin fushinsa ya hauhawa to, yakan yayyaga abu da karfi. Fass haka Haroon yaji sautin, yagewar sabon hiramin nan. Shi kuwa Jabeer idonshi ya ƙara rumtsewa yanayi mai ci gaba da fatattaka hiramin. Murmushi Haroon yayi cikin tare da fara ɗaukar shi video. Yanayi dan tsokana. A can sashin Hajia Mama kuwa, ganin shiru-shiru Jabeer bai shigo bane, kamar yadda ya saba in yayi tafiya ya dawo yakan, Batul kuwa, ta gaza zaune ta gaza tsaye, ta ƙenƙesa ado da kwalliya tamkar mai zuwa gasar kyau. A karo na barka tai ta kalli Hajia Mama, cikin zaƙuwa tace. "Yakura, muje, side ɗinshin mana, mu duba lfy kuwa har yanzu bai shigoba." Ajiyar zuciya Hajia Mama ta sauke, tare da miƙewa tace. "Muje Batul ni kaina, na banyi zaton zai kai iwar haka bai shigoba, dole akwai abunda ya tsareshi". Da haka suka fito, suka nufi sashin Jabeer ɗin. Kasan cewarta matsayin uwa, yasa sam bata da hijabi da sashin, haka yasa, sarkin ƙofar na ganinta suka rusuna tare dayi mata kirari kana ta wuce. A falon suka samesu, zaune. Haroon ya tasashi gaba da kallo da wayarshi, shi kuwa Jabeer, idonshi a rumtse, bakinshi na motsawa a hankali, yana maimaita, tasbihen daya zame mishi abokan rayuwa. Kana hannunshi nata yage sabon hiraminshi. Haroon ne ya amsawa Mama sallamarta, tare da cewa. "Barka da fitowa Hajia Mama". Da sauri ta ƙarasa gabansu, kujerar dake kusa dasu ta zauna, cikin tarin kula tace. "Haroon da kai ake tafe kenan? Ya yar uwata, yaushe ka dawo?". "Haroon lfy kuwa me akayiwa Jabeer? Waya taɓa minshi? Waya taɓo ɗan lelen Umaymah'nshi Da Sitti'nshi?". Cikin lumshe ido Haroon yace. "To Hajia Mama wacce tamɓaya ɗaya zan amsa miki, ta ƴar uwarki ko ta ɗan rigimarku, mutun in yayi fushi sai yayi ta yage-yage, wannan in ya samu dama in yayi fushi ya samu ya damƙi ƴar mutane a hannunshi tabbas zai yageta, dan ko namiji da kyar zai iya ƙwatar kanshi". Murmushi mai cike da kulawa tayiwa Haroon kana, ta kalli Batul da zauna gefenta, ta zubawa Jabeer idonu tamkar zata cinyeshi ɗanye, wani irin sonshi da ƙaunarshi takeji, jiki da zuciyarta, Kekyawan sumar kanshi ta zuwa, idanu a hankali ta dawo da idon kam tattausan sajen da yayi fuskarshi ƙawanya, har kan gashin gemunshi da ya kai kamu ɗaya, yayi baƙi sitib dashi ya konta lib sai sheƙi yakeyi, jajayen laɓɓan bakinsa, da suke motsawa ne ta zubawa kwayar idanunta. Shi kuwa Sheykh Jabeer, sanadin tasbihin da yakeyi ne, yaji zuciyarshi tayi fes, fushin da yakeji duk ya kau. A hankali yakejin tsikar jikinshi na amsa sautin yam-yam tana sanar mishi ana kallonshi. Yunƙurowa yayi ya tashi zaune, kana a hankali ya fara buɗe idanunshi. Da sauri ya kauda ƙwayar idanunshi sabida ganin kwayar idanun Batul cikin nasa, Hajia Mama kuwa, cikin sanyi tace. "Innallaha ma'assabirin". Idonshi ya kuma lumshewa, wannan abu shike ƙara sashi jin ƙarfin guiwar zama cikin masarautarsun. Sabida yayi dace, da uwar da take ƙara bashi tarbiyar da yasan itace dai-dai tana danne dukkan baƙin cikinta, domin ta sama mishi nitsuwa. Duk da kasancewar shi malami. Tana ƙara nusar dashi. A hankali yace. "Barka da safiya Mama". Murmushi tayi kana tace. "Barka dai, Muhammad Jabeer. Garkuwa mai nagarta, Yau na tashi da tsantsar farin ciki , tunda maji muryarka da asuba, meya ɓata maka rai daga dawowa?". Cikin sanyi yace. "Babu komai Mama, Sheykh Abdulkareem, da ahlinshin duk sun gaisheki". Murmushi tayi tare da cewa. "Tsoho mai ran ƙarfe, kakanmu bawan Allah, yana lfy ko?". "Alhamdulillah". Yace mata, yana mai sa hannu ya ɗauki hular da Jamil ya ajiye a kusa dashi ya ɗaura a kanshi, sabida wani irin kallo da yaga Batul nayiwa suman kanshi. Ita kuwa Batul ido ta ɗan lumshe, ganin yadda ya tamƙe fuskarshi ya watsawa gefen da take kallon, ƙasaita. A hankali ta buɗe idonta kana ta sauƙesu kan sajenshi, Wani gajeren tsaki yaja, tare da kauda fuskarshi. Ita kuwa Butul mgnar zuciya takeyi. "Masha Allah, Ya Jabeer, komai kayi kyau kakeyi, ya Allah ka tabbatarmin da mafarkina mana, wannan kekkyawan bawa naka ya zamo mijina, domin shine mijin daya dace dani, mijin kece raini da nunawa sa'a, Uhumm jin kai da ƙasaita ba, kayi naka, kafin ka shigo hannuna, in sha Allah, sai na zama sarauniya ka zama bawana." A hankali tace. "Ya Jabeer ina kwana". Shiru yayi kamar bai jitaba, Allah ya sani ya tsani kallo a rayuwarsa ta duniya, baya kuma son mace, da rashin kamun kai. Hajia Mama kuwa ganin yadda ya takurene yayi kici-kici da fuska, yasa ta ɗan, kalleshi tare da cewa. "Jabeer Batul ke gaidaka, itama jiya tazo". Kanshi ya ɗan rusunar tare da miƙewa tsaye, cikin sanyi yace. "Masha Allah". Daga nan ya ɗanyi taku biyu zuwa uku, kana yace. "Mama barin inje inyi shirin jumma'a". Murmushi tayi tare da cewa to. Dan ta fahimci zillewa yakeyi. Daga nan shi dai yayi, ciki. Su kuma suka, fita. Haroon kuwa Data ya kunna, Umaymah ya turawa video ɗin da yayiwa Jabeer da yana cikin fushin. A can Rugar Bani kuwa, yau tun safe, su Shatu suka baro asibitin, sabida, matasan mayaƙan cikin garin Shikan ɗin sai kai komo sukeyi, cikin asibitin. kana sai zuwa sukeyi maja'iunsu, suna mitin. Bisa dukkan alamu, sunada wata manufa, ganin hakane, yasa likitoci musulmai, suka bada shawarar a kwashi marasa lfyar a medasu cikin asibitin babban birnin Ɓadamaya, sabida su nan babban likitansu ya hanasu duba kowa. Da wannan shawarar ne, aka kwashi duk marasa lfyan da taimakon yan agaji aka shiga dasu cikin Adamawa. Dan an fara rade-raɗin wai fulanin Rugar Bani sunce zasu ɗauki fansa, to shisa ƙabilar ɓachama suma suketa guzurutsoma, har ta kai da matakin in dare yayi matasan hausa fulani na cikin garin ma zauna cikin garin Numan, sai su futo suyi ta yawo da makawai suna kare amguwanninsu. Kana suma ƙabilar ɓachama sai su fito da makamai suna kare amguwanninsu. Shatu kuwa basu wuce cikin Ɓadamaya ba, sabida Ummiy ta dawo hayyacina ta, hakama Junainah ta dawo haiyacinta da ƙarfin addu'o'in da Aysha da Bappa keyi. Dan haka su cikin Rugarsu-suka koma. Shatu kuwa, tunda Junainah ta gaya mata batun ɓacewarsu Ya Giɗi da kuma kashe ya Lado da akayi, har zuwa yanzu bata daina kukaba. Koda Ba'ana yazo wurinta daren jiya, da yaji lbrin sun dawo babu abinda takeyi sai kuka. Shi kuwa Ba'ana, baƙin cikinsa shine da Ummiy ds Junainah da Bappa suka rayuwa, Shiyasa yanzu, yayi musu nasu shirin mutuwa namu samman. Inda Bugulu Maman Ma'ans ta gasa zabbbin da Ba'ana ya yanka, kana ta daka musu, yajin borkono, da busasshen kan maciji. Ta barbaɗa musu, kana ta yaryaɗa man shanune da ya gauraya da dafin macijin cikin man shanun da tayi musu gashin dashi, kana ya nufi, bakin garkensu, da akoshin gasassun zabbin. Sannan ya aika aka kira mishi Shatu, cikin kuka Rafi'a tacewa ɗan aiken yaje, ya zazzaɓi ke damunta. Koda yaron yaje ya gaya mishi, sai yace zai a kira mishi Junainah, Koda yazo ya gaya musu, Sai Junainah ta miƙe tabi bayan ɗan aiken. Kasan cewar garken nasu ba nisa, tafiya kaɗan tayi ta isa, ta isa ta zauna a bakin ƴar bukkarsa da yake, cikin. cikin disashewar muryar hawaye na zuba tace. "Ya Ba'ana, kaje ka dubo jikin Ya Junaidun ne?". Juyowa yayi ya fuskanceta da kyau, cikin sanyi yace. "Eh naje na dubashi, jikinshi da sauƙi, ke ya naki jikin? Ya Ummiy da jiki". Cikin sanyi tasa hannu ta share hawayenta dake shatata kana a hankali tace. "Ummiy jikinta da sauƙi sai dai har yanzu bata mgn, Adda Shatu kuma sai kuka takeyi". Hararanta yayi a fakaice, ji yake kamar ya jawota ya caka mata mashi ya mata kisan zahiri sai kuma ya fasa, Kanshi ya kauda tare da tura mata akoshin gasassun zabbin nan kana yace. "Ayyah sannu Junnuna, kiyi haƙuri dena, kuka, kici nama, sai kije kicewa Mata, tazo zan gaya mata inda su ya Giɗi suke". Cikin rawan jikin jin yunwa tace. "Yauwa bani inci dama yunwa nakeji, tun jiya banci komaiba, tunda muka dawo, bamuyi girkiba." Da sauri ya turo mata akoshin tare da buɗe mata fefeyin. Cikin rawan jiki irin na masu jin yunwa tasa hannu ta...! Uhummm Allah kaimu gobe lfy, mu ƙara sa free page, daga PAGE 15-16 an gama. By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 15 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘 *Littafin GARKUWA na kuɗine, daga wannan PAGE 15 da 16 FREE PAGE sun ƙare, turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276, ko ki turo dubunki ɗaya rak dan shiga Special Group, wanda anfi yawan posting, ta wannan asusun zaki turo 1k ɗin 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276.* ```Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki in dai kin san kin sayi littafina ne ko zaki sayane ɗan ki fitar min dashi na roƙeki da Allah da Manzonsa🙏🏻 kada ki saya, in kuwa har kin sayane kawai gaya min in biyaki kuɗin ki ki barmin littafina, mu rabu innahu annahu.``` Akwai kayyakin gyara namu mata setin amare da masu jego, da masu kwaskwarima, idan kina buƙatar saya ko sari, tuntuɓi wannan number tawa 09097853276. Hannu tasa ta jawo pepeyin jin yana ce mata. "Kici kije da gudu ki kira Mata, tazo in gaya mata, su Ya Giɗi sun kusa dawowa ta dena kuka, anji lbrin inda suke". Rufe akoshin tayi kana ta miƙe da sauri tace. "Da gaske ya Ba'ana an ji inda suke?". Cikin haɗe fuska yace. "Na taɓa yimiki ƙarya ne?". Da sauri ta jujjuya kanta kana tace. "Bari inje in gaya mata tazo sai inci naman a gida". Da sauri yace. "A a jeki kirata, in tazo sai ki tafi da naman, kije kuci keda Ummiy da Bappa da ita ƙawar Mata, ita kuma zan bata nata a nan". Ai tana jin hakan ta juya ta tafi, da sassarfa. Tana isa gida, ta kamo hannun Shatu, cikin haki tace. "Adda Shatu taso, taso muje ya Ba'ana zai gaya miki inda su ya Giɗi suke, yace anji lbrinsu". Wani irin zabura tayi, hakama Rafi'a dake bakin ƙofar kitchin ɗinsu. Cikin tarin kaɗuwa tace. "Ke Junainah, kada kiyi mana ƙarya". Cikin haki tace. "Wallahi tallahi, haka yace min zo muje kiji". Da sauri ta kamo hannun Rafi'a tace. "Adda Rafi'a kema zo muje tare". Cikin jin daɗi Rafia tace. "A a Junainah kuje, Ni kuma kafin ku dawo nayi mana abinda zamuci, da sauri tace. "A a Adda Rafi'a ki bari kar kiyi girki, Innar ya Ba'ana ta aiko mana gasassun zabbi yanzu zan amso mana su sai muci". Murmushi tayi kana tace. "To sai kinzo". Ita kam Shatu tuni ta fita, ta nufi Garkensu Ba'ana. Ita kuwa Ummiy ido kawai ta zuba, musu tana son ta kira Shatu ta hanata zuwa amman ta kasa. Ita kuwa Rafi'a kitchin ɗin ta shiga. A can garkensu Ba'ana kuwa. Yana hango Shatu, ya saki wani irin ajiyan zuciya, ido ya zuba mata, Gaba ɗaya ta rame tayi fiyau da ita, fuskarta tayi jazir alamun yawan kuka, kana, ga kumbura da idanunta sukayi. Da sauri take tafiya, sai dai tanayin takun a hankali ne, doguwar rigace a jikinta ta atampa, hijabi da ta saka wanda yazo mata har guiwa. Ta ɗan ja hulan kan hijabin dan ya ɗan kare mata kumburarrun idanunta. Wani zafi yakeji a ransa, Allah ya sani baya son ganin Shatu cikin damuwa duk ƙaƙantar-ta, yakanyi komai na zalumci, amman baya yi kan Shatu, shi kanshi ya yarda shi tantirine, azzalumi, kuma mugu, hakanan kuma ya yarda so gsky ne kuma so ɗaya ne tak kuma ya sani duniya ta sani yana son Shatu, yana son sama mata farin ciki a rayuwarta, yana son su rayu tare. Shiyasa yake son rabata da kowa nata wanda suke ƙoƙarin ganin sun hanasu Kasancewa mata da miji. Wani farin buzu ya shimfiɗa mata a bakin ƴar bukkartasa, tun kafin ta ƙara so. Tana isowa, murya can ƙasa tace. "Assalamu alaikum." Ido ya zubawa fuskarta cikin tausayawa yace. "Mata ki zauna". Murya a disashe tace. "Ya Ba'ana ka amsa sallamar mana". murmushi ya ɗanyi kana yace. "Mata na amsa bakijini bane". A hankali ta zauna bisa buzun, cikin sanyi ta lumshe idonta da takeji sun tsastsafo da zafafan hawaye, murya na rawa tace. "Ya Ba'ana, wai anji lbrin su ya Gaini?". Matsowa yayi bakin bukkar, ido ya ɗan zubawa fuskarta, sabida lumahe idon da tayi batasan yana kallontaba ganin hawayenta na zubowa ne yashi yin mgna, a hankali yace. "Mata, kiyi haƙuri, ki kontar da hankalinki, in dai yayunki suna raye, zan nemisu, ko dan farin cikinki, ki bar kuka Mata, bana son ganin hawayenki inajin ƙuna a raina". Ya ƙarishe mgnar murya can ƙasa. Cikin rawan murya tace. "Ya Ba'ana, ya zanyi? Ina zansa raina in ji sanyi, zuciyata tana ƙuna, Yayuna huɗu kab na rasasu lokaci ɗaya, bani da wa wanda zan nuna a faɗin nahiyar nan ince ga wani na a duniyar, babu ya Giɗi, wanda shine tamkar aboki ƙawa aminiya, abokin faɗata abokin dariyana, Babu ya Seyo, yaya mai kamar uwa, sabida yawan tausayinshi da nuna ƙaunarshi gareni, ko uwa iya abinda zata nunawa ɗanta kenan, babu ya Gaini da yake tamkar uba, babusu babu gawansu babu lbrinsu. An kashe min ya Lado da yake GARKUWA a gareni. Ya Ba'ana, ya zanyi in banyi kukaba, Ina zan fara nemansu, Ni macece inada rauni, ta ina zan nemosu? An kashe mana Innarmu". Ta ƙarishe mgnar tana mai kife kanta bisa guiwowinta ta saki wani irin kuka mai tsuma zuciya, cikin kuka taci gaba da cewa. "An kashe Inna, sanadin haka Ummiy na ta zama tamkar zautacciya, duk gidan dake cikin Rugar Bani babu gidan da ba'a kashe a ƙalla mutun biyarba a ƙaramin kari, suwaye ne ya Ba'ana, me mukayi musu? Me suke nema damu? Me muka tsare musu? Me laifinmu dan mun kasance Fulani makiyaya?". Karon forko a rayuwarsa da yaji rauni har ta kaishi ga zubda hawaye, koda yake raunin soyayyace, cikin zubda hawaye murya na rawa yace. "Mata gani, zan zame miki madadin uwa, uba, yayunki, Inna, zan zame miki Garkuwa, in sha Allah bazan bari ki cutuba, zan bada raina domin kare naki, zan nema miki farinciki da dukkan abinda na mallaka na duniya, zan zame miki adalin miji, Mata ki dena kuka, kiyi haƙuri". Cikin shessheƙan kuka ta ɗago kanta, ta zuba mishi ido, tabbas kuka yakeyi kamar yadda ta zata, cikin mamaki tace. "Ya Ba'ana meyasa kake kuka?". Hannun yasa ya sharce hawayenshi, karon forko a rayuwarsa da yayi abu ya gommace bayiba karo na forko a rayuwarsa da yayi mugunta yaji dana sani kan sace su Gaini. Da yatsarsa manuniya ya nunata, da mamaki tace. "Nice na saka kuka?". Kanshi ya gyaɗa mata, cikin al'ajab tace. "Me nayi maka?". Motsowa yayi ta bakin bukkar sosai can cikin sassanyan murya yace. "Kukanki ne yasani kuka Mata, farinci bazai samu gurbi a rayuwataba, muddin ke kina cikin ƙunci, dan Allah ki daina kuka,". A hankali tasa tafin hannunta ta share hawayenta. Shi kuwa Ba'ana, wani babban kura tanɗu yajo, cikin sanyi ya ajiyeshi gabanta a tsakiyarsu. Cikin sanyi yace. "Shatu". Da sauri ta ɗago kanta ta kalleshi domin yauce karo na forko rana ta forko a tarihin rayuwarta da taji ya kirata da Shatu, cikin mamaki tace. "Na'am ya Ba'ana". Girgiza kanshi yayi kana ya fara fito da wasu sabbin aska cikin zabirar da yanzu ya jawota, a hankali ya ɗago ya kalleta cikin yaƙini yace. "Shatu, zan faɗa miki abinda, babu wanda ya sani a kaina a duniya, Shatu zan nuna miki abinda duk duniya ban yarda da in nunawa kowaba, sabida ban yarda da kowaba sai ke ɗaya rak Shatu, nasan zuciyarki ciki da woje, ke mai imanice, bazaki taɓa zalumtata ba, bazaki bari a kuma zalum ceniba. Na amince da soyayyarmu, zamu rayu a tare har gaban abadan." Ido kawai ta iya zuba mishi. Ganin Junainah ta iso wurin ne, yasashi jawo akoshin gasassun zabbin gabanshi. Ita kuwa Junainah da sauri ta kuma sa hannu zata jawo akoshin. Kanshi ya jujjuya mata alamun ta bari. Cikin kwaɓe fuska da ɗan karen kwaɗayi da yunwar da takeji yana azalzalar ƴaƴan hanjin cikinta tace. "Yah Ba'ana ka bani mana yunwa nakeji". Cikin sanyi yace. "Bazan bayar ba". Da sauri tasa hannu ta zari akoshin tayi gaba Shatu ce ta fara kiranta tana. "Junnu! Junnu!!! Junnuhhh!". Ina bata kulata bama bare ta juyo. Shi kuwa Ba'ana ajiyan zuciya yayi tare da mgnar zuci. "Uhummm ƙuda garin kwaɗayi kya mutu, kwaɗayinki ne zai karki". Kai ya gyaɗa wa Shstu kana ya juyar da kanshi. Ita kuwa Aysha shiru tayi tabi Junainah da ido. Shi kuwa Ba'ana cikin sanyi ya wore ƙafafuwan sa, takalmin roba na sau ciki wato, tashi kabi shanun dake ƙafarsa ya zare. Sabbin askan ya ɗauka, kana ya fito da wasu ƴan kananun layu guda biyu. cikin yaƙini yace. "Shatu, kinga waɗannan layun?". Kai ta gyaɗa mishi cikin yin kici-kici da fuska. Jinjina mata kai yayi kana yaci gaba da cewa. "Wadannan sune, maƙurar, mgnin kariya da zan saka a jikina, zan sasu a gaban idonki, wannan ƙaramar ita zan saka a dundunyar ƙafar dama, itace kuma layar, ƙarfe, mudin wannan laya tana jikina, to wlh babu wani ƙarfe dake kan doron duniya da zai shiga jikina". Cikin mamaki tace. "Koda bulet ne!?". Kanshi ya gyaɗa mata tare da cewa. "Koda menene, kuwa su wannan sabbin layune, wanda babu makarinsu, sai dai ina na ciresu a jikina, ita wannan da zan saka a ƙafar hagu, layar zanace. Duk sihirin mutun bazai karyashiba, zan iya ɓacewa inje ko ina, makarinta abu ɗaya ne!". A hankali tace. "To menene makarinta?". Cikin sauƙe wani nannauyan numfashi yace. "Idan wata rana dubuna zaicika za'iya kamani, to ammanfa tabbas, zan iya ɓacewa sai dai in ba'a barni na sha ruwaba, amman muddin akabani ruwa nasha zan iya ɓacewa." Da sauri tace. "Ya Ba'ana dubunka ya cika kuma, kamar wani mugu ko maiyin mugun abu". Da sauri ya fizge mgnar da cewa. "Eh to ai yanzu zan fara fataucin nemo. Suya Yaya Giɗi ne, kinga kuwa, sai yadda hali yayi". Ajiyan zuciya ta sauƙe kana tace. "To ita layar ɓatan da ta ƙarfe menene makarinsu?". Kanshi ya ɗan jingina da bakin bukkar ido ya ɗan zuba mata, kana cikin sanyi yace. "Uhum makarinta sai in an samu maza tagwaye, da matar da bata al'ada sunyi tuwon sabon geron da za'a shuka a tsakiyar garken fulanin kana tuwon za'ayishi da garin dakan hannune, kuma maza tagwayen sune zasu tuƙa tuwon kana matar da mijinta ya tara da ita batayi wonkan tsarkiba, ta kwashi tuwon , to su kam in naci, tuwon gaba ɗaya sihirin jikina zai karye, in kuma ba haka sai dai ina an tsaga dundunyar ƙafar tawa an ciresune kafin makami ya iya min illa". Cikin wani irin sanyi tace. "In sha Allah zaka nemosu lfy ka dawo dasu lfy, zanyi ta addu'a Allah ya baiyanasu." Kanshi ya tanƙwasar kana a hankali yace. "Uhum sai daifa Shatu akwai wasu bulalin da aka bani tabbacin zasu worwore duk wani asiri da kafi da nayiwa jikina, Amman duk da haka bazasu worwore waɗannan layunba, sai dai an bani tabbacin, muddinfa aka dakeni da wannan bulalin zan ji azabar dukan, da zai iya ɗauke raina". Cikin mutuwar jiki tace. "Bazama su dakeka ba, Ya Ba'ana". Kanshi ya mirgina kana, yasa hannu ya ɗauki askarnan, kawai sai ya datsata kan dundunyar ƙafar damanshi, Da ƙarfi Shatu tasa salati tare da rufe idonta, gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi murya na rawa tace. "Innalillahi ya Ba'ana zaka kashe kanka". Cikin harshen fillanci yace. "Ai bazanji zafinba Mata, bari yanzu in ɗinkesu, buɗe idonki ki gani." Cike da tsaro tace. "Bazan iyaba, ina tsoro". Jin hakane yasa bai kuma ce ta buɗe idonba, har saida ya gama cusa layun kana yasa ƙayar aduwa ya rinƙa hudawa yana ɗinkawa da zaren, gashin bindin shanu, saida ya gama yace ta buɗe idonta. Cikin tsoron ta zubawa wurin ido, ga jini ya ɓata ko ina, Sai kuma ta ƙurawa ƙafafuwan ido ganin yana shafa musu man shanu sai wani tafasa wurin yakeyi, cikin mintuna uku duk wurin yayi tib-tib kamar ba shiba. Cikin tsoro tace. "Ya Ba'ana, ka dena irin wadannan abubuwa, wallahi shirka ne, tsafine babu kyau! Haramunne." Ganin yadda ya haɗe fuska ne yasa tace. "Kayi haƙuri, shiyasa tun forko ina son ince maka ba kyau bana son kana irin wadannan abubuwan". Murmushi ya ɗanyi kana yace. "In kin sake min mgnar, bulala ɗaya zan ɗauko cikin bulalin shaɗi na, in zaneki da ita sau ɗaya kiji irin zafin da masu gangancin cewa suna sonki, sukeji a jikinsu." Cikin tsoro tace. "Bazan sake bama Ya Ba'ana wadannan, bulalin da kake tsumasu da dafin kunama ai Ni kam na sani bulala ɗaya zakamin zan mutu". Da sauri yace. "Azubillah, Mata kada ki sake cewa zaki mutu, domin duk randa kika mutu nima zan mutu, sai dai batun gsky ko Mata, duk mutumin da kikaga ya iya jure bulalin shaɗi na, har ya kai matakin nasara, to wlh ki sani ki shaida, jarumine, irin jaruman da sunyi ƙaranci a duniya." Hannu tasa ta kange fuska daga wani irin kallo mai cike da so da yake mata, Tabbas Ba'ana ba barbarene, amman yanada wani irin kyau mai ban mmki, a hankali tace. "Ya Ba'ana wai da waye kake kamane?". Cikin murmushin da ya bayyana kyawawan haƙoransa yace. "Ni da kakata Maman babana nake kama, ita kuma ba kanuribace, fulatamare ce ita". Cikin sanyi tace. Murmushi ya ɗanyi kana yace. Cikin sanyi tace. "Haba shiyasa mana kake da kyau sosai". Wani irin kallo ya mata tare da cewa. "Eyeh ashe Ni kekyawan ne Mata, ke dama shine baki taɓa gaya min ba inji daga bakin wacca nafiso fiye da komai a duniya dan inji daɗi, kin bari sai wasu can keta cemin wai ni kekyawan ne". Da sauri ta miƙe tare da cewa. "Sai anjima, Mai kyau ka tashi kaje ka tafi masallacin kaga lokacin sallan jumma'a yazo anata tafiya". Da murmushi ya rakata. Ita kuwa da haka ta tafi gida, sabida tuni wasu masallatan har sun fara huɗuban sallan jumma'a. Tana shiga gida ta samu. Rafi'a, Junainah, Ummiy da Bappa, gaba dayansu a. Cikin Babban birnin Ɓadamaya, a cikin masarautar Joɗa, kuwa. Tuni masallacin Lamiɗo Nuruddee, ya cika yayi maƙil da bani adam tako ina zuwa, akeyi. Masallacin ya cika tab tamkar zai fashe, shiru kakeji babu wani amon sautin ɗan adam dake tashi, sai sautin muryarsa. Yana tsayene cas kan ƙafafunshi, Wata dan datsetsiyar, shaddar Super Nour ce a jikinshi wacce take Brown color a ƙalla kuɗinta zai kai dubu ɗari da ashirin, shaddar irin mai mai ɗinnane, Yayi kauri cikin kayan ko dan yanayin suturar da ya sakane, boxes ce fara ƙal yasa a ciki, sai snglet itama fara ƙal, kana sai Rigar half jomfar yaddan dake jikinshi sai wonɗota, wanda sunyi cib-cib da madaidaicin jikinsa, Kana sai watta tattausar doguwar al'kyabbar sa, Golding color, sai wani irin sheƙi takeyi, sai hirami fari daja irin mai ɗigo-ɗigo nan, yayi masa sakin manyan Dattawan bai lonƙosashi, ya barshi a zube bisa kafaɗunshi, sai ta gaban goshinsa da ya ɗan matseshi ya bada ɗan tsini dai-dai kan karan hancinsa, Sai baƙin zagayen daya ɗaura bisa kam hiramin. Kana sai wasu takalman shi dake can bakin ƙofar shuga masallacin ta ƙofar liman, takalman irin na sarauta ne half cover, wanda suma fari da ɗigon jane. Yayi wani irin kyau mai ɗaukar hankali haibarsa da kimarsa da dottakunsa sunyiwa fuskarshi ƙawanya, sajen nan nashi yayi lib-lib tamkar anayi wa koren ciyawa bayi, sai wani irin sassanyan ƙamshin turaren OudKareem ɗin sa, dake tashi a jikinsa. Muryarsace ta cika ko ina na yankin. Shiru mutanen wurin sukayi kowa na jin, wa'azin yana ratsasu. Yana Hudbane akan, wuraren da ya dace namiji ya gani a jikin matar da yake neman aurenta, yana kan hankali, bisa wuce gona da iri da mafiya matasan yanzu keyi, a kan wannan dama da Allah ya basu. Gyara tsayuwarshi yayi, tare da haɗe hannayenshi wuri ɗaya, ya haɗe bakin al'kyabbar jikinshin. Cikin tattausan lafazi mai ratsa kunne da zuciyar duk mai sauraro da imani yaci gaba da cewa. "Aure wata muhimmiyar hanya ce, wanda idan aka ƙullashi zai bawa ma'auta daman saduwa, tsakaninsu, ba tare da wata ƙyama ba, kuma ta hakane ma'autan zasu zama sutura ga junansu. Kamar yadda Allah maɗaukakin sarki ya faɗa, a Suratul Baƙara aya ta , 187:- (HUNNA LIBASUN-LAKUM WA, ANTUM LIBASUN-LAKUM). Ma'ana su mata suturane gareku maza, sannan ku maza suturane garesu (Su Matan)." Gyara zaman al'kyabbar sa yayi tare da kallon tarin dubban al'ummar Annabi dake zaune gabansa, hankalin da nitsuwar kowa na kanshi. Sai ɗan haskem cameras da yake gilmawa ta kanshi da sauran na kusa dashi, shaidar ana naɗar sautin muryarsa nayin huɗuban. Cikin nitsuwa yaci gaba da cewa. "Saboda haka, ya zama dole mutun, ya nitsu ya maida hankali ya zaɓi abokiyar zama ta gari da zata zame mishi sutura ya zame mata sutura, wajibine kuma kayiwa kanka da jikinta iyaka har sai an biya sadaki, an kuma ɗaura aure, shaidu sun shaida sannan zaka samu nitsuwa da ita. Domin shi aure, yana samar da nitsuwa tsakanin ma'auranta. Ɗan Adam bazai samu cikakkiyar nitsuwa a gidansa ba sai in har yanada mata, wacca ya aura. Domin zata ɗebe mishi kewa, ta sa shi ya samu nitsuwar hankalinshi. Saboda zamansu tare, a ƙarƙashin inuwar aure zatayi mishi maganin kaɗaci. Kamar yadda Allah, (A.A.W) ya faɗi a Suratul Rum aya ta 21:- (WA MIN AYATIHI AN KHALAKA LAKUM MIN ANFUSAKUM AZWAJAN LITASKUNUW ILAIHA WA JA'ALA BAINAKUM, MA WADATAN WA RAHMA INNA FII ZALIKA LA AAYAATIN LIKAUMIN YATAFAKKARUN). Yana daga cikin ayoyin da Allah mai girma ya halitta mana mataye daga kawunan mu. (Mataye da muke aure da su) domin su sami nitsuwa junanku, sannan kuma ya sa muku soyayya a tsakanin ku tare da Rahma da tausayawa juna. Lallai a cikin wannan al'amari akwai ayoyi abin lura ga jama'a'an da suke masu tunani". Gaba ɗaya taron al'ummar babu, hayaniya ko motsi shiru kakeji, Baba Nasiru kuwa, yana dai zaune ne cikin sahun da masallacin amman ji yake tamkar ya shaƙo wuyan Jabeer sai ya kaishi ƙiyama, Baba Bashiru ne dake gefenshi, ya ɗan kalleshi tare da yin ƙasa da murya yace. "Ya Nasiru ka nitsu mana ka koyi danne abinda ke ranka". Cikin tarin baƙin ciki yace. "Haba Bashiru ya zanyi in iya danne abinda ke raina, bayan da kai sani dama duk sauran yan uwanmu, mahaifinmu ko sarautar sarkin ƙofa bai bamuba, Tunda ya bawa Ya Muhammad, Galadima, yana rasuwa, madadin a maida sarautar Galadima kaina, ko kan Hashim tunda shi ubanshine Galadima, sai ya ɗauki wannan sarautar ya bawa, Jafar shi ɗan rashin adalci." Murmushi Baba Bashiru yayi tare da cewa. "To ai kuma dai gashi ya haukace ko? Ina dai yanzu sarautar tafi ƙarfinsa, dole dai ya barta". Cikin fusata Baba Nasiru yace. "To ɗaya barta ya haukace ɗin ma, ya maidota ga ƴan ɗakinmu ne, inji, wancan tsohon ya bawa, waishi ya bawa ƙaninshi, ai shima ɗan tsohon sarkine Sannan kana ganin yadda ya kuma ɗaukar sarautar GARKUWA ya bawa Jabeer, sannan babban tashin hankalin kanaga yau tare suka fito ɗakin labbare dashi wannan munafikin yaro, waishi Sheykh ɗan iska anyi asiri anyi tsafi duk baya kamashi yadda mukeso". Barrister Kamal ne dake gefensu, yayi ɗan wani guntun tsaki cikin tsuke fuskarsa, da jin haushin yan uwan nashi yace. "Ya Nasiru kufa, ji tsoron Allah, ku tuna, cikin Masallaci kuke, kuma ba kyau liman na huɗuba ana. Surutu." Wani irin mugun kallo Baba Bashiru ya watsa mishi tare da cewa. "To ɗan masu matacciyar zuciya, wa'azin da yakeyi ai tun kan a haifi uwarshi mun sani". A kufule Barrister Kamal yace. "Ƙaryane, da kun san abunda ya sani wala Allah da zuciyarku ta tsarkaka". Shiru yayi tare da fuskantarta Inda limamin take jin yana cewa. "Halaccin kallon matar da mutun yakeso ya aura. Haƙiƙa munsan matarka abokiyar rayuwarka ce. Kuma gonarka ce da zakayi shuka a cikinta, sannan kuma gareta zaka samu konciyar hankali. Kuma shi manufar yin aure ya hana kallon wata ko wasu matan wanda ba nakaba da dai makamantansu Irin hakan. IN KUWA HAKANE TO LALLAI AKWAI BUƘATAR SAI MUTUN YA ƊARJE! YA ZAƁA. Haka kuwa baya yiwuwa sai ka kalleta sosai da sosai. Saboda mahimmancin haka nema shariyar musulunci ta yardar maka da ka kalli wacce kakeso zaka aura da kyau. Don ka tabbatar da wancan abubuwan da aka ambata a sama. Kuma wannan dama da Shari'a ta bada ta bada shine, a matsayin halasci na wurin mafi yawan malamai, kuma wannan Halascin da akace halasne ya haɗa da cewa. Shin ta yarda ka kalleta, ko bata yardaba, halasne in dai ka kalleta. Kuma wannan hukuncin haka yake a wojen mafiya yawan malamai, sai dai Malikiya, sunce shi hukuncin Halascin ya dogara ne, in ta bashi izinin amma in bata bashi izinin ba to bai halasta ba. Haka kuma shi wannan hukuncin halascin an samo shine daga, hadisin Abu Huraira (Allah ya ƙara masa yarda) yace, wani mutun ya nemi auren wata mata, ƴar Madina, sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa: "Shin ka kalleta kuwa?". Sai mutumin yace, wa Manzon Allah (S.A.W) "A'a ban kalleta ba". Sai Manzon Allah (S.A.W) yace. "Tafi ka kalleta, domin mutanen Madina sunada wata illa a idanunsu." A wata ruwayar kuma da Abu Dauda ya ruwaito. Daga Jabir Bin Abdullahi cewa: Lallai Manzon Allah (S.A.W) yace. "Idan ɗayanku zai nemi aure to idan ya sami ikon kallonta wato kallon abin da zai burgeshi zuwa ga aurenta, to ya aikata hakan, (ma'ana ya kalleta) Jabir yace sai na nemi wata mata, daga cikin ƙabilar Banu Salma na kasance ina bibiyanta har sai da naga abin da zai birgeni a aurenta. Ɗan zagaitawa yayi kana yayi gyaran murya tare da cigaba da cewa. "To matasanmu na yanzu suna, fakewa da waɗannan hujjojin, suna fakewa da guzuma su harbi karsana, suna fakewa da hadisai suyi haramtaccen kallo, wata sun fake da rama suci ɗanyen gari. Hattara gareku iyayen yara maza da mata, Gargaɗi gareku matasa, bari in tuna sar daku wuraren daya halasta ka kalla a jikin matar da kake son ka aura. Dangane da inda ya kamata ka kalla, a jikin macen da zaka aura. Malamai sun kasu kan wannan hukuncin, saboda ba su, sami hadisin da ya yi bayani keɓantaccen wuri wanda aka keɓe ko aka ce nanne kawai za'a kalla ba, wannan shi ne musabbabin da suka karkasu kamar haka: 1 Mafiya yawan malamai sun tafi, cewa in mutun yana neman auren mace, yana iya duban fuskarta da tafukan hannunta. A Duba Fiƙhu wadi Juzu'i na 2. Shafi na 20 sannan kuma a cikin Fiƙhu Sunnah Juzu'i na 2 shafi na 24 wasu malamai sun ƙara yin bayani da cewa idan mutum ya dubi fuska mace, zai gane kyawunta, in kuma yadubi Fuskarta zai iya fahimtar cewa, mai ni'imtaccen jiki ne wato mai tattausan fata jiki, ko kuma mata marar ni'iman jiki. Sheikh imamul Al-Auza'i yana cewa. "Mai neman aure yana iya kallon wuraren nama dake jikin mace da zai aura. Duba cikin Fiƙhu Sunnah Juzu'i na 2 shafi na 24. Sheikh imamul Dauda kuwa yana cewa: Mai neman aure yana iya kallon dukkan jikin matar da zai aura, shima an samu daga Fiƙhu Sunnah Juzu'i na 2 shafi na 24. Ɗan tsagaitawa yayi tare da ɗago kekyawan tsintsiyar hannunshi ya kalli agogon Daimond dake ɗaure samfarin Gucci, Ganin lokacin salla ya ƙara tone yasashi yin gyaran murya tare da ci gaba da mgna gaggauce, yace. " A wata ruwayar kuma da aka samo daga Abudurrazaƙ Umar Sa'idu ɗan Mansur yace, (Amirul mu'minin) ya nemi auren ƴar Sayyidina Aliyu (R.A) wanda ake kira da Ummul-Kulsum, sai, Aliyu ya ambata masa ƙanƙantarta, sai yace. Zan turo ita idan ka ganta tayi maka matarka kenan, sai ya aiketa wuri shi. Lokacin da taje sai ya yaye suturar da ya rufe ƙwaurinta. Sai tace. (Ba don kai Amirul mu'minin bane da na tsole ko buge idonka, (wato da na mareka) idan muku dubi, wannan in har maganar ya inƙanta to ana iya yin hakan. Anan kenan in har ka kalleta batayi maka ba, to ka kama bakinka kayi shiru. Kada ka faɗi wata magana wanda zata iya cutar da ita. In kana ganin kai bata baka sha'awa ba, to tana iya bawa wani sha'awa ya aureta, domin ko wanne icce da ma tsincinsa, kuma abincin wani guban wani. Allah yasa mu dace, lokacin salla yayi, bari muyi salla sai in Allah ya kaimu sati mai zuwa sai muyi bayani kan halaccin mace ta kalli mijin da zata aura. Daga nan yayi addu'an kana, ya juya ya fuskanci gabas, tare da tada iƙama bayan yayi addu'an. Bayan an idar da sallane, suka fito, a jere. Ta ƙofarsun dai suka shiga, inda duk ahlin masarautar suke bin nan bayi da hadimai da sauran fadawa kusa, duk ta babbar ƙofar suke bi. Kusan a jere a jere suke tafi. Kasan cewar zasuyi tafiyar zuwa Rugar Bani ne yasa Mai martaba Lamiɗo ke sauri. Hakama Sheykh Jabeer, wanda Jalal, Jamil, Jafar, Haroon, Imran, Hashim ke tare dashi, A hankali ya tsaya jin muryar bappanshi ƙanin Abbanshi Baba Nasiru kenan na ce mishi. "Kai! Jabeer tsaya". Tsayawa yayi cak ba tare daya juyo ba, Suma sauran duk tsayuwa sukayi, Kusan a tare Baba Nasiru da Baba Bashiru. Suka isosu. Cikin haɗe fuska Baba Nasiri yace. "Jabeer, in dai aure kake so ai gwara ka fito fili ka gaya mana, mu bazai gagara ba mu aurar maka koda yar baiwace, tunda shi ubanka zuciyarshi ta mace, baya iya tsinanawa kansa komai." Da sauri ya rumtse idonshi, Jalal kuwa wani irin kallo ya watsa bappanun nasu, Shi kuwa Jabeer shiru yayi bai tanka musuba, Baba Basiru ne ya ne ya bugi kafaɗarshi tare da cewa. "Kodai kafi ganewa yawon zinace- zinacen daka saba ɗin ne? Kafin burin a barka ba mata, kana zaune ka tsufe a gida ka fake da rigar malumta kana iskanci a cikin tsarkakekkiyar masarauta ko". Ido ya zuba mishi babu ko kebtawa, ganin haka Baba Basirun ya ɗauke hannunshi dake kan kafaɗarshi. Dai-dai lokacin kuma Barrister Kamal da Dr Aliyu suka iso wurin. Suna isa Ya Jafar yayi saurin kamo hannun Ƙanin shi Sheykh Jabeer, ya fara ja da sauri alamun su tafi su bar wurin gaba ɗaya, jikinshi rawa yakeyi. Ganin hakane Haroon ya kalleshi cikin larabci yacewa Jabeer. "Ɗan uwana mu tafi". Barrister Kamal ne ya kalli Jabeer cikin sanyi yace. "Jabeer jeka, ku tafi kada ka biye musu, tunda sun girma basu san sun girma ba." Jin hakane yasa Jabeer ya juya ya fara tafiya. Jalal kuwa wani harara ya watsa musu kana ya juya yabi bayan yayunshi. Jafar kuwa Jan hannun Jabeer yakeyi a kiɗime gaba ɗaya jikinshi karkarwa yakeyi tamkar mazari. Ganin haka yasa Jabeer ya jashi ya kaishi sashinsu, ya damƙa hannunshi wa Juwairiyya kana yace mata ta kula dashi, yanzu zai fita shida Lamiɗo. Jiki a mace Juwairiyya ta mishi fatan a dawo 'lfy. Ƙarfe biyu da rabi dai-dai suna cikin motoci, wanda a ƙalla sun kai su goma. Motar forko Waziri ne wanda yake ɗane ga Yayar Lamiɗo. Sai Galadima, da Wambai, Ɗaya motar kuma Ɗan iyane da Sallama, da sarkin Dawaki, da sarkin fada, Sai motar da Lamiɗo ke ciki, shida Garkuwa wato Jabeer sai Haroon sai kuma Hashim da Laminu, ƙanin Hashim wanda duk yaran Gimbiya Saudatu ne matar babban yayansu Habibullah wato Abbansu Jabeer, wanda da shine Galadima. Ɗaya rasune aka bawa Ya Jafar sarautar wanda kwananshi goma da sarautar, komai na rayuwarsu ya sauya. Sai motar dake binsu wanda Jalal, Jamil, Imran Sulaiman ɗan Barrister Kamal, suke ciki. Sai sauran motocin fadawa kamaru, Ɗan kazagi, mai yiwa sarki fadanci da kuna dogari mai riƙewa sarki laima, da sarki mota da dai sauransu. A jere a jere motocin ke tafiya. Gudu sukeyi mai ɗan yawa sabida ganin yamma ta ƙarato, gashi basu je bama bare su fara shirin dawowa. Gudu sukeyi, kana fadawansu, rirtiƙe da bulalin dogaye. Kai tsaye Rugar Bani suka nufa. Koda suka iso cikin garin Shikan, sunga alamun garin babu lfy, har yanzu dan sai matasan ƙabilar ɓachama da hausawa suketa yawo a garin ko wanne na bawa yankinsu kariya. Suna isa cikin Rugar Bani. Gaba ɗaya mutanen Rugar duk inda suka gilma sai a bisu da ido, Yara maza da mata sunata guduwa suna shiga cikin gidajensu. Kai tsaye tsakiyar garin suka nufa wanda nanne fadar Arɗo Bani taken kuma lokacin duk manya da yara maza tsoffi da dattawan garin duk suna harabar wurin sabida yau jumma'a duk suna dawowa kiwo da wuri. Kuma duk a tsakiyar garin suke taruwa sabida bawa garinsu kariya, domin har yanzu suna cike da taraddadin abinda akayi musu. Kuma ya rigada yanzu an ƙure haƙurinsu sunata shirin ɗaukan fansar rayukan da aka kashe musune. Fiw-fiw haka motocin keta gilma mutane suna wucewa tara da tada ƙura sabida babu kolta a garin sai yashi. Sai sauti da ƙugin mitocin ne ya cika kunnuwan mutanen garin baki ɗayansu. Motocin na isowa wurin. Gaba ɗaya mutanen Rugar dama baƙin mutanen maƙotansu sauran rugage duk suka miƙe tsaye. Tare da gya tsayuwarsu, suka gyara riƙon da sukayiwa sanduna su. Ba tsoro ba fargaba sukayiwa motoci goma nan zobe, suka sasu a tsakiya. Cikin sauri Sarkin dogarai ya buɗe marfin motar da yake ciki, ya fito tare da zungureriyar bulalarashi. A take kuma Ɗan zagi ma ya fito. Da sauri duk sauran fadawanma suka firfito kowa da zungureriyar bulalarashi. Cikin ɗaga murya ɗanzagi yake cewa. "Ta kawarka lfy Sarki Nuruddeen Bubayero Joɗa, sarki ɗan sarki jikin Sarki,uban sarki kakan sarki. Jama'ar gari sun gaisheka, Da sauri duk sauran fadawan suka, firfito cikin motar. Sarƙin motane yazo ya buɗe wa Sarƙi ƙofar. Dogari kuwa matsowa yayi da sauri ya buɗe wata ƙatuwar laima, gaba ɗaya sukayiwa ƙofar motar labule da mamyan jajayen rigunansu, yayin su duk sawunsu babu takalma, sannan kawu nansu naɗe cikin wasu ƙatti-ƙattin rawanunnuka masu girma babu kunne ko ɗaya a jiki. Gaba ɗaya mutanen Rugar kuwa, sai ƙara tsuke fuskokinsu sukeyi, cikin jin haushin zuwa sun. Can cikin motar kuwa Haroon ne saƙale da wayarshi a kunne cikin sanyi yake mgn sabida kada Lamiɗo ya jiyoshi, haka kuwa babu mai jinshi sai Jabeer. Cikin sanyi ya ɗan kalli Jabeer kana yaci gaba da mgna a hankali yace. "Umaymah ni dai hankali na ya tashi, da irin wasu mutane da wasu abubuwan da akeyiwa su Jabeer a masarautar su, Umaymah, meyasa bazasu bar musu sarautar da Masarautar tasu gaba ɗaya bane, sai kinga fa yadda Jazlaan dinki ke fuskanta ƙalubale fa." Cikin wata iriyar murya Umaymah tace. "Yanzu kuna inane?". Kanshi ya ɗan jujjuya kana yace. "Uhum ni ina zan san inda muke, na dai san munzo wata Rugar fulani ce, wai GARKUWAN FULANI nasu ya kawo musu ziyara dan ja-janta musu abinda ya faru, kuma gaba ɗaya mutanen rugar naga sai Wani irin kallo suke mana kamar dai zasu huce a kanmu ne". Cikin wani irin tattausan murmushi mai nuna jin daɗi tace. "Bawa Jazlaan wayar". A hankali ya miƙa Jabeer wayar tare da cewa. "Umaymah ce". Cikin sanyi yace. "Kace tayi haƙuri sai mun koma zan kirata". Da sauri ya like mishi wayar a kunne jin tana cewa. "A a amshi wayar". Ɗan haɗe fuska yayi kana ya amshi sallamar da tayi mishi. Kana ya meda kai jikin kujerar murya can ƙasa yace. "Umaymah, Na gaji tunda muka dawo ban hutaba, yau da sassafe wannan tsohon ya sani shara kamar wani bawanshi haka ya sani na share mishi wannan ɗakin nasu na gado wanda in dan ta nine rusashi za'ayi gashi yanzu kuma ya kwasoni zuwa wata rugar FULANI da duk makamaine a hannunsu, ko wa zasu daka". Cikin wani irin jin daɗin daya bashi mamaki mai yawa tace. "Ko kai zasu dakane Jazlaan, Sheykh Jabeer, yasha zana a hannun Fulani". Cikin sanyi yace. "Su kashe Ni dai Umaymah, ke kin sani tunda nake a duniya, ba'a taɓa dukana ba, sabida koda iba yaroma ban taɓa yiwa Mama da Ummi laifin da zai kaisu ga yimin dukaba, Abba na kuma baya dukanmu, Umaymah kema baki taɓa koda marina ba, to kuma wa kika ga zai dakeni a faɗin duniyar nan banda ruwan sama". Murmushi tayi wanda har saida yaji sautin cikin sanyi tace. "Allah ya tabbatar da al'khairi cikin tafiyar naku, ka dai lura kaine GARKUWAR dole da duk abinda zai cutar da Lamiɗo ko masarautarku ko sunanta dole kai ne zaka zame musu Garkuwa, so dan Allah bana son kayiwa Lamiɗo musu bare gardama a cikin duk abinda zai umarceka". Cikin sanyi yace. "To Umaymah, in na koma zamuyi mgna". Daga nan sukayi sallama, cikin mamaki ya kalli yadda gaba ɗaya manyan hakimai sun firfito, ga Lamiɗo ya fita amman yana tsaye bakin ƙofar motar. Cikin sauri ya kalli Hashim tare da cewa. "Hashim Lfy kuwa naga duk suna tsaye, garin basu da abin zamane daza'a karrama baƙi?". Cikin nitsuwa Hashim yace. "Uhum cewa sukeyi, wai sun yafe ziyara da ja-jantawar Lamiɗo". A wojen kuwa, cikin ɗaga sauti Danzagi yace. "Hattara dai fulani mai ƙasar ne gaba ɗaya, ke tsaye tsakiyar garinku, maza ku bada masauƙi". Ya ƙarishe mgnar yana jujjuua bulalar hannunshi haka sauran fadawan. Cikin fillanci ɗan aiken Arɗo Bani ya buɗe murya da ƙarfi cikin harshen fillanci tare da cewa. "Maza ku bada hanya mai martaba ya iso fadar Arɗo Bani". Jin haka gaba ɗaya taron al'ummar fulanin suka fara buɗa hanya, Har gaban rumfar da Arɗo Bani ke ɗauke baƙi, inda aka shimfiɗe wurin da manyan taburmaii kana aka malale manyan kilisai irin namu na fulanin dawa. Bappa Malam Liman Alhaji Haro Alhaji Umaru, Musu, da kuma Ardo Duno da Arɗo barwa maƙotansu, duk suka mimmiƙe tsaye sai dai gaba dayansu fuskokinsu babu wal-wala, asalima wasun cikinsu jikinsu har ɓari yakeyi, dan fushi da zafin zuciya. A can cikin ƙauyen Bonon kuwa, Ba'ana da sauran ƙabilum ɓamawam duk suna gaban dodon tsafinsu Bonon ɗin, Da gudu Maman Ba'ana ta iso wurin cikin Yaren ɓacamancin ta sanar dasu zuwan, sarki Lamiɗo da tawagarsa, jin hakane yasa, Ba'ana ya miƙe jiki na rawa ya nufi rugartasu. Su kuwa sauran yace in yaje yaga da matsala zai kirasu. Nan ya tafi su kuma sukaci gaba da dariyar mugunta. A cikin Rugar Bani kuwa, Bukar Baban Ba'ana ne yayi wata iriyar fitinenneyar murmushi mai cike da mugunta dan son haddasa fitina, ta yadda zai samu masarauta Joɗo da kanta ta shiga matsala. Kutsawa yayi tayi cikin mutane har ya samu ya shigo gaba-gaba. Lamiɗo kuwa da tawagarsa taku sukeyi cikin al'farma da ƙasaita. Su Waziri, Galadima, Wambai, Ɗan iya, ɗan buram, duk suna biye dashi a baya, Dogari na rike mishi da laima, fadawa kuma na zazzaune a ƙasa, gefe da gefe, Ɗanzagi kuwa muryarsa ce cika wurin baki ɗaya duk da hayaniyar da wurin kedashi. A hankali Jabeer ya sako sawunshi woje, yana taka ƙafarshi ta dama kan ƙasar garin, yaji zuciyarshi ta buga da azaban ƙarfi har saida ta kaishi da rumtse idonshi tare da ambaton. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". A saman red lips ɗinshi. da ƙarfi yasa hannunshi ya dafe ƙahon zuciyarshi, tare da kuma maimata. "Hasbunallahiwani'imanwakil". Sabida ji yayi tamkar zuciyarshi zata fasa ƙirjinshi ta faɗo ƙasa. Jalal, Jamil, kuwa ido suka zuba mishi, sabida ganin yadda ya rumtse idonshi, sabida suna bakin ƙofar motar, sune ma suka buɗe mishi marfin. Haroon kuwa da Hashim da Laminu, jira suke ya fita kafin su fita. Cikin mugun tsana Laminu ya kalli Jabeer ɗin da ya yunƙura ya fita, zuwa yanzu, wani irin harbawa da tsalle zuciyarshi keyi, wani irin masifeffen fargaba, da kaɗuwa ne suka dirar masa lokaci ɗaya. A hankali duk suma su Haroon suka fito, a tsakiya sukasa Jabeer kana bayinshi na biye dasu a baya. A hankali ya gyara tattausan al'kyabbar jikinshi, tare gyara hiramin kanshi ya kange kekyawar fuskarshi. Takun da yakeyi ne ya ƙarawa shigarsa ta al'farma daraja, ya fito tamkar balarabe, gaba da baya, kamalarsa da kwarjini shi ya cika dukkan idanun bani adam dake kan doron ƙasar wannan wurin. Ya Hashimu ne da ya samu ya dawo gida jikinsa da sauƙine, yayi wani irin kabbara mai ratsa zuciya, cikin sanyi yace. "Ziyararku tayi haske sabida kun zo mana da mai hasken addini a jiki da zuciyarshi". Ga mamakinshi sai yaji Ɗanzagi na cewa. "GARKUWA ya amsa Sheykh Jabeer Jikan sarki tsatson sarki gaba da baya". Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali yake takunda yasa al'kyabbar sa buɗuwa tana bajewa, sabida ɗaga hannunshi da yayi yanai musu sallama irin ta addinin Musulunci. Mafi akasarin mutanen tafukan hannunshin suka zubawa ido, sabida kai da ganin tafin hannunshi kasan ya gauraye da ni'imar ambaton sunan Allah da rike littafi al'ƙur'ani, da kuma jin daɗin. Shi kuwa Jabeer ƙara sarƙafe carɓin shi yayi cikin yatsun hannunshi, kana, ya fuskanci gefen hagunshi, ya ɗanga musu hannu tare dayi musu sallamar kamar yadda yayiwa yan gefen damanshi. A haka har suka isa tsakiyar ƙaton filin. Inda Lamiɗo da sauran tawagarsa ke zaune. Bisa fararen kujerun robar da anka jera musu cikin rumfar suka zazzauna. Bayan sun amsa musu sallamar da sukayi. Cikin nitsuwa Lamiɗo ya kallesu tare gyara zamanshi. Muryar Ɗanzagi ce ta karaɗe wurin da cewa. "Gyara kimtsi. A saurara dai Lamiɗo jikan ɗan Lami Bubayero jikan Lamiɗo Joɗa zaiyi mgna". Wani irin harara suka watsawa Danzagin, shi kuwa Lamiɗo cikin nitsuwar datattaku tace. "Da farko dai zan fara da baku haƙurin zalumcin da akayi, muku, Allah ya jiƙan wanda suka rigamu gidan gsky." Da ƙarfi Ɗanzagi yace. "Amin". Su kuwa dattawan ido kawai suka zuba mishi. Shi kuwa Lamiɗo a hankali yaci gaba da cewa. "Ina mai baku haƙuri da kuma umarnin kada kuce zaku ɗauki mataki domin ramuwa." Kamar daga sama sukaji Muryar Bakur yana cewa. "Babu wani sarkin da ya isa ya hanamu ɗaukar fansa sai, Ubangijin daya busa mana, numfarfashi". Da ƙarfi Wani dogarin ya ɗago zabgegiyar bulalarshi ya zabgawa Bukar. Wanda saida yayi tsalle ya kurma ihu. Cikin tsauri Lamiɗo ya ɗagawa duka fadawanshi da hadimanshi da dogara shi hannu alamun kada su sake dukan kowa. Saura su Waziri kuwa duk shiru sukayi, Jabeer kuwa, a hankali yaci gaba da tasbihin da yakeyi, sabida danne abinda yakeji zuciyarshi nayi. Shi kuwa Lamiɗo cikin sanyi ya fara mgna, dan yasan zafin rashin da sukayi ne yasa sukace sai sun rama, a hankali ya kalli fuskokin dattawan da yasan sunje mishi har fadanshi dan neman zaman lfy, cikin kula ya kalli Arɗo Bani tare da cewa. "Arɗo Bani zaku haƙura, hukuma da masarauta ta bi muku kadun cutar damu da akeyi, ko zaku ɗauki makami dan ramawa?". Cikin tarin kufula da harzuƙa da kuma son cinma wata gagarumar manufar da ya daɗe yana fatan ya samu da sai yau, fuska a haɗe yace. "Babu wani wanda zan kuma hana ɗaukan makami, Dan kare kanshi da ramuwar kisar gillan da akeyi mana." Cikin tarin Mamaki da al'ajabi Bappa da sauran dattawan suka buɗe baki tare da kallon Ardo Bani, Jabeer ma idon ya buɗe cikin sanyi yace. "Baba Ardo kayi haƙuri, muyi aiki da al'ƙalami, domin al'ƙalami yafi tokobi, ina nan inata shirin samar da tsaro na musamman kan FULANIN ƙasarmu da nake shugabanta." Cikin nuna tsantsar fushi da son fusata Lamiɗo Arɗo Bani ya dakawa Jabeer tsawa tare da cewa. "Kada rufe min baki, meka sani akan Fulani? Me ruwanka damu? Damuwarmu ta shafeka ne? Ina kake sanda ake kashe mana mata, yara, jikoki, mu kanmu bamu tsiraba, in munje mun kai kukanmu a koremu tamkar karnuka, sabida duk baku san darajar fulani ba." Cikin sauri Ɗanzagi yace. "Hattara dai Ƙaramin Ardo, wannan sarkine na fulɓe masarautar filɓe ce gaba da bayanta". Cikin ɗaga Muryar Ardo Bani yace. "Tafi can baƙin bawa, bawan banza bawan wofi mai ka sani kan fulɓe, meka sani banda bauta da fadanci, masarautar da kuke bautawa bata san menene fulɓe ba". Cikin sauri Waziri ya yunƙura zaiyi mgna, da sauri Lamiɗo ya dakatar dashi, sabida zuwa yanzu zuciyarshi ta fara tafasa, yaya daga kawowa mutane ziyara dan ja-jantawa suke neman tozarta mushi masarauta. Cikin ɓacin rai ya kalli su Bappa daketa kama hannun Arɗo bani daketa fizge-fizge yana kwaza musu baƙar mgna, cikin fushi yace. "Masarautar Joɗa ɗince bata fulani ba?". A harzuƙe Arɗo Bani yace. "Tabbas dan data fulanice, da an bamu kariya da tsaro, da an duba kukanmu, a kashemu a hanamu ɗaukar fansa, an kuma kasa bamu tsaro. Nan da mukaje ina shi jikan naka da yake matsayin Garkuwan Fulani, yana can ƙasashen woje, da iya dukiyar da ake bashi tsaro da kariya shi rai ɗaya ta kai a kula da fulanin daji dubu a kuma basu tsaro. Yau kwana uku da kashe mana mutane sai yau zaku ɗebo manyan riguna kuzo mana da batun wai kada mu rama, sara da suka da yanka mana mutane da akeyi, Kaida kab zuriyar ka da masarauta ka, babu mutun ɗaya da zai iya jurar koda bulalar *(SHAƊI)* ma bare sara da yanka da suka da wuƙa a hakan kuke ganin kanku Fulani". Cikin tarin zafin ƙuna da tafasar zuciya Waziri yace. "To me kuke so muyi muku, tun randa akayi abun munzo bamu sameku ba". A harzuƙe Bukar yace. "Ƙarya ne babu wanda yazo". A hankali Jabeer ya buɗe baki da nufin zaiyi mgna sai yaji Lamiɗo na cewa. "Uhum jinina kuke cewa ba fulaniba, to ko jaririn da aka haifa yau a jikin masarautar Joɗa zai iya jurarar bulalar SHAƊI bare manya ko ɗan baiwa zai iya bare jinina ƴaƴana ko jikokina, ko kun manta masarautar Joɗa ce tushen Shaɗi?". Cikin son harzuƙa Lamiɗo Arɗo Bani yace. "A da can baya ba, yanzu kuma da aka san lusarai ake haifa a masarautar inji an haramta shaɗi a masarautar, yau in kun isa fulani ka bada ɗan ka ko jikanka ayi gasar Shaɗi dashi, in ya iya jurewa, to mun yarda mun gamsu ku fulanine ku masarautar Fulani, in kuwa kun kasa fidda goninku to, ku ba masarauta fulɓe bace." Wani irin karkarwa jikin Lamiɗo ya fara sabida fusata, wai suda masarautarsuce tushen fulɓe a ƙasar, su ake cewa ba fulani ba, har ake kiransu lusarai, Galadima, Waziri, Wambai, Ɗan iya, Ɗan buram, Ɗan Maliki, Sarkin Dawaki. Gaba ɗaya hankalinsu yayi masifar tashi sabida ganin tsananin fushi da tashin hankalin Sarki Lamiɗo. Jamil Jalal Haroon kuwa , hankalinsu na kan Jabeer bisa alamun yana cikin wani hali. Shi kuwa Jabeer bugun da zuciyarshi keyi ne yasa, Hankalinshi tashi, ƙarfin addu'o'in da yakeyi ne, yashi iya fahimtar abinda suke cewa. Kamar daga sama kamar cikin mafarki, sukaji murya Lamiɗo na cewa. "Ga jikana, Jabeer GARKUWAN FULANI, na badashi a matsayin matashi mai yin gasar Shaɗi ku fito da duk gwanin da kukega shine makurar gwayen yankinku. Ayi Shaɗi dashi yadda zaku samu gamsuwar yakai matsayin ya kasance GARKUWAN FULANI". Tunda ya amɓaci sunan Jabeer, Sarkin Fada yayi wani irin murmushi mai cike da jin daɗin alamun burinshi zai cika. Hakama Arɗo bani wani irin asirtaccen murmushi yayi. Jala, Jamil, Haroon, Hashim, Imran, Galadima, kuwa wani irin zazzaro ido sukayi. Cikin tsananin kaɗuwa da firgicin batun Lamiɗo suka zuba mishi ido. Bukar kuwa cikin karaji yace. "Ba'ana Bukar shi zai kara dashi." Ya ƙarishe mgnar da fatan Ba'ana ya kashe wanda aka kira da Jabeer tunda jikan Lamiɗo ne. Jabeer kuwa wani irin kallo yayi kakan nashi, irin kallon nan. Na lallai kam tsohon nan ka haukace, ka zauce, ai bani bakam ko inuwata bazaku kuma gani a garinkuba bare kuyi wannan gwajin dashi. Ga mamakinsu kab sai sukaji Arɗo Bani na cewa. "A yau ɗinan kuma Yanzun nan, a kuma nan za'ayi gasar Shaɗi in har kun isa fulani." Sosai Lamiɗo yaji hakan bai mishi ba dan a zotonshi za'asa ranane ya koma ya shirya Jabeer kafin ayi gasar, to fahimtar ƙuresu suke neman yi, yasashi gyara zamanshi cikin danne fargabanshi na anya Jabeer zai iya jura yace. "Na Aminc....! Yau bisa wani uzuri ban samu yin posting da wuriba, kana kuma ba editing a gurguje na watsoshi, bari in nemo PAGE 16 ko zuwa yan da yamma ne. By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘 *GARKUWA* PAGE 16 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘 *FREE PAGE SUN ƘARE DAGA WANNAN PAGE 16 DIN IN DAI KIKAGA LITTAFINA GARKUWA BA TARE DA KIM BIYA NA SAKI A GROUP BA TO NA SATANE, DAN ALLAH DA MANZONSA KADA KU FITARMIN DA LITTAFI DAN ALLAH KU BARI IN SAMU KUƊI zuwa makka😂😂😂* *Littafin GARKUWA na kuɗine dan Allah da Manzonsa kada ki karanta na sata, kada ki watsamin littafi a sata, turo katin MTN na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 ki biya ki karanta cikin aminci ba tare da haƙƙi naba. Ko kuma ki biya 1k domin shiga Special Group wanda cikin sati biyu rak za'a gama Part 1, da izinin ubangiji kana a shiga 2, turo dubunki ɗaya ta wannan asusun 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidan biyanki ta wannan number 09097853276 in baki da halin biyan dubu ɗaya ko baki da ra'ayi kina iya turo ɗarinki uku kacal da ban tsauwalaba sabida halin rayuwa da muke ciki. Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki kada ki sai littafina in dai kin san niyarki ki saya ki fitar da shine in kuma. Har kin sayane to dan Allah da Manzonsa gaya min in baki kuɗinki in cireki a group na, dan Allah🙏🏻 nace badon niba* "Na Amince!". Cikin tarin mamaki Jalal, Jamil, Imran, Haroon, Hashim, da duk sauran tawagar Lamiɗo suka, zazzaro ido cikin tarin mamaki da al'ajabi, sam basuyi zaton jin haka daga gareshi ba, Ya Salmanu kuwa wani irin farin cikin mara misaltuwa ne, ya rufewa, domin yana ganin ikon Allah da yake nuna mishi zahirin abinda yake nuna mishi a mafarkansa tsawon kwanakin da yake a gadon asibiti. Ba'ana kuwa da tun ɗazu ya iso, wani irin ihu yayi mai cike da farin ciki, da jin daɗin yana ganin zaiyi abinda gaba ko kashe mutanen Rugar Bani sukayi gaba ɗaya, masarautar Joɗa bazata kulasuba, Wani irin tsuma da karkarwa jikinshi keyi sabida azabar muguntarsa dake tasowa. Arɗo Bani ma wani murmushi manufa yayi tare da cewa. "To, ina gwanin naku?". Cikin karaɗi Ɗanzagi, ya kalli Jabeer tare da cewa. "Malami ba faɗen Allah, malamai magada annabawa, Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa, GARKUWAN sarki Lamiɗo, jikan sarki, mai martaba Nuruddee. Jarumin Masarautar Joɗa." Gimtse bakinshi yayi ganin wani irin kallo mai ma'anoni da yawa da Jabeer ke watsa mishi, Cikin yin ƙasa da murya tare da tsuke fuskarsa, ya ɗan ronƙofo kanshi, kusa da Lamiɗo murya a kausashe yace. "Wannan tatsuniyar da kukeyi, bafa koyarwan shariya bace". Da sauri Lamiɗo ya katseshi da cewa. "Eh amman koyarwar Masarautar Joɗa ce". Cikin kufula yace. "Ya ina ce maka Allah kana cemin gadon masarautar Joɗa ce". Cikin haɗe fuska da ƙasaita Lamiɗo yace. "Eh ba addini bane, kuma sai an yishi dan gadon masarautar muce". Kanshi ya kuma motso dashi jikin kakan nashi cikin taɓe fuska yace. "Okay to ai sai ka tashi, ka tsaya su zaneka ciki da woje". Cikin kausasa murya Lamiɗo yace. "Kai ne dai zaka tashi". Cikin watsawa kakan nashi wani kallo na lallai ma tsohon nan kanka ya kwance yace. "Ai bani bane sarkin, kaine sarkin ko?". Cikin faɗa Lamiɗo yace. "To ko Ubanka bai isa in sashi abu yace bazaiyi ba". Jin muryar Lamiɗo ta ɗan yi samane, yasa fadawanshi suka miƙe tsaye, Ware rigunansu sukayi, suka kamgesu da jajayen rugunan nasu, ta yadda babu mai ganinsu, Cikin haɗe fuska Jabeer yace. "Yesss shi bazai ƙiba, tunda kai ubanshi ne, Ni kuwa babu wanda zai sani in zauna in bawa wani ƙaton fatar jikina ya zane, kai jimin zancen son zuciya, kai ni kaɗaine jikanka, a duniya, a nanma baga Ya Hashim ba ai shine babban jikanka, zancen gsky na gaji da wannan tirsashe-tirsashen naku, kanada ƴaƴan ai, ka kira ɗaya daga cikin ya'yan ka yazo ya wakil ceka mana, Amman ni dai kam Muhammad Jabeer babu wani tsohon da zanyiwa mubaya'a in tsaya wani gardin makiyayi ya ɗimeni, tunda ba faɗin Allah bane". Ya ƙarishe mgnar yana yunƙirin tashi tsaye. Da sauri Galadima yasa hannu ya kamo nashi, fuskar ya kwaɓe tare da komawa zaune yana gyara hiramin kanshi da al'kyabbar jikinshi, Cikin tausasa harshe Galadima yace. "Jabeer kafa san ma'anar GARKUWA a masarauta." Cikin sanyi da ganin kima da darajar dottijon Jabeer ya kwaɓe fuska tare da cewa. "Nifa shiyasa wannan mulkin bawai sonshi nakeyi ba, sabida wannan tsarabe-tsaraben daba na addiniba, a buwayi mutun dashi, yaya nasan abu ba Allah ne da manzonsa suka wajabta mana shiba, ace in zauna a cutar dani." Cikin sanyi Waziri ke jujjuya mishi kai a hankali yace. "Jabeer Garkuwa fa, kake dole ka kare martabar Masarautarmu kana ka nunawa su fulanin da kake Garkuwarsu kai Jarumine". Rai a ɓace ganin sufa da gske sukeyi, cikin dakiya yace. "Bana so, ita wannan sarauta ta GARKUWAN FULANI ku bawa duk wanda kukeso, ni ban nemaba dama". Shiru Haroon yayi dan gskya harga Allah shi wannan abun yazo masa a bazata. Jalal kuwa cikin haɗe fuska yace. "Wannan ma ai zancen banza ne, An bawa Ya Jafar Galadima, ko kwana ashirin baiba a kai, aka birkita masa rayuwa, kana yanzu kun likawa Hamma Jabeer wani GARKUWA kun kwasomu kun kawomu Rugar fulani, wai kuna cewa ayi gasar duka dashi." Da sauri yayi shiru ganin Jabeer ya ɗaga mishi hannu. Jamil kuwa tuntuni idonshi ke tsastsafo ruwan hawaye dan gani yake so ake a kashe Hammansu a ƙarar da ƴaƴan ɗakinsu, Laminu kuwa ɗan Gimbiya Saudatu matar bappansu Sheykh kuma Kani ga Yah Hisham wani irin dariyar jin daɗi yakeyi. Shi kuwa Lamiɗo, wayarshi ya zaro, Mai alfarma Sarki Jalaluddin ya kira wanda yake kane ga Jabeer. Wanda ya haifi Mamanshi. Bayan sun gaisane yayi mishi bayanin abinda ke faruwa, jin haka yasa yace ya bawa Jabeer wayar. A tsakar filin Rugar Bani kuwa, tuni. Arɗo Bani ya bada dama na suduka yana shekantawa gari cewa. Ana gamgamin Shaɗi yanzu-yanzu tsakanin Ba'ana da kuma jikan Sarki Nuruddeen. Tuni an firfito da ganguna anata kaɗe-kaɗe da bushe-bushen sarewa, kana ana buga babban gangan dake tsanar da makotan Rugar Bani sauran rugage alamun za'ayi Shaɗi yanzu. Kafin kace kobo, Rugar Bani ta cika tayi maƙil da mutane, Maza da mata, matasa da tsoffi, sabida an san duk sanda za'ayi Shaɗi ana bada sanarwar, kwana uku kafin nan to jin wannan na gaggawa kuma da jikan Sarki za'ayi yasa, mutane taruwa, gashi ranar jumma'ace, duk matasan rugogin suna, gida tunda suka dawo sallan jamma'a. Rugar Bani ta cika tayi maƙil da bani adam, tako wacce kusurwa tsastsafo akeyi kusufa-kusufa. Jin karan tamɓarin ganganr Shaɗi ne ya ƙara gaiyato mutane harda na cikin garin Shikan, tuni ƙabilun Bonon sun garzayo cikin Rugar Bani. Bukar kuwa mahaifin Ba'ana shida kanshi yaje, cikin Garkensu ya ɗauko tukunyar tsumin bulalim shaɗin da Ba'ana ke tsumasu da dafin kunamai da sauran sihirurruka, na dodon tsafinsu Bonon. Matasa majiya karfi ne keta ɗebo ruwa, cikin rijiyoyin garin. Suna jiƙa taron wurin dandamalin, da za'ayi gasar kaɗe-kaɗen duk sun taru sun cika kunnen kowa. Jabeer kuwa bugun da zuciyarshi keyi shiyafi komai tada mishi hankali. A can cikin gidajen Rugar kuwa, duk yan samari da yara sun firfito. A gidansu Shatu kuwa, Tunda taji Shelan da Nasuduka yakeyi cewa gasar Shaɗi tsakanin Ba'ana da jikan sarki. Kuka ta farayi, cikin tashin hankali da kiɗima ta kamo hannun Ummiy da tayi shiru sai ido take binsu dashi, murya na rawa tace. "Ummiy kijifa, zasuyi ya kashe, wani wanda baijiba bai ganiba, sunfa san illar dake cikin bulalinshi." Ganin Ummiy dai ba mgna zatayi ba, yasa ta kamo hannun Junainah cikin tsananin tashin hankali tace. "Junainah ki gudu, kije kicewa Bappa kada ayi gasar nan, Ni dai a bari na haƙura zan auri ya Ba'ana a yadda yake, zan zauna dashi, zanyi ƙoƙarin gyara mishi, rayuwa na gaji, kada a sake cutar da wani a kaina". Da sauri Rafi'a ta kalleta jin ta kamo hannunta cikin zubda hawaye tace, "Rafi'a wlh ya Ba'ana zai iya kashe mutun a kaina, da dafin kunamai yake tsuma bulalinshi, da wani tsafin, me ribata ayi ta cutar da mutane a dalilina, babu fa wani mahaluƙin da zai iya cin Ya Ba'ana gasar Shaɗi, babu wanda zai iya jurar azabar bulalinshi fa." Cikin sauri ta miƙe tare da miƙar da Junainah, sai kuma duk suka koma suka zauna, Jin muryar maƙocibsu Sarkin aska, yana cewa. "A a Shatu kada ki tura kowa, kada kuma kije kin tsumayi sakamakon gasar yau in sha Allah zata banbanta da na baya . Yanzu ma Arɗo Bani ne ya aikoni da in gargaɗeki." Yana faɗin haka ya juya da sauri ya fita, kana ya nufi wurin gasar. Da ido suka bishi. Ita kuwa Junainah da sauri ta miƙa ta nufi kitchin ɗin su, tana cewa. "Yauwa Adda Shatu, barin in kawo mana gasassun zabbin da Ya Ba'ana ya kawo mana muci. Ɗazu da nace muci Adda Rafi'a ce, tace mujiraki." Cikin sanyi Rafi'a tace. "Yauwa Junainah kawo mana, muci yau tunda gari ya waye bamuci komaiba." Gyara zansu sukayi, kana ta kalli Shatu cikin kula tace. "Dan Allah Shatu muci abinci, kinga Ummiy ma taƙi cin komai ganin, yadda kiketa kuka tunda kikaji ɓatansu ya Giɗi da rasuwar Ya Lado da Inna." Cikin zubda hawaye ta gyaɗa mata kai, sabida ita kanta tasan tana jin wani irin masifeffen yunwa, tamkar zai kasheta. Da sauri Junainah ta nufosu riƙe da akoshin gasassun zabbin da aka zuba dafin macijin a cikin. A can cikin tsakiyar garin Rugar Bani kuwa. Tuni su Ba'ana an gama shiryawa zalumci, domin dama ai a ƙa'ida shi zai fara duka, Yana tsaye sai zagaya filin yake yana zane iska, makaɗa da mabusa nata yi mishi kirari. A cikin wurin da Fadawa suka kange Lamiɗo da tawagarsa kuwa, anata kai ruwa rana da Sheykh Jabeer, Cikin kufula, yake cewa Sarki Jalaluddin da suke waya dashi. "Nifa babbar matsalarta wannan abun da za'ayi ba *Sunna* bace ba kuma *Farilla* bace, ba kuma *Mustahabbibace*, kai ko a babin *Makaruhi* ban taɓa cin karo da wannan banzar al'adar da kukeso in yarda ayita dani ba, Ina kuma da yaƙini in da zan bajeta a babin musulunci, kai tsaye za'a iya karhantashi, sabida ai cutar da kaine kuma, Musulunci bai yarda mutun ya cutar da kanshi ba, haka kurum kuce wai in tsaya a zaneni, inji shi kanshi kakan Lamiɗon Joɗo da yaji haza a gasar Shaɗin shine ya hana wannan al'adar a masarautarsa sannan yanzu ace za'a saketa a kaina bayan tsawon shekaru 145 ba'ayishi ba, tun zamanin jahiliyan ma an bar abu sai yanzu ku tara abu a kaina, to wallahi bafa zai yiwuba." Cikin kufula Sarki Jalaluddin yace. "To ya kakeso ayi ɗan masu ilimi kowa jahiline sai kaine mai ilimi sabida tsabar tsoro da ɗan karen son jiki kana gudun abinda zai taɓa lfyarka shine zakayi ta jawo mana wasu dogin falsafofi, a hir ɗin kafa Jabeer ko uwarka bazan sata abu taimin musuba". Gaba ɗaya sun hautsuna mishi zuciya, Ji yadda suketa zageshi, dan kawai yace bazaiyi abinda al'adace ba addiniba sai wani ce mishi suke ko uwarka ko ubanka, bayan sun san baya kuran hakan, rai a ɓace yace. "Uwata kace ai tunda ita ai ka haifa ba niba ko?, zancen gsky bafa za'ayi wannan abunba, sun daɗe basu ce mana lusaraiba, dolene, sai sun yarda mu fulanine, kai yau nifa ba bafulatani bane. A kirani da ko wacce ƙabilar ma in anga dama aikin kawai!". Yana faɗin haka ya katse kiran. Laminu kuwa da yake cikekken ɗan jarida, tuni yana naɗe komai a faifai jawaban su. Shi kuwa Sarki Jalaluddin, ido ya zubawa wayar jin jikan nashi ya katse kiran, murmushi yayi, irin nasu na manya, kana da sauri ya kira, Umaymah. A can Babba birnin Katsina, kuwa Gimbiya Khadijah Umaymah kenan , wacce take matar ɗan Sarkin Tsinako, Kekkyawar mata mai cikar haiba nitsuwa, tana kishinɗe, bisa wata tattausar doguwar kujera, yayinda Hadimanta biyu ke mata tausa. Jin wayarta na suwane, yasa ta buɗe idanunta dake lumshe, tunda sukayi waya d, ɗan ta Haroon ke gaya mata inda sukaje da ƴaƴan ƴar uwarta mafi soyuwa a rayuwarsu ne, taketa murmushi. Ganin sunan mahaifinta ne yasa tayi saurin amsa kiran. Bayan sun gaisane, Sarki Jalaluddin ya ɗanyi murmushi cikin nitsuwa yace. "Khadijah, kira ɗan ki, ki bashi umarnin bin umarnin mu, domin yana nuna mana ai bamu muka haifeshi ba, bazamu tirsasashi ba". Cikin tarin girmamawa tace. "Ranka ya daɗe, me kukeso in bashi umarni a kai nasan bazaiyi min musuba". Cikin jin daɗi yace. "Kice dashi ya amince da gasar da za'ayi". Cikin sauri tace. "To An gama yanzu kuwa, in sha Allah zaku sameshi mai biyayya a gareku". Daga nan sukayi sallama, Kana ta kirashi, sau biyu tana kiranshi baya ɗagawa, sabida kanshi ya ɗau zafi yana ganin za'a tirsasashi ya cutar da kanshi. Ga wani irin azabebben tsinkewa da zuciyarshi keyi, Ji yake tamkar zata faso ƙirjinsa ta fito, tayi ta tsalle a doron ƙasa. Gashi duk tsoffin Masarautarsun sun zagayeshi. Kowa da abinda ke ce mishi. Ga uban kiɗen-kiɗen dake hawa mishi kai. Ita kuwa Umaymah ganin bai amsa kiran bane, yasa ta kira Haroon yana ɗagawa tace. "Ina Jazlaan bashi wayar". Da sauri yace. "To Umaymah uwar Garkuwa gashi nan ido ya raina fata". Cikin barkwancinta da yaron nata tace. "Kaci gidanku Haroon Ni ɗana ba ragobane". Murmushi yayi tare da cewa. "To mu gani a ƙasa mana Umaymah". Yana faɗin haka ya miƙa Jabeer wayar wanda yake cewa Lamiɗo. "Bafa zan yiba, tsohon nan gwara ka miƙe kaje ayi da kai tunda kaine sarkin Masarautar Joɗa, Ni nan babu abinda na sani bayan nonon uwata sai al'ƙur'ani da hadisai, sai likitancin da kuka sani na karanta a dole badon raina yasoba, tun ina yaro kullum Ni a cikin sani dole kuke da tsabar rainin hankali, kaje a jibgeka, Ni kuwa nayi al'ƙawarin zan jinyaceka, Lamiɗo Joɗa." Ya ƙarishe mgnar yana amsar wayar da Haroon ke miƙo mishi cikin faɗa yace. "Mitsss wai meye kaketa tura min wannan argar wayar taka ne?". Cikin mamaki Haroon yace. "Kan uba Jabeer wayar tawace ma arga, wayar da kuɗi ta sun kai rabin million To inma argace Umaymah ce bisa layi". Ba tare da ya kara wayar a kunneba yace. "Hello Umaymah". Cikin tausayi Jalal yace. "Hamma Jabeer baka kai wayar kunneba". Lips ɗinsa ya taune tare da cewa. "Au, zama su sani yin abu da yawa". Haroon kuwa mamaki yakeyi domin karo na forko kenan da yaji Jabeer yace Hello a madadin Assalamu alaikum, da shine abinda yakeyi. Ita kuwa Umaymah tana jin ya kara wayar a kunne shi ya kira sunanta cikin rauni. Murya a kausashe tace. "Jabeer". Da mamaki ya amsa dan sama da shekaru goma sha biyu kenan da Jazlaan take kiranshi, cikin sanyi yace. "Na'am Umaymah". Cikin bada umarni tace. "Jabeer ka tashi maza yanzu ka shiga fagen gasar nan ayishi da kai, bana son musu umarnine ba shawara ba". Cikin sauri ya zaro siraran kyawawan idanunshi, Dai-dai lokacin kuma Lamiɗo ya miƙe tsaye cikin tashin hankali da kiɗima da firgici da baƙin cikin dakatar da gasar Shaɗi da akayi a masarautarsu ya sani da anayi da Jabeer bazai ƙalubanceshi ba, cikin sanyi yace. "Zanje za'ayi dani, zan tabbatar da darajar masarautatarmu bata rusheba." Da ido yabi Dottijon kakan nashi wanda a ƙalla ya kai shekaru 91 a duniya. Cikin kauda kai yace. "To Umaymah yadda kikace haka za'ayi amman bari in kira Sheykh Abdulkareem in sanar mishi in ya amince dai zanyi". Da sauri tace. "A a ban yafe ka kirashi ba, wato don kasan in ka kirashi zai kira Sitti da Mai alfarma Jalaluddin da Sarki Nuruddeen ya dakatar da duk abinda za'ayin, tunda na san cemishi zakayi ba addini bane, al'adace, to ban yardaba maza tashi". Ganin Ya Hashim na miƙa masa wayarshi ne yasashi cewa Umaymah. To cikin sanyi. Yana amsa wayar da Ya Hashim ya miƙa mishi yaki Muryar, mahaifinshi cikin sanyi da kuma alamun yana kukane yace. "Jabeer ashe har kayi girman da Lamiɗo zai umarceka da yin abu kaƙi yi mishi mubaya'a, Ashe har na haifi ɗan da zai ja da mahaifina." Cikin sanyi da rauni yake jujjuya kai murya na rawa yake cewa. "A'a Abba, kayi haƙuri kada kayi kuka a kaina." Bai kulashiba yaci gaba da cewa. "Jabeer Ashe zuciyarka har tayi tauri da kangarewar da kanaji kana gani za'a daki mahaifina a gaban idonka, bazaka zame mishi GARKUWA ba, Jabeer wannan shine tukuicin tsantsar son da mahaifina keyi muka, wanda har ya jazamin ƙiyayya a wurin yan uwana sunaga ya fifitaku kan sauran jikokinsa Especially ma kai Jabeer komu daya haifa baya nuna mana son da yake nuna maka, shine zaka bari a dakeshi mutun mai shekaru 91 da ɗaya a duniya kai me shekaru 30 bazaka iya zame mishi GARKUWA ba?". Cikin rauni da ƙunar zuciya, ya miƙe tsaye hannunshi yasa ya kamo na Lamiɗo cikin tarin ƙuna da zafin rai da takaici yace. "Na Amince, zanyi gasar na yarda, ka koma ka zauna". Wani irin farin ciki ne ya ziyarci, zuƙatansu gaba ɗaya, sai dai kowa da irin manufar farin cikinsa. Jin haka yasa fadawan janye labulen da sukayi musu. Shi kuwa Lamiɗo hannunshi yasa ya kamo hannun Jabeer, cikin tsantsar farin ciki da al'fahari da ƙasaita ya fara taku, suna ratsawa cikin taron. Kana fadawansu na biye dasu a baya. Ɗanzagi yana. "Takawarka lfy Sarki mai daraja Lamiɗo ɗan Lamiɗo jikan Joɗa. Gyara kimtsi". A haka har suka isa cikin asalin dandamalin da aka jiƙashi jilak da ruwa, sabida hana ƙura wanzuwa. Gaba ɗaya taron mutanen wurin maza da mata manya da yara, Jabeer suka zubawa ido, sabida duk wanda ya ganshi yaga sahihin Balarabe, mai kamala da nitsuwa, uwa uba kima da haiba, ƙwarjini shi ya cika dukkan idanun magautanshi dake wannan yanki, yayinda masoyanshi ke taraddadin abinda zai faru. A tsakiyar filin suka tsaya, hannunsu dake raƙe dana juna Lamiɗo ya ɗaga tare da fuskantarta gabas, kana ya juya yamma, ya kuma juyawa kudu da Arewa, sannan suka dawo tsakiyar filin, Cikin ƙasaita, yace. "Ga GARKUWAN FULANI, kuma daga Wannan nasarar da zaiyi a gasar nan, Zai tabbatar GARKUWAR Masarautar Joɗa, GARKUWA kuma mai ikon zama inda yaso a cikin fada". Dariya Bukar yayi kana ya ɗaga hannun Ba'ana da yaketa wani abu da ƙirjinshi kamar damisa, Cikin isa da yaƙini da al'fahari yace. "Mu kuma ga namu Garkuwan, da muke da tabbacin bai taɓa gasa ya faɗiba". Sake hannunshi Lamiɗo yayi kana ya juya ya koma ya zauna, cikin rumfar da akayi musu masauƙin. Al'ƙalin gasar ne yazo tsakiyar taro, kamar ko yaushe, hannun Ba'ana ya kamo, ya ɗaga sama, hakan yasa, gaba ɗaya makiɗa da mabusa suka ƙara sautin kiɗe-kiɗen su, wanda Jabeer ke jinsa har tsakiyar kansa, Allah ya sani, baya son hayani koda dai-dai da ƙwayar zarra ne, ga wani masifeffen fargaba da tsinkewar da zuciyarshi keyi, yanaji tamkar yasa hannunshi ya toshe kunnuwanshi. Ɗan wani gajeren tsaki yaja sabida Allah ma ya sani baya son kallo, to kuma yanajin yadda idanun mutane ke yawo a jikinshi. Shi kuwa al'ƙalin gasar, yana sake hannun Ba'ana yazo ya kamo hannun Jabeer, Da sauri ya juyo ya kalleshi sabida kamo hannunshi da yayi sai yaji tamkar hannun jariri ya kamo dam laushi da taushin fatar, hannun sanyi ƙalau, girgiza kanshi yayi cikin tausayawa, sabisa, ya za'ayi ace mai wannan taushin hannun fatarsa ta iya jurar azababbun bulali masu masifar zafi. Ɗaga hannun Jabeer yayi sama. Yana mai nunawa taron mutanen shi a matsayin dashi za'a gwabza. Shi kuwa Sheykh Jabeer, duk abinda akeyi idonshi na cikin ɗan siririn farin galashi mai garai-garai dake liƙe a fuskarshi, Hannunshi kuma riƙe da carɓinshi, kana bakinshi ambaton sunan Allah. Cikin tarin mamaki ya kalli, Al'ƙalin gasar tare dasa hannunshi ya riƙe bakin al'kyabbar jikinshi cikin haɗe fuska yace. "Me hakan!?". Cikin saurin rusunar da kai Al'ƙalin gasar yace. "Za'a cire kayan jikin naka ne!". Cikin tarin mamaki ya zazzaro ido waje, a baiyane yace. "Akan me kenan, suturar da Allah yayi min a matsayin mulmi, in killace kaina, shine zaku yayemin a cikin dubban dubatan mutane?". Cikin dakiya Al'ƙalin ya ɗan kalleshi domin kwarjinin Jabeer ya cika masa fuska cikin sanyi yace. "Allah rene, ƙa'idar gasar ce, ba'ayi da kaya a jikin mutun sai ɗan kamfai, kawai ake bari a jikin mutun". Cikin kufula da harzuƙa yace. "To bada niba, Ni nan Muhammad Jabeer wallahi banyi lalacewar da zan tsaya tsirara a gaban jama'a ba". Yana faɗin haka ya juya a fusashe, zai fita cikin taron. Ganin hakane yasa Galadima, yayi saurin tasowa, kana Ɗan buram na biye dashi a baya, tareshi sukayi tare da kamo hannunshi. Da sauri suka juyo suna. Kallon gungun wasu matasa wanda suka kece da dariyar ƙeta cikin hausarsu ta ƙabilu suke cewa. "To ku ɗan naku ko yadda ake gudanar da gasar ma bai sani bane? Ya zaiyi zaton da wannan shigar tasa za'a dakeshi, to ai ko bulali dubu za'ayi mishi ba jinsu zaiba, Kai Ɗan kazagi, ka gaya mishi nan ba cikin masallaci bane. Nan wurin shaɗi ne". Jiyo hakane ya sa ran dukkan musulman wurin ɓaci. Sabida sun fahimci kafuraine masuyin wannan zancen. Galadima kuwa da Ɗan buram sun ɗauka abin wasane, a zatonsu zasu shawo kan Jabeer a sauƙaƙe, amman ina ya tiƙe yace babu wani zinɗiƙin ƙaton da zai sashi ya yaye suturar dake jikinshi. Dariyar da su Arɗo da sauran mutane keyine ya hautsuna lissafin Lamiɗo. Cikin harzuƙa ya taso, har kamar zaiyi tuntuɓe ya nufi inda su. Waziri, Wambai, Ɗan buram, Ɗurɓi, Da Galadiman, cikin tashin hankalin alamun akwai wata babbar manufa da Galadima ke son cimmawa cikin lamarin ya riƙe hannun Jabeer tare da cewa. "Haba Jabeer kai wanne irin mutun ne mai kafiya da taurin kan tsiya, yaya muna binka kana zillawa, muna haɗaka da Allah da Manzonsa amma kana tunzuramu, wallahi da yau sai anyi gasar nan!". Cikin tsananin ɓacin rai yace. "In tsaya a tozarta ni kuke so. Ayimin tijara kukeso, da wanne idon zan kalli al'ummar Annabi da jiki tsirara". Cikin kufula Waziri yace. "Waya ce maka tsirarane?". Murya a sama yace. "Tsirara ne mana! Tunda sunce wai dagani sai Boxes zan tsaya, ka kuwa san ko Mahaifiyata data haifeni tun ina shekaru shida a duniya bana tsayuwa a gabanta dagani sai ɗan kamfai, tunda nake Mahaifiyata, Mahaifina, Yayuna, Uncles, na Aunty's na, babu wanda ya taɓa dukana, sabida ban cutar dasu da komaiba bare su hukuntani da duka haka kurum rana tsaka kunce in tsaya a dakeni, na yarda, sannan yanzu kuma ace nai tsirara, kai bafa wanda zan yiwa mubaya'a akan hakan..!." Tas! Yaji sauƙan wani irin gigitaccen mari sai dai babu wanda ya ga sauƙan marin sabida suna tsakiyarsu Waziri ne, kuma sauran mutanen garin duk kowa bayan su Waziri suke iya gani. A harzuƙe ya ɗago kanshi, Lamiɗo ne ya gani tsaye a gabanshi. Jan hannunshi yayi da iya ƙarfin shi na tsufa. Tsakiyar filin suka koma, cikin fushi yace. "Galadima zoka cire mishi kayan." Da sauri Galadima ya motso gabanshi. Su Waziri kuwa duk suka koma cikin Rufarsu masauƙinsu. Wani irin tsuma da karkarwa jikin Jabeer ya farayi, tun sanda yaji sauƙan marin. A take idanunshi nan su kaɗa sunyi wani irin masifeffen juyewa sunyi jazir, Hatta lips ɗinshi karkarwa sukeyi. Wani irin tarin baƙin cikin da bai taɓa jin irinsa ba a duniya ne, ya lulluɓe masa zuciya. Koda randa Ya Jafar ɗinsu ya zauce, baiji makamancin wannan ɓakin cikinba. Ji yakeyi Tamkar ya haɗiyi zuciyarshi ya mace ya bar duniyar kowama ya huta, Rumtse idonshi yayi da azaban ƙarfi lokacin da yaji, Galadima ya gama komce masaƙalan al'kyabbar jikinshi, kana ya buɗe shi, yayi ƙasa dashi, har saida ya cire hannayenshi a ciki. Haroon dake gefensu ya miƙa wa al'kyabbar, kana a hankali ya kuma matsowa gareshi, hannunshi yasa saman kanshi ya ɗage zagayen baƙin abin da yake kan Hiramin, kana yasa hannunshi ya janye hiramin. Kekyawar fuskarshi ta fito ras, tattausan baƙin gashin kansa dake kwance lib-lib ya baiyana, wanda hakan yasa kaso 70 cikin ɗari na dubban mutanen dake wurin suka zuba ƙwayar idanunsu kanshi, da yawa tasbihi da ta'ajjudin irin kyau da haibar da Allah ma ɗauka kin sarki yayi mishi sukeyi. Jalal kuwa ji yake tamkar ya rinƙa kurma ihu, Allah yasani baya son abinda zai cutar musu da Hammansun, Jamil kuwa tuni hawaye yake zubdawa, Ya Hashim, Imran, Sulaiman, kuwa dukkansu sunkuyar da kawunansu sukayi ƙasa. Laminu kuwa wani irin masifeffen jin daɗi yakeyi, hakan yasa ya ƙara kutsowa cikin filin hakan ya bashi daman yin viewing da kyau. Shi kuwa Jabeer tafarfasar da zuciyarshi keyi yayi masifar tsananta lokacin da yaji, Galadima ya zare mishi tattausar rigar shaddar dake jikinshi. jin yasa hannunshi yana shirin zare mishi singlet ɗin jinshi ne yasashi, ƙara ambaton sunan Allah da sauri-sauri, sabida ji yakeyi tamkar ya buɗe ido ya shaƙo moƙoshin Galadima sai ya sumar dashi, tabbas da ace al'ƙalin gasarne ke cire mishi kaya da tuni ya daku. Cak ɓari da karkarwan da jikinshi keyi ya bari, Lokacin da yaji Galadima yasa hannunshi ya kwance zariyar dogon wondon jikinsa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun, Hasbunallahiwani'imanwakil. Allahumma ajjirni fi musubati!!.." Ƙasa idawa yayi, jin an saɓule wondon jikinsa yayi ƙasa, da ƙarfi ya buɗe kwayar idanunshi da suka koma tamkar garwashin wuta. Tafarfasar da jininshi keyi shine abu mafi tartsatsi a rayuwarsa. Hannunshi Galadima ya jawo da ƙarfi wanda dole yasa ya ɗaga sawunshi ya tsallake wondon ya zama babu komai a jikinshi dagashi sai Boxes wanda Allah yayi mai ɗan tsawone yazo har kusa da guiwarsa saidai a matse yake. A tsakiyar filin ya tsaidashi kana ya juya ya koma ya zauna kusa da Lamiɗo. Jalal ne ya sunkuya ya ɗauki wondon da sauri ya miƙa wa, Haroon. Shi kam Jabeer zuwa yanzu, Ya sani a duniya ba'a taɓa yi mishi tozarci sama da wannan ba, ji yakeyi a duk faɗin duniya babu garin daya tsana sama da garin Rugar Bani, bai taɓa jin haushi da tsanar wani abu a duniya ba sama da mutanen garin Bani, ji yakeyi ya tsanesu gaba ɗayansu, ya tsani komai nasu, baya so da fata da sha'awan komai nasu. ƙasar garin ma da yake tsaye a kai ya zuba mata ido ji yake tamkar ya ƙonata ta sauya launi daga farin yashi zuwa baƙin yashi. A tsakiyar taron kuwa, da sauri al'ƙalin gasar ya jawo hannun Ba'ana da ya zaro wata asirtaciyar bulalar tsamiya, daga cikin randar bulalinshi sai wani motsi bulalar keyi tamkar tanada rai. Bayan Jabeer al'ƙalin gasar ya kawoshi. Yana sake hannunshi masu busar al'gaita da sarewa suka farayi da ƙarfin su. Lokaci ɗaya kuma ranar data take buɗe tarwal ta lumshe. Mutanen kuwa sai tasowa da ife-ife akeyi. Kallo kuma kab ya dawo kan farar kekyawar fatarshi da kekyawan baƙin tattausan gargasa yayi mishi ƙawanya, iya kyan fatarshi kaɗai ya ishi ɗan adam kallo. Da ƙarfi Jabeer ya taune lips ɗinshi, yana maiji tamkar zai hudasu sai ambaton sunan Allah yakeyi, babbar yatsar ƙafarshi ta dama yasa yana caka ƙasar garin, kana yatsunshi na hannun kuwa yasa babban yana zagaye kan ƴar manuniyarshi. A yadda yake jin zafi da ƙuna da baƙin ciki a cikin zuciyarshi ya tabbatar babu wani abu da za'ayi mishi a yanzu yaji zafinsa fiye dashi, to me za'ayi mishi mai zafi sama da tsiraiceshi da akayi. Ba'ana kuwa cikin dariyar mugunta da sautin amo mara daɗin ji, ya taƙar-kara ya ɗago bulaliyar asirin nan, da iya ƙarfin shi ya zabga mishi ita a tattausar fatar tsakiyar bayanshi. Da ƙarfi su Jalal kab suka rumtse idanunsu. Lamiɗo kuwa wani irin kallo yayiwa Jabeer da yayi. Wani ir.....! Biya darinki uku kacal domin jin wannan labari har ƙarshe. Dan Allah da Manzonsa kada ku fitarmin da littafina. Wannan shafin nakune gaba ɗaya waɗanda suka karanta FREE PAGE🤝🏻😘🥰 By *GARKUWAR FULANI*Ido Laminu ya rumtse da ƙarfi. Ganin Sheykh Jabeer yayi wani irin tsayuwa na ingarman, jarumin namiji nitsuwa da kamala, sai lips ɗinshi dake motsawa a hankali yana ambaton Allah. Shi kuwa Ba'ana cikin tsantsar mugunta, ƙeda, da zalumci ya ɗago bulalar nan da azaban karfi ya zabgawa mishi ita a inda ya zabga ta forko. Wanda yasa gaba ɗaya mutanen wurin suka rumtse idanunsu. Especially Lamiɗo da tawagarsa, Shi kuwa Sheykh Jabeer, zuciyarshi ta rigada ta gama tafasa, idonshi baya ganin komai sai wani irin azabebben duhu, kunnuwanshi basa jin komai sai sautin muryar mahaifinshi da kuwa Umaymah. Da suke bashi umarnin cewa dole yayiwa Lamiɗo mubaya'a. Wani irin azaba mai girgiza ran mutun a jikinsa yakeji yana sukarshi har cikin ƙahon zuciyarshi, sai dai duk wani sihiri na jikin bulalar duk baya tasiri a jikinsa illa dai dafin kuna min kam tabbas yana jinsu. Barmuji wanda shine al'ƙalin gasar kuma mai irga bulalin. Da sauri ya rumtse idanunshi lokacin da Ba'ana ya tsulawa Jabeer bulala ta biyar waccee, a take jini ya fara tsastsafo duk inda ta konta. Arɗo Bani kuwa da Bappa da Alhaji Haro da Alhaji Umaru, da Sarkin aska, da sauran dattawan garin da kewayensa wani irin fargaba ne da taraddadi mai firgitarwa suke ciki. Gaba ɗaya bakunamsu addu'o'in ne a ciki. Laminu kuwa tuni yanata ɗaukar duk abinda ke faruwa a ƴar ƙaramar na'ura sa. Yanayi yana dariyar farin ciki. Jalal kuwa da sauri ya rumtse idanunshi kana ya koma baya. Jamil kuwa cur-cur yake zubda hawaye ganin yadda jini ke tsastsafo wa, a tsakiyar bayan Hammansun. Haroon da kanshi tsoro ya rufeshi, yaji ranshi ya fara zargin anya kuwa bada biyu aka haɗa wannan gasarba. Muryar Barmuji ce ta cika wurin gaba ɗaya da alamun tsananin tausayawa yace. "Goma!". Alamar anyi mishi bulala ta goma kenan. Shi kuwa Sheykh Jabeer Idonshi a buɗe suke, sai dai basa ganin komai sai duhu na tsantsar baƙin cikin abinda sashi yayi cikin bainal nasi a sashi tsayuwa da ɗan kampai, Idanun nashi suna buɗe ras. Launin su kuma ya sauya daga farin zaiba, zuwa jazir tamkar wanda maciji ya watsa dafi a cikinsu. Gaba ɗaya fararen faratun yatsun hannunshi sun rine sunyi jazir tamkar wanda aka ƙunsawa jan lalle. Ji yakeyi tamkar tsikarinshi akeyi da bakin allurai. Tabbas duk da bai san dafin kunama ko macijiba, ya gane cewa akwai gubar dafin wani abu a jikin bulalin da ake tsula mishi tamkar za'a zare ranshi dasu. duk ta inda hudar gashi yake a jikin shi, ji yakeyi tamkar ana soka mishi ƙarin kunamai. Bukar kuwa, wani irin murmushin farin ciki yakeyi, ji yakeyi kamar ya fito ya taka rawa dan farin cikin ganin halin da jikan Sarki ke ciki. Muryar na rawa Barmuji yaci ga da irge. "Goma sha ɗaya! Sha biyu! sha uku! sha huɗu! sha biyar!!!." Cikin sauri Haroon ya iso inda suke, hankali a tashe ya kamo hannun Barmuji cikin sanyi yace. "Kai kasheshi zakuyi ne? Bulalin har nawa ne za'ayi?". Cikin rawan murya Barmuji yace. "In sha Allah bazai mutuba, bulali Hamsin za'ayi a ƙa'idar gasar, ba abinda zai sameshi tunda har gashi ya juri bulali 15 wanda a tarihin gasar Ba'ana babu wanda ya taɓa jurar koda bulala biyar ne". Da ƙarfi Hashim ya zaro ido tare da cewa. "50 wannan ai zalumci ne". Da sauri Galadima ya miƙa ya nufi tsakiyar taron ganin Jalal ya nufi inda suke gadan-gadan bisa dukkan alamu kamo hannun ɗan uwan nashi zaiyi yaja su tafi. Da sauri Galadima ya kama hannunshi cikin ɗaga murya yace. "Kai Jalaluddin ina zakaje?". Cikin faɗa yace. "Zan ja ɗan uwana mu tafi, in ku bakwa sonshi bakwa da buƙatar shi, mu muna sonshi munada buƙatar shi, a rayuwarmu domin mu dai shine farin cikinmu, shine silar zamanmu cikin masarautarku, da tuni kun koramu tamkar karnuka, shine kuka haɗa Deel a kashe mana shi, to kuji ku sani zamu bar muku masarautarku in dai ganinmu ne bakwa tson yi." Cikin faɗa Galadima yaja hannunshi yaje ya ajiyeshi gaban Lamiɗo. Yana mai jin tausayin yaran. Da ƙarfi Barmuji yace. "Ashirin da biyar! Ashirin da shida!". Zuwa wannan lokacin gaba ɗaya jikin Al'Sheykh Jabeer Habeebullah yayi ruɗu-ruɗu. Tuni farin boxes dake jikinshi ya cika da jinin dake gangarowa ta bayansa da cikinsa, inda bulalin suke taɓawa duka. Babbar yatsarshi ta ƙafar damanshi da yatsun hannunshi kawai yake motsawa, wanda suke nuna alamun yana nan da rai daram da kuma haiyacinsa. Bayan wannan babu abinda yake motsawa a jikinshi, Cake ƙasar garin yakeyi da yatsar kafar tashi. yatsun hannunshi kuma, motsasu yake yana tasbihi dasu, wanda shima cikin zuciyarshi yake ambaton Allah dayi mishi kirari da kyawawan sunayenshi. Zafin da yakeji a jikinshi tabbas ya wuce zaton mai zato. Taune lips ɗinshi na ƙasa yayi da fararen haƙoranshi tamkar zai hudasu, sai dai har cikin ƙashin haƙoran nashi yake jin azabar dafin dake cikin wadannan bulalin masu masifar siddabaru, sai dai babu wani siddabaru da yayi tasiri a kanshi ko a jikinsa domin shi Allah ya riƙe, Ba'ana kuwa tsafi ya riƙe. Wannan gasace tsakanin gsky da ƙarya, bawai gasar caɗi bane kamar yadda mutanen wurin ke kallo. Haka yasa duk da safin wannan bulalin sam basu kai zafin da yakeji a ranshi na sashi ya tsaya gaban dubban al'ummar garin da ɗan guntun wonɗo a jikinshi ba. Allah ya sani shi mai kunya ne, kuma shi mai suturce kanshine, shida kanshi yana jin kunyar kanshi da kanshi. Baya zama haka ko a ɗaki sabida yana tuna in mafa ya kaɗaice yana tare da Raƙib da Atib Mala'iku makusantan ɗan adam, wanda in ka bar tsiraicinka ma su kauda ido sukeyi daga gareka. Shiyasa shima yake kauda ido daga kan kanshima bare wani. Allah ya sani babu wani abu da aka taɓa yi mishi a duniya ya ƙona mishi rai sama da wannan abun. Tabbas da an barshi hakama, yafi jin zafin hakan sama da waɗanan bulalin. A ranshi yake wani irin kuka mai cin rai yana mgnar zuciya. "Anci min zarafi an wulaƙantani an tozarta ni a gaban waɗan mutanen da wasun cikinsu zindigan kafuraine. An barni tamkar mara kima da galihu, wannan shine iya maƙurar zalumcin da akayiwa rayuwata a karo na biyu". Sam baya jin zuciyarshi tanada raunin da zai iya zubda hawaye kan bulalin nan shiyasa ko zafinsu bai zame mishi abin zubda hawaye ko ihu da bakiba ko gudu ko wani motsi. Zuwa yanzu hankalin kafuran ƙabilar ɓachama ya yi masifar tashi domin wannan shine karo na forko a rayuwar tarihin Ba'ana da ya zana mutun bulalin shaɗi har talatin da takwas baiyi ihuba bai zubda hawayeba, bai sumaba, bai faɗi ba, bai guduba. Kai wannan abun yayi tsamari wannan wanne irin mutum ne, anya kuwa mutun ne ko al'jan. Ya Salmanu kuwa, cikin tsanani kuka cur-cur da hawayenshi sabida yasan azabar da Sheykh Jabeer yakeji. Juyawa yayi ya fuskanci gabas, sujjada yayi tare da fashewa da wani masifeffen kuka mai cike da rauni murya na rawa yake cewa. "Ya Haiyu ya ƙaiyum, ya ziljalali wal ikram. Ya Allah ka ƙarawa wannan bawa naka dauriya da jarumta, ya Allah ka bashi ikon jure wannan azabar, ya ubangiji ka sanyaya mishi masifun dake jikin waɗanan bulalin, ya ubangijin taliƙai ka hana wannan mugun mushirkin bawa naka samun nasara, ya Allah ka kare musulminka kan wannan kafurin matsafin da baya salla". Kuka sosai ne yaci ƙarfin Ya Salmanu. Bappa ma wani irin raunine ya rufeshi tabbas kowa zaiyi tunanin Jabeer yana jin azabar duniya. Sai dai kasan cewarsa Jarumin namiji haka yasa babu wata alama da ya nuna na yana jin zafi ko ciwo. Sosai kuwa hakan ya tada hankalin kafuran. Lamido da Galadima kuwa kallon juna sukayi tare da yin murmushi irin nasu na manyan fada, murmushi ne mai manufofi. Jalal kam kife kansa yayi a cinyar Lamiɗo ya saki kuka mai sauti. Haroon ma hawaye yakeyi zuwa yanzu. Hankalin duk tawagar Lamiɗo yayi masifar tashi, ganin yadda wani irin azabebben zufa ya tsinkowa Jabeer tun daga tsakiyar kanshi, zufar nan take gangarowa har kan jikinshi gaba ɗaya, saida ya jiƙe yayi jilak tamkar an kwaza mishi ruwa bokati ɗaya. Wani irin karkarwa jikin shi, ya farayi yana tsuma yana ɓari, gaba ɗaya jikinshi karkarwa yakeyi. wanda duk fulanin wurin suka fahimci cewa tabbas. Zai iya cinye gasar zai kuma iya faɗuwa. Shi kuwa Sheykh Jabeer daga can cikin naman jikinshi yake jin jikinshi na rawa tamkar mazari. Zuciyarshi kuwa wani irin duka takeyi, wanda muddin kana kusa dashi zakaji yadda take bada sautin harbawa. Hankalin Ba'ana yayi ƙololuwar tashi, ganin har yayi mishi bulala ta arba'in da biyar. Baiyi ɗaya daga cikin ababen da zai hanashi cin gasar ba. Ganin hakane ya juya a fusashe, bulalin hannunshin ya wurgar kana ya sunkuyo kam ranɗar bulalin tsafinshi, bulali biyar ya zaro, ya haɗa su ya damƙesu cikin hannunshi. Cikin azaban ƙarfi ya ɗagosu ya yarfawa Jabeer su a tsakiyar kanshi. Wani irin azabane ya ziyarci ƙoƙon ranshi, wanda hakan yasa yaji wani irin fitsarin azaba yana cika mishi mara. Jinine ya tsinko ta kafaɗunshi, yana bin cikinshi, bai gama jin azabar waɗannan ba ya kuma zarma mishi su a cinyoyinshi. Da sauri Arɗo Bani ya miƙa tsaye daga sujjadar da yayi jin ihun mutane, suna cewa. "Ka karya dokar gasa ba'a haɗa bulali biyuma bare biyar kasheshi zakayine. Cikin wani irin isa ta jarumta da jinin sarauta Sheykh ya buɗe kwayar jajayen idanunshi, Barmuji da yayi kansu da nufin kama hannun Ba'ana ne, Ya ɗagawa hannunsa alamun daka dakatarwa alamun ya tsaya kada ya iso ya bar Ba'ana yayi komai ba komai. Cikin tsananin mamaki duk al'ummar wurin suka zuba musu ido ganin jarumta ziraran miraran tana tsaye da sawunta. Shi kuwa Barmuji cikin rauni yaci gaba da nufosu yana cewa. "A a Sheykh bazan barshi ba, ai ya karya ƙaida da dokan gasa". Ya ƙarashe mgnar yana isowa inda suke. Cikin tsananin takaici da firgicin ganin faɗuwa a karo na forko na rayuwarshi, Ba'ana Ya zargawa Barmuji bulalin da ƙarfi. Wani azabebben ihu Barmuji ya narka tare da fara tsalle yana yarfa hannunshi yana zagaya wurin hawaye na shatata mishi sabida azabar da yakeji, cikin ihun azaban bulalin da aka yarfa mishi sau ɗaya, fitsari na tsiyaya a sawunshi yace. "Arba'in da takwas!". Ta gabanshi ya dawo ya shauɗa mishi na arba'in da tara, wanda yasa Jamil yin tsalle yazo gabanshi cikin kuka yace. "Kasheshi zakayi ne?". Cikin tsananin azabar da yakeji ne ya buɗe jajayen idanunshi ya kalli ta inda yaji muryar Jamil. Hannunshi yasa ya ture Jamil gefenshi. Shi kuwa Ba'ana wani irin ihu yayi tare da buga tsalle yayi sama kana ya zabga mishi bulala ta hamsin kuma ta ƙarshe. Wani irin dogon numfashi Jabeer yaja tare da buɗe idonshi kan fuskar Lamiɗo daya iso hango dishi-dishinsa yana nufo inda suke. Wani irin ihu da karaji Ya Salmanu ya kurma da azaban ƙarfi, Wanda ya haɗe ya gauraye da busar sarewa da al'gaita da dukan gamgar jami, aka saki a tare. Wani irin sowa da ihu da hargowane ya cika illahirin gaba ɗaya Rugar Bani, Wanda mutane fulani suketa rawan farin cikin jarumtar Jabeer, Arɗo Bani da sauran dattawan rugar kuwa gaba ɗaya sujjadar godiya sukayi wa Ubangijinmu sarki gagara misali. Gaba ɗaya an zagaye Sheykh Jabeer. Wanda shi kuma ya juyawa Haroon baya alamun yasa mishi suturarsa. Da tsananin rawan jiki. Haroon ya wore al'kyabbar, ya zura mishi ita kan jikinshi daketa zubda jini. Yana jin Haroon ya saka mishi Al'kyabbar ya ɗago kafaɗunshi ya gyara zaman al'kyabbar. Jiki na rawa yasa hannunshi ya kama gefe da gefen bakin al'kyabbar ya hadesu a jikinshi ya suturce kanshi ya kare kanshi. Barmuji na shirin kamo hannunshi yayi maza. Ya ɗaga mishi hannunshin kana ya juya ya nufi inda motoncinsu ke jere. Jalal da na ganin haka yayi maza yayi gabanshi. Marfin motar ya buɗe mushi tun kafin ya iso. Cikin taron kuwa, tuni Ba'ana da matasan ƙabilar ɓachama, sun ɗauki ranɗar bulalin tsafinshi sun nufi Bonon da tarin baƙin ci dan ganin Sheykh Jabeer bai faɗi gasarba, kuma ga mutanen fulani daketa yi musu dariya da ihun rashin nasarar su. Hakan yasa suka tafi dan sun sani a ƙa'ida sai Jabeer yayi jinya ya worke da azabar da Ba'ana ya shayar dashi kafin ya dawo ɗaukar fansa. Cikin taron kuwa cikin kukan rauni Arɗo bani ya rusuna gaban Lamiɗo da tawagarsa murya na rawa yace. "Sauran ɗaukar fansar da zaiyi a duk sanda ya worke a duk sanda yaga dama, fatana kuyi shirya bulalin tarihin masarautarku, domin ramuwa akan wancan taƙadirin da baya jin koda harbin bindiga baya shigarsa. Ina yakun farin cikin nasarar da Jabeer yayi a yau, ina kuma fatan yayi nasara a ramuwar da zaiyi a wannan kuma in yayi nasarar mu zaku taya farin ciki, ko ba komai zamu rabu da wancan taƙaɗirin." Cikin wani irin tarin ƙuna Lamiɗo ya gyaɗa kanshi. Kana ya juya yayi gaba Dogari na rike masa da laima ɗanzagi na cewa. "Gyara kimtsi, a bada hanya, sarki ya barku lfy". Waziri da Wambai Ɗan buram Ɗurɓi Da iya duk suka mara mishi baya. Hakama Arɗo Bani da sauran dottawan wajen sukayo musu rakiya. Sheykh Jabeer kuwa. Yana tafe Galadima na biye dashi a baya. Haroon kuma na gefenshi. Suna isa yasa kai ya shiga cikin motar, kana Haroon da Hashim suka mara mishi baya, da sauri sarkin mota ya maida ƙofar ya rufe. Kana ya buɗewa Lamiɗo motar, gefen bayansu Jabeer ya shiga, kana Galadima ya shiga kusa dashi, sannan aka rufe motar saura duk kowa ya shiga motar da yazo ciki. Sannan duk suka rurrufe motocin. Kana suma Fadawa da dogarai suka shiga nasu motoci biyun. Ɗaya tayi gaba, sauran motocin suka bisu a baya, ta Lamiɗo na tsakiyarsu, kana ɗaya ta fadawan ta biyo bayan uku da ke bin bayan ta Lamiɗo. A haka suka ja motocin a jere a jere suka bar cikin Rugar Bani. Cikin Rugar kuwa kowa ya tafi cikin al'ajabi da farin ciki. Da yawa gani sukeyi kamar dai Jabeer ba mutun bane. Sauran dottawan kuwa, zama sukayi cikin fadar bayan sunyi sallan la'asar ne, Bukar yazo ya tsaya tsakiyarsu cikin rashin mutunci yace. "Kuyi kuka da kanku akan duk abinda zai faru gaba". Kafin ma su bashi amsa tuni ya juya ya tafi. Su kuwa nan sukaci gaba da al'ajabi da tuanjidin Jarumtar Jabeer. A cikin motocin kuwa, mutanen ko wacce mota da abinda kowa ke tunawa. Wani irin azabebben gudu sukeyi tamkar zasu tashi sama, sabida bin umarnin Lamiɗo wanda shi kuwa ya bada izinin gudun ne, dan ganin yadda Jabeer keta zubda jini, ga wani irin masifeffen karkarwa da jikinshi keyi. Gudu sukeyi a 360 musamman ma da suka samu suka hau kan babban titin Shikan wanda zai sadasu da cikin babban birnin Ɓadamaya. Shi kuwa Sheykh Jabeer, wani irin karkarwa jikin shi keyi, idanunshi jinsu yakeyi tamkar zasu zazzago su faɗo ƙasa, sabida wani irin masifeffen azaba da yakeji. Ji yakeyi tamkar ya haɗiyi zuciyarshi sabida masifar fushi da harzuƙa da zafin rai, babban abinda ya tsananta fushinsa shine yadda yaga lokacin sallan la'asar ya gota musu, akan shirmen banza da wofi da zalunci an hanashi yin salla kan lokacin ta. Hannunshi yasa ya fizge rigarshi da ke hannun Haroon dake ta sa hiraminshi yana tare jinin dake zubomishi ta ƙeyanshi. Taune lips ɗinshi yayi tare da sa hannun shi, ya kama wuyan rigar cikin ƙarfi yaja ji kakeyi, Fasss sautin yagewar sabon saddan. Ido suka zuba mishi gaba ɗayansu, Ya Hashim kuwa jiki narawa ya kira Dr Aliyu wanda yake ƙanine ga mahaifinshi da kuma Abbansu Jabeer ɗin. A can baya kuwa inda Galadima dake zaune gefen Lamiɗo ne daya bashi umarnin ya kira sarkin gida ya sanar mishi ayi tanadin jinyar Shaɗi cikin gaggawa. Da sauri Galadima ya zaro wayarshi ya kira sarkin gida. Cikin tashin hankali yake mgna a woya bisa alama duk da sarkin gida yake mgn. "Ladodo, kayi maza yanzu ka sanarwa tsohon sarkin Shaɗin masarautar Joɗa yayi maza ya haɗa tsumin igiyar bulalin shaɗi, ya kaiwa Jakadiyarsu Jabeer, A shirya duk wani abun buƙata, domin Jabeer yana zubda jini sosai." A can masarautar kuwa Sarkin gida yana jin haka ya miƙa ya nufi, sashin kananan sarakuna kai tsaye gefen Sarkin Shaɗin ya nufa, ya sanar mishi umarnin da aka bada, ai nan take Sarkin Shaɗin da sarkin Gida, suka shiga bayan sashin mai martaba Lamiɗo, inda bishiyoyin tarihi dana gargajiya da magunguna suke. Forko bishiyar Goruba suka fara sassaƙan jikinshi. Wanda shine babban makarin dukan shaɗun. Sai kuma suka haɗa da wasu tsirran,. Koda suka gama kai tsaye gefen Jakadiya da sauran ma biyanta suka nufa, Nan suka bata dukkan abinda suka ɗebo, suka kuma yi mata bayani. Kana sukace maza ta haɗa su ta dafa, Sauran kuma sai sun dawo Lamiɗo ya shiga ɗakin sirri ya ɗebosu. Cikin tsananin tashin hankali da rawan jiki Jakadiyarsu ta amshi magunguna, ta nufi sashin Jabeer ɗin. Cikin gaggawa ta shige kitchin ɗin shi, ta fara harhaɗa magunguna tana dafawa. A can cikin motar kuwa cikin tashin hankali Ya Hashim yayiwa Dr Aliyu duk bayanin abinda ya faru da halin da Jabeer ke ciki. Ya ƙara da cewa, a shirya komai na bashi taimakon gaggawa. Jin hakane yasa Dr Aliyu tada motar Ambulance wanda take nan cikin asibitin dake cikin makarantar nasu, tazo bakin asalin babban gate ɗin masarautar nasu. Kana ya kira babban abokinshi Dr Sanju wanda ba indiyene wani aikine ya kawoshi ƙasar, tuni suka iso bakin gate ɗin, cikin motar Ambulance ɗin suka shiga suka zauna tare da haɗa duk wani abu na taimakon gaggawa da za'ayi mishi. A cikin motar kuwa, gaba ɗaya ya gama yage rigarsa ya fizge wonɗonma ya yageshi fata-fata. Ganin wani irin kallo da yayi Haroon ne, yasa Haroon yin maza ya matsa tare da yin mgnar zuci. "Ka gani ko Lamiɗo hegen tsoho kai ka dace ka zauna kusa dashi. Inma yagawarne ya yage ka". A zahiri kuwa fuska ya ɗan haɗe tare da cewa. "Kafa gama yaga kayanka yanzu nawane suka rage a jikina, naga ji kake kamar ka yagamu, yaseen to bamu muka kar zomonba". Dai-dai lokacin kuma, sarkin ƙofa ya buɗe musu ƙofar babban gate ɗin. Kana suka kutsa kai. Suna shiga ko parking basu gama dai-dai tawa ba Jabeer ya sa hannu ya buɗe marfin motar, ƙafarshi ya zuro woje, wanda ganin haka yasa Dr Aliyu ya fito da sauri. Sai dai kafinma ya fito tuni Jabeer ya fito cikin motar ya nufi asalin ƙaramin gate ɗin da zai sadaka da asalin cikin farfajiyar. Kusan a tare suka fito daga motocin gaba ɗayansu. Cikin tsananin tashin hankali Ya Hashim ke ƙwalla mishi kira, amman ina bai ko juyo inda sukeba. Baya kuma jinsu sosai sabida duhu da jirin da yake gani. Da gudu Haroon da Jalal Jamil suka biyoshi a baya cikin rauni Jamil ke cewa. "Hamma Jabeer dan Allah ka tsaya Baba Aliyu zai dubaka, kaga fa har yanzu jinin bai daina zuba ba." Ina ai baya tare dasu tafiya kawai yakeyi, ba tare da yasan inda yake jefa ƙafarsa ba. Ganin hakane Dr Aliyu ya koma cikin Ambulance ɗin ya jata ya nufi inda yake, sai dai tuni har ya shiga cikin asalin farfajiyar. Haroon, Jalal, Jamil, Hashim, ɗan Barrister Kamal Sulaiman, da Imran, duk suna biye dashi a baya da dudu-gudu da sassarfa. Lamiɗo da tawagarsa kuwa, koma sukayi cikin motocin sukaja, suka nufi cikin gidan. Shi kuwa Sheykh Jabeer tuni ya isa bakin side ɗinshi. Cikin tsananin rawan jiki da duhu ya kusa kanshi ciki. A babban falon ya samu Jakadiyarsu, tana ganinshi ta miƙe tsaye cikin tsananin tashin hankali ta tsaya ganin ya ɗaga mata hannunshi ɗaya, kana yasa hannunshi ɗaya kuma ya dafe kanshi. Cikin wani irin kerma yake wani irin taku da jan wani irin dogon numfashi ya nufi part ɗin shi. Yana shiga falonshi na musamman, su Haroon na shiga babban falon. A nan su Jamil kan suka tsaya, shi kuwa Haroon da sassarfa yabi bayanshi. Yana shiga falon nashi ya hangoshi ya shiga bedroom ɗin shi. Ya kuma maida ƙofar ya rufe, kai tsaye bathroom ya wuce yana shiga wani irin duhu ya rufe idanunshi a hankali ya tafi... A can Rugar Bani kuwa, kuwa Junainah har ta shiga kitchin ta sunkuyo zata ɗauki akoshin naman gasassun zabbin, sai kuma ta fito a guje. Kai tsaye inda ake gasar Shaɗi ta nufa, haka ta rinƙa kutsawa cikin taron, har ta isa gaba-gaba kusa da ya Salmanu, ganin irin dukan da akeyiwa wannan kekyawan mutumin data ganine yasata kuka da ihu. Kukanta ne yasa Salmanu kuka, ya kuma ja hannunta ya fito baya da ita. Hannunta ɗaya riƙene yaji yadda jikinta ke karkarwar kamar mazari, bayan yayi sujjadar ya ɗagone. Yace mata maza ta koma gida. A haka ta koma tana kuka. A inda ta bar Shatu dasu Rafi'a da Ummiy anan ta dawo ta samesu. Kai tsaye kitchin ɗin ta nufa, da sauri ta ɗauko akoshin ta fito ta nufi inda suke, cikin rawan jiki ta sunkuyo ta sauƙe musu akoshin ta ajiye a tsakiyarsu, kana itama ta zauna a kusa da Ummiy dake jingine da jikin bishiyar mangoro. Jiki na rawa tasa hannun ta janye fefeyin da aka rufe akoshin da shi. Wani irin lumshe ido Rafi'a tayi, sabida wani irin ƙamshin daya buɗe hancinta, Ummiy kuwa ido ta zubawa akoshin tana jin yawun bakinta na tsinkewa, Shatu kuwa gyara zamanta tayi sabida wani irin azabebben ƙugin yunwa da cikinta yayi. Cikin sanyi suka gyara zamansu gaba ɗaya, a hankali Shatu ta riƙe hannun Junainah cikin zubda hawaye tace. "Jeki wonke hannunki sai kizo, da plet da ƙaramin akoshi mu ɗibawa Bappa mu sawa Ummiy a plet ɗin". Cikin sanyi ta tura baki kana ta miƙe tsaye, gindin randunarsu ta matso, yar ƙaramar butarta ta ɗauka ta wonke hannunta, sannan ta nufi cikin madafarsu. Tana shiga ta ɗauki ludeyi da ƙaramin akoshi kana da pilet sannan ta fito. Tana fitowa tazo ta zauna gabansu, ta miƙa Shatu, cikin sanyin jiki tace. "Bawa Rafi'a ta ɗiba musu, wlh jikina duka rawa yakeyi". Amsar pilet ɗin Rafi'a tayi ta fara ɗibawa Ummiy rabin zabuwa. Kana ta sawa Bappa gudar da romonta, Tana cewa. "Garkuwa yunwace fa, ace mutun ya wuni ya kuma kwana baici komaiba ya kuwa wuni ba abinda yaci ai dole kiji jiri, gashi yawan kukan da kikeyi ne yasa miki zazzaɓi." Ta ƙarishe mgnar tana rufewa Bappa nashi kana tace. "To muci". A tare suka saka hannunsu cikin akoshin. Junainah ce ta fara yago tattausan farin tsokar ƙundun zabuwar cikin haɗiye min yau ta kai hannunta bakin t....! Dan Allah da Manzonsa kada ku fitarmin da littafina, in kinsan Zaki fitarne gaya min in baki kuɗinki, dan Allah. By *GARKUWAR FULANI*Ta kai hannun ta, kusa da bakinta kenan Wani ƙaton gadamgare ya faɗo jikinta. Wani irin tsalle tayi tare da rauza ihu, ta faɗa jikin Aysha tuni tayi fatali da akoshin gasassun zabbin nan ya ɓare ƙasa kirib. A firgeci Ummiy ta yunƙuro tare da nufar inda suke, wanda hakan yasa tayi fatali da akoshin da akasawa Bappa zabbuwar da kuma take wanda aka zuba mata a plet ɗin ya ɓare cikin lallausan yashin garin. Ita kuwa Junainah gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi, fizge-fizge takeyi tana ƙwaƙumar Shatu. Sabida ita ji takeyi kamar dai har yanzu ƙadangaren yana jikinta. Cikin kiɗima Shatu ta ruggume ta, tare da cewa. "Ke Junainah ki bar ihun ƙadangaren ma ya razana da ihun da kika kurma ya sauƙa ya tafi." Jin hakane yasa ta tashi zaune tare da zazzaro ido, Rafi'a kuwa dariya tasa tare da cewa. "Kai Junainah yaseen kin cucemu, kallifa yadda kikayi fatali da akoshin nan". Cikin sanyi Shatu tace. "Haba wannan abu dai Allah yayi ba raban mu bane, Ni dama can haka nan in naga naman sai inji zuciyata ya tsinke ashe ba rabanmu bane, da muncima da mun harar dashi. Ita kuwa Ummiy jan hannun Junainah tayi kana ta zauna kusa da Shatu. A hankali ta jingina kanta da kafaɗan Shatu, Rafi'a kuwa miƙewa tayi ta shiga kitchin ɗin su. Abincin data dafa musu ta kawo musu. Ta ajiye gefe, sannan ta ɗauko tsintsiyar kwakwa ta share ta kwashi naman kab ta maidashi cikin babban akoshin, ta rufe, sannan taje ta wonke hannunta kana tazo ta zauna suka fara cin abincin. A can cikin fadar masarautar Joɗa kuwa. Jin jiri na ɗibanshi ga duhu dake rufe mishi ganine ya sashi, tafiya a hankali tare da dafa jikin gini. A haka har ya isa bakin Jakuzin, A hankali ya zare al'kyabbar jikinshi, ya wurgar dashi can gefe, kana ya tura ƙofar ya Jakuzin ya shiga, tsayuwa yayi tsakiyarshi, hannun na rawa ya buɗe shawan ruwan ɗumi. Wani irin numfarfashi wahala ya sauke lokacin da yaji ruwan ɗumi yana ratsa raɗi-raɗin azabobbun bulalin da yasha. Wasu irin hawaye masu masifar zafine yaji suna tsastsafo mishi cikin jijiyoyin kekyawan idanunshi, sai dai basu kai ga damar samun zobowa ba. Wani irin tsuma duk illahirin sashin jikinshi ya fara, zafin ruwan yakeji har cikin ƙoƙon ranshi, wani irin karkarwa haƙoranshi sukeyi har suna dukan juna, kat-kat. Kanshi ya sunkuyar tare da buɗe idanunshi a hankali, ruwan dake gangarowa daga jikinshi yana bin ƙasa in da zai gangara yake kallo, sabida zakace jinine ba ruwaba, Sabida yana wonke mishi jinin jikinshi. Haka ya tsaya a ƙasan ruwan ɗumin har saida yaga jinin ya daina zuba kamar da fari. Sannan yasa hannunshi ya ɗauki daddaɗan sabulun wankan shi, ya fara murza sabulun taki wani sashi na jikinsa, wani irin wahaltaccen ƙara yayi lokacin da sabulun ya ratsa inda ya farfashe a jikinsa, cikin rauni yace. "Wayyo Allah na! Wayyo Mamey na zan mutu, zafi zai kasheni tun kafin cikar burina." Ci gaba yayi da murza sabulun tare daci gaba da cewa. "Wayyo Umaymah wayyo Ummi". Sai kuma ya taune lips ɗinshi kana ya rumtse idanunshi yayi ta murza sabulun tako ina yanayi ruwan ɗumi na dukanshi. A haka yayi wonka ya wonke duk wani jini dake jikinshi yayi fes. Al'wala yayi, kana ya fito cikin Glass ɗin sannan ya ɗauki wanni tattausan baby towel fari ƙal ya ɗaura a ƙirjinshi ya sauƙo har zuwa guiwansa. Hannunshi yasa ya murza farin boxes dake jikinsa wanda ɗazu yake jiƙe da jini yanzu kuma yayi fari tas. Murza boxes ɗin yayi har ƙasa, kana ya ɗaurashi kan al'kyabbar jikinshi da ya cire, Cikin Woshing mashine yasasu, Kana ya fara yin taku a hankali ya iso gaban drower'n glass ɗin dake cikin bathroom ɗin. Wani tattausan gajeren wondo fari tas mai ratsin sky blue ya saka, gajeren wondon yazo mishi har guiwarsa, kuma mai ɗan faɗine, Wata tattaunawar riga mai guntun hannu wacce itama farace da ratsin Sky blue, ya saka, kana ya zaro wata ɓakar tattausar jallabiya doguwa har ƙasa tazo mishi daya zurata, Wani hulan taɓa kaji Hadisi ya kifa kan suman kanshi dake da ɗan damshin ruwan ɗumin. A hankali yake taku sabida zuwa yanzu wani fitinenne zazzafan zazzaɓi yakeji. Jiki na rawa ya fito, bisa sallayarshi dake shimfiɗe a wata ƴar kusurwa yaje ya hau. Yana hawa kan sallayar ya fuskanci gabas, yaji zuciyarshi tayi wasai, baya tuna komai, baya kuma jin ciwon komai a jiki da zuciyarshi sabida kushi'i da tawakkali da kyutata ibada baya jin komai sai hasken farin cikin ibada. Kabbara ya tada tare da niyar sallan la'asar daya mannata bisa laruri ya makarar dashi. A falonshi kuwa, hankalin Haroon ya tashi yana nan tsaye bakin ƙofa yana ta magiyar ya buɗe mishi, bai saniba shi yana can har cikin bathroom ɗin shi. Yana nan tsaye, mai Martaba Lamiɗo da Galadima suka iso tare da Sarkin Shaɗi. Cikin sanyi yacewa Lamiɗo. "Ya shiga ciki kuma ya rufe ƙodar ta ciki, inata kiranshi baya amsawa. Murmushi Lamiɗo yayi kana, yacewa Galadima. "Muje". Kusan a tare suka fito falon. Suka zauna, kana ya kira Abba, yace yazo yasa ɗanshi ya buɗe musu ƙofar. Jin hakane yasa Abba tahowa da sauri. A can babban falon kuma. Cikin damuwa Jamil ya labartawa Jakadiyarsu da Aunty Juwairiyya abinda ya faru. Ga mamakinsu sai sukaga Jakadiyarsu tayi wani ƙayataccen dariya cikin sakekkiyar murya tace. "Alhamdulillah wannan shine abinda muka daɗe muna jira tsowon shekaru da dama. Kuma jinyarsa abune mai sauƙin". Cikin ruɗani Jalal yace. "Ummi kuka daɗe kuna jira kuma?". Kai ta jinjina mishi, kana ta miƙe ta nufi kitchin dan harhaɗa aikin da akasata. A nan Abba yazo ya samesu. Jalal na ganinshi ya kauda kanshi. Hakama Jamil Imran kuma bayanshi yabi suka nufi side ɗin Jabeer ɗin. A falo ya samu iyayen nashi, Cikin girmamawa ya rusuna yayi Lamiɗo Barka da yammaci kana ya matso kusa da baƙin ƙofar Bedroom ɗin Jabeer cikin ɗaga sauti yace. "Muhammad! Muhammad Jabeer! Jabeer!! Jabeeey!!! Ka taso maza kazo ka buɗe min ƙofar nan ina jiran ka". Jabeer kuma da yanzu yake raka'ar ƙarshe, sam hankalinshi baya ga jin kiran Abbanshi domin a yanzu yana gaban Ubangijinmu ne. Haroon kuwa wayar dake kunnenshi ya gyara riƙewa cikin shaƙiyancinsa yace. "Uhumm Umaymah ke dai kicewa Sarki Jalaluddin da Sarki Abubakar baban Daddy na, suyiwa masarauta Joɗo gudumowar suturu. Domin yau dai ran ƴan maza ya ɓaci, nasan sai ya yayyage kab wani abu mai yaguwa a masarautarsu". Cikin wani irin farin cikin wannan labarin da Umaymah taji tayi kekkyawan dariya tare da cewa. "Haroon yayan naka kakeyiwa tsiyako?". Cikin tura baki yace. "Allah ko Umaymah kecema kike sawa Jabeer yana rainani wai yayana". Da sauri tace. "To ba yayanka ɗin bane?". Cikin yamutsa fuska yace. "Yayan kwana arba'in, shiyasa yake min kallon kobo biyu da sisi, sabida yana jin kuna ce mishi yayana, wani lokacin har cemin yaro yakeyi dan tsabar son girma da manyance, Ni mamaki da yake bani kawai sai in zuba mishi ido in naga yana min faɗa kamar wani ɗan cikinsa". Murmushi Umaymah tayi kana, tace. "Gobe zuwa jibi in sha Allah ina nan zuwa Masarauta Joɗo, sabida zanzo in lallashi ɗana nasan yayi zazzafan fushi tunda yaƙi kula Dr Aliyu ma". Daga nan sukayi sallama. Shi kuwa Sheykh Jabeer saida ya isar da sallameshi yayi addu'o'in shi Kafin ya tashi a hankali ya nufi bakin ƙofar sabida zuwa yanzu zanan bulalin sunyi tsami ga zazzaɓi daya mishi rubdugu. A hankali ya murɗa key ɗin ƙofar ya buɗe ta, kana ya juya ya koma kan gadonshi, sabida rawa da jikinshi keyi na zazzafan zazzaɓi da wahala. Yana konciya ya lumshe idonshi tare da fara karanta Suratul Khaf kasancewar yau yammacin jumma'a ne. Su kuwa a falo suna jin sautin buɗe ƙofar, suka zubawa ƙofar ido ganin shiru bai fitobane yasa. Galadima da Haroon suka nufi cikin ɗakin. Jim kaɗan da shigarsu Galadima ya fito da sauri ya kira sarkin Shaɗi, da Lamiɗo kana da Abba. A tare suka nufi cikin ɗakin, suna shiga Haroon ya fito. Babban Falon ya koma ya nufa yana kiran Jakadiyarsu da sunan da suke kiranta. "Ummi! Ummi!!". Da sauri ta fito kitchen ɗin riƙe da filas da kofuna, sai kuma wani ɗan kwarya mai kyau ruwan ciki na tururi. Da sauri ta miƙa mishi tare da cewa. "Yauwa Haroona gashi kai musu da sauri". To yace kana ya amsa ya juya ya koma, can cikin ɗakin Jabeer ɗin. Zaune suke gaba ɗayansu, shi kuma yana konce ya duƙunƙune cikin wani jibgegen blanket mai masifar kyau da taushi. Sai karkarwa yakeyi tamkar mazari, Cikin sanyi Lamiɗo ya ɗan janye borgon tare da cewa. "Jabeer!". Duk da azaban zafin da yake ciki, bai hanashi buɗe idonshi ba, wani irin mugun kallo ya watsawa Lamiɗo, murmushi sukayi baki ɗayansu kana cikin lallami Galadima yasa hannunshi ya kamo nashi cikin sanyi yace. "Jabeer tashi ko? Tashi kasha mgni". A kufule yace. "Bazan shaba ku barni in mutu tunda hakan shine fatanku". Da sauri Abba ya kauda kai tare da yin wani faffaɗan murmushi kana, ya juyo ya kalleshi cikin bada umarni yace. "Muhammad tashi. Maza tashi kasha mgni". Kanshi ya ɗan gyaɗa kana a hankali ya fara yunƙirin tashi zaune. Ganin hakane Haroon yayi saurin taimaka mishi ya tashi zaune. Idonshi ya rumtse sabida ji yake kamar har cikin ƙasusuwan jikinshi ake tsikara da bakin allurai gashi duk inda hudar gashi yake a jikinsa sai ya ɗan tasa kamar wurin da cinaka ya ciza. Cikin tarin kula da wani mashahurin farin ciki, Lamiɗo da kanshi ya amshi haɗin maganin da sarkin Shaɗi yayi mishi a wani ma dai-dai cin kofi. Hannunshi yasa ya amshi kofin kana ya kaishi bakinshi, fuska ya kwaɓe sabida gafin mgnin da yaji a jikinshi. Cikin bada umarni Abba yace. "Ka shanye duka". Ido ya rumtse kana ya kafa kanshi ya shanye shi tas. Miƙa musu kofin yayi, kana ya amshi wani kofin da Abbansu ke miƙa mishi, Shima shanye shi yayi tas. Yana miƙa wa Lamiɗo kofin. Ya fara wani irin gyatsa mai ƙarfi, gyatsan a jere a jere. Cikin sanyi Haroon yace. "Sanno my broz". Ina babu halin amsawa dan gyatsan ya tsananta, wani irin zufane ya keto mishi daga tsakiyar kai har kan babbar yatsarshi. Wani irin murɗane ya fara ɗibanshi tamkar zai tsinke mishi ƴaƴan hanji. Cikin wani irin zabura ya fara wani irin yunƙiri. Sai gashi yanata kela wani irin baƙin amai akan tattausan blanket ɗin nan. Murmushi Sarkin Shaɗi yayi tare da kallon aman da kyau kana ya juya ya kalli Lamiɗo da Abba yace. "Da dafin kunamai yake tsuma bulalinshi, ga nan dafin yake amayarwa." Murmushi Galadima yayi tare da cewa. "Uhumm kaji mugun banza ko". Shi kuwa Abba ido ya zubawa Jabeer ganin yadda yaketa kela amai, fuskarshi nan tayi jazir, jijiyar kan goshinsa nan ta tashi ta miƙe samɓal. Haroon kuwa tallafeshi yayi yanata ce mishi sannu. Sai dai yayi kusan 30 minutes yana kwara amai kafin ya koma ya jingina da jikin Haroon yanata wasu irin zafafan numfarfashi tare da lumshe idonsa. Da sauri Lamiɗo yasa hannunshi ya tattare blanket ɗin ba tare da aman ya ɓata ko maiba. Ya dunƙuleshi ya miƙa wa sarkin Shaɗi. Da sauri Sarkin Shaɗi ya miƙa Abba wani butan duma. Sannan ya amshi borgon. Shi kuwa Lamiɗo Haroon ya kalla tare da cewa. "Cire mishi wannan rigar". Da sauri Haroon yace to kana ya fara kiciniyar cirewa mishi jallabiyar. Duk da yana galabaice saida ya ɗan ja tsaki tare da ture hannun Haroon cikin muryar dake baiyana a wahalce yake yace. "Bana so ku barmin rigata". Hannunshi Abba ya buge tare da cewa. "Bakinka bazai mutu bako". Shiru yayi yana gani Haroon ya cire mishi rigar cikin murmushin da ganin jarumta da ƙarfin hali irin na Jabeer Galadima yace. "Cire wannan ta cikinma". Ba musu ya bari Haroon ya cire mishi rigar, Wani irin zaro ido Haroon yayi gani duk jikinshi yayi shatin zanen irin manyan kunama nan". Lamiɗo da Galadima da Sarkin Shaɗi kuwa murmushi sukayi tare da haɗa baki wurin cewa. "Uhum dafin ya gama fita, cikin jininshi." Abba kuwa hannun ya haɗa ya miƙa wa Lamiɗo dake mishi alamun zai zuba mishi abu a hannun. Wani haɗin mgnin ya zuba mishi cikin tafin hannunshi. Murzawa yayi kana, ya shafa a duk jikin Jabeer. Wani irin sassanyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da lumshe idonshi. sabida wani irin sanyin da yaji yana ratsashi har cikin ƙasusuwan jikinshi. Tuni wani bacci mai fitinenne daɗi ya kwasheshi. Nan suka gama yi mishi komai. Kana suka fita, Dr Aliyu kuwa da Ya Hashim suka shigo bisa umarni Lamiɗo. Drip and injections Dr Aliyu ya ɗaura mishi tare dasa ruwan alluran a cikin ƙarin ruwan da akeyi mishi. Ganin sun gama yi mishi komai ne, suka fita suka tafi. Suka bar Haroon kaɗai. Dan in ruwan ya ƙare ya cire mishi. A falo kuwa Ya Hashim nayi musu bayanin ya samu bacci jikin da sauƙin duk sai suka tashi suka nufi masallaci. Jakadiyarsu da Aunty Juwairiyya aka bari a wurin. Sum jin shiru ba motsin Haroon yasa suka tafi sashin Juwairiyya dan bawa hadimanta umarnin shiga kitchen. Bayan awa ɗaya kuwa ruwan ya ƙare ya cire mishi. Ganin yana bacci ne yasa ya shiga wonka. A can cikin gidan kuwa. Sashin Gimbiya Saudatu zaune take a bisa bakin gadonta ita da Laminu ɗan ta na biyu video da yayi a Rugar Bani na zabgar Jabeer yake nuna mata, cike da tsantsar jin daɗi, sai dariyar mugunta sukeyi. Babban ɗan ta Ya Hashim ne, zaune can gefensu, ya zuba musu ido, yana nazartansu, to sukuma me sukeji a zuƙatansu, akan Jabeer da sauran ƴan uwansa shin duk wannan ƙiyeyyar ta mecece". Muryar Baba Nasiru suka jiyo a falon yana sallama. Da sauri Gimbiya Saudatu ta miƙa tsaye tare da kamo hannun Laminu tace. "Zo taho muje gacan ƙaramin Babanku". Da sauri suka nufi hanyar fita, wani irin kallo yayiwa Ya Hashim tare da jan tsaki cikin faɗa tace. "Banza mara zuciya, wanda bai san masoyansa da maƙiyansa, ai dai duk abinda nakeyi a kankane". Tana faɗin hakan suka fice. Jiki a mace yabi bayansu, Allah ya sani baya son cutar da Jabeer da sukeyi. A falon ya samesu zaune harda Baba Bashiru sunata sheƙa dariyar mugunta. Gefe can ya zauna ya zuba musu ido. Bayan sun ɗan tsagaita dariyar ne, Baba Nasira ya nisa tare da cewa. "Allah kenan maji roƙon bawa, gashi ya amsa min addu'o'in da nai a safiyar yau ɗin nan, Yadda na wuni da baƙin ciki, shi kuma zai kwana da azaba". Cikin sauri Gimbiya Saudatu tace. "Ai Ni nafi kowa farin cikin wannan dukan Kawo wuƙa da akayi wa wannan hegen yaro mai jajayen kunnu, yaro sai hegen baki da rashin tsoro duk barazanar da akeyi mishi baya kashe bakinsa. Musamman ni kam ina mgna kafinma in sauƙe numfashin ya bani amsa ga shegen azanci. Ɗan is abun buga cincim yau dai babu wannan bakin ai". Cikin dariyar ƙeta Laminu yace. "Ai wlh Umma ni so nayi a kashe hege a can, mu binneshi a waccar ƙaramar Rugar mu dawo salum salum abinmu". Cikin murtuke fuska Baba Basiru ya kallesu tare da cewa. "Ai Ni yau ko mutuwa yayi ban huce baƙin cikin dana shaƙa ba lokacin da naga ya fito ɗakin sirri da Lamiɗo har yanzu in na tuna zuciyata bugawa takeyi, to wai ma meye hakan ke nufi. Da farin ɗan uwanmu da aka bawa Galadima ya rasu dare ɗaya, ana biyu aka bawa wancan hegen yaro mai nisan kwana Jafar ɗin sarautar. Wannan abu shi yafi komai tada mana hankali, tunda dama duk cikinmu yaran Lamiɗo babu wanda ya ba koda sarautar fadanci ce sai Yaya Muhammad, to kuma dan ya rasu sai a maida sarautar kam jikoki a tsallake ƴaƴan duka." Cikin tafasar zuciya Laminu yace. "Yo waya ma sani ko sune suka kashe mana Babanmu dan mulkin ya koma hannunsu, ku kuma kuka barsu". Da sauri Baba Nasiru yace. "Muka barsu kuma, ai Allah ne zai barshi ba mu in bamu ɗauki mataki ba, Allah ya nuna ikonaa yanzu shi Jafar ɗin kallon me akeyi mishi?". Da sauri Gimbiya Saudatu tace. "Mahaukaci tuburan". Dariya sukayi kana cikin rashin gamsuwa Laminu yace. "To kuma duk da haka ai ba'a dawo da sarautar kanmu ba sai, aka bawa ɗan tsohon sarkin wannan bappan naku mai farin gemu. Bayan nan kuwa duk bawa kowa mulkin komai ba, dan sakacinku an ɗauki mulkin Garkuwa an bashi." Cikin sanyi Ya Hashim ya harari ƙanin nashi tare da cewa. "Laminu kafa ji tsoron Allah ka tsarkake zuciyarka, ka raba kanka da wannan zalumci da kafurar zuciya". Cikin zafi Gimbiya Saudatu tace. "Rufe min baki, samodaran banza sako tumaki ɓallo jakai,". Cikin sanyi yace. "Umma badake nakeyi ba da". Cikin mgnar in-ina Baba Nasiru yace. "Tafi daga nan damu kakeyi mana, ka fake da Laminu, maza tashi ka bamu wuri". Miƙewa yayi ya fita ya bar musu wurin ya nufi sashinsa wurin iyalanshi. Su kuwa nan sukaci gaba da sabgogin gabansu. Nan Gimbiya Saudatu ke cewa. "Sai gobe da sassafe zanje in salon hegen balaraben nan". Dariya Laminu yayi tare da cewa. "Yau da yaga haza, yaga zai zanu sai cewa yayi, wai shi ba bafulatani bane, a kirashi dama duk ƙabilar da akaga dama". Playing video yayi ya miƙa wa su Baba Basiru tare da cewa. "Jaridar safi ta gobe da safe da wannan labarin zai fito a shafin forko nako wanne kamfanin jarida, Kana wannan abun shine hirar da BBC Hausa da kanshi zasuyi karin kumallo dashi. Sai wannan lbri da video da hotuna sun bazu tako ina, dan ina jirane sai jaridu sun fidda shi kafin in watsashi kafafen yaɗa labarai na duniyar gizo-gizo". Cikin tsananin jin daɗi suka jinjina wa basirar Laminu. A can sashin Gimbiya Aminatu kuwa, kekyawar tsohuwar bafullatana ƴar kimanin shekaru 61 sosai hankalin ta ya tashi jin labarin abinda ya samu jikanta mafi soyuwa a gareta. Cikin rawan jiki ta miƙe tare da juyawa zata nufi Side ɗin ta. Da sauri Lamiɗo yayi gyaran muryar dake mata nunin ta zauna ta nitsu. Cikin tashin hankali ta koma ta zauna tare da cewa. "Allah Rane zanje in duba halin da yake cikine". Cikin ƙasaita da bada umarni yace. "Koma ki zauna ki nitsu kin ga magriba ta ƙara to. Bawai zan hanaki zuwa bane, ki bari ayi sallan magriba da isha'i sai ki aika Jakadiya ta dubo miki in idonshi biyu sai kije". Ba don ta soba ta amince da hakan. Hajia Mama kuwa, tana jin lbrin abinda ya faru daga bakin Abba, kai tsaye daga sashinsa sashin Jabeer ɗin ta nufa. A falo ta samu Haroon kadai zaune cikin shigar kakanan kaya. Cikin tashin hankali da kiɗima da firgici ta nufi hanyar side ɗin. Jabeer ɗin ido na zubda hawaye. Da sauri Haroon ya miƙa tsaye cikin sanyi yace. "Mama ya samu bacci ne, kuma Dr Aliyu yace kada a tadashi, jikin da sauƙi ma sosai ki kontar da hankalinki". Ina hankalinta bai konta da hakanba, saima ƙara kutsa kai cikin falon side ɗin shi takeyi. Cikin sanyi ta tsaya jin Haroon na ce mata. "Dan Allah Mama kiyi haƙuri, Allah kuwa jikin da sauƙin, Abba da Lamiɗo da kansu suka kula dashi, yanzu haka bacci yakeyi." Cikin tashin hankali murya na rawa tace. "Haroon hankali na ya tashi sosai, ina tsoron kada a cutar min dashi kamar yadda akayiwa Jafar." Hannunta ya kamo kana yaja suka dawo falo, cikin sanyi yace. "In Sha Allah babu wani abinda zai sameshi, in Allah ya yarda an gama samun nasara a kansu, yanzu warakace ke kusantosu, in sha Allah duk sarƙaƙiyan dake sarƙafe cikin masarautarku da mutanen cikinta zai worwore, za kuma ayi walƙiya kowa zai ga kowa!". Wani irin lumshe ido tayi tare da cewa. "Allah yasa haka". Cikin kontar mata da hankali yace. "Amin Amin. Umaymah ma tace tana nan tafe". Cikin tarin mamaki da baiyana tsantsar jin daɗin ta tace. "Alhamdulillah kai naji daɗin wannan mgnar ko ba komai in tazo ai zan samu wacce zan tattauna damuwar raina, sabida hirar waya bata wadatar wa". Murmushi yayi tare da nuna mata hanyar fita cikin tsokana yace. "Wato kun san ɗan naku ragone shiyasa duk kuka tashi hankulanku." Cikin share hawayenta tace. "Haroon yayanka nefa". Tura baki yayi tare da cewa. "To naji Hajia Mama je kiyi salla lokacin salla yayi, kinji an fara kiran salla". Da haka ta fita. Shi kuwa Haroon a hankali ya nufi cikin ɗakin, kamar yadda yabar Ya Jafar zaune a tsakiyar gado yasa Jabeer a gaba, yana karatu tare da gyara mishi rufuwar shi. Haka ya sameshi yanzuma, Kuma har zuwa yanzu idonshi bai daina zubda hawaye ba. Kana ganin fuskarshi zaka hango zazzafan so da ƙanan da tausayin ƙanin nashi cikin ƙwayar idonshi. A hankali Haroon ya matsosu. Cikin sanyi yakai hannunshi ya kamo hannun Ya Jafar ɗin. Kanshi ya ɗago ya zuba mishi ido. Murya cike da rauni Haroon yace. "Ya Jafar tashi kazo muje masallaci lokacin salla yayi. Muje muyi salla muyiwa Sheykh Jabeer Addu'o'in samun lfy". Kanshi ya gyaɗa sabida in dai abu na ibadane to bai kasance jiɓeɓɓe a kanshi ba. Sunkuyo wa, yayi ya sumɓaci goshin Jabeer kana, ya sauƙo kan gadon. ƙofar Bathroom Haroon ya nuna mishi da yatsa. Shiga yayi bayan ya fitone, shima Haroon ya shiga ya sabunta al'wala kana, suka fita. A babban falon suka samu, Aunty Juwairiyya da Jakadiyarsu suna shirya musu abinci bisa dinning table. Cikin kula Aunty Juwairiyya ta kalli Haroon murya a sanyaye tace. "Haroon ya jikin nashi dai?". Ɗan tsayawa yayi tare da cewa. "Alhamdulillah gsky zama muce ya worke, sabida ya amayarda duk wani dafin dake jikin bilalin yanzu naga shatin kunaman ma duk sun ɓace a jikinshi, ya zama sai shatin bulalin". Murmushi Jakadiyarsu tayi tare da cewa. "Suma nanda kwana uku in sha Allah babu tabonsu a jikinshi. Na gaya muku ai jinyar Shaɗi ba abu mai wuya bane a masarautar Joɗa, yanzu da asibiti aka kaishi, koda ko ƙasar waje za'a fiddashi a ƙalla sai anyi watanni uku ana jinyarshi, in yanada nisan kwana ya worke da kyar in kuma kwananshi sun ƙare ya cika a can. Amman yanzu yana tashi bacci zaiji sauƙin sosai". Cikin mamaki suka zuba mata ido. Jalal da Jamil da yanzu suka shigone suka haɗa bakin wurin cewa. "To wai Ummiy meyasa naga kamar farin cikin, abun kikeyi keda ko ruwan sama bakya son ya taɓa lfyarmu mu bare ɗan gatanki". Kanta ta ɗan jijjiga tare da cewa. "Abune mai duhu shekarun ku baiyi yawan da zaku gane haskenba, su kansu magautan Jabeer duk basu san ƙarfin iko da sani da shaharar wannan masarautar akan al'adun Shaɗi bane,." Jafar ne yayi gaba bayan ya duba agogon hannunshi ganin hakane duk suka bi bayanshi. A can Rugar Bani kuwa, bayan anyi sallan bamgrib, anyi Isha'i. Shatu, Rafi'a, Ummey, da kuma Bappa sai Autar gidan Junainah dake konce gefen Ummey duk sunyi shiru. Suna jin Bappa yana basu lbrin yadda komai ya faru a wurin gasar cikin sanyi yaci gaba da cewa. "Tabbas akwai abinda Allah yake nufi da wannan bawan, haƙƙun nasan Allah bazai bari a zalumceshi haka nan banzaba, inaji a jikina akwai wani babban al'amari mai girgiza zuƙatan mutane da zai faru a nan gaba". Cikin sanyin murya Rafi'a tace. "Bappa meye sunan jikan sarkin ne?". Cikin sanyi Bappa yace. "An faɗa amman na mance sunan". Sallamar da wani yaro yayine ya sasu maida hankalinsu kanshi, bayan ya rusuna ya gaisa Bappa ne yace. "Bappa ana sallama da Shatu wai tazo". A hankali Shatu dake zubda hawaye ta juyo ta kalleshi. Bappa kuwa cikin girma yace. "Waye ne?". Wani irin azabebben ajiyan zuciya Shatu ta sauƙe jin yaron yace. "...! By *GARKUWAR FULANI* "Ya Salmanu ne yake kirantan, yace tayi haƙuri tayi sauri ta fito." Cikin sanyin jiki Shatu ta manna kanta jikin kafaɗar Rafi'a. Shi kuwa Bappa, gyaran murya yayi tare da cewa yaron. "To je kace mishi tana zuwa." Jin haka yasa yaron ya juya ya fita. Miƙa Bappa yayi kana ya kalli Shatu murya a sake yace. "Shatu tashi kije, kiji dame yake nemanki". Cikin sanyi tace. "To". Kana a hankali ta miƙe dan cika umarnin Bappa. Rafi'a kuwa, miƙewa tayi ta shiga cikin ɗaki, gyara musu wurin konciya tayi, sannan tazo ta shigar da Junainah kana ta cewa Ummey su shiga, jiki a saɓule Ummey ta miƙe suka shiga. Bappa kuwa turakanshi ya shiga. A can ƙofar gidan kuwa. Bisa ɗan dakalin ƙofar gidan nasu, suka zauna. Tunda suka zauna tayi shiru, kanta na sunkuye tana wasa da ƴan yatsunta, kana hawaye na ɗigowa kan tafin hannunta. Shi ma Ya Salmanu shiru yayi, tamkar bazaiyi mgna ba. Farin wata kuwa ya fito ras ya haska ko ina, alamun yau watan ya kai kwana tara ko goma. Kanshi ya ɗan juyo ya ɗan kalleta cikin tsananin tausayawa ya fidda numfashi mai zafi tare da cewa. "Shatu!". Shiru bata amsa mishiba sai dai ɗago kanta tayi tana kallonshi hawaye na kwaranya, wani irin murmushi yayi cikin sanyi da harshen fillanci yace. "Bazan hanaki kukaba, Shatu, sabida koni kaina nakan zubda zafafan hawaye a duk sanda na tuna yayuna ƙannena makusantana, abo kaina da aka kashe, wanda basujiba basu ganiba. Nakanji zuciyata na tafasa, tafasar da nakejin bazai taɓa gushewa ba sai na ɗauki fansa." Cikin rawan murya tace. "Ya Salmanu fansa kuma?". Kanshi ya gyaɗa mata tare da cewa. "Uhum fansar dai, tunda hukuma da gwamnatin da masarautun gargajiya basu ɗauki mataki kan abinda akeyi mana ba. To mu zamu ɗaukarwa kanmu." A hankali tace. "Ta yaya ɗin bayan duk an kashe matasa majiya ƙarfin. Cikin kaso goma na mutanen Rugar Bani an kashe kaso 6 huɗune suka rage. Me amfanin ramuwa, wlh da zan faɗa aji da mun bar musu garinsu kawai mu koma wani wurin". Gyara zaman shi yayi ya fuskanceta da kyau cikin sanyi yace. "Ko wani ɗan adam ina ya shiga dumuwa, ire iransa ke shige mishi ya magance matsalar. Yanzu da ɗan jarida ɗaya aka kashe zakiga zakiji yadda ƙungiyoyin yan jaridu zasu magantu, sai ya zama babu wani rahoton da zasu buga sai na kashe ɗayansu da akayi. Hakama da za'a kashe police officer ɗaya zakiji yadda hukumar zatayi ta bincike da ɗaukar mataki har sai sun gano wayene sun kuma ɗauki mataki. Da za'a ƙona kamfani ɗaya ire irensa kamfanoni sama da dubu zasu iya shiga fadan. Hakama in da za'a taɓa ɗan kasuwa to zakiji yadda duk yan kasuwa zasuyi ta kumfar baki. Da za'a kashe manomi ɗaya to zakiji yadda gungun manoma zasuyi rubdugu kan mgnar. Da za'a taɓa bafaden wata masarauta zakiji duk masarautun ƙasarnan sun amsa. Haka abin yake. Duniyar ta zama waka sani? waya sanka? Mu kuwa Fulani bamu san kowa ba bayan Allah da Manzonsa, bamu da wani namu a siyasance. To tunda haka abin yake, muma da wannan salon zamuyi amfani. Muna nan munata raba goron gaiyata wa duk al'ummar fulanin makiyaya a duk inda suke a cikin duk faɗin duniyar nan, in dai sunada damar zuwa to su zo!. Su kawo mana agaji, wlh in sha Allah da izinin ubangiji sai mun yaƙi kafuran Bonon sai mun kashe dodon tsafinsu Bonon mun hallakashi a doron ƙasa, Shatu mun kai matakin da wallahi babu mahaluƙin da zai dakatar damu. Sai mun kauda Shirka da waɗannan mushirkan a wannan yankin." Ido ta rumtse wasu hawaye masu ɗumi suka zubo mata. Cikin muryar dake nuna ƙunar ranta tace. "Ya Salmanu wane mataki ake ɗauka kan neman su ya Giɗi kuma?". Kanshi ya jinjina tare da cewa. "Yana cikin matakin shiga cikin ƙabilar mu yaƙesu, mu kuma bincika ko sun ɓoye su Giɗi a cikin garin nasu". Ajiyan zuciya taja tare da cewa. "Allah ya taimaka". Amin Amin. Murmushi yayi kana yace. "Kinji batun gasar da akayi ko da nasarar dake tinkarar rayuwarki ko?". Cikin sanyi tace. "Kaiya ya Salmanu ina kake da tabbacin nasara mutumin da bamu san irin fansar da zai ɗaukaba, naso ace kaine kai wannan nasarar da nafi kowa farin ciki". Murmushi mai ciwo yayi a ranshi kana yace. "Nan ɗin ma muna zaton farin ciki, duk da akwai tarin ƙalubale, mu dai in mun samu wani ya ci Ba'ana a gasar Shaɗi kin san yayi al'washin zai bar ƙasar nan gaba ɗaya ko?". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Uhum in bai sauya salon ba dai". Cikin jin daɗi yace. "Ba zai sauya saloba, dole zai bar ƙasar sai dai shiri zaije ya ƙara, kafin ya dawo kuma, an aura min ke, shi kuma jikan sarki. Muyi musu mubaya'a, mun yarda su masarauta Joɗo fulani ne". Cikin tsananin jin daɗi tace. "Allah ya tabbatar da haka ya Salmanu yasa kuma a samo su Ya Gaini cikin Bonon don Ni dai nafi zaton can suka kaisu. In anyi gasar an cishi, ya bar kasar, a ɗaura aurenmu a ranar". Da sauri tasa tafin hannunta ta rufe idanunta alamun jin kunya, Shi kuwa Salmanu murmushi yayi tare da cewa. "Iye yan Matana an girma, me ma za'ayi mana?". Cikin kunya tace. "Ban saniba". Murmushi yayi kana yace. "Ni ai bazan manceba tunda yanzu burin mu na kusa da cika, ayi mana aure, nima haka ne tsarina ana watsewa gasar suna tafiya, za'a ɗaura mana aure. Kinga gashi dama na samu aiki a babban birninmu. Sai mu tafi can abinmu ko Wannan mugun saurayin naki ya dawo bazai samemu ba". Murmushi tayi shi kuwa ido ya zuba mata yana jin tarin farin ciki. *DAN ALLAH DA MANZONSA DA DARAJAR IYAYENKI DA SUKA HAIFEKI SUKA BAKI TARBIYYA, KADA KI FITARMIN DA LITTAFINA DAN AL'FARMA ANNABI DA AL'ƘUR'ANI, KU DENA FITAR MIN DA LITTAFI DAN ALLAH🙏🏻😭😭😭 Especially ku ƴan SPG na roƙeku da Allah🙏🏻😭😭 Da sauri ta gimtse dariyarta, cikin sanyi da tsoro ganinshi tamkar gilmawar walƙiya sai gashi a gabansu. Wani irin azabebben tsorone ya rufe Salmanu amman sai ya dake, cikin ƙarfin hali da kalato jarumta ya kame jikinshi dake rawa. Cikin ɗan rawan murya yace. "Me haka, zuwa babu sallama?". Wani mugun kallo ya watsa mishi tare da cewa. "Kiyaye bakinka idan maza suna wuri." Cikin dakiya Salmanu yace. "Ina mazan!? Ai ni banga wani na miji a nanba sai mata maza. Ai namiji shi zai iya sa namiji ɗan uwanshi zubda hawaye ko tsuma da faɗuwa, a dai yanzu ai babu wani namiji a Rugar Bani da kewaye sama da Jarumin da bulalar SHAƊI bata sashi zubda hawaye ba Sheykh nake nufi". Wani irin zabura Ba'ana yayi ya nufi kansa alamun zai shaƙeshi. Da sauri ya tsaya jin Shatu ta saki ihu tare da cewa. "Bana so ya Ba'ana in dai kana son farin ciki na, to kada ka dakeshi ko ka cutar dashi da komai". Wani irin kallo ya mata mai cike da tuhuma da razana da kuma karaya, Ita kuwa Shatu cikin rawan murya tace. "Ya Salmanu ka tafi, bana so kaje ka bar koya min komai". Cikin sauƙe ajiyan zuciya na tsoro. Salmanu ya juya ya tafi. Shi kuwa Ba'ana, zama yayi inda Salmanu ya tashi, cikin taraddadin ko dai Shatu bata sonshi ne, ya nuna mata gefenshi. A hankali ta zauna, shiru tayi tana sauƙe shessheƙan kuka. Cikin ƙuna da baƙin cikin rashin sa wancan ɗan birni mai fata kamar ta jariri kukanne ya sakar mishi fargaba, cikin sanyi yace. "Mata!". Bata kalleshi ba kuma bata dena shessheƙan ba. Kiranta ya kuma yi a karo na uku. "Mata!". Cikin disashewar muryar tace. "Na'am". Juyowa yayi ya fuskanceta da kyau a hankali yace. "Mata bakya so nane!?". A bazata tambayarshi tazo mata, ta ina kuma ta yaya zatace mishi bata sonshi, bayan tasan abin da yayi mata shekarun baya, dama fansar shi ta soshine kuma ta aureshi, da wanne bakin zatace mishi bata sonshi. wasu zafafan hawaye masu ɗumi ta zubda. Haƙiƙa ya Ba'ana mugune amman a iya saninta a kanta ya zama mugun, tunda sai wanda ya nuna baya sonta dashine yakewa mugunta, Babbar matsalarshi mushirkine kuma baya salla. Cikin rawan murya da kuka tace. "A a Ya Ba'ana Ni bance bana sonka ba". Da sauri yace. "Uhhmmm to meyasa bakya ganin laifin Salmanu akan duk abinda yake min, ko dai shi kikeso ne Mata!?". Da sauri ta jujjuya mishi kai sabida sanin ko jinkirin bashi amsa tayi zai iya yiwa Salmanu illa. Cikin rawan murya tace. "Bana son ka cutar da shine sabida, shi ya janye batun soyayyarsa gareni. Ka kuma sani karatu yake koya min amatsayinshi na wanda ya samu karantarwa a wata jami'a, Yana sona da al'khairi kai kuma kana ƙinshi, ko dai ka manta ka ce min zaka so duk wanda yake sona da al'khairi yake kuma taimaka min". Jiki a mace ya gyaɗa mata kai, sai kuma ya rumtse idanunshi da yakejin suna cikowa da hawaye yace. "Lokuta da dama sai inga kamar bakya farin cikin ganina, a madadin farin ciki sai inga tsorona cikin ƙwayar idonki." Juyowa tayi gareshi da kyau cikin kuka tace. "Ba kai ke bani tsoroba, abinda kakeyi ne yake sani tsoronka, ya Ba'ana ka bar wannan asirce-asircen babu kyau shirka ne, wanda yake ɗaya daga cikin manyan zunuban da Ubangiji ya haramtawa mumini yin tsafi haramun ne". Kanshi ya jingina da jikin gini yana kallonta tamkar yau ya fara ganinta, A hankali ya fara mgna cikin muryar da bata taɓa jin rauninta a muryarsa ba yace. "Mata ina sonki, wallahi Allah kenan rantsuwar musulmai, ina sonki, son da ni kaina bansan adadinshi ba, Duk abinda nakeyi a kanki nefa, Shatu ki min uzuri, na roƙeki kiyi min ɗa'ar riƙe tukuicin abinda nai miki a baya, Ki soni koda rabin yadda nake sonki ne. Kiji tausayina Shatu ina jin tsoron kada ƙaddara ta rabamu,". Kekkyawar fuskarshi ta zubawa ido, tana gani. Irin kyan da Allah yayi mishi sai dai sam babu kyan hali ya zama kyan ɗan maciji. Cikin sanyi tace. "Ya Ba'ana tsoro kuma?". Kai ya gyaɗa mata cikin sanyi yace. "Eh sabida muddin aka rabamu, zan zamewa fulani babban ƙalubale a rayuwarsa, kuma duk wanda yayi sanadin rabuwata da ke, wallahi zaiga toskun rayuwar duniya, zaiyi dana sani, zan zama mugun zahiri. Na san ke Kum bakya son hakan. Yau kuma fargaba na, yafi na baya yawaita da wannan jikan sarki ya iya daurewa azabar bulalina baiyi ƙollaba." Wani irin ajiyan zuciya taja tare da cewa. "Babu komai ya Ba'ana Ni dai ina tayi mana addu'an ALLAH yayi mana zaɓi mafi al'khairi a rayuwata, ya kuma shige min gaba a dukkan motsina". Ido ya zuba mata babu ko ƙebtawa, cikin sanyi yace. "Nine mafa al'khairinki Mata". Da sauri tace. "Baka saniba". A zafafe yace. "Na sani mana". Cikin tsoro tace. "Kai masanin gaibu ne kenan?". Miƙewa tsaye yayi tare da cewa. "Ehh kusan haka tunda nayi duba a kanki". A hankali tace. "Wa'iyazubillah. Duba ba gsky bane, zai iya maka ƙarya". Hannu ya ɗaga mata da sauri kana ya nuna mata hanyar shiga gida. A hankali ta tashi tsaye cikin sanyi tace. "Allah ya baka haƙuri ya shiryeka". Ta ƙarishe mgnar tana ƙoƙarin yin kuka. Da sauri ya juyo cikin sanyi yace. "Kada kiyi kukan mata, nayi haƙuri. yanzu na fasa jiran Sai kin gama karatu ayi mana aure. Duk randa wancan malamin ya dawo ya rama gasar Shaɗinsa. Za'a ɗaura auren mu a ranar, domin Koda duk bulalin duniyar nan zai zabgeni dasu wlh bazaici nasara a kainaba domin idona ba idon da zai zubda hawaye a kanki bane bilali ɗaya nake tsoro kuma babu wanda yasan inda suke. In kuwa aka samu wani akasin dama bazai samuba, to zan bar ƙasar nan zan koma ƙasar Cameroon can babban birnin Yahunde, inbi cikin Rugar wasu fulanin. Sai dai ko bana nan duk wanda ya aureki ya auri ajalinsa." Bata iya tanka mishiba, a haka ya juya ya tafi. Kana ita kuma ta koma cikin gida. A cikin masarautar Joɗa kuwa. Sai da akayi sallan isha kafin. Su Haroon suka dawo gida. Suna tafe, Abba da Lamiɗo da Galadima, da Dr Aliyu da kuma Sarkin Shaɗi. Suna biye dasu a baya. Kai tsaye wucewa sukayi har bedroom ɗin Jabeer har yanzu bacci yakeyi. Sai dai tunda lokacin salla yayi yaketa jin baccin ba daɗi sai dai kuma Allah bai bashi ikon farkawa ba. Dubashi sukayi tare da ƙara shafa mishi wasu magunguna kana suka fita suka tafi. Hakama Gimbiya Aminatu tazo itama har ɗaki sai dai samunshi yana bacci yasa ta tafi. Bayan fitanta ba daɗe Barrister Kamal da ɗan sa Sulaiman sukazo. Suma har ciki suka shiga suka dubashi. Kana suka tafi. A ranan a daren gaba ɗaya mutanen masarautar kowa yaji lbrin abinda ya faru. A falon su Jafar duk sukaci abinci. Ganin dare ya tsalane yasa Juwairiyya jan hannun Jafar suka tafi. Jalal, Jamil, Ya Hashim kuma sukayi musu saida safe kowa ya tafi side ɗin shi. Jakadiyarsu kuwa itama ta nufi sashinta, Ya zama dagashi sai Haroon. Sha biyu da rabi dai-dai na dare. Haroon zaune kan wata doguwar kujera irin ta sarakuna dake cikin ɗakin. Waya yakeyi da Jannart, yana konce ne dagashi sai boxes. Waya sukeyi irin ta mosoyan da shaƙuwarsu tayi yawa, Wani irin miƙa yayi wanda gaba ɗaya gabban jikinshi suka amsa. Cikin tarin kasala da masifeffen shauƙi yace. "Wash Allah na". Cikin kashe murya da ta ingizo Bukatarsa tace. "Ohhh sorry Ya Haroon meya faru gaya min me yasameka". Cikin sakaliyar murya yace. "Haroon yunwa yakeji". Sam bata fahimci inda batunshi ya dosaba haka yasa cikin haɗa fuska tace, "Ya Haroon ka dawo gida, shi Hamma Jabeer ba matace dashi ba, bare ya kula da cikinku, na kuma san in kuna Side ɗinsa ba wani zuwa wurin Aunty Juwairiyya zakuyiba, kuma itama fama takeyi da mijinta. Ni gsky ka dawo Tsinako nasan Umaymah zata kular min da kai da kyau, ko kuma kazo Masarautarmu Leddi julɓe, nida Sitti mu kula da kai". Murmushi yayi tare da cewa. "Masarauta Joɗo fa masarautace mai daraja, da karrama baƙo baki san asalin tarihin inda masarautar tasamu suna Joɗa bako. Baby kada ki damu kular da muke samu ko sarki mai mata huɗu da kwarkawara biyar baya samu. Tako wani sashi na gidan abinci hadimai ke kawowa Side ɗin Sheykh a ƙalla wani lokacin kusan abinci kala goma muke riska, kinsan fulani ba marowata bane. Kawai matsalar wannan yunwar rashinki ne, a kusa yasa nake jina ina tashi sama kamar doki". Cikin kunya da kauda zancen tace. "Ya jikin Hamma Jabeer shugaban tuzuran ƙasar mu?". A hankali ya juyo kanshi ya kalli bisa makeken gadon da Jabeer ke kai. Da sauri ya katse kiran bayan yace mata. "Ina zuwa". Kan gadon ya nufa, jabeer ɗin yana ƙoƙarin tashi zaune. Hannunshi daya miƙa zai taimaka mishi, ya buge cikin haɗe fuska yace. "Yanzu ƙarfe nawa?". Wayarshi dake hannunshi ya duba cikin zuba mishi ido yace. "Ƙarfe ɗaya dai-dai". Cikin tsuke fuskarsa tamkar zaiyi kuka yace. "Shine ka barni ina bacci kamar kafurin da bashi da addini. Anyi sallan bamgrib baka tasheniba, anyi Isha'i baka tasheniba, daga wannan masifeffen bacci mara daɗi mai cike da mafarkai marasa daɗin da nasan rashin yin salla a lokacin sane ya jazamin su. Iya wunin yau duk so kuke kuyi min asarar lokuta masu muhimmanci da daraja, kun sani na makara la'asar da magriba hakama isha." Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye, Tare daci gaba da cewa. "Da fari ansa ni na tsaya gaban jama'a da baiyana surata, Aka ɗora min da duka kana, akasa na makara sallan la'asar, Yanzu kuma mangriba da isha'inma kun barni ina baccin asara na makara, sabida baka san darajar yin salla a cikin jam'i da kuma yin ta cikin lokacin ta ba ko?". Cikin taɓe baki Haroon yace. "Kasan ai ni ba musulmi bane, ban san komaiba". Harara ya dannawa Haroon tare da cewa. "Kai ka gayawa kanka, Ni bana kafurta mutum, abinda na sani dai kai tsarin yahudu da nasarane, To bari kaji, Ni bani da laifin komai sabida bacci nakeyi, mai bacci kuma al'ƙalami ya sauƙa kansa har sai ya farka. Kai dake ganina ina bacci lokacin salla yayi idonka biyu baka tasheniba haƙƙin a kanka ya rataya." Ya ƙarishe mgnar yana shiga bathroom tare da cewa. "Ka cire idonka a kaina banza mai kallo kamar mayun wancan garin mugayen". Murmushi Haroon yayi tare da komawa ya zauna bisa kujerar. Shi kuwa Sheykh Jabeer wonka ya kumayi da ruwan ɗumi, kana ya kimtsa cikin irin suturun da yake ta'ammali dasu, in yana gida. kana ya ɗaura wata farar jallabiya kai. Sannan ya fito bayan ya shafa mai ya fesa turare. Yana fita ya fara ramuwar sallan daya wuceshi yana bacci. Haroon kuwa falo ya fita abincin da yasan zai iya ci ya kawo mishin A ƙalla awa ɗaya yayi kafin ya tashi kan sallayan Gaban gadonshin ya dawo ya zauna bisa tattausan carpet ɗin da ke shimfiɗe a wurin mai kalar Sky blue and white. Sosai yaji daɗin jikinshi, sai dai har yanzu yana jin raɗaɗin bulalin. Tea kawai ya iya sha. Kana a hankali yace wa Haroon. "Canza min beshit ɗin nan da blanket ɗin." Hararanshi Haroon yayi tare da cewa. "Zan koma, yaseen na gaji da mulkinka da sarautar da kake ji dashi. Ji yadda ka medani tamkar wani bawanka ko hadimin gidanku, kuma duk abinda zanyi maka sai ka cini gyara, mutum ba'a iya mishi sai masifa kake min kamar dai nine nace a zaneka". Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye tare da gimtse dariyarshi, sabida ganin kallon da Jabeer ke mishi. A haka dai ya sauya komai na gadon kafin suka, hau suka konta. Tsaki Jabeer yaja tare da cewa. "Ni dama ka tafi wancan ɗakin sabida zancen gsky kasan ni bana son takura. Sabida zaka hanani sakewa yadda nakeso". Cikin gajiya Haroon yace. "Allah babu inda zan fita inje". Da haka dai Haroon yayi bacci. Shi kuwa Sheykh Jabeer karatu yayi tayi har biyu da rabi tayi kana, ya buɗe tafin hannunshi yayi addu'o'in bacci. Falaƙi 3 Nasi 3 ƙulhuwa 3 Ayatulkursi'u 1 kana amarrasulu 1 tofa a tafin hannunshi ya shafa a jikinshi. Kana ya kuma yi. Haka ya tofa a tafin hannunshi ya shafa a jikin Haroon Wanda tuni ya ɓingire, Shi kuwa Jabeer wannan al'adar rayuwarsa ce daya saba, kan Jalal da Jamil sabida suma haka suke bingirewa, shikeyi tofi ya shafa musu. Washe gari Lamiɗo baiyi zaton Jabeer zai samu fitowa masallaci ba, Shiyasa limamin dake jansu salla in baya nan ya fito ya jasu salla, yayinda Jabeer ke cikin sahun forko. Wannan yasa mutane sukayi zaton ciwon ne yayi tsamari bai samu ya fitoba. Ana idar da salla kuma ya fito yayi cikin gida sabida. Fushi yakeyi da wannan tsohon ya sani in ya tsaya kuma zai dameshi da wata falsafarshi da zaici karo da addini. Ƙarfe takwas dai-dai. Barrister Kamal da Ya Jafar, da kuma Baba Basiru ne zaune dashi a falon shi. Suna zaune anan Jalal ya shigo cikin yanayin damuwa yace. "Hamma Jabeer, Umma na falo tazo dubaka da jiki." Cikin yamutsa fuska yace. "Wacece hakan?". Cikin fusata Baba Basiru yace. "Ashe uwarka ma bazaka santa ba, ina dai baka san wacece Umma ba". Wani irin kallon ido cikin ido Sheykh yayiwa Baba Basiru, sai kuma ya ɗora ƙafarshi ɗaya kan ɗaya, cikin ƙasaita ya kalli Jalal tare da cewa. "Mene Umman!?". Ya sani sarari Gimbiya Saudatu ake cewa Ummu . Gyara tsayuwa Jalal yayi tare da gyara zaman belt ɗin ƙugunshi yace. "Matar tsohon Galadima marigayi, Baba Muhammad ce Ummar Gimbiya Saudatu." Da sauri Baba Basiru yayiwa Jalal daƙuwa tare da cewa. "Kan uwarka hegen yaro ɗan shila". Shi kuwa Jabeer ƙafarshi ya fara kaɗawa. Barrister Kamal kuwa ido ya zubawa Fuskarta Jabeer da Jalal. Cikin sanyi da tausasan laffuza yace. "Jabeer tashi muje ka gaisa da ita tunda ta taso tazo har nan dubaka da jiki". Kanshi ya gyaɗawa Barrister Kamal ɗin wanda suke cewa Baba Kamal wanda yake mahaifin Sulaiman, sa'an Jabeer. Da hannu yayiwa Jalal alamun yaje yace, yana zuwa. Shi kam Baba Basiru bayan Jalal yabi. A babban falon suka zauna shida Gimbiya Saudatu da Laminu da kuma Baba Nasiru. Jalal, Jamil, Haroon, Jafar, kuwa duk suna can Dinning area kan dinning table sunayin breakfast. A jere suka fito falon shida Barrister Kamal. Suna isowa tsakiyar falon. Cikin wani irin taku mai cike da ƙasaita da rashin tsoro. Ya kalli Gimbiya Saudatu dake zaune bisa kujerar zamanshi. Yatsunshi biyu ya haɗa ya kaɗa mata tare da mata alamun tashi min kan kujera. Cikin wani irin kallo mai nuna tsantsar fushi da tsana da zazzafan ƙiyayya ta fara mgna cikin ɗaga sauti tace. "Hegen yaro mai idanun mujiya, Ni kakeyiwa wannan iskancin dan kan uwar..!". Kasa ƙarisa zagin da tayi nufin yi tayi jin yana cewa. "Kan uwarki ko? Ki ƙara sa mana kikaga ikon wanda ya hana mata gemu ya baiwa maza! Maza tashi min kan kujerar zama tunda ba wancan jiɓeɓɓen tsohon akun bane seyota". Wani irin zabura Baba Nasiru yayi tare da ɗaga hannu zai kifeshi da mari, kamar a mafarki yaji an riƙe mishi hannunshi da sauri ya juyo. Ido ya zaro cike da mamakin ganin wanda ya riƙe mishi hannunshi cikin tafasar zuciya da ƙuna yace. "J....." By *GARKUWAR FULANI* Cikin wani zare ido na masifa yace. "Jalal ni ka riƙe wa hannu". Shima idon ya zare tare da cewa. "Ba iya rikeshi kaɗai zanyi ba, in dai zai taɓa lfyar ɗan uwana a gaban idona, datseshi zanyi gaba ɗaya in wurgar". Ya ƙarishe mgnar da ƙarfi tare da yarfa hannunshi. Wani irin asirtaccen murmushi Barrister Kamal, yayi tare da kallon ɗan shi Sulaiman hannunshi ya dunƙule ya jinjina wa Sulaiman ɗin. Kana suka koma suka zauna bisa kujera. Shi kuwa Jabeer hannun ya nunawa Gimbiya Saudatu alamun ta tashi. Mirtsitsi tayi tare da gyara zamanta. Wani irin firgitacen tsawan da Jalal ya danna matane yasa, ta miƙe tsaye ba tare datasan ta miƙa ɗin ba. Cikin ƙasaita Jabeer ya baza tattausar al'kyabbar jikinshi, Kana ya matso ya zauna bisa kujerar ƙafarshi ɗaya ya ɗora bisa ɗaya. Gyara hiramin kanshi yayi tare dayin gyaran murya kana ya kalli ƙannen mahaifin nashi kauda kanshi yayi ganin yadda suke wani irin cika da batse sun cika sunyi tamtsan da fushi. Ita kuwa Gimbiya Saudatu zama tayi a kujerar dake kallon tashi kujerar. Itama ɗaura ƙafa ɗaya tayi kan ɗaya. Cikin iya tijara ta watso sabbin jaridu gabanshi. Jaridar bankaɗa da kuma kamfanin jaridar hantsi wato leƙa gidan kuwa. Murmushin muguntan tayi tare da cewa. "Ga sakamakon sa insa da kayi dani jiya, na yau kuma shima yana nan tafe. Nayi maka murna darajar labarin ya kai matsayin da shine a shafin forko na jaridun". Da sauri Jalal ya sunkuyo yasa hannunshi ya ɗauki jaridar banƙaɗa. Jiki na tsuma ya ɗago ya kalli Gimbiya Saudatu cikin tashin hankali yace. "Wannan ƙarya ne, da babu jahilin da zai yarda dashi, wlh bazaku taɓa cin nasara ba." Hankali a tashe ya miƙawa Haroon jaridar tare da cewa. "Ya Haroon gani zancen banzan da aka rubuta kan hotunan Hamma." Da sauri Haroon dake sauƙowa kan stpes ɗin sauƙowa falon daga dinning area, ya ƙaraso. Hannuyasa ya amshi jaridar. Wani irin azabebben zufane ya fara keto mishin ganin abinda aka rubuta a jikin jaridar. Jin jikinshi na rawane ya sashi zama kusa da Sulaiman. Ummi kuwa dake tsaye a dinning area tana haɗawa. Jafar abin da zaici, gaba ɗaya ido ta zubo musu cikin taraddadin me aka rubuta. Ita kuwa Gimbiya Saudatu wata iriyar shaƙiyiyar dariya tayi tare da cewa. "Ya haka dai ƴan kanzagi, ku bawa shi uban gidan naku, jaridar yage me aka rubuta, daga nan sai inga bakinshi da baya mutuwa da bada amsa ko zai iya cewa wani abu." Baba Nasiru da Baba Basiru, ma fuska cike da farin ciki suka zauna. Laminu kuwa miƙewa tsaye yayi tsakiyar faffaɗan falon cikin ɗaga sauti yace. "To tunda bazaka iya bashi ba, bani ni in karanta mishi." Yana ƙarishe mgnar yasa hannunshi ya amshi jaridar. Cikin ɗaga sauti ya fara karanta rubutun dake rubuce a ƙasan hoton da gefe da gefenshi. "Abun kunya, ya baiyana jikan sarki Nuruddeen Bubayero ɗaga Habibullah, Yayiwa ɗiyar Fulani fyaɗen da yasa. Hanun Sarki Lamiɗo ya kama hannun Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero wanda yake limamin masalacin ƙofar sarki ya miƙa shi ga hukumar addini musulunci. Gashi anayi mishi bulalin haddi kamar dai yadda Musulunci ya wajabta. Wani irin murmushi Jabeer yayi, hannunshi yasa ya shafa tattausan gemunshi. Cikin rashin karaya ya kalli Haroon cikin nitsuwa yace. "Ɗan wannan abun ne kuke zaton zai kashe wannan bakin nawa da yake rayuwa da ambaton Allah!? Shin ko kun mance tsawon shekaru da dama ana fataucin rufe bakin Ya Jafar, shima har yau baku samu nasarar hanashi ambaton Allah ba, Duk sharrinku ya zame mushi al'khairi, tunda baya wani motsi ba tare daya kira sunan Allah ba, ikirarin ku na ya zauce, ya tabbata kune zautattun". Sai kuma ya ɗan kalli Gimbiya Saudatu, murmusawa yayi tare da cewa. "Baki nafa bazai mutuba sai in nufashina ya bar jikina, batun shiga ɗakin sirri kuma, nifa wannan abin da kuketa haƙilo a kai ba wani baƙon abun bane a wurina. sarauta a cikin jin jikina yake." Sai ya kuma juyo ya kalli Haroon da jikinsa yayi la'asar da lamarin su, miƙewa tsaye yayi tare da cewa. "Haroon wai ɗan wannan makircin nasune ya kashema jiki. To kontar da hankalinka. Ni nan Muhammad Jabeer ƙi gudune sa gudu. Tun kan suyi tunanin yin abu a kaina na nazarci abun." Juyowa yayi ya kalli Baba Nasiru cikin tsareshi da ido yace. "Kaje duk inda ake saida jarudu ka bada farashin one million akan ko wanne jarida kaga in za'a fito maka da wannan jaridar, in bada wannan ƙwaya ɗayar kaga dai itama kuma gata a gabana." Cikin tarin mamaki suka zuba mishi ido. Shi kuwa gaban Laminu ya isa cikin isa ya miƙa mishi hannunshi tare da cewa. "Bani shi nan". Cikin tsananin tsoro da firgici ƙarara. Jiki na rawa Laminu ya miƙa mishi. Sabida kwarjin Jabeer ya mishi nauyi a idonshi ya kuma san artabu dashi ba daɗi. Ita kuwa Gimbiya Saudatu wani murmushi tayi mai cike da taraddadi da al'hini da nazarin yadda zataga bayan wannan yaron mai bakin tsiya. Jaridar gabanta ta miƙa mishi. Kanshi ya girgiza tare da kaɗa mata yatsarshi manuniya cikin rashin tsoro da ƙasaita yace. "Ba kifa kai matsayin da zaki nuna min wani abin da idanuna basu rigaya sun ganiba ko basu san dashiba domin ke a makance kike rayuwarki, Ni kuwa nan da kike gani idona buɗe suke ras. Ita wannan itace tayi bayanin abinda ya faru na gsky a Rugar itace tai bayanin cewa bulalin shaɗi akayi min bana Haddiba to sai me kuma!?". Shiru sukayi gaba ɗayansu. Kowa da abinda yake nazarta a ranshi sai bugawar da zuciyoyinsu keyi. Buɗa al'kyabbar jikinshi yayi tare da kuma haɗe ta cikin fillanci yace. "In kun gama ihun ku ficemin daga Side ɗina Dan ba haɗamu akayi ba. Kuma ku sani (MOH ALLAH WUJI FURƊATA)." Yana faɗin haka ya juya ya nufi falonshi. Ita kam Gimbiya Saudatu ta cika tayi maƙil. Baba Nasiru da Baba Basiru kuwa, A kufule suma suka fita. Haroon kuwa ido ya zuba musu. Barrister Kamal kuwa murmushi yayi mai tarin ma'anoni kana shima ya fita Sulaiman na biye dashi. A hanyarsu ta komawa side ɗinsu ne, Gimbiya Saudatu ta kalli Laminu cikin takaici tace "Banza kawai me tsoron zuci me dan ya matso kusa dakaii ka wani firgita ka razana har ɓari jikinka keyi ka miƙa mishi jaridar, da zamu iya kaita a tallata". Wani irin wawan ajiyan zuciya Laminu yayi tare da cewa. "Uhummmm Umma kenan wato, fa duk wannan kumfar bakin da kikeyi abinda yasa kike yinta da jin daɗin yinta, dan wancan Jabeer ɗin bai taɓa kifa miki bari bane shiyasa. Wallahi Allah da ya taɓa marinki da waɗannan hannayenshi da kike ganin taushinsu kamar na jarirai shakka babu, wlh suma zakiyi sai an yayyafa miki ruwa". Cikin kufula Baba Basiru yace. "Kai tafi daga nan banza mai zuciyar mata, ji abinda kake cewa kan mari ɗaya tak daya taɓa yi maka". Wani irin kallo Laminu yayi musu kab lokacin da suka shiga falon Gimbiya Saudatu. Cikin rumtse idonshi sabida tuno marin da Jabeer ya kifa mishi randa yayi gangancin zai zageshi. Da sauri ya buɗe idanunshi cikin kara yace. "Yesss sabida baku ya shararawa mari ɗayanba shiyasa. Kuna sanefa mari ɗayan da yayi min. A take kunnena ya rinƙa zubda jinin da Ni dai har yau bansan ta inda ya ɓulɓuloba, wlh Allah lokacin daya mareni kusan suma nayi, har yau in na tuno marin sai inji kunnena yayi gummmmm". Cikin zafi Gimbiya Saudatu ta yunƙuro zata surfawa ɗan nata masifa, sai ta kuma komawa ta zauna jin Baba Nasiru na cewa. "Uhummm Dafa gskyar Laminu, in dai Jabeer ya ɗauki hannun mahaifinshi to tabbas, suna da zafin hannu mai ban tsoro, In dai ya gado hannun Ya Habibullah to fa duk abinda suka mara wlh in dai dabbace sai dai a matso mata da wuƙa, in kuwa mutum ne to, tabbas zai sha azaba mai raraɗi. In jifa ne ma sukayi ma basa saɓawa saiti sai sun samu abin harinsu, in kuma tsuntsune ko ƙananan halittu tofa in suka harba sai lahira." Sai kuma ya ɗan tsaya ya kallesu cikin dakiya yace. "Munada buƙatar sabon shiri, akanshi, zamuyi mgnin bakinshin nan da baya mutuwa". Cikin takaici Gimbiya Saudatu tace. "A duk cikin ababen da ake dangantawa dasu babu, abinda yafi cimin rai kamar meda, zoo ɗin masarautar sade ɗin Jabeer. Wlh duk sanda najiyo kukan Ɗawisun Masarautar da sauran tsuntsaye nakiji kamar in je in samisu shinkafar tsuntsaye suci su mace kab ɗinsu kowa ma ya huta." Barrister Kamal dne dake, Jinsu ta window ɗin falon. Ya jinjina kai tare da jan hannun Sulaiman suka tafi yana mai cewa. "Uhum naku burin dai baza taɓa cikaba in sha Allah". Su kuwa nan sukaci gaba da tattaunawa yadda shirunsu a kanshi zai kaya. Jakadiyarsu kuwa saida taga fitansu ta sauƙe ajiyan zuciya. Jafar kuwa saida yaga Barrister Kamal ya fita kafin jikinsa ya dena rawa da karkarwa. Shi kuwa Haroon da sauri yabi bayan Jabeer cikin sauƙe nannauyan numfashi yace. "Wato kai bakinka bazai mutu bako." Cikin kufula ya juyo ya kalli Haroon jin ya yace mishi irin Abinda kullum Abba yake cemishi. A hatsale yace. "Eh bakina bazai mutuba ba kuma zan bar ko wanne taƙadirinba, duk wanda yace dani tak zai samu amsa dai-dai da zancensa. Wannan zarerriyar matarfa ta kiyayeni, kadafa ta fusatani, tam!". Ya ƙarishe mgnar da taune lips ɗinshi. Cikin sanyi Haroon yace. "Nifa tsorona ɗaya Jabeer kada su cutar da kai, so dan Allah duk abinda zasuyi maka kosu Jalal da ya Jafar kada ka tanka musu. Yanzu wannan sharrin ya zamuyi dashi?". Wani irin kallo yayiwa Haroon cikin sauƙe numfashin yace. "Tuni na magance ta, na saye jaridun, tun kafin a fiddasu, shima dan ya ɗauka ne tun kafin inji inje wurin. Kuma gashi shima a hannun yanzu sai dai su nemo wani sharrin. Kuma batun basu amsa, da sun gane sun dena sako Mahaifiyata a duk abinda zasuyi min da Ni dai ko kallo basu isheni ba." Cikin sauƙe numfashin Haroon yace. "To Alhamdulillah Allah ya kare gaba". Amin yace tare da zama bisa kujerarshi ta musamman wacce take kyautace ga Sheikh Abdulkarim. Tab ɗin shi ya ɗauka ya fara wasu yan dube-duben. Anan falonshi suka zauna, shida Haroon. Jin muryar Gimbiya Aminatu na ratso falon ne yasa Haroon yin murmushi cikin sabo da tsohuwar yace. "Yauwa Gimbiyar Lamiɗo kizo kiyiwa wannan jikan naki faɗa". Murmushi tayi mai ƙayatarwa, a hankali ta ƙara so cikin falon ita ɗaya hadimanta suka tsaya a can babban falo da abincin data kawo mishi. A hankali tayi taku zuwa gabanshi gefenshi ta zauna, cikin sanyi ya kalleta. Ita kuwa cikin kulawa tace. "Jabeer, ya jikin naka". Cikin harshen fillanci yace. "Da sauƙi". Yadda ya bata amsa a taƙaicene yasa ta kalli Haroon tace. "Yaci wani abu kuwa?". Da sauri yace mata ehh. Cikin kula tace. "Me yaci!?." Murmushi yayi cikin tsokana yace. "To da sanyin safiyar nan dai an sanshi magantuwa". Dariya ta ɗan yi tare da cewa. "Taso kuzo kaci abinci". Kanshi ya girgiza mata tare da cewa. "Bana buƙatar komai, kawai ki gayawa wannan dottijon mijin naki da sufanshi baya gaya mishi dai-dai ya gargaɗi Gimbiya Saudatu ta dena zuwa min side ɗina. In kuwa taƙi wata ran zan bar Jalal yayi mata ɗan karen duka". Murmushi tayi tare da cewa "To naji taso muje kaci wani abun". Dai-dai lokacin Lamiɗo da Galadima suka shigo. Ɗanzagi da dogari kuma suka tsaya a can bakin ƙofar shigowa falon. Bayan sun zauna ne Lamiɗo yace. "Ya ƙarfin jikin?". Rai a ɓace yace. "Ai baka da case da raina da lfyata, ko in samu sauƙi ko kada in samu ba matsalarka bace, tun da gani kake iyayena sun haifa maka nine dan ka bawa wasu ƙattin daji su dakani". Murmushi Lamiɗo yayi cikin tsokana yace. "To wai in ban basu kaiba wa kake son in basu?". A hatsale yace. "Ka basu kanka mana, me zai hana kai ka tuɓe gwanjinka a zaneka, dan masifar rainin wayo sai ka nunani, duk da tarin jikokinka da suke wurin." Murmushi Galadima yayi tare da cewa. "Yanzu dai jikin da sauƙi gashi, har zanar ta maidaka mataɗaci, ka fara shiri nan bada dadewa ba za mu koma ka rama". Da sauri ya ɗago kanshi daga kallon Tab ɗinshi ya zuba musu tare da nuna kanshi. Ido suka zuba mishi. Shi kuwa cikin tsuke fuskarsa tamkar zaiyi ruwan jini yace. "Ni! Ni!! Ni!!! Muhammad Jabeer Kuma a wancan garin, me zanje inyi a can, wannan garin ko a mafarki bana fatan Allah ya gwada minshi, dan Wallahi Allah kenan duk duniya babu garin da na tsana sama da wannan garin. Na tsani garin bana ko son jin makamacin sunan garin. Da garin da mutanen garin gaba ɗaya basa cikin jadawalin jerin mutanen da zuciyata zata sosu har gaban abadan me na samu a wannan garin banda tozarci da ɓaƙar azaba." Murmushi Lamido yayi kana cikin son jikan nashi ya dafa kafaɗarshi tare da cewa. "A makon-nan ma kuwa zaka koma wannan garin da izinin Allah". Mgnar Lamiɗo ta ƙarshe da yace da izinin Allah ne yasashi yin shiru. Haka suka ƙaraci mgnarsu bai kuma ɗago kanshi ya kallesu bama bare ya kulasu. Bayan sun tafine. Ummi da Gimbiya Aminatu suka samu suka sashi ya ɗanci abinci. Zuwa azahar kuwa sai ga Sarkin Musulmi Jalaluddin da Sitti. A sashin Gimbiya Aminatu Sitti ta sauƙa shi kuwa Jalaluddin a sashin amininshi Lamiɗo ya sauƙa. Saida akayi sallan la'asar kafin suka isa sashin, Jabeer. Sosai suka nuna mishi kulawa da gata, Inda yaketa son huce haushin da yakeji a kansu tunda sune dai suka sashi yin wannan abun a bisa dole. Hajia Mama kuwa daɗi kamar ta goya Sittin dan kulawa da so. Sai washe gari. Suka koma Laddi julɓe sunan jihar da nanne asalin tushen masarautar sarkin Musulmai yake. Mama kam hankalinta ya konta ganin jikin Jabeer yayi sauƙin sosai. Batul kuwa babu nacin da batayiba ta samu ta ganshi ido da ido abin yaci tura. A haka kwanaki sukayi ta tafiya, ana bawa Jabeer kula tamusamman. Yayinda Sarkin Shaɗi kuwa yake ta tsuma bilalin Shaɗin masarautar Joɗa wanda a ƙalla tsawon kusan shekaru ɗari biyu da wani abu. Suna binne cikin ramin tsuminsu Wanda da dafin macijin gadin masarautar ake tsumashi. Umaymah kuwa tana shirin zuwa duba jikin ɗan ƴar uwar tata ɗa mafi soyuwa a gareta sama da ƴaƴan data haifa a cikinta ma. Yau kwana biyar da faruwan abun. Sosai jikinshi yayi ras. Yaune kuma Umaymah ke tahowa jirgin yamma zata biyo. Shi kuwa Jabeer zuwa yanzu ko mgnar kowarshi wannan garin ba'ayi sabida irin ɓacin rai da yake baiyana a fuskar shi, in an mishi mgnar zuwa garin. Allah ya sani yana jin ya tsani wannan gari tsana mai tsanani. Yana masifar jin kunyar komawa na wannan garin da a tsakiyarshi akashi cire suturarshi ya zauna dagashi sai boxes. Yakanji kamar ya faɗi ya mutu in ya tuna garin. Ƙarfe biyar dai-dai motocin da suka ɗauko Umaymah suka iso cikin harabar masarautar. Dai-dai lokacin kuma Hajia Mama da Batul suna gab da shiga sashin Jabeer, A tsakiyar falon sukayi kiciɓis dashi. Yana sanye cikin tufafin da sune suturarshi, al'kyabbar ruwan madarace, sai kayan dake cikin al'kyabbar su kuwa ruwan bonbitane, yayi wani irin masifar kyau, sai ƙamshi yake bazawa tako ina. Fuskarshi ta fito ras cikin hiraminshi ruwan madara, Wani irin ƙyalli da sheƙin kyau yakeyi. Duk da ba murmushi a kan fuskarsa amman ana iya gano tsantsar farin cikin da yake ciki. A hankali yake taku, Ya Jafar na biye dashi a baya, Cikin tarin kula da nuna soyayyarsa Hajia Mama tace. "Masha Allah, Ɗan Umaymah yayi kyau, ga farin ciki ya wadaci kekyawan fuskarnan taka". Kanshi ya ɗan kauda ya kalli Ya Jafar daketa jan hannunshi su fita, cikin nitsuwa yace. "Sun isoma". Cikin jin daɗi tace. "Eh haka dai Jamil ya gaya min". Ta ƙarishe mgnar tana juya baya tare da Batul da cikin sanyi tace. "Ya Jabeer ya jikin?". Cikin jan gajeren tsaki yace. "Lfyata lau". Murmushi tayi sabida jin zazzaƙar muryar shi. A tare suka fito su Mama na gaba shida Jafar suna baya. Suna fitowa harabar Side ɗin shi. Motarshi da Sheykh Abdulkareem yasa aka taho mishi da ita wacce bai taɓa hawantaba, asalima gani yake tamkar almozzaranci ne, sai yau ya bawa Haroon key ɗin ta yace a ɗauko mishi Umaymahnshi, shi bazai je ɗaukotaba sabida. Lamiɗo yace bazai fitaba. A hankali ya tsaya ganin hancin motarshi ƙirar Mercendes benz maybach Exelero wacce ta kai kimanin $8 million dollars. Da sauri ya ƙarasa jikin motor. Hajia Mama na biye dashi. Yana isa inda suke yasa tattausan hannunshi ya buɗe marfin motar. Karo na forko da naga murmushi a fuskarshi, cikin tarin shaƙuwa da kulawa yace. "Marhababuki ya Umaymah, ta faddal". Wani irin murmushi Umaymah tayi cikin tsantsar so tasa hannu ta kamo hannunshi daya nuna mata alamun ta fito. Wani irin yalwataccen murmushi mai nuna tsantsar jin daɗi ya kumayi lokacin da yaji tasa hannunta tsakiyar kanshi. Da sauri ya rusuna a bakin motar cikin sanyi ya manna kanshi da guiwowinta dake zuro woje, kanshi ta shafa tare da cewa. "Allah yayi maka al'barka ya kare mana kai da kariyarsa mai tarin yawa ya iya maka abinda idonka baya gani". Amin Amin, su Haroon da Jalal, Jamil, Hibba, ƙanwar Haroon, da kuma Imran, Sulaiman, Aunty Juwairiyya dake kusa da Umaymah. suka amsa tare da murmushi a fuskokinsu. Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya tashi kana ya buta hanya ta fito. Tana fitowa Hajia Mama ta ƙara so gareta cikin tarin baiyana jin daɗi ta ruggume Umaymah tare da cewa. "Ta ɗanki kawai kikeyi, mu har mun kusa mu bushe a tsaye". Murmushi Umaymah tayi tare da cewa. "Afwan ya Aunty kin san in Jabeer na yana wuri bana ji da ganin kowa sai shi". Haroon ne ya taɓe baki tare da cewa. "Uhumm ai mun saba ganin wariyar launin fata". Hannunta tasa ta ɗan zunguri Haroon tare da cewa. "Kishi". Jamil ne ya ɗan kallesu lokacin da suka ɗunguma suka nufi Sade ɗin Jabeer cikin tura baki yace. "Allah ko Mama kada ki bari Umaymah ta sauƙa a sade ɗin Hamma in dai ba sade ɗinmu zata sauƙaba Muda muke ƙanana sai ta sharemu saishi. Tunda hakane ta sauƙa side ɗinkin". Cikin dariya Umaymah ta juyo da sauri ta kalleshi tare da cewa. "To Jamil harda kai, wato kaima ɗan team ɗin Haroon ne ko? To sha kuriminka Aunty bazata shiga tsakanin uwa da ɗaba, ko Hajia Mama?". Ta ƙarishe mgnar tana kallon Hajia Mama daketa murmushi cikin jin daɗin tace. "Haka kuma ɗa bazai shiga tsakanin ya da ƙanwaba, Gaba ɗaya Jabeer ya kwace mana ke". Murmushi mai kama da dariya sukayi gaba ɗayansu lokacin da suka shiga cikin falon. Shi dai Jabeer sai murmushi yakeyi. Ya Jafar kuwa in yaga Jabeer na murmushi sai shima ya ɗanyi murmushi. Aunty Juwairiyya ce ta ɗan kalli Batul dake gaida Umaymah sakin fuska tace. "Matar ƙani yau tun safe ban jikiba". Wani irin murmushin jin daɗi tayi Allah yasani in Aunty Juwairiyya tace mata matar ƙani tana jin daɗi. Cikin happy tace. "Yau a kitchen na wuni inayiwa Umaymah girkinsu na larabawa". Murmushi Juwairiyya tayi tare da cewa. "Yo ai na rigaki, dama girkin bare bari kikayi mata". Kanta ta ɗan juya takalli Sheykh Jabeer dake zaune kusa da Umaymah, in zaiyi mata mgna sai ya juya harce zuwa larabci. A ranta take addu'o'in Allah ya nuna mata ranar da zata zauna kusa dashi haka a matsayin abar sonshi. Tattausan Lips ɗin shi masu kama da kunnen fure ta kalla. sunan jazir sai sheƙi sukeyi a cikin tattausan sajenshi da gemun tamkar an shafa musu mai. Allah ya sani randa ta samu lips ɗin nan a matsayin mallakinta, tabbas sai ta kusan haɗiyesu. Hajia Mama da kanta da ita da Aunty Juwairiyya ne suka rinƙa kawowa Umaymah abubuwan motsa baki yaran yar uwarta na zagaye da ita, Hibba ce yar autarta ta ƴar kimanin shekaru 16 kalli Jabeer cikin cikin sanyi tace. "Hamma Jabeer Aunty Jazrah tace in gausheka, wai yaushe zamuje". Kanshi ya juyo ya ɗan kalli Hibba cikin son yarinyar yace. "Hibba auta yaushe kikeso muje". Da sauri tace, sai na tambayi Aunty Jazrah". Murmushi yayi kana ya kalli Aunty Juwairiyya yace. "A shigar mata da kayanta, a ƙara gyara mata masauƙinta, yafi fadar Jalaluddin kyau". Dariya sukayi baki ɗayansu. Shi kuwa Sheykh Jabeer kamar ba shi yayi mgmar ba. Ita kuwa Umaymah da Hajia Mama hararanshi suka ɗanyi tare da cewa. "Ai babu fadar da zatafi fadar shi kam, shinefa gatanka". Murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "A a kam Allah ne gatana, shi kuma da yake son ayi ta ɗimata". Juwairiyya kanta tayi mamakin sakewar Jabeer sosai Duk wanda ya ganshi zaiga tarin farin ciki tare dashi. Nan dai suka zauna akayi ta hira. Saida aka kira magriba ne, duk suka miƙe sukaje sukayi al'wala. Batul kuwa tafi kowa farin cikin, zuwan Umaymah ko ba komai ta samu ganin Jabeer yadda take so. Bayan an idar da sallan isha'i ne suka dawo masalacin. A nan bisa dinnin area. Suka zauna nan sukaci abinci. Koda suka gama ne, sunata hira a falon harda Jakadiyarsu. Jabeer ne da yanzu ya fito falonshi cikin nitsuwa yace. "Kai dan Allah ku barta ta huta mana". Sai ya kuma ɗan kalli Umaymah tare da cewa. "Umaymah muje ki gaisa da Lamiɗo, ya kirani yanzu yanata min ihu a kunne wai yaji kin iso tunda yamma kuma ban kai mishi keba". Da sauri ta miƙe tare da cewa. "To muje". Hibba ce ta tashi da nufin binsu sai kuma ta zauna, jin Jabeer nace mata. "Zauna Hibba saida safe kuje da Jalal." Sai ya kuma kalli Jakadiyarsu cikin taushin murya yace. "Ummi muje". Itama da sauri ta miƙa. A tare suka fito yana gaba Umaymah na binshi, Jakadiyarsu na bayansu. Suna tafe cikin jin daɗi ko ina yayi lib sai sanyin korayen ciyawi da furannin da dogayen bishiyoyin gwanda da ayaba da sukayiwa ko ina ƙawanya. Suna isa ƙofar Gimbiya Aminatu da sauri. Sallama ya basu hanya, wanda a ƙa'ida sai ya shiga ya nemawa mutun izinin shiga kafin ka shigo. So amman Jabeer baida hijabi da sashin kakanin nashi, shiyasa kai tsaye suka wuce. Shiru babban falon babu kowa. Haka yasa suka wuce sashin Lamiɗo, a hankali yayi sallama, Cikin murmushin Lamiɗo ya amsa sallamar tare da cewa. "Bismillah, ku shigo". Kusan a tare suka kutsa kai cikin tamfatsen falon nashi. Wani irin kallo sukayiwa juna, Ganin...! By *GARKUWAR FULANI**MEVYASA? ME YAYI ZAFI SHI BA WUTABA? ME RIBARKU A CIKIN FIDDA LITTAFINA WOJE KU WATSASHI WA DUBBAN MUTANE? ME FA'IDAR HAKAN? NIYARKU KO TUNANIN KI, KADA WASU SUZO SU SAYA NE? A ZATONKI DANKU DAN KU ƁATA MIN RAINE? KO KUNA ZATON ZAKU HANANI SAMUN BINDA ALLAH YA RIGADA YA ƘADDARA YA RUBUTA RABO NANE? Nayi matuƙar mamakin al'ummar Annabi, Ni a zatona a iya hasashena, idan mace dan Allah da Manzonsa da darajar iyayen na kai ƙololuwar makurar roƙonda duk musulmi zai yi min al'farmar abinda na roƙa! Sai dai abin tsoro ashe abin ba haka bane, to wannan abun shine kadai ya bani tsoro, lallai kam tabbas muna akiruzzaman. Ai na sani kuma kuma mutanen kirki waɗanda kuka sai littafina da zuciya ɗaya kun sani dole za'a fitar da littafi. Sabida ba kaina farauba kuma ba kaina ƙarauba. Sabida haka kuyi haƙuri, dan Allah kuyi haƙuri, kuyi haƙuri da abinda wasu daga cikinku keyi. Alhamdulillah tunda na'annabi basa ƙare wa, tunda har gobe saya akeyi, wasu suna ganin gana satan a gabansu, amman sai su kauda ido suzo gareni su biya kuɗinsu a sasu a group ina godiya gareku* Bayan Allah da Manzonsa da darajar iyayen dana haɗa mutane dasu bani da wani tsumi ko dabarar tsira daga sharrin masu zuciyar da basu san girman Allah da Manzonsa da darajar iyayensu ba. Domin duniya gaba ɗaya tana fama da gubar irin waɗannan. Iya tsaro dai kamar na bankuna, to amman me ana samun masuyin kutse a ciki har suyi sata. Manyan kampanunnuka na duniya ma suna fuskantar ɓarayj yan kutse, hakama ƴan Film suke fama da wannan matsalar, to mu ma rubuta suwaye mu da zamu tsira dasu, Roƙona anan dan Allah da Manzonsa abar maimaita mgnar a cikin groups ɗin GARKUWA. Su masu fitarwa dai na fita haƙƙinsu tunda inai musu posting sau biyu a rana kamar yadda na faɗa, su sukaji suka gani suka fitar, to wannan can musu. Ina da mutanen da nake matuƙar ganin kimarsu da darajar su a SPG shiyasa, bazan tanka musuba. *Fatan al'khairi VIP groups ƴan dari uku ina al'fahari daku, kun bawa maras ɗa kunya, shiyasa tun forko nace Ni kune VIP na, duk da nasan kuma ɗin a cikinku tabbas akwai masu fiddawar, to amman dai naku baya zama illa kamar na SPG. Ina yinku ɗari bisa ɗari.* Wlh rubutu yafi sauƙi akan mu'amalat da wasu taƙadiran da yake jarabtan marubuta da mgna dasu, ya ilahi ya mujibadda'awati, kai ina jinjina muku marubuta fama da wasu mutanen, wato da a haɗaka mgn da wasu gwara kawai a baka renon shanu garke guda na wuni ɗaya, domin shi dabba yasan abinda ake kira da makiyayinsa, amman wasu mutanen basu san darajar Allah da Manzonsa ba bare iyayensu. Allah ya kyau. Allah ka haɗamu da mutanen kirki. *Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan layin 09097853276, ko ki turo dubu ɗaya ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276.* *Zan ƙara roƙo ba domin irinku kangararruba a a sai dan masoyan Allah da Manzonsa, dan Allah kada ku fitarmin da littafina. In kin san kin sayane dan ki fitar min da littafina to dan Allah da Manzonsa kizo kimin mgn ta pc kice kawai GARKUWA bani kuɗina bazan iya saya ban fitarba, wlh Salim alim zan meda miki kuɗinki in biki da godiya, in kuma baki sayaba zaki saya dan ki fiddane dan Allah kada ki saya. Dan Allah in kin rigada kin saya kuma Please turo ac no ɗinki kawai kadama kiyi mgnar kamai a take zan meda miki kuɗinki in cireki in miki godiya🙏🏻* Lamiɗo da Galadima da Sarkin Shaɗi. Bisa alamu wata mgna mai mahimmanci suke tattaunawa. Murmushi Lamiɗo yayi tare da kallon Umaymah cikin kulawa yace. "Khadijah lale da zuwa Masarautar Joɗa." Da sauri Umaymah ta ƙarasa gabansu, cikin ladab ta zauna gabanshi tare da duƙar da kai tace. "Allah rene Barka da dare". Kanshi ya jinjina irin na sarakuna kana yace. "Barka dai Khadijah kinzo lfy, ya Sarki Aliyu?". kakan Haroon kenan wanda ya haifi baban shi. Cikin girmamawa tace. "Yana lfy yace yana gaidaka". Kanshi ya jinjina, kana ya ɗan kalli Jabeer dake danne-danne a wayarshi. Ya hakimce ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya. Jakadiyarsu kuwa tayi shiru a gefe kusa dashi. Galadima da Sarkin Shaɗi kuwa, murmushi sukeyi suna kallon Jabeer. Gyaran murya Lamiɗo yayi kana cikin dattaku yaci gaba da cewa. "Ina amsawa, ya kika samu jikin ɗan naki?". Cikin murmushi ta juyo ta kalli Jabeer kai ta rusunar ganin samfa hankalinshi baya kansu cikin yin ƙasa da murya tace. "Alhamdulillah na samu jiki ya worke!". Galadima ne wanda yake ƙanine ga baban Lamiɗo ya amshi zan da cewa. "To sai ki sanar mishi batun komawa Rugar Bani, dan ramuwa bisa cika ƙaidar..". Shiru yayi bai ƙarisaba jin muryar Jabeer yana cewa. "Ƙa'idar Allah da Manzonsa ne da zai zama dole sai an cika, ba ƙa'idar wani zalumci da tozarcinba". Kanshi ya ɗan tanƙwara a wuyanshi. Kana ya zamo kaɗan ya zauna gaban Umaymah cikin nuna rauninshi yace. "Ayyah Umaymah kada kice min inje, Please Umaymah ki fahimci wannan abunfa al'adace ba addini ba, kuma abune da kai tsaye zamu iya ce mishi makaruhi in ma bamu haramtashi ba, ya za'ayi inje in sake tuɓe kayan jikina a gaban duniya wai dan in daki wani. Ni bana so. Ba dai sune suka kainiba, suka kuma ce a dakeni, to dan me zasu buwayeni da sai munje na rama". Haɗe fuska Umaymah tayi cikin kafeshi da ido tace. "Ni bana iya yiwa iyayena musu. Jabeer tabbas na sani al'adace ba addiniba, amman ka sani duk wani abun da zakaga ya faru a duniya to akwai dalilin faruwarshi, kada kace zaka tsananta bincike tabbas lokacin zai baiya mana dalilin. Bana son gardama kawai kaje Dan ALLAH". Hannunshi yasa ya dafe kanshi, kana yayi shiru Umaymah ta gama dashi da tace dan Allah, ya sani tabbas da a madadinsa Ayyah ɗin da yace forkon mgnar da ya mata da ya rigata cewa Dan Allah da shike nan yasan zatayi shiru. Shi kuwa Lamiɗo murmushi yayi tare da kallon Umaymah cikin jin daɗi yace. "Allah ya miki al'barka". Da sauri tace. "Amin ya Allah". Galadima kuwa, murmushi yayi tare da jinjina kai. Jakadiyarsu ma cikin jin daɗin tasirin mgnar Umaymah akan Jabeer take murmushi sabida ta sani. Shi mutunne mai kaifi ɗaya, in yace eh tofa eh ɗince inko yace a a to a'ance. Especially baya son duk wani abu da zaici karo da addininshi. Kanshi ya jinjina Umaymah alamar shikenan idonshi yayi jazir alamun dole akasashi yin abinda baya so. Kana ya kalli kakarsa dake murmushi tsuke fuskarsa yayi tare da cewa. "Gimbiya Aminatu muje ki bani gashin da kikayiwa Lamiɗo". Cikin dariya Gimbiya Aminatu tace. "Iye gashinsama zan baka?". Da ƙarfi yace. "Eh shi zaki bani, ai in dukane kam ya iya zille kanshi ya turani. Shine dan gashinsa zakice iye". Murmushi tayi tare da bin bayanshi, ganin Lamiɗo na mata alamun taje ta bashin. Nan sukaci gaba da hira, suna tattauna wasu mahimman al'amuran da sirrine garesu iya su biyar. Wato Lamiɗo, Galadima, Sarkin Shaɗi, Umaymah, Jakadiyarsu. Bayan su babu wanda suke yarda da sanin sirrin Jabeer. A hakanma kuma a suɗinma akwai wani sirrin da babu wanda ya sanshi sai Lamiɗo da Umaymah. Suna zuwa har falonta suka wuce. Wani kekyawan akoshi mai masifar kyau ta ɗauko mishi. Ta ajiye a gabanshi. Inda yake zaune a ƙasa bisa carpet ya naɗe sawunshi. fork ɗin dake saman fefeyin ya ɗauka. Daddageggen gaseshen jan namane wanda yaji wuta ya gasu gashin tukunyar ƙasa yayi tiɓis. Sai wani irin ƙamshi na musamman yakeyi, A hankali yake sa Fork ɗin yana yagan tattausan tsokokin yana sawa a baki. Ita kuma tana zaune gefenshi. Tafashesshen madaran shanu mai ɗan ɗumi ta miƙa mishi a wata ƴar ƙwarya mai kyau. Taune naman yayi tare da haɗiyewa kana cikin zuba mata ido yace. "Dole sai na karɓa da hannun nane? Ki ajiye mana. Da wanne hannun zan amsa tunda inacin abinci dana daman". Murmushi tayi tare da cewa. "Dole sai ka amsa, bazan baka shi a ƙasa". Kanshi ya ɗan rausayar tare da cewa. "Allah ya nuna min ranar da za'a bar. Wannan tsare-tsaren shamfi na masarautar Joɗa. Komai da ƙaida da yadda ake yinshi". Ita dai miƙa mishi ƙwaryar takeyi dole ya ajiye spoon ɗin yasa hannunshi ya amsa. Nan suma sukaci gaba da hira. Sai kusan sha ɗaya Umaymah da Jakadiyarsu suna fito. A nan Gimbiya Aminatu ta ajiyesu suma saida sukaci gashin nata kafin suka tafi. Kafin su isa Side ɗinsa dai sha biyun dare tayi. Haka yasa suna isa suka samu ba kowa a falon. Sai Haroon da suke jiyo muryar sa, a falon Jabeer. Cikin nitsuwa ya matso kusa da Umaymah a hankali yace. "Sai da safe Umaymah kiyi bacci ki huta." To tace har ta juya zata tafi sukaji Muryar Haroon yana cewa. "Abba yazo wurinki zaku gaisa bai samekiba, nace mishi kun tafi wurin Lamiɗo yace, to saida safe ya gaidaki da hanya Hajia Mama ma yanzu ta fita, tace Lamiɗo ya riƙe mata ƙanwa". Murmushi tayi tare da cewa. "To Allah ya bamu al'khairi saida safen". Amin Amin suka ce. Kana shida Haroon suka wuce Side ɗinsa. It's kuma Umaymah da Jakadiyarsu suka wuce. Side ɗin da kullum in dai Umaymah tazo nan take sauƙa. Suna shiga suka samu, tuni Hibba tayi bacci, wannane ya basu damar tattauna wasu mahimman sirrukansu. Nisawa Umaymah tayi bayan ta saurari jawaban Jakadiyarsu Jabeer cikin tsantsar tafasar zuciya da tarin baƙin ciki tace. "Uhummm suyi dai Ni nan ina dai-dai- da ƙugun ko wanne shege da shegiya, In sha Allahu zasusha mamaki. Zasuga yadda Ubangiji ke ikonsa, ban cire raina ƴar uwarta zata sake rayuwar enci da salama, da izinin Ubangiji zataga sakayar waɗanda suka cutar da ita da yaranta a gaban idonta. Cikin zubda hawaye Jakidaya tace. "In sha Allah, sai farin ciki ya dawo, a sashinta, inata addu'a a kullum a cikin dukkan sallolina, Allah ya kare ahlinta, ya kuma baiya gsky tayi halinta kowa ya gani". Amin Amin Umaymah tace tare da share hawayenta. Washe gari ranar Alhamis. Ta kama yau kwana shida da faruwar gasar Shaɗi, kana gobene za'a koma dan ramuwa, A goben kuma zai cika kwana goma da kisan gilla da kafurai ƙabulun Ɓachama sukawa Fulanin Rugar Bani. Misalin ƙarfe sha biyu na safe. Fadar Sarkin Nuruddeen Bubayero Joɗa, cike take maƙil da tawagarsa kama daga. Galadima, Waziri, Wambai, Dan buram, Dan iya, Ɗan isa, Ɗan Kade, Sarkin fada, Sarkin yaƙi, Sarkin Dowaki, Sarkin Gabas, Sarkin Kudu, magayaƙi, Jarma uban doma, Makawa Ɗurɓi, Turaki, Da dai sauran members ɗin masarautar baki ɗayansu, an cika anyi maƙil. Sallama na tsaye can bakin ƙofar shigowa. Dogari kuma suna tsaye gefen hagu da daman Lamiɗo. Suna rike da mafici sunayi mushi fifita, ɗanzagi kuma yana gefe, Kana wasu fadawan duk suna gefen. Gyaran murya Lamiɗo yayi tare da gyara zaman shi cikin shugarsa ta sarakuna masu al'farma, a hankali yace. "To da farko dai fatan duk kowa na lfy". Da sauri Ɗanzagi yace. "Sarki ya gaisu yana yi muku fatan alkhaiy". Sai ya kuma juyo ya kalli Lamiɗo tare da cewa. "Godiya suke." Kanshi ya ɗan jingina da tattausar kujerarsa da masu son gadonta sunfi a ƙirga, cikin ƙasaita yace. "Kamar dai yadda muka tattauna, kwanakin baya akan sarkin Garin Shikan, to yanzu zan zantar da hukunci. Sarkin aike na bada umarni kaje garin Shikan ka karɓo min sandar sarautar Shikan ka kawo min shi, yau ɗin nan. Kaje da jagorancin Galadima, da Matawalle da Makawa, sai sarkin yaƙi". Da sauri duk suka runsunar da kayu kansu tare da cewa. "An gama". Nan take kuwa suka miƙa suka tafi. A cikin gida kuwa. Tunda asuba da Jabeer da tawagar ahlinshin suka dawo masallaci. Kai tsaye ɗakin Umaymah ya nufa, suna biye dashi a baya. Bisa sallaya suka sameta riƙe da al'ƙurani mai girma tana karatu cikin tsananin nitsuwa. Ganin hakane duk suka fito falo. Nan Aunty Juwairiyya taja Ummi suka tafi side ɗin ta da Hibba da ƴar aikinta suka shiga kitchen. Jalal kuwa shine yaje wurin Ya Jafar, don bashi mgni kamar yadda Jabeer ya umarceshi. Jamil kuwa waya yakeyi da sabuwar budurwarsa da ya samu. Wacce yake masifar sonta, Ko yaushe suna liƙe da juna a waya. Haroon kuwa a falon Jabeer ya zauna yana kallon lbrin CNN. Shi kuwa Sheykh Jabeer. A hankali ya wuce ta gaban Haroon. Gefen gabas ya fuskanta, inda labulaye sukayiwa wurin ƙawanya. A hankali yasa hannunshin ya yaye labulen. Wani ƙofa ya buɗe a . Sai ga wani ɗan siririn corridor. Shiga yayi, kana ya saki ƙofar ta koma ta mannu da ƙofar sai dai bata rufuba. A hankali yake taku cikin nitsuwa, Lips ɗin shi na ɗan motsawa alamun tasbihi yakeyi. Tafiya mai ɗan tsawo yayi sai gashi ya kuma riski wata ƙofar. Hannunshi yasa ya murɗa key ɗin ya buɗe, ƙofar. Sai ga kuma wata ƙofa irin ta ƙarafuna kana dai iya hango woje. Buɗe wannan ƙofarma yayi. A hankali ya kutsa kai. Wani irin sassanyan ajiyan zuciya mai tsawo yaja ya sauƙe a hankali. Idonshi ya lumshe sabida wani irin sanyi mai masifar daɗi daya ratsa mishi jiki da zuciya. Wani irin ɗan madaidaicin Garden Park ne mai masifar kyau.da sanyi da tsaruwa. Daga nan bakin ƙofar daya fito ɗin. Tayis ne fari tas a malale iya ganinka, sai gefen damanshi da bishiyoyin ayaba masu masifar duhu da sanyi dake jere reras. Gefen hagunshi kuma bishiyoyi mangoro ne irin yan duƙus-duƙus ɗin nan ke jere, Reras. A hankali yake taku yana tafe yana tasbihi. Yana jin kukan tsuntsaye mai daɗin ji yana ratsashi. Tafiya kaɗan yayi sai gashi ya baiyana a wani irin wurin mai masifar kyau. Wasu yan zagayen gini dakalin bulok bibbiyu akayi a ƙalla sunfi hamsin. A ciki ko wanne zagayen akwai bishiyar dabino. Na gabanta inabi na gaban inabi tuppa, kana sai Yazawa, sai kuma na tsada, daga tsada sai na kanya, sai goruba da na giginya. Cikin ko wanne zageyen kuma ƙasanshi koriyar ciyawa ce mai sanyi. Can tsakiyar filin kuma wata iriyar ƙoramace mai masifar sanyi, Ruwanshi na kwance fari ƙal-ƙal bakin wurin kuma jeren bishiyoyi goibane wanda sukayiwa kwaramar inuwa. Gaban ƙoramar kuma wasu irin kujerun silver ne masu masifar kyau da sansi a jere a ƙalla sun kai goma zuwa ashirin. Can gefenshi kaɗan kuma wani shingene aka zagaye da waya. Shuke-shuken gargajiya akeyi a wurin. Nan kusa da ƙoramar kuma shingen farar waya akayi a cikin ta wanda akayi ƴan ɗakuna-ɗakuna a cikin. Tsuntsaye ne a ciki iya ganinka ko wanne da muhalli shin. Kama daga Tattabaru farare ƙal-ƙal. Sai kuma tsuntsu carki jajaye masu kyan launi ga kuma kanari da suke blue. Sai kuma zabbi da suke yawo a ƙasa tako ina. Can bakin ruwan kuma agwagin ruwa ne sunfi ɗari ƙwa-ƙwa. Sai kuma zabbin daji. dangin tsuntsaye dai babu irin wanda babu. Ido ya zubawa tsuntsaye tamkar mai son yin magana dasu. A hankali ya sunkuyar da kanshi jin tattausan gashin Ɗawisun Masarautar Joɗa da ya kai shekaru masu tarin yawa. A hankali ya rusuna tare dasa tafin hannunshi ya shafa dai-dai ƙunɗun Ɗawisun inda wurin yake mai kalar blue mai kyau sabida Sheykh blue ne kalar da yafi so. A hankali ta fara taku, ta juya mishi baya kana ta ɗaga bindinta sama samɓal har yana iya taɓo geminshi. Wani irin takun ƙasaita tayi kana ta buɗa fikafikinta ta bazasu, ta fara tafiya a hankali. Wannan itace suntsuwar da muddin mutun ba jinin Masarautar Joɗa bace, in ka shigo mata gaba gaɗi ba tare da an gabatar mata kai ba, zatayi ta yagune mutun tana caccakarshi. Amman muddin dai kai jinin Masarautar Joɗa ne, kana shiga zata zo gabanka. Tayi maka hakan. Sai dai kuma bayan yin hakan in mutun nada wata zazzafar nasaba a masarautar misali shine sarki maici to in tayi wannan baza fikafikinta takanyi ta zagaya sarki sau bakwai kafin ta tsaya a gabanshi sai sarkin ya umarceta data tafi kafin zata tafi. To babban abinda ya ƙara jazawa Jabeer matsala a rayuwarsa shine, Duk sanda yazo gaban tsuntsuwar Ɗawisun nan sai tayi mishi wannan abin da zagaya sau bakwai abinda a tarihin masarautar sarki kawai yakeyiwa abin. Matsalar abin a gaban Barrister Kamal da kuma Baba Bashiru da Abba sai Lamiɗo ne ta fara yimishi wannan abun. Tofa ta bakin Baba Basiru ne mgnar ta zaga kunnen mazauna masarautar Joɗa. Babban tashin hankalin masu son gadar wannan kujerar, shine yadda side ɗin Jabeer ke kusanci da Garden ɗin da take ciki. Tashin hankalinsu ya ƙara tsananta ne tun randa Suka ga Lamiɗo yasa an buɗawa Jabeer hanyar shiga wurin ta cikin falonshi ba sai ya zagaya yabi hanyar da kowa ke bi ba, Ya zama shida Lamiɗo sune masu hanya kowa daga falonshi zai shiga wurin. A hankali Jabeer yayi murmushi tare da kallon yadda tsuntsuwar ta gama zagayashi kana tazo ta tsaya gabanshi tare da baza fikafikinta. Cikin harcen Larabci yace mata. "Fatana dai ba bauta min kikeyi ba! Domin babu wani abin bautawa da gsky sai Allah, wanda shine ya halicce ni ya halicceki. Ni kuma ba kowa bane face halittarsa, sai dai na kasance cikin halittarsa mai girma da karrama fiye da komai, dan shi da kanshi yace. Walaƙad karramna bani Adam." Wani irin juya kai tsuntsuwar tayi kana ta meda fiffigefa ta rufe, kafin ta juya ta nufi wani kekyawan wurin da aka ware mata, inda take tare da yayanta da mijinta. Juyawa yayi can gefe ya hango wasu yan kyawawan tsuntsaye farare A bakin ruwan. Ga tattabarun sun zagaye wurin da sauran tsuntsayen. A hankali ya zauna a wata kujera mai kamar gado. Kishinƙiɗa yayi kana ya lumshe idonshi yana maijin yadda sassanyan iskar wurin ke ratsashi. Karatun al'ƙur'ani ya fara cikin sassanyan murya mai daɗin sauraro. Umaymah kuwa tunda ta fito, sai ta nufi sashin Hajia Mama, hira sukayi sosai cikin shaƙuwa irin ta yan uwa. Suna zaune a nan Abba ya shigo. Tana ganinshi tai murmushi, shima murmushin yayi tare da cewa. "Maman yara". Cikin sakin fuska tace. "Na'am Yaya". Murmushi mai cike da zafi da ƙuna wanda ya baiyana har kan fuskarshi yayi kana ya zauna gefenta. Gaisawa sukayi cikin danne ababen dake cin ransu. Hajia Mama kuwa, tuni sai hawaye take zubdawa. A hankali Umaymah ta miƙa mata handkin dake hannunta alamun ta share hawayenta. Bayan ta share hawayenta ne, Abba ya miƙa tare da cewa. "Kin gaisa da Mom Imran kuwa? Da Salma". Fuska a ɗan haɗe tace. "A a". Miƙewa yayi tare da cewa. "To muje ku gaisa." Binshi tayi a baya suka nufi inda yace ɗin. A falo suka samu Mom Imaran tana ganin. Sun shigo tare da Hajia Mama tayi wani irin haɗe fuska, cikin nuna ko in kula tacewa Umaymah. "Yaushe kikazo?". A daƙile tace. "Jiya". Kanta ta ɗan kauda tare da cewa. "Ya hanya". Alhamdulillah tace a taƙaice. Cikin kufula Hajia Mama tace. "Mu tafi". Miƙewa Umaymah tayi kana Abba ma ya miƙa sashin Amaryarshi Salma ya nufa da ita. Suna shiga tana jin muryarshi ta fito, da sauri ta nufe shi da nufin zata ruggumeshi da sauri yace. "Ga Umaymah tazo". A take taja birki ta tsaya cikin gyatsine tace. "Ya kike kinzo lfy, ki gaida mutan gida". Cikin wani irin kallo Umaymah tace. "Uhummmm kema ki gaida mutan gidanku". Tana faɗin haka ta juya ta tafi abinta. Hajia Mama na biye da ita. Ita kuwa Salma tana ganin fitansu ta ruggume mijinta. Koda suka koma Side ɗin Hajia Mama bata daɗe a nanba ta nufi sashin Gimbiya Aminatu. To bata fito nan ɗinba sai shabiyu saura. Koda ta dawo Haroon da Jakadiyarsu da Aunty Juwairiyya kawai ta samu a falon. Sai kuma Jalal da Hibba da suke dinning area suna zaune bisa kujerun Dinning table ɗin. Sun sa plet a tsakiyarsu da kofunan tea a hannunsu, alamun sai yanzu sukeyin breakfast. Cikin kula Aunty Juwairiyya tacewa Ƙanwar mahaifinta ɗin. "Umaymah muje kuci abinci rana tayi fa". Murmushi tayi tare da son danne ɓacin ranta tace. "Alhamdulillah Juwairiyya Ni kuma da nakeda Hajia Mama ga Gimbiya Aminatu, ai naci nayi nak." Cikin sauri Jakadiyarsu ta e. "Ga kuma Matar Barrister Kamal ma ta aiko miki abin kari. Gimbiya Saudatu ma ta aiko miki". Murmushi tayi tare da cewa. "A ajiye minshi sai anjima, kinga Juwairiyya kada ki shiga kitchen yau kizo mu wuni hira abinmu, abinci tako ina zaizo". Cikin sanyi Juwairiyya tace. "Uhummm Umaymah ke har zaki iya cin abinci waɗanan mutane ai Gimbiya Saudatu ba abin wuya bane tasa mana guba muci duk mu mutu. Sai dai muci na gidan Barrister". Kai Jakadiyarsu ta jinjina alamun eh. Cikin ɗan ɗaga murya Umaymah tace. "Haroon!." Da sauri ya amsa tare da tahowa inda take. Gefenta ya zauna tare da cewa. "Umaymah gani". Ba tare da ta kalleshiba tace. "Ina Jazlaan?". Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Y shiga Garden". Kai ta ɗan jinjina mishi tare da zubawa Jalal ido. Ita Hibba sai murmushi takeyi shi kuma fuskarshi kamar boss. A hankali ta miƙa ta nufi falon Jabeer ɗin. Da sauri ta kalli Haroon tare da cewa. "Ina zakaje". Baki ya ɗan tura tare da cewa. "Umaymah inda zakije mana". Cikin tsokana tace "Sirri zanyi da ɗan". Tana faɗin haka ta juya ta nufi can. Shima Haroon yana biye da ita a baya. A hankali take taku har ta isa inda yake. Gefenshi ta zauna tare da zuba mishi ido. Cikin kula tace. "Jazlaan". Cikim nitsuwa ya buɗe idonshi tare da kallon inda tarin tsuntsayen nan suke, Lokaci ɗaya idanunshi suka kaɗa sukayi jazir. lips ɗinshi ya fara motsawa da nufin yin mgna amman ya gagara, sai wani irin kuka mai ƙarfi da yake son ƙawance mishi daga can ƙasan zuciyarsa. Hakan yasa lips ɗinshi karkarwa tamkar mai jin sanyi. Umaymah kuwa. Tuni hawaye sun wonke mata fuskarta tana mai kallon tsuntsayen. Ganin Haroon yasa tayi mishi alamun ya kawo mata ruwa. Ba musu ya juya ba tare da yayi mgn ba jim kaɗan ya dawo da goran ruwa da glass cup. Ruwan ya tsiyaya a kofin ya miƙa Umaymah. Cikin sanyin murya tace. "Ga ruwan sanyi kasha, nasan zakaji sanyin ƙunan da kakeji a ranka". Ta ƙare shi mgnar tana miƙa mishi cup ɗin. Amsa yayi yayinda gaba ɗaya jikinshi karkarwa yakeyi alamun tsananin tarin baƙin ciki duniya. Da kyar ya iya shan rabin kofin. Nan ta gyara zamanta tare da kamo hannunshi ta fara tausar zuciyarshi kan abinda tasan shine babban matsalarshi. A garin Bani kuwa zuwa yanzu hankali ƙabilar ɓachama yayi matsifar tashi, tsoro mai tsanani ya rufesu. Tsoron da yasa da yawansu suka rinƙa guduwa suna koma cikin babban birnin Ɓadamaya, Wasu kuma su tafi wasu jihohin. Sabida sun gama tsinkewa da goron gaiyata da fulani keta raɓawa babu dare babu rana birni da ƙauye duk inda suka san fulani na nan sai da suka aika musu goro Wannan ne yasa mafiya yawan kafuran aran na kare. Inda hakan ya fusata Habban Ɓacama. Har ta kaishi ga cewa, duk ba ɓacamen da yasan tsoron fulanine ya sashi guduwa to kada ya kuskura ya sake dawo mishi garinshi garin Shikan. To wannan abun shiyasa wasu suka fasa guduwa, wasu da basuyi nisaba suka dawo. To kuma kwatsam sai gashi yau an aiko an karɓin sandar sarautar Shikan dake hannunshi Wannan abun yasa da yawa mutanen cikin Shikan Maza da mata hausa fulani da Ɓacamawa da sauran ƙabilu suka kuma rinƙa fecewa sabida, suna ganin yanzu dai shi kanshi Sarki Shikan bashi da madafa bashi da ƙarfi tunda an karɓe sandar sarautar shi. To hakane yasa, ya rinka bin ƙauyuka Especially mutanen Bonon da kewaye ya rinƙa zugasu da ingiza su cewa, nanfa garinsu ne ya zasuyi su gudu kan Fulani. Kuma ma suda sukeda dodon tsafinsu Bonon ai shi kadai ya ishi fulanin. Da haka yasa duk ƙabilun Ɓacamawa na ƙauyukan basu guduba. Sunata shirin faɗa yayinda cikin garin Shikan kuma yayi shal ko ina shiru babu mutane. Cikin garin Bani kuwa, iya tsoronsu da suka gani a cikin kafuran ya sasu jin daɗi tunda gashi har suna guduwa subar garin da suke musu gadara da gori a kanshi da cika bakin sai sun kori Fulani a garuruwansu. To tabbas sunada nasara akan fansar da zasu ɗauka, zasu ramane dan nemawa kansu enci. Sun san iya sau ɗaya in sun nunawa arnatakun nan zasu iya gwabzawa dasu zasu barsu su sarara. Haka yasa suke jin ƙarfin guiwar yin abun. Ba'ana kuwa yanata ƙara shirya kanshi, sabida ramuwar gasar da za'ayi. Ya Salmanu kuwa yanzu ya fara jajir cewa, yana fakewa da jarumtar Jabeer yana gasawa Ba'ana maganganu. Sosai ya ƙara shigewa Shatu a mako ɗayan nan. Kuma tana jin daɗin hakan. Ta sake sosai. Zuwa yanzu kuma jikin Ummey yayi sauƙi garawau sai dai har yau bata taɓa yin mgna ba ta zama tamkar kurma. Da dare bayan sallan isha'i, tana zsune ita da ya Salmanu suna hira cikin nitsuwa tace. "Ya Salmanu gobene zamuje asibiti mu dubo su Junaidu da sauran marasa lfy dake cikin Genaral Hospital Ɓadawaya, dan naji ƙishin-kishin ɗin wai har yanzu babu likitan daya dubasu." Cikin gamsuwa da hakan yace. "Eh hakan yana da kyau, kuje in sha Allah muma jibi asabar zamuyi gamgami muje, danma goben jumma'a ne da munje tare". Sai kuma ya ɗan kalleta tare da cewa. "Da yaushe zakuje?". Cikin sanyi tace. "Da safe zamuje, in anyi sallan azahar zan dawo, amman Rafi'a zata wuce makaranta". yace. "To ke sai yaushe zaki koma?". "Sai Ummey ta ɗan ƙara samun sauƙi. Ni da na so mu kaita asibiti kan batun rashin mgnar tata. Gyara zaman shi yayi tare da cewa. "Wannan ba matsala bace, wlh firgici da tsoro ne yasata hakan". Haka dai sukaci gaba da hirarsu. Washe gari ranar jumma'a, misalin karfe sha biyu dai-dai suka fito zasu tafi asibitin. A bakin lambun garinsu sukayi kiciɓis da Ba'ana nan ya tsaidata dole suka zauna. A can cikin masarautar Joɗa kuwa, Lamiɗo, Galadima, Sarkin Shaɗi, da Jabeer ne tafe a hankali suka shiga cikin Garden ɗin nan. Ta gefen Lamiɗo, suna shiga suka nufi inda katon curin dake wurin shekara da shekaru. Shi dai Jabeer binsu yakeyi baiyi magana ba, Koda suka isa wurin zama sukayi dabas a ƙasa. Dole shima ya zauna, cikin sanyi Lamiɗo yace. "Assalamu alaikum Jaimi". Da mamaki Jabeer ya kalleshi, Hiraminshi ya gyara tare da cewa. "To yau kuma". Da sauri Galadima yasa hannunshi ya rufe mishi bakinshi. Hannunshi yasa ya janye hannun Galadima tare da cewa. "Yo ai ba sai ka rufe min bakiba, in kace nayi shiruma zanyi, sai dai ina naga abin saɓon Allah ko tsireni za'ayi sai na faɗa". Dafe kai Galadima yayi tare da tsuke fuskarsa. Ganin haka ya taɓe baki tare da ɗaga kafaɗunshi ya ɗan buɗasu alamar, ban damuba. Sarkin Shaɗi kuwa bai kallesu bama. Wani irin zabura Jabeer yayi cikin tsananin firgici da kaɗuwa lokacin da yaga wani irin h ....! By *GARKUWAR FULANI*Ganin wani irin hayaƙi fari tas yana fitowa, tako wacce ƙofa na jikin curin. Da sauri Galadima yasa hannunshi ya kamo hannun Jabeer yaja da ƙarfi. Alamun ya nitsu ya zauna, cikin mamaki ya zubawa tarin hayaƙin dake bulbulowa daga ƙofofin ramin shirgegen curin. Su kuwa ga ɗayansu hankali konce suke zaune. Ido ya zuba musu tare da cewa. "Me hakan?". Da sauri Lamiɗo ya girgiza mishi kai hakanne ya sashi jan gajeren tsaki tare da cewa. "Nifa ba son wannan soki burusun naku da surkunlenku nakeyi ba. Me gamina da ku da tsare-tsaren naku. Fisabilillahi me wannan?". Cikin faɗa Lamiɗo ya sa hannu zai bugi bakinshi da sauri ya kauce. Cikin hatsala Lamiɗo yace. "Wannan bakin naka da baya mutuwa, komai sai kayi inkarin a kai tabbas sai na kashe bakin nan". Wani kallo yayi mishi tare da cewa. "Uhumm ai babu mai kashe bakin Muhammad Jabeer sai Allah". Ganin zaija suma suyi surutune ya sasu kauda idonsu kanshi. Bayan kusan mitinu goma, sai ga hayaƙin nan ya bar fitowa, Sai wani irin huci. Da sauri Jabeer yace. "Nifa zan tafi, inma kun mance in tuna muku yau jumma'a ace, inada abinda yafi wannan abun naku mahimmanci a rayuwata ta duniya da ƙiyama, yanzu gashi har kusan sha biyu." Murmushi sukayi baki ɗayansu ba tare da sunce mishi komaiba. Sabida dama sun san za'ayi haka kam. Sabida kowa ya sani shi Jabeer yana barranta da duk irin waɗannan ababen gado na sarauta shiyasa sarautar kanta shi bata ɗaɗashi da ƙasa ba. Da sauri ya buɗe siraran idanunshi da kyau. Sabida ganin wani irin ƙaton maciji ya sako kanshi cikin babban ramin da yafi girma. Da sauri yace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun!." Sai kuma ya zubawa maciyar nan idanu. Tana fitowa cikin ramin ta, zuɗuɗuɗuɗuɗu. Haka yake zaro jikinshi. Haƙiƙa dole duk wanda bai taɓa ganin macijinba bai kuma san da zamanshi ba, dole ya razana. Dan ma shi zuciyarshi na cike da tsoron Allah so irin wadannan ababen ba kasafai suke firgitashiba. tashinsa fahimtar ko wani ɗan abin sihirin za'ayi mishi ne. Wani dagon numfashi yaja mai ƙarfi ya sauƙe ganin. Yadda macijiyarna taketa keta fitowa taƙi ƙarewa. Su dai su Lamiɗo shiru sukayi a zaune. Saida ta gama fitowane, ya rage iya bindinta sai gashi ta fito bindinta na kananmaɗe da wasu irin kitsastsun bulalin da ka gansu kasan tsoffine. A hankali ya turo bindinshi gaban Lamiɗo, Ya ajiyesu, sai kuma ya sumkuyo da kanshi ya zaro harshensa ya rinƙa lasar bulalin nan saida suka fito ras kamar an wonkesu. Kana ta juya ta nufi cikin curin zuɗuɗuɗuɗuɗu ta koma, Kamar forko sai ga hayaƙin. Wani nannauyan numfashi Jabeer ya sauƙe tare da cewa. "Uhum inda ranka kasha kallo. Oh ni Muhammad Jabeer an ɗauramin jakar tsaba za'a jazamin kaji su bini su tsastsageni. Du wai wadannan abubuwan na menene wai dan Allah". Ya ƙarishe mgnar yana kallonsu baki ɗayansu, fuskarshi cike da alamun fargaban gudun saɓawa ubamgijinshi. Su kuwa saida hayaƙin ya gama ɓacewa baki ɗaya sannan Lamiɗo ya fara miƙewa kana suma duk suka miƙa. Sarkin Shaɗi ruggume da bulalin. Juyawa sukayi zasu nufi hanyar da zata ɓullo ta falon Lamiɗo, da sauri ya ɗan motsosu tare da cewa. "Dan Allah shi wannan abun me amfanin zamanshi a nan? Wurinda Kum san duk baƙin da suke zuwa tako wani sashi na duniya ganin abin tarihin masarautar Joɗa muna kawosu nan. Yanzu in wata ran yunwa ta koroshi ya fito ya cutar da mutane fa me zakuce?". Cikin ƙosawa da mgnar Galadima ya gyara riƙon da yayiwa sandarsa cikin sanyi yace. "Bata tare da yunwa, macijiyar da duk wata sai an ajiye mata motar ƙwai a cikashi da kiret-kiret na ƙwai shine abincinsa". Da sauri Galadima ya nufi hanyar fita. Lamiɗo kuwa tuni sun tafi. Ganin sun tafi sun barshi a nan a tsayene. Yasashi sauƙe numfashin tare da juyawa ya nufi, ƙofar da zata sadashi da falonshi. A hankali yake taku, cikin kasala da mutuwar jiki, da mgnar zuci. "Wai ya zanyine? Wanna wacce irinyar masifeffiyar rayuwace? Yaushe zamu samu Allah ya gama tsarkake mana wannan masarautar Joɗa ya rabata da wadannan tsarabe-tsaraben gargaji. Wannan wacce iriyar fitinace?". Dogon numfashi yaja lokacin da ya shigo falonshi, babu kowa, can babban falo ma babu kowa bisa dukkan alamu duk sunje shirin sallan jumma'a ne. A hankali ya kutsa kai cikin bedroom ɗin shi. Kai tsaye bathroom ya wuce. Jallabiyar jikinshi da hirami da vest ɗin ya cire, Cillasu yayi cikin injin wonki. A hankali yake taku kanshi a sunkuye dagashi sai boxes Sky blue. A hankali ya shiga cikin wurin wonkan. Kamar yadda ya saba haka yayi wonkan jumma'a anshi. Bayan ya fitone ya nufi drower'n glass ɗin dake cikin bathroom ɗin. Wani tattausan Baby towel ya ɗauka bisa saman kafaɗunshi ya ɗauri ya fara gogewa, yana tsane ruwan jikinshi. Kana a hankali ya ɗauki wanni babban towel ɗin ya ɗaura daga saman ƙirjinshi. Wanda ya sauƙo har guiwa shi, a hankali yasa hannun ta ciki ya fara murza boxes ɗin yayi ƙasa, dashi yana zuwa sharabanshi ya riƙe shi ya zare ƙafa ɗaya, kana ya zare ɗayar ma. Lallaɓeshi yayi ya matse kana ya shanyashi kan ƙarfin silver da yake na shanya. Farar jallabiya ya zura a jikinshi, kana ya kwance towel ɗin. Dashi ya goge suman kanshi. Cikin hamzari ya fito bedroom, Kai tsaye gaban dreesing mirror ya nufa, mai ya shafa a dukkan sashin jikinshi. Kana ya taje tattausan suman kanshi tare da shafa mishi manshi, wani Duaol jannah mai masifar daɗi ya shafawa jikinsa, kana ya ɗauki wani ƙaramin kum ya tace tattausan sajenshi ya kontar dashi lib-lib hakama gemunshi. Saida ya gama komai na gaban Mirror kana ya nufi babban drower'nshi da sauri-sauri yakeyin komai. Wani tattausan jallabiya mai masifar kyau da taushi fari ƙal ya zaro. Kana ya ɗan yi sama da kanshi ya kalli cikin tsep ɗin ƙarshe na drower'n inda al'kyabbanshi suke jere a kimtse tamkar shagon saidasu. Hannu yasa ya zaro wata sabuwa dal tana cikin ledanta tana haɗe da hiramin ta da komai. Rufe wannan wurin yayi kana, ya buɗe wani sashin inda ƙananan kayan shi ke jere, boxes and singlet ya zaro farara ƙal suma sabbi ne. Da sauri ya rufe drower'n kana yazo ya ajiyesu bakin gadonshi. Ba tare da ya cire jallabiyar jikinshi ba, ya saka boxes ɗinshi saida ya dai-dai-ta zamanta a jikinshi da kyau ya kimtsa komai nashi yadda zaiji daɗi tafiya, kana ya zare jallabiyar ya ajiyeta bakin gadon Singlet ɗin ya yasa, sannan ya ɗauki farar tattausar jallabiya mai dogon hannun ya saka, jallabiyar daya cire ya ɗauka ya gaban ƙaton drower'n nashi ya nufa, wani side ɗin ya buɗe nan ya saƙalata. Kana ya dawo bakin gadon. Ledan al'kyabbar ya farka da ƙarfi da kuma sauri sabida ganin tuni ƙarfe ɗaya da rabi tayi, yasan yanzu masallacin ya cika maƙil da mutane. Ɗan gajeren tsaki yaja, tare da ci gaba da warware al'kyabbar. Yana gamawa ya zurata a jikinshi, al'kyabbar baƙace, sai gefen bakinta da akayiwa kolliya da wani zare mai masifar kyau Golding color irin mai sheƙi da ɗaukar ido, hakama, kan kafaɗunsa har zuwa hannunta anja zirin irin wannan kolliyar. da sauri ya dai-dai-ta zamanta a jikinshi, kana Ya juya ya nufi, gaban dreesing mirror da hiraminshi a hannunshi, Yana isa ya ajiye baƙin abin, kana ya ware farin hiramin shima da kolliyar Golding color a jikinshi, ya ninkeshi kamar yadda muke ninke dankwali, bayan ya gama ne. Ya ɗaurashi a kanshi ya dai-dai-ta zamanshi kana, ya ɗauki baƙin abin wanda shima an zagayeshi da Golding color ya sakashi a akanshi, ya fito ras tamkar a Saudia. Allah ya sani yana masifar son wannan shigar da jin daɗinta a jikinshi babu takura babu matsi gashi ka suturtu da kyau mayu masu kallon tsiya irinsu Jazrahda Batool duk basa iya ganin komai a jikinshi ba. Da sauri ya nufi wurin aje takalma shi wanda yake na glass ne marfin ya buɗe kana, ya ɗauki wasu takalma irin nasu na sarauta Golding color ne kuma half cover ne, zura jajayen sawunshi yayi a ciki, kana ya koma gaban mirror, wani kolba turaren OudKareem mai masifar ƙamshi mai sanyi, ya fesa a duk sashin jikinsa. Kana yasa hannunshi ya ɗauki carbinshi. Farin galashi ɗan siriri ya manna a idonshi. Kana ya juyo da sauri zai fita, sai kuma ya tsaya cike da mamakin ganin. Haroon tsaye ya zuba mishi ido. Ya buɗi baki zaiyi faɗa sai kuma yayi shiru jin Haroon na cewa. "Kada kace zakayi faɗa Lamiɗo ne yace inzo in kiraka, lokaci na tafiya fa." Bai kulashi ba kawai yayi gaba, da sauri Haroon ya bishi tare da cewa. "Wannan baza ƙamshi haka sai kace wurin amarya zakaje, gsky kayi kyau sosai masha Allah". Bai kula Haroon ba sabida addu'o'in da yakeyi. Amman duk da haka saida ya bawa Haroon amsa a zuciyarshi, yake cewa. "Akwai wani wuri da yafi cancanta da ɗan adam yayi shiga ta tsabta da kyan shiga da ƙamshi sama da masallacin ne? Innal masajida lillafa, duk duniya da babu wurin da Allah ya keɓanta yace dakinshine sai masallatai. Nan zamu gana dashi. Domin idan mu bama ganinshi ai shi yana ganin mu". Murmushi Haroon yayi, dan Jabeer bai san mgnar da yakeyi a zuci ta fito filiba. A haka dai suka shiga Masallaci. Dole yau a gaggauce yayi Kudbar jumma'a dududu 15 minutes yayi yana kudbar kan halaccin mace ta kalli mijin da yakeson aurenta, kamar dai yadda yayi al-ƙawari a wancan satin. Daga nan aka kabbarta sallah. A can Rugar Bani kuwa. A hankali Shatu ta ɗago kanta ta kalli Ba'ana jin tunda suka tsaya baice mata komaiba, ganin yadda ya zuba mata idone yasata, saurin yin ƙasa da kanta, cikin sanyi muryar tace. "Ya Ba'ana zamu tafi rana tanayi fa!". Wani dogon numfashi ya ja ya sauƙe da ƙarfi, kana a hankali ya ƙara matsowa kusa da ita da sauri tayi baya cikin tsoro, hannunshi ya ɗaga mata alamun karta gudu, kai ta jujjuya tare da ƙara matsawa cikin rawan murya tace. "Ba kyau ina tsoro". Kanshi ya jingina da jikin bishiyar gamjin da suke ƙasanta, ido a rufe yace. "Da dai inada niyar cutar dake, da bamu kawo zuwa yau ban cutar dakeba Shatu, kadafa ki mance tun kina ƴar tatsitsiyarki nake sonki kuma nake tare dake, dare da rana, kada ki mance kullum sai kinje gidanmu da dare da asuban fari kin amsowa Ummey mgninta, da har ina son cutar dake da tun wancan lokacin zan cutar dake. To amman bani da niyar cutarki, ina sonki ne sabida Allah, da kuma gsky da zuciya ɗaya, Shatu koda zaki ƙi yarda dani a kan komai dan Allah ki yarda dani cewa ina sonki, na kuma soki a baya zan soki har gaban abadan, wlh babu ƙarya a cikin soyayyarki a zuciyata, Shatu sonki shine babban raunina a duniya. Har yau babu wani abu dake firgitani da bani tsoro sai rasaki. Babu wani abu na duniya daya taɓa sani zubda hawaye sai soyayyarki, dan Allah ki dena zaton dan na matso kusa dake zan cutar dake, ki amince dani in baki abinda idonki zai buɗu da gane sihiri duk ƙanƙantarshi". A hankali take juya mishi kai cikin sanyi tace. "Na sani Ya Ba'ana wlh na yarda da kai akan soyayyata, na sani bazaka cutar daniba, tunda baka cutar dani a bayaba, nasan kana sona, na kuma yarda da son gsky kakemin, to amman ni bana son wadannan abubuwa asirce-asircen sabida haramun ne. A hankali ya zame jikinshi ya zauna kan jijiyan bishiyar. Ganin haka itama tayi sauri ta zauna bisa guiwowinta ta durƙushe a ƙasa. Cikin mamaki tace. "Dan Allah ya Ba'ana meyasa kwanan nan duka sai kayi ta zubda hawaye a gabana, hankalina yana tashi." Kanshi ya ɗan ɗaga ya kalli sama, a hankali yace. "Shatu ina sonki zan kuma soki har iya numfashin na, bazan bari wani abu ya rabani da keba, in kuma akasamu wani ya zama ƙaddarar rabani dake, to shi kuwa tabbas zan rabashi da rayuwarshi, kiyi haƙuri in dai a kanki ne zan iya yin komai, na kuwa san duk duniya babu wanda yasan hanyar da za'abi a kamani ko aci galaba a kaina, sai ke ranki ke ɗaya tak ce kikasan duk wani sirrina ban saniba ko zaki iya min halacci ki sirranta min rayuwata". Da sauri tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa. "Ya Ba'ana ai rayuwa a hannun Allah take, wata ƙilma in rigaka mutuwa, kuma in dai nice in sha Allah bazan baiyana sirrinka dan a cutar da kaiba, ko ba komai kana soma kuma kace dan zaka nemo su ya Gaini ne kayi wannan tsarin gudun kada mugaye su cutar da kai, Ni na sani Ya Ba'ana waɗannan layun bazasu kareka ba, sabida ba hanyar Allah ka biba amman ni zanyi ta maka addu'a". Ido ya zuba mata a zahiri da baɗininta gsky ta faɗi dan yaga hakan cikin ƙwayar idanunta. A hankali ya jawo tandun duma dake rataye a kafaɗunshi, cikin sanyi yace. "Ga ruwa kisha". Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa. "Bana jin ƙishi". Tura mata tandun yayi gabanta tare da cewa. "Eh ba mgnin ƙishi bane, kishi dan kiji sanyi a zuciyarki naga kina kuka". Cikin share hawayenta tace. "Ba kai bane ka sani kukan kana ta barmin amanar sirrikanka bayan kuma shi amana rikeshi nada girma da nauyi da wuya". Murmushi yayi tare da cewa. "Zaiyi wuya ki riƙe kenan?". Da sauri tace. "In sha Allah zan riƙe". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "Bazaki sha bako?". Kanta ta gyaɗa mishi alamar eh. Kana ta miƙa tsaye, gaba ta ɗan yi kusa da Rafi'a, tace. "Rafi'a mu tafi". Murmushi yayi tare da cewa. "Rafi'a ku tsaya". Cikin tsoronshi Rafi'a tace. "To Ya Ba'ana". Da sauri ya ƙara so gabansu, tare da cewa. "Mata ɗago hannunki mu gani kinada zobene?". Kai ta girgiza alamar a a babu. kana ta ɗaga hannunta na dama, Yatsarshi ya karkaɗa mata tare da cewa. "Lalala ɗago hannun hagu mu gani". Cikin gajiya ta ɗago hannunta, fararen tausasan zara-zaran yatsunta suka zubawa ido gaba ɗayansu. Babu zobe ko ɗaya a yatsunta, Murmushi yayi kana yace. "To bari in baki zoben ziyara, koda bakya tare dani, duk lokacin da na nake kusa dake kawai zakiga zoben a yatsunki". Da sauri ta buɗe baki da nufin cewa a a. Kawai sai tayi shiru ganin wani irin zoben azurfa mai masifar ƙyalli da sheƙi sai ɗauke ido yakeyi. Ta juyo zata ce mishi a a Ya cire sai kuma tayi shiru ganin ya ɓace daga gabansu. Yatsunta tasa da nufin cire zoben da sauri ta barshi jin tamkar yatsunta zasu tsinke. Rafi'a kam tuni tayi gaba, haka yasa itama tabi bayanta. Suna zuwa bakin titin suka samu motar zuwa cikin Ɓadamaya. A can cikin masarautar Joɗa kuwa, Bayan an idar da salla, kamar kullum Lamiɗo ya gaggaisa da mutane, talakawan garinshi. Shi kuwa Jabeer dashi da tawagarsa duk sun nufi cikin gida. Sabida Galadima nata ce mishi su tafi cikin gida su fara shirin tafiya. Haka yasa duk suka nufi cikin gidan masarauta. A nan babban farfajiyar suka ɗan tsaya. Ido Jabeer ya ɗan zubawa jerin motocin da a ƙalla sun kai ashirin da biyar zuwa talatin an bisa alamu anyi manyan baƙi ne ko kuma za'ayi fita mai mahimmanci. Cikin suka wuce a falo suka samu Umaymah, Hajia Mama, Aunty Juwairiyya, da Ummi, duk suna zaune suna ɗan hira. Hibba kuwa tana kitchen. Suna isowa ta fito da sauri jin muryarsu. A hankali ta isa gefen Jalal cikin yin ƙasa da murya tace. "Ya Jalal kazo kaci abinci karku tafi bakaci komaiba". Kanshi ya ɗan gyaɗa mata, Jamil ne ya hararesu tare da cewa. "Allah shi ƙara, ai in dai Jalal ne kaɗan kika gani da gwatsalel, mutumin da ba'a iya masa bare a masa gwaninta". Haroon ne ya ɗanyi dariya tare da cewa. "Haka suke shida Jabeer yadda suke kamanninsu iri ɗaya hakama halinsu". Da sauri Jamil ya zare ido tare da ɗan ja da baya yace. "Tab a a Ni dai wlh bance hakaba". Jabeer kanshi Jamil ya bashi dariyar da dole ya ɗan murmusa, tuni sukuma sauran dariya sukeyi. Ya Jafar kuwa shi ganin murmushin Jabeer shine ke sashi murmusawa. Ita kuwa Hibba tura baki tayi ta koma gefe ta zauna alamun tayi fushi, baibi ta kantaba, sai Jamil ɗin ne ya ɗan lallasheta, haka dai sukayi ta yar raha, saida Lamiɗo ya aiko su fito kafin. Suka miƙa duk suka fita, shi kuwa Sheykh Jabeer gefensu Hajia Mama da Umaymah ya ɗan rusuna kusa da Umaymah a hankali yace. "To Umaymah bari inje bisa umarnku ba don raina yaso ba". Murmushi tayi tare da cewa. "Allah ya bada Sa'a ya kaiku lfy ya kuma dawo daku lfy, Allah ya tabbatar mana da al'khairan dake cikin wannan tafiyar, al'farma Annabi da Alqur'ani". Amin Amin suka amsa baki ɗayansu, Hajia Mama dasu Ummi ma duk sukayi mishi addu'a, kafin ya fito. Yauma kamar ranar mota ɗaya suka shiga da Haroon da Lamiɗo da Ya Hashim da Laminu. Kana sauran tawagar sarki. Daga nan suka nufi hanyar fita gari su nufi garin Shikan. A cikin motocinsu kamar na ranan. A tsakiyar garin Ɓadamaya ne suke tafiya sun zo dai-dai bakin Genaral Hospital Ɓadawaya. Lamiɗo ya bada umarnin cewa su shiga cikin asibitin zai kai ziyarar dubiya wa marasa lfya. Nan take kuwa suka jujjuya akalan motocin. Suka fara kutsa kai cikin asibitin. Da ƙarfi Jabeer ya rumtse idanunshi tare da furta. "Lahaulawalaqutailla billah". A hankali sabida wani irin masifeffen bugu da zuciyarshi tayi da ƙarfin masifa. Wani irin taraddadi ya diro masa. Ya ilahi shine abinda ya ambata a saman lips ɗin shi. Dip dab dip dab dip dab dip dab haka zuciyarshi ke harbawa da bugawa a tare a tare, addu'o'in ya fara karantowa a zuciyarshi da harshenshi, yadda suke ƙara kutsawa cikin asibitin haka bugun zuciyarshin ke ƙaruwa. Anan cikin asibitin kuwa, A maraba da baƙi Shatu take tun zuwanta sabida, anan aka juye duk fulanin da suka samu rauni sanadin wannan faɗan, an zubesu a wurin gwamnatin jiha kuma tayi burus da batunsu sam bata bawa likitoci damar dubasuba, Sai ma cewa sukayi sai fulanin sun nemo polices kafin a karɓesu. Su kuma dama ƴan agaji ne ma suka taimaka suka kawosu nan ɗin ma. Zuwan Shatu ne da Rafi'a da ta samesu a yashe hankalinta ya tashi. Ranta yayi matuƙar ɓaci nan ta haura gidan sama inda can jerin jadawalin officer's ɗin DOCTOR'S suke. Rafi'a na biye da ita tana rabka mata kira. "Garkuwa! Garkuwa!! Ke GARKUWA!!! Ina zakije ne wai?". Sam bata kula Rafi'a ba sabida abin da akayiwa ƴan uwanta yayi masifar ci mata rai. Ganin yadda take gudu-gudu da sassarfa ne yasa itama Rafi'a ta fara Binta da gudu-gudu da sassarfa. Yayinda kuma dai-dai lokacin Lamiɗo da tawagarsa ma ke tafe suna shiga cikin gidan saman. Lamiɗo ne a gaba sai Jabeer da Galadima dake gefenshi da Sarkin Shaɗi. Kana su Waziri da Wambai Matawalle da Makawa Ɗurɓi Turaki Tafida da dai sauransu, kana Dogari na rike da laima wa Lamiɗo, Ɗanzagi kuwa ya kware murya yanata. "Gyara kimtsi sarki ya gaisheku". Kana sauran fadawa masu red and blue ɗin Uniform kuwa da tabka-tabkan rawuna babu kunne ko ɗaya suna biye dasu a baya da gefe gefe, suna tafe babu takalma, ga dogin bulali masu masifar tsawo da kauri suna jansu a ƙasa. Lamiɗo, Galadima, duk shigar manyan kaya na sarakuna, masu al'farma sukayi. Shi kuwa Sheykh Jabeer shigarsa ta al'farma na limamai yayi, wannan yasa kwarjinshi ya fi nasu. Daga nesa zakace yafi shekarunshi in ka hangoshi sabida kamala da haibarsa da suka baiyana a fili. Laminu kuwa tuni yayi gaba yana ɗaukar shigowarsu. Sabida aikinshi na jarida dama neman rohotone aikinshi. Sanadin saurin da suke ɗanyi ne yakesa al'kyabbar jikinshi ɗan buɗewa tana bazuwa hakan sai ya zama kamar ƙasaitace tasa yake wannan abun a wurin mai kallonshi. Gaba daya duk ta inda suka zo wucewa, sai ya ɗaga hannunshi duka biyu, yayi musu sallama tare da cewa. "Ya mai jiki?". In sunce da sauƙi. Sai yace. "Laah Ba'as ɗuhhuru in sha Allah". Duk inda suka gilma sai an bisu da ido. Especially Jabeer da babu wanda zai kalleshi bai ƙaraba Tuni labari ya kai ga kunnen Dim din asibitin. Lokaci ɗaya ya kikkira DOCTOR'S ɗin ta wayar salulu ya sanar musu su kimtsa komai su kula da kowa yadda ya dace. Mai martaba Lamiɗo na cikin asibitin. Ita kuwa Shatu tana haurawa sama. Ido take ɗagawa ta duba sunan Office da mai Office ɗin Office na forko taga musulmine haka yasa ta kutsa kai ciki. Zaune yake babu kowa sabida duk majinyatan sun tafi. Wasu an duba su, wasu kuma korarsu akayi da cewa yau half day ne, sabida haka su tafi. Da mamaki ya ɗago kanshi jin an shigo mishi Office babu sallama. Da sauri yace. "Waye?". Sabida cikin shigar yan matan larabawa take. Arabian gawd ne mai masifar kyau da taushi a jikinta wanda samanshi yake a dai-dai jikinta ƙasa shi kuma yake a buɗe, wasu irin duwatsune a jikin rigar tun daga sama har ƙasa sai wal-wali sukeyi suna ɗaukar ido. Tayi rolling kanta da ɗan kwalin rigar fuskarta ta fito ras a ciki. Wasu takalmi Golding color ne masu ɗan tudu dai-dai misali sai Ƴar ma dai-daiciyar hand bang mai masifar kyau shima Golding color ne, sai wayarta ƙirar iPhone 11. Fuskarta babu kolliya sai dai duk da haka bai hanata yin kyau ba gashin girarta ya konta lib-lib. Sai dai kuma ta rufe fuskar da tattausan Niƙab sai dai bashi da duhu sosai. To wannane ya hana Dr Salim ganin fuskanta, ita kuwa Shatu cikin tsananin ɓacin rai da zafin tozarcin da akayi wa yan uwanta tace. "Dr Salim". Cikin Mamaki yace. "Na'am". Yatsarta tasa tana nuna mishi maraba da baƙi ta wondon shi, cikin rauni tace. "Dr Salim na tabbatar kai musulmine, kuma nasan kasan cew manzon Allah yace shi musulmi ɗan uwan musulmine! Shin ko ka mance hakane, da ka kasa taimakawa yan uwanka musulmai da kafurai sukayi musu rauni akazo aka watsar dasu a nan kuma kuka ƙi dubasu meyasa, ko dan kawai sun kasance fulanin dajine laifinsu?". Cikin sanyi Dr Salim yace. "Wallahi umarni ne ba'a bamuba daga sama". Cikin tafasar zuciya tace. "Umarni wanne irin umarni kuma zaku jira bayan Allah da Manzonsa sun baku dukkan dama da umarnin taimakawa ɗan uwanku musulmi muddin kunada dama". Miƙewa tsaye yayi tare da cewa. "Dim ɗinmu ne ya hanamu dubasu". Cikin kufula tace. "Kan kafurar uwarshi! wato a cikin asibitima sai an mana ƙabilan ci, dan Allah Dr kuje ku taimakawa bayin Allancan". Cikin jin ƙarfin guiwa ya juya, ya fita, ya nufi can. Ita kuma haka ta rinƙa bin duk Office ɗin da taga na musulmi ne tana shiga. Tawagar Lamiɗo kuwa suna isa baƙin wani tamfatsetsen Office Sheykh Jabeer, ya ɗan kalli Lamiɗo tare da cewa. "Ni bari in shiga office na, ko mutun biyar in duba kafin ku gama zagayawa". Cikin gamsuwa da hakan Lamiɗo yace. "To bisimilla". Nan ya nufi babban barandar da Nurses suke tare a wurin maza da mata. Jamil kuma na biye dashi da System ɗinshi a hannunshi. Hakama Haroon ya biyoshi. Nurses ɗin kuwa suna hangoshi duk suka mimmiƙe tare da cewa. "Sir barka da zuwa". Barka dai yake ce musu tare da ratsawa yana wucewa. Su kuwa sun taru a wurin ne dan tawagar Lamiɗo na wucewa su sauƙa ƙasa su duba Fulanin nan kamar yadda Dim ɗinsu ya basu umarni sabida kada Lamiɗo ya gansu a yashe a ƙasa yasan abun bazai mishi daɗi ba. Suna ganin ya shiga Office ɗin suka juya da nufin zasu tafin sai kuma suka tsaya jiyo muryar Shatu na cewa. "Ku tsaya ina kuma zakuje? Baku da aikin yi ko? Amman da yake ba taimako ne a zuƙatankuba kun bar bayin Allah a wulaƙance ko?". Cikin masifar Nurses da su ba komaiba sai iya ciwa mutane zarafi a hatsale tace. "Ke kuma waye". Kallonta Shatu tayi sama da ƙasa tare da kallon rubutun dake saman aljihun rigarta ganin sunan arniyace ga kai da gashin doki ga uban faratu kamar na jaki yasa taja tsaki tare da cewa. "Banyi da keba, da masu hijabi nake mgn". Yadda tayi mgnar da ƙarfi ne yasa, su Jabeer ma jiyo muryarta, wanda shi kuwa zuwa yanzu yana jin zuciyarshi zata iya faɗowa ƙasa dan bugawar da takeyi. Jin muryar wata nurse ɗin tana cewa. "Wannan ma ai iskanci ne". Cikin taɓe fuska ya nunawa Jalal yatsa alamun ya buɗe mushi ƙofar yaga meke faruwa da suka cika mishi kunne da hayaniya. Da sauri Haroon yabiyo bayan Jalal suka fito. Shi kuma Sheykh Jabeer komawa yayi ya jingina da jikin kujerar shi. Tare da rage girman idonshi ya zubawa bayan Shatu ido. Ita kuwa Shatu cikin zafi ta kalli arniyar nan da tace mata wannan ma ai iskanci ne tace. "A kul kada ki kuskura ki sake kira min iskanci a gabana, ke kika sanshi ba niba, ke kika taso cikinsa". Sai kuma ta juya harce cikin fillanci tace. "Shegu masu wari". Sai kuma ta juyo ta fuskancesu da kyau, Haroon kuwa da Jalal ido suka zuba mata cikin mamaki. Shima Jabeer idon ya zuba mata so yake yaji meyasata ihun nan. Ita kuwa Shatu cikin sanyi ta fuskanci musulman ciki murya a ɗan tashe tace. "Kada dai ku manta nace daku nakeyi masu hijabi sabida nasan kun san ma'anar Al'muslim akul muslim. Kun kuma san girma da daraja da kuma wanda ya faɗi hakan". Cikin gamsuwa duk suka ɗaga mata kai, rai a ƙuntace tace. "To meyasa kuka bar waɗanan can bayin Allah'n a tozarce a yashe a maraba da baƙi koda dreesing na raunuka su bakuyi musuba, menene laifinsu, kawai dan sun kasance fulanin daji, shiyasa DOCTOR'S da Nurse's kab bazaku jiƙansu ba". Cikin sanyi ɗaya daga cikinsu tace. "Ayyah yanzuma can zamu tafi. Sabida sai yanzu Dim ya bamu umarni". Wani dogon tsaki taja tare da cewa. "Daga baya kenan yau kwanansu goma cib babu wanda daya dubasu, sai da suka gama jigata". Tsaki arnan ciki sukaja tare da juyawa suka tafi. A hankali Jalal ya juyo ya kalli Hammanshi da yake cewa. "Rufe min ƙofa wannan ta cika min kunne da ihu". Da sauri yace to. Haroon kuwa murmushi yayi tare da juyowa zai shiga ciki kafin Jalal ya rufe ƙofar. Da sauri ta juyo jin takun mutun a bayanta, Cikin muryar umarni tace wa Jalal. "Kai mai kamar larabawa tsaya kada ka rufe ƙofar, Office ɗin na arne ne ko musulmi?". Cikin dariya Haroon yace. "Na musulmi ne". Taku ta fara tare da nufo cikin Office ɗin. Wani irin sunkuyawa Jabeer yayi ya kifa ƙirjinshi kan babban Glass table dake gabanshi, sabida ji yakeyi tamkar kan zuciyarshi take taku. Ji yakeyi zuciyarshi zata fashe tsabar yadda take bugawa da azaban ƙarfi yadda take ƙara matsoshi haka bugawa zuciyarshi ke ƙara tsananta. Cikin mamaki ta zubawa Office ɗin ido. Office ne mai matukar girma da kyau da tsaruwa, kai bakace Dr Office bane in ba ɗan wannan gadon da labulanshi da sauran kayan aiyukansu ka ganiba. Duk da sai sati-sati yake zuwa nan Office ɗin tsab-tsab sai wani irin sanyi da ƙamshi yakeyi, cikin taɓe fuska tace. "Me hakan shima DOCTOR baida lfy ne? Kodai tsabar wulaƙanci ne?". Murmushi mai kama da dariya Haroon yayi sabida yasan babu abinda Jabeer ya tsana yake kuma tsoro kamar a tsaya a kanshi ana mgna da ƙarfi, yo shi ko a hankali kake mgna sai yace kana mishi ihu a kai bare kuma wannan da take tsaye a kusa dashi kuma tana mgna da ƙarfi cewa zaiyi haushi takeyi." Shi kuwa Sheykh Jabeer hannunshi yasa yana dafe ƙahon zuciyarshi da yakejin yana tsalle. Rafi'a kuwa tsaye tayi a bakin ƙofar tana kallon ikon Allah. Sauran Nurses ɗin kuwa suma, tuni sun tafi, maraba da baƙin. Ita ko Shatu a hankali ta ƙara motsowa gaban table ɗin hannunta tasa ta bug... 😂😂😂😂tsawon shekaru labarin littafin GARKUWA yana kimtse a kaina da zuciyata. Ni kaina in na tunoshi sai nayi murmushi nayi shauƙi sarƙaƙiyarsa kan hanani baccin dare inyi ta nazartan lmrin lbrin GARKUWA, nakanji murmushi da daɗi in na tuna lbrin nakan zubda hawaye wasu lokutan wasu lokutan nakanji jikina yayi sanyi da rayuwar duniya, labarin Garkuwa bazaka ganeshi ba, sai in ka karantashi duk iya lbrin mai labartawa bazai labarta maka yadda komai yakeba, Uhummm Allah ya nuna mana ƙarshensa, salon soyayyar Sheykh ta musamman ce.. Masoyan Parvina kuna sani dariya. Masoyan Shatu kuna burgeni. Ina masoyan Boleru jinjinan girma gareku. Masoyan Sheykh ina sonku, Sheykh yana gaidaku. Masoyan Jalal yace ku dena kallonshi. Masoyan Umaymah tace ku tayata da addu'a Allah ya yaye musu matsalarsu. Wai Ya Ba'ana baida masoya ne? Allah sarki Ba'ana ina sonshi dan al'khairin da yayiwa Aysha a baya. To wai wane al'khairi yayi mata ne? Littafin GARKUWA na kuɗine in kina buƙatan Normal group turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276. In kuma special Group kikeso kiyi min TRANSFER ɗin dubu ɗaya rak ta asusun na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276. Masu turo katin mtn numbers ɗin zaki turo ba hotonba. By *GARKUWAR FULANI* Ta ɗan buga table ɗin, tare da cewa. "Malam ka tashi kaje ka taimakawa yan uwanka musulmai! in kuma baka da lfy ne ka nemi bokaye irinka su duba lfyarka". Zuwa yanzu gaba ɗaya jikinshi tsuma yakeyi ta ciki. Kanshi ne yakeji yana jujjuya mishi sabida yadda ta konkotsa glass table ɗin da kanshi ke kife a kai. Ga kuma sautin muryarta da yake jinshi har tsakiyar kanshi. Da sauri ya ɗago kanshi tare da ware matsakaita kyawawan idanunshi na zaiba. Cikin sauri Haroon ya matsoshi ganin idanunshi sun cika tab da ƙwalla sai sheƙi sukeyi alamun suna iya zubda ƙollan a ko wanne lokacin. Cikin harɗewar murya ta larabci yacewa Haroon. "Please ka fitar da ita a nan, ta matsa kaina zata fasa min dodon kunne". Ita kuwa Shatu cikin tarin mamaki da al'ajabi ta zaro manyan idanunta tare da cewa. "Laaah!". Sai kuma ta fara ɗan ja da baya tare da cewa. "Afwan baka da lfy ne!?." Wani irin fitinenne murmushi Haroon yayi tare da cewa. "Eh baya jin daɗi ne, ɗan fita zamu kira wasu bokayen suzo su dubashi". Cikin sauri tace. "Subahanallahi bokaye kuma?". Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. "Yesss ba haka kikace ba, ya nemi bokaye ƴan uwanshi su dubashi". Kanta ta ɗan dafe tare da cewa. "No kada ka munana min zato, ina nufin likita bokan turai ka gane ko?". Da sauri taja da baya ganin Jabeer ya miƙa tsaye da ƙarfi. Shi kuwa Sheykh Jabeer tsayuwanta kusa dashi barazana ce ga zuciyarshi tabbas zata iya faso ƙirjinshi ta fito. Ganin yadda ya haɗe fuska ya nuna mata hanyar fitane, yasa ta juya ta fita. Shi kuwa Jabeer komawa yayi ya zauna tare da sauƙe wasu tagwayen ajiyan zuciya a jere a jere. A hankali yake jin bugun zuciyarshin na ɗan dai-dai-ta kamar dai yadda yaji kafin ta shigo. Sai kuma ya fara jin zuciyarshi na tsinkewa ras-ras kamar dai tana tsoron kada wani abu yayi nesa da itane. "Ya ilahi ya mujibadda'awati ya hayyu ya ƙayyum". Sune kalaman da Jabeer yaketa maimatawa a saman lips ɗinshi. Haroon kuwa wani irin kallo yakeyi ma Jabeer mai cike da nazari. Jalal ma kallonshin yake cike da tarin mamaki duk da sun san baya son akeyin mgn da ƙarfi a kanshi, to amman idonshi bai taɓa ciko da hawaye ba, sai yau. Ita kuwa Shatu, ido ta zubawa Rafi'a da ta tsareta da ido, cikin yin ƙasa da murya tace. "Rafi'a dama, wannan shugaban tuzuran ƙasar nan, yana aiki anan asibitin gwamnatin jihar nema?". Kamo hannunta Rafi'a tayi tajata sukayi gaba. Haroon kuwa dariya yayi sabida, duk da rage muryarta da tayi sunji abinda tace, sabida wurin da suke ɗin yanada amsa kuwar amo. Cikin yin ƙasa da murya sosai Rafi'a tace. "Garkuwa ki nitsufa ki rufa mana asiri, kin ko san waye wannan?!". Shiru sukayi dukansu lokacin da suka juyo wata kekyawar mata tana bawa wasu ƴan mata Nurses a ƙalla sun kai goma lbri. Ido Rafi'a da Shatu suka zubama wannan matar cewa. "Shi wannan Dr Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa, ba kamar sauran mutane bane, shi mutunne da Allah yayi masa wasu baiwa da nasabobi masu tarin yawa". Wata ƴar kekyawar cikinsu ne ta ɗan lumshe ido tare da cewa. "Allah ya sani Aunty ina sonshi, ina son wa'azin shi, muryarshi kawai in naji yana zuba larabci sai inji bani da sauran damuwa a duniya, sai dai shi kuma yana nan kamar dutse!". Da sauri Matar nan tace. "Ai bazai yiwuba, wlh bazai taɓa kulakiba, duk nacinki da korkosarki, shiyasa wasu ke raɗe-raɗin shi waliyi ne!". Numfashin ta sauƙe tare da ci gaba da cewa. "Duk matsayinki, kyanki, mulki, sarauta, gata, ilimi!. ko da meye kike taƙama dashi a duniya ya fiki abin". Kusan a tare suka haɗa baki wurin cewa. "Kawai dan shi jikan sarkine sai yafi mu komi?". Kanta ta jinjina tare da gyara zaman ta cikin sanyi tace. "Ba haka bane. Bari kuji kaɗan daga cikin nasabarsa. Kunga forko dai shi mutum ne wanda ubangijin yayi mishi baiwar ilimin addini dana zamani. Yana ɗaya daga cikin manyan malam da Afirka gaba ɗaya take ji dashi. Sabida a ƙiyasin malamai babu yaro matashi mai jini a jiki da tarin ilimin addini kamarshi. Tun yanada shekaru takwas a duniya ya haddaci al'ƙur'ani mai girma. Sannan ya fara karatun littafai shine matashin da yakeda haddar hadisai zunzurutunsu a kanshi sama da dubu ashirin. Kunji wannan darajeta da tasa ko manyan mutane suke girmama shi. Sannan shi jinin Masarautar Joɗa ne ta wurin mahaifinshi. Ta wurin mahaifiyarshi kuwa shi jinin sarki Jalaluddin ne, masarautar sarkin Musulmai. Kana ta wurin kakarshi data haifi mamanshi. Asalin balarabiyar saudiya ce, wacce zuriyarta ne limamen Harami. Kunga nasaba kan nasaba kenan. In kyau ne na halitta, babu irin kyan da bai ganiba, In kuwa kuɗine, ku leka ƙasan gidan saman nan zakuga ayarin motocin da sukayi mishi rakiya, to ko kakan nashi Lamiɗo motar da yake hawa bata kai ta Jabeer ba. Uwa uba shi mutun ne da ya ƙoshi da sunna, baya son bidi'a. Shi mutun ne wanda ya samu kekyawan zato a wurin mutanen duniya ake mishi shaidar salihi, mumini, mai tausayi." Da sauri suka ƙatseta da cewa. "To Aunty meya hanashi yin aure har yanzu?". Cikin maida numfashi tace. "Allahu alamu, sai dai ance kamar shi bana miji bane!". Cikin sauri wata tace. "Kai mgnar. Duniya dan Allah kiji zancen ƴan shashi faɗi. Bita da ƙulli har an samo sharrin da aka liƙa mishi bawan Allah." Rafi'a kuwa kai ta jinjinawa Shatu alamun kinji ko, ita kuwa Shatu zuru tayi kamar makahon daya tsinka garaya". Cikin sauri wacce tace tana sonshin tace. "Wlh ni dai ko shi bana miji bane zan iya zama dashi a hakan in da zai yarda muyi aure". A hankali Shatu ta gyara riƙon da tayiwa wayarta tana ɗaukar su video. A hankali matar nan ta nisa tare da cewa. "Uhum Nafeesat kenan ai kuwa da wuya ya aureki duk abinda zakiyi. Sabida kin ga Dr sugzana yar India ce ƙabilar buramin bautar wuta takeyi. Tace tana sonshin, tace in dai zai aureta zata musulunta, amman yaƙi". Da sauri ɗaya dake cinsu tace. "Sabida me yaƙi duk da tayinta na shiga addinin Allah?". Cikin sanyi matar tace. "Yayi bayani kuma manyan malamai sun gamsu da hujjarsa, inda yace, tace dole sai in zai aureta zata musulunta, kenan badon Allah zata musulunta ba sai dan sonshi. Ta kuma ce in sunyi aure duk yaransu rabasu zasuyi rabi suyi addininshi rabi suyi addininta bi ma'ana wasu suyi bautar wuta wa iyazubillah. Yace wannan dalilin yasa bazai aureta ba, kuma shi baya sonta, ya kuma gargaɗi mata su dena cewa suna sonshi. Dan shi yanzu al'majiri ne sai ya girma zaiyi aure". Dariya sukayi baki ɗayansu. Jin hakane yasa Rafi'a yana Shatu suka ci gaba da tafi. Su kuma waɗancan sukaci gaba da hirarsu. Tafiya kaɗan sukayi suka samu wasu yan mata da samari suna hira ɗaya daga cikinsu na cewa "Ni tsarin Sheykh Jabeer yana masifar burgeni a rayuwata. Shifa tunda yake a duniya babu wani mahaluƙin da zaice yaga koda singalalin hannunshi ne a waje. Mutum ne da Allah yayi mishi sutura, yake kuma suturce kanshi." Cikin dariya wani yace. "Kai nima yana burgeni sai dai tsarinshi na wai mata su dena yafa gyale, su rinƙa yin shigar zurmuƙa-zurmuƙan hija baine bai minba, to mu matasa taya zamuyi ta kallonsu munajin daɗi. Ni wlh wani lokacin a kallonma nake biyan buƙatar damuwata sai dai inje inyi wonka". Cikin tashin hankali ɗaya daga cikinsu yace. "Ouzubilla, ka nemi gafar Allah wlh zina kakeyi". Cikin zaro ido yace. "Kai malam dakata ni banyi zinaba". Cikin sanyi babban nasu yace. "Wlh kayi sabida ita zina ai kashi-kashi ce akwai ta ido akwai ta kunne haka kuma akwai ta zahiriya, fisabilillahi ka kalli yar mutane na tafiya har kaji ka biya buƙatar ka?". Kai ya gyaɗa musu cikin sanyin jiki. Nan sukayi ta mishi nasi daya kame idanunshi Da sauri suka wuce su. Ita kuwa Rafi'a cikin murmushi tace. "To bari in baki amsar tambayar ki. Yana zuwa nan asibitin sau ɗaya cikin ko wanne sati. In yazo kuma ranan duk wanda ya duba magani kyautane, in kuma aikine kyautane. Kinga Hospital ɗin school ɗinmu shi kuma a wata yake zuwa sau ɗaya, Nanam da kyar ya yarda, yanada asibitinshi mai zaman kanshi can yafi maida hankali". Ajiyan zuciya Shatu tayi tare da cewa. "Uhum can yake tara kuɗin bayin Allah ya ƙwamushewa dai". Kai Rafi'a ta jujjuya tare da cewa. "No ba haka bane, duk abinda zan ce miki bazaki gamsuba in sha Allah sai Next month in ciwon mararki ya tashi, zan kaiki can zakiga zahiri. Amman dai daga sunan asibitin zaki iya fahimtar manufarsa". Kallonta ta ɗanyi tare da cewa. "Menene sunan asibitin?". Ƙara saurin tafiyarsu sukayi tare da cewa. "Ballitai Hospital". Kanta ta gyaɗa alamun gamsuwa da sunan asibitin kana taja hannun Rafi'a suka tafi can maraba da baƙi. Abin mamaki suna isa suka samu. Kusan rabin DOCTOR'S din asibitin duk suna wurin. Duk DOCTOR'S ɗin da Shatu tayiwa mgna sunzo nan sunata basu taimakon gaggawa. Kana ga Nurses tako Ina, sunata tura marasa lfyan ana basu gadaje. Cikin abinda bai gaza awa ɗaya da rabi ba. Komai yayi dai-dai hatta waɗanda za'ayiwa aikin anyi musu. Bisa umarnin Lamiɗo kana ya rinƙa bin gadajensu yana ajiye musu kuɗi dubu biyar-biyar. Sosai wannan abun yayi masifar yiwa Shatu daɗi, tana kallon dattijon tamkar wani nata, Godiya sosai sukayi musu da zasu tafi, suna fita nan sukayi kiciɓis da Jabeer da yanzu ya fito ɗakin tiyata. Ita kuwa Shatu Junaidun Junainah ta kalla lokacin da aka dawo dashi daga ɗakin tiyata, Inda aka ɗinke mishi inda aka sareshi. Cikin murmushin yace. "Adda Shatu zamu kwana ko?". Murmushin jin daɗi tayi tare da cewa. "A a Junaidun yanzuma zan tafi, kasan Ummey ba lfy, amman jibi ma zanzo gobe su ya Salmanu zasu zo, yanzu dai hankalinmu ya konta tunda kun samu kulawar likitocin yanzu sai matsalar abinci". Cikin sanyi Sumaye matar marigayi Sarkin bakansu, tace. "La abinci kam bamu da matsalarshi, tako ina zakiga musulmai na dafo abinci suna kawo mana sadaka, harda kayan zaƙi da kuɗi wasu ke bamu". Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah yau kam mutanen Rugar Bani zasuji lbri mai daɗi". Cikin kula tace. "Toni yanzu zan tafi in Sha Allah gobe akwai masu zuwa, Allah ya baku lfy". Ta faɗi tana kallon sauran mutanen nasu. Haka Rafi'a ma tayi musu fatan lfy kana suka fita tare. Adaidaita suka shiga, saida ya kai Shatu tasha kafin. Ya wuce da Rafi'a school ɗin su. A can wurinsu Lamiɗo kuwa ganin lokacin sallan la'asar yayine yasa Jabeer cewa, suyi salla a masallacin asibitin kafin su tafi. Haka kuwa akayi, sai gashi masallaci ya cika maƙil da bani adam, saida suka idarne kana suka kama hanyar tafiya garin Rugar Bani. A cikin motocin kuwa kowa da abinda yakeyi. Shi kuwa Sheykh Jabeer tsuratul Khaf yake karantawa a hankali. Hakama Lamiɗo. Su Jalal kuwa kowa na ruggume da waya. Haroon ma waya yakeyi da Umaymah tana tambayarshi sun isane. Nan yake gaya mata inda suke da abinda sukayi. A cikin Rugar Bani kuwa, kamar ko wacce ranar jumma'a yauma hakane. Tunda aka taso sallan jumma'a suka dawo tsakar garinsu suka zauna suna ƙara jadda mitin ɗin su na ɗaukar fansa. Zuwa yanzu garin yana amsar baƙoncin Fulanin da suka gaiyata tako wani sashi na Afirka. Sunata shirye-shiryen su. Suna cikin masallaci suna sallan la'asar ne suka rinƙa jiyo, shigowar motoci cikin Rugarsu kamar bazasu ƙare ba. Cikin nitsuwa sukaci gaba da sallan su. Su Lamiɗo kuwa suna shiga garin ganin tsit kuma alamun ana salla, sai yace su tsagaita gudun. Jabeer kuwa zuwa yanzu tuni zuciyarshi ta fara luguden dukan ƙirjinshi ya rasa wannan abu na menene? Yanzu wannan karo na huɗu kenan yana jin wannan abun a rayuwarsa, ya kuma gwada kanshi yaga bashi da BP dan sani BP nayin hakane ya sashi godawa. A jere a jere sukayi parking motocinsu cikin nitsuwa, Dogarai da fadawa suka fito suka zagaya motocin. Bayan sun idar da salla sunyi addu'o'insu ne kana suka fito. Gani fadawa da dogarai ma kaɗai ya ganar dasu waye yazo. Dan haka cikin karrama da mutun-tawa Arɗo Bani ya nufi inda suke. Sosai dogarai sukayi mamakin yadda wannan karon kuma yakeyi kamar ya haɗiyesu dan farin cikin zuwansu saɓanin wancan karon da yayi ta aunawa Lamiɗo boma-boman baƙaƙen maganganu. Jiki na rawa ya juyo ya kalli matasan tare da cewa. "Maza ku shiga cikin gidan ku fito da dardumai da kilisai kuzo ki shimfiɗa. Ina sarkin kiɗa maza a fito da gangaguna a fara sanarwa. Mabusa ku fito." Ai kuwa cikin abinda bai gaza 25 minutes ba aka gama shirya komai. Tuni mutane sun cika sunyi maƙil ko ina ya cika da bani adam. Kiɗe-kiɗen da bushe-bushen sarewa da al'gaita kuwa tuni ya cika illahirin garin tako ina mutane ke shigowa. Ba'ana da tun jiya yake cikin ɗakin dodon tsafinsu Bonon. Jin al'gaita Shaɗi ne, ya sashi fitowa bayan ya gama shafe magunguna. Dama yayi zaton wannan hegen mai jajayen kunnuwan zaizo shiyasa tun jiya ya shiga ɗakin sirri dan a dafashi da kyau. Jinsu ne yasa ya fito dashi da tawagarsa suka nufi Rugar Bani. Lamiɗo kuwa da tawagarsa a hankali cikin ƙasaita da kwarjini suke taku har i zuwa cikin rumfar karan da aka malale musu kujeru da kilisai. Bayan sun zaunane duk dattawan wurin sukazo suka gaida Lamiɗo da tawagarsa. Jabeer kuwa ji yake tamkar ya kira Sojoji su zo su zazzane mishi mutanen garin gaba ɗayansu ko zaiji ya huce da abinda sukayi mishi. Sam baya son ganin fuskokinsu, ga toshe mishi kunne da sukayi da wannan bushe-bushen sarewa. Ga bugun zuciyarshin dake neman zautar dashi. Allah ya sani baya son ganin ko ƙasar garinne. Cikin kula da nitsuwa da kamala Bappa ya kalli Jabeer ɗin tare da cewa. "Yaro ya ƙarfin jikin naka". Ba tare daya ɗago kanshiba ya amsa, sabida jin muryar tanada kamala. A hankali yace. "Alhamdulillah". Gaba ɗayansu suna farin cikin ganin Jabeer yazo cikin ƙoshin lfy. Sunyi masifar mamaki ganinshi garau ya worke cikin mako ɗaya tak. Wannane ya ƙara sawa Ya Salmanu wani farin ciki na ban mamaki. A hankali Bappa yace. "Masha Allah, Allah ya ƙara sauƙi". Idonshi ya ɗan ɗago ya kalleshi, haka nan yaji dottijon ya cika mishi ido a hankali yace. "Amin ya Allah". Bukar ne ya ɗan kalleshi tare da cewa. "Yanzu yaron nan kaine? Ka sake zuwa garin nan lallai baka son ranka". A daƙile Jabeer yace. "Inuwa tace". Galadima ne ya ɗan kalleshi tare da mishi alamun kada yayi mgna. Kwaffa yayi tare da murtuke fuska. A hankali su Arɗo bani suka koma wurin zamansu. Kana Barmuji ya fara sanarwan ana son ganin Ba'ana a tsakiyar fili. Wannan abu shine na forko a tarihin shi a nemeshi yazo tsakiyar fili dan a rama gasar da yayi. Haka yasa cikin karsashi da buɗa ƙwanji yayi wani irin tsalle ya faɗo tsakiyar taron. Juyi ya farayi da ihu da ɗaga hannunshi sama, saida yayi kusan sau goma kafin yacewa Barmuji. "Ka gayawa yan kallo in dai an cini gasa zan tafi in bar ƙasar nan, zan koma ƙasar Cameroon nida ƙasar nan sai dai ziyara, Dan ba'a yin jarumai biyu a gari ɗaya kamar yadda ba'a sarakuna biyu a gari ɗaya." Wani irin ihu da shewa gaba ɗaya mutanen suka ruɗe dashi lokacin da Barmuji ya sanar da ikirarin Ba'ana. Kana dattawan garin kuma kowa da abinda ke cikin ransa Arɗo Bani dasu Bappa kamar su haɗiye haƙorinsu dan daɗi. Arɗo Bani ne ya ronƙofo kusa da Lamiɗo cikin nitsuwar datattaku yace. "Allah rene, bisimilla GARKUWA ya fito fage shi ake jira." Kai ya gyaɗa mushi kana ya juyo ya kalli gefen damanshi inda Jabeer ke zaune cikin shigarsa ta al'farma, yayi masifar kyau, yana zaune cikin kamala sai lips ɗinshi ke ɗan motsawa a hankali alamun tasbihi yakeyi. Cikin yanayi girma da bada umarni da tsare fuska Lamiɗo yace. "Jabeer kai ake jira tashi kaje muyi abinda ya kawomu." Fuskarshi ya tsuke tare da lumshe idonshi, muryar Galadima da yajune yasashi buɗe idonshi. Shi kuwa Galadima hannu ya miƙa ya kamo hannun Jabeer, tare da fara ja alamun zai miƙar dashi tsaye. Cikin mamaki Jabeer ya zubawa tsohon ido wanda yake Bappa ne ga Lamiɗo, in banda ƙarfin hali inashi ina iya ɗaga Jabeer. Muryar Lamiɗo yaji yana kuma cewa. "Jabeer DAN ALLAH KA TASHI". Tsaki ya ɗan ja kana ya yunƙura ya miƙa a hankali. Cikin jin daɗi Galadima ya kama hannunshi yaja suka fara taku, zuwa cikin taron. A hankali yake bin bayan Galadima kana fadawa na biye dasu. Al'kyabbar shi ya ɗan gyara mahaɗinta. Suna isa tsakiyar taron. Mabusa da makaɗa duk suka kaceme wurin da bushe-bushen sarewa da al'gaita kana da kaɗe-kaɗen. Barmuji ne ya matso bayanshi da alamun zai cire mishi Al'kyabbar shi. Da sauri Barmuji ya dakata sabida ganin wani irin lallo da Jabeer ya watsa mishi cikin tabbatarwa yace. "Kada ka sake gangancin ciremin suturar da Allah yayi min har abadan. In kuwa ka gwada tabbas zakaji yadda raɗaɗin marin tafin hannuna yake, in kunnenka ya kuramce ansan kuramtane yasa bazakaji gargaɗi da kashedi na ba!". Ya ƙarishe mgnar da tafasar zuciya, cikin tsuma Barmuji ya rusuna tare da cewa. "Duk da dokar gasa ce, anyi maka wannan lamunin tunda kaine mai duka ba kai za'a dakaba". Ba'ana kuwa wani murmushi jin daɗi yayi sabida yasan yin duka da ƙatuwar riga haka, zai takurashi bazai samu damar zage ƙarfin shi ya zabga mishi bulaliyar ba. (Allah sarki Ba'ana bai san zafin hannun Sheykh bane. Sarkin Shaɗi ne, ya miƙe tsaye tare da tanɗun shantun da a ciki suka zuro bulalin nasu. Ya nufi wurinsu Jabeer yana zuwa. Yasa hannunshi ya zaro bulala ɗaya daga cikin bulalin ya miƙa mishi. Hannun yasa ya amshi bulalar. Kana ya gyara al'kyabbar jikinshi. Shi kuwa ba'ana gabanshi ya matso ya tsaya ya buɗa sawunshi, kana, yasa hannunshi duka biyu ya riƙe ƙugunshi, ya buɗa ƙwanjinshi da kyau. Sheykh kuwa ƙasar garin ya zubawa ido, yana tuno irin zafi da ƙunar sashi cire kayanshi da sukayi satin daya gabata, yana tuna raɗaɗin da zuciyarsa ta masa a wannan lokacin. Busar sarewa da akayi azaban ƙarfi ne, tabbacin an bada dama a farane. Yasa Jabeer gyara riƙon da yayiwa bulalar, yana maiji cikin ransa da jikinsa zai rama dukan azaba da wannan ya mishi. Yanajin zai ramane kuma dan tsorotar dashi kan sake dukan wani. Yasani in sha Allah daga kanshi baza'a sake wannan gasar daba adadin bane, yayi niyar yin ramuwar ne dan tare wannan ɓarakar zai ramane ko zai samu ya huce tsanar da yayi mutanen garin, sabida kasan cewarsu Musulmai ƴan uwansa baya son yayi musu irin wannan tsabar lokacin ɗaya fushinsa na ranar ya dawo. Shiyasa ya murza yatsunshi da kyau tare da matsawa gefe kaɗan, Rumtse bubalar yayi a tafin hannunsa da kyau, kana ɗagata tare kuma da cewa Bismillah, ya fara da sunan Allah kana ya ɗaura da fara karanto ayatul shifa sannan ya zabgawa Ba'ana ita a tsakiyar bayanshi. Gaba ɗaya hankali da idon kowa bisa fuskar ba'ana yake. Shi kuwa ba'ana wani irin murmushi yayi tare da kallon gefe da gefenshi kana, yayi fito alamun babu wani abu da yaji dai yaji tsikar jikinshi yana tashi yar-yar. Arɗo Bani da sauran dattawan kuwa har ji sukeyi tamkar su kamo hannun Jabeer suyi ta zabgar Ba'ana babu ƙaƙƙautawa. Shi kuwa Jabeer wani bulalan ya kuma shimfiɗa mishi a tsakiyar bayanshi tare da sunan Allah. Still murmushi yayi sai dai wani irin masifeffen bugawa da zuciyarsa tayi ya tsinke ras. A karo na uku ya tabka mishi bulalar a tsakiyan kafaɗunshi wannan karon baiyi murmushi ba, ƙebta idonsa yayi, tare da gyara tsayuwa sai kace dutse ake tabkawa bulalin. Fargabane ya fara dukan ƙirazan dattawan Fulani, yayinda ƙabilar ɓachama kuwa, suketa ihu da tsalle da fito da kiran ba'ana suna ƙara mishi ƙarsashi. Bulala ta biyar Jabeer ya kuma tsula mishi, still babu sauyi. Cikin sauri Arɗo Bani ya juyo ya kalli Lamiɗo dake zaune. Ko ajikinshi dashi da tawagarsa, Sarkin Shaɗi kuwa murmushi ma yakeyi. Cikin fargaba, Arɗo Bani yace. "Allah rene Lamiɗo wannan yaron bai iya duka da ƙarfi bane? Ko dai ba bulalin masarautarku bace!?". Wani irin kallo mai cike da mamaki da kuma tuhuma Lamiɗo yayi mishi. Sai kuma dai ya kauda kanshi. Ɗanzagi ne yace. "Hattara dai Arɗo , Masarauta Joɗa sun wuce aro, zuba ido kaga ikon Allah". Bulala ta bakwai ne, Jabeer ya ɗago ya tsulala mishi ita a gadon bayanshi. Da sauri Ba'ana ya rufe ƙwayar idanunshi sabida wani irin tashi da yaji tsikar jikinshi yayi. Tsikar jikinshi bai gama konciya ba, yakuma jin Jabeer ya rausa mushi wata bulaliyar, da sauri ya buɗe idonshi sabida. Wani irin Yar-yar da yaji tsikar jikinshi tana zubawa duk gashin jikinshi ya miƙe tsaye. Bai gama dawowa nazarin meyasa yakejin hakaba ya kuma jin wata bulaliyar. A hankali yaji zufa ya fara keto mishi duk ta inda hudan gashin jiki yake a fatarsa. Murmushi yakeyi har yanzu sabida bawai zafi yakeji ba, sai dai fargaba ta rufeshi, sabida jin alamun sihirurrukan jikinshine ke fecewa. A haka Jabeer yayi ta tsula mishi bulala har zuwa bulala ta goma sha ɗaya. Ata goma sha biyu ne, da ya tsula mishi yayi wani irin gantsarewa sabida wani irin azabebben ƙaiƙayi da yaji wurin yanayi mishi. Da sauri yasa hannunshin a bayanshi alamun zai sosa. Ife-ife da sowan da matasa suka farayi ne da Muryar Barmuji na cewa. "Dokar gasa banda susa". Da sauri ya dawo da hannunshin tare da cewa. "To ya dane karatun da yakeyi, bana so, ya dena kira min sunan Allah". Wata bulalar Sheykh ya zabgawa shege tare da cewa. "Sunan uwarka zan kira maka in ban kira sunan Allah ba?". Arɗo Bani kuwa wani irin ajiyan zuciya mai ƙarfi yaja. Shi kuwa Ba'ana wani irin masifeffen ƙaiƙayi ne yakeji a duk inda Jabeer ya zuba mushi bulala, a bulala ta goma sha biyar ne, da aka zuba mushi. Yayi wani irin gantsarewan da yafi na ɗazu. Wani irin azabebben zafi da raɗadine yakeji yana tsarga mishi jiki da zuciya. Zuface ta ketomishi tako wanne sashi na jikinshi. Cikin sauri Jabeer ya juya bulalar ya amshi ta biyu ya haɗa data forkon. Ya damƙesu a hannun hagunshi. Wanda dama shi badamene kuma bahagone duk abinda hannun damanshi kan iya yi to na hagun yana fi iyawa. Sai dai kasamcewarshi mutun mai ilimi da sanin addini shiyasa yake amfani da hadinsin nan da Manzon Allah ke cewa. A cikin dukkan abinda zamuyi mu wakilta dama a forko, har dai sai in shiga bayan gidane aka ware shiga da ƙafar hagu. To juya hannun yayi da hannun hagunshi, kana ya riƙe mahaɗin al'kyabbar jikinshi da hannun damanshi. Gyara tsayuwarshi yayi kana ya ɗaga bulalar da ƙarfi ya zubawa Ba'ana a tsakiyar bayanshi. Wani irin azabebben ihu mai ƙarfin amo da karaji Ba'ana ya kurma tare da fara karkarwa kar-kar tamkar mai farfaɗiya. Ihun da ya kurmane yayi masifar tada hankalin dukkan kafurai magoya mayanshi. Arɗo Bani kuwa a gabansu Lamiɗo ya tashi tsaye ya juya ya fuskanci al'ƙibila yayi sujjada. Bappa ma da kanshi wani irin murmushin jin daɗi yakeyi. Hakama duk sauran dottawan. Shi kuwa Ba'ana wani irin azabebben kuma masifeffen zafi yakeji a dukkan sashin jikinshi. Wani irin tsalle ya buga da ƙarfi lokacin da aka kumayi mishi bulala ta ashirin. Wani irin tsuma da karkarwa jikinshi keyi hatta Ba'anansa miƙewa tayi tana karkarwa, wata tafasashiyar zuface ta sinƙo mishi, zafi yakeji har cikin ƙoƙon kanshi da zuciyarshi. Bulala ta ashirin da biyu akayi mishine yasashi fashewa da wani irin kuka mai azaban ƙarfi wani irin masifeffen fitinenne fitsarin azaba ya fara kwaranyo mishi, ihu mai cike da azaba yayi. Wanda gaba ɗaya rugar saida kowa ya jiyoshi. Ƙabilar ɓachama kuwa gaba ɗaya suma kuka suka saka. Shi kuwa Ba'ana da ƙarfi ya faɗi ƙasa yana burbuwa, tamkar wanda yayi al'janu. faɗuwanshi ƙasane yasa Jabeer rusunowa ya rinƙa tabka mishi bulalar, ihu da burbuwa da rarrafe alamun guduwa Ba'ana yakeyi cikin azaba da karaɗi da kuka yake cewa. "Wayyo! Wayyo!! Wayyo Bonon!!! Ka ceceni zan mutu zai kasheni. Wayyo Bononnnnnn! Yau bakayi min ranaba, ga bulalin karin sihirina sun iso gareni wayyoooooooo Bonon meyasa baka gaya minba na hudu tun kan wannan malamin ya kasheni ya karya min komai na jikina da sunan Allah." Ya ƙarishe mgnar da ƙarfi tare da miƙewa tsaye ya fuskanci kudu. Ya ɗiba a guje ya ari ta kare ya nausa a guje. Wani irin taku Jabeer yayi tare da biyoshi baya da sassarfa abunka da dogon mutun sai gashi ya isoshi a gigice ya fara kai mishi bulalin hagu da dama, Jin azabar ta zarce azabar da yake zatone, yasa Ba'ana kurma ihu da kururuwan da yasa kab mutane suka nufosu. Gudu yakeyi Jabeer na binshi yana zaneshi har ya fiddashi cikin taron gaba ɗaya. Barmuji ne ya riƙe hannun Jabeer tare da cewa. "A dokar gasa Shaɗi in dai ya gudu ka bishi ka korashi cikin farfajiyar shike nan ya faɗi a gasa kaci. Kuma bazai sake samun damar shiga gasarba bazai kuma sake zama a garinba." Wani irin busar sarewa da al'gaita kana da kiɗe-kiɗen tsantsar farin ciki, al'ummar Rugar Bani suka farayi. Sunayi suna zagaye Jabeer. Haroon kuwa da Arɗo Bani da Galadima miƙewa sukayi cikin farin ciki suka ruggumeshi. Jamil, Jalal, Imran, Hashim, Sulaiman. Suma kab farin cikine ya cika musu zuƙata. Laminu kuwa ji yakeyi tamkar ya shaƙo Jabeer ya karshi sai dai tabbas dama ya zaci aha dan shi mari ɗaya nema Sheykh ya masa ya kusan suma, shiyasa ya tausayawa Ba'ana. Lamiɗo kuwa jinjina kai yakeyi yana tattausan murmushi. Koda su Galadima suka ruggumeshi, Arɗo Bani kuwa kama hannunshi yayi ya ɗaga sama alamun yaci gasar Shaɗin. A haka suka iso gaban Lamiɗo hannunshi yasa ya dafa kan Jabeer tare da sanya mushi al'barka. Mutane kuwa duk an kacame da farin ciki. Ya Salmanu kuwa kusan suma yayi tsabar masifar jin daɗi. Alhamdulillah yau dai burinshi ya cika ya samu konciyar hankalin duniya an ɗauka musu fansa, shida masoyan Shatu na baya, harma da yayanshi. Jan gefe makaɗan suka sabi, da sauran zugar jamar gari. Jabeer kuwa mamaki yakeyi yadda yaga. Fulani nata shigowa garin tako ina wasu bisa dawakai wasuma ƙan raƙuma. Lamiɗo kuwa waya yakeyi da amalun a sirrance yake mgnar sabida ko Jabeer ɗin dake kusa dashi baya jinshi. Bisa umarnin Arɗo Bani ne aka rinƙa fito da ƙwaran nono da fura da dambu da ƙwaran zuma, Ana kawowa su Lamiɗo. Wanda fadawa da dogarai ne sukasha. A hankali Jabeer ya kalli Lamiɗo cikin gajiya yace. "To ai sai ku tashi mu tafi ko!". Shiru Lamiɗo yayi mishi, ganin hakane, ya gyara hiramin kanshi kana ya kuma cewa. "Mu tafi ko". Galadima ne yace. "Ai bamu gamaba". Cikin sauri Haroon yace. "To meya rage kuma?". Galadima ya buɗe bakin zai bashi amsa kenan. Sai kuma duk suka juyo suna kallon wasu tsala-tsalan motocine masu masifar kyau da tsada, suna shigowa Rugar Bani a jere-a jere. Cikin fidda numfashi Haroon ya ɗan kalli motocine da mamaki yace. "Ha Jabeer kalli wannan kamar tawagar motocin Uncle Abdulkarim da Abudulfata kalli kamarfa harda Jadda". (Sarki Jalaluddin suke cewa Jadda) Sai kuwa ya juyo ya kalli Lamiɗo cikin nitsuwa yace. "Lamiɗo lfy kuwa?". Kanshi ya gyaɗa mishi alamar eh Lfy kau. Shi kuwa Sheykh Jabeer cikin nitsuwa yake kallon ayarin motocin a fakaice tabbas. Su Jalaluddin ne da yaranshi. Kana ga kuma Baban Haroon, ga kuma su Dr Aliyu da Barrister Kamal da su Baba Basiru Baba Nasiru dama duk sauran manyan masarautarsu. Da sauri ya juyo ya kalli Lamiɗo da nufin yin tambaya sai kuma yayi shiru ganin Lamiɗo na mgna da Galadima da kuma wani amintaccen bafadanshi. Tsaki ya ɗan ja tare da cewa. "To wannan ƙus-ƙus du na menene, ku duk abinda babu kyau kuna jin daɗin yinshi." Shiru yayi ganin motoci sama da talatin ne suka shigo Rugar. Kana duk manyan mutanene kuma sun fito cikin motocin sun nufo inda suke zazzaune. Wanda tuni Arɗo Bani yasa an kuma firfito da taburman cikin masallacin su. Kana yasa an fito da sauran dardumai da kilisai anzo an shimfiɗa. Suna isowa sarki Jalaluddin da Abba suka dafa kafaɗun Jabeer tare da sanya mushi al'barka kana suka zauna gefenshi ya zama sun sakashi a tsakiya. Kusa dashi Abbanshi ya zauna, Kana Jalaluddin ya zauna kusa da Abban. Lamiɗo kuwa na kusa dashi shida Galadima. Da sauri Haroon dasu Jamil kan sukabi bayan fadawan da suka nufi motocin da sukazo yanzu da ido. Shi kuwa Sheykh Jabeer ido kawai ya zubawa wayarshi. Yana wasu aiyukanshi a ciki. A hankali ya ɗago kanshi ya kalli Haroon dake taɓashi. Da yatsa Haroon ya nuna mishi gabanshi. A hankali ya juya kanshi ya kalli inda Haroon ke nuna mishi. Fadawane da hadimansu keta jido katon-katon ɗin sweet ga kuma fufun goro shima sunata jidowa suna ajiyewa a gabansu Arɗo Bani. Cikin mamaki ya kalli Lamiɗo tare da cewa. "Me za'ayi da wannan kuma? Kamar wanda suka zo ɗaurin aure!". Da sauri Galadima yace. "Eh ashe ka gane ai ɗaurkin auren ne". Cikin mamaki Haroon yace. "Aure kuma? To auren waye?". Lamiɗo ne ya kalleshi cikin isa yace. "Auren Muhammad Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa!". Wani irin yunƙura Jabeer yayi zai miƙe, cikin tsananin haɗe fuskarnan tamkar zatayi aman jini ya kalli Lamiɗo tare da yunƙurin miƙewa yace. "Zancen banza kenan a wurin banza, ai wlh baka isaba, wlh Lamiɗo kafa kiyayeni kanafa shigemin rayuwa, ka fita hanyata ka fice min a ido kar in rintsa da kai fa kadafa ka bari in juyo kanka". Ya ƙarishe mgnar da miƙewa tsaye. Sai kuma ya juyo jin an kamo hannunshi an medashi zaune, a fusace ya kalli inda yaji anja hannun nashi ganin Sarki Jalaluddin ne ya riƙo hannunshi ya sashi kuma tsuke fuskarsa cikin faɗa yace. "Jadda sakarmin hannu bana so! Bana son abinda kuke min da rayuwata, wlh gwarama kun tashi mun tafi, dan babu ruwana dan Ni bazanyi aure ba". Da sauri ya juyo jin muryar Abbanshi yana cewa. "...! Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276, sai in saki cikin Normal group wanda a kwana talatin za'a gama littafin. Ko kuma kiyi min TRANSFER ɗin dubu ɗaya ta asusuna na Jaiz 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276. Sai in saki a Special Group inda cikin mako biyu kacal za'a gama Part 1 da izinin ubangiji. By *GARKUWAR FULANI* Wata iriyar zuface ke tsastsafo mishi bisa goshinsa, Kamar an watsa mishi ruwa. Ya kamo lip ɗin shi na ƙasa yana taunewa. Hannunshi dake cikin blanket ta zubawa ido. Dan son gano abinda yakeyi, shiru tayi sawon 5 minute kana, a hankali ta ɗaura tafin hannunta kan goshinta, tare goge mishi zufar, daketa tsastsafowa duk da sanyin A/C dake ratsa ɗakin. Idonshi ya saisaita lumshe su da yayi, ya sani Umaymah ce. sabida babu mai shigar masa ɗaki kai tsaye sai ita. Babu kuma mai taɓa mishi goshi haka sai ita. Cikin kula tace. "Jazlaan!". A hankali ya gama buɗe idanunshi da sukayi jazir alamun tarin ƙuna da yakeji a ransa. A hankali tace. "Jazlaan!." Ta kuma kiranshi a karo na biyu. A hankali ya motsa lips ɗin shi alamun zai amsa mata. Amman Ina zafin da zuciyarshi keyi ya danne harshensa hafimtar hakane yasata, nuna damuwarta a hankali tace. "Kaci abinci?". Ƙarya ba ɗabi'arsa bace ba kuma halittarsa bace, duk ɗacin gsky zai faɗeta, bare a kan kashi. Kanshi ya girgiza alamun baiciba. Cikin sanyi tace. "To Muje kaci koda abu mara nauyi ne!." Da ƙarfin ya fizgo mgnar. "Bazan ci ba". Ta sani yadda yayi mgnar, ta kubce masane, dan in ransa a ɓace yake baya mgna, ɓacin ran mai limini kenan babu faɗe-faɗe bare hargowa ko buge-buge. Sanin ko ya zatayi bazai cin bane, kamar yadda ya faɗa mata yasa, ta miƙe a hankali kanshi ta shafa tare da cewa. "Saida safe". Kai kawai ya iya gyaɗa mata, Haka ta fara tafiya, tana kallon yadda yake motsa hannunshi cikin blanket tabbacin. Wani abun yake yagewa. Yadda ta bar Haroon haka ta sameshi saida safe tayi mishi kana ta wuce ta tafi. A can Rugar Bani kuwa. Kamar yadda Ba'ana ya ɗaukarwa kanshi al'ƙawari haka ya bar ƙasar ya nufi ƙasar Cameroon Kai tsaye Yahunde ya nufa, cikin rugagen Fulani, yana tafiyarne da ɗan sauran tsafi da sihirin dake jikinsa. A haka ya nausa cikin ƙasar Cameroon da yake jihar Ɓadamaya tana bakin bodar ƙasar ne. Fulanin Rugar Bani kuwa, a daren wannan ranar sukayi gangamin ramuwa, suka faɗawa ƙauyukan kafuran ƙabilun ɓacamawa dake cikin Shikan da kewayenta. Allah ya basu nasarar yaƙan kafuran nan. Har suka samu damar ƙona ƙauyem Bonon wanda shine zuciyar ƙabilar ɓachama, kamar yadda Abuja take zuciyar Nigeria. Cikin daren suka ƙona ƙauye dama dodon tsafinsu Bonon da suka ɗauka a matsayin Ubangiji su sun ƙonashi sun ɓadda shi a doron duniya sai dai tarihinsa. Wannan labarin shine labarin. Da gidajen rediyo dana tv da jaridu sukayi. Breakfast dashi yayinda akayita kuzuzuta cewar Fulani sun zama ƴan ta'adda sun farma garuwa da yaƙi. Uhummm wannan shine halin da Fulani ke rayuwa a ciki. A zalimcesu, kaji cib duniya babu mai yin mgn su kai ƙorafinsu a koresu. Gwamnatin kasar data jiha suyi kamar basujiba. In fulanin sun rama na lokaci ɗaya sai asa musu sunan ƴan ta'adda ko yan tada zaune tsaye, har ana ikirarin korarmu.😭😭😭 Hankalin ƙabilun Ɓacamawa dake cikin Shikan duk suka ari ta kare. Hausawa da Fulani kuwa kowa ya koma, cikin gidansa. Domin Allah ne yabi kadunsu. Sarkin Shikan da kanshi yayi masifar girgiza da yawan da Fulani sukayi cikin garinshi da kewaye. Gashi an ƙone dodon tsafinsu nasu kuma babu abinda ya samu fulanin. Hakane yasa shi kanshi ya arce, sai abu ya lafa ya dawo. Su kuwa Fulani bayan sun gama. Suka tsaya suka bawa yaransu da tsoffinsu mafaka, domin su basu kashe yara da tsoffi da mataba. Anyi an gama, kafin hukuma tazo, ta ƙara sai saita Komai. A cikin masarautar Joɗa kuwa. Washe gari da safe. Lbrin ya rinski Sarki Nuruddeen, shine ya bada umarnin kada a kama bafulatani ko ɗaya. Aysha ce zaune gaban Umaymah Aunty Juwairiyya na gefenta ita da Hibba, cikin kula Umaymah tace. "Yauwa Aysha kinga wannan ki ɗauke ta matsayin yayarki ita ɗin yar babban Yayanmu ne wanda na nuna miki jiya. Mijinta kuma ya'yan Jabeer ne, Side ɗinta na kusa da naku. In kinga duk wani abun da baki fahimta ba ki tambayeta, in kin gaji da zaman kaɗaici zaki iya shiga wurinta, da wurin Mamanku, da kuma nan wurin Gimbiya Aminatu". A hankali ta ɗan kalli Aunty Juwairiyya, tare da cewa. "Ina kwana Aunty". Cikin jin daɗi Aunty Juwairiyya tace. "Lfy lau ya baƙunta". A hankali tace. "Alhamdulillah!".Hibba ce ta ɗan tsuke baki cikin sanyi tace. "Shike nan ai, an gabatar mata da kowa sai ni aka ware". Murmushi Aunty Juwairiyya tayi tare da cewa. "To Aysha ga Hibba wutar Umaymah, duk family itace auta a jikokin Sitti na nan ƙasar". Murmushi ta ɗan yi sabida ganin yadda Hibba tayi sai Junainah ta faɗo mata a rai. Ita kuwa Hibba motsata tayi tare da cewa. "My happiness". Cikin murmushi Aysha ta nuna kanta, alamun "Nice my happiness?". Murmushi Hibba tayi tare da cewa. "Yes haka Umaymah tace wai kece farin cikin ahlimu da izinin ubangiji". Murmushi tayi tare da sunkuyar da kanta. Haka nan taji tana jin sonsu a ranta, Especially Umaymah da Hibba. Aunty Juwairiyya kuwa da Ummi breakfast Suka gabatar mata, kana suka fita. Umaymah da kantane ta haɗa mata tea mai kauri ita da Hibba kana ta zuba musu abincin da Aunty Juwairiyya ta kawo musu tare da cewa. "Bismillah kuci abinci". tana faɗin haka ta miƙa ta fita, Ita kuwa Hibba da tsauri ta gyara zamanta tare da ɗaukan Fork ta matso gaban plate ɗin da aka zuba mata soyyyan dankali da kwai, hannun tasa ta soki guda biyu tare da ɗagowa zata kai bakinta, sai kuma ta tsaya tare da zubawa Aysha ido ganin ta riƙe mata hannunta. Cikin sanyi da ɗan sakin jiki da Hibba ta girgiza mata kai tare da cewa. "Kada kici wannan abincin". Cikin juya ido Hibba tace. "Meyasa!?". Kai ta jujjuya mata kana ta gyara zamanta, tare da ɗan kallon ƙofar shigowa ta gefen idonta. Wani kekyawan Foodflaks da aka kawo daga sashin Gimbiya Saudatu ta jawo tare da cewa. "Ki ɗiba a nan kici". Cikin mamaki. Hibba tace. "Aunty Aysha, ai Bama cin abincin gidan Gimbiya Saudatu, kuma naga Hadimanta ne suka kawoshi". Cikin rashin gane manufar zancen Hibba tace. "Meyasa bakwa ci?". Juyawa Hibba tayi ta kalli bayanta kana ta juyo ta kalleta da kyau kana a hankali tace. "Bata son Hamma Jabeer dama duk ƴan uwanshi, cewa take zata kasheshi in ta samu dama, shiyasa Umaymah take hanamu cin abinci ta". Wani irin nannauyan ajiyan zuciya ta sauƙe tare da kallon Hibba cikin cushewar tunani ta kalli jerin kulolin da a ƙalla sun kusa takwas a gabansu. Cikin sanyi tace. "Buɗe su mu gani". Jin hakane yasa Hibba buɗe su ɗaya bayan ɗaya. ita kuwa ido take zubawa duk kular da Hibba ta buɗe. Kular ƙarshe wacce ke ɗauke da Chicken Ball's mai zafi sai turiri yakeyi da ƙamshi. ta nunawa Hibba tare da cewa. "Kici wannan". Murmushi Hibba tayi kana tace. "Yauwa shinema na Gimbiya Aminatu kuma ta iya girki tsohuwar hakana hadimanta, a plate ta zu musu. Kana suka faraci suna ɗan korawa da ruwan tea mai zafi da kauri. Sunaci Hibba nata janta da hira duk da ita Aysha zuciyarta a cushe yake. Bayan sun gamane, Hadiman Gimbiya Aminatu suka shigo suka tattare komai suka gyara wurin bisa umarni Jakadiya. Ganin Aysha ta ɗan saki jiki da Hibba ne yasa, Umaymah ta wuce Side ɗinsa ita da Umminshi. A falo suka samu Jafar, Jalal, Jamil, Haroon. Suna bisa kujerun Dinning area, Aunty Juwairiyya tana zuzzuba musu abincin. Murmushi Umaymah tayi cikin jin daɗin ganin su, da wal-wala hatta Jalal fuskarshi a sake take. Jamil ne ya kalleta lokacin data ƙara so kusa dasu, cikin murmushi yace. "Umaymah mu sai yaushe za'a nuna mana Amaryar a gabatar mata damu, ta sanmu da kyau". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Ai ku tun daren jiya nagabatar da sunayenku da matsayinku gareta". Haroon ne ya ɗan kurɓi tea tare da cewa. "Yo ai Ni dai ba sai an gabatar daniba, domin nasanta tun safiyar jiya kafinma a ɗaura auren ko Jalal?". Taɓe baki Jalal yayi tare da cewa. "To ni mamaki nakeyi, ko dai dama ita tazone dan taga wanda za'a aura mata". Umaymah ce ta ɗan zauna kusa da Jafar tare da kallonsu kana tace. "Babu sam ita kanta bata saniba bata zata ba bata tsammaci aurenta a jiyaba. Sai dai arashi kukayi, Ni tun jiya da kuka gayamin nasan arashi ne kawai ya haɗaku a asibitin. Bata san komaiba akan auren nan hakama iyayenta, basu da zaɓine kawai dan sun san ƙa'idar gasar Shaɗi ne hakan yasa sukayi haƙuri." Kai Jalal ya jinjina tare da cewa. "Uhummm mu dai yanzu yan kallone. Dan na sani tabbas yanzu za'a fara buga Game ɗin yanzu wasan zai soma". Cikin yin ƙasa da murya Jamil yace. "Sosai ma, dan kuwa akwai kitimurmurar da za'ayi a masarautar Joɗa, wannan Ustaz Sheykh Malam akarmakallahu Hamma Jabeer ɗin, salonshi na dabanne a dukkan lamuran yauda kullum wannan auren dai zamuga ya zai kasance!". Ya ƙarishe mgnar da yin ƙasa da murya sosai, yanayi kuma yana kallon hanyar falon Sheykh Jabeer. Cikin haɗe fuska na wasa Umaymah tace. "Al'khairi shine zai wanzu". Murmushi Haroon yayi tare da cewa. "Inafa al'khairi a wannan abun da bashi da tushe, ni kaina naji baƙin cikin wannan al'amari, auren Muhammad Jabeer ya zama kamar a munafuce a ɓoye babu wani shiri bare kimtsi kun bari an auro mishi mace kamar auren ƴar tsana". Jafar kam abincinsa yakeci, ba tare da ya kulasuba. Jamil kuwa sai murmushi yakeyi. Jalal kuwa shiru yayi alamun nazari. Ummi kuwa ware wasu kyawawan Foodflaks takeyi gefe. Tare da abinci a cikinsu. Bayan ta gamane ta ajiyesu gefe. Tare da cewa Umaymah. "Ga breakfast ɗin Sheykh". Kai Umaymah ta gyaɗa mata. Nan sukaci gaba da hira. A can Side ɗin Mama kuwa, Tunda batun auren Jabeer ya basu ya riski kunnuwan ahlin masarautar Joɗa, kowa da abinda ke ransa. Batool kuwa hankalin Mama in yayi dubu ya tashi, bisa irin kukan da Batool ketayi har cewa takeyi ta gane ai dama Mama bata son ya aureta. Da kyar ta samu tasha kanta, Gimbiya Saudatu kuwa, da Baba Nasiru da Baba Basiru da Laminu. Zaman gaggawa suka tanada. Suna tattauwana wannan baƙin lbrin da bai musu daɗi ba. Zaune yake gaban wani ƙasurƙumin boka matsafi. Cikin tsantsar tashin hankali da kiɗima yace. "Boka Tsitaka haka mukayi da kai? Yaushe ka fara min ƙarya kan aiyukan da nake baka? Ya za'ayi kwatsam rana tsaka ace wannan shegen yaron da nakeji tamkar in kasheshi yayi aure? Da kai mukayi mgna a nan tsawon shekaru kace min ka, kashe min wutsiyar ɗan iska mai jajayen kunnuwa, babushi ba mace har yaumal ta ƙunun nadi. Ka bani tabbacin. Har gobe sihirin na bibiyarshi, kace min duk sanda zanen kan macijin ya isa kan tsaitin ƙahon zuciyarshi zai mutu kowama ya huta. Sai kuma jiya kamar sauƙan aradu ace yayi aure!". Wata iriyar razanenniyar dariya mara daɗin amo boka Tsitaka ya kece da ita, wanda har saida tsaunuka da kwazazzaban dake wurin suka amsa amonta. Dariyar mugunta yakeyi babu ƙaƙƙautawa, har saida baƙon nashi ya fara hatsala cikin tashin hankali yace. "Wannan ai insakanci ne, in bazaka iyaba ina nemo wasu matsafan. Ya zan zo da matsalata da sanyin safiyar nan kai kuma ka kama min dariya, Ni mahaukacin gidanku ne?". Cikin dariyar boka Tsitaka yace. "To ai tashin hankali na banzane, kana kokonto kan aikin da shekaru goma sha biyu yana cinsa yana bin jikinshi. Kana zaton ya karye ne? To bari kaji wannan sihiri yana nan a jikinshi, har kwanan gobe wutsiyarsa bata harbawa, baya jin kanshi a namiji. Ba kuma zaiji yadda maza kejiba har abadan. Iya bincikena banga mai mgnin da zai gani aikin da mukayi mushiba. Auren da akayi mishi, da ya sani tabbas da zai watsa abun. In kuwa kana zaton sihirin yana sauƙa kaje ka dubu, zanen bindin maciciyar da yake tun daga kan ƴar babbar ƴatsar ƙafarshi ta dama, zaka samu kan macijiyar ya ƙetare ƙugunshi. Na kuma gaya maka duk sanda kan macijiyar ya isa kan ƙirjinshi, saman nononshi, zai mutu, kuma yadda zai bar duniya haka ƙannenshi da wanshi zasubar masarautar Joɗa har abada yadda ba'a tambayi yaushe matacce zai dawo duniyaba haka suma baza'a tambaya ba." Cikin ɗan jin daɗi baƙon bokan yace. "To ai dole hankalina ya tashi, kaida kace min bazai wuce shekaru biyar ba zai rasu gashi yanzu shekaru goma sha biyu bai mutuba". Cikin zare ido boka Tsitaka yace. "Kai ai mun ma yi dacen yin asirin da wurine, tun kafin ya gama girma da yanzune sam bazai kamashiba, mutumin da baya rabuwa da sunan Allah a bakinshi. Yaronda ko yaushe da al'wala yake zama, ai badan hakaba da tuni mun hallakashi". Cikin ɗan samun nitsuwa baƙon ya direwa Boka Tsitaka kuɗi kana ya miƙa ya fice. A can wurinsu Umaymah kuwa. Suna cikin hira, Umaymah ta ɗan juyo a hankali ta kalli hanyar fitowa falon Sheykh Jabeer, sabida jin ƙamshin turaren shi. Murmushi mai cike da jin daɗi tayi ganinsa cikin shiga ta al'farma, kamar yadda ya saba. Wata jallabiya blue color ce mai taushi a jikinshi. Sai al'kyabbar da ya ɗauka samanta shi kuma peach brawn mai ɗan karen kyau sai sheƙi yakeyi, kana sai hira minshi shima Peach brown da ɗigo-ɗigon white. Sai takalmansa sau ciki masu kyau, baƙaƙe kana sai ɗan abun saman hiramin shima baƙi. Taku yakeyi cikin nitsuwa da haiba da kamala, fuskarshi cike da kwarjini da ƙasaita. Hannunshi na riƙe da Tab ɗinshi. Idonshi na kanta yana sarrafata da hannun damanshi yayinda hagunshi ke riƙe da ita. Sai wani irin ƙamshi yake bazawa a duk inda ya wulga. A hankali yake taku amman da alamun sauri yakeyi. A tsakiyar falon ya tsaya, tare da kallon inda suke zaune. Ganin Umaymah ta nufoshi ne yasashi gyara tsayuwarshi. Tare da ɗan kallon ta, kana yana mai amsa gaisuwar su. Jalal da Jamil. Tana isowa inda yake ya ɗan kalleta, cikin yanayin rauninshi dake baiyana in yana gabata, a hankali yace. "Umaymah ina kwana". Cikin kula tace. "Lfy lau Alhamdulillah Jazlaan ya gajiya da jikin!". A taƙaice yace. "Alhamdulillah". Sai kuma ya ɗan juya yayi taku uku zuwa biyar ya isa Dinning area, kana Umaymah na biye dashi. Dafa kujerar da ya Jafar yake a kanshi yayi tare da sunkuyowa ya kalli fuskarshi da kyau, sai kuma ya ɗan kalli Aunty Juwairiyya cikin kauda kanshi a kanta yace. "Ya jikin nashi?". Cikin sanyi tace. "Alhamdulillah jiki kam da sauƙi sosai, dan tunda ka dawo zaiyi baccinsa lfy ba tashin hankali in lokacin tashinsa yayi kuwa ba hargowa zai tashi yayi al'wala yayi ta nafilfilinshi". Cikin yanayin jin daɗin zance yace. "Alhamdulillah. In sha Allah komai zai dai-dai-ta domin babu cutar da bata da waraka sai dai ina ba'a gano mgninshi ba". Hannunshi ya gyara da kyau yadda Jafar zaiji daɗin riƙon da yayi mishi. Umaymah kuwa cikin daƙile fuska tace. "Zauna kaci abinci". Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta, cikin tonƙoshe kai bisa kafaɗunshi ya ɗan taɓe baki kana a hankali yace. "Sai na dawo". Shiru tayi sabida ta lura sauri yakeyi. Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Jakadiya cikin sanyi yace. "Ummi lfy kuwa na ganki haka ba walwala". Nisawa tayi tare da cewa. "Ina fa zanyi wal-wala bayan Sheykh na cikin yanayin fushi, da rashin jin daɗi alamun na gaza riƙe amanar da uwar ɗakina ta danƙamin kenan". Wani ɗan guntun tsaki yaja tare da kallonta da kyau cikin sanyi yace. "Ba komai Ummi kin riƙe duk amanar da aka baki, ba matsalar komai fa". Cikin ɗan sakin fuska tace. "To Alhamdulillah, yanzu ina zuwa?". Bayan Jalal ya ɗan matso tare da cewa. "Vallai zan je inada zama na musamman da sauran likitocin, domin jaddada musu kula da marasa lfyan da aka kai jiya". Kusan a tare sukace to Allah ya taimaka". Amin yace a taƙaice kana ya tsare Jalal da ido cikin tuhuma yace. "Jamil jiya ina ka kwana?." Cikin mamakin ya akayi Hammanshi ya gane bai kwana a gidaba ya ɗan sunkuyar da kanshi cikin sanyi yace. "Club naje to bamu taso da wuriba ne, sai na biya gidansu a bokina Hayatuddeen na kwana a can". A hankali yasa hannunshin ya kamo kunnenshi tare da matseshi da yatsu sa biyu. Da ƙarfi Jamil ya saki ƙara tare da cewa. "Wayyo Hamma Jabeer bazan sakeba, na tuba". Bai sakeba sai ma kauda kanshi da yayi yana kallon Umaymah cikin rauni yace. "Kinji ba, shi kullum yana Club music sai kace ɗan ma kaɗa ko maroƙa, yaje ya kwana cikin yan iska azo ayi ta musu video ana yaɗawa duniya, ana liƙa sunana a ƙarshen sunayensu a social media kamar nine uban daya haifesu. Haka kenan zanyi ta fuskar ƙalubale ina rasa yadda zan karesu ko in zagesu." Ya ƙarishe mgnar rai a ɓace. Ita kuwa Umaymah faɗa ta fara yiwa Jamil. Shi kuwa gaban Jalal ya tsaya tare da kafeshi da ido. Cikin tura baki Jalal ya fara bayani ba tare da an tambayeshi ba yace. "Shiya shiga sabgata Ni kuma na dakeshi". Cikin nuna ɓacin rai yace. "Da yake kaine sarkin duka, ko kunyan Baba Kamal bakaji ba, ka kama Salis da duka kawai dan ka wuce da MP kana danna waƙe-waƙe da suɓale wonɗo shine tsokanar?". Cikin yin ƙasa da kai yace. "To ai zaginka yayi wai ilimi ka na banza tunda gamu a lalace bakayi mana wa'azi mun shiryuba, shiyasa Ni kuma na mishi aikin wanda ba shiryayyu ba". Kwaffa yayi tare da cewa. "Zagi kuma na nawa? Ba kune ke jazamin zaginba, kada ka yarda in sake jin ka taɓa shi Uhummm!". Ya ƙarishe mgnar da kwaffa. A hankali Jalal yace. "Kayi haƙuri in sha Allah bazan sakeba". Nan duk suka nufo cikin falon. Suna isowa Hajia Mama na shigowa Batool na biye da ita a gefe. Jafar kuwa da sauri ya koma bayan Sheykh tare da riƙe hannunshi ya fara ja alamun su tafi. Shi kuwa Sheykh ƙara tsuke fuskarsa yayi ganin Batool cikin sauri ya gaida Mama, ta amsa fuska a sake tare da sanya masa al'barka. Kana ya nufi hanyar fita, da sauri Jafar yabi bayanshi. Umaymah kuwa da Ummi da Juwairiyya da Batool nan suka zauna suna ɗan hirarsu. Jalal kuwa da Jamil a tare suka fita, shi kuwa Haroon falon Jabeer ya koma. Yana shiga ya kira Jannart bayan sun gaisa take tambayarshi yaushe zai je masarautarsu nan yake ce mata. Yana nan tafe a satin nan. Shi kuwa Sheykh Jabeer yana fita kai tsaye Valli Hospital ya nufa. Asibitinshi mai zaman kanshi. Asibitin da duk nahiyar Ɓadamaya babu kamarshi. Asibitin da in kana cikinsa zakayi zaton a ƙasashen turawa kake. Haka lamarin yaci gaba da tafiya. Babu mai yiwa Sheykh Jabeer batun Aysha. Itama Aysha gani take kamar ziyara tazo ba aureba. Tunda ita dai da idonta bata taɓa ganin mijinba, sai dai taji sunanshi. Sosai ta shaƙu da Hibba da Umaymah, hakama Gimbiya Aminatu da Ummi. Lokuta da dama takan shiga Bathroom tai ta kuka sabida begen ƴan uwanta. Yau kwananta uku cur a gidan. Idonta ma baiga ranaba. Umaymah kuwa a sashin Jabeer yana fita. Wata tirela ta iso har bakin Side ɗin shi. Nan aka fara sauƙo da kayayyakin ɗaki na amare. Ana shigarwa ciki. Kana masu aiki na ɗaure komai suna kimtsashi. Sai kusan la'asar suka gama komai kafin. Suka tafi kana su Umaymah suka taho. Suna shiga asalin babban falon, Aunty Juwairiyya da Hibba suka haɗa baki wurin cewa. "Wow masha Allah, Kai Umaymah ƙara so da sauri kiga falon nan yadda ya zama fadar masarauta". Da sauri Umaymah da Ummi suka ƙara so. Masha Allah! Masha Allah!! Masha Allah!!! Shine abinda kawai Umaymah keta mai-mai tawa, sabida kyau da tsaruwan falon yayi masifar kyau. Kasan cewar falon irin ƙaton nanne mai faɗi da tsawo. Wasu irin kujeru ne Daimond set masu masifar kyau da tsada, a shirya a cikin tamfatsen falon.masu Golding color mai ɗan karen sheƙi sai surkin Brown color mai sheƙin gaske da ratsin ruwan madara.. Kana haka ma kalan labuyen falon masu tsawo da faɗi da taushin gaske.sai wani table na glass mai Golding color da aka ajiye a tsakiyar falon bisa wani tattausan carpet mai azabar kyau. Sai wani babban Tv dake liƙe a jikin bongon, kana gefen dama kuwa wani babban majigine manne wanda yake baiyana rubutun Kur'ani reras daki daki. Can gefen kuwa steps ɗin hawa Dinning area ne, wanda aka canza Dinning table and chairs ɗin, Aka zuba wasu masu masifar kyau da tsadan gaske. Ba'a wani cika falon da tarkace ba, amman yayi matuƙar kyau. Tafiya kaɗan zakayi ta gefen hakun zaka ratsa cikin wani madaidaicin falo. Yayinda na Jabeer yake hannun dama. falon ɗakin da Umaymah ke tsauƙa in tazo kenan. 2 bedroom ne wannan falon yake dashi ko wanne da bathroom a ciki. Kana sai Dinning area matsakaici daga nan gefen Dinning area kuma akwai ɗan ƙaramin corridor wanda zai sadaka da kitchen da store. wasu irin datsa-datsan kujeru masu masifar kyau da ɗaukar hankali aka kimtsa a falon wanda komai na ciki. Peach and white coffee ne mai ɗan karen kyau. Hakama Dinning table and chairs ɗin. Still labulayen ma hakane. Sai kuma cikin bedroom ɗin wanda duk girmansu ɗaya, haka yasa aka shirya wasu tagwayen gadaje masu masifar kyau suma Golding color ne mai sheƙi da ɗaukar ido. Saɓanin side ɗin Jabeer komai Sky blue and white ne, wanda hakan yasa kana shiga sashinsa sai kayi zaton a sararin samaniya kake rayuwa. Komai yayi kyau. Especially kitchen ɗin dake matsakaicin falon. Domin wancan kitchen ɗin dake babban falon ba'a taɓa shi ba, hakama Side ɗin Sheykh. Sai kuma sama wanda shi a rufe yakema, sam babu kowa a ciki. Sosai fa su Umaymah suka yaba da kyan shirin da akayiwa wurin. Nan suka zauna a falon. Umaymah ce ta kalli Jakadiya cikin sauƙe numfashin tace. "Alhamdulillah, gobe kuma zakiyi musu jagora shida matarshi su zaga ta gaida ahlin masarautar Joɗa, ta gansu su ganta su san juna, gudun kada a haɗu a wani wurin ba'a san junaba". Wani gwauron numfashin Ummi ta sauke tare da cewa. "A nan gizo ke tsakar ko ta ya zamu samu, Sheykh yayi wannan al'adar yadda ya dace ake kuma yinta, kinsanshi mutunne mai kunya, koda yana son abunma bare ba wani son abun yakeyi ba". Cikin yarda da kai Umaymah tace. "Kada ki damu yana ɗaya daga cikin dalilin da yasani, na zauna sai naga kamun ludeyin zaman nasu." Haka dai suketa tattaunawa, Suna nan zaune Gimbiya Saudatu ta shigo tare da hadimanta, kana da Laminu da Baba Basiru da Baba Nasiru. Cikin isa da ƙasaita ta nufi kujerar da duk canjin da akayiwa falon ba'a canzashi ba sabida kujerace ta masarautar Jalaluddin, cikin isa take taku yayinda ta bawa ƙofar shiga baya. Cikin gatsali ta kalli Umaymah data tsareta da ido. Kallon uku saura tayi mata kana tace. "Duk mutun muna fuki abin tsorone. Amman munafurcin balaraben Mutun yafi na kowa muni da bada tsoro. In banda salon munafurci ayi aure yau kwana uku a gaza fito da amarya a nunata ga mutanen masarauta, bare a fanshi idonta." Ta ƙarishe mgnar tana kai mazaunanta bisa, Kujerar. Sai kuma tayi maza ta miƙa, jin muryar Jabeer da yanzu ya shigo, ko mgnar ta, ta ƙarshe baijiba. Cikin isa da ƙasaita da rashin tsoronta, da kuma tsare fuska alamun Ni bani da lokacin ki, kuma ni ba sa'an yinki bane ya nuna mata hanyar fita da yatsarshi tare da yamutsa fuska cike da ƙarfin zuciya ya kalleta ita da ƙannen Mahaifin nashi yace. "Fice min daga gida, bacci na dawo zanyi so banda lokacin jin ihunku na kar...! By *GARKUWAR FULANI* "Muhammad!". Ya kira babban sunanshi tare da jawo hannunshi, ya zaunar dashi bisa kujerar da ya tashi a kai. Cikin wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da tsoron abinda suke shirin aikatawa, ya kalli Mahaifin nashi, kana ya juyo ya kalli Lamiɗo da Galadima gefen damanshi ya juyo ya kalli Jadda cikin rauni ya kuma kalli mahaifin nashi tare dayin ƙasa da murya yace. "Abba kada ka bari su ɗaura auren nan, dan Allah kace musu su bari, kada su ɗaura". Ya ƙarishe mgnar cikin tashin hankali da ɓacin rai da tarin rauni a fuskarshi. Cikin zuba mishi ido Abbanshi yace. "Meyasa? Sabida me za'a bari!? Meyasa baka so!?." Kanshi ya jujjuya tare da haɗe hannayenshi wuri ɗaya ya fuskanci mahaifin nashi cikin sanyi yace. "Ni dai bana so. Abba dan Allah kada ka bari suyi. Bana son garin nan bare mutanen cikinsa, kuma bawai haka banza naƙi auren nan ba, Abba inada matsala, Please Abba na tuba dan Allah kace su bari. In yaso a ɗaura da wani amman banda ni kam". Lamiɗo ne ya kamo hannunshi cikin isa yace. "Auren' nanfa, kamar ma an ɗaurashi an gama, domin babu wani abu ko wani mahaluƙin da ya isa ya hana wannan ɗaurin auren, gwarama ka kontar da hankalinka. Tunda ka iya jure bulalin aiko tabbas dole ka aureta, babu shakka dole sai ka aureta, bazai yiwu a dakeka a kantaba sannan ka barmusu itaba." Cikin jin haushin wannan fitinenne tsohon ya kwace hannunshi daya riƙe tare da cewa. "Haka kenan kullum zanyi ta wahala a bisa wasu dalilanka da bana addiniba, me ruwanka da dukan da akayi min, ba dai kai-kasa dole aka dakeni ba". A hankali Galadima yace. "Eh da kuma bakayi kukaba, baka guduba, yau kuma kasa yayi kuka ya gudu ai dole ka aure matar da a kanta aka haɗaku gasar, tunda mu dai ba sakarkaru bane, bare ace bamu san dokar gasar Shaɗi ba." Wayyo Jabeer ji yakeyi tamkar ya mammake tsoffin nan dan tarin baƙin ciki. Rai a ɓace yace. "Bakufa fini sanin kainaba, tunda nace muku bana son aure, bazan kuma yi aureba, to ku barni mana, rayuwata ce ko taku, ko dole ne duk wata matsalata da sirrin rayuwata sai kun sani! Nace muku bana son wannan garin na tsani garin bana son mutanen garin karankatab ɗinsu. Bani babu su, in kuma kukayi gangancin cusa min wata muguwar yarsu, tabbas! lallai ilaihin! A kanta zan rama sauran bulali ashirin da wancan ƙaton gardin ya min, hamsin, ni a talatin ya gudu". Kai Jadda ya girgiza tare da cewa. "Ka rama mana kaida matarka, ka rama ka kuma jinyace ta". Shiru sukayi sabida jin muryar Dr Aliyu da kuma Galadima da Arɗo Bani da Bappa suna tabbar wa juna lfyar yaransu, cikin Mamaki ya kalli Galadima dake cewa. "Muma ɗanmu lfyarshi lau, Namiji ne". Cikin sanyi Jabeer yace. "Ji maƙaryacin tsoho, wai lafiyata lau, ko yaushe ya zama likita ya gwadani. Harda wani karkacewa yana zuba ƙarya ko farin gemunshi bai martaba-ba". Jin Abbanshi ya daki gefen ƙafarshi ne yasashi yin shiru. A nan a gabanshi a gaban mahaifinshi. A gaban dubban al'ummar fulani makiyaya daketa tsastsafo tako wani sashi na duniya, a kuma gaban Lamiɗo da tawagarsa hakama Jalaluddin da tawagarsa. Aka ɗaura auren Muhammad Jabeer da Aysha. Bisa koyarwan addinin Musulunci. Sosai su Jalal, Jamil, Hashim, Haroon, Sulaiman. Sukayi mamakin wannan aure na ba zata. Ba zato ba tsammani. Bayan an gama dai-dai-ta komai an ɗaura auren ne, kuma. Lamiɗo ya kalli Arɗo Bani, cikin girma da ƙasaita yace. "Yanzu zai tafi da matarshi." Cikin sanyi da al'hini Bappa yace. "Allah rene yanzu kuma!?". Galadima ne ya amshi zancen da cewa. "Haƙƙun yanzu zamu tafi da ita!". Arɗo Bani ne yayi murmushi mai cike da jin daɗin yace. "To ba laifi ai, muje a fito muku da ita". Shi kuwa Bappa ido ya zuba musu. Dan shi a zatonshi ba yau zasu tafin mishi da Shatunsa ba. Nan duk suka ɗunguzuma, suka shiga motocin. suka nufi ƙofar gidansu Shatu. Ya Salmanu kuwa, tuni ya shiga cikin gidan su. Ya shiga ɗakinshi yana ta kuka kamar yaro. Bai tsamci haka abin kan iya juyewa ba, Ba'ana ya rasa Shatu shima ya rasata. Suna isa ƙofar gidansu, duk motocin suka tsaya. A hankali Bappa da Arɗo Bani suka kutsa kansu cikin gidan. A tsakar gidan suka samu. Shatu na zaune dan dawowarta kenan, hannunta tasa ta tallabe haɓarta ta zubawa su Junainah ido, shigowarta gida kenan daga dawowarta. Cikin Ɓadamaya su Binto suka shigo gidan a guje suna ce mata wai an ɗaura aurenta da ɗan sarkin da akayi gasar Shaɗi dashi. Jin hakane yasata yin murmushi tare sauƙe dogon ajiyan zuciya na gajiyar tafiyar da tayi, ido ta lumshe tare da cewa. "Auren kuma wasane, da zai zama an aura min wani wanda ba'a san halinshi ba, ko ƴar tsana ma ai ba'a aurar da ita a hakaba bare ni". Ta faɗi mgnar cikin fargaban ganin yadda suketa rantse mata. Duk da bawai ta yarda da zancensu bane. Junainah kuwa dariya takeyi tare da ɗan tsalle-tsallenta tana cewa. "Yeeh Auren Addana yazo, zanyi gayyan fati muyi gaɗa". Cikin zuba musu ido, ta zauna gefen, Ummey dake ta Binta da ido, cikin sanyi tace. "Ummey na dawo! Ya jikin naki!?." Da sauri ta gyara zamanta tare da zubawa Ummey ido, cikin mamaki take kallonta ganin idanunta nata zubda hawaye ne, yasata cikin ruɗani da tashin hankali da fargabar abinda ke shirin faruwa da ita da rayuwarta. A kiɗime tace. "Ummey meya sameki? meya saki kuka? Jikin ne yake miki ciwo?." Sam Ummey bata iya mgna ba, sai kukan da takeyi, hakanne yasa zuciyar Shatu karaya, cikin rauni wasu hawaye masu ɗumi suka fara tsiyayo mata. Hakan ya ƙara ingiza kukan Ummey hakama, Junainah sai ta raɓa gefensu tayi, zurui a zatonta aure abun daɗi ne ba kukaba to gashi taga su kuma kuka sukeyi. Sosai Shatu takeyin kuka mai tarin dalilai. Suna isa Bappa yasa hannunshi ya kamo nata, cikin sanyi yace. "Taso kizo". Ido cike da hawaye ta mike tsaye bisa umarnin Bappa. Shi kuwa Bappa cikin sanyi ya kalli Ummey da Junainah yace. "Kada kuyi kuka, kuyi mata addu'o'in samun nasara a cikin wannan al'amari, muyi mata fatan aurenta ya zamo haske ne a rayuwarsa shi mijin da ahlinshin baki daya, fatanmu aurenta ya zamo ƙungiyar da zata jawo gskya cikin raminda aka binneta ya fito da ita kowa ya gani." Shiru Ummey tayi sai hawayen da suke kwaranya. Hakama Shatu hawayenta wani na korar wani. Ita kuwa Junainah faɗawa jikin Ummey tayi sukaci gaba da zubda hawaye. Bappa kuwa hannunta yaja suka juya suna nufi hanyar fita. Da kayanta na ɗazu wanda taje Genaral Hospital Ɓadawaya dasu, hatta hand bag ɗinta na rataye a kafaɗarta wayarta na ciki. Cikin mamaki take bin bayan Bappa, tare da yin taku a hankali tana bin bayanshi yadda yake jan hannunta. Arɗo Bani kuma na biye dasu a baya. Suna fitowa ƙofar gidan, Haroon da Jalal suka juyo suka kalli juna, Cikin tarin mamakin ganin kamar yarinyar ɗazuce. Shi kuwa Sheykh Jabeer yana zaune cikin motar, shi ɗaya dan duk sun fita. Da sauri ya dafe saitin ƙahon zuciyarshi jin ta tsananta bugawar da yakeyi. A hankali ya maida bayanshi ya jingina da sit ɗin tare da rufe idonshi. Yana mai jin sanyin A/C na ratsa mishi jiki da jini da zuciya. Amman duk da haka zuface ke tsastsafo mishi a jikinshi sabida bugun da Zuciyarshi keyi ya wuce misalin. A hankali ya juya kanshi ya kalli gefen hagunshi inda yaga motar Jadda da kuma Dr Aliyu ne da Barrister Kamal ke jere a wurin. Bappa kuwa a hankali yake taku, yana nufo inda Lamiɗo ke tsaye Dogari na riƙe masa da laima, Ɗanzagi da fadawa na zube a kasa. Ita kuwa Shatu cikin rawan jikin jin idanun mutane na yawo a jikinta dan ma Allah yasa akwai niƙab a fuskarta. Take bin bayanshi. Shi kuwa Sheykh Jabeer yadda suke ƙara matso inda yake haka bugun zuciyarshin keta tsananta. Suna isa gaban Lamiɗo Bappa ya miƙawa Lamiɗo hannunta cikin sanyi da nitsuwa da taushin lafazi yace. "Allah rene, ga Aishatu matar Muhammad Jabeer. Gata amana bisa jagoranci ka, nasabarka da yardarka. Da kamala da nitsuwa da na gani a fuskar yaron yasa naji ƙarfin guiwar baku aurenta. Ba tare da fargaba ba, yanzu kaine kaka kuma jagora a gareta". Sai ya kuma nuna Barrister Kamal da shima yana cikin wakilai, shi a zatonsa ma shine mahaifin Jabeer cikin sanyi yace. "Kai kuma kaine matsayin mahaifi a gareta ku zame mata dangin ta data rasa, naso ace da mata a masu ɗaukanta, dan in danƙa amanarta a hannun macce yar uwarta. Amman ba komai, na baku amanarta dan Allah kada a cutar da ita, domin nima ta kasance amanace a uwurina, domin ƴaƴan mu da muka haifama amanace Allah ya bamu kuma abun kiyayewa, bare kuma ɗiya irin Shatu ɗiyace da take da nasabobi masu yawa a gareni". Cikin gamsuwa Lamiɗo yasa hannunshi ya amshi hannunta daketa karkarwa, tuni niƙab ɗin fuskarta ya jiƙe jilak da ruwan hawaye. Cikin Dattaku Lamiɗo yace. "In sha Allah zan kula da dukkan lamuranta tamkar yadda nake kula dashi Jabeer, kuma kada ka damu akwai masu meye mata gurbin uwa ƙanwa yaya dama duk danginta a cikin masarauta Joɗo, baƙoma baya kukan maraici bare kuma, matar sashin jinina". Cikin sanyi da wasu hawaye Bappa yace. "To Ngd matuƙa". Arɗo Bani ne ya dafashi tare da cewa. "Ka sanya mata al'barka a cikin aurenta ba zubda hawaye ba." Sosai Haroon ya zuba mata ido. Shi kuwa Sheykh Jabeer da mamaki yake kallon Bappa dake zubda hawaye. A hankali su Bappa suka ɗan ja da baya. Shi kuwa Lamiɗo ya juya ya nufi motar riƙe da hannunta. Haroon ne yayi saurin buɗe musu marfin motar, suka nufoshi gadan-gadan. Jalal kuwa ido ya zubawa yatsun hannunta da Lamiɗo ke riƙe dashi. Shi kuwa Jabeer idonshi ya rufe da ƙarfi. Sai kuma ya buɗesu, dai-dai lokacin Lamiɗo ya kawota bakin ƙofar motar tare da cewa. "Mamana kiyi bismillah ki shiga da ƙafar dama". Cikin shessheƙan kuka ta gyaɗa kai tare da yin bisimilla kana ta ɗan sunkuyo, sai kuma kukan ya kubce mata. Shi kuwa Jabeer da sauri ya buɗe marfin motar ta gefen hagunshi. Kamar gilmawar walƙiya ya fita cikin motar. Dai-dai lokacin da Shatu tasa ƙafarta ciki. da sauri yasa hannunshi ya buɗe motar Jadda tare da shigewa ciki yaja marfin ya rufe sabida ji yayi zuciyarshi zatayi bindiga, wani irin dogon ajiyan zuciya ya sauƙe mai ƙarfi. Ita kuwa Shatu, a hankali ta shiga ta zauna, don batama lura da shi bane tabbas dai taga mutun ya fita cikin motar. Tana shiga Haroon ya maida marfin ya rufe Shida Lamiɗo suka koma sit ɗin bayan wannan sabida su a zatonsu Jabeer na ciki. Ganin Lamiɗo ya shigane yasa duk kowa ya shiga motarshi. Hakama Jadda ya shiga ya zauna hankalinshi na woje. Sai da akaja motocin suka fara tafiya ne, ya juyo da sauri jin Jabeer na jan wani ja'irin tsaki mai tare da ajiyan zuciya. Cikin mamaki Jadda yace. "Haaahh kai kuma Meya kawoka nan? Yaushe ka shigo min mota!?". Bai kula Jadda ba, asalima yi yayi tamkar bai jishiba. Haroon kuwa cikin dariya ya ɗan bugi sit ɗin da yake zaton yana wurin cikin juya harcen Larabci yace. "Masha ALLAH, gasar Shaɗi tayi mana rana mun rabaka da gwauranci". Murmushi Lamiɗo yayi tare da kallon Haroon yace. "Saura kai". Murmushi yayi tare da cewa. "Ni ai nan kusa za'ayi". Jin shirune, yasa Haroon yayi shiru, Azotonshi ya ƙin mgna da shariyar ne suka zowa Jabeer bare, yasan yanzu a cike yake. Su Jalal kuwa kab da al'hini suke tafeyi. Jadda kuwa yayi iya mgnarshi yayi shiru ganin bai kulashi ba. A haka suka isa cikin Masarauta Joɗo. Suna isa kuwa Jabeer ya fito ya nufi Side ɗinsa, fitowarsa cikin motar Jadda ne yayi matuƙar bawa Haroon da Lamiɗo mamaki. Haroon kuwa bayanshi yabi da sauri. Suna shiga Side ɗinsa kuwa suka samu babu kowa. Suna gama tsayuwa Sallama ya nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu bisa umarni Lamiɗo. Yana shiga a babban Falon ya samu. Umaymah, Ummi, Aunty Juwairiyya, Hibba, Adda Rumana wacce take yayarsu Jabeer yar farin Abba kenan, sai mai bin mata Rumaisa. Kana sai Gimbiya Aminatu dake tsakiyarsu, sai hadimanta. Koda ya sanar musu, sun iso. Kusan duk a tare suka miƙe sai Gimbiya Aminatu ce bata tashiba da hadimanta. Su kuwa da sauri suka nufi woje, Umaymah ce gaba sai Aunty Juwairiyya dake biye da ita a baya riƙe da wani tire wanda samanshi ke ɗauke da al'kyabbar irin tasu ta matan masarauta da kuma wasu sauran tarkace. Suna fitowa motar na isowa har bakin wurin. Da sauri suka nufi jikin motar. Ita kuwa Zuwa yanzu ta tsagaita da kukanta, sabida ababen da take gani a cikin masarautar ya shallake tunanin mai tunani, gaba ɗaya jikinta tsuma yakeyi, sabida idonta na gane mata ababe na ban tsoro. Cikin ranta take mgnar zuci. "Innalillahi wa innailaihi rajiun, wannan wanne irin gidane? Me yake faruwa da mutanen masarautar? Sunko san gskyar junansu?". Da sauri ta rumtse idanunta sabida wasu irin hayaƙi da take gani yana tashi tako ina na gidan yayiwa gidan rumfa gaba ɗayansa. A da sauri ta buɗe idonta jin an kamo tafin hannunta, Umaymah kuwa cikin tsantsar jin daɗin da farin ciki maras misaltuwa tace. "Marhababiki ya binti". Wani irin azabebben tsinkewar zuciya da firgici da razanine ya daki zuciyar Shatu a lokaci ɗaya. Da sauri ta ƙara ware idanunta, dan son kallon matar da take jawota tare da cewa. "Kiyi bismillah ki fito da ƙafar dama, ki riƙe hannuna da kyau ɗiyata, ki kalleni nan nice jagorarki ki taka ƙafarki a inda zakiga na taka tawa". Ido ta zuba mata, tare da fitowa a hankali. Tana fitowa bakin ƙofar Umaymah tasa hannu ta amshi al'kyabbar da Aunty Juwairiyya take miƙa mata. Kangeta tayi kana tasa mata al'kyabbar, sannan ta gyara mata rufuwarshi da kyau ta rufa mata hularshi. Yadda sam mutun bazai samu damar ganinta ba. Ga niƙab ga kuma hular al'kyabbar da lu'ulu'u danke reto a fuskarta. Da sauri Aunty Juwairiyya ta matso tare da cewa. "Marhabin yar uwarta, Alhamdulillah yau kam na samu yar uwa". Adda Rumana ce ta matso kusa da ita tare da yin mgna da fillanci tace. "Sannu da zuwa Masarautar Joɗa ƙanwata". Adda Rumaisa kuwa murmushi yaketayi tare da matsowa, haka suka sata a tsakiya. Jakadiyarsu kuwa sai bin takun ƙafar Shatu takeyin da ido. A haka suka zagayeta, kana hadimai suka mara musu baya. A haka suka isa babban falon Gimbiya Aminatu. Suna isa Umaymah ta kaita har gabanta ta ajiyeta, Cikin tsantsar jin daɗi tace. "Alhamdulillah Gimbiya yau dai ga sabuwar Gimbiya dan yanzu itace amarya ba keba". Cikin dariyar jin daɗi Gimbiya Aminatu tasa hannu ta kamo hannun Shatu da Umaymah ke miƙa mata tare da cewa. "Kishiya ban haushi, ta isa ta zama Gimbiya zakisa yanzu in korata woje". Dariya sukayi baki ɗayansu. Yayinda tuni hadimai mata suketa jere ababen maƙulashe a gaban Shatu. Danginsu, Zuma, Madarar shanu, Da ƴaƴan itatuwa masu sanyi. Ita dai Shatu ƙasa tayi da kanta, tana jin fargaba da kuma tsoron wannan bahagon gidan data shigo. Su kuwa nan sukayi ta mata hidima da nuna mata so. Ganin magriba ta ƙara to ne yasa, Umaymah ta jawo hannunta ta kaita wani ɗaki dake nan kusa dana Gimbiya Aminatu. Tare da cewa. "Yauwa ɗiyata kiyi salla. Za'a kawo miki abinci, kada kici komai sai nazo". Cikin sanyi ta gyaɗa mata kai. Ita kuwa Umaymah hannu tasa ta fara zare mata al'kyabbar, koda ta cire mata shi, cikin kula tace. "Cire niƙab ɗin, babu mai shigowa nan yanzu sai nida Gimbiya Aminatu da Juwairiyya sai Jakadiyarsu". A hankali tace. "To". Haka nan taji duk wani yarda na duniya ta sauƙeshi kan wannan kekyawar mata mai fara'ar nan. A hankali tasa yatsunta ta kamo niƙab ɗin ta ɗin ta yayeshi. Wasu irin tagwayen numfarfashi Umaymah ta sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!". Da sauri ta juyo ta ruggume Jakadiyarsu a hankali tace. "Alhamdulillah Ummin Jabeer itace. Wlh itace". Cikin wani irin tarin jin daɗi Jakadiyarsu ta ɗan kalli Shatu, tare da yin murmushi mai cike da ma'anoni. Jakukkunan dake hannunta ta ajiye, kana ta iso kusa da ita ido ta zubawa fuskarta kana tace. "Ɗiyata menene sunanki?". Cikin yin ƙasa da ido Shatu tace. "Aysha". Kusan a tare sukace masha ALLAH. Nan Umaymah kam ta juya da sauri ta fita. Ita kuwa Jakadiyarsu Jabeer shirya mata kayan data shigo dasu takeyi a drower'n. Tare da bata umurnin taje tayi al'wala. Umaymah kuwa tana fita kai tsaye Side ɗin Jabeer ta nufa. Shiru ba kowa, da kamar duk sun tafi masallaci ne. Aunty Juwairiyya da Hibba kuwa suna sashin Juwairiyyan. Ummi kuwa na can wurin Shatu. Kai tsaye ɗakin da nanne masaukin ta, ta nufa. Bathroom ta faɗa ruwa ta ɗan watsa tare da yin al'wala kana tafito tazo ta kabbarta sallah. Ita kuwa Shatu zaune take bisa sallayan. Tunda ta idar da sallan bata tashiba. Sai kanta data jingina jikin gadon da take gefenshi. A hankali ta rumtse idanunta tare da motsa laɓɓanta tana karatun al'ƙur'ani cikin sanyin murya, Ummey da Junainah ne suka faɗo mata a rai shine ya sata zubda hawaye wasu na korar wasu. Kewarsu da begensu, ya tuno mata su Ya Gaini da marigayi ya Lado. Ummi kuwa itama bisa sallayan take tana lazumi. A haka har lokacin sallan isha'i yayi. Jin wata zazzaƙar murya mai matsifar daɗi na karatun. Hannun tasa ta share hawayenta dan jin karatun takeyi yana ratsa mata zuciya ya tsananta zubar hawayenta. A hankali ta miƙe itama ta kabbarta sallan isha'i. Hakama Ummi. Bayan an idarne. Ummi ta miƙe tsaye ta ninke abin sallan, kana a hankali take taku har kusa da ita. Cikin sanyi ta zauna bakin gadon tare dasa hannunta tsakiyar kanta a hankali tace. "AYSHA kuka kikeyi!?." Da sauri ta jujjuya kai alamar a a tana mai share hawayenta. Cikin kula Ummi tace. "Kuka mana kikeyi, gashi kinata zubda hawaye! Kiyi haƙuri kinji ko Aysha ki bar kuka, in kinji kewan mamanki ki kalleni a matsayinta, in kinji kewar yayarki ki kalli Juwairiyya a matsayinta, in kuma yayu maza kikaji kewarsu ki kalli Jalal da Jamil a matsayinsu. In wani abu na damunki ki gayawa Sheykh, shine mijinki kuma majiɓancin lamuranki in kinji kewar ƙanwa mace ki kalli Hibba a matsayinta,". Bata hafimtar kalaman wannan matar, bare tasan me take nufi saboda babu mutun ɗaya da ta sani cikin mutanen data kira mata. Abu ɗaya ta fahimta Sheykh shine wanda wai tace shine mijine ko majiɓancin lamurane, bata sanshiba bai kuma santaba ta ina zai jiɓanci lamuranta, Shin ta yaya zata zauna a wannan gidan da tun shigowarta take ganin ababe masu ban tsoro." Jin tayi shirune yasa. Ummi shafa bayanta tare da cewa. "Jikinki na rawa zazzaɓi kikeyi ne?." Cikin sanyin murya tace. "A a sanyi nakeji". Da sauri ta ɗan miƙe tare da cewa. "To bari in rage gudun A/C'n". Ragewa tayi kana tazo ta zauna kusa da ita. Umaymah kuwa tana idar da sallan isha'i, ta miƙe ta dawo sashin Gimbiya Aminatu. Tayi matuƙar mamaki ganin batun auren Jabeer ya karaɗe masarautarsu gaba ɗaya, taki wani sashi kawo abincin amarya akeyi. Ita da kanta da Gimbiya Aminatu sukayi ta shigar da Foodflaks ɗin abincin cikin ɗakin da take suna jerawa a gabanta. Shi kuwa Sheykh Jabeer bayan an salla. Ya fito kamar koda yaushe su Jalal na biye dasu a baya. Haroon kuwa suna tafiya a jere, suna cikin tafiya duk suka tsaya fuska a haɗe Jabeer ya juyo ya kalli gefen hagunshi da yaji an dafa kafaɗarshi, Jadda ne ya ɗan kalleshi kana ya kauda fuskarshi ba tare da yace mushi komaiba. Murmushi Jadda yayi cikin sakin fuska yace. "Ƙarfe tara dai-dai jirginmu zai tashi. Zamu koma da kawunan naku duka". Cikin muryar dake nuna cewa yana cikin tsananin ɓacin rai yace. "Allah kiyaye hanya". Ya ƙarishe mgnar tare da juyawa yaci gaba da tafiyarshi. Shi kuwa Jadda murmushi ya kumayi, fahimtar Sheykh yana tsananin fushi da baƙin cikin abinda sukayi mishi. Lamiɗo ne ya kalli Aminin nashi tare dayi mishi alamun ya barshi. Su tafi. Daga nan suka juya duk suka nufi, sashin Lamiɗo, inda aka gama shirya manya-manyan Foodflaks a tsakiyar falonshi bisa wani tattausan Turkey carpet mai masifar kyau da taushi. Nan suka zauna sukayi Dinner sunayi suna hira, Tare da yaransu. Bayan sun gamane, suka miƙe dan tafiya Airport sabinda lokacin tafiyarsu ya kusa. Kusan a tare suke fito zuwa babban falon dake tsakanin side ɗin Lamiɗo dana Gimbiya Aminatu. Bayan sun zaunane, Sallama yaje ya sanarwa Gimbiya Aminatu cewa Sarki Jalaluddin yana neman Umaymah da Amaryar Sheykh. Jin saƙon Sarki Jalaluddin daga bakin hadimanta da Sallama ya isarwa saƙon ne yasa ta miƙe ta nufi ɗakin da Umaymah take. A cikin ɗakin kuwa, cikin kula Umaymah take gabatarwa Aysha da abin ci dana taɓa ka lashe dana motsa baki. Adda Rumana kuwa kamar tasa mata abinci har bakinta, Itako Aysha kanta a sunkuye, ta zubawa kulolin abincin ido tana ganin ikon Allah dake wanzuwa cikin kayayyakin cimar, da sai dai gidan wane da wanen. Fahimtar kunya ne ya hanata cin komai yasa suka fito falo suka barta, da Umaymah kawai wacce taketa janta a jiki ganin hakane yasa, ta ɗan yarda taci abincin kaɗan. Suna zaune a nanne Gimbiya Aminatu ta shigo ta sanar musu saƙon sarki Jalaluddin nan, Umaymah ta sake saka mata wata al'kyabbar cikin jin daɗi tace. "Aysha ki saki jikinki dani, ki gaya min dukkan abinda kikeso, yanzu kinga wurin kakanunki zan kaiki. Sarki Jalaluddin mahaifina ne, wanda kuma shine mahaifin maman mijinki, ɗaurin auren sukazo shida yayunmu da ƙannenmu maza yanzu zasu koma jiharmu ne. Kinga wannan kuma Gimbiya Aminatu itace ta haifi mahaifin mijinki. Kana Sarki Nuruddeen ɗan Sarki Bubayero jikan sarki Joɗa, shine kakan mijinki. Mu ma mahaifiyarmu na Raye mijinki ne yasa mata suna Sitti, tana jiharmu ita bata samu zuwaba sai daga baya zata zo". Ajiyan zuciya tayi tare da kamo hannunta kana taci gaba da cewa. "Mijinki ɗan babban family ne gaba da bayanshi. A ƙalla zai ɗaukeki shekaru goma cikin masarautar Joɗa data musulmai baki gama sanin adadin dangi da yawan yan uwan mijinki ta gefen mahaifiyarshi da mahaifinshi ba. Yanzu muje su ganki ki gansu." Cikin sanyi tace. "To Aunty". Murmushi Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa. "Ba Aunty ku bace, Mijinki Malam Jabeer yafi yarda da ita fiye da kowa a dangin mahaifiyarshi, Umaymah yake kiranta". Kai ta gyaɗa tare da mgnar zuciya. "Ikon Allah". Ita kuwa Umaymah murmushi tayi kana tana hannunta suka fita. A falo suka samu Jakadiyarsu, da sauri Umaymah tace. "Yauwa kinga wannan itace Jakadiyarsu, itace ta rainesu tun suna yara, bayan mahaifiyarsu babu wanda yasan halin Jazlaan sama da ita a cikin wannan masarautar, ki kasance mai bin umarnin ta, domin itace idonki cikin wannan masarautar, Jazlaan a matsayin uwa mahaifiya yake kallonta ba baiwar gidansu ba". Cikin nitsuwa Aysha ta gyaɗa kai tare da cewa. "Nagode". Ita kuwa Ummi murmushi tayi tare da bin bayansu. Suna isa bakin ƙofar tayi musu iso bayan ta shiga ta sanar musu da isowarsu. A hankali suka shiga, cikin nitsuwa take bin takun Umaymah. Ita kuwa Umaymah har gaban Sarki Jalaluddin da Sarki Nuruddeen taje da ita, cikin shaƙuwarta dasu, ta ajiyeta a gabansu tare da cewa. "Jadda ga amaryar Sheykh Jabeer a sanya musu al'barka". Murmushi yayi tare da kallon Aysha. Wani nannauyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Allah ya sanya al'khairi ya basu zaman lafiya. Allah yasa tazo mana da hasken da zai kore duhun daya meye hasken idanunmu". Amin Amin suka amsa baki ɗayansu. Uncle Abdulkareem ne ya ɗan kalleta cikin sanyi yace. "Allah yayi miki al'barka dake da mijinki ya baku zaman lfy mai ɗorewa". Kanta ta ƙara sunkuyawa, Ita kuwa Umaymah matsota tayi tare da cewa. "Kinga ɗan ɗago kanki ki kallesu. Kinga ga Mahaifina. Ga Sarki Lamiɗo". Sai kuma ta nuna Abba dake zaune cikin murmushi tace. "Ga wannan shine mahaifin Jabeer mamanshi kuwa sai gobe a bisa ƙaidar masarautar keda shi Jakadiyarsu da Sallama zasuyi muki jagora ku zagaya cikin masarautarsu baki ɗayansu a nuna miki ahlinsu to da ɗakin mamanshi za'a fara kaiki". Kinga wannan shine babban Yayanmu sarki mai jiran gado. Ga kuma wa ƙaninmu Abdulmumin." Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa. "A a Khadijah a rana ɗaya kikeso ɗiyar taki tasan komaine? Ai abun da wuya, dole sai a hankali zata gane mu". Murmushi Jakadiyarsu tayi tare da cewa. "Hakane kam. Amman gwara an gabatar mata da manya". Sarki Jalaluddin ne ya gyara zamanshi tare da cewa. "To Khadijah mu yanzu zamu wuce, ke kuma sai yaushe?". Murmushi tayi tare da kallon gefen damanta inda Haroon ke zaune da wani kekkyawa mutun mai matsakaici shikara. Mi kama dashi wanda bisa dukkan alamu babanshi ne. Kauda kanshi yayi daga kallon da Umaymah keyi mishi, cikin ƙasaita alamun shima jinin sarauta ne, yace. "Ni kada ki wani kalleni, bance komaiba". Murmushi dattawan sukayi baki ɗayansu, Haroon ma murmushin yakeyi. Ita kuwa Umaymah kauda zance tayi da cewa. "Yauwa Aysha kinga wannan shine Haroon ɗan uwa kuma aboki amini abokin faɗan Jabeer. Akwai kuma ɗan yayanmu Ibrahim shine shaƙiƙin Jabeer shi yana Cairo, amman kwanan zai dawo ki ganshi." Jadda ne ya kuma tsareta da cewa. "Khadijah yaushe zaki koma?". Cikin sanyi tace. "Jadda in Abban Haroon ya amince zanyi wata ɗaya rak, sabida ganin yadda lamuran zasu tafi. tsakanin yaran, ita kanta Aysha tana buƙatar makusanci tare da ita, sabida baƙonci a irin gidajenmu abune mai wuya ga wanda ba irin gidajen ya taso ba". Murmushi Abban Haroon yayi tare da cewa. "Ba laifi na Amince, Amman bazaki ɗauki azumi a nan bada". Da sauri tace. "Na yarda". Haroon ne ya ɗan juya idonshi alum lissafi kana yace. "Ke nan sati uku zakiyi tunda azumin saura wata ɗaya". Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa, Jadda ne ya kalli Jakadiya tare da bata umarnin su tafi ita da Aysha. Gane abinda yake nufine yasa ta kamo hannun Aysha suka fita. Gimbiya Aminatu na biye dasu a baya. Gyaran murya Jadda yayi bayan sun fita, cikin nitsuwa da girma ya kalli Umaymah tare da cewa. "Alhamdulillah Khadijah, aure dai an ɗaura, duk da tarin tsana da ƙin abin da ɗan naki keyi. Haƙiƙa baya son wannan abun da akayi mishi. Naga fushi da tashin hankali mai tarin yawa a ƙwayar idanunshi da fuskarshi. Ina da yaƙini bisa halin Jabeer in ya tsani abu tofa ya tsaneshi kenan har gaban abadan, wannan shine babban tashin hankali na, Sabida yanada lafiya da tsayuwa kan kaifi ɗaya. Ya gayawa kakarshi Sitti babu wani gari na duniya da yakejin ya tsana sama da wannan garin. Yace baya son garin da mutanen garin. Sabida anci mishi zarafi a garin a gaban kafurai an tozarta shiga ta addinin Musulunci". Shiru sukayi baki ɗayansu, tabbas sun san hakane mgnar Jadda. shi kuwa Jadda a hankali yaci gaba da cewa. "Yanzu kubar Yarinyar a ta kwana a nan. Kana a ɗan ɗaga kafa har sai an gyara mata inda zata zauna, kamar ko wacce amarya. Sannan kada kuyi mishi mgnar auren bare ita yarinyar, in anyi haka fushinsa bazai tsanantaba, zaici gaba da al'amuran rayuwarshi, tunda shi mutum ne mai ibada da kuma aiyuka". Murmushi Haroon yayi tare da cewa. "In dai baza'ayi mishi mgnarta ba, to wallahi mancewa zaiyi da ita da babinta ma gaba ɗaya". Lamiɗo ne ya gyara zama tare da cewa. "Ya isa". Murmushi Umaymah tayi sabida ta lura har yau su Lamiɗo basu gama sanin Jabeer da halaiyarsa ba. Shi dai Jadda nan ya jadadda musu cewa, kada suyiwa Sheykh Jabeer mgnar sai an gama gyara komai na sashinta. Ko gaisuwar su bari sai bayan kwana uku a zagaya da ita cikin Masarautar. Nan dai sukayi sallama suka, tafi baki ɗayansu. Suna tafiya, Umaymah ta koma ɗakin da Aysha take, nan ta samu Ummi na zaune da ita. Nan ta zauna ta suka ɗan yi hira ganin alamun gajiya da bacci a tattare da itane yasa, sukayi mata saida safe suka fita suka tafi. Ratsawa sukayi wurin Gimbiya Aminatu suka mata saida safe kana suka fita suka tafi. Cikin tsananin jin daɗi suke tafiya, har suka iso bakin. Mashigar sashinsa, cikin nitsuwa sukaci gaba da tafiya. Shiru ba motsin komai suna gab da isa bakin ƙofar, suka tsaya cikin zaro ido, suka kalli Laminu da Gimbiya Saudatu, cikin haɗe fuska da zafi Umaymah tace. "Aoozubikalimatillahi taaa'ammati minshirin makalaƙa!." Cikin tsantsar tsanarta Gimbiya Saudatu tace. "A kanki hegu masu jajayen kunnuwa". Tana faɗin haka taja hannun Laminu suka fita. Su kuwa Umaymah da sauri sukayi ciki. A falo suka tsaya. Ba kowa a falon haka yasa tayi sauri ta nufi arear'n Side ɗin Jabeer, a falo ta samu Haroon konce bisa kujera. Yana ganinta ya tashi zaune. Cikin gimtse dariyarshi murya a hankali yace. "Yau duk kayan ahlin masarautar Joɗa sai an yagesu baki ɗayansu." Ya ƙarishe mgnar yana nuna mata ƙofar ɗakinshi. A hankali ta kutsa kai cikin ɗakin tare da yin sallama. Can ta hangoshi kan gadon yana konce rigingine, idonshi a lumshe, a hankali takeyin taku tana nufo inda yake. tare da mgnar zuci. "Wato harda sharrin Haroon zayiwa ɗan Umaymah". A hankali ta zauna bisa bedside drower'n. Idonta ta sauƙe bisa goshinsa, cikin mamaki ta juyo ta fuskanceshi da kyau ganin yadda Goshinsa ke....! By *GARKUWAR FULANI* "Kamar tsoffin karnuka". Cikin fusata Gimbiya Saudatu ta miƙe tsaye tare da nufo inda yake. Shi kuwa kanshi ya jinjina tare da cewa. "Kinyiwa kanki Garkuwa da kika tashi daga kan kujerata". A hatsale tace. "Wai kai a zatonka tsoronka nake jine ko meye?". Da sauri ya jujjuya mata kai tare da tsuke fuskarsa alamun baison sautin amon muryanta da take ɗaga mishi, a daƙile yace. "A a, na isa inyi zaton tsorona kikeji. Ke da bakinji tsoron Allah'n daya halicce ki bama, ina zakiji tsoron wani bawa nashi, ai masu tattausan zuciya suke tsoro". Hannu Baba Nasiru ya ɗago da alamun zai kifeshi da mari. Ba zato yaji ya kama hannunshi, kana ya ɗan juyo fuskarshi gareshi, cikin sakekkiyar murya yace. "Wai ku meyasa bakwa gane, yare da harshenmu na bani adam ne? Meyasa kukafi son Yaren dabobbin marasa hankali, a zatonka ka kai matsayin da zaka ɗago hannunka ka mari fuskanta?". A hatsale ya fuzge hannunshi tare da cewa. "Da uwarka kakeyi, kasan wacece dabbar ai!. Ɗan hegiya mai jajayen kunnuw..!". Shiru yayi bai ƙarisa mgnarba ganin wani irin kallo da Jabeer ke mishi, ido cikin ido. Kana ya ɗaga hannunshi na dama, yana ɗan buga bayan tafin hannun damanshi cikin tafin hannunshi na hagu. Still idonshi na kan fuskar ƙanin Mahaifinshi, miƙar da tafin hannunshi yayi, tare da mishi alamun datsa a cikin tafin hannunshi, kana cikin danne fushinsa, dan baya son su gane abinda ke masifar ci mishi rai, sai dai duk danniyarsa ya rigada, sun gane babu abinda ya tsana a duniya sama da azagar mishi mahaifiyarshi bare a suffantata da ƙaddararta, da binta da kalaman bita da ƙulli. Baba Basiru ne, yayi wani irin dariyar mugunta kana ya ɗan matsa baya kaɗan cikin izza yace. "Datse mana wuya zakayi, dan a zagi waccar munafukar da Allah ya nuna mata ishara tun a duniya". Murmushi mai rauni yayi kana yace. "Mahaukaciyar tsohuwar ku ko! Eh na gane lallai kam, batunka haka yake". Cikin fiffiƙewa suka fara kumfar baki ina dalilin zaicewa uwarsu mahaukaciyar tsohuwa". Daga nesa za'a iya jiyosu. Shi kuwa ko Aunty Juwairiyya dake Dinning area bata jiyo abinda yake faɗa. Domin cikin nitsuwarsa yake zaro musu, duk amsar mgnar da sukayi mishi tunma kafin harshensu ya huta. Gimbiya Saudatu kuwa, a masifance tace. "Ai asirinku zai tonu nan bada dadewa ba, munafukar kakar takace, tayiwa mahaifiyarsu asiri ta haukatata dan baƙin kishi irin nata". Murmushi yayi ganin yadda ƙannnen mahaifinshi keta ihu uwa karnuka. Allah ya sani lamarinsu yana bashi mmki har yau ya rasa me yayi musu mai zafi a duniya da suke gaza danne tsanarshi a aransu. Me Mahaifiyarshi tayi musu da suke masifar tsanarta?. Kanshi ya juya ya kalli Umaymah daketa murmushi mai cike da jin daɗin yadda yake komai a nitse. Juyawa yayi zai nufi gefen hanyan falonshi. Sai kuma ya ɗan tsaya ganin Gimbiya Saudatu tasha gabanshi. Cikin danne shakkarsa tace. "A haka zaku ƙare. Komai na muna furci, anje anyi aure a muna furce a ɓoye, sannan an kawota yau kwana uku kenan an kasa fito da ita a nunawa mutane ita, dan masifar rashin gsky. Ko dai cikin shegene da ita yasa kuke ɓoyeta." Da sauri Umaymah ta ƙara so inda suke, cikin tsuke fuska tace. "A kanki shege zai samu, in sha Allah bazai samu a tsatson yar uwata ba, kin kuma yi gaggawa, da yake dama aikin shaiɗan ne dole zakiyi ta aikatashi. Ki koma ki wanke idonki zai kawo miki Amaryarshi matarshi kuma uwar ƴaƴan shi, har Side ɗin ki, cikin falonki, har gaban ki. Kinaji zai gabatar mata ke da munanan ɗabi'unki dan tasan irin zaman da zatayi dake". Laminu ne yace. "Ke kuma waya kasa dake, ki bari ƴan gida suyi mg...!". Wani irin tsalle yayi ya koma baya, jin marin da Jalal wanda yanzu ya shigo ya kifa mishi ta bayanshi. Da sauri Baba Nasiru da Baba Basiru suka juyo kan Jalal, alamun wai zasu dakeshi. Karkata kai yayi ya kallesu da gefen ido. Kana a hankali yasa hannunshin ya ɗaga rigarshi, wata ƴar madai-daiciyar bindiga AK 47 ya zaro a ƙugunshi . Wani irin wawan birki sukaja, tare da cewa. "Eh lallai babu shakka masarautar Joɗa ta raini tantirin ɗan ta'adda bindiga, wato abin har yakai ka matakin riƙe bindiga". Kanshi ya tankwashe tare dasa bakin bindigar yana sosai tattausan sajenshi irin na Hamma Jabeer ɗin shi. Kana da bakin bindigar ya nuna musu hanyar fita. Ai a jere suka juya suna fita. Gimbiya Saudatu na cewa. "Duk wanda yaci tuwo dani, tabbas miya zaisha. Amaryar munafurcin a fito da ita mu ganta in an taki gsky". Laminu ne ya amshi zancen da cewa. "Menene ma abin gani a Bororiyar daji". Da haka dai suka fita. Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin kallo na tuhuma, da tarin mamaki yakeyiwa Jalal. Bindiga a hannunshi, shi kuwa Jalal ganin yadda duk suka zubawa bindigar idone yasashi. Meda ita cikin rigarsa. Kana ya juya da sauri ya nufi hanyar fita. Jabeer bai ce mishi komaiba. Yana ganin ya fitane shi kuma ya juya, ya nufi falonshi. Bedroom ya wuce, a hankali ya zauna bakin gado, tare dasa hannunshi yana buɗa bakin al'kyabbar jikinshin sai kuma yasa hannu shi na dama ya dafe kanshi, kalmar amarya mata ya maimaita a fili. Wani irin rumtse idanunshi yayi da ƙarfi Allah ya sani shi yama mance, batun wannan jagulellen auren da akayi kamar na wasan yara. kanshi ya ɗago a hankali ya kalli Umaymah dake shigowa da sallama a bakinta. Gefenshi tazo ta zauna bisa bedside drower'n tana fuskantarshi. hannunshi yasa, ya fara cire hiramin kanshi. ita kuwa Umaymah cikin hikima tace. "Idan mutun yana yi maka fatan ci baya to kayi mishi nuni da nasarorin rayuwarka, ban cika son takura maka akan baka umarnin yin abubuwan da baka soba, to amman bani da zaɓi akan duk wata al'ada ta masarautar Joɗa, da cikin masarautarmu ne, tabbas inada damar hana wani abun da saka wani abun." Cikin rauni ya kalleta da idonshi da sukayi jazir a hankali yace. "Me Mahaifiyata tayi musu mai zafi da suka sata a gaba ita da ah'linta. Duk abinda sukeyi Mata bata kulasu, bare ta kai ga ramawa, tana haƙuri akan komai, haka yasa suke zaton tsoronsu takeji. Ita kullum yanayi musu uzuri. su kuma kullum fatansu su cutar da ita har dai suka samu nasarar cutar da rayuwarta sannan muma basu barmu ba. Ni na gaji da zama cikin masarautar Joɗa, zan bar musu garin gaba ɗaya". Sauƙe numfashin tayi tare da cewa. "Basu da nasara a rayuwarsu. Nasara ɗaya ce garesu kuma sun yi ta. Ta ƙare musu". Sai kuma ta ɗan kalleshi cikin sanyi tace. "Jazlaan!". A hankali ya amsa mata. Fuska ta ɗan raunata kana a hankali tace. "Yau kwanan matarka uku a gidan nan!". Da sauri ya kauda fuskarshi a kanta wani irin haɗe fuska yayi tare da taune lip ɗin shi na ƙasa ta ciki. Shi ya mance da wannan batun yana rayuwarshi hankali konce. Wannan kariyar matar Gimbiya Saudatu tazo ta tono zancen. Ita kuwa Umaymah a hankali taci gaba da cewa. "Baka gantaba! Baka nemeta ba! Baka san halin da take cikiba! Baka nunata wa ah'linku ta masarautar Joɗa, a matsayin ta, na matarka. Lamiɗo yayi mgna har ya turo Umminka taxo ta sanar maka, sai tace bata so ɓacin ranka. Abbanka yace shi bazai ce maka komaiba, sabida babu abinda baka saniba kan al'adar masarauta. Yace kada wanda yayi maka mgna akan matarka sabida. kai ba jahili bane, duk ka fimu sanin haƙƙin mace akan mijinta. Yace kunya tashi kake son yi a idon mutane!". Kanshi ya fara jujjuyawa a hankali yace. "Me kukeso inyi! Umaymah ya kuke son inyi? Bazan iya juya kaina in dawo yadda kukeso bafa, daga yadda Allah ya halicce ni". Cikin hikima da sanyi tace. "Ka shirya gobe, ka gabatar da matarka ga ƴan uwanka da iyayenka". Hannunshi biyu yasa ya dafe kanshi. Tare da rufe idonshi, sabida sarawar da yaji kanshi nayi. sai kuma ya ɗan kalli Umaymah jin tana shessheƙan kuka. Cikin sanyi yace. "To!". Murmushi tayi tare da shafa kanshi kana ta juya ta fita da sauri. Kai tsaye sashin Gimbiya Aminatu ta wuce, ta sanar mata yadda sukayi da ɗan nata. Shi kuwa Sheykh Jabeer, a hankali ya miƙe al'kyabbar jikinshi ya zare, kana ya nufi bathroom da jallabiyar. Yana shiga ya zare jallabiyar da snglet ɗin. Kana ya shiga wurin wonkan. Ruwan sanyi ya sakarwa kanshi. sabida sarawar da kanshi keyi, tun ihun dasu Baba Basiru sukayi mishi a kanshi. Ga kuma wani sabon zance na zagaye idanun mayu da kulullukan masu konciyar ɗaukan rai na masarautarsu. A ƙalla yayi mituna biyar ruwan sanyin na zubo mishi a tsakiyar kai, kafin ya fara sauƙe ajiyan zuciya alamun kan ya fara lafawa. Al'wala yayi kana ya fito. A nan drower'n glass dake bathroom ɗin nashi ya kimtsa kanshi cikin wasu datsastsen yadi mai masifar kyau Super Nour, Noble blue mai ɗan karen kyau, tattausan yadine mara nauyi, kana yanada ɗan shara-shara kaɗan, riga da wonɗo ne dai-dai jikinshi rigar half jomfa ne wanda aka watsa mishi aiki da da baƙin surfani. in ka tsura mishi ido sosai zaka iya hango shatin snglet and white boxes jikinshi. Wani Oud mai daɗin gaske ya fesa. Kana ya fito. Baƙar fula ya kafa a kanshi wanda ya bawa tattausan gashin kanshi damar baiyana ta gefe da gefen kanshi da kuma ƙeyanshi. Fararen kyawawan Ƙafafunshi, ya zura cikin. Wasu tattausan takalma baƙi. Sai kuma yasa hannu ya ɗauki carbinshi. Agogon dake liƙe saman mirror ya kalla, Lokacin sallan la'asar yayi, dan haka dole babu baccin tsakanin azahar da la'asar ɗin da ya dawo yi. A masallaci ya samu su Haroon da Jamil. Bayan anyi sallan ne kowa ya kama sabgogin gabanshi. Shi Jabeer komawa gida yayi. Ya saka garen kayan jikinshin kana. Ya fito, Ummi ya samu tsaye a tsakiyar falon, cikin kula tace. "Zaka fitane?". Kai ya gyaɗa mata alamar eh. ba tare da damuwar rashin bata amsarba tace. "Da yan rakiya ko kai ɗaya?". Yana gyara zaman hular kanshi yace. "Ni kaɗai. Zanje gidan Malama Abubakar ne!". Murmushi tayi tare da cewa. "Ka gaida minshi". "In sha Allah zaiji. Umaymah fa?". Gane abinda yake nufine yasata cewa. "Tana can sashin Gimbiya Aminatu, wurin ɗiyarta Amarya Aysha". Kanshi ya ɗan sunkuyar ba tare da yace mata komai ba, ya fita. Malam Abubakar shine, malamin da ya fara ɗiga mishi harafin Ba''un a allon shi, wato Be a fillance, Basinmi'arra a hausance ko?. A wurin shi yayi sauƙan forko, sai dai zuwa yanzu, shi Jabeer shike ƙara wa Malam Abubakar sani, akan Nahawu da Tajwid sabida shi da karatun zaure yayi. Umaymah kuwa, ita da kanta ta sanarwa Lamiɗo cewa, gobe Sheykh zai gabatar da amaryarshi. Haka yasa, ta fara shirya Aysha, shiri na musamman. Cikin Hadiman Juwairiyya ɗaya daga cikinsu. Mai suna saratu, itace Umaymah tasa ta yarfawa Aysha zanen lalle mai ɗan karen kyau. Kana Ummi da kanta ta wonke mata kai sabida ita keyiwa Juwairiyya ma. Sosai ta fito ras. Ita kuwa Shatu duk abinda sukeyi Mata. Tunanin Hibba al'hinin da tun randa tazo bata kuma ganinta ba. tana son ta tambayesu ta rasa ta ina zata fara, dole dai haka ta haƙura tai shiru. Washe gari ranar talata. Da hantsi, ko ina na sashin Gimbiya Aminatu sai ƙashi yakeyi, sabida shiri da kimtsa amarya. Umaymah da kanta take kimtsata, wani irin dakekken wagambarine mai matukar kyau Royal blue, tasaka doguwar rigace. Tayi cib-cib da jikinta. wani irin ɗauri ɗan kwali Aunty Juwairiyya ta murza mata a kanta, irin mai stpes ɗin nan. Kana sai wata farar al'kyabbar masarauta fara ƙal mai kolliyar zaren aiki da ulunta Royal blue. da surkin Golding color mai sheƙi. Wasu fararen takalma masu ratsin Sky blue ne a kekyawan kafarta da yasha jan lalle, takalman basu cika tsini da tuduba, sai dai kuma ba dab da ƙasa bane. Tayi kyau iya kyau, sai ƙamshi da sheƙi take zubawa. Umaymah ce ta kama hannunta har zuwa falon Lamiɗo, wanda bai rigaya ya fita fadaba. Gefen Gimbiya Aminatu ta ajiyeta, kana tace. "Bari inje inzo da Angon." Murmushi Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa. "To kuyi sauri dai". To tace kana ta fita. A can sashin Sheykh Jabeer, kuwa. Da alamun wonka ya fito, a nitse yake kimtsawa, cikin wani fitinenne yadi mai taushin gaske. yadin Royal blue ne mai masifar kyau. rigar half jomfa yar tsukekkiya, tsaki ya ɗan ja lokacin daya gama dai-dai-ta zaman rigar a jikinshi sabida tayi kib-kib a jikinshi har kamar ta ɗan matseshi. Wondon kuma irin mai iya kuibin sawune, irin sakun wondunan ahlul sunna. a hankali ya iso gaban drower'n da hulunanshi da hirami da baƙin abun saman hiramin ke jere a ciki. Har yasa hannunshi bisa wani farin hula, sai kuma ya sunkuya ya ɗan kalli. Kanshi. Fuskarshi ya ɗan tsuke, sai kuma ya ɗan juyo jin muryar Haroon yana cewa. "Wow masha Allah, gsky kayi kyau, Please ka fita haka mana, ka ganka ɗan saurayi mai jini a jika, amman in kasa al'kyabbar nan, sai kwarjininka yayi yawa yaseen. Ni kaina sai inji ina shakkarka,". Kai ya ɗan shafa kana yasa hannunshi ya zaro hiraminshi fari da baƙin zagayen. ɗaya marfin drower'n ya buɗe tare da zaro wata dakekkiyar al'kyabbar fara mai ratsin blue na zaren aiki gaba da bayanshi. Gaban gado ya dawo yana warware al'kyabbar tare da cewa Haroon. "In na fita a haka ai ji zanyi kamar babu tufafi a jikina, sabida sunyi min kaɗan." Ya ƙarishe mgnar yana zura al'kyabbar a jikinshi. Masha Allah, Haroon yace. Kana ya matsoshi yana tayashi gyara zaman al'kyabbar yana cewa. "Duk shigar da kayi tana maka kyau, in na ganka ba al'kyabbar sai inga kamar kafi kyau. In kuma kasa al'kyabbar sai inga kafi kyau". Baice dashi komaiba yaci gaba da gyara sakun hiraminshi, saida ya gama dai-dai-ta hiramin sai ya juya ya nufi, wannan drower'n da hulunanshi ke jere a steps biyu na sama. Biyu na ƙasan kuma jerin takalmanshi ne. Fararen takalma masu taushi ya saka ƙirar Gucci, Zara-zaran yatsunshi sarari sabida ba sau ciki bane ba kuma half cover bane. turare ya fesa, tare da sa hannunshin ya shafa sajenshi. Kana ya kalli Haroon daketa ɗaukar shi hoto. Cikin tura baki Haroon yace. "Na bari, nasan yanzu zakayi ƙorafi, yanzu ina zakaje?". Yana fita yace. "Valli Hospital, akwai yaron da zan duba aikin da akayi mishi". Bayanshi ya biyo tare da cewa. "To sai ka dawo". Ni zamuje wurin Budurwar Jamil taga babban yayanshi. Wani kallo ya mushi tare da cewa. "Allah ya shiryeka babban kobo". Dariya Haroon yayi tare da cewa. "Eh naji na yarda, zanje yaro ya samu matsala da ita tanata wahal dashi ba dole inje in dai-dai-ta musu matsalar ba". Juyowa yayi jin abinda Haroon yace cikin sakin gajeren murmushi yace. "Uhumm yaushe ka zama luwali, bani da lbri, to kai taka matsalarma yaushe ka warware ta, kun iya cikamu da zancen ku ƴan soyayya ne, kuma bakuma san yadda ake soyayya da magance matsalolin ta da tattalinta gudun ta lalaceba". Wani irin dariya mai sauti Haroon yayi tare sara mishi. Da sauri ya juya, da nufin tafiya, sai kuma yaga Umaymah na tsaye a gabanshi. Hannunta tasa ta kamo nashi tare da janshi suka fara tafiya. Cikin sanyi yace. "Oh Umaymah ina zamuje?". Haroon kuwa baki ya taɓe tare da cewa. "Wlh gobe zan koma in sha Allah, komai sai an nunawa mana ƴan ubanci". Dariya Umaymah tayi tare da cewa. "Allah kiyaye hanya". Da sauri yace. "To na fasa tafiya". Suna gab da fitane yace. "Umaymah sakeni karmu fita a haka". Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa. "To taho". To yace mata kana yabi bayanta. Suna tafiya cikin ƴar faffaɗan hanyar da bishiyoyin namijin gwanda yayi musu ƙawanya, shiyasa wurin yayi sanyi. A hankali ya kalleta lokacin da suka iso. Bakin ƙofar Gimbiya Aminatu. tare da cewa. "Umaymah me zanyi a ciki?". Hannunta tasa ta kamo nashi. Kawai ta kutsa kai ciki. Dole ya bita a baya. Yana saka ƙafarsa cikin falon yaji zuciyarshi ta buga, da ƙarfi, lokaci ɗaya ta fara harbawa da sauri-sauri. Cikin sanyi yace. "Umaymah barni a nan". Bata kulashi ba taci gaba da janshi tayi har bakin ƙofar falon Lamiɗo. wani irin rumtse idanunshi yayi yin yadda zuciyarshi ke barazar fashewa. Da sallama a bakinta, suka shiga. Yayinda Lamiɗo da Abbanshi suka amsa mata. Cikin wani irin azabebben bugun da zuciyarshi keyi, yasa ƙafarshi cikin falon. yayinda Umaymah ke riƙe da hannunshi tana mishi jagora har zuwa gaban Lamiɗo da Galadima da Abbanshi da kuma Malaminshi Malam Abubakar. Kana ta tsaya dashi kusa da Aysha tare da rusunawa. Yayinda shi kuma cikin fargabar yadda ƙirjinshi keyi ya rusa a hankali ya zauna bisa tattausan carpet ɗin dake shimfiɗe a wurin. Dib, dab, dib, dab, dib, dab. Haka zuciyarshi keyi. yayinda itama Aysha da bai lura da ita Bama haka zuciyarta keyi, sabida jin an mutun ya zauna kusa da ita. A hankali ya lumshe idonshi, sabida bugawar da zuciyoyinsu keyi a tare yasa, ƙarfin nashi bugun ya ɗan ragu kaɗan. Cikin nitsuwa ya kalli Abbanshi kanshi a sunkuye yace. "Barka da safiya Abba". Cikin kula yace. "Barka dai". Sai ya kuma kalli Malamin nashi cikin kamala yace. "Allah hokke sabbugo, Malam Barka da zuwa ya gida?". Cikin nitsuwa Dattijan yayi murmushi tare da cewa. "Alhamdulillah Sheykh Jabeer ya hidima". Alhamdulillah yace, kana ya kalli Lamiɗo da Galadima. sai kuma ya kauda kanshi. murmushi Galadima yayi tare da cewa. "Mu bazaka gaishemu ba kenan?". Ɗan tsuke fuskarsa yayi tare da cewa. "Gaggawa dai aikin shaiɗan ne". Murmushi Lamiɗo yayi sabida ya fahimci duk abinda zasuyi, sai ya cisu gyara ta kuma fuskar gsky. Galadima ne yace. "To ni bari in gaisheka Ina kwana". Kanshi ya jinina mishi tare da cewa. "Kayiwa kanka tanadin lada ashirin, a madadin kaɗan da zaka samu in ni na ɗaga maka gaisuwar. Lfyta lau Alhamdulillah." Ya ƙarishe mgnar da amsa gaisuwar. Dariya sukayi kana, ya kalli Lamiɗo a daƙile yace. "Ina sauri dan inada aikin yi, menene kasa aka jawoni nan". Ya ƙarishe mgnar a hankali yadda Abbanshi da Malaminshi bazasu jiba. Kana ya ɗan muskuta ya matsa gefe yayi nesa da Aysha sabida wani tsalle da yakeji zuciyarshi nayi, a madadin bugun da takeyi kafin ya zauna kusa da ita. Cikin zuba musu ido. Lamiɗo yayi murmushi sabida sunyi masifar dacewa da juna, shigarsu da ta zamo iri ɗaya tayi matuƙar yi musu kyau. Cikin wasa irin na kaka da jika yace. "Ga amaryar taka baku gaisaba, ku gaisa sai ka kaita kuje ka gabatar da ita". Fuskarshi a haɗe yace. "Hakan addinine ko al'ada?". Da sauri Galadima yace. "Al'adace kuma sai kayi ta". Ta gefen ido ya kalli Galadima tare da cewa. "Da ba Galadima za'a bakaba, da sarkin raya al'adu za'a baka". Shiru yayi jin Abbanshi na cewa. "Allah ya bamu nisan kwana, kaima watan watarana a gabanka yaranka zasuyi min haka Muhammad". Cikin yin ƙasa da kai cikin girmamawa da karrama mgnar mahaifin nashi yace. "Sun isa! Suyi maka haka in barsu". Murmushi Malam Abubakar yayi tare da cewa. "Kamar yadda ka isaba". Shiru yayi gane manufarsu. Jin duk sunyi shiru ne, yasashi ɗago kai ya kallesu. Suma shi suka zubawa ido, da sauri yayi ƙasa da kanshi. Ita kuwa Aysha shiru tayi tamkar ruwa ya cinyeta, tanajin yadda suke musayan kalamai. Sai dai bata fahimtarsu domin, tuno nata ahlin. Gyaran muryan da Abbansa yayine yasashi ɗago kai ya kalleshi. Cikin bada umarni Abba ya nuna mishi Aysha tare da cewa. "Kama hannunta kuje, ka gabatar da ita, ka fara daga sashin ƙannen Lamiɗo, sai na Mamanku, daga nan kuje wurin Gimbiya Saudatu, dama sauran matansu Babanku Nasiru". Bisa dole yace. "To kana ya yunƙa ya miƙa, da sauri Umaymah ta miƙe tazo ta miƙar da Aysha. kana ta kamo hannunta ta miƙa mishi alamun ya riƙe hannunta. Cikin tsuke fuskarsa da kwaɓeta tamkar zai ɗaura hannunshi a ka ya kurma ihu. Ya zuba mata ido. Muryar Abbanshi ce ta katse tsayuwar da yayi kamar an dashi. "Riƙe hannunta ku je". A hankali ya ware tafin hannunshi da Umaymah ta kamo kana lokacin guda yaji zuciyarshi tana tsalle da harbawa, kamar dai tana mararin wani abu. Hannun Aysha Umaymah tasa mishi cikin nashi tare da meda yatsunshi ta rumtsesu. Dam-daradam-dam haka zuciyarshi tayi wani masifeffen bugun mai kama da na aradu kana tafara wani irin tsalle. Ita kuwa Aysha, wani irin tsuma jikinta ya fara lokacin da taji tattausan yatsun hannunshi da fatar tafin hannunshi ya rumtse nata. Hannun wani irin masifeffen tsoro da kunyane suka diro mata, a lokaci guda. Shi kuwa Sheykh wani irin asirtace kuma ɓoyeyyen dogon ajiyan zuciya ya sauƙe mai sanyi, jin gaba ɗaya zuciyarshi ta koma ta nitsu tabar wannan tsinkewar da bugawar da tsalle tayi lib a cikin ƙirjinsa. Jin muryar Jakadiya ne yasa, Sheykh Jabeer, yin ƙarfin halin ɗaga ƙafarshi ta dama. Jin ya ɗan yi gabane yasa itama, ta ɗaga ƙafarta ta hagu, sai hakan ya bada wata dama ta musamman, ya zama suna ɗaga ƙafafuwan su, a tare kana suna taku a jere. Sai dai shi ɗin ya ɗan kereta kaɗan. "Masha Allah. Tabarakallah,". Sune kalaman da Umaymah ke Maimaitawa, lokacin da take biye dasu a baya. Lamiɗo da kanshi da Galadima sunga wani irin dacewa na musamman a tsakin Muhammad Jabeer da Aysha. Abba kuwa murmushi yakeyi mai baiyana jin daɗi. Malam kuwa, Addu'o'in yaketa jero musu na fatan al'khairi da zaman lafiya da nitsuwa da samun zuriya ɗayyiba. A hankali suke taku yayinda kowa zuciyarshi ke bin takun sawunsa, A haka suka fito babban falon Gimbiya Aminatu nan suka samu Ummi. Tana ganinsu ta miƙe da tsauri tayi gabansu, hadimai hudu cikin na Gimbiya Aminatu kuwa, sukayi bayan Umaymah dake bayansu. Shi kuwa Sheykh Jabeer suna fitowa yayi wani irin saurin sake hannunta tare da janye nashi, Sabida shi ji yake tsikar jikinsa na tashi tamkar ya riƙe wutan lantarki ne sabida masifar tsuma da yaki naman jikinsa nayi. Murmushi Umaymah tayi ganin still dai suna tafiya a jere a jere suna wani irin taku mai ƙayatarwa. Suna fitowa, suka samu sallama a bakin mashigar wurin. Nan ya shaida musu, duk sashukan gidajen anje anyi sallama dasu an kuma basu daman shiga. Tafiya kaɗan sukayi daga sashin Gimbiya Aminatu, ta gefen hagunshi, suka ɓullo farfajiyar wani babban part, Jakadiyarsu na gaba suna biye da ita a baya, Umaymah na biye dasu. A hankali suke taku cikin ƙasaita hadimai da fadawa na mara musu baya. Suna shiga ciki, suka samuwa wata dattijuwar tsohuwa mai tarin shekaru. Cikin murmushin da muryar tsufa tace. "Malamai magada annabawa, lallai yau inada babban baƙo da babbar baƙuwa." A hankali suke tafiya har zuwa gabanta, inda take zaune bisa tattausan carpet hadimanta na kewaye da ita. wanda biyu daga cikinsu, suka tashi da sauri suka kawo ababen motsa baki suka jera a gabansu. Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya kalli tsohuwar da take matar ga Galadima. Cikin kula yace. "Barka da safiya Innano". Cike da kula tace. "Barka dai Malam Muhammad, mun samu ƙaruwa ko". Kanshi ya gyaɗa mata a hankali haka yasa duk basu ganiba sai ita da yake gabanta. "Cikin muryar tsufa tace. "Allah ya sanya al'khairi. Ya baku zaman lafiya. Yasa matarkace iya rai da mutuwa. Ya azurtaku da zuriya ɗayyiba." Da Sauri Umaymah ta amsa da Amin Amin hakama sauran baki ɗayansu. Ita kuwa Shatu, cikin saisaita nitsuwarta ta ɗan kalli tsohuwar tare da cewa. "Ina kwana". Murmushi tayi tare da kai hannunta ta kamo hannun Shatu, tafin hannunta ta buɗe ta zuba musu ido, na yan wasu ɗakiƙu kana tace. "Lafiya lau, ya baƙu ta?". A hankali tace. "Alhamdulillah". Jakadiyarsu ce ta ɗan rusuna tare da cewa. "Mun barki lfy". Kai ta gyaɗa kana tayiwa hadimanta umarni su miƙo kyautar da take gadon masarautarsun ce farin gyale ne mai kyau da taushi. Umaymah ce ta amsa ta miƙa hadiman dake bayanta. Kana suka miƙe suka fita. Daga nan sashin wani sashin na kusa dashi suka shiga. Wanda yake sashin ƙannen Lamiɗo ne. Saida suka gama da sashukan manyan masarautar. Kana suka nufi sashin Hajia Mama. Tuni tasan da zuwansu. haka yasa ta kimtsa ta tsara komai na tarban surkar tata. A matsayinta na uwar ango. Har can cikin bedroom Ummi ta wuce, su kuma suna biye da ita a baya. Suna shiga suka sameta, zaune bisa kilishi, Batool na gefenta, wacce son ganin amaryar ne, ya hanata tafiya. Hadimanta kuma na zagaye da ita. Suna shigowa ta tashi zaune daga kishingiɗar da tayi. Cikin tsananin baiyana farin cikin ta, ta nunawa Jabeer kusa da ita. a hankali suka iso suka zauna gabanta. Umaymah kuwa gefenta ta zauna. Ummi ko na bayansu hadiman kuma suna can falo. Hannunta tasa ta kamo hannun Jabeer. Cikin fara'a tace. "Alhamdulillah Muhammad Jabeer, Allah ya sanya al'khairi ya baku zaman lfy". To shifa suna ɗaure mishi kai, da tarin addu'o'insu na al'khairi, shi dai ba sonta yakeba ba kuma zama da ita zaiba, to me zai wahal dashi da zaice Amin Amin. Umaymah da Jakadiyarsu ne suka amsa da Amin Amin kamar dai yadda sukayi a sauran wuraren. Batool ce ta kalli Shatu cikin isa tace. "Amarya ki ɗago kanki mana kinga gaban uwar mijine kike". Duk da taji mgnar Batool sai tayi kamar batajiba, Abubuwan ci da sha dake gabansu ne, Hajia Mama ta jawo wani ɗan ƙaramin tray da cups biyu ke kanshi. Gyara zama tayi da kyau, tana murmushi ta kalli Shatu dake mgna a hankali. "Ina kwana Mama". Cikin kula tace. "Lfy lau ɗiyata ya baƙun ta". Alhamdulillah tace, tare da tsurawa madara da zumar da Hajia Mama ta zuba musu cikin kofu nan ido. a hankali ta ɗan muskuta kaɗan tayi baya, tare da ƙara yin ƙasa da kanta. ita kuwa Hajia Mama, kofin ta ɗauka ta miƙa mata. Tare da cewa. "Gashi ɗiyata amshi kisha." Cikin sanyi murya can ƙasa ta girgiza kanta tare da cewa. "Alhamdulillah". cikin nuna kulawa da so Hajia Mama ta ƙara miƙo mata kofin tare da cewa. "A a ɗiyata, amshi kisha, wannan al'adace ta masarautar Joɗa, dole in marabceki dashi." Kai ta kuma girgiza alamun ya isheta. da sauri Umaymah ta matso kusa da ita tare da cewa. "A a Shatu amshi kisha kinji ko?". Cike da mamaki ta ɗan kalli Umaymah ta gefen idonta. jin Umaymah na ƙoƙarin matso da kofin kusa da itane yasa tayi mgna cikin ɗan ɗaga murya tace. "Bana shan madarar". wani irin kallo mai cike da damuwa Hajia Mama tayi mata tare da cewa. "Subahanallahi, bakya sha, kuma, amai yake sakine? Ƙa'idane da dole kishi". Ta ƙarishe mgnar cikin damuwa. Ita dai Shatu shiru tayi idonta na bisa kofunan madarar. Ummi ce ta matsota tare da cewa. "Shatu amshi kisha koda kurɓa ɗaya ne". Cikin rawan murya tace. "Bana sha". Jin alamun rawan murya irinta an takura mutum ne, yasa duk sukayi cirko-cirko suna kallon Madarar. Zuwa can Hajja Mama ta sauƙe wani bahagon ajiyan zuciya, kana ta ɗauki ɗaya kofin ta miƙa Jabeer tare da cewa. "To gashi kai kam kasha naka". Zamanshi ya ɗan gyara tare dasa hannun damansa ya amshi kofin. Wani irin zaro ido Shatu tayi. Kallon kofin takeyi tamkar zata maida kwayar idanunta cikin kofin. duk jikinta tsuma yakeyi, wani irin masifeffen bugawa ƙirjinta yakeyi da ƙarfi. Shi kuwa Sheykh Jabeer zaune yake riƙe da kofin, ya fuskanci Hajia Mama da kyau. Ita kuwa Hajia Mama hannunta tasa ta kamo ɗaya hannun Jabeer da baya riƙe da kofin. Kana ta miƙowa Shatu hannun alamun ta miƙo mata hannunta. Ƙara runsunar da kanta tayi tamkar bata gane me take nufiba. Cikin murmushin Hajia Mama tace. "Kawo hannunki ko ɗiyata". A hankali ta ƙara maida hannunta baya, dai-dai lokacin kuma Jabeer ya ɗago kofin ya kai saitin bakinshi da niyar zai sha. cikin hikima ta muskuta ta ƙara matsowa jikinshi da sauri ta ɗago hannunta kamar zata miƙawa Hajia Mama hannun. sai kuma ta ɗan kaikaice, ta buge c...! Ƙaƙa tsara ƙaƙa By *GARKUWAR FULANI* "Kamar tsoffin karnuka". Cikin fusata Gimbiya Saudatu ta miƙe tsaye tare da nufo inda yake. Shi kuwa kanshi ya jinjina tare da cewa. "Kinyiwa kanki Garkuwa da kika tashi daga kan kujerata". A hatsale tace. "Wai kai a zatonka tsoronka nake jine ko meye?". Da sauri ya jujjuya mata kai tare da tsuke fuskarsa alamun baison sautin amon muryanta da take ɗaga mishi, a daƙile yace. "A a, na isa inyi zaton tsorona kikeji. Ke da bakinji tsoron Allah'n daya halicce ki bama, ina zakiji tsoron wani bawa nashi, ai masu tattausan zuciya suke tsoro". Hannu Baba Nasiru ya ɗago da alamun zai kifeshi da mari. Ba zato yaji ya kama hannunshi, kana ya ɗan juyo fuskarshi gareshi, cikin sakekkiyar murya yace. "Wai ku meyasa bakwa gane, yare da harshenmu na bani adam ne? Meyasa kukafi son Yaren dabobbin marasa hankali, a zatonka ka kai matsayin da zaka ɗago hannunka ka mari fuskanta?". A hatsale ya fuzge hannunshi tare da cewa. "Da uwarka kakeyi, kasan wacece dabbar ai!. Ɗan hegiya mai jajayen kunnuw..!". Shiru yayi bai ƙarisa mgnarba ganin wani irin kallo da Jabeer ke mishi, ido cikin ido. Kana ya ɗaga hannunshi na dama, yana ɗan buga bayan tafin hannun damanshi cikin tafin hannunshi na hagu. Still idonshi na kan fuskar ƙanin Mahaifinshi, miƙar da tafin hannunshi yayi, tare da mishi alamun datsa a cikin tafin hannunshi, kana cikin danne fushinsa, dan baya son su gane abinda ke masifar ci mishi rai, sai dai duk danniyarsa ya rigada, sun gane babu abinda ya tsana a duniya sama da azagar mishi mahaifiyarshi bare a suffantata da ƙaddararta, da binta da kalaman bita da ƙulli. Baba Basiru ne, yayi wani irin dariyar mugunta kana ya ɗan matsa baya kaɗan cikin izza yace. "Datse mana wuya zakayi, dan a zagi waccar munafukar da Allah ya nuna mata ishara tun a duniya". Murmushi mai rauni yayi kana yace. "Mahaukaciyar tsohuwar ku ko! Eh na gane lallai kam, batunka haka yake". Cikin fiffiƙewa suka fara kumfar baki ina dalilin zaicewa uwarsu mahaukaciyar tsohuwa". Daga nesa za'a iya jiyosu. Shi kuwa ko Aunty Juwairiyya dake Dinning area bata jiyo abinda yake faɗa. Domin cikin nitsuwarsa yake zaro musu, duk amsar mgnar da sukayi mishi tunma kafin harshensu ya huta. Gimbiya Saudatu kuwa, a masifance tace. "Ai asirinku zai tonu nan bada dadewa ba, munafukar kakar takace, tayiwa mahaifiyarsu asiri ta haukatata dan baƙin kishi irin nata". Murmushi yayi ganin yadda ƙannnen mahaifinshi keta ihu uwa karnuka. Allah ya sani lamarinsu yana bashi mmki har yau ya rasa me yayi musu mai zafi a duniya da suke gaza danne tsanarshi a aransu. Me Mahaifiyarshi tayi musu da suke masifar tsanarta?. Kanshi ya juya ya kalli Umaymah daketa murmushi mai cike da jin daɗin yadda yake komai a nitse. Juyawa yayi zai nufi gefen hanyan falonshi. Sai kuma ya ɗan tsaya ganin Gimbiya Saudatu tasha gabanshi. Cikin danne shakkarsa tace. "A haka zaku ƙare. Komai na muna furci, anje anyi aure a muna furce a ɓoye, sannan an kawota yau kwana uku kenan an kasa fito da ita a nunawa mutane ita, dan masifar rashin gsky. Ko dai cikin shegene da ita yasa kuke ɓoyeta." Da sauri Umaymah ta ƙara so inda suke, cikin tsuke fuska tace. "A kanki shege zai samu, in sha Allah bazai samu a tsatson yar uwata ba, kin kuma yi gaggawa, da yake dama aikin shaiɗan ne dole zakiyi ta aikatashi. Ki koma ki wanke idonki zai kawo miki Amaryarshi matarshi kuma uwar ƴaƴan shi, har Side ɗin ki, cikin falonki, har gaban ki. Kinaji zai gabatar mata ke da munanan ɗabi'unki dan tasan irin zaman da zatayi dake". Laminu ne yace. "Ke kuma waya kasa dake, ki bari ƴan gida suyi mg...!". Wani irin tsalle yayi ya koma baya, jin marin da Jalal wanda yanzu ya shigo ya kifa mishi ta bayanshi. Da sauri Baba Nasiru da Baba Basiru suka juyo kan Jalal, alamun wai zasu dakeshi. Karkata kai yayi ya kallesu da gefen ido. Kana a hankali yasa hannunshin ya ɗaga rigarshi, wata ƴar madai-daiciyar bindiga AK 47 ya zaro a ƙugunshi . Wani irin wawan birki sukaja, tare da cewa. "Eh lallai babu shakka masarautar Joɗa ta raini tantirin ɗan ta'adda bindiga, wato abin har yakai ka matakin riƙe bindiga". Kanshi ya tankwashe tare dasa bakin bindigar yana sosai tattausan sajenshi irin na Hamma Jabeer ɗin shi. Kana da bakin bindigar ya nuna musu hanyar fita. Ai a jere suka juya suna fita. Gimbiya Saudatu na cewa. "Duk wanda yaci tuwo dani, tabbas miya zaisha. Amaryar munafurcin a fito da ita mu ganta in an taki gsky". Laminu ne ya amshi zancen da cewa. "Menene ma abin gani a Bororiyar daji". Da haka dai suka fita. Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin kallo na tuhuma, da tarin mamaki yakeyiwa Jalal. Bindiga a hannunshi, shi kuwa Jalal ganin yadda duk suka zubawa bindigar idone yasashi. Meda ita cikin rigarsa. Kana ya juya da sauri ya nufi hanyar fita. Jabeer bai ce mishi komaiba. Yana ganin ya fitane shi kuma ya juya, ya nufi falonshi. Bedroom ya wuce, a hankali ya zauna bakin gado, tare dasa hannunshi yana buɗa bakin al'kyabbar jikinshin sai kuma yasa hannu shi na dama ya dafe kanshi, kalmar amarya mata ya maimaita a fili. Wani irin rumtse idanunshi yayi da ƙarfi Allah ya sani shi yama mance, batun wannan jagulellen auren da akayi kamar na wasan yara. kanshi ya ɗago a hankali ya kalli Umaymah dake shigowa da sallama a bakinta. Gefenshi tazo ta zauna bisa bedside drower'n tana fuskantarshi. hannunshi yasa, ya fara cire hiramin kanshi. ita kuwa Umaymah cikin hikima tace. "Idan mutun yana yi maka fatan ci baya to kayi mishi nuni da nasarorin rayuwarka, ban cika son takura maka akan baka umarnin yin abubuwan da baka soba, to amman bani da zaɓi akan duk wata al'ada ta masarautar Joɗa, da cikin masarautarmu ne, tabbas inada damar hana wani abun da saka wani abun." Cikin rauni ya kalleta da idonshi da sukayi jazir a hankali yace. "Me Mahaifiyata tayi musu mai zafi da suka sata a gaba ita da ah'linta. Duk abinda sukeyi Mata bata kulasu, bare ta kai ga ramawa, tana haƙuri akan komai, haka yasa suke zaton tsoronsu takeji. Ita kullum yanayi musu uzuri. su kuma kullum fatansu su cutar da ita har dai suka samu nasarar cutar da rayuwarta sannan muma basu barmu ba. Ni na gaji da zama cikin masarautar Joɗa, zan bar musu garin gaba ɗaya". Sauƙe numfashin tayi tare da cewa. "Basu da nasara a rayuwarsu. Nasara ɗaya ce garesu kuma sun yi ta. Ta ƙare musu". Sai kuma ta ɗan kalleshi cikin sanyi tace. "Jazlaan!". A hankali ya amsa mata. Fuska ta ɗan raunata kana a hankali tace. "Yau kwanan matarka uku a gidan nan!". Da sauri ya kauda fuskarshi a kanta wani irin haɗe fuska yayi tare da taune lip ɗin shi na ƙasa ta ciki. Shi ya mance da wannan batun yana rayuwarshi hankali konce. Wannan kariyar matar Gimbiya Saudatu tazo ta tono zancen. Ita kuwa Umaymah a hankali taci gaba da cewa. "Baka gantaba! Baka nemeta ba! Baka san halin da take cikiba! Baka nunata wa ah'linku ta masarautar Joɗa, a matsayin ta, na matarka. Lamiɗo yayi mgna har ya turo Umminka taxo ta sanar maka, sai tace bata so ɓacin ranka. Abbanka yace shi bazai ce maka komaiba, sabida babu abinda baka saniba kan al'adar masarauta. Yace kada wanda yayi maka mgna akan matarka sabida. kai ba jahili bane, duk ka fimu sanin haƙƙin mace akan mijinta. Yace kunya tashi kake son yi a idon mutane!". Kanshi ya fara jujjuyawa a hankali yace. "Me kukeso inyi! Umaymah ya kuke son inyi? Bazan iya juya kaina in dawo yadda kukeso bafa, daga yadda Allah ya halicce ni". Cikin hikima da sanyi tace. "Ka shirya gobe, ka gabatar da matarka ga ƴan uwanka da iyayenka". Hannunshi biyu yasa ya dafe kanshi. Tare da rufe idonshi, sabida sarawar da yaji kanshi nayi. sai kuma ya ɗan kalli Umaymah jin tana shessheƙan kuka. Cikin sanyi yace. "To!". Murmushi tayi tare da shafa kanshi kana ta juya ta fita da sauri. Kai tsaye sashin Gimbiya Aminatu ta wuce, ta sanar mata yadda sukayi da ɗan nata. Shi kuwa Sheykh Jabeer, a hankali ya miƙe al'kyabbar jikinshi ya zare, kana ya nufi bathroom da jallabiyar. Yana shiga ya zare jallabiyar da snglet ɗin. Kana ya shiga wurin wonkan. Ruwan sanyi ya sakarwa kanshi. sabida sarawar da kanshi keyi, tun ihun dasu Baba Basiru sukayi mishi a kanshi. Ga kuma wani sabon zance na zagaye idanun mayu da kulullukan masu konciyar ɗaukan rai na masarautarsu. A ƙalla yayi mituna biyar ruwan sanyin na zubo mishi a tsakiyar kai, kafin ya fara sauƙe ajiyan zuciya alamun kan ya fara lafawa. Al'wala yayi kana ya fito. A nan drower'n glass dake bathroom ɗin nashi ya kimtsa kanshi cikin wasu datsastsen yadi mai masifar kyau Super Nour, Noble blue mai ɗan karen kyau, tattausan yadine mara nauyi, kana yanada ɗan shara-shara kaɗan, riga da wonɗo ne dai-dai jikinshi rigar half jomfa ne wanda aka watsa mishi aiki da da baƙin surfani. in ka tsura mishi ido sosai zaka iya hango shatin snglet and white boxes jikinshi. Wani Oud mai daɗin gaske ya fesa. Kana ya fito. Baƙar fula ya kafa a kanshi wanda ya bawa tattausan gashin kanshi damar baiyana ta gefe da gefen kanshi da kuma ƙeyanshi. Fararen kyawawan Ƙafafunshi, ya zura cikin. Wasu tattausan takalma baƙi. Sai kuma yasa hannu ya ɗauki carbinshi. Agogon dake liƙe saman mirror ya kalla, Lokacin sallan la'asar yayi, dan haka dole babu baccin tsakanin azahar da la'asar ɗin da ya dawo yi. A masallaci ya samu su Haroon da Jamil. Bayan anyi sallan ne kowa ya kama sabgogin gabanshi. Shi Jabeer komawa gida yayi. Ya saka garen kayan jikinshin kana. Ya fito, Ummi ya samu tsaye a tsakiyar falon, cikin kula tace. "Zaka fitane?". Kai ya gyaɗa mata alamar eh. ba tare da damuwar rashin bata amsarba tace. "Da yan rakiya ko kai ɗaya?". Yana gyara zaman hular kanshi yace. "Ni kaɗai. Zanje gidan Malama Abubakar ne!". Murmushi tayi tare da cewa. "Ka gaida minshi". "In sha Allah zaiji. Umaymah fa?". Gane abinda yake nufine yasata cewa. "Tana can sashin Gimbiya Aminatu, wurin ɗiyarta Amarya Aysha". Kanshi ya ɗan sunkuyar ba tare da yace mata komai ba, ya fita. Malam Abubakar shine, malamin da ya fara ɗiga mishi harafin Ba''un a allon shi, wato Be a fillance, Basinmi'arra a hausance ko?. A wurin shi yayi sauƙan forko, sai dai zuwa yanzu, shi Jabeer shike ƙara wa Malam Abubakar sani, akan Nahawu da Tajwid sabida shi da karatun zaure yayi. Umaymah kuwa, ita da kanta ta sanarwa Lamiɗo cewa, gobe Sheykh zai gabatar da amaryarshi. Haka yasa, ta fara shirya Aysha, shiri na musamman. Cikin Hadiman Juwairiyya ɗaya daga cikinsu. Mai suna saratu, itace Umaymah tasa ta yarfawa Aysha zanen lalle mai ɗan karen kyau. Kana Ummi da kanta ta wonke mata kai sabida ita keyiwa Juwairiyya ma. Sosai ta fito ras. Ita kuwa Shatu duk abinda sukeyi Mata. Tunanin Hibba al'hinin da tun randa tazo bata kuma ganinta ba. tana son ta tambayesu ta rasa ta ina zata fara, dole dai haka ta haƙura tai shiru. Washe gari ranar talata. Da hantsi, ko ina na sashin Gimbiya Aminatu sai ƙashi yakeyi, sabida shiri da kimtsa amarya. Umaymah da kanta take kimtsata, wani irin dakekken wagambarine mai matukar kyau Royal blue, tasaka doguwar rigace. Tayi cib-cib da jikinta. wani irin ɗauri ɗan kwali Aunty Juwairiyya ta murza mata a kanta, irin mai stpes ɗin nan. Kana sai wata farar al'kyabbar masarauta fara ƙal mai kolliyar zaren aiki da ulunta Royal blue. da surkin Golding color mai sheƙi. Wasu fararen takalma masu ratsin Sky blue ne a kekyawan kafarta da yasha jan lalle, takalman basu cika tsini da tuduba, sai dai kuma ba dab da ƙasa bane. Tayi kyau iya kyau, sai ƙamshi da sheƙi take zubawa. Umaymah ce ta kama hannunta har zuwa falon Lamiɗo, wanda bai rigaya ya fita fadaba. Gefen Gimbiya Aminatu ta ajiyeta, kana tace. "Bari inje inzo da Angon." Murmushi Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa. "To kuyi sauri dai". To tace kana ta fita. A can sashin Sheykh Jabeer, kuwa. Da alamun wonka ya fito, a nitse yake kimtsawa, cikin wani fitinenne yadi mai taushin gaske. yadin Royal blue ne mai masifar kyau. rigar half jomfa yar tsukekkiya, tsaki ya ɗan ja lokacin daya gama dai-dai-ta zaman rigar a jikinshi sabida tayi kib-kib a jikinshi har kamar ta ɗan matseshi. Wondon kuma irin mai iya kuibin sawune, irin sakun wondunan ahlul sunna. a hankali ya iso gaban drower'n da hulunanshi da hirami da baƙin abun saman hiramin ke jere a ciki. Har yasa hannunshi bisa wani farin hula, sai kuma ya sunkuya ya ɗan kalli. Kanshi. Fuskarshi ya ɗan tsuke, sai kuma ya ɗan juyo jin muryar Haroon yana cewa. "Wow masha Allah, gsky kayi kyau, Please ka fita haka mana, ka ganka ɗan saurayi mai jini a jika, amman in kasa al'kyabbar nan, sai kwarjininka yayi yawa yaseen. Ni kaina sai inji ina shakkarka,". Kai ya ɗan shafa kana yasa hannunshi ya zaro hiraminshi fari da baƙin zagayen. ɗaya marfin drower'n ya buɗe tare da zaro wata dakekkiyar al'kyabbar fara mai ratsin blue na zaren aiki gaba da bayanshi. Gaban gado ya dawo yana warware al'kyabbar tare da cewa Haroon. "In na fita a haka ai ji zanyi kamar babu tufafi a jikina, sabida sunyi min kaɗan." Ya ƙarishe mgnar yana zura al'kyabbar a jikinshi. Masha Allah, Haroon yace. Kana ya matsoshi yana tayashi gyara zaman al'kyabbar yana cewa. "Duk shigar da kayi tana maka kyau, in na ganka ba al'kyabbar sai inga kamar kafi kyau. In kuma kasa al'kyabbar sai inga kafi kyau". Baice dashi komaiba yaci gaba da gyara sakun hiraminshi, saida ya gama dai-dai-ta hiramin sai ya juya ya nufi, wannan drower'n da hulunanshi ke jere a steps biyu na sama. Biyu na ƙasan kuma jerin takalmanshi ne. Fararen takalma masu taushi ya saka ƙirar Gucci, Zara-zaran yatsunshi sarari sabida ba sau ciki bane ba kuma half cover bane. turare ya fesa, tare da sa hannunshin ya shafa sajenshi. Kana ya kalli Haroon daketa ɗaukar shi hoto. Cikin tura baki Haroon yace. "Na bari, nasan yanzu zakayi ƙorafi, yanzu ina zakaje?". Yana fita yace. "Valli Hospital, akwai yaron da zan duba aikin da akayi mishi". Bayanshi ya biyo tare da cewa. "To sai ka dawo". Ni zamuje wurin Budurwar Jamil taga babban yayanshi. Wani kallo ya mushi tare da cewa. "Allah ya shiryeka babban kobo". Dariya Haroon yayi tare da cewa. "Eh naji na yarda, zanje yaro ya samu matsala da ita tanata wahal dashi ba dole inje in dai-dai-ta musu matsalar ba". Juyowa yayi jin abinda Haroon yace cikin sakin gajeren murmushi yace. "Uhumm yaushe ka zama luwali, bani da lbri, to kai taka matsalarma yaushe ka warware ta, kun iya cikamu da zancen ku ƴan soyayya ne, kuma bakuma san yadda ake soyayya da magance matsalolin ta da tattalinta gudun ta lalaceba". Wani irin dariya mai sauti Haroon yayi tare sara mishi. Da sauri ya juya, da nufin tafiya, sai kuma yaga Umaymah na tsaye a gabanshi. Hannunta tasa ta kamo nashi tare da janshi suka fara tafiya. Cikin sanyi yace. "Oh Umaymah ina zamuje?". Haroon kuwa baki ya taɓe tare da cewa. "Wlh gobe zan koma in sha Allah, komai sai an nunawa mana ƴan ubanci". Dariya Umaymah tayi tare da cewa. "Allah kiyaye hanya". Da sauri yace. "To na fasa tafiya". Suna gab da fitane yace. "Umaymah sakeni karmu fita a haka". Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa. "To taho". To yace mata kana yabi bayanta. Suna tafiya cikin ƴar faffaɗan hanyar da bishiyoyin namijin gwanda yayi musu ƙawanya, shiyasa wurin yayi sanyi. A hankali ya kalleta lokacin da suka iso. Bakin ƙofar Gimbiya Aminatu. tare da cewa. "Umaymah me zanyi a ciki?". Hannunta tasa ta kamo nashi. Kawai ta kutsa kai ciki. Dole ya bita a baya. Yana saka ƙafarsa cikin falon yaji zuciyarshi ta buga, da ƙarfi, lokaci ɗaya ta fara harbawa da sauri-sauri. Cikin sanyi yace. "Umaymah barni a nan". Bata kulashi ba taci gaba da janshi tayi har bakin ƙofar falon Lamiɗo. wani irin rumtse idanunshi yayi yin yadda zuciyarshi ke barazar fashewa. Da sallama a bakinta, suka shiga. Yayinda Lamiɗo da Abbanshi suka amsa mata. Cikin wani irin azabebben bugun da zuciyarshi keyi, yasa ƙafarshi cikin falon. yayinda Umaymah ke riƙe da hannunshi tana mishi jagora har zuwa gaban Lamiɗo da Galadima da Abbanshi da kuma Malaminshi Malam Abubakar. Kana ta tsaya dashi kusa da Aysha tare da rusunawa. Yayinda shi kuma cikin fargabar yadda ƙirjinshi keyi ya rusa a hankali ya zauna bisa tattausan carpet ɗin dake shimfiɗe a wurin. Dib, dab, dib, dab, dib, dab. Haka zuciyarshi keyi. yayinda itama Aysha da bai lura da ita Bama haka zuciyarta keyi, sabida jin an mutun ya zauna kusa da ita. A hankali ya lumshe idonshi, sabida bugawar da zuciyoyinsu keyi a tare yasa, ƙarfin nashi bugun ya ɗan ragu kaɗan. Cikin nitsuwa ya kalli Abbanshi kanshi a sunkuye yace. "Barka da safiya Abba". Cikin kula yace. "Barka dai". Sai ya kuma kalli Malamin nashi cikin kamala yace. "Allah hokke sabbugo, Malam Barka da zuwa ya gida?". Cikin nitsuwa Dattijan yayi murmushi tare da cewa. "Alhamdulillah Sheykh Jabeer ya hidima". Alhamdulillah yace, kana ya kalli Lamiɗo da Galadima. sai kuma ya kauda kanshi. murmushi Galadima yayi tare da cewa. "Mu bazaka gaishemu ba kenan?". Ɗan tsuke fuskarsa yayi tare da cewa. "Gaggawa dai aikin shaiɗan ne". Murmushi Lamiɗo yayi sabida ya fahimci duk abinda zasuyi, sai ya cisu gyara ta kuma fuskar gsky. Galadima ne yace. "To ni bari in gaisheka Ina kwana". Kanshi ya jinina mishi tare da cewa. "Kayiwa kanka tanadin lada ashirin, a madadin kaɗan da zaka samu in ni na ɗaga maka gaisuwar. Lfyta lau Alhamdulillah." Ya ƙarishe mgnar da amsa gaisuwar. Dariya sukayi kana, ya kalli Lamiɗo a daƙile yace. "Ina sauri dan inada aikin yi, menene kasa aka jawoni nan". Ya ƙarishe mgnar a hankali yadda Abbanshi da Malaminshi bazasu jiba. Kana ya ɗan muskuta ya matsa gefe yayi nesa da Aysha sabida wani tsalle da yakeji zuciyarshi nayi, a madadin bugun da takeyi kafin ya zauna kusa da ita. Cikin zuba musu ido. Lamiɗo yayi murmushi sabida sunyi masifar dacewa da juna, shigarsu da ta zamo iri ɗaya tayi matuƙar yi musu kyau. Cikin wasa irin na kaka da jika yace. "Ga amaryar taka baku gaisaba, ku gaisa sai ka kaita kuje ka gabatar da ita". Fuskarshi a haɗe yace. "Hakan addinine ko al'ada?". Da sauri Galadima yace. "Al'adace kuma sai kayi ta". Ta gefen ido ya kalli Galadima tare da cewa. "Da ba Galadima za'a bakaba, da sarkin raya al'adu za'a baka". Shiru yayi jin Abbanshi na cewa. "Allah ya bamu nisan kwana, kaima watan watarana a gabanka yaranka zasuyi min haka Muhammad". Cikin yin ƙasa da kai cikin girmamawa da karrama mgnar mahaifin nashi yace. "Sun isa! Suyi maka haka in barsu". Murmushi Malam Abubakar yayi tare da cewa. "Kamar yadda ka isaba". Shiru yayi gane manufarsu. Jin duk sunyi shiru ne, yasashi ɗago kai ya kallesu. Suma shi suka zubawa ido, da sauri yayi ƙasa da kanshi. Ita kuwa Aysha shiru tayi tamkar ruwa ya cinyeta, tanajin yadda suke musayan kalamai. Sai dai bata fahimtarsu domin, tuno nata ahlin. Gyaran muryan da Abbansa yayine yasashi ɗago kai ya kalleshi. Cikin bada umarni Abba ya nuna mishi Aysha tare da cewa. "Kama hannunta kuje, ka gabatar da ita, ka fara daga sashin ƙannen Lamiɗo, sai na Mamanku, daga nan kuje wurin Gimbiya Saudatu, dama sauran matansu Babanku Nasiru". Bisa dole yace. "To kana ya yunƙa ya miƙa, da sauri Umaymah ta miƙe tazo ta miƙar da Aysha. kana ta kamo hannunta ta miƙa mishi alamun ya riƙe hannunta. Cikin tsuke fuskarsa da kwaɓeta tamkar zai ɗaura hannunshi a ka ya kurma ihu. Ya zuba mata ido. Muryar Abbanshi ce ta katse tsayuwar da yayi kamar an dashi. "Riƙe hannunta ku je". A hankali ya ware tafin hannunshi da Umaymah ta kamo kana lokacin guda yaji zuciyarshi tana tsalle da harbawa, kamar dai tana mararin wani abu. Hannun Aysha Umaymah tasa mishi cikin nashi tare da meda yatsunshi ta rumtsesu. Dam-daradam-dam haka zuciyarshi tayi wani masifeffen bugun mai kama da na aradu kana tafara wani irin tsalle. Ita kuwa Aysha, wani irin tsuma jikinta ya fara lokacin da taji tattausan yatsun hannunshi da fatar tafin hannunshi ya rumtse nata. Hannun wani irin masifeffen tsoro da kunyane suka diro mata, a lokaci guda. Shi kuwa Sheykh wani irin asirtace kuma ɓoyeyyen dogon ajiyan zuciya ya sauƙe mai sanyi, jin gaba ɗaya zuciyarshi ta koma ta nitsu tabar wannan tsinkewar da bugawar da tsalle tayi lib a cikin ƙirjinsa. Jin muryar Jakadiya ne yasa, Sheykh Jabeer, yin ƙarfin halin ɗaga ƙafarshi ta dama. Jin ya ɗan yi gabane yasa itama, ta ɗaga ƙafarta ta hagu, sai hakan ya bada wata dama ta musamman, ya zama suna ɗaga ƙafafuwan su, a tare kana suna taku a jere. Sai dai shi ɗin ya ɗan kereta kaɗan. "Masha Allah. Tabarakallah,". Sune kalaman da Umaymah ke Maimaitawa, lokacin da take biye dasu a baya. Lamiɗo da kanshi da Galadima sunga wani irin dacewa na musamman a tsakin Muhammad Jabeer da Aysha. Abba kuwa murmushi yakeyi mai baiyana jin daɗi. Malam kuwa, Addu'o'in yaketa jero musu na fatan al'khairi da zaman lafiya da nitsuwa da samun zuriya ɗayyiba. A hankali suke taku yayinda kowa zuciyarshi ke bin takun sawunsa, A haka suka fito babban falon Gimbiya Aminatu nan suka samu Ummi. Tana ganinsu ta miƙe da tsauri tayi gabansu, hadimai hudu cikin na Gimbiya Aminatu kuwa, sukayi bayan Umaymah dake bayansu. Shi kuwa Sheykh Jabeer suna fitowa yayi wani irin saurin sake hannunta tare da janye nashi, Sabida shi ji yake tsikar jikinsa na tashi tamkar ya riƙe wutan lantarki ne sabida masifar tsuma da yaki naman jikinsa nayi. Murmushi Umaymah tayi ganin still dai suna tafiya a jere a jere suna wani irin taku mai ƙayatarwa. Suna fitowa, suka samu sallama a bakin mashigar wurin. Nan ya shaida musu, duk sashukan gidajen anje anyi sallama dasu an kuma basu daman shiga. Tafiya kaɗan sukayi daga sashin Gimbiya Aminatu, ta gefen hagunshi, suka ɓullo farfajiyar wani babban part, Jakadiyarsu na gaba suna biye da ita a baya, Umaymah na biye dasu. A hankali suke taku cikin ƙasaita hadimai da fadawa na mara musu baya. Suna shiga ciki, suka samuwa wata dattijuwar tsohuwa mai tarin shekaru. Cikin murmushin da muryar tsufa tace. "Malamai magada annabawa, lallai yau inada babban baƙo da babbar baƙuwa." A hankali suke tafiya har zuwa gabanta, inda take zaune bisa tattausan carpet hadimanta na kewaye da ita. wanda biyu daga cikinsu, suka tashi da sauri suka kawo ababen motsa baki suka jera a gabansu. Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya kalli tsohuwar da take matar ga Galadima. Cikin kula yace. "Barka da safiya Innano". Cike da kula tace. "Barka dai Malam Muhammad, mun samu ƙaruwa ko". Kanshi ya gyaɗa mata a hankali haka yasa duk basu ganiba sai ita da yake gabanta. "Cikin muryar tsufa tace. "Allah ya sanya al'khairi. Ya baku zaman lafiya. Yasa matarkace iya rai da mutuwa. Ya azurtaku da zuriya ɗayyiba." Da Sauri Umaymah ta amsa da Amin Amin hakama sauran baki ɗayansu. Ita kuwa Shatu, cikin saisaita nitsuwarta ta ɗan kalli tsohuwar tare da cewa. "Ina kwana". Murmushi tayi tare da kai hannunta ta kamo hannun Shatu, tafin hannunta ta buɗe ta zuba musu ido, na yan wasu ɗakiƙu kana tace. "Lafiya lau, ya baƙu ta?". A hankali tace. "Alhamdulillah". Jakadiyarsu ce ta ɗan rusuna tare da cewa. "Mun barki lfy". Kai ta gyaɗa kana tayiwa hadimanta umarni su miƙo kyautar da take gadon masarautarsun ce farin gyale ne mai kyau da taushi. Umaymah ce ta amsa ta miƙa hadiman dake bayanta. Kana suka miƙe suka fita. Daga nan sashin wani sashin na kusa dashi suka shiga. Wanda yake sashin ƙannen Lamiɗo ne. Saida suka gama da sashukan manyan masarautar. Kana suka nufi sashin Hajia Mama. Tuni tasan da zuwansu. haka yasa ta kimtsa ta tsara komai na tarban surkar tata. A matsayinta na uwar ango. Har can cikin bedroom Ummi ta wuce, su kuma suna biye da ita a baya. Suna shiga suka sameta, zaune bisa kilishi, Batool na gefenta, wacce son ganin amaryar ne, ya hanata tafiya. Hadimanta kuma na zagaye da ita. Suna shigowa ta tashi zaune daga kishingiɗar da tayi. Cikin tsananin baiyana farin cikin ta, ta nunawa Jabeer kusa da ita. a hankali suka iso suka zauna gabanta. Umaymah kuwa gefenta ta zauna. Ummi ko na bayansu hadiman kuma suna can falo. Hannunta tasa ta kamo hannun Jabeer. Cikin fara'a tace. "Alhamdulillah Muhammad Jabeer, Allah ya sanya al'khairi ya baku zaman lfy". To shifa suna ɗaure mishi kai, da tarin addu'o'insu na al'khairi, shi dai ba sonta yakeba ba kuma zama da ita zaiba, to me zai wahal dashi da zaice Amin Amin. Umaymah da Jakadiyarsu ne suka amsa da Amin Amin kamar dai yadda sukayi a sauran wuraren. Batool ce ta kalli Shatu cikin isa tace. "Amarya ki ɗago kanki mana kinga gaban uwar mijine kike". Duk da taji mgnar Batool sai tayi kamar batajiba, Abubuwan ci da sha dake gabansu ne, Hajia Mama ta jawo wani ɗan ƙaramin tray da cups biyu ke kanshi. Gyara zama tayi da kyau, tana murmushi ta kalli Shatu dake mgna a hankali. "Ina kwana Mama". Cikin kula tace. "Lfy lau ɗiyata ya baƙun ta". Alhamdulillah tace, tare da tsurawa madara da zumar da Hajia Mama ta zuba musu cikin kofu nan ido. a hankali ta ɗan muskuta kaɗan tayi baya, tare da ƙara yin ƙasa da kanta. ita kuwa Hajia Mama, kofin ta ɗauka ta miƙa mata. Tare da cewa. "Gashi ɗiyata amshi kisha." Cikin sanyi murya can ƙasa ta girgiza kanta tare da cewa. "Alhamdulillah". cikin nuna kulawa da so Hajia Mama ta ƙara miƙo mata kofin tare da cewa. "A a ɗiyata, amshi kisha, wannan al'adace ta masarautar Joɗa, dole in marabceki dashi." Kai ta kuma girgiza alamun ya isheta. da sauri Umaymah ta matso kusa da ita tare da cewa. "A a Shatu amshi kisha kinji ko?". Cike da mamaki ta ɗan kalli Umaymah ta gefen idonta. jin Umaymah na ƙoƙarin matso da kofin kusa da itane yasa tayi mgna cikin ɗan ɗaga murya tace. "Bana shan madarar". wani irin kallo mai cike da damuwa Hajia Mama tayi mata tare da cewa. "Subahanallahi, bakya sha, kuma, amai yake sakine? Ƙa'idane da dole kishi". Ta ƙarishe mgnar cikin damuwa. Ita dai Shatu shiru tayi idonta na bisa kofunan madarar. Ummi ce ta matsota tare da cewa. "Shatu amshi kisha koda kurɓa ɗaya ne". Cikin rawan murya tace. "Bana sha". Jin alamun rawan murya irinta an takura mutum ne, yasa duk sukayi cirko-cirko suna kallon Madarar. Zuwa can Hajja Mama ta sauƙe wani bahagon ajiyan zuciya, kana ta ɗauki ɗaya kofin ta miƙa Jabeer tare da cewa. "To gashi kai kam kasha naka". Zamanshi ya ɗan gyara tare dasa hannun damansa ya amshi kofin. Wani irin zaro ido Shatu tayi. Kallon kofin takeyi tamkar zata maida kwayar idanunta cikin kofin. duk jikinta tsuma yakeyi, wani irin masifeffen bugawa ƙirjinta yakeyi da ƙarfi. Shi kuwa Sheykh Jabeer zaune yake riƙe da kofin, ya fuskanci Hajia Mama da kyau. Ita kuwa Hajia Mama hannunta tasa ta kamo ɗaya hannun Jabeer da baya riƙe da kofin. Kana ta miƙowa Shatu hannun alamun ta miƙo mata hannunta. Ƙara runsunar da kanta tayi tamkar bata gane me take nufiba. Cikin murmushin Hajia Mama tace. "Kawo hannunki ko ɗiyata". A hankali ta ƙara maida hannunta baya, dai-dai lokacin kuma Jabeer ya ɗago kofin ya kai saitin bakinshi da niyar zai sha. cikin hikima ta muskuta ta ƙara matsowa jikinshi da sauri ta ɗago hannunta kamar zata miƙawa Hajia Mama hannun. sai kuma ta ɗan kaikaice, ta buge c...! Ƙaƙa tsara ƙaƙa By *GARKUWAR FULANI* Ta bugi kofin madarar, ba zato ba tsammani, Jabeer yaji kofin ya tsumbce mishi. ya faɗi gefenshi. Tass ya fashe madarar ta kwaranye a ƙasa. Cikin sauri da tsuƙe fuskarshi ya juyo ya kalleta. Itama ɗin shi take kallo. Ido cikin ido sukayi da ita a karo na forko a rayuwarsa duk da yasan sun taɓa haɗuwa. Kallon kwaɗayye mai irin bakin Junainah, tayi mishi. Sai kuma ta janye ƙwayar idanunta cikin nashi da sauri. Sabida wani irin kallon da taga yanayi manata. Umaymah da Ummi kuwa, kallon junansu sukayi, cikin yanayin son gane ya akayi kofin ya faɗi dan basuga sanda ta ta ɗan buge mishi hannunta. Hajia Mama kuwa cikin tashin hankali da kiɗima ta kalli Umaymah tare da cewa. "Akwai matsala, ita batasha, shi nashi ya kwaɓe." Sai kuma ta maida dubanta ga Shatu cikin alamun damuwa tace kawo hannunki na dama." Still maida hannun nata tayi baya, ba tare da tace komaiba. Ummi ce ta ɗanyi ƙasa da murya tare da cewa. "Miƙa mata hannunki ku gaisa". Murya can ƙasa tace. "Yana ciwo". Ta ƙarishe mgnar da jin haushin kanta da ƙaryar da suka satayi. Batool ce ta kalleta sama da ƙasa kana cikin gyatsine tace. "Umaymah ai wannan ba irin matar Sheykh bac." Sai kuma ta haɗiye ragowar mgnar dan ganin wani irin kallon daya watsa mata na alamun. Ki kama kanki da kiran sunana a bakinki. Wani dogon ajiyan zuciya Hajia Mama ta sauƙe cikin fargaba tace. "Tashi Kuje ku gaida sauran. Allah yayi muku al'barka ya baku zaman lafiya. In sha Allah babu komai". Kamar jira Shatu takeyi a basu izinin tashi tayi fit ta miƙe. Da tarin mamaki Umaymah da Ummi suka miƙe, dan abubuwan da suka faru da yanayin Shatu, ya tsaya musu a rai. Shima Sheykh Jabeer miƙewa, yayi kana suka jere suka fita. Sai dai Shatu na ɗan sassarfa. Cike da mamakin wannan abun suka nufi Side ɗin Gimbiya Saudatu. A falonta suka sameta tana hakimce bisa kujerar ikonta, ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya tana karkaɗa ƙafar cike da izza. Ummi na gabansu suna bayanta Umaymah na bayansu. Cikin rusunar da kai Jakadiyarsu ta durƙusa gefenta tare da cewa. "Barka da safiya Gimbiya Saudatu, ga Sheykh Jabeer ya kawo miki da amaryarsa!". Cike da izza ta ɗan kallesu sama da ƙasa, kana ta nuna musu gabanta. Alamun su zauna, cikin sanyi Shatu ta rusuna tare da sunkuyar da kai ta zauna gabanta. Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin kallo yayi mata, mai cike da ma'anoni, gefen ta ya kalla inda wata kujerar ke kusa da tata komansu iri ɗaya. Taku yayi cike da ƙasaita ya isa gaban kujerar, kana ya juyo ya zauna kan kujerar. Hakan yasa ya fuskanci Shatu da Umaymah. zaman ƙasaita da isa yayi. wani mugun kallo take binshi dashi har ya zauna. Ita kuwa Shatu kanta a duƙe tana murzam ƴan yatsunta. Umaymah ce ta ɗan taho zata zauna kusa da ita, a hankali ya jujjuyawa Umaymah kai, alamun. A a kada ta zauna a ƙasa. gane manufarsa ne, yasa ta zauna bisa kujera. Shiru kakejin falon, sai takun sawun hadimanta dake kawo ababen motsa baki, suna ajiyewa gaban Shatu. Suna gama jerawa suka koma can gefen. Jin shiru-shirun yayi yawane yasa Shatu ɗan ɗago kwayar idanunta, ta kallesu. A ranta take mgnar zuci. "Ikon Allah, ohoho ni Shatu wannan wanne irin bahagon gidane, mai cike da sarƙaƙiya da tubkar baƙin zare, To ko dai ita wannan ɗin kurmace." Muryar Gimbiya Saudatu ce ta ƙatse mata tunani ta, cikin isa da izza ta kalli Sheykh Jabeer, kana ta juyo ta kalli Shatu, murya a daƙike tace. "Bakiyi sa'an mijiba, yarinya duk da gashi kamar kinada nitsuwa". Ido Shatu ta jujjuya cikin hular al'kyabbar jikinta. Shi kuwa Sheykh Jabeer, ko ta kan mgnar ta bai biba, sabida ai dama ya tsammaci, hakan kai ta juyo ta kalli Umaymah cikin ɗagawa tace. "A buɗe min fuskar amaryar in ganta da kyau, inga wanne irin idone da ita". Bata rufe bakintaba taji yana cewa. "Baza'a buɗe ba!." Murmushi Umaymah tayi sabida tsamar Sheykh Jabeer da Gimbiya Saudatu wani lokacin yadda kasan shi ubanta ne, haka yake mata mgna da yanke hukunci kai tsaye a karan kanta ma bare akan abinda ya shafeshi. ita kuwa Shatu a hankali take juya ƙwayar idanunta, tana kallon sawun Gimbiya Saudatu. cikin al'kyabbar ta ɗan juya idonta da kyau ta maidasu, kan kyawawan fararen sawun Sheykh, wanda suke tamkar ka taɓa jini yayi yo tsalle ya fito, sabida taushi da laushin fatar Wanda duk mutun mai zama da al'wala da yawan karatun al'ƙur'ani tafin hannunshi da ƙafarshi sukanyi wani kala mai masifar kyau da ɗaukar hankali koda baƙin mutun ne sai fatar hannunshi dana ƙafarshi sunyi kyau na musamman, hakama kuma fatar jikinshi wannan shine baiyanennen darajar zama da al'wala da yawan ambaton Allah kenan. Da ƙarfi ta rumtse idanunta tare da buɗe su. kan babbar yatsar kafarshi ta zubawa ido, sosai da sosai. wani ɗan zane baƙi mai suffar tafiyar maciji ta gani. sai dai bata samu ganinshi ras yadda take soba, shiyasa taketa zare ido, shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya ɗan turo ƙafar damanshi gaba. Dan ya gyara zaman ɗayan a kanta. Hakanne ya bawa Shatu damar zubawa yatsun nashi ido, suna nan zara-zara alamun mutum ne mai matsakaici tsawo. Ras zanen bindin maciciyar nan yake kan babbar yatsarshi. har zuwa bisa rumfar ƙafar kamar zanen dayis, cikin tarin mamaki da al'ajabi take bin zanen da idanunta. har inda igiyar takalminshi ya tsare zanen. Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe a hankali. sabida rashin ganin ƙarshen wannan zanen, da kuma inda ya nufa, da kuma ganin ya saman zanen yake. Hankalinta kab ya tafi ga zanen shiyasa bata jin ta ƙaddamar da Gimbiya Saudatu ke zubawa ba. Muryar ta taji da ɗan ƙarfi tana cewa. "Bata da sunane? Ke me sunanki". Ta ɗago kai da nufin yin mgna kenan sai kuma tayi shiru. jin Umaymah na cewa. "Sai kisa mata naki sunan, ba sai kiji namu ba". A gyatsine ta kalli Umaymah kana, ta ɗan matso bakin kujerar, hannu tasa ta ɗauki tupa cikin jerin ƴaƴan itatuwan da aka jera a gaban Shatu. miƙa wa Shatu tayi tare da cewa. "Kici kada ki tafi bakici komaiba,". A hankali tace. "Alhamdulillah!". Cikin sauri Gimbiya Saudatu tace. "A ni ba'a zuwa sashina a tafi ba abinda akaci". Hannu ta miƙa ta amshi tupan kana ta riƙe shi. Shi kuwa Sheykh Jabeer miƙewa tsaye yayi alamun tafiya hakane yasa. Suma suka miƙa suka fita. Daga nan kai tsaye Side ɗin. Baba Nasiru suka nufa. A falo suka samu matarshi da yaranshi dama shi kanshi. Bayan sun zaunane. ya kallesu sama da ƙasa yace. "Dama baku zauna ba, a hakama na ganku. ba sai kun zauna ba". Cikin sanyi ƴarshi Jamila ta ɗanyi ƙasa da murya tare da cewa. "Ayyah Baba ka barsu mu gaisa". Haɗe fuskarshi yayi sabida yasan irin masifeffen son da Jamila keyiwa Jabeer lokuta da dama, takanyi ta kuka in taji abubuwan da mahaifinta yakeyi mishi. shi kuwa Sheykh Jabeer tuni ya zauna ya harɗe ƙafa, Jamila kuwa cikin nitsuwa ta gaidasu kana. Ta kawo musu abin sha, Ummanta ku ko kallo Bata ishesuba yadda itama bata lallesu ba. Haka dai suka fita suka tafi. gidan Baba Basiru kuwa suna shiga ya tashi ya bar musu wojen. Daga nan suka shiga gidan Barrister Kamal Baba Kamal kenan. Yana ganinsu ya tashi ya ruggume Sheykh tare da cewa. "Masha Allah, Alhamdulillah yau dai Allah ya nuna min ɗana da matarsa". Zama sukayi bayan sun gaisane yayi musu addu'o'in al'khairi. Daga gidanshi gidan Dr Aliyu sukaje, wanda yake mutun mai mutunci da kamar Barrister Kamal. Sosai suka jima a sashinsa, yayi musu addu'o'in da sanya al'khairi da al'barka. Daga nan kuma sai Sashin Mom tsakar gidan Abbanshi. Maman Imran, ba yabo ba fallasa ta amsa musu. Daga nan wurin Amryar Abbansu sukaje, wanda suka sameshi a can. Daga nan sukaje gidan Ya Hashim da sauran ƴan bappanunsu. Gida na ƙarshe dai gidan Aunty Juwairiyya ne, can suka samu Hibba da Ya Jafar. Bayan sun gaisane, Umaymah ta ɗan matso kusa da ita cikin sauƙe numfashin gajiya tace. "Ɗago kanki Shatu kinga nan ƙofar Aunty Juwairiyya ce, ga mijinta shine babban yayan Jabeer, kuma yanada matsalar ƙwoƙolwa. Yanzu daga nan Side ɗinkin zamu wuce, wanda yana nan kusa da nasun. Sai gefen nakun kuma nasu Jalal ne." A hankali ta ɗago kanta ta kalli Ya Jafar, yana riƙe da hannun Jabeer yana karatun shi a hankali. Cikin sanyi tace. "Ina kwana yaya!". Kafaɗarta Umaymah ta dafa tare da cewa. "Baya mgnar komai a duniya inba karatuba, sai dai yanajin komai kuma yana gane komai in an gaya mishi amman fa baya mgna kam in ba karatuba." Cikin tsananin rauni da tausayawa, idonta cike da ƙwalla tace. "Allah sarki, Allah ya bashi lfy". Karon forko kenan tunda suko fito dashi taji ya amsa addu'a duk da tarin addu'o'in da akayi ta musu sai yanzu taji yace. "Amin ya Allah". Hakama Umaymah da Jakadiyarsu da Hibba sai dai duk ya riga su amsawa. A hankali take ɗan satan kallonshi a fakaice. Hibba ce ta janye mata hankali da cewa. "Aunty Shatu kin gaji kam. muje ki huta, gashi azahar ta kusa ma." Ɗan guntun murmushi tayi tare da cewa. "Uhum". Umaymah ce ta miƙe ita da Ummi kana sukace. Taso mu tafi, yanzu Hibba zata cikaki dan zance." Cikin murmushi Aunty Juwairiyya tace. "Ayyah Umaymah ku bar mana ita mana". Ummi ce tace. "Lokacin sallafa ya ƙara to". "Hakane kam". Juwairiyya tace tare da ɗaukar Foodflaks dake kan dinning table, tabi bayansu tana cewa. "Hibba ɗauko sauran!". To tace kana ta suggumi sauran tabi bayansu. Nan suka bar Jabeer da Ya Jafar ɗin. A babban falon suka zauna. Aunty Juwairiyya da Hibba suka ajiye Foodflaks ɗin bisa Dinning table, kana suka dawo tsakiyar falon. Umaymah ce ta miƙe tare da kallon Shatu, tace. "Taso mushiga ciki, kiga tsarin wurin naku". Miƙewa tayi cikin alamun gajiya, domin zagaye masarautar Joɗa babban aikine mai zaman kanshi. Donma su sun saba, ita kuma bafulatanar dajine tafiya baya bamu tsoro. Bayan Umaymah tabi, ta gefen Dinning area ta ɗan ratsa da ita, Suka shiga cikin kitchen, juyowa tayi ta kallesu Ita da Hibba, "Nan shine babban kitchen ɗin ki, dake babban falonki. Shine wanda in kinada aiki mai yawa, kamar na salla ko azumi, ko zakiyi ki aikawa surakanki. Hadimai zasu iya shigowa su tayaki." cikin fahimta tace. "Toh". Hibba ce ta ɗan ƙara so shigowa ciki tare da cewa. "Kai wanga kitchen badai girmaba, gashi komai a tsare gonin kyau. Kalarsa green and white komai na ciki gwanin kyau". Murmushi suka ɗan yi kana, Umaymah ta juya dasu. Daga nan cikin kitchen ɗin ta gefen dama akwai wata ƙofar da sai ka hau stpes huɗu. A gefen ƙofarne wani datsetstsen Fridge mai girma yake kwance. Haurawa sukayi kana Umaymah ta tura ƙofar ta shiga. Store ne mai zaman kanshi. akwai komai na buƙatar rayuwa, sai dai ba mai yawa bane. Shatu ta ɗan kalla tare da cewa. "Ga kuma store ɗinki. Nan za'a ke aje miki duk wani abun buƙata". Kai ta gyaɗa, kana suka fito. Wata ƙofar daketa hannun hagu ta nuna mata suna buɗe wa suka fito. Sai gasu bisa wata baranɗa mai girma, kana can ƙasan barandar fulawine da kuma pompona ke jere iya ganinka, Daga sama kuma igiyoyin shanya ne da a ƙalla sun kai huɗu. sai saman barandar kuwa, injin wanki ne. Nan dai ta nuna mata komai na wurin kana suka dawo cikin gida. Suna shigowa falo. Sheykh na shigowa. A nitse yake taku, kanshi na sunkuye yana kallon wayarshi da yake lallatsawa. Umaymah ce ta ɗan bi bayanshi tare da cewa. "Zo nan Shatu". Cikin zuba bayansu ido. Ta ɗan gyaɗa kai, tare da taka sawunta a hankali tabisu. Hibba kuwa gefen Aunty Juwairiyya ta zauna. Shi kuwa yana shiga falon nashi, ya juyo ya ɗan kalli Umaymah cikin kwaɓe fuska yace. "Umaymah, Dan Allah ni bana son ana shigomin da wasu ababen cikin Side na, bare rayuwata, me wancan abun da kika kira zaizo yi anan?". Ido ta kafeshi dasu hakane, yasa yayi ƙasa da kanshi. tare da shigewa bedroom yana cewa. "Dan Allah iya kar abun can falo". Ƙeyanshi Umaymah ta zubawa ido. "Wato ma wai wancan abun, lallai ma Jazlaan". Juyawa tayi ta ɗan leƙo a corridor ta hangota, murmushi tayi tare da cewa. "Taho mana". Kai ta kuma gyaɗawa tare da ƙara saurinta tafiyarta a hankali. Suna shiga falon, tayi wani irin ɓoyeyyen ajiyan zuciya mai sanyi, sabida wani irin masifeffen sanyi mai gauraye da ƙamshi mai ɗan karen daɗi da taji ya bugu jiki da zuciyarta. lumshe idonta tayi, kana ta buɗe su a hankali jin Umaymah na ce mata. "Nan falonshi ne, namusamman ba kowa ke shigo mishi wurin kai tsaye ba. dan ko Juwairiyya bata shigo mishi nan, kana akwai ƙannenshi ƴan uba maza da kuma Jalal basa shigo mishi nan. Jamil kan shiga in baya nan in zai dawo shikeyi mishi shara da gyaran wurin. Jalal kuwa yakan iya shekara ƙafarshi bata tako nanba. Sai kuma Ya Jafar ɗin sa, shi kam bashi da hijabi da Side ɗin Jabeer, yakan shiga har cikin Bedroom nashi wani zubin har bathroom. Sai kuma Haroon da Ibrahim su dama, dan su yasa aka gina sama wai masauƙinsu in sunxo. To ammanfa in sunzo a ɗakinshi suke ko motsi zasuyi tare zasuyishi. Sai kuma yayan Hibba, Hibbab shi na hannun damanshi ne. Dan haka daga yanzu in dai yayi tafiya kece, zakiyi aikin da Jamil keyi". A hankali tace "to". Haura step ɗin Dinning area ɗin shi dake falon wanda akayiwa ƙawanya da wani irin labule mai masifar kyau. Labulen ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu kama dana Daimond. wasu farare wasu Sky blue wasu Royal blue. suna da wani irin haske mai wal-wal. Cikinsa kuma. Wani badaidaicin Dinning table ne mai kujeru shida nan uku nanma uku sai wani fridge ma daidaici. Gefensa show glass ne mai kyau wanda yake ɗauke da cups and plates and spoons and forks Mug. Da dai sauran ƙananan abeben buƙata. sai woshing hand Baby, dake liƙe a can gefe. sosai tsaruwan wurin yayi kyau, komai Sky blue and white. Abun sai ya zama kamar a duniyar taurarin yake yadda walwalin ke haska ko ina. Falon kuma yanada ɗan karen duhu, domin saida Umaymah ta kunna musu wuta. Bedroom nashi ta nuna mata da yatsa. "Ga makwancinsa, sai kuma wancan ɗakin shi ba mai kwana a cikin ɗakine na musamman babu mai shiga ciki sai shi ni Lamiɗo Galadima, domin ɗakin aikinshi ne". Ita dai da to take bin Umaymah, sabida sanyin falon yana gab da sata kuka. Allah ya sani bata son sanyi ko kaɗan. Ta kuma lura su kuma mayun sanyi ne. Falon suka fito. Nan dai suka samu su Hibba nata hira da Ummi. Side ɗin ta suka nufa. Cikin kula tace. "Ga Side ɗinki ga falonki ga kitchen ɗinki." Ta ƙarishe mgnar suna shiga kitchen ɗin. A hankali take kallon komai na Kitchen ɗin kalarsa Pink and white. Sosai tsarin wurin yayi kyau. daga nan Dinning area Suka shiga ta nuna mata kana suka fito falon. Suka shiga bedroom ɗinta komai ya tsaru. Kuma komai sabone fil gwanin burgewa. juyawa Umaymah tayi tare da cewa. "Wancan ɗakin kuma masauƙi nane in nazo." Cikin ɗan murmushi tace. "Ayyah". Ƙofar Bathroom Umaymah ta nuna mata tare da cewa. "Azahar tayi shiga kiyi al'wala kiyi salla sai kizo muyi Lunch". to tace kana Umaymah ta juya ta fita. Shi kuwa Sheykh Jabeer, yana shiga ya maida ƙofar Bedroom ɗin ya rufe shiyasa Umaymah bata gwada shiga da itaba. Shi kuwa bathroom ya wuce wonka da al'wala yayi, ya sauya kaya. Kana ya fito cikin shigarsa ta musamman ya nufi. Masallaci. Koda sukayi salla suka fito. Falon ganin bata fito bane yasa, Umaymah cewa Hibba. "Jeki kiramin ɗiyata". Da sauri Hibba ta juya ta nufi ɗakinta. Kwance ta sameta bisa sallayar da tayi salla, ta kife kanta cikin hijabin jikin nata, bisa dukkan alamu kuka takeyi. jin shigowar Hibba ne yasa tayi saurin share hawayenta, tare da juyowa, cikin mamaki Hibba ta zuba mata ido. A hankali tace. "Aunty Shatu meya sameki kike kuka". Murmushin ƙarfin hali ta ƙaƙalo tare da cewa. "Kuka kuma Hibba". Cikin sauri tace. "Eh mana gashi idonki yayi ja". Miƙewa zaune tayi da kyau cikin sanyi tace. "No bacci na fara, shiyasa kikaga hakan". Kai Hibba ta gyaɗa kana tace. "To taso mu tafi falo Umaymah tace kizo muyi Lunch". Hannu tasa ta ɗan shafa cikinta tare da cewa. "Kamar na ƙoshi fa". Murmushi Hibba tayi tare da cewa. "Tab ai Wlh taso kawai mu tafi, dan Umsymah bazata barki bakici abinci ba". To tace kana ta miƙe ta ninke sallayan. Sabida gajiya ne da bege da kewar yan uwanta ne ya sata kuka da kuma jin yunwar ta mutu a cikinta. Suna fitowa su Umaymah duk suka miƙa, Dinning area suka nufa. Bayan duk sun zaunane, Ummi, ta miƙe da nufin saka musu abincin. Da sauri Aunty Juwairiyya ta miƙe tare da cewa. "A a Ummi ki huta bari in saka mana". Foodflaks ɗin dake kusa da ita ta ture tare da jawo wanda suka shigo dasu. Ummi ce ta ɗan kalleta tare da cewa. "Ya kika ture wancan?". Baki ta ɗan taɓe tare da cewa. "Uhummm wai fa Gimbiya Saudatu ce, ta turowa amarya abinci dan salon munafurci". Wani irin kallon ƙasa-ƙasa Shatu tayi mata tare da zuwa abincin data buɗe ido, cikin mgnar zuciya take cewa. "Uhumm wai zata cewa wata muna fuka, muguwa Itan ko meye sunanta!?". Sai kuma ta kalli Umaymah jin tana cewa Juwairiyya. "Ni zubo min na gidan Hajia Mama naga tuƙeƙƙen tuwone da biyar zogale". To Aunty Juwairiyya tace kana ta zuba mata. da sauri Shatu ta ɗan kalli Umaymah lokacin da aka saka mata mal-malan tuwon farar ɗanyar shinkafa, tare da miyar a side sup. Sai kuma ta juyo ta kalli Hibba da Ummi da tuni sun ja plate ɗin da Aunty Juwairiyya ta saka musu. Couscous and vegetables sup, mai ɗan karen kyau da ƙamshi. Da sauri ta jujjuya kanta lokacin da Aunty Juwairiyya ta turo mata na plate ɗin gabanta, cikin sanyi tace. "La da baki saminba". Da mamaki Umaymah tace. "Sabida me?". Sunkuyar da kanta tayi tana tunanin. suma ta yaya zata hanasu cin abincin. jin Ummi ta kuma mata tambayar da Umaymah tayi matane yasa ta ɗan kallesu. Ta buɗe baki zatayi mgnar kenan. Sheykh ya shigo da sallama, a bakisa. kusan a tare, suka amsa masa. A fakaice ya ɗan kalli Aunty Juwairiyya kana yace. "Kije ki bawa Ya Jafar mgninshi". To tace tare da miƙewa da sauri ta fita. Ita kuwa Shatu, wata nannauyan ajiyar zuciya ta sauƙe. Kana tasa hannunta ta ture plate ɗin gaban Umaymah tare da jawo na gaban Ummi da Hibba, Ido suka zuba mata cike da mamaki. Ita kuwa cikin sanyi ta kallesu tare da cewa. "Dan Allah kada kuci wannan abincin. Kuci wancan ne". Jabeer dake ƙoƙarin shigewa falonshi ne, a ranshi yace. "Uhumm lallai kam wannan abun wato itace ma zata zaɓa musu abinda zasuci". Hibba kuwa da sauri tace. "Aunty Shatu abincin gidan Gimbiya Saudatu fa kike cewa muci." Ganin kallon mamaki da tuhuma da Umaymah da Ummi keyi matane yasata yin ƙasa da kanta cikin jin tausayinsu a ranta tace. "To in bazaku cishiba, Umaymah bari ni in shiga kitchen nida Hibba yanzu zan girka muku duk abinda kukeso". Ko inda suke Sheykh Jabeer da yanzu ya fito zai wuce baiba, yacewa Umaymah. "Zan fita". Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa. "Allah kiyaye hanya, ya bada Sa'a". Amin Amin yace, hakama Ummi tai mishi addu'a. Ita kuwa Shatu kanta na sunkuye, Umaymah ce ta ɗan kalleta cikin nazartan yanayin ta, da yin tunani hakafa ɗazuma taƙi shan madarar Barka da shigowa masarautar Joɗa da Hajia Mama ta bata, ta kuma amshi tuppar da Gimbiya Saudatu ta bata, yanzu kuma tace kada suci abinci Juwairiyya. Wannan abun shi yafi komai tsayawa Umaymah a rai. Yaya daga shigowarta zata kasabto wasu hasashen a ƙwaƙwalensu. Kai ta jinjina tare da cewa. "Hibba sa mana abincin Gimbiya Saudatu, muci". Jin hajane yasa Shatu jawo Foodflaks ɗin ta fara saka musu. Ita kuwa Hibba ta kwashe plate ɗin da Juwairiyya tasa musu ta kaisu kitchen. Nan sukaci abincin kowa da abinda ke ransa. Ita Shatu bataci na kirki bama. Sabida ta lura da kallon da Umaymah keyi mata kamar da tuhuma. Suna gamawa suka tattare wurin ita da Hibba. tuni su Umaymah kuwa suna falon. Suna gamawa suka fito falo. da sauri ta kamo hannun Hibba suka wuce falonta har bedroom ɗinta. Suna shiga Haroon, Jamil, suka shigo. Shigarsu ba jimawa Jalal ma ya shigo. Nan sukayi ta hira. to ganin yanzu ta shigane yasa Umaymah bata kirata dan tazo taga ƙannen mijin mataba. Suko. Suna cin abinci suka fita sabida kiran sallan la'asar, daga nan kuma basu kuma shigowa falonba sai kusa goma na dare kafin nan kuwa tuni Shatu da Hibba sunyi bacci ma. Washe gari ranar Laraba, da safe. Aunty Juwairiyya ta shirya musu breakfast kamar yadda ta saba, koda su Umaymah basa nan, abincin Sheykh a sashinta yake duk da ma, yakan iya wata biyar baisa abincin nata a bakinshi ba. sai dai Ummi Jakadiyarsu ta ɗan dafa mishi irin ababen da yafi so yaci lokuta da dama kuma na rayuwarshi da Lamiɗo yake cin abinci a Side ɗin kakarsa Gimbiya Aminatu shiyasa bai fiye cin wanda ake kawowa sashinsa ba. Jalal Jamil Ummin suke cin wannan abincin. To sashin Hajia Mama kullum za'a kawo Side ɗin shi. Hakama gidan Barrister Kamal da Dr Aliyu yawanci suma sunasa ana kawo mishi. kana gidan Baba Nasiru ma, yawanci ana kawowa. Especially kamar yanzu da su Umaymah ke nan. To yauma haka abin yake tako ina an kawo musu breakfast, na maraba da zuwan amarya. Koda suka zauna cin abinci. Kamar jiya da dare, haka yauma Shatu ta ɗan kalli Aunty Juwairiyya cikin hikima tace. "Aunty Juwairiyya asaka mana na gidan Gimbiya Aminatu". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Wato kema irin mijin nakine, kuna son girkin Gimbiya, kunsan nata yafi naku na zamani daɗi da lfy". Murmushi Shatu tayi cikin jin sanyi da daɗin basu fahimci manufarta ba. Sun fara ci kenan. Jalal Jamil suka shigo. Dama Haroon, Ya Jafar, oga Sheykh Jabeer suna falonshi. can Ummi ta kai musu nasu karin. Cikin murmushin Umaymah tace. "Yauwa Jalal kuzo nan, kuga Aunty Amaryankun." Matsowa gefenta Jalal yayi tare da kallon Shatu a fakaice kana yace. "Uhumm aini na santa, taje ta tasa min ɗan uwa gaba har cikin Office dinshi tana mishi ihu a kai". Cikin sauri ta ɗan kalleshi tabbas ta ganeshi ta kuma tunashi Umaymah ta ɗan kalla tare da cewa. "Sherri ne, Umaymah ni banyi ihuba". Murmushi Jamil yayi tare da cewa. "Eh ai ba ihun kukaba, shi da mijin naki duk bauɗaɗɗun mutanene, da zaran kin ɗan yi musu mgna da murya a sama to cewa sukeyi, wai kayi musu ihu". Ya ƙarishe mgnar yana kallon corridor fitowa falonshi. Murmushi Hibba tayi tare da cewa. "Ga baki ga tsoro". Aunty Juwairiyya ce ta nuna musu wurin zama tare da fara zuba musu abincin. Ita kuwa Shatu murmushi kawai ta ɗan yi, sai taji hawaye na neman cika mata ido. Zamansu hakan ya tuna mata yayunta, ko ina suke? Wani hali suke ciki? Ko ya jikin Ummeynta? Ya Junainah keyi da kewarsu. Ba ya Lado, Babu Ya Gaini, Babu Ya Seyo, babu Ya Giɗi, sannan nima an kawoni nan an cusani cikin wani irin bahagon gida mai wuyar ganewa". A hankali tasa tafin hannunta tana share hawayenta cikin hikima. Ɗan juyowa tayi ta kalli. Umaymah dake cemata. "Shatu, ga Jalal da Jamil tagwaye ne, sune ƙannen Sheykh Jabeer da suke binshi yanada wasu ƙannen Affan baya ƙasar. Sai Imran ɗan amaryar Hajia Mama mom. sai kuma yayunsu mata, kin san su ai ko? Rumaisa da Rumana". A hankali ta gyaɗa kai alamar eh. Ita kuwa Umaymah su Jalal ta kalla tare da cewa. "Ga Auntyn ku, matar Hammanku". Jamil ne ya ɗan yi dariya tare da cewa. "Allah ya ɗaiyiba". Murmushi sukayi tare da cewa. "Amin Amin." Nan dai sukaci sukasha kana suka dawo falon. Kamar jiya haka yauma suka wuni. Umaymah da Ummi na yawan yi mata dukkan bayanin komai na Side ɗinta. Washe gari ranar. Al'hamis, da yamma taja Hibba suka koma falonta. Cikin yin ƙasa da murya tace. "Yauwa Hibba sammin wayarki. Wallahi na nemi tawa har na gaji ban ganiba tun a Side ɗin Gimbiya Aminatu". Da sauri Hibba tace. "Dama kinada wayane? Kuma ya ɓata baki faɗawa Umaymah". Da sauri ta jawo hannun Hibba tare da cewa. "Ina zakije?." "Zanje in gayawa Umaymah mana". Ta bata amsa tana cire code ɗin wayarta-ta tare da miƙa matashi, da sauri tace. "A a ki bari ke dai bani aron taki bari in kira Bappa na". Ajiye mata wayar tayi bisa cinyarta kana ta wuce ta fita. Ita kuwa Shatu, da ido ta rakata, jin tana ta rabkawa Umaymah Kira tun kafin ta fita. Ajiyan zuciya ta sauƙe tare dasa hannun ta ɗauki wayar. Jujjuya wayar tayi tare da miƙewa ta nufi bedroom ɗinta. Number Bappa ta saka, kana kirashi. tare da kara wayar a kunne mugu ɗaya ana biyu, aka amsa kiran. Wani irin murmushi tayi jin muryar Junainah tana cewa. "Bappa! Bappa ga wayarka ana kiranka". Da sauri tace. "Ƙanwaliya". Cikin wani irin mamaki da jin daɗin Junainah tace. "Laaaaah Adda Shatu, kece? Ina kike? Adda Rafi'a tazo jiya wai tana neman wayarki baya shiga, Bappa yace mata ai anyi miki aure, taita kuka tace to ya batun karatunki, Bappa ma ya nemi number ki baya shiga. Ina kika ajiye wayar ne to Adda Shatu". Cikin sanyi tace. "Wayar ta ɓata ne Junainah". Cikin tura baki tace. "To mijinki ya saya miki mana". Ido ta lumshe tare da cewa. "Ina Ummey na? Ya jikinta?". Cikin sauri tace. "Ummey tana na Kitchen, yanzu jikinta da sauƙi tana mgna kaɗan-kaɗan, ko ɗazuma itace tace. "Bappa ya kira mata ke!." Cikin tsananin jin daɗi tace. "Alhamdulillah, kai mata wayar". Da sauri ya juya ta nufi kitchen tana cewa. "Ummey! Ummey ga Adda Shatuna". Da sauri Ummey ta fito, ta amshi wayar. Cikin murya mai cike da sanyi tace. "Aysha na!". "Wasu zafafan hawayene, suka zubo mata, Cikin rawan murya tace. "Na'am Ummey na! Ya jikinki?". Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Jiki da sauƙi, Shatu yaushe zaki zo?". Bappa da yanzu ya iso daga rakiyar da yayiwa Rafi'a ne, yayi murmushi tare da cewa. "Bani wayar nan". A hankali cikin girmamawa ta miƙa mishi wayar. Shi kuwa amsa yayi tare da karawa a kunne. jin muryar bappa yanayi mata sallama ne yasata jin sabbin hawaye masu masifar ɗumi, sabida tausayinshi. Duk da tsufanshi mugayen ƙabilar ɓachama basu barshiba, sun kashe mishi babban ɗan shi. Kana sun tafi da uku, sun barshi cikin zulumin suna raye ne ko sun mutu? A ina suke? Me akayi musu? Me sukeyi? Sannan itama data rage anyi mata wani irin bahagon auren da yafi kama da na mulkin mallaka. Muryarsace ta katse mata mgnar zuci da takeyi da cewa. "Shatu kina Lfy ko?". Murya na rawa tace. "Lfy lau Bappa, amman bana jin daɗin gidan, ina kewarku, ya jikin Ummey na? Ya lbrinsu su Ya Gaini an samu wani lbrin ko har yanzu shiru? Ya Ba'ana bai muku komai bako? Ya tafi ne ko yana nan?". Murmushi yayi tare da cewa. "To Shatu wacce tamɓaya ɗaya zan amsa miki'. Tana kuka tace. "Duka". Cikin hikima da jinƙai irin na iyaye yace. "To sai kinyi shiru kin dena kuka". Da sauri tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa. "Na bari". Taku biyu yayi zuwa uku kana yace mata. "Ba'ana bai mana komaiba! Ya gudu ya bar ƙasar ma baki ɗaya! Jikin Ummey ki da sauƙi sosai! Su ya Giɗi munata addu'a in Sha Allah, in Allah ya yarda zasu baiyana garemu da izinin ubangiji. Kafuran nan kuma mun rigada mun karya ƙarfi su yanzu bazasu sake samun damar cutar da muba, in Sha Allah munfi ƙarfi su." Sai kuma ya ɗan tsagaita jin, tana murmushi mai ɗan sauti alamun jin daɗi, a hankali yaci gaba da cewa. "Rafi'a tazo, nayi mata bayanin komai, kuma in ta dawo zata zo, in an barta zata shigo". Da sauri tace. "Zan gayawa Ummi ta sanarwa sarkin ƙofa in tazo a barta ta shigo". Cikin danne ainihin tarin ƙunar watsewar gidanshi yace. "Yauwa to haka zakiyi. Sannan in sunƙi yarda kada ki damu. Umarnine gareki, kibi dukkan umarnin mijinki, kiyi mishi biyayya a cikin dukkan lamuranshi nasan bazai saki mugun abuba, kada ki saɓawa umarninshi. Kada kiyi komai saida amincewarsa. Ki kasance mai kula da lamuran rayuwarsa kada ki bar wani abun cutarwa tare dashi. Yanzu shine gatanki. Shine madadin Giɗi, Ganin, Seyo, Lado, ƙannenshi mata ki kallesu tamkar Junainah, mahaifiyarshi ki kalleta kamar Ummeynki, yan uwan mahaifiyarshi ki kallesu kamar yadda kike kallon innarku, yanzu sune ƴan uwanki. Domin naki basa kusa Ki zama GARKUWAR sa". Shiru yayi jin kuka na son kubce mishi. Ita kuwa tuni hawaye na kwaranya daga cikin manyan idanunta. Cikin sanyi yace. "Gobe zamu tafi, lardinmu, zamu koma can na wani lokaci". Wani irin tsananin razana da tsoro ta zaro ido tare da cewa. "Bappa zaku tafi Kardi kuma!? Ni ku barni a nan ba kowa nawa!?". Cikin sanyi yace. "Zamu dawo Shatu. Donke zamu dawo. Dole muje, in sanarwa iyayen innarku abinda ya faru da ita da yaranta. In kuma gayawa yan uwana halin da nake ciki a kan ɓatan yayunki, bayan salla zamu dawo. Can zamuyi azumi. Bakiga yanzu a nan ko tinkiya ba'a bar manaba". Cikin gamsuwa da zancen Bappa ta ɗan danne shessheƙan kuka tare da cewa. "Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy. Amman Bappa ku barmin Junainah mana, a kawo min ita mana in samu iƴar uwa kusa dani". Cikin tausasamata zuciya yace. "Kada ki damu, su nan bazasu barki da maraiciba. Sai mun dawo zan kawo miki Junainah da kaina". Kit kiran ya ƙatse sabida kuɗin sun ƙare. Hibba da tun ɗazu ta shigo tana gefenta ne, ta ɗan kalleta cikin sanyi tace. "Aunty Shatu, meyasa kikace bakya jin daɗin zama a gidan nan? Munayi miki wani abune?". Cikin zubda hawaye ta jujjuya mata kai. Hibba bazata fahimci halin da take ciki ba, bazata gane matsalar rayuwarta ba. Ita kuwa Hibba cikin sanyi tace. "Aunty Shatu nima ƙanwarki ce, duk abinda zakisa Junainah tayi miki nima kisani zan miki kinji ko". Cikin share hawayenta tace. "To Hibba ngd". Murmushi Hibba tayi tare da cewa. "Yauwa kuma Umaymah ta aika Ya Jamil ya sayo miki sabuwar waya iPhone". Cikin sanyi da son tsaida hawayenta tace. "Ngd". Haka yammacin ranar ta yishi a bedroom ɗin ta. Sai Hibba dake ɗebe mata kewa ne. Da Umaymah taga basu fito bane itama taje. Washe Gari yau Jumma'a, kuma yaune ta cika sati ɗaya cib a gida. Kuma tunda yazo gidan sau uku taga Sheykh Jabeer, tun randa ya wucesu, suna batun abinci bata sake ganinshi ba, koda a gilme ne. Yanzu ta saba da Umaymah Sosai hakama Ummi Ita da Hibba kuwa shaƙuwa ta fara ƙarfi a tsakaninsu. Tana jin Hibba kamar Junainah. Jamil da Jalal Haroon suna ɗan zama asha hira dasu. Yau ne kuma Haroon zai tafi Leddi julɓe, sabida yayi masifar kewan Jannart ɗin shi, wacce taƙe ƙanwace ga Aunty Juwairiyya, kuma ƙawance ga Ibrahim. Ƙarfe ɗaya dai-dai, Sheykh Jabeer, ne tsaye gaban dreesing mirror yana fesa turare bayan ya gama shirin jummarsa tsab. Yau shigar baƙar Al'kebbar da farar jallabiya yayi. Yayi wani irin kyau mai cike da sheƙi. Kusan a tare suka jero da Haroon wanda yake cikin shigar ƙananan kaya. Su kuwa suna falon suna, zaune. Jamil da Jalal da Ya Jafar kuwa suna tsaye alamun fitowar Sheykh suke jira. A hankali Shatu ta ɗan ɗago kanta jin wani irin masifeffen ƙamshi mai daɗin shaƙa. Da sauri ta janye ƙwayar idanunta, Sabida idonta da suka faɗa cikin ƙwayar idanunshi. Wanda shi kuwa Jalal yake kallo ganin wani shegen wondo wai shi crezi ne ko meye ne oho, duk yana ɓuɓɓule har kana iya ganin farar fatar cinyarsa. ga saɓulellen wonɗo ga kafurin aski. fuskarshi ya tsuke tare da jan gajeren tsaki wanda shiyasa Jalal juyawa, ya nufi hanyar fita yana cewa. "To Ni banifa da manyan kayan nan, yanzu bari inje in duba ko inada jallabiya sai in saka a kai zan biyoku daga baya." Da ido suka bishi. Haroon da Jamil kuwa murmushi sukayi. A haka suka fita suka tafi. Har sunje bakin ƙofar fita ba tare da ya juyoba yace. "Umaymah ku tashi lokacin salla yayi". Ya ƙarishe mgnar suna fita To tace. Kana suma su Ummi suka nufi ɗakinsu. Aunty Juwairiyya kuma ta wuce Side ɗinta. Ita kuwa Shatu da Hibba suka tafi ɗalinta. Hibba ce ta fara shiga tayi al'wala. Sannan itama Shatu ta shiga. Tana fitowa daga bathroom ɗin tayi wani irin....! Uhummmmmm tuni mun gama shimfiɗan lbrin GARKUWA yanzu dai muna cikene dumu-dumu . By *GARKUWAR FULANI*Tsayuwa tare da kasa kunnuwanta. Tana jin sautin zazzaƙar muryashi. Yana kudba. Akan laduban fuskantar watan Ramadan wanda zuwa yanzu kwanaki ne suka rage. A hankali ta fara taku tana Nufo inda Hibba ta shimfiɗa musu sallaya. Ita kuwa Hibba ido ta zuba mata ganin yadda ta kasa kunne. Cikin murmushin tace. "Aunty Aysha me kikeji". A hankali tace. "Wannan me sunan malamin da yake huduban nan. Kamar inada wa'zuzzukanshi amman kuma, ban san sunanshi ba, kamar dai kam nasan wannan Muryar". Murmushi Hibba tayi tare da cewa. "Lallai ma kam Aunty Aysha wai muryar Hamma Jabeer ɗin ne ma kike cewa kamar kin santa, kamafa kikace, lallai kam my Aunty". Da sauri ta kalli Hibba domin zuwa yanzu ta gane waye suke cewa Hamma Jabeer, Ko Sheykh, ko Jazlaan, ko Muhammad wani lokacin Umaymah na kiranshi haka. Ta kuma fahimci wai shine mijin da aka aura mata. Ta kuma gane sun taɓa haɗuwa sau biyu kafin yau. ganin tayi nisa a tunnine yasa Hibba cewa. "Aunty Aysha". Murmushi ta ɗan yi tare Dasa hannun ta amshi hijabin da Hibba ke miƙo mata. Cikin ranta take mgnar zuci. "Uhumm mutun duk rayuwarsa tana cike da ƙalubale da matsaloli Magauta sun sashi a tsakiya kota ina ya juya suna tare dashi. Amman bauɗewa ta hanashi ganewa, sai anyi mgn yace wai anayi mishi ihu a kai. ko shi kunnen macijine dashi da yafi kowa jin sauti. sai iya lillibka ɗika-ɗikan al'kyabbar yanata ɓoye jiki kamar wani mace". Mitsss ta ɗanja gajeren tsaki tare daci gaba da zancen zuci. "Yana nan jiki duk matsaloli ya bari mutun yaga iya inda abunda ke kan yatsunshi ma, ya gagara, shine kullum cikin al'kyabba har ƙasa uwa shine limamin harami. Sai an kasheshi a banza yasa ƙannenshi da iyayenshi a matsala. Danni matsalar rashin yayuna har huɗuma ya isheni damuwar duniya bazan ƙarawa kaina damuwar waniba". Da sauri ta juyo ta matso kan sallayar sabida jin har masallacin sun sallame sallar, sabida ta daɗe a tsaye tana zancen zuci. Nan dai sukayi salla, kana Hibba ta miƙa ta fita Ita kuwa Shatu, sabuwar wayarda aka saya mata jiya da sabon layi aka haɗa mata komai ne, tasa hannunta, ta jawo. tare da komawa ta kwanta bisa sallayar. Layin Bappa tasa kana ta kira. Jin bata shiga bane yasata gane, sun tafi kenan. Cikin sanyi ta kira ɗaya layin na wancan ƙasar tasu. Cikin sa'a kuwa ya shiga sai dai ba'a ɗagawa. Sau uku ta kira jin ba'a ɗaga ba, ta haƙura. Number Rafi'a tasaka ta kira. Tana ɗagawa tace. "Rafi'a Garkuwa ce". Cikin tsananin jin daɗi Rafi'a tace. "Alhamdulillah Garkuwa ya kike? Ina kike? Ashe kuma abinda ya faru kenan. Alhamdulillah mun rabu da matsalar Ba'ana, jiya naje Rugar Bani, wai yau su Bappa zasu tafi Lardi". Cikin murmushi tace. "Kai Rafi'a kimin mgna da ɗaɗɗaya mana zanfi ganewa". Cikin dariya tace. "Eh kyace haka mana kinyi bulunbuƙui a masarautar Joɗa". Cikin sanyin jiki taja numfashin tare da cewa. "MASARAUTAR Joɗa ko matsala, komai a bai-bai yake Rafi'a, bana fahimtar komai, tunda nazo cikin wannan masifeffen masarauta kaina a juye yake. Jina nake kamar a rami". Cikin rauni tace. "Rafi'a abubuwan sunmin yawa, da wanne zanji. Tabbas nayi farin cikin tsira daga tarkon ya Ba'ana, to amman ƙaddara batayi min adalciba data kawoni wannan wurin. Kin sani Allah ya sani ina son Ya Salmanu". Da Sauri Rafi'a ta katseta da cewa. "Kice Astagafirullaha kada ki mance da auren wani a kanki kike cewa kina son wani". Hawayen da suka cika mata ido ta share tare da cewa. "Bana sonshi! Bana ko son ganinshi, kuma shima hakane baya sona baya son ganina. sauƙina ɗaya da shima ba sona zaiyiba, kowa zaiyi rayuwarshi babu ruwanshi da wani shiyasa hankalina bai tashi sosaima, sai dai ina cikin tarin damuwa Rafi'a, babu Ya Giɗi,Gaini, Seyo, Lado, Inna. Sannan Junainah,Ummey da bappa da nake gani inji sanyinma wai sun tafi Lardi, ya zanyi inji farin ciki, ga wannan gida mai mutantani daban-daban wasuma naga tsanar shi wancan mai jajayen kunnuwan zasu ɗora a kaina, ko uwar meye haɗina dashi, da magautanshi zasu haɗa dani a ƙiyayyarsa, suji dashi mana, tunda bansan meya shuka musuba, dan shima na lura ba kanwar lasa bane bakine dashi, kan ace ɗirin yake ce musu konɗi, rashin tsoronshi na bani tsoro." Murmushi Rafi'a tayi tare da cewa. "Yanzu dai ya batun karatunki?". Cikin sauƙe numfashi tace. "Zan gayawa Umaymah". Cikin shaƙuwarsu Rafi'a tace. "To sai na shigo, dan mgnar bazata ƙare a wayaba". Da sauri tace yaushe zakizo?". Cikin sauƙe numfashi tace. "In sha Allah dai kafin azumi zan shigo". Cikin sauri tace. "Kafin azumi kuma azuminfa da ɗan saura bama kice gobe ko jibiba, Rafi'a in bakizo minba wa nake dashi da zai zomin?". Ta ƙarishe mgnar cikin rauni, Cikin tausayin Rafi'a tace. "To gobe ko jibi in sha Allah". Cikin jin daɗi tace. "To sai kinzo." Daga nan sukayi sallama. A ranar da yamma Haroon ya wuce jiharsu Jannart inda nanne masarautar sarkin musulmai take. A hankali dai kwanakin sukayi ta gungurawa suna cuɗewa Ramadan nata ƙara gaba towa. Yayinda duk al'ummar Annabi suketa shirye-shiryen tarban watan Ramadan. Yau dudu saura kwana bakwai ne ake zaton za'a fara azumi, in bai cikaba ma kwana shida. Tuni Umaymah nata shirin komawa Jihar Tsinako sabida Abban Haroon ya matsa ta dawo sabida shirye-shiryen Ramadan. Ita kuwa Umaymah tana jiran kayan auren data aika a haɗo mata a Dubai su isone. wanda ƙawarta ce ta bawa aikin kuma ƴar nan cikin jihar Ɓadamaya ne! Yau Lahadi ne, ta kama ranar bautar al'jihun baya ne. Wannan yasa duk manya-manyan Coci na cikin garin Ɓadamaya ya cika maƙil da mabiya bayan addinin Kirista ci. A hankali motocinsu suka fara fitowa cikin masarautar Joɗa, suna kama babban hanyar da zata sadasu da asibitin taraiya na jihar wato Genaral Hospital Ɓadawaya. Kamar kullum haka tawagar take, Lamiɗo zaije kai ziyarar dubiyar marasa lfy kamar yadda ya saba duk ƙarshen mako. A ƙalla motocin sun kai goma. Suna tafiya a jere a jere. Har suka iso yankin da asibitin yake, inda nan babbar hanyar hada-hadan cikin garin ne, wanda babbar kasuwar jiharma take kan titin. Wani tabkeken cocine mai zaman kashi a bakin babban titin LCCN, yana ta hannun hagu. Kana ta hannun dama kuma wani tsabtaceccen masallacin juma'a ne mai ɗan karen girma, haka ya zama suna fuskantar juna masallacin da cocin. Kana sai an wuce ta gabansu za'a ratsa konar shiga asibitin. To kasan cewar duk ranar jumma'a ƴan agaji na toshe hanyoyin daga ƙarfe sha biyu da rabi zuwa kan a idar da sallan jumma'a su buɗe, sai kafuran nan suma suka tsiri duk ranar Lahadi tun shida na safe zasu, Toshe hanyoyin nan, sai shida na yamma. Wanda hakan ke jawo cinkoson ababen hawa ata yankin wuri. Sai ya zama duk masu son yin salla a wannan masallacin jumma'a to ranar a sai tsare musu hanya, sai dai masu zuwa da ƙafa. Wannan abun ya damu musulmai, koda aka kai ƙorafi ga gwamnatin jihar sai cewa tayi. "Ita bata son fitina, a bar kowa yayi addininshi salin alum". Haka musulmai suka haƙura dan a zauna lfy. To masarautar Joɗa bata da wannan lbrin sai yau da suka fito ranar lahadi da yake kullum asabar suke zuwa. A jere a jere motocin ke tafi kasan cewar da sanyin safiya ne, lokacin sun gama rufe hanyoyin kana sunata tsastsafowa gabas da yamma kudu da Arewa. Cikin Mamaki motar su Lamiɗo da saura duk suka tsaya, sabida ganin motocin gaba sun tsaya. da sauri Sallama ya fita, tare da dawowa baya. zuwa gaban motar Lamiɗo yayinda Motar Sheykh Jabeer kuwa take can bayansu, shi sauri yake zaije Valli Hospital dan yiwa wata mata aiki. Rusunawa Sallama yayi tare da cewa. ("Allah rene halkaleru en mabɓi labi mai".) Allah rene kafurai sun rufe hanyoyin". Da sauri sarkin ƙofa ya fito yazo ya buɗewa Lamiɗo marfin yadda zasuji juna da kyau. Cikin mamaki Lamiɗo yace. "Lfy meya faru zasu rufe hanyoyin". Da sauri dubagari yace. "Ai haka sukeyi duk ranar Lahadi, su hana mutane sakewa su rufeshi tun safe sai yamma". Cike da Mamaki Galadima da yanzu ya iso wurin yace. "To duk hakan na menene?". Cikin sauri Duba gari ya ɗan rusuna tare da cewa. "Wai sabida musulmai na rufe hanyar duk ranar jumma'a sabida bada tsaro wai suma shine suka tsiri, hakan ankai mgnar wa gwamnatin kuma ta goyi bayansu". Cikin ta ajjudi suka kalli juna, kana cikin bada umarni Lamiɗo yace kaje kace, su buɗe hanyar yanzu nan. Kuje da sarkin aike". Nan take suka juya suka nufi can inda yaransu ƙananan ke tsaye su kakkafa Road closed and stop. Suna zuwa jim kaɗan suka dawo. Tare da cewa ai yaran sunƙi sabida sunce Gwamnatin jihar ta amince musu da haka. Wannan mgnar yayi masifar tasa zuciyar Lamiɗo. Cikin ɓacin rai ya zaro wayarshi ya danna mai girma Gwamnan kira. Inda yace maza, ya bawa kafuran nan damar buɗe waɗannan hanyoyin da suka rufe. Ba kunya gwamnan yace, to ai. Dokace Allah rene da kunbi wata hanyar ai yafi ko." Cikin tsananin tarin takaici Lamiɗo yace. "Muje duk ku shiga mota, mu canza hanya." Sun shishiga kenan sai kuma sukaji. matasa irin wanda suke gefen wurin suna cewa. "Jahan! Jahan!! Jahan!!!". Da Sauri Duk suka fara leƙawa suna kallon wanda ake kira da Jahan, ɗan jarida mai zaman kanshi wanda jihar Ɓadamaya da kewaye ke alfahari dashi. Duk da ya kasance Musulmi mai sunaga ba nasu bane, kafurai kuma suna alfahari dashi a matsayin nasune. Cikin isa da karsashi yake taku cikin wasu irin zafafan ƙananan kaya masu masifar kyau. Jahan kekyawane aji ƙarshe a kyau, fari ne ƙal hanci har baki shiyasa da yawa kance shi iyamurune, idanunshi farare ƙal-ƙal gashin kansa gwanin kyau sai dai kafurin askin dake kanshi. Yaran suna hangoshi suka matsa. Shi kuwa Jahan da kanshi ya buɗe hanyoyin gaba ɗaya. Kana ya nufi motar fadawa dake gaba. Haɗe hannunshi yayi wuri ɗaya tare da. Musu alamar suyi haƙuri kana ya musu alamar su wuce. Daga nan motar Waziri ya nufa, suma ya basu haƙuri. Haka yayi tayi har gaban motarsu Lamiɗo, cikin sanyi ya rusuna gaban marfin motar, tare da jinjinawa Lamiɗo kana yace. "Tuba muke Lamiɗo, ga hanya an buɗe". Wani irin sanyi da daɗi Lamiɗo yaji, gashi duk da Gwamnatin ta kasance ta musulmi siyasa ta hanashi adalci. Gashi wanda ba nasu ba ya zantar da adalci". Haka ya rinƙa bawa mutanen cikin motocin haƙuri suna wuce. a haka har yaje mota ta ƙarshe, Yana isa yasa hannu ya buɗe marfin motar. Wani irin kallo mai cike da ma'anoni yakeyi mishi. sai kuma yayi wani munafukin murmushi. Ganin hakane ya ja motarshi ya tafi. Washe gari ranar Litinin. Da hantsi Hajia Kubra aminiyar Umaymah ta iso. da yan rakiyanta. Kai tsaye har bakin part ɗin Sheykh Jabeer sukayi parking. Kana ta shiga cikin Cikin farin ciki suka ruggume juna ita da Umaymah cikin dariya Umaymah tace. "Hajia Kubra amman kin shamma ceni". Murmushi tayi tare da cewa. "Ato ai naga kin zaƙu kina son ki koma Tsinako ne nace bari dai in hamzarta indawo". Ta ƙarishe mgnar tana zama tare da miƙa Jalal car key ɗin ta tace. "Yauwa Jalal Jamil ku shigo da kayayyakin." To sukace kana suka amshi key ɗin suka fita. Nan suka buɗe motoci biyun wanda tazo a ciki da wanda drever'nta yazo a ciki. Nan suka rinƙa kwatsar akwatunan suna shigarwa. Set biyune masu fasifar kyau da tsadan gaske. Umaymah kuwa tuni tasa Juwairiyya ta cika Hajia Kubra kayan kwalam a gabanta. Robar Inabi ta ɗauka tana buɗewa ta kalli Umaymah cikin raha tace. "Hajia Khadijah ina ɗiyar tamu". Cikin murmushin Umaymah ta ɗan juyo ta kalli ƙofar falon Shatu tare da cewa. "Hibba! Hibba!!". "Na'am". Hibba ta amsa tana miƙewa tsaye Kizo keda Aysha ga Mommy Kubra tazo". Cikin jin daɗi Hibba ta miƙe tare da cewa Shatu. "Wayyo Aunty Aysha tashi muje". Cikin nitsuwa ta miƙe tsaye, mayafin Arabian gawd ɗin dake jikinta ta gyara. Kasan cewar shi guntu yasa bai ida rufe mata jelan gashin kanta data tubkeba. Suna fitowa Hibba ta faɗa jikin Hajia Kubra tare da cewa. "Oyoyo Mommy Kubra". Ruggume Hibba tayi tare da cewa. "Oyoyo My Muhibbat". Sai ta kuma kalli Shatu dake ƙoƙarin rusunawa. da sauri ta riƙo hannunta tare da cewa. "Zo nan kusa dani kema ɗiyata ce, bakya ganin yadda Hibba tayiin". Murmushi tayi sabida fara'ar matar ya burgeta cikin sanyi yace. "Mommy Ina wuni". "Lfya lau ɗiyata ya gida ya baƙun ta?". Cikin girmamawa tace. "Alhamdulillah". Hibba ce ta zamo daga jikinta tare da cewa. "Mommy wannan kayanfa?". Murmushi Hajia Kubra tayi tare da cewa. "Na Aunty Shatu ne". Da sauri ta zamo tare dasa hannunta zata buɗe akwatin dake gabanta, cikin haɗe fuska Umaymah tace. "To uwar azarbaɓin, waya saki. Tashi kije ki kira min yar uwata kice mata ga saƙon sun iso". Da sauri ta miƙe tare da cewa. "Aunty Aysha zo muje Side ɗin Hajia Mama mu kirata". Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa. "A a sai kin dawo". Tana faɗin haka ta miƙe ta koma falonta. Ummi Aunty Juwairiyya da Umaymah kuwa kallon junansu sukayi. Hajia Kubra ce tace "Kunya ko". Murmushi Umaymah tayi tare da badda zancen da haka. Ita kuwa Hibba da sauri taje ta kira Hajia Mama, aiko kusan tare suka taho, da Botool. Koda sukaje Umaymah ta aika Ummi a matsayin ta na Jakadiyarsu take ta sanarwa Gimbiya Aminatu tazo taga kayan auren da ta haɗa amryar Jazlaan ɗin ta. Bayan duk sun zone, Suka bubbuɗe akwatunan, goma sha biyun nan duk cike suke maƙil da kayayyakin bukatar amare. Abun sai wanda ya gani. Lokacin da aka buɗe akwatunan turaruka gaba ɗaya Side ɗin ya cika da ƙamshi tako ina. Manyan akwati biyu aka cika da dogayen riguna masu masifar kyau da tsada da taushi. Sai kuma biyu da aka cikasu da atampopi da shadda da lace. Sai kuma babba daya da aka cikashi maƙil da laffaya masu azabar kyau da tsada, babu kalan da babu a ƙalla sun kai kala ashirin da huɗu. Sai biyu daga ciki ƙananan kayane birjik Sai wani babban bakko, da aka cikashi da takalma a ƙalla kala goma sha biyar, bakwai daga ciki sunada hand bang, hudu daga ciki pase garesu. hudu kuma masu siffan sayyadane masu kyau. Sai kuma kayan tarkacen mayuka da sabulai na jiki da kai. Kai abun dai masha ALLAH. Da sauri Hibba ta zari takalma uku daga ciki takalmomin ta nufi bedroom ɗin ta da sassarfa tana cewa. "Aunty Aysha bari inzo ki gwada takalman nan, Ni dai sai inga kamar zasuyi miki kaɗan.". Tana shiga ta ajiye mata takalman a gabanta tare da cewa. "Gwada mu gani". Sosai takalman sukayi mata kyau, haka yasa ta zura ƴar kekyawar farar ƙafarta. Ai kuwa tayi mata cib-cib cikin dariya Hibba tace. "Ashe dai zai miki dai-dai". Murmushi tayi tare da gyaɗa tare da cewa. "Uhumm ba kin raina ƙafar tawaba". Daga nan ta juya, ta koma falo, nan ta samu Hajia Mama na cewa. "Wannan kaya haka Khadijah kin kashe kuɗinki a banza ƙanwata wannan yarinyar ba matar auren Muhammad bane". Cikin yin ƙasa da murya Umaymah tace. "Karkice haka Hajia Mama". Cikin ɓacin rai tace. "Khadijah ai dole ince haka, ke har yanzu baki gane cewa wannan yarinyar ba matar ahlin masarautar Joɗa bace, a gabanki fa, taƙi shan madarar Barka da zuwa Masarautar Joɗa. ta kuma kwaɓar dana hannun Jabeer wanda shine na Barka da zama magidanci. Hakafa zatayi ta kwaɓar da duk wani abun ci gaba ko nasara a rayuwarsa." Batool ce ta ɗan gyara zamanta cikin danne baƙin cikinta tace. "Uhummm a tsallake ƴan uwa jinin sarauta aje a kwaso mishi bagidajiya ba fullatanar daji, ba dole tayi halin dabbobiba tunda cikinsu ta tashi. Tasan menene masarauta bare tasan ƙai dojinshi da kuma, nasabarsa." Ta ƙarishe mgnar tana son maida hawayenta. Allah ya sani tana son Sheykh Amman ta lura, Hajia Mama taƙi sa baki abin yayi gashi har an auro mishi wata. Cikin murmushin Umaymah tace. "Batool zaki auri mai matane?". Cikin sauri tace. "In wanine bazan auri mai mataba, amman in Hamma Jabeer ne, wlh ko mata uku gareshi da ƙwar-ƙwara biyar in zai aureni zan yarda in zama ta tara, Kowa ya iya allonsa ya wonke". Murmushi Hajia Kubra tayi tare da cewa. "A lallai kam". Ita dai Hajia Mama miƙewa tayi ta fice rai a ɓace. Gimbiya Aminatu kuwa, murmushi tayi tare da cewa. "Ji ƙarfin hali ita kafin uban Jabeer ya arota Allah ne kaɗai yasan adadin dukiyar da aka narka. Sam iyayen mazan yanzu sai a hankali." Cikin sauri Hajia Kubra tace. "Matan ƴaƴan ma na yanzu ba irin na da bane. Shiyasa aketa samun matsala tako ina kowa kansa ya sani". Ita dai Umaymah murmushi tayi tare da cewa Juwairiyya. "Juwai keda Hibba kuje ku kimtsa mata komai a ɗakinta ku shirya mata drower'nta. Kana ku kimtsa mata kan dreesing mirror. Kai kuma Jamil ɗauki bakon takalman nan ka juye takalman. Juwairiyya kisa Shadda bakwai lace bakwai, atampa bakwai, kampala Bakwai, swiss voile bakwai. A cikin atamfofin kisa Super wax biyu English wax biyu, Holand biyu sai swiss atampa ɗaya. Sai kusa a bakon. Jamil sai ka kaisu wurin telan Juwairiyya. Ayi ɗinkunan da wuri." Haka kuwa akayi akani komai yadda tace. Bayan sun gama kimtsa mata komai da jera komai a muhallin shi ne, Suka fita, sannan Umaymah ta shigo, gefenta ta zauna cikin nitsuwa tace. "Ɗiyata ga kayan sawarki naso ace sun iso tun kafin yau. To sha'anin nesa, shiyasa kikaga bai iso da wuriba, duk kayan nakine kisa wanda kikeso a sanda kikeso. Sabida ke akayi komai." Cikin tarin jin daɗi da ganin darajar ta tace. "Ngd Umaymah Ngd matuƙa, Allah ya saka da al'khairi". Amin Amin tace kana ta miƙa tare da cewa. "Naga kina son dogayen riguna ranar da zan aika kince su kikafi so, gasu an kawo miki su da yawa". Murmushi tayi tare da cewa. "Nagode sosai Umaymah Allah ya ƙara girma". Amin Amin tace kana fita. Ita kanta Shatu tasan babu ƙaranta a duk kayan da aka jinbga mata. Komai mai kyau ne. Yau talata da hantsi suna zaune a falon. Hadimai sukayi sallama da Jakadiyarsu, bayan ta basu izinin shigowane. Suka fara shigowa suna wucewa kitchen da kayayyakin abinci kamarsu shinkafa ta tuwo buhu biyu ta wara buhu biyu, sai gero ƙaton buhu, wanda a surfe yake, taliyar manya data yara katon biyar-biyar, kiret-kiret na ƙoyaye biyar, jarakunan mai dana manja bibbiyu katon ɗin maggi ɗaya dasu doya da dankalin turawa mai yawa. Haka suka rinƙa jida suna kaiwa store. Bayan sun gamane, Umaymah ta kalli Aysha cikin yin ƙasa da hannu ta miƙa mata dubu biyar. Kana tace. "Engo basu tukuici, wannan daga store ɗin masarautar Joɗa ne, duk ko wani sashi haka ake kai musu in Ramadan ya kawo kai." Cikin jin kunya tasa hannu ta amshi kuɗin kana ta miƙa Hibba tare da cewa. "Hibba basu". Da sauri Umaymah ta girgiza mata kai, sai kuma ta kalli hadiman suna shirin fita tace. "Kuzo matar Sheykh na kiranku". Ɗaya daga cikin sune, ya dawo. a hankali ya iso ya rusuna gaban Shatu tare dayin ƙasa da kanshi. Cikin nitsuwa yace. "Gashi mun gode Allah ya kaimu baɗi lfy". Amin Amin suka amsa baki ɗayansu. Kana ya amsa ya miƙe ya fita. Su kuwa sukaje sukaci gaba da hirarnsu. Washe gari kuma ranar Laraba. Wanda ana zaton kwana huɗune ya rage Ramadan, koma biyar. Umaymah ce zaune ita da Sheykh, ido ya zuba mata har ta gama mgnar da yakeyi na batun ran jumma'a fa zasu koma. ta jaddada mishi kadafa ya mance yanzu yanada mata. Kanshi ya jingina jikin kujerar tare da son kauda wannan zancen yace. "Jadawalin jerin malam da zasuyi tabsirin Ramadan a jahohi mabanbanta ya fito". Cikin alfahari da hakan tace. "Wacce jahar kuma aka turaka bana?". Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa. "Tun da da nake ta son a barni a jihata, kullum sai a turani wata jihar, sai bana kuma da nake son in tafi wata jihar suka barni a nan". murmushin jin daɗin hakan tayi tare da cewa. "Alhamdulillah kaga darajar aure ko". Bai tanka mataba, itama bata jira ya tanka matanba tace. "Ya batun tafiya umarah kuma". Kanshi ya ɗan ɗago ya kalleta hannunshi yasa ya shafa sajenshi cikin nitsuwa yace. "Sha biyar ga watan zan tafi". Da sauri tace. "Zaka tafi ko zaku tafi?". Kanshi ya ɗan dafe tare da nazarin ya zai yanke mgnar cikin nitsuwa yace. "Eh zamu tafi". Yalwataccen murmushi tayi sabida bata gano manufarsa ba. Cikin kula yace. "Kefa yaushe zakuje". Tana ƙoƙarin miƙewa tace. "Shatara ga watan Ramadan zamuje". Da sauri yace. "Umaymah". Komawa tayi ta zauna tare da cewa. "Na'am". Cikin kwaɓe fuska yace. "Muna mgna kuma zaki tafi, me zakije kiyi ne a can ". Cikin murmushin tace. "Zanje wurin Aysha akwai mgnar da zamuyi". Ba tare da ya san waye kuma wacce mai suna Shatu'n ba yace. "Uhumm shike nan". Cikin kula tace. "Ko akwai wani abu ne?". Kai ya girgiza mata, ganin haka yasa ta miƙa ta fita. Shi kuwa ya miƙa ya shiga bedroom ɗin shi dan yana son yin baccin tsakanin azahar da la'asar, sabida wannan baccin yanada al'fanu. Dan zai taimakawa mutun wurin tashi da dare. Ita kuwa Umaymah a falo ta samu. Shatu da Ummi. Dan Hibba tana can sashin Aunty Juwairiyya. Gyara zamanta, tayi tare da kallon Ummi cikin nitsuwa da shaƙuwarsu tace. "To Ummin Jabeer, Ni dai tafiya ta ƙara to in Allah ya kaimu, jibi jumma'a zamu tafi, zan barki da sauran aikin". Cikin sauri Ayshs ta ɗago kanta ta kalli Umaymah cike da fargaba tace. "Umaymah tafiya?". Ta ƙarishe mgnar cikin sanyi. Ido Umaymah ta ɗan zuba mata cikin karantar yanayin da take ciki tace. "Eh Aysha zamu tafi jibi da yamma jirginmu zai tashi zamu tafi Hibbab ya dawo yace yana kewar Hibba". Da sauri tace. "Ayyah Umaymah dan Allah kada ki tafi da Hibba, ayyah Umaymah a bar mana Hibba". Ta ƙarishe zance fuska cike da rauni". Shiru Umaymah tayi sabida ganin hawaye suna shirin zubo mata, sai kuma ta miƙa da sauri ta nufi ɗakinta, sabida jin bazata iya danne hawayen nataba, Allah ya sani ta saba da Hibba sosai, itake ɗebe mata kewar Junainah, Umaymah ke meye mata gurbin Ummeynta, sannan wai duk zasu tafi. Tabbas ta saba da Ummi amman ba kamar Umaymah. Sam tama kasa yarda da Juwairiyya kam ma. Koda ta tafi, Umaymah da Ummi murmushi sukayi. Cikin sanyi Umaymah ta fara mgn da Ummi bisa dukkan alamu mgnace ta sirri domin nima banjisuba. Na dai ga daga ƙarshe duk suna zubda hawaye. Bayan sallan isha'i ne Hibba ta nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu. Dan amsowa Hamma Jabeer ɗinsu aiken da ya mata. Bayan ta dawone ta ajiye Foodflaks a gaban Umaymah tare da cewa. "Umaymah gashi, a kai mishi". "Jeki gayawa matarshi tazo ta kai mishi." To tace tare da juyawa ta nufi falon Shatu. Ganin bata falone yasa ta wuce bedroom. A kwance ta sameta bakin gado. Ta konta rubda ciki, tanayin kuka mai sanyin sauti. da sauri ta zauna gefenta tare da cewa. "Aunty Shatu meya faru?". da sauri tasa tafin hannunta ta shere hawayen, kana ta miƙe zaune hannun Hibba ta kama ta riƙe tare da zuba mata ido cikin sanyin murya tace. "Please Hibba mu zauna kada ki koma, ki cewa Umaymah zamuyi azumi a nan." Shiru Hibba ta ɗanyi kana ta ɗan yi murmushi tare da cewa. "To zan gaya mata, kuma kema ki gayawa Hamma Jabeer in shine yace mata ta barni bazata hanani ba." Cikin sanyi tayi shiru, alamun nazari, ta ina? kuma ta yaya? yaushe zata mishi mgna? Mutumin da ko kallon inda take bayayi! Anya kuwa yama sanni ne?!. Tayi mgnar zuci. Ita kuwa Hibba cikin murmushi tace. "Allah muwa in kin gaya mishi za'a barni". kai ta jinjina tare da komawa zata jingina da kan gado, da sauri Hibba ta kamo hannunta tare da cewa. "A' a taso Umaymah tace kizo". To tace tare da miƙewa, a tare suka fito falon. Cikin kulawa Umaymah ta nuna mata Foodflaks ɗin. "Ɗauki ki kai mishi falonshi". da sauri ta zaro ido cike da mamaki, gane hakane yasa Umaymah kauda kanta, ita kuwa Shatu shiru tayi tare da zubawa kulolin idanu. Muryar Ummi ce ta kuma ratsa kunnuwanta. "Ɗauki ki kai mishi in dare ya ɗan yi nisa bazai cibafa". Bazata iya musu musu da gardama ba. haka yasa cikin sanyin jiki ta sunkuyo ta ɗauki Foodflaks ɗin, kana ta juya a hankali ta nufi corridor da zai kaita Side ɗinsa, tafiya takeyi cikin nitsuwa kanta a sunkuye. A bakin ƙofar falon ta ɗan tsaya cikin sanyi murya can ƙasa tayi sallama , yadda ita kanta batayi dan wani ko zaton wani yajiba. Yana can Dinning area, yana zaune bisa ɗaya daga cikin chairs ɗin Dinning table ɗin. Yasa System nashi a gaba. hankalinshi duk yana kai, ga woyoyi a ƙalla uhu suna gefenshi. sai cup mai cike da madarar shanu mai ɗumi. Murya can ƙasa bisa saman tattausan jajayen laɓɓansa ya amsa sallamar da ya jita raɗau cikin kunneshi sai dai bai fahimci mai muryar kai tsayeba, asalima ji yayi kamar muryar Umaymah ce. A hankali ta turo kanta ta yaye labulen kana ta sako ƙafanta cikin, falon da bata son koda kallon ta inda yake, ba don bai mata kyauba sai dan wasu manyan dalililai da abubuwan da take gani tako ina a falon, A hankali take taku, i zuwa inda ta hangoshi zaune ya bawa ƙofar shigowa baya. cikin nitsuwa ta take step ɗin forko, tare da ɗago kai ta kalli ƙeyanshi. baki ta murguɗa tare da taɓe bakin kana ta manna mishi harara bisa tattausan suman ƙeyan nashi. A haka ta ƙara motsowa, shi kuwa Sheykh Jabeer tabbas yasan da mutun a bayanshi. Ya kuma gano wancan abun ne, shiyasa ko ta kanta baiba. Aikin da yasha mishi kai yakeyi ba kama hannun yaro. Da sauri ta ajiye Foodflaks ɗin bisa glass ɗin Dinning table ɗin, wanda hakan ya bada wani sautin. Idonshi ya ɗan rumtse tare da buɗesu, kana yaci gaba da aikinshi ko gefen da take bai kalla ba. Ita kuwa sai ruwan harara taketa manna mishi tako ina. kana kuma dai tana tsaye bata juya ba. a ƙalla 55 second bata tafiba, bata kuma ce mishi komaiba, sai hararan da takeyi mishi har ta fara jin idonta na ciwo, sabida harara ba ɗani'arta ta yau da kullum bane, sai in tana masifar jin haushin mutun da tsanarsa take mishi wannan abun. Bai kulataba, ganin ba kulata zaibane yasa ta ɗan ja wani gajeren tsaki can cikin maƙoshinta, a zatonta baijiba. shi kuwa Sheykh Jabeer kanshi ya ƙara rusunarwa sabida sam ya lura wannan abun ba kunya ne dashiba. Cikin murhuɗa baki da harara tace. "Dan Allah ka cewa Umaymah ta bar min Hibba muyi azumi a nan". Ta ƙarishe mgnar da ɗan ƙarfi. Shiru yayi tamkar bai jitaba ko baisan da ita a wurinba, Sabgogin gabanshi yakeyi tamkar babu wani halittan dake wurin. cikin kufula ta kuma cewa. "Dan Allah kace a barta muyi azumi anan". Ko gezau baiba. Sai dogayen fararen yatsunshi da yake sarrafawa bisa ma dannin System ɗinsa tamkar shiya ƙirƙirota. Shi sauƙinshi ɗaya tunda yanzu zuciyarsa ta dena bugawa da tsinkewa in mayyar tana kusa. A karo na uku ta kuma yin mgna tare da juyawa ta fita. Bai kulataba bashi kuma da niyar kulata. Ita kuwa Shatu cikin takaicin sheretan da yayi ta fito. Ita in ma badon batun Hibba ba mai zai sa tayi wa wannan mutumin mai ɗan karen mannin hauka da ƙasaita mgn. A falo ta samu su Umaymah dasu Jalal, gefen su ta ratsa ta wuce, da sauri Hibba tabi bayanta. Tana shiga tace. "Aunty Aysha me yace?". Cikin nuna damuwarta tace. "Uhum yace Umaymah ce taƙi, sai dai in ita zamuyiwa mgn". Ta ƙarishe mgnar da nazarin ta yayama zata cewa Hibba tayi mgna bai ko kalli inda takeba bare ya kullata. Hibba kuwa da sauri ta juya tare da cewa. "To bari inje in lallashi Umaymah." To tace wanda. Tunima Hibba kam ta fita. A gaban Umaymah ta zauna cikin sanyi tace. "Ayyah Umaymah dan Allah a barni inyi azumi anan, kinga Aunty Aysha ta roƙi Hamma Jabeer yace ki barni yace kin yarda ne, gata can tana fushi". Cike da mamaki da jin daɗin yadda akayi sukayi mgna dashi, har ya gaya mata yadda sukayi dashi jiya kan ta bar Hibba tace a a. Jamil ne ya ɗan kalli Umaymah tare da cewa. "Dan Allah Umaymah ki barta, in anyi salla Ni da kaina zan dawo miki da ita tunda jakar ratayawarki ce ita". Cikin dariya Ummi tace. "Eh dan Allah ki barta in dai mahaifinta zai yarda, kinga tana ɗebewa ɗiyar taki kewa". Murmushi Umaymah tayi kana, ta kalli Jalal da bai sa musu bakiba. Aunty Juwairiyya ma magiya take a bar Hibba, hakane yasa Umaymah tace to ba matsala zata bar musu ita aron wata ɗaya ran salla dai zata koma, cikin jin daɗi sukace sun yarda. Ai da gudu fa Hibba taje ta gayawa Shatu. Sosai taji daɗi har ta ɗan saki jiki. Shi kuwa Sheykh Jabeer, ko inda Foodflaks ɗin suke bai kallaba, sabida ba tsarinshi bane cin abu mai nauyi in dare yayi, haka yasa iya madarar yasha, kana yaci gaba da aikinshi. Washe gari ranar Alhamis, wuni Umaymah tayi tana shirye-shiryen komawa. Ta sallami duk mutanen da take mutunci dasu a fadan. Dama cikin masarautar Joɗa cewa Gobe jumma'a da mangriba zata koma. Washe gari ranar jumma'a, da misalin karfe sha biyu. Duk suna zaune a falon harda Jafar, Jalal, Jamil, Imrane, Ya Hashim, duk suna cikin shigar jumma'a. Dakon fitowar Sheykh suke jira. Umaymah da Ummi da Aunty Juwairiyya kuwa, suma suna nan, cikinsu ana ɗan hira. Hibba kuwa da Shatu suna kitchen dan Hibba tace in Shatu ta iya awaran couscous ta koya mata. Suna nan zaune, Hajia Mama da hadimanta Suka shigo. Cikin jin daɗi Umaymah tace. "Yanzu nake tunanin zanzo Side ɗinki Adda na". Murmushi tayi tare da cewa. "Oh ai bazaki zoba, yadda kike tsakiyar yaranki yar uwa kam an manceta". Murmushi sukayi baki ɗayansu, Batool da yanzu ta shigo da wasu hadiman suna rirriƙe da manyan bokitayen kande tsiraran masu cike da markaɗeɗɗen gyaɗa na kunu da miya sai ƙananan su kuma turaren wutane a ciki da biyu ɗaya dakekken yajin daddawa ɗaya dakekken yajin borkono komai bibbiyu. Sai galullukan man shanu. Da na zuma sai na Humra, kana sai manyan bako guda biyu. cikin murmushin Umaymah tace. "Iye Addana me na samu hakane?". Cikin sakin fuska tace. "Abubuwan daɗi nasan kina son kayayyakin gargajiya". murmushi tayi tare da cewa. "Duka wannan ai yamin yawa". Kallon kayayyakin tayi tare da cewa. "Keda su Ummi ne, suma za suyi amfani dashi a Ramadan, Musamman ma da ɗan naki anan zaiyi azumi bana". Cikin jin daɗi Umaymah ta kwallawa Hibba kira tare da cewa. "Kizo keda Aunty naki". To sukace kana suka kashe Gas ɗin da yake dama sun gama aikin. Suna isowa Hibba taje ta zauna kusa da Hajia Mama da sauri tare da cewa. "Hajia Mama an barni a nan zamuyi azumi". Cikin murmushi ta shafa kanta tare da cewa. "Kai naji daɗi na." Sai ta kuma kalli Aunty Juwairiyya tare da cewa. "An kai miki naki kayan Side ɗinki". Godiya tayi. Ita kuwa Umaymah hannun tasa ta jawo bako ɗaya ta zuge zib ɗin shi ta fara fiddo ledodin dake ciki wanda dakekken busasshen kayan miya ne kamarsu. Kuka, kuɓe, daddawa, citta, kanumfari, ganyen na'ana, zogale, da dai ire-iresu ne a ɗaɗɗaure a manyan ledodin masu layin baki da fari. Cikin jin daɗi kayayyakin Umaymah tace. "Kai nako gode naji daɗin kayan miyar nan, dan mu wurinmu suna wuyar samuwa." Sai kuma ta juyo ta kalli Shatu dake zaune gefenta, Tayi wani irin kici-kici da fuska babu alamun wal-wala. Cikin nuna jin daɗi tace. "Ɗiyata ga kyautan Hajia Mama, komai bibbiyu ne ɗaya naki ɗaya nawa ne, kiyi godiya". Cikin wani irin kallo mai cike da ma'anoni da sarƙafe-sarƙafe ta gyara zamanta, tare da komawa ta jingina da kujera, ƙafarta ɗaya ta ɗaura bisa ɗaya tare da fara karkaɗa ƙafar cikin fuska a haɗe kana a daƙile ta nuna kayan tare da cewa. "Bama so, Umaymah Bama buƙata". Cikin tarin mamaki da al'ajabi duk suka juyo gareta suka zuba mata ido. Ummi da Umaymah kuwa har suna haɗa baki wurin cewa. "Sabida me? Akanme zakice bakya so?". Ba tare da ta kallesu ba tace. "Ba cewa nai bana soba, cewa nayi bamaso, itama Umaymah bata so." Cikin tsananin mamaki suka bushe suna kallonta, Jalal ne ya zuba mata ido cikin haɗe fuska. Hajia Mama kuwa wani irin kallo mai cike da tsoro da mamaki da al'hini da jin tsanar Shatu cikin ranta, ta rasa me wannan yarinyar take nufi da ita, ta kasa gano me take gadara dashi. Cikin tarin takaici da zafin rai tace. "To kuma baki isa da gidan ba, Bare ki zana layi a biki, ke in banda rashin sanin darajar manya har zaki gaya min haka, ko gidanku ba manya ne?." Cikin isa da ɗaga murya tace. "Yesss! Gidanmu babu manya irinka, Bama so bazamu amsaba ki tattara tarukucenki kije ki bawa wasu can ba dai muba". Cikin tashin hankali Umaymah ta daka mata tsawa tare da cewa. "Ke Aysha ki nitsu kisan da waye kike mgna". Cikin ɗaga murya tace. "Na sani Umaymah na sani nasan da wacece nake mgna kece bakisan wacece itaba". Cikin mamaki da sauri Sheykh ya ƙarisa fitowa cikin tamfatsen falon shi. sabida ya gama shirin jummarsa, jiyo hayani da hargowane yasa ya nufo falon da sauri. To jiyo muryar Umaymah ne yasashi buɗe ƙofar falon da hamzari ya fito. Da sassarfa ya nufo falon. Dai-dai lokacin daya isone, Aysha ta miƙe tsaye cikin faɗa da tsawa ta nunawa Hajia Mama da hadimanta da Batool hanya tare da cewa. "Maza ku tattara waɗannan banzayen tarkacen naku ku tafi dashi, ku ɓace min da gani. Ku fita daga nan! Ku fitarmin gidana". Ta ƙarishe mgnar da ƙarfi. Wani irin miƙewa tsaye Umaymah tayi tare da yin sauri tasa hannunta ta....! By *GARKUWAR FULANI* Ta kamo hannun Jalal da ya miƙe tsaye da nufin yarfa mata mari. Cikin wani irin masifeffen tsana, Hajia Mama takalli Shatu. Kana da sauri ta juya ta nufi hanyar fita. Sheykh da tunda ya fito yake tsaye tamkar an dashi ne, yayi saurin bin bayanta tare da cewa. "Hajia Mama! Mama!! Mama dan Allah kiyi haƙuri, kizo karki fita Please Mama karki fita, babu wata halitta da zata miki iyaka da sashina, in kin tafi kenan kinbi umarninta." Cikin tashin hankali yake waɗannan kalaman yana mai binta a baya. Jamil kuwa miƙewa tsaye yayi ya zubawa Shatu idanu tamkar zasu faɗo ƙasa. Aunty Juwairiyya kuwa, wani irin kallo mai sarƙafe da ma'anoni takeyiwa Shatu. Ya Jafar kuwa wani irin kallo mai surke da murmushin jin daɗi yakeyiwa Aysha. Ummi kuwa tuni jikinta rawa yakeyi da abinda ya faru. Imran, Ya Hashim, kuwa ido suka zubawa sarautar Allah. Hibba kuwa kuka takeyi tare da riƙo hannun Shatu tana ja tare da cewa. "Aunty Aysha ki bari, Mamace fa! Kizo mu tafi ɗaki". Tanayi tana jan hannun Shatu da ƙarfin tsiya, dole yasa Shatu ta bita a baya. Umaymah kuwa wani irin tashin hankali da tafasan zuciyane ya dirar mata lokaci ɗaya. Da wani irin kallo tabi bayan Aysha dashi. Duk wanda ya ganta yasan tana cikin tashin hankali. Gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi. Sun daɗe a haka, da kyar dai Cikin wani irin tafasan zuciya ta saki hannun Jalal. Tare da komawa ta zauna. Da yatsa ta nuna musu hanyar fita daga falon. Murya a hargitse tace. "Kul kada ka sake tunanin gigin ɗaga kayi nufin taɓa lfyar Aysha, bana so kul. Maza Ku tafi masallaci". Sai lokacin suka jiyo sautin muryar Jabeer yana Hudba. Wanda daga jin muryarsa kasan yana cikin baƙin ciki. Wani irin numfarfashi Jalal ya sabke tare da yin koffa kana ya juya ya nufi hanyar fita shi matsalarsa meyasa Umaymah na mgn Aysha na mgn Umaymah na hanata abu tanayi. Haka su Jamil da su Imran da ya Hashim da Ya Jafar suka fita. Ita kuwa Aunty Juwairiyya wani irin tashi tayi ta fita ta nufi Side ɗin ta. Ya zama Ummi da Umaymah ne kaɗai suka rage a falon. Shiru sukayi tamkar ruwa ya cin yesu. "Uhuhhmmmm". Umaymah ta fesar da wani zazzafan numfashi mai ɗumi. Hakama Ummi tagwayen numfarfashi masu nauyi ta sauƙe. Kallon juna sukayi, cikin shiga al'hini wannan al'amari cikin tsoro da karaya Umaymah tace. "Toh wai meye hakan? Meke faruwa ne? Me hakan yake nufi? Kaina ya kulle. Wani zagon kasan kuma aka shirya tsakanin Shatu da Hajia Mama ko dai dama da zagon ƙasan ne?. Wake saƙa gadar zare, muna na bi ta kai ya rubta da mu". Wani numfashin Ummi ta fesar tare da cewa. "Tabbas akwai babban al'amarin dake faruwa wanda bamu saniba Ni tsorona ɗaya kada a juya ƙoƙwalwar yar mutane." Shiru sukayi cikin ta'ajjudin al'amarin. A hankali suka miƙe a tare suka nufi ɗakinsu jin har an idar da sallan a masallacin. Al'wala sukayi kana sukayi salla daga bisani suka, fara tattauna wani abu na sirrin masarautar Joɗa. A cikin ɗakin Shatu kuwa, tunda suka shiga ta kwanta bisa gado. Bacci tayi bacci, hakama Hibba. Sai ƙarfe uku dai-dai Shatu ta tashi. Cikin kasalan baccin da bai gama isarta ba, ta miƙe ta shiga bathroom. Wonka tayi tare da al'wala. Bayan ta fitone, ta tada Hibba, ita kuma ta kabbarta sallah. Kafin ta idarma Hibba ta fito, gefenta tazo itama ta kabbarta sallan. Basu tashi bisa sallayan ba, sukaji kiran aallan la'asar. Haka yasa sukayi sallan. Suna idarwa Hibba ta miƙe ta nufi ɗakin Umaymah. Ita kuwa Shatu ninke sallayar tayi kana ta dawo gaban dreesing mirror. Mai ta shafa tare da ɗan murza fauda a fuskarta, kama ta shafa man baki. A cikin sanyi taje gaban drower'nta, hannu tasa ta buɗe drower'r, wata tattausar doguwar riga mai masifar kyau ta zaro. Kalar rigar Black blue mai sheƙi, saman rigar a ɗan tsuke daga ƙasan ƙugunta kuma a buɗe, yanada wasu duwasu kamar na Daimond daga sama har ƙasan gaban rigar. Hannunta kuma masu faɗi. Tayi kyau sosai cikin rigar, dogon gashinta ta haɗa ta tubke wuri ɗaya ta kitse jelar kana ta nannaɗe jelar a ƙeyarta, sannan tayi rolling kanta da mayafin wanda dai dai inda zai zauna a goshin akwai duwatsun. Turare ta fesa, kana cikin sanyi da kasala ta nufi, falo. A falon ta samu, Hibba a kwance tayi shiru. Ganin bata gan fitowarta banema, Yasa ta nufi inda take gefenta ta zauna tare da cewa. "Hibba ɗauko mana awaran". Cikin sanyi Hibba tace. "To". Kana ta miƙe ta nufi falon, jin shiru ba kowa a cikine, yasa ta nufi kitchen a hankali-hankali. Foodflaks ɗin da suka sa awaran da suka soya ta ɗauko. Tana dawowa ta zauna kusa da Shatu tare da cewa. "Gashi". Kai ta gyaɗa mata tare da nuna mata kitchen ɗin ta, tace. "Ɗauko mana plate da roban yajin da Gimbiya Aminatu ta aiko mana. Kizo mana da ruwa". Ba tare da tace komaiba ta juya ta tafi. Bayan ta dawone suka zauna suka fara cin wanda suka zuba. A can falon Hajia Mama kuwa, duk mgnar da Umaymah da Ummi keyi, shiru tayi ta zuba musu ido. cikin sanyi Umaymah tace. "Addana kiyi haƙuri, kin san yaran sai a hankali, dan Allah kada kisa wani abun a ranki wata ran ko ance tayi miki bazatayi ba". Murmushi tayi mai cike da ma'anoni kana tace. "Uhummm ba komai Khadijah jekici gaba da shirin tafiyarki, karki damu kinji". Ido suka zuba mata domin duk basu gamsu da mgnarta ba, to amman ya zasuyi tunda tace ba komai. Haka suka tashi suka dawo falon. Yau su Jalal ma basu zoba. Shi kuwa Sheykh Jabeer, tunda aka idar da sallan azahar ya dawo, ya wuce su Umaymah a falon ba tare da yace musu ƙalaba. koda ya shiga ɗakin ya samu yayi bacci tsakanin azahar da la'asar kamar yadda ya saba, hakan bai samuba. Sabida abubuwan dake ranshi. Bathroom ya shiga ya sakarwa kanshi ruwan sanyi, tare da fara yage towel ɗin dake hannunshi. haka yake tsaye a ƙasan ruwan har saida yaji an kira sallan la'asar. Nanne ya fita ya tafi masallacin. Bayan an idar da sallan ne ya dawo gida. Ganin babu kowa a falon ne yasashi zama, bisa kujerarsa. Ƙafarshi ɗaya ya ɗaura kan ɗaya. A haka su Umaymah suka sameshi. Gefenshi Umaymah ta zauna bisa kujerar dake kusa dashi. Ummi kuwa gabanshi ta zauna bisa carpet. A hankali ya buɗe kwayar idanunshi. Cikin tarin ɓacin rai ya kalli Ummi tare da cewa. "Ummi ina wannan fitsarerren abun da bai san darajar manya ba!?." Cikin sanyi Ummi tace. "Allah ya huci zuciyarka tuba takeyi, in sha Allah bazata sakeba, Hajia Mama da kanta ta yafe mata". Gyara zamanshi yayi tare da cewa. "Ummi ko dai kece kika bata dama da matsayin yiwa Mama hakane?". Cikin sauri tace. "Wanne ni wlh bani bace". Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Umaymah da itama shi take kallo cikin ɓacin rai yace. "Umaymah har akwai wani abun da zai hana mama shigowa sashina? Har yaushe waccar babyn robar ta samu dama da ikon bada izinin shiga da fita cikin sashina da abinda ya shafi rayuwata? Me take nufi dani da iyayen nawa." Kauda ido Umaymah tayi daga kallonshi kana a hankali tace. "Ba isa bane! Akasi aka samu! Nifa inaga har yau Shatu'n bata gama sanin mutanen masarautar Joɗa da kuma dangantakar makusan tankaba, ayi mata haƙuri a mata uzuri a dai wannan karon". Juyowa yayi ya kalli Ummi tare da cewa. "Ummi a kira min waccar abar". Da sauri Ummi ta miƙa tare da cewa to. A falon ta samesu, cikin fuskar da babu yabo babu fallasa ta kalli Shatu dake gefen Hibba da alamun ta cire hannunta a cin awarar kanta ta ɗan kauda tare da cewa. "Kizo Sheykh yana kiranki". Kai ta gyaɗa tare da cewa "Toh". miƙewa tayi taje Dinning area ta wonke hannunta, kana tazo tabi bayan Ummi. A gabanshi Ummi ta zauna ganin haka itama ta zauna a gabanshi. shiru tayi tana kallon yatsun fararen sawunshi. Shi kuwa kanshi na gefe ba tare da ya juyo ya kalleta ba yace. "Ke ki shiga hankalin ki, kisan abinda kikeyi da wanda zakiyi! Ke har kin kai matakin da isar da zaki ƙaddamar min da iko da isa a cikin gidana? Ko dai ce miki akayi gidan nakine?". Kai ta gyaɗa mishi alamun eh ance mata gidan natane!. Wani irin tsuke fuskarsa yayi tare da ci gaba da mgna dan shi bai ga sanda ta gyaɗa kanba hakama Umaymah, sai Ummi ce kaɗai ta gani, su kuwa sai murmushi sukayi. Cikin kausasa murya yace. "In baki san darajar manya da iyayeba, to ki zama kurma bebiya makauniya a cikin giddannan kafin Ubangiji ya zantar da Hukuncin da ikon zamanki da barinshi dan ikone na Allah bana waniba. Har kin isama Mama tazo ki koreta dan idonki basu da ɗigon kunya. Ko karen gidannan baki da ikon hanashi abu da sakashi bare Mama. ke ta bawa abun ne da zakice bakya so. Kece mai bakin mgn uwar fitsararru ko?". Sam abinda bai saniba zuwa yanzu hankalinta, tunaninta nitsuwarta, jinta, da ganinta duk suna kan farar ƙamarshi ta dama, da zanen maciji ke liƙe kamar macijin na tafiya. Wani irin ba hagun numfashin ta sauƙe a hankali, tare da rufe manyan idanunta da azaban ƙarfi. Sabida gani takeyi Tamkar macicijin ne ma da kanshi ke manne a jikinshi yana kuma motsa ɗan bindinshi dake saman babbar yatsarshi. A hankali ta buɗe idanun kana tabi kan rumfar ƙafar da ido, inda take ganin zanen maciyar yabi. Kasan cewar a zaune yake ya kuma ɗan tattare al'kyabbar jikinshi. Shi yasa tana iya ganin har ƙarshen rumfar tafin ƙafar nashi. Inda iya nan jallabiyar jikinshi ta rufe. da sauri ta ƙara rusunar da kanta wai ko zata ga ci gaban tafiyar macijiyar. Umaymah ce ta ɗan kalleta cikin wata iriyar murya tace. "Ki tashi muje ki bawa Hajia Mama haƙuri, ku nemi yafiyarta ki kuma kiyaye gaba, kinji". Cikin sanyi tace. "Toh". Still Bata miƙeba, cikin ɗan ɗaga murya yace. "Tashi muje yanzu ki bata haƙuri, in ta haƙura kinyi babban Sa'a". cikin sanyin jiki ta miƙe tsaye. Shima miƙewa yayi, Ummi kuwa da sauri ta nufi ɗakin Shatu. Jim kaɗan ta fito da wata kekyawar al'kyabbar matan masarauta ta zuramata. Bayan ta gama gyrashi ne, tasaka hular. Shi yayi gaba ita kuwa. Tabi bayanshi Umaymah da Ummi suka biyo bayanshi. Suna isa bakin mashigar farfajiyar Side ɗin Hajia Mama, ta tsaya gis tare da yin ƙasa da kanta. Ummi ce tace. "Muje mana". Shiru batayi mgna ba, jin hakane yasashi juyowa, karon forko kenan da ya zubawa tsawonta ido. cikin ɓacin rai yace. "Muje ki lashe aman da kikayi da kanki". Cikin sanyin sauti tace. "Ni bazan shigaba". Da mamaki Umaymah tace. "Innalillahi wai ke Ayshs wani irin taurin kaine dake? Menene manufarki?". Murya can ƙasa yana rawa alum zatayi kuka ta kalli Umaymah tace. "Kiyi haƙuri Umaymah ki gafarceni, amman ni bazanje ba, in kuma zanje to ku ku koma, zanje ni ɗaya zan bata haƙuri". Cike da al'ajabi Umaymah tace. "To sabida me bazaki je da muba". Cikin faɗa Sheykh yace. "Sabida muna furci mana, ba zuwa zatayi ba, shiyasa zatace sai dai in ita ɗaya zataje, maza wuce muje a gabana zaki bata haƙuri". Cikin sanyi Umaymah tace. "Jazlaan barta mu tsaya mu jirata anan in dai zataje ita ɗayan". Kanshi ya dafe tare da cewa. "To wai Umaymah mu bayaninta ne da zamu tsaya muna jiranta". Ummi ce ta mishi alamun yayi haƙuri ya yarda. Shiru yayi tare da komawa gefen jerin bishi yoyin namiji kwanɗa ya zauna bisa kujerun silver dake zagaye da wurin wanda ko wani side akwaisu. Itama Umaymah da Ummi zuwa sukayi suka zauna. Ita kuwa Shatu a hankali ta fara taku ta nufi cikin farfajiyar, suna hangota har ta isa bakin ƙofar. turawa tayi ta shiga, kana ta maida ƙofar ta rufe. Bayan kamar 37 minutes ta fito. Cikin wani irin tafiya mai baiyana tsantsar jin daɗi, fuska cike da fara'a ta nufosu. A hankali ta isa gabanshi ciki ɗan ɗaga murya tace. "Na bata haƙuri ta yafe min, ta samin al'barka. Kaima kayi haƙuri ka yafe min". Da mamaki suka kalleta. Shi kuwa Sheykh Jabeer wari irin kallon tuhuma yayi mata, kana ya miƙe tsaye tare da cewa. "In ma ƙarya kikayi, ni ba'amin ƙarya". Sai ya kuma kalli Umaymah tare da cewa. "Umaymah kuje ki ƙarisa shirinki bari inje wurin Hajia Mama". To tace kana taja hannun Shatu suka tafi. Shi kuwa da Ummi suka nufi cikin Side ɗin Mama. Bayan sallan isha'i, cike suke a falon. Gaba dayansu, Umaymah zaune a tsakiyarsu da jakarta, Sheykh Jabeer na yi mata addu'o'in isa lfy suna amsawa da Amin Amin. Bayan sun shafa addu'o'in ne ta miƙe tsaye, tare da kallon su baki ɗaya, murya na rawa tace. "Jazlaan zan tafi, zan bar hankali na, a nan ko na koma banda nitsuwa, kullum ina cikin taraddadin abubuwanda yake faruwa, Jazlaan na sani kaine GARKUWAR yayanka da ƙanneka. Ga wani sabon nauyi ya ƙarun maka. Aysha baƙuwace bata san komaiba kam al'amuran Masarautar Joɗa, dan Allah in tayi abinda ba dai-dai ba kuyi mata uzuri. Ita komai a sabon abu zata ganshi abinda bata taɓa ganiba. Mun rabata da iyayenta yayunta ƙannenta mun kawota tsakiyarmu, mu kasance mata adalan masu masauƙi. Na sani Jazlaan ka fini sanin haka da kuma haƙƙoƙinta da suka rataya gareka." Sai ta kuma kalli sauran yaran yar uwarta ɗin tace. "Jalal, Jamil, Aysha matsayin yar uwarku take, yayarku ce, matar yayanku. Bana son raini especially kai Jalal, ban gamsu da irin mu'amalat ɗin ka da itaba. Babu wanda yake nuna min yadda nakeso a kanta sai Jafar, a duk sanda ya ganta zaiyi mata murmushi kamar yadda yake min, in yaga bata nan zaiyi ta dube-duben da nasan da yanada baki zai tambayeni lfyarta. Zan bar Hibba saboda itane, bana son taji kanta a matsayin bare." Shiru sukayi gaba ɗayansu sabida yadda take kuka da yin mgna tamkar mai bar musu wasiya, ko wacce wani tsohon damuwa ya taso mata. Sharce hawayenta tayi tare da cewa. "Ummin Jabeer zan tafi zan barki da sauran aiki, dan Allah ki kula da Shatu da mu'amalarta da Hajia Mama, ki nuna mata uwar miji ba abun rainawa bace". Sai kuma ta miƙowa Aysha da taketa kuka hannun ta jawota tsaye ruggume ta tayi cikin zubda hawaye tace. "I dan akaga damuna ana zaton yabanya zatayi kyau, kallon damuna nakeyi miki a cikin ahlin yar uwata. Ina jin zaki zamo mana haske mai yaye duhun daya maye ganinmu, tun kafin yau ni na sanki a mafarkina Allah ke nuna min ke a matsayin matar Jazlaan ɗin na, kuma Allah yana nunamin abubuwa da dama a kanki a cikin mafarkaina, wasu kuma sunma tabbata na gansu. dan Allah ki riƙe min Jazlaan amana, ki lura da ƙannenshi yadda zaki lura da naki ƙannen ki kula da Jafar kada ki tsoraceshi bazai cutar da keba ki ɗaukeshi a Matsayin wa". Cikin zubda hawaye Shatu tace. "In Sha Allah Umaymah zan kiyaye zan kuma zamo yadda kike zatonta, koda sanadin haka zan rasa jigo biyu na rayuwata rai da lafiya ta". Kalaman Umaymah da Aysha kuramen baƙine da su kansu ɗaya bata fahimci abinda ɗaya take nufiba, hakama ɗayar, bare su Jalal dake tsaye. Jawo Hibba tayi ta haɗa su ta ruggume, kana ta jawo Juwairiyya tace. "Ku duk yara nane ku zauna lfy". Gaba ɗaya da to suka amsa. Cikin sauri Umaymah ta sakesu kana ta miƙa wa Ummi hannu sukayi musababa, tare da bar mata sallahun yaran. Daga nan suka fita, gaba ɗayansu. Sai Shatu da Hibba da suke kuka, ganin hakane Ummi ta dawo ta zauna dasu. Jabeer da Jafar da Umaymah kuwa Side ɗin Mama sukaje, tayi sallama da ita, suka rabu suna hawaye. Daga nan Side ɗin Lamiɗo da Gimbiyar shi sukaje. Nan sukayi sallama dasu kana suka fito, inda suka samu Jamil da Jalal sun kawo musu motoci. Daga nan suka shiga suka tafi Airport tare da rakiyar motocin fadawa guda uku ya zama motoci biyar ne suka tafi kaita Airport. A gida kuwa, da kyar Ummi ta samu ta lallashi Shatu da Hibba da cewa in basuyi shiruba, zata, sa akai Hibba Airport ta tafi da Umaymah. jin hakane yasa Hibba tayi shiru. Ita kuwa Shatu dama ba kuka mai sauti takeyi ba, zubda hawaye takeyi. Ƙarfe tara dai-dai jirginsu Umaymah ya tashi zuwa jihar Tsinako. A gida kuwa tuni Shatu da Hibba sun shiga kuma har sunyi bacci sabida kukan da sukayi. Ita kuwa Ummi tana falo, saida taga dawowarsu sannan taje ta shiga ɗakinta dan yanzu ta dawo da zama a nan kenan ɗakin da Umaymah ke sauƙa in tazo. Washe gari ranar asabar kuwa, haka suka wuni gidan shiru ba daɗi gaba e kewar Umaymah ta hanasu jin daɗin gidan. Ranar ne kuma duban forko na watan Ramadan. Tunda magriba tayi, al'ummar musulmai keta cekinta labarin ganin wata. Wannan ya tambayi wancan wancan ya tambayi waccan. Jira kawai akeyi aji lbri ko gani. Yayinda duk irin wannan rana duk inda yanki musulmai suke a faɗin duniya suna jimirin da tsumayin lbri. A wasu wuraren har matasa maza da dattawan kanyi dandazon da fuskanta yamma dan ganin watan Har dai akayi sallan magriba babu ƙaƙƙarfan lbrin ganin wata. Bayan anyi sallan isha'i ne, Sarki Nuruddeen Lamiɗo kenan ya tara hakima shi a fada suna jiran ko akwai ta inda labari zai riskesu. Kasan cewar ana yanayin damuna ne yasa ba ko ina keda yaƙinin ganin watarba. Sheykh Jabeer kuwa, wanda ranar bai samu yayi salla a masallacin Masarautar Joɗa ba. Sabida wata ƴar tafiyar da yayi, sai bayan Isha'i ya dawo. Kai tsaye Side ɗinsa ya wuce. Yana shiga falon wayarshi dake cikin al'jihunsa ta fara suwa a hankali. Gefen Ummi ya iso tare dayi mata sallama. cikin kula tace. "Sai yanzu?". Kai ya gyaɗa mata yana mai amsa wayar. Sannu da hanya tace mishi. Cikin sauƙe numfashin alamun gajiya yace. "Yauwa Ummi sannu da aiki". Sai kuma ya kara wayar akunnen shi cikin nitsuwa yace. "Wa alaikassalam". Ɗan jim yayi kana yace. "Alhamdulillah". ya ƙarshe mgnar yana shiga cikin falonshi. Shatu kuwa dake gefen Ummi shiru tayi tare da binshi da ido. A can falon shi kuwa zama yayi bisa kujera tare da fara zare al'kyabbar daka hannunshi, wayar na kunnenshi yake cewa. "Eh Jadda Alhamdulillah rahotanni sun nuna cikin Ɓadamaya al'umma da yawa sunga watan Ramadan. Kuma nima naga watan Ramadan da idona". Cikin jin daɗi Jadda yace. "Alhamdulillah, ko yanzu mun samu gamsassun hujjoji daga bakin salihan bayi, Dan jihar Tsinako sarki Abudulfata da kanshi ma yaga watar ya sanarmin. Hakama jihar Noki, Jaltarba, Magom, Shibb, da dai sauran jihohi mu na arewaci anga wata sosai tako ina. Kana yanzu kuma munyi mgna da Sheykh Abdulkareem shima yace anga wata. Mu nan jihar Leddi julɓe kusan kowa yaga wata." gyara zamanshi yayi tare da cewa. "To Alhamdulillah. Allah ya nuna mana ƙarshen sa lfy, yasa muribantu da watar al'farma Annabi da Alqur'ani". Amin Amin Sarki musulmai Jalaluddin, yace. Kana ya sallameshi. Daga nan aka bada sanarwan anga wata, inda shi Sarki Jalaluddin ya kira manyan masarautun gargaji yana shaida musu. Kana manema labarai duk sukayi dandazon zuwa, nan aka sanar tako ina musamman kafafen yaɗa labarai na yanar gizo. Nan take ko ina ya ɗauka. Suna zaune a falon suna cikin hira. Sukaji wani irin ƙara mai firgitarwa da bada tsoro. darararam-dam sautin ƙarar bindigar toka mai ƙarfin amo. Wani irin tsalle Shatu tayi tare da motsowa jikin Ummi, tare da toshe kunnuwanta, sabida sake jin ƙaran. Gaba ɗaya jikinta kerma da kerketa yakeyi, Cikin tsoro take cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun, hasbunallahiwani'imanwakil!". Da sauri Ummi ta riƙon hannunta datasa ta toshe kunnuwanta cikin ɗaga sauti take cewa. "Shatu ba komaifa, kada ki razana bindigar sanarda ganin watane! Shaidar gobe zamu tashi da azumi". Cikin tsinkewar zuciya tace zamo daga kan kujerar ta zauna a ƙasa kusa da sawun Ummi, wani irin duka ƙirjinta keyi didib didib, didib. Murmushi Hibba tayi tare da cewa. "Aunty Aysha tsoro haka". Cikin yamutsa fuska tace. "Ya kamata ku gayawa duk wani baƙo wannan bahugawar al'adar taku in ba hakaba wata rana tsoro zai kashe irina". Sheykh da tun ihunta na forko yana bakin corridor yana kallon yadda take karkarwa, wani irin murmushin muguntane ya tsubce mishi. Sai kuma ya tsuke fuskarsa kamar bashi yayi gajeren murmushi ba, cikin faɗa yace. "Nifa bana son sakarci sam bafa na son anamin ihu a ka da hargowa a gida". Cikin tura baki ta bishi da ido. Shi kuwa fita yayi yana murmushi a cikin zuciyarshi tare da magar zuci. "Ga rashin ta ido ga tsoro, ga tsiwa da fitsara ga makirin karaya. Ai da anyi ta sakin sautin bindigar har sai tayi fitsari a zani". Da haka ya wuce ya nufi fada, nan suka fara tattauna yadda lamuran zasu tafi. Ummi kuwa murmushi tayi ganin irin kallon harara da Shatu ta raka Sheykh dashi. Cikin murmushi tace. "Taso ki zauna muyi mgna". A hankali ta miƙa ta hau bisa kujerar da Ummi take ta zauna, Hibba kuwa, tuni ta nufi Side ɗin Aunty Juwairiyya. Gyara zama Ummi tayi tana fuskantar ta da kyau, Cikin nitsuwa tace. "To Alhamdulillah kinga anga wata gobe zamu tashi da azumi in Allah ya kaimu, akwai ƙarin aiyuka a Side ɗin nan wanda ko da can baya ko Sheykh bayanan yana ajiye komai na buƙatar rayuwa akanyi girki a nan kamar akwai mace, sabida anan su Jalal, Jamil, Hashim Sulaiman Imran Affan in yana nan suke shan ruwa." To yanzu bana Sheykh ba inda zaije sabida a jerin jadawalin malaman tabsir da ake turawa jihohi bana ba'a turashi ko inaba tunda ya girma ya fara tabsir sau ɗaya yayi azumi a nan shekarar da ciwon Jafar ya tsananta, to anane naga zahirin yadda yake gudanar da al'amuran rayuwarshi cikin Ramadan. To bana ma. Anan cikin Ɓadamaya zaiyi tabsir ɗin shi. To aiyukan mu sunada yawa. Dole kisan yadda tsarin komai ke tafiya." Cikin sauƙe numfashin ta gyara zama ta fuskanci Ummi da kyau kana a hankali tace. "To". Itama gyara zama tayi da kyau kana tace. "Azumi goma sha biyar zaiyi a nan, ƙarishen 15 ɗin a ƙasa mai tsarki zaiyi su. Ma'ana zai tafi Umrah. Sannan yanada masallatai uku da yake tabsir a kullum. Da safe misalin karfe sha ɗaya na safe zai tafi masallacin jumma'a na cikin kasuwa, a can zaiyi tabsir sai ƙarfe shabiyu saura mintuna goma zai taso. Daga nan kafin ya iso masarautar Joɗa tafiyar mintuna goma ne. sha biyu dai-dai, zai zauna tabsir masallacin Masarautar Joɗa. Sai ƙarfe ɗaya na rana zai tashi. Daga nan bazai dawo gidaba, sai anyi sallan azahar. To ana idar da salla zai shigo, gida al'adar rayuwarsace tun yana yaro. Zaiyi baccin awa ɗaya tsakanin azahar da la'asar. Ƙarfe uku dai-dai na yamma zai tashi zaiyi wonka, ya canza shiga, kafin ya gama an kira salla. Yana fitowa zai wuce masallacin Masarautar Joɗa, inda yake limanci ana idar da salla zai tafi masallacin jumma'ar dake jami'ar Joɗa. Inda zaiyi tabsir daga ƙarfe huɗu zuwa biyar na yamma zai taso. Akan hanyar shi ta dawowa yana tsayuwa wurin mashigar laleko zai sayo kayan buɗa baki ƴaƴan itatuwa. Yana dawowa zai ajiyesu. Ya wuce Side ɗinsa, wonka zaiyi kana yasa sauƙaƙƙun kaya, ya dawo falonshi ko ya wuce cikin Garden acan zaiyi ta karatun al'ƙur'ani ko kuma wani lokacin ya ɗan konta ya huta. Kafin lokacin shan ruwa, Ni kuma da hadimar da Gimbiya Aminatu ke bani duk Ramadan ta tayani aiki. Tuni mun gama aikin buɗa baki. An shirya komai a dinning table, nasu Jalal kenan. Suma kuma gab da magriba zasu zo. Shi ma zai fito yakan zauna tsakiyar Jalal da Jamil ko kuma tsakiyar Jalal da Jafar. Baya cin abu mai nauyi iya karshi dabino da inabi da tuppa, sai ruwan zam-zam wanda dashi yakeyin buɗa baki. Daga nan zai wuce masallacin Masarautar Joɗa wani lokacin zai fita dasu wani lokacin zai rigasu fita. Ana shirya mishi abincinsa na musamman a ajiye mishi a dinning table ɗin dake can falonshi a Foodflaks ɗin shi na musamman, wani lokacin Gimbiya Aminatu ke aiko mishi. In ya fita bazai dawoba sai anyi sallan isha'i Dana asham. Amman su Jalal su zasu dawo suci abinci kafin isha'i sai su koma masallacin. Idan ya tashi daga Masallacin kai tsaye zai wuce. Gidan radiyo ABC Ɓadamaya, inda yake gabatar da shirin. "Fatawa. Za'a ayi mishi tambaya kan Ramadan dama sauran abinda ya shafi addini yana amsawa, wasu kan tura tambayoyin wasu kuma kira sukeyi a da number da ga suke badawa, suyi tambaya ya bada amsa. Ƙarfe takwas da rabi ake fara shirin tara dai-dai ake gamawa. Tara da mintuna ashirin yake isowa gida". Ɗan tsagaitawa tayi ta kalli Shatu dake cewa. "Tab agogo sarkin aiki to shi baya gajiya ne, ga azumi ga zirga-zirga ga kuma duk inda yaje dole ba shiru zaiba mgna zaiyi ai ƙishi zai mishi illa". Murmushi tayi tare da cewa. "To ai in yaje gidan radiyo tarba ta musamman akeyi mishi, sai dai shi ba ko ina yake cin abinci ba tunma yana yaro. Ko a gida nan ba abincin kowa yake ciba. To shiyasa tara da rabin nan zai dawo a gajiye cikin yunwa, to nan zaici abinci sosai. Kana yayi wonka zuwa sha ɗaya dai yayi bacci. To ƙarfe biyu kuma zai tashi, wani lokacin ma biyu bayayi zai tashi yayi ta nafilfilinshi da karatun Alqur'ani. Daga nan kuma baya komawa bacci. Har ayi sahur ayi sallan asuba. In ya dawo yayi Azkar, to nanne yake samun yayi bacci mai tsawo dan tun bakwai da rabi ko takwas na safen zaiyi bacci sai goma zai tashi ya fara shirin tafiya masallacin jumma'a na kasuwa." Kallonta ta ɗan yi tare da cewa. "Kin gane lokutan da yake aiki Dana hutuwa dana bacci ko dana cin abinci ko?". Cikin murmushi tace na gane. "Da safe zai sha bacci son ranshi, daga takwas zuwa goma kafin ya tashi ya shirya. Yaje masalacin jumma'a na kasuwa sha ɗaya tayi yayi tabsir ɗin awa ɗaya, daga nan ya dawo masallacin Masarautar Joɗa, shabiyu ya fara tabsir sai ƙarfe ɗaya ya gama, ayi salla ya dawo. Ya sake shan baccin awa ɗaya. Kafin kuma ayi la'asar ya tafi masallacin Joɗa state University. Yaje yayi tabsir in ya dawo, kuma ya lokacin hutawane har magriba. Daga nan kuma ayi buɗa baki a wuce masallacin daga can a wuce ABC. Sai tara a dawo. To yaseen wataran yunwa zata kadashi a hanya, ƙattin rigunan nan da yake sawa sune zasu jashi su kaishi ƙasa. To ma wai Ummi to yaushe yake zuwa aiki kuma?". Murmushi tayi tare da cewa. "To in baya garin an turashi wani state ɗin yana zuwa aikin ne?". Kai ta girgiza alamun a a. Cikin murmushin Ummi tace. "Shiyasa ko yana nan in dai a Ramadan ne baida lokacin zuwa Valli Hospital, bare Genaral Hospital ko kuma Asibitin jami'ar Ɓadamaya. Shine dalilinshi na ƙin yin aiki a asibitin gwamnati sai ƙarshen sati-sati yake zuwa sau ɗaya, duk wanda zai duba kyautane aiki". Naɗa hannunta tayi tare da cewa. "Batun yunwa ta kadashi kuma, yanzu aikin kine, kula da abinda zaici". Taɓe baki tayi tare da cewa. "To shi wannan da tsarabe-tsaraben falsafa nasan irin abinda zai cine ma. Mutun fuska a haɗe kullum kamar mai damuwar rashin jigo". Miƙewa Ummi tayi tare da cewa. "To kika sani ko hakanne. Kuma ai gani duk abinda kike son sani a kanshi tambayeni. Abincin da yafiso kuma yafi son ganyayyaki, fruits and vegetables sai kuma kayan ruwa, kana yana son nama da kifi in an mishi irin sarrafawar da yakeso. Sannan yana son abincin gargajiya wasu lokutan musamman a wurin yin sahur. Kai ta jinjina tare da cewa. "Uhumm lallai kam, wannan ai yafi Lamiɗo ma iya ƙasaita". Dariya tayi tare da cewa. Zo muje store kiga kayayyakin da yasa aka kawo ɗazu." To tace tare da miƙewa tabi bayanta. Suna shiga kitchen ɗin suka ɗan haura suka taka steps ɗin da zai sadasu da ƙofar store wanda wani ƙaton freezer ke konce a wurin sai ma dai daicin Fridge. Hannu Ummi tasa ta buɗe freezer'n. Motsowa tayi tare da zaro ido ganin yadda aka cika freezer'n maƙil dasu Kabej Karas kokumba green beans, masu kyau sabbi. Ɗaya sashin kuma nama ne jibge sai kifi a gefe, Sai ɗaya Fridge ɗin kuma cike yake da ababen sha na ya'yan itatuwa dana kwalba. Rufewa tayi kana ta buɗe mata drower'n kitchen cabinets ɗin. Kiret-kiret ɗin kwaine kusa goma suke jere a wurin ɗaya gefen kuma katon ɗin manyan gongonayen madara da millo ne. Sai katon ɗin sugar irin mai ƴaƴan nan. Sai katon ɗin Lipton. Da ganyen na'ana. Sai can gefe kuma su maggine da sauran kayan ɗanɗano. dasu kanan fari citta da dai sauransu. Cikin yin hamma tace. "Ummi duk yaushe aka kawosu?". Juyawa tayi suka nufi cikin cikin store tace. "Ɗazu da yamma kina bacci ya dawo, suda Jalal da Jamil". Kai ta gyaɗa tare da bin bayan Ummi. store ɗin cike yake da kayan masarufi na buƙatar rayuwa. Danginsu shinkafa, gero, waken suya, wake ƙosai dasu alale, sugar katon-katon na taliyar manya data yara, da dai sauransu. Sai kuma doya da dankali dake jibge a gefe, kana sai al'basa da sauransu. Fitowa sukayi kana suka dawo kitchen. tukunya Ummi ta ɗaura tare da ɗebo nama tazo ta wonke sabida an yanka wasu dai-dai misalin na miya, wasu kuma anyisu dogo-dogon yanka. a tukunyar ta zuba shi, kana ta ɗauko al'basa mai girma ta yayyanka a ciki. Sannan tasa tafarnuwa kaɗan kana tasa garin citta da kanamfari. Tare da maggi da kori da sauran kayan ɗan-ɗano. Kana ta kunna Gas ɗin ta ɗaura tukunyar, ɗanyen kuɓewa ta ɗebo ta miƙawa Shatu tare da cewa. "Wonke ki yanka min shi". To tace tare da amsa ta wonke kana ta fara yankawa, ita kuma Ummi al'basa da tattasai da tatuhu kaɗan ta ɗiba ta wonkesu kana ta markaɗesu dai-dai yadda takeso. Zuwa lokacin kuma gaba ɗaya kitchen ɗin dama Side ɗin gaba ɗaya ya cika da ƙamshin tafashen naman. Juyeshi tayi a wani kwano. Kana tasa mai kaɗan tasa manja kaɗan. Tare da watsa jajjagen kayan miyar, ta soyasu. Kana tasa naman da sauran ruwan tafashen. ta kuma ɗauko bandan kifin tarwaɗa bandanshi, ta gyara ta wonƙeshi da ruwan ɗumi. ta watsa a ciki. Sannan tasa ɗan dakekken yajin daddawa kaɗan." sannan ta rufe tukunyar. ta amshi kuɓewar tana ƙarisa yankan. Tukunyar data ɗaura ruwan tuwo ta ɗan kalla ganin yana tafasane tace. "Gacan garin semo na tankaɗeshi ɗibi kiyi mana talge." To tace tare da juyawa ta ɗebo tayi talgen. Ita kuwa kuɓewar ta saka, kana ta tsalli ɗan toka ta saka. Bayan wasu yan daƙiƙu miyar tayi lugub tayi kyau tayi kalar kore mai kyau. sabke tukunyar tayi kana tasa, man shanu a ciki. Sannan ta meda tukunyar gefe. Tuwon ta tuƙa ya ɗan turara kafin ta kwasheshi tana yin mal'mala tana sawa a leda. Saida ta cika wani madaidaicin Foodflaks mai ɗan girma. Kana ta ɗauka ruwan zafi. Ta tafasa tea ta ɗura a flaks tare da tarfa kanumfari da citta sai na'am. Sannan ta rufe, ta kimtsa komai a kitchen ɗin. Ganin Shatu nata Hamma ne tace. "Jeki kwanta tunda mun gama aikin. Sai kuma da asuba." Cikin alamun bacci tace. "To Ummi saida safe". Ta fita tana haɗiye minyau dan ƙamshin da miyar keyi. A falo taci karo da Hibba Aunty Juwairiyya ta rakota, da Foodflaks a hannunsu alamun abincin sahur ne a ciki. Cikin baccin da takeji tace. "Mun yi girki ma, Aunty Juwairiyya". Kai Juwairiyya ta ɗan gyaɗa tare da cewa. "A lallai kam sannu da aiki". Ta ƙarishe mgnar tana ajiye kulolin bisa dinning table. Ita kuwa Shatu harara ta watsawa kulolin tare da wucewa tayi ciki. Hibba ce ta biyo bayanta bayan tayiwa Aunty Juwairiyya Saida safe. Har sun shiga Ummi ta kira wosu. Falo suka dawo duk suna hamma alamun bacci, ganin Hamma Jabeer na zaune ne, gasu Jalal gaba ɗaya yasa suma suka ƙarasu cikin falon. Gyara zanshi yayi tare da kallon Hibba da Aysha da duk alamun bacci ya cikasu, cikin sakekkiyar murya yace. "T....! Uhummm Ramadan da daɗi, Ya Allah ka nuna mana ka kaimu watan lfy ka nuna mana ƙarshensa lfy ka maimata mana. Rayuwar Masarautar Joɗa a Ramadan yanada tsari da masifar daɗi da burge duk musulmi. Kabcen Shatu da Sheykh a kwanakin Ramadan da bikin salla yana sani murmushi da shauƙi.😘🥰🤝🏻 By *GARKUWAR FULANI* "To Alhamdulillah. Allah ya kawomu watan Ramadan, wata mai tarin al'farma da al'barkatu da tarin ni'imomi. Mutane da dama Allah bai basu wannan damarba, da yawa sun rasu. Wasu kuma basu da lfy, basu san me sukeyi ba ko a ina suke, bare su ribaci wannan dama da Allah ya bamu. An ga wata wanda haka keda tabbacin gobe zamu tashi da azumi. Duk kuyi niya, ɗaukar azumi talatin ko talatin ba ɗaya." Sai ya kuma ya ɗan tsagaita tare da kallonsu Jalal da Jamil cikin sanyi yace. "Dan Allah Jalal Jamil ku nitsu kunsan halin da muke ciki. Kun san matsalar rayuwarmu kunsan damuwarmu, wannan dama ce da zamu yi amfani da ita wurin tsananta addu'o'in ba dare ba rana. In sha Allah, Wata rana komai zai dai-dai-ta domin Allahu sami'uddu'a ne. Jamil kaji tsoron Allah ka ribaci wannan watar, ka raba kanka da zuwa club, ka yayewa kanka masifar nacin liƙewa mata da waya." Juyowa yayi ya ɗan kalli Jalal kana yaci gaba da cewa. "Jalal yawon bin yan iska da wani shegen shiga mara kan gado ba tsarine na Musulmin ƙwarai ba. Aunty Juwairiyya Hibba Ummi Ke uwar bacci". Ya ƙarishe mgnar da kallon gefenda Shatu da take zaune tana ɗan lullumshe ido, da sauri ta waresu don a sama taji muryar tasa. Baki ta tura tare da sunkuyar da kanta, shi kuma jenye idonshi yayi daga gefen da take cikin ɗan ɗaga sauti yace. "Watan Ramadan ya bambanta da sauran watanni. Domin a cikin watanne daren laylatul Ƙadir yake, kuma a cikin watanne Allah ya sauƙe al'ƙur'ani mai girma. Kana a cikin watar akwai ranakun da malamai sukeyi hasashen a daren laylatul Ƙadir yake, Daren 21, 23, 25, 27, 29. Sai dai ba'a tabbatar, da sahihin rana ɗaya tsayeyye ba ƙauli mafi rinjaye shine ranar 27. Abi mafi kyau shine kada mutun ya sake koda dare ɗaya na Ramadan ya wuceshi. Mu raya dararen da ibada da ambaton Allah, wajibine mutum ya tsare bakinsa, da munanan zantuka walau a baki walau a rubuce a social media, Domin mu ribanci watar da ambaton Allah da samun ruɓanyar lada, wannan abubuwane da kullum nake gaya muku su, sai dai aiki dasu ya gagareku." Kusan haɗa baki sukayi wurin cewa. "In Sha Allah zamuyi ƙoƙarin kiyayewa". "Allah yasa yace, tare da sallanmansu duk suka fita sai Ya Jafar da Ummi. Ganin yadda Hibba keta zuba hamma ne ya sashi cewa. "Muhibbat tashi Kije ki kwanta". Kusan a tare ta mike ita da Shatu. da sauri yace. "Banda ke". Cikin bacci ta turo baki tare da cewa. "Ayyah dan Allah fa". Murmushi Ya Jafar yayi tare da zuba mata ido. Wanda koda baya mgna ana iya gano yadda yake sonta a ranshi, so kuma irin son da yakeyiwa su Hibba. Ummi ce ta ɗan kalleta tare da cewa. "A barta tai bacci aiki mukeyi tun ɗazu". Shiru bai kulasuba, ganin haka ita kuma tabi bayan Hibba. A zatonta bai saniba, har sunje bakin ƙofar taji yace. "Saura ki binƙire kiyi ta bacci, kada ki tashi ki raya daren. Sai gari ya waye ki buwayi mutane da ife-ife da rashin kunya". Ya ƙarishe mgnar cikin jin haushinta tare da Binta da kallon fitinenneyar yarinya. Ganin Ya Jafar ya miƙa ya juya zai fitane yasa yayi saurin. Bin bayanshi ya rakashi kana ya dawo ya konta. Ummi ma ta konta. Ƙarfe ɗaya da rabi Sheykh ya tashi yayi ta nafilfilinshi tare da jere addu'o'in da neman warakar damuwar rayuwarshi data ahlinshin. Ummi ma tuni ta tashi. Ƙarfe uku ta fito. Falon hango haske a ɗakun Shatune ya tabbatar mata sun tashi. Kitchen ta wuce. gas ta kunna ta ɗumama musu miyar, kana ta haɗa plate spoons and cups tazo ta jere bisa Dinning table. Sannan ta koma kitchen ta ɗauko musu drinks and water masu sanyi tazo ta jere komai yadda ya dace. Kana ta dawo falon ta zauna riƙe da carbinta. Ƙarfe huɗu dai-dai su Jalal suka buga ƙofar sanin sune yasa, ta tashi ta buɗe musu. Suna shiga ana buga bindigar sanarda mutanen masarautar Joɗa cewa lokacin sahur yayi. Bayan mintuna talatin kuma za'a kuma sakin bindingar. Cikin gudu Shatu ta fito falon jiki na rawa, kiciɓis tayi da Ummi da takeda niyar zuwa ta ta kirasu suzo suyi sahur. Ruggume Ummi tayi ƙam-ƙam tare da neman inda zatasa ranta. Allah ya sani tana tsoron ƙaran abu biyu, ƙaran aradu da walƙiya da kuma ƙaran harbin bindiga". Cikin mamaki Ummi tace. "Oho Aysha duk wannan tsoron na ƙaran harbin bindiga ne, lallai kuwa in baki sababa kafin Ramadan ya ƙare zakisha wuya." Hibba ce ta fito tana dariya tace. "Allah ko Ummi ana ɗaukan alhaƙin Aunty Aysha". Babban Falon suka nufo yayinda duk jikinta ke karkarwar." Dinning area Suka wuce. Bayan duk sun zaunane Ummi tace Hibba tasa musu abinci. Buɗe kulolin tayi. Jolof ɗin taliya da kifi Aunty Juwairiyya tayi, sai kuma Flaks ɗin kunun gyaɗa. nasu kuma tuwon semo da miyar ɗanyar kuɓewan sai tea da sauran kayan sha. Ta zubawa kowa abinda ranshi keso. ita dai Shatu mamakin abincin Aunty Juwairiyya na yau takeyi sabida idonta bai gano mata wani mugun abu a cikiba. Haka yasa itama shi taci. Da kunun. duk sunyi nisa a yin sahur ɗin. Amman shi bai fitoba, Sai ƙarfe huɗu da rabi ya fito. A hankali ya iso Dinning area ɗin gaban washing hand Baby ya ɗan tsaya tare da wonke hannunshi. Ita kuwa Shatu tana ganinshi ta ɗanyi gyatsa tare da cewa. "Alhamdulillah kana ta miƙe". Kujerar dake gefen Jalal ya zauna, Yana zama ita kuma ta juya ta nufi cikin falon. Shi bai ma kalli inda takeba. Cikin falo ta koma hannunta riƙe da cup ɗin kunun da take sha. Cikin kula Ummi tace. "Sai yanzu?". ta ƙarishe mgnar tana zuba mishi tuwon semo da miyar ɗanyar kuɓewar da yaji nama da kifi da man shanu. gyara zamanshi yayi tare da cewa. "A jinkirta sahur a gaggauta buɗa baki Ummi Manzon Allah yace." Murmushi tayi tare da cewa. "Hakane". Bismillah yayi tare da gyara zaman shi, ya fara cin abincin. yaci mai ɗan yawa dan daren jiya baici komaiba. tea ta haɗa mishi. Hannunshi ya wonke kana ya amshi tea ɗin ya fara sha. Jalal, Jamil, kuwa ci sukayi sukayi haninƙan kana suka miƙe zasu tafi. Cikin kallonsu yace. "Kadafa kuje ku kwanta, kuyi al'wala ku wuce masallaci." To sukace kana suka tafi. Shi kuwa yana gama yin sahur ɗin ya koma Side ɗinsa, Wonka yayi tare da al'wala kana yayi shigarsa ta farar jallabiya. Bayan sun idar da salla gari ya ɗanyi hasken ya taso ƙeyansu, suka dawo gida. Side ɗin su suka wuce. raka Ya Jafar yayi har Side ɗinsa kafin yazo ya shiga sashinsa. Shiru falon babu kowa, bisa alamu kuwa tuni Ummi ta kimtsa ta share da goge ko ina, ta sassake labulaye, tare da sa turaren wuta mai ƙamshi. Kana ta kashe hasken ko ina, babu abinda ke tashi sai ƙamshi da sanyin A/C da karatun Alqur'ani mai girma da kuna. Falonshi ya nufa yana shiga, ya zauna a falo, Dua Azkar ya fara yi cikin zazzaƙan muryarshi. Bayan ya isane kuma ya fara karatun al'ƙur'ani. Sai bakwai da rabi dai-dai ya shafa addu'a kana ya wuce bedroom ɗin shi. Wutan ya kashe tare da ƙara ƙarfin gudun AC. sannan ya nufi luntsumemen gadonshi ya kwanta bisa gefen damanshi tare dasa hannun ya jawo blanket ya rugu. A hankali lips ɗinshi ke motsawa, alamun tasbihi yakeyi. Cikin 13 minute bacci mai daɗin gaske ya kwasheshi". Haka can wurinsu Shatu ma, saida tai karatun al'ƙur'ani sosai kafin ta konta hakama Hibba. Ummi kuwa wonka tayi tayi al'wala ganin bakwai ta wuce ne tayi walahan ta raka biyu. Kana tayi karatu sai ƙarfe tara da rabi ta konta take kuwa bacci yayi awon gaba da ita. Ƙarfe goma dai-dai ya tashi daga baccin da yakeyi. Wonka yayi tare da al'wa kana ya fito ya kimtsa cikin shiga ta al'farma. Turare mai ɗan sanyi ya fesa kaɗan kana. Ya ɗanyi tafiya kaɗan zuwa gefen Bedside drower'n dake tsakanin gini da gado, wanda akwai tazarar fili mai ɗan faɗi ana yake shimfiɗa sallayarsa wurin ya zama keɓantaccene. Walaha, yayi raka biyu kana yayi addu'o'in yau da kullum ya shafa, miƙewa yayi ya ɗauki System ɗinshi ya riƙe a hannunshi, kana ya ɗauki woyarshi ɗaya cikin su huɗu da suke bisa Bedside ɗin. A hankali yake taku, har ya fito tsakiyar falon. Shiru gidan tamkar babu mai rai a ciki. A haka ya buɗe ƙofar ya fita, tare da ja musu ita ta baya. Koda ya fito asalin farfajiyar masarautarma ko ina shiru kakeji, sai ɗan zirga-zirgan fadawa da hadimai masu tattara ɗan sharan dake ko wanne bakin part. Suma kowa a hankali yake aiki alamun akwai bacci tare dasu. Motarsa kirar Tolls Royce, wacce kuɗinta zai iya kai kimanin Billion 4, 959,630, naira. Baba Lado shine Drevernshi da sauri ya taso yana suka tafi. Daga nan masallacin jumma'a na kasuwa ya wuce. Sha ɗaya saura ya isa, inda ya samu tuni masallacin ya cika yayi maƙil da al'ummar Annabi maza yara da manya tsoffi da tattawan, yan kasuwa sun cika sunyi maƙil iso warshi kawai dama ake jira. Motarshi na gama tsayuwa yan agaji suka rufa mishi baya, babban cikinsu ne ya buɗe mishi marfin motar tare da ɗan rusunawa yace. "Barka da safiya Malam". Cikin tsananin kulawa Sheykh Jabeer ya kalli dottijon da ya kai ya haifeshi. Hannu ya miƙa mishi tare da cewa. "Barka dai Baba Sule Ya ibada". Cikin jin dadi yace. "Alhamdulillah". Sai kuma ya kalli sauran wanda yawanci bazasu wuce sa'annim ƙaninshi mai binshiba Affan kenan, Murmushi yayi tare da basu hannun yana mai tuna cewa tabbas da Affan yana ƙasar nan To bana a Ɓadamaya zaiyi azumi, kuma ya sani da yanzu suna tare anan, dan shi ba irinsu Jalal bane. Zagayeshi sukayi suna buɗa mishi hanya yana wuce. Ta kofar da liman ke shiga ya shiga. sit kakeji da yake duk mazane, gashi kuma ansan ƙa'idarshi shi baya son surutu in yana tabsir. Zama yayi tare da kallon ɗan agajin dake saƙala mishi abin ɗaga sauti mgn a jikin al'kyabbar jikinshi. Yayinda wasu kuma suka koma bayanshi wasu suka tsaya gefenshi, yan ɗaukan awazin kuma na gidajen Radio da TV duk sun kafa na'ura su a gaban table ɗin da yake zaune. Bayan an gama kimtsa mishi komaine, ya gyara zamanshi tare da kallon alaramma Abdulƙadir wanda shine zai jamishi baƙi. System ɗinshi ya buɗe tare da gyara mata zama, haka shima Alaramma Abdulƙadir yayi da Qura'an ɗin gabanshi. Gyara murya Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero yayi tare da fuskantarta taron al'ummar dake gabanshi cikin ɗan ɗaga sauti yace. "Bismillah rahmanirrahim. Assalamu alaikum warahmatullahi wa barka tuhu. Innal hamdalillah nahmaduhu wanasta inuhu wanastagfiru wana uzubillahi min shururi am fusina wa sai'yi ati amalina. Manyahadillahu fala mudillah, famanyuddul fala hadiyala wa asshahu'alla'ila'ha'illalahu wahdahu lasheri kallah, wa asshahadu annamuhammadan abduhu warasulu. Ya ayu allazina amanuttaƙullaha haƙƙa tuƙatil wala ta mutunna illah wa antum muslimun ya ayu hannasu taƙu rabbakum. Kalakum min nafsin wahida, wa kalaƙa minha zaujaha wa bassa minhuma rijalan khasiran wa nisa'ah wattaƙullah lazitasa'aluna bihi, wal'arhama innallaha kana alaikum raƙiba, ya haiyu allazina amanutaƙullah wa ƙulu ƙaulan sadidah yuslahlakum amalakum wayagfirlakum zunuba kum, waman yuɗillah wara sulahu, faƙadfaza fauzan azeema ambaduhu fa inna'asdaƙal hadisi kitabullah wa'ahsanal hadi hadiyu Muhammadin (S.A.W) wa sharal umuri muhdasatuha fa innakulla mudasatin bidi'a wa kulla bidi'atin balala wa kulla balaltun finnar." Nufamshi ya sauƙe mai ɗan nauyi sabida jan dogon numfashin da yayi, kana ya kalli taron al'ummar musulmi dake zaune gabanshi manya da yara, masallacin yayi maƙil har woje. Kusan gaba ɗaya taron jamar suka haɗa baki wurin cewa. "Wa alaikassalam warahmatullahi wa barka tuhu". Kanshi ya ɗan rusunar tare da ci gaba. Gyara masaƙalin abin sautin mgnar dake wuyan al'kyabbar jikinshi yayi tare da cewa. "Alhamdulillah. Kamar yadda aka saba haɗuwa a wannan masalaci mai Al'barka bana kuma Allah ya ƙaddara dani za'ayi. Kamar yadda aka fara a wancan shekarar, zan ɗaura a kan darasin da Malam Abubakar ya fara, duba da kasantuwar mafiya yawa yan kasuwa ne, to zamuyi maudu'in bisa haƙƙin tauye mudu, da kuma barin salla ta wuce dan gudun cinikayya ya wuce ka." Daga nan ya shiga cikin shirin gadan-gadan. Yayinda gaba ɗaya mutane sukayi tsit suna jin nasiharsa da hujjoji da yake jawowa daga al'ƙur'ani zuwa ahadisai, yana shigarsu yana ratsa musu jiki, jini, da zuciya. Musamman dama mutane nason wa'azinshi. Haka yasa koda lokacin tashi yayi sai suka ga kamar miti biyar sukayi ba awa ɗaya ba. Yana tashi a wurin yan agaji sukayi mishi rakiya, har bakin motarshi. Daga nan Masallacin Masarautar Joɗa ya nufa. Sha biyu dai-dai tayi mishi yana cikin masallacin tuni an shirya an kimtsa komai yadda abu zai tafi, shiyasa yana isa shida Alaramma Abdulƙadir suka fara. A can cikin masarautar Joɗa kuwa. Dai-dai lokacin Shatu ta fito cikin ɗakinta ta nufi falo. Shiru babu kowa, haka yasa ta wuce kitchen da nufin yin wonke-wonken da sauran gyara-gyare ganin komai tsab-tsab ne yasa ta dawo falonta. A hankali ta nufi ɗakin Ummi. daga bakin ƙofa ta tsaya tare da yin sallama. Cikin kula Ummi ta amsa mata tare da cewa. "Ki shigo mana". To tace kana ta shiga, cikin sanyi tace. "Ina kwana Ummi". Murmushi tayi tare da cewa. "Lfya lau Alhamdulillah, amman yanzu dai ina wuni ne ko". Cikin murmushi tace. "Eh hakane fa, yanzu har sha biyu da rabi tayi". Murmushi tayi tare da cewa. "Ai tunda naji Sheykh ya fara tabsir nace to rana ta tsala". Shiru suka ɗan yi tare da kasa kunne, ras muryarshi ke tashi sabida ansa amsa kuwa ta cikin masarautar. shiru Shatu tayi tare da yin ƙasa da kanta tana mai lumshe ido, Allah yasani tana masifar son tabsir ɗin shi, in taji yana jan baƙi sai take jinta kamar a harami take. Ummi ce ta ɗan kishin ƙiɗa tare da cewa. "Gyara zamanki muji wa'azin." Kai ta ɗan ɗago tare da cewa. "Ummi naje kitchen zan mana wonke-wonken na samu an gyara komai ba dai ke kikayi aikinba?". Cikin maida hankalinta ga sauraron tabsir ɗin tace. "Nice nayi, amman daga yau Saratu zata na zuwa tanayi wanke-wanke da share-shere da yan gobe-goben da dai sauran ƴan wasu aiyuka, kamar fere dankali ko doya da tsinkan ganyen ko wanke wake ko jiƙa shinkarfa masa da kai markaɗe, duk itace zatayi mana, mu kuwa in munyi azahar mu shiga kitchen, zatake ɗan taimaka mana da wasu aiyu kan. Amman banda girki, hadimar Gimbiya Aminatu ce, amman duk azumi nan ake bamu ita". Cikin gamsuwa da hakan tace. "To ba damuwa Ummi, amman dan Allah in ɓata zoba, kada kice zakiyi aikin ki barshi ni zanyi". Murmushi tayi tare da cewa. "Zama tazo, kullum da asuba ana idar da salla zata zo. In ta gama aiyu kanta kafin ƙarfe goma dai zata tafi, sai anyi sallan azahar kuma zata zo. Daga nan kuma sai mun gama aikin buɗe baki, ta tafi dana Gimbiya Aminatu da nata, sannan sai ansha ruwa anyi sallan isha'i da asham sai ta dawo tayi yan wonke-wonken da taimaka mana aikin sahur, to in ta tafi kuma sai washe gari in anyi sallan asuba ta dawo." Cikin ɗan fito da idonta tace. "Wannan zirga-zirga haka Ummi to ta zauna anan kawai mana ta huta". Juyowa tayi ta ɗan kalleta kana tace. "Mijinki ba irin waɗannan mutanen bane, baya son a turo mishi yara suzo suyi ta zirga-zirga a kanshi, kinga duk lokutan da take zuwa basa haɗuwa." Baki ta ɗan taɓe tare da yin mgna a zuci. "Kai mutun komai tsari, wannan babu shakka baida gskya ne wannan ɓoye-ɓoyen waya sanima ko cin zan-zanane a jikinshi da saɗaure wata ƙil shiyasa yake kima tabka-tabkan Al'kyabbar ajikinshi dan ya boye abubuwan". Murmushi Ummi tayi dan ta lura Shatu bata san mgnar ta fito fili ba. Shiru Shatu tayi ganin alamun Ummi na jin wa'azin, Hakane yasa tayi shiru sabida kada ta takura mata. Ƙarfe ɗaya dai-dai na rana, akayi addu'a aka rufe taron sai kuma Goben in Allah ya kai rai. Da yawa mutane basu fitaba, mafi akasari Kur'anai suka ɗauka suna karatu. Kamar yadda Sheykh yakeyi. Ƙarfe ɗaya da rabi aka kira sallan azahar. Miƙewa Shatu tayi tare da cewa. "Ummi bari inje inyi salla zan zo muyi wata mgna". Cikin binta da ido Ummin tace. "To". Bayan anyi sallan azahar an idar ne, ta fito ta nufi ɗakin Ummi, ganin bata nan ne, yasa ta nufi falo, nan kuwa ta sameta zaune bisa kujera. gefenta taje ta zauna. Tana zama wata ƴar matashiyar budurwa ta shigo, cikin nitsuwa tazo ta rusuna gabansu tare da gaidasu, Cikin kula Ummi tace. "Yauwa Saratu kin zo ko?". Cikin nitsuwa tace. "Eh Ummi nazo ɗazu bakwa nan sai na koma sai yanzu na kuma zuwa". Kai ta jinjina tare da cewa. "Yayi kyau,". Inda Shatu take ta ɗan kalla tare da cewa. "Ɗiyata ga Saratu. Saratu ga Saiyada Shatu matar Sheykh Jabeer". Cikin mamaki da dariya sunan da Ummi ta liƙa mata wai Sayyada, ta kalli Saratu tare dake gaisheta cikin ladabi da biyayya, fuska a sake ta amsa. Cikin sanyi Saratu tace. "Ummi me za'ayi ne?". Gyara zama Ummi tayi tare da cewa. "Ki wonke shinkafar masa dama na jiƙata, kana ki gyara mana ganyen alaiyahu, sannan ki fere Arish. Sai kuma ki jajjaga kayan miya, ki yanka al'basa mai ɗan yawa." Cikin nitsuwa da bin umarni tace. "To Ummi". Ta ƙarishe mgnar tare da miƙewa ta nufi kitchen, tana shiga ta fara aiyukan da aka sata. A falon kuwa, gyara zama Shatu tayi tare da kallon Ummi cikin sanyi tace. "Ummi dama mgnar da zamuyi ko!." Sai kuma tayi shiru tana nazari, jin muryar Ummi nace mata, "Uhum ina jinki faɗi". Sunkuyar da kanta tayi a hankali tace. "Uhumm dama cewa, zanyi in ba matsala a rinƙa yin abun buɗa bakin ana kaiwa masallacin Masarautar Joɗa mana, tunda dole talakawan gari na zuwa nan sallan magriba." Murmushi mai yelwa Ummi tayi tare da cewa. "Allah sarki, Shatu mai tausayi, ba matsala amman ki tambayi mijinki in ya amince dai ba matsala, dama kuma ana fitar da abinci a sashin Gimbiya Aminatu, da Gimbiya Saudatu da kuma gidan Galadima, da Hajia Mama. Da gidan Dr Aliyu da sauran duka, kuma ko Juwairiyya ma tanayi". Murmushi ta ɗanyu tare da cewa. "To Ummi muma ai muna son ladan wannan aikin". Da sauri tace. "A sosai ma kuwa. Sai dai ki sanar da maigidankin in ya yarda yanzu incewa Saratu ta ƙara hannun sosai". cikin kwaɓe fuska tace. "To Ummi shi wannan sarkin zirga-zirgan ina zan ganshi?". Cikin yin ƙasa da murya Ummi tace. "Yana falonshi yanzu ya dawo, yana wucewa kina fitowa, jeki sameshi da sauri kada yayi bacci ya zama kin tadashi a bacci dan babu abinda yafi ɓata mishi rai sama da ya fara bacci a tadashi". Cikin juya ido tace. "Ummi to ni me zan ce mishi?". Murmushi Ummin ta kumayi kana tace. "Abinda kika cemin shi zaki ce mishi, tashi kije musan yadda zamu fuskanci aikin". Ta ƙarishe mgnar tana miƙar da hannunta, a hankali ta miƙe tsaye, doguwar rigar jikinta ta gyara tare da yane mayafinshi. Ganin ta tsaya ne yasa Ummi cewa" "kije mana." Allah yasani badon tana son ladan aikin ciyar da marasa ƙarfi da basu abin buɗa bakiba da bazata sake zuwa tambayar abu wurin wannan kurman ganganɗinba, tun randa taje tana mishi mgnar yacewa Umaymah ta bar musu Hibba ya shareta take jin haushinsa in ta ganshi kamar ta ɗirka mishi dundu a baya. Muryar Ummi data kuma jine yasata, juyawa, ta nufi corridor'n da zai sadata da falonshi. A hankali take taku, tana jin sanyin tayis ɗin wurin na ratsa mata ƙafa, sallama tayi a bakin kofar tare da kutsa kai ciki, tana mai murtuƙe fuska. Bisa 1 str ta sameshi zaune, da alamun waya yakeyi da Umaymah. Dan taji yana kiran sunanta. Gefenshi ta ɗan tsaya tare da kallonshi ta wutsiyar ido. Shi wai ko shi kaɗai ko a ɗakinshi shi ɗaya sai ya zauna da kima-kiman riguna, ganshi wata ƙil basa damunshi". Haka taketa maganar zuci, har ya gama wayar da yakeyi bata, saniba. shi kuwa baibi ta kantaba yaci gaba da ɗan aikin da yakeyi a wayar. Jin shirune yasa ta ɗan kalleshi, ganin ya gama wayar da yakeyi ne yasa, cikin dakiyar murya tace. "Uhummm dama so nake in ba matsala ko zamu rinƙa yin abin buɗa baki ana kaiwa masallacin, da kuma bawa bayi nasu daban". Bai kulata ba, asalima yamutsa fuskarshi yayi, ya lura wannan abar bata gama iya sanin makamar mgna ba, ji yadda take mgn a kaikace. Kamar ba ba fullatanaba, bayan anyi ittifaƙin bayan larabawa babu ƙabilar dake da luggar iya sarrafa harshe sama da Fulani. Shiru tayi tare da tura baki kana ta ɗan murguɗashi, tare da cewa. "Ayyah ka amince mana?". kanshi ya sunkuyar tare da ɗaga system ɗinshi ganin biyu dai-dai ta cika. Miƙewa tsaye yayi tare da motsa lips ɗinshi a hankali yace. "Eh". Da sauri ta juya ta fita tana hararan bayanshi. Shi kuwa bedroom ɗinshi ya wuce. Rage kayan jikinshi yayi kana yasa hannunshi ya jawo pillow'nshi ya wurgar can gefe gaban gadon inda babu carpet, a hankali ya kwanta a wurin, Gudun kada daɗi gado yasashi yayi baccin da zai makara sallan la'asar, Yana konciya ba jimawa yayi bacci. Ita kuwa cikin jin daɗin amincewar da yayi, tacewa Ummi. "Ummi ya yarda yace muyi". Miƙewa Ummi tayi tare da nufar kitchen a tare suka shiga. Tana cewa. "Yauwa to taho mu gayawa Saratu abinda za'ayi. A tsaye suka sameta a tsakiyar kitchen ɗin kusa da kitchen table, tana gyara ganyen. "Yauwa Saratu kin wonke shinkarfa masan ne?". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Eh na wonke,kuma mafa tun ɗazu da nazo kuna kuma bacci na jiƙa wani, sai dai hannuna ya zarce yayi yawa, yanzu ina gama tsinkar ganyen zan kai markaɗen ne in na dawo an kwaɓashin sai in fara firan Arish ɗin". Ajiyan zuciya Ummi tayi tare da cewa. "Mugamshin". Babbar robar dake gefenta ta jawo tare da cewa. "Gashi kinga yayi yawa wlh mancewa nai sai naga kamar na gidan Gimbiya Aminatu zan jiƙa shiyasa, kinga da na haɗa da wanda kika jiƙan yayi yawa sosai, ko zamu rabashi biyu". Murmushi Shatu tayi ganin shinkafar tanada yawa, kai ta gyaɗa tare da cewa. "Ba matsala hakanma yayi dama mai yawan akeso". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Ga kuma ƙullun na dafa tun ɗazu har yayi sanyi, shiyasa nake sauri in kai markaɗen naga lokacin yayi nisa". Motsowa tayi inda take tare da cewa. "Ɗauki markaɗen ki kai bari in ƙarisa wannan aikin". Cikin mamaki tace. "A a bar". Da sauri ta katseta da cewa, jeki". To tace cikin mamakin sauƙin halinta ta ɗauki robar jiƙeƙƙiyar shinkafar da ta kai mudu biyar har ta ɗaura a kai, Ta kuma sauke jin Shatu na cewa. "Yauwa naga akwai murjejjiyar gyaɗa, ɗebo, da wata shinkafar kizo ga dabino da kwakwa a nan ki haɗa ki jikasasu ki tafi dasu, na kunune kafin a markaɗa wannan na masan shinma ya jiƙa sai a markaɗa miki shi. Da sauri ta juya tayi yadda tace ɗin tanayi tana nuna mata dai-dai yadda takeso, saida ta gama kana rufe babban roban da marfinshi sannan ta ɗaura ƙaramin a kai ta tafi. Ita kuwa Shatu matsowa tayi taci gaba da tsinkan ganyen, ita kuma Ummi freezer'n ta buɗe tare da ɗebo kayan ciki mai yawa, tazo. Ta wonƙeshi fes, kana ta watsa al'basa mai yawa a ciki, Sannan tasa citta,kanamfari, cory tare da sauran kayan ɗanɗanon. Gas ta kunna ta ɗaura tukunyar, sannan ta dai-dai-ta wutar. Wani babban roba ta ɗauko kana ta nufi Store Arish ta ɗebo mai ɗan yawa tazo tana fereshi cikin ɗan injin ɗin firar lokaci ɗaya tayi nisa a fitar. Ita kuwa Shatu tana gana gyaran ganyen ta ɗebo kayan miya tazo ta jajjagasu yadda takeso. Kusan a tare suka gama da Ummi. Wankeshi Ummi tayi bayan ta yishi tsillk-tsillk kana ta sashi a tukunya, tare ɗan yaryaɗa gishiri, ta rufeshi. Ta ajiye gefe. Ita kuwa Shatu cikin kula ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi me za'ayi da ganyen?". "Miyan da za'aci masar dashi". To bata amsa tana komawa cikin Freezer'n fruits ta ɗebo. Tazo tana wonkesu tare da shiryasu cikin tray mai girma, kana ta shirya wasu kuma a wani ɗan madaidaicin tray mai masifar kyau. rufesu tayi kana taje tasasu cikin Fridge. It's kuwa Shatu can nama ta ɗebo dai-dai misali wonƙeshi tayi tasa a tukunya tare dasa kayan ƙamshi dana ɗanɗano. ta ɗaura a wuta. Ummi kuwa ruwan tea ta ɗaura a ɗaya murhun dake gas ɗin babbane. Naman na sulaluwa ta kwasheshi tasa mai saida yayi zafi tasa al'basa, ya soyu yana ƙamshi kafin tasa jajjagen kayan miyar ta, Ya soyu kana ta ƙara wonƙe ganyen miyar yazo tasa, ta soyashi da kyau. kana ta zuba naman da sauran ruwan miyan. Tasa duk sauran kayan hadin ta rufe tukunyar. Sosai Ummi tayi mamakin yadda ta haɗa miyar, to sai dai bata damuba sabida sanin ko wacce mace da yadda take sarrafa girkinta, kai yadda kakeyi daban in wani ya gani yayi mamaki, yadda wani keyi da ban in ka gani kayi mamaki. Cikin ƙanƙanin lokaci dai suka haɗa duk aiyukan da zasu iya ajiyesu ba tare da sun samu matsalaba. Ita tayi miyar masan, ta kuma ƙarisa ferfesun kayan cikin da Ummi ta fara. Ummi kuwa ta tafasa musu tea ta ɗuɗɗura a flaks, Kana ta tafasa Arish ɗin. Dai-dai lokacin kuma Saratu ta dawo. Ita Ummi ce ta ɗan amshi ƙullun masar tare da cewa. "Gskya mun ɗan makara aikin Masar nan gashi ni hannuna baya tashi da wuri". Da sauri Shatu ta matso tare da miƙawa Ummi roban markaɗen kunun. Tace. "Ba matsala Ummi ni hannuna na tashi da wuri. Yanzu tace mana marƙaden kunun bari in kwaɓa mana Masar." Haka kuwa akayi Ummi ta fara tacewa. Ita kuwa kulun dafaffiyar ɗanyar shinkafar ta murmusa cikin marƙaden Masar, Kana tasa fulawa tare da yis kaɗan sannan ta tarfa gishiri kaɗan. Kana ta rufeshi a robar dan babbace, motso da robar tayi kusa da Gas ɗin yana ɗan jin ɗumin wuta. Gefen Ummi ta dawo wacce ta gama tace markaɗen A babbar tukunta ta zuba shi kana ta ɗaura kan wuta tare da dai-dai-ta wutar tanayi tana motsa kunun. tare da ɗan tarfa wanda ta rage, da surkin lemun tsami. Cikin Sa'a ɗaya ta dama kunun shinkafar fari ƙal tamkar madara. Sugar tasa ta juye a a ƙatuwar kula kana tasa a maidaciyar kula, Sannan tasa a flaks ɗaya, sai kuma tasa a Mug mai marfi duk ta kimtsasu gefe. Tuni Side ɗin ya ɗin ke da ƙamshi miyar masan da ferfesun nan. Buɗewa tayi ganin miyar tayine ta sauƙe ta maida gefe. Kana ta kalli Ummi tace. "Ummi je kiyi salla la'asar tayi, in kin dawo sai inje inyi". To Ummi tace ta fita tana mamakin saurin aikin Shatu. Koda taje tayi sallan ta dawo ta sameta tana sauƙe tukunyar ferfesun. ganin Ummi yasa tace. "Yauwa Ummi komai yayi dai-dai yanzu kaskon tuya zamu daura kinga kullun ya tashi". Cikin mamaki Ummi ta kalli Robar da taga har kullun na shirin zubewa. Ita kuma ɗiba tayi a wata roba kana duk tasa yankekken al'basane a ciki Sannan tasa sugar ta gauraya, sannan ta matso da kasko biyu, juyowa tayi ta kalli Saratu tace. "Yauwa Sara matso. Ke ki rinƙa yi kina sawa a wannan babban kulan in ya cika kisa a wannan shima. Ummi ke kuma kisa mana namu anan suyanki mukeson ci". Murmushi Ummi tayi kana tace. "To jekiyi salla". To tace kana ta fita. Ita kuma Ummi ta juya ta kalli Sara tare da cewa. "Kema kije kiyi salla". Cikin ci gaba da aikinta tace. "Ai nima nayi". "To shike nan". Ummi tace kana sukaci gaba da tuyan. A falo ta haɗu da Hibba da Jamil, sai dariya yakeyi cikin dariyar yace. "Yauwa Aunty Shatu dama idonki nazo in gani, dan ga Hibba kam ta kusa kasawa". Murmushi tayi dan bata da sauran ƙarfin yin dariya. Cikin ɗan fito da idanunta da suka ɗan faɗa tace. "Gani ras dani". Dariyar ƙeta mai cike da alamun yunwa da ƙishi yayi tare da cewa. "Inafa ras kalli yadda idonki ya fito kamar kinyi azumi goma". Murmushi tayi kana tace. "Um bari inje inyi salla". Sai ta kuma kalli Hibba dake lankwabe tace. "Sannu Hibba kwanta ki huta". Jalal da yanzu ya shigone ya ɗan taɓe baki tare da cewa. "To me tayi da zata huta tunda fa gari ya waya in anga ta tashi dai yin salla ne, tun tuni birgima take a tayis wai sanyi take nema". Dariya sukayi mata baki ɗayansu, Ita dai Shatu ciki ta wuce. Salla tayi kana ta fito. Koda tazo kitchen ta samu Hibba na suya musu Arish ɗin, tayi mamaki. Cikin wasa tace. "Kawo in karɓeki jeki kwanta". Cikin sanyi tace. "Ai Hamma Jabeer ne yace min in ina aiki bazanji wuya ba, zanfi ganin lokaci ya gudu". Dariya sukayi mata kana kowa yaci gaba da aikinshi. Ita Shatu miyar sahur na asuba ta ɗaura musu. Cikin ikon Allah shida dai-dai suka gam kan aikinsu. Bayan Shatu'n ta taya Hibba suya kwai daban, ta jerasu a Foodflaks, in ta ajiye fefeyin soyayyan ƙwai da yaji haɗi da diddigin kifi, sai ta zuba soyayyan Arish a kai kana ta kuma rufeshi da fefeyin kwai haka ta rinƙa jerasu saida ta cika kulan. Ummi kuwa ta sawa Saratu komai nata. Sannan suka kimtsa wurin fes suka fito da komai suka jera a dinning table. Nan duk suka wuce ɗauki. Wanka sukayi, kana sukayi al'wala sannan suka fito falo. A nan suka samu Imran, Jalal, Jamil, Sulaiman. Cikin gajiya Ummi tace. "Yauwa Jalal ku ɗauki manyan kulolin nan ku kai masallaci. Sauran madaidaitan kuma ku ajiyewa sarkin bayi. A bawa bayi da hadimai". Murmushi Jamil yayi tare da cewa. "Eh lallai bana bayi sun samu uwar gijiyar data tuna dasu, bayan kuma anayi musu nasu na daban". Cikin lumshe ido Shatu tace. "Eh suma suci abinda muke dafawa da kanmu, ba sai na gandun nasuba". Miƙewa sukayi suka ɗauki kulolin sun zo falon kenan Sheykh na shigowa, wani hadimi na biye dashi da manyan ledodi cike da ƴaƴan itatuwa. Kusan a tare suke mishi sannu da dawowa. Murya a bushe alamun ƙishi yake amsa musu kana ya nunawa Ummi leda ɗaya yace. "Ummi a wonke wannan a haɗa da dabino mudu uku a basu su kai masallaci". Ya ƙarishe mgnar yana wucewa. Da sauri Ummi tace to. Ta miƙe kenan Shatu tace. "Ummi zauna bari in wanke sun". To tace kana ta koma ta zauna. Ita kuma taje ta wonke ta zubasu a tray kana ta ɗauko plates and cups masu yawa, tazo ta miƙawa Imran. Da sauri suka amsa suka tafi. Jim kaɗan suka dawo, cikin gajiya Jamil yace. "Ummi ansha ruwafa mun samu Ladan na cin dabino". Da sauri Hibba ta miƙa tare da cewa. "Su ladanannan haka suke basa kiran salla sai sun sha ruwa." Dariya sukayi mata kana suma suka miƙe sukabi bayanta. Zama sukayi bisa kujerun kowa da abin yake hari. Sai dai kab ɗibsu da dabino suka fara. Ummi ce ta kalli Shatu tare da nuna mata babban tray'n da aka shirya komai na buɗa cikin Foodflaks guda 3 madaidata masu kyau, sai plate ɗin da aka shirya fruits masu ɗan karen sanyi, tupa, inabi ,kankana, abarba, gwanda, Lemu, ayaba, kana da dabino, da kwakwa, Sai goran zam-zam madaidaci, kana sai cup da tea spoon a ciki, sai fork and knife a gefe da gefen plate ɗin dake cike da fruits ɗin komai biyu akasa. Kulolin kuma ɗaya masane a ciki, ɗan namiyar kuma miyar Masar ne, sai ɗayan kuma, soyayyan ƙwai da dankalin, ɗayan kuma ferfesun kayan cikin ne. Cikin nitsuwa Ummi ta ɗago tray ta miƙa mata tare da cewa. "Yauwa gashi kai mishi lokacin shan ruwan na tafiya, yanzu zakiga ya fito". Cikin sanyi da gajiya ta amshi tray'n kana ta nufi falon nashi, cikin nitsuwa take takun, a hankali tayi sallama tare da kutsa kai cikin falon. A can bisa Dinning area ta hangoshi yana zaune, kan kujera ɗaya, ya kuma jawo ɗaya kujerar ya ɗaura sawunshi a kai ya miƙesu, System ɗinshi na bisa cinyarshi. A hankali take takowa saman steps ɗin tare da ratsa cikin jeren ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu darajar sheƙin Daimond sai sunkuyar da kanta tayi sabida ɗauke mata ido da suke. A hankali ta isa kusa dashi, cikin tura baki tare da ɗan murguɗashi ta ajiye tray'n, a tsakiyar table ɗin. ɗago kanta tayi da niyar ta ɗan juya, ta fita. Wani irin buɗe idanin tayi gaba ɗaya tare da zubasu, bisa sharaban ƙafarsa ta dama, wanda sanaɗin zaman da ya ɗan yi ya miƙe ƙafafuwan nashi bisa ɗaya kujerar ne yasa suka ɗan baiyana, wani irin kallo mai cike da ɗimuwa takeyiwa zanen dake bisa ƙafarshi ta dama, da sauri ta rumtse idanunta tare dasa hannun hagun ta kama kanta sabida wani irin sarawa da ya farayi da ƙarfi. Cikin sauri ta juyo tare da miƙa hannun damanta ta sauƙeshi kan...! Akwai kayan gyara na amare da uwar gidaye da masu jego, ga mai buƙatar saya ga number ta 09097853276 By *GARKUWAR FULANI* Ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu darajar sheƙin Daimond da yayiwa wurin labule. Yayin da kuma hankalinta da idonta duk suke kan ƙafar tashi tana kallon zanen da take gani har kamar motsawa yakeyi a jikinshin, da kuma suffar macijiya. A hankali ta ɗago ƙafarta tare da take step ɗin forko, hankalinta kuwa duk yana baya, har ta juya kanta gaba ɗaya sam ganinta baya gaba. Cikin rashin sa'a kafar ta tsallake step ɗin forko bata isa kan dandamalin ta biyu ba, ta sauketa, cikin akasi ƙafar ta sule tare da yin shuuuuu tayi gaba. Wani ƙara mai ɗan karfi irin na maiyin azumi ta sake tare da rumtse idanunta da ƙarfi tana jiran taji ta ina ɗin ta zai karye. Wani irin ihu ta kuma sakewa, lokacin da taji ta faɗi gib a kan stpes ɗin kanta ya bugi dandamalin sama. A hankali ya juyo kanshi ya kalleta a fakaice, Ba tare da yace mata ko ƙalaba ya juyar da kanshi ya fuskanci tray'n data ajiye mishi, plate ɗin fruits ya ɗan buɗe kana, ya ɗauki Fork ɗaya, janye ƙafafuwan shi, yayi ya sauƙo dasu ƙasa kana ya gyara zamanshi ya fuskanci Dinning table ɗin da kyau. Fork ɗin yasa ya fasa cikin dabino da yake irin na kwali nanne mai laushi ne, ture ɗan yayi gefe kana ya soki dabinon a hankali ya kai bakinshi, bayan yayi addu'o'in buɗa baki. Ido ya lumshe jin lokacin da sanyi da zaƙi da ɗanɗanon dabinon ya game mishi baki. Ita kuwa Shatu kuka tasa tare da riƙe ƙugunta, da kanta cikin muryar kuka take cewa. "Wayyo Allah na. Wayyo Ummey na, bayana ya karye ƙuguna ya ɓalgace, kaina ya fashe ƙeyana ya tarwatse". Ta ƙasa Glass ɗin table ɗin ya ɗan kalleta, kana ya maida kanshi yaci gaba da cin dabino, yana maijin wani irin masifeffen dariya na taso mishi jin raki da Shatu ke zubawa. Saida yaci ƙwaya bakwai, kana a hankali ya fara tsira Fork ɗin kan ƴaƴan inabi masu masifar sanyi da daɗi, ci yakeyi yana jin ƙishin daya addabi moƙoshinsa na wucewa. saida ya tsinke nonon inabin kab ya cinye, kana ya fara soka kankana da akayiwa ƙaƙanan yanka kana aka barbaɗa garin madara a samansu, shima shanye rabinshi yayi. Wani sassanyan gyatsa yayi tare da ture tray'n gefe. Ita kuwa Shatu sosai taji zafin faɗuwan ga azumi ga gajiyan aiki ga faɗuwa ga haushin yadda duk ihun da tayi babu wanda ya kulata, bare a kawo mata agaji, abun ya haɗe mata sai hawaye share-shere ta tabbatar da a gidansu ne tayi wannan ihun da gaba ɗaya iyayenta da yayunta da ƙanwarta duk suna kanta, da tuni an ɗagata a wurin ma. Bege da kewa da kukan rashin yan uwanta da watseman ahlinsu ne ya tunzura hawayenta. Ta kasa tashi sabida jikinta duk rawan yunwa da gajiya yakeyi ba ƙarfi sam. A hankali ya miƙe tsaye bayan ya sha ruwan zam-zam mai ɗan sanyi kan ƴaƴan itatuwan da yaci. System ɗinshi ya ajiye kan Dinning table ɗin, tare da wayarshi. Gefenta ya ɗan ratsa ya fara taka steps ɗin tare da kallonta a fakaice. Yana gab da sauƙane ya ɗan motsa lips ɗinshi tare da cewa. "Kaɗan kenan in dai baki dena samin ido a jikina ba, Faɗuwa harda kareireyewa zakiyi in baki kiyayi yimin kallon ƙurillaba, na lura ku mutanen wancan dajin bakuda abinda kukafi so sama da kallon killataccen wuri na jikin mutun. Muddin baki dena satan kallon jikina ba, sai waɗannan mayatattun idanun naki sun tsiyaye kin huta ki zama makauniya babu ɗan jagora. Kiyi dai a hankali ko kya samu ki mutu da idonki,". Ya ƙarishe mgnar yana tafi kamar bashi yayi mgnar ba. Ita kuwa Shatu hannun tasa ta sharce hawayenta tare da rakashi da hararan kai mugune. A falon ya samu su Ummi sunata dariya. Cikin sauri ya kalli su Jamil yace. "Kai wannan dariyar na menene, ku taso mu tafi masallaci". Cikin dariya Jamil yace. "Allah ko Hamma Jabeer ina zaton Hibba bata taɓa azumi ba sai bana. Ga yadda ta dawo wuni ɗaya, wai a haka kuma har ta fara lissafin wai yauwa yau mun kai ɗaya mun rage". Ɗan gajeren murmushi yayi tare da cewa. "Muhibbata tashi kije kiyi salla sai ki ɗan konta ki huta kafin a kira isha'i ko". Cikin sanyi tace. "To Hamma MJ". Jalal kuwa cikin yin ƙasa da murya yace. "Gobe ma zakiyi ne ko zaki huta". Cikin kwaɓe fuska tace. "Zanyi Umaymah tace, bana ko ɗaya in nasha sai na biya". Murmushi ya ɗan yi tare da cewa. "Ashe dai kin girma". Da sauri ta sunkuyar da kanta, shi kuwa yabi bayansu Jamil. Duk sukayi gaba, Sheykh kuwa na bayansu. har yaje tsakiyar falon sai kuma ya ɗan tsaya jin Ummi na ce mishi. "Shetu fa". Cikin saurin tafiya masallacin yace. "Tana can ta faɗi wai ko ta karye ne naji tana cewa ban dai san mataba". Yana kaiwa nan ya fita, ita kuwa Ummi da sauri ta miƙe cikin zaro ido tace. "Karaya kuma? Innalillahi yaushe". Tayi maganar tana nufar falonshi, A bakin ƙofar shigowa sukayi kiciɓis da ita, da sauri ta tareta tare da tallabota, jin yadda jikinta ke rawane ta jawota suka fito falon cikin tausayawa tace. "Sannu Shatu". Cikin tausaya Hibba taketa jera mata sannu. Ajiyeta bisa kujera Ummi tayi tare da cewa. "Baki sha ruwan ba ma ko?". Kanta ta gyaɗa mata alamar eh. Hakane yasa Ummi tacewa Hibba ta ɗebo mata, abin shan ruwan a take kuwa ta kawo mata. Bayan tasha ruwanne duk suka nufi cikin ɗaki dan yin salla. Daga yin sallan magriba su Jamil suka dawo sukaci abinci kafin aka kira sallan isha'i, kana suka koma akayi sallan isha'i da asham sannan suka nufi harkokin su. Shi kuwa Sheykh Jabeer daga Masallacin gidan Radio Ɓadamaya ya wuce, wurin yin shirin Fatawa. Sai tara dai-dai ya dawo, gida. A kitchen ya jiyosu. Bisa alamu duk girkin abincin sahur sukeyi. Shi kuwa bayan ya shiga, wonka yayi-yayi shirin bacci kana ya fito falonshi. Soyayyan Arish da kwan ya ɗanci tare da tarfa ferfesun ya ɗan ci. masa biyu. Jin cikinsa yayi tib ne, ya miƙe ya dawo falon. zama yayi bisa kujera yana kiran Umaymah, tana ɗagawa tace. "Jazlaan ina autata, ya azumin yau dai?". Gajeren murmushi yayi tare da cewa. "Umaymah autarki akwai raki, yau ita har ta fara lissafin an kai ɗaya saura 29/28". Dariya ta ɗanyi tare da cewa. "Kaɗan ma daga aikin Hibba". Sai kuma tace. "Ina ɗiyata kuma, ya azumin?." Kanshi ya ɗan jingina da kujera kana yace. "Alhamdulillah". Jin muryar Haroon na cewa. "Wai ɗazu ina ka shigane inata kiran wayar ka baka ɗagawa". Gyara zamanshi yayi tare da kurban coffee ɗinshi kana yace. "Na bar wayar a gida, da ɗaya na tafi na Fatawa". "To ya Amarya?". "Ban sani ba". Cikin dariya Haroon yace. "Allah baka haƙuri". Amsar wayar Umaymah tayi sukaci gaba da mgnar kan tafiyarsu Umrah. Daga bisani sukayi sallama, ya miƙa ya nufi ɗakin baccinsa. A kitchen kuwa, bayan sun gama komai na sahur ne. Ummi ta cewa Shatu taje ta ɗauko Foodflaks ɗin dake falonshi. To tace kana ta juya ta tafi. Koda ta shiga ɗan kalle-kalle tayi ganin baya nan, yasa ta harari falon ma gaba ɗayatare da cewa. "Mugu". Sannan ta ɗauki kwanukan ta fito. Duk sauran abincin Saratu suka haɗawa ta kai musu ita da sauran hadiman. Wanke-wanke tayi kana ta tattare komai sannan ta wuce part ɗin su. Su kuma ganin har goma tayi ne, yasa sukayiwa juna saida safe duk suka shiga. Yauma kamar daren jiya haka sukayi. Washe garima haka suke tafiyar da rayuwarsu. Cikin tsari da kuma samun damar hutu da ibada dan ribatar watan Ramadan ɗin. A hankali aka fara nisawa cikin watan Ramadan, kwanaki suna ɗan mirginawa da kaɗan-kaɗan. Yau wunin azumi na biyar kenan. Da hantsi bayan sunyi walaha sunyi karatun al'ƙur'ani. Sanin yanzu Ummi na jin tabsir ɗin da yakeyi a masallacin Masarautar Joɗa ne yasa, Shatu tana gaisheta ta fito. Hibba kuwa Side ɗin Aunty Juwairiyya ta nufa. Ita kuwa Shatu falonta ta fito. Bisa kujera ta zauna, tare da kiran number Junaidu wanda Rafi'a ce, ta batashi data tare da bata haƙurin bazata samu zuwaba, sabida yayanta yazo sun koma jiharsu tare. Ringing ɗaya ana biyu Junaidun ya amsa kiran ganin sabuwar number ne ya sashi cewa. "Ban gane wake mgna ba". Cikin jin daɗin yadda taji muryarshi ras alamun ya samu lfy tace. "Junaidu Adda Shatu ce fa". Da sauri ya tashi zaune bisa kekyawan gadon asibitin da yake kai tare da cewa. "Laah Adda Shatu kece? Wlh ban gane muryarki ba, Adda Shatu ya gida ya kwana biyu, ya kewan gida, ya lbrinsu Junainah". Cikin sauri tace. "Kai Junaidu duka wannan tambayoyin, ka bari mana in tambayeka ya jikinka, yasu Iri da Laure da Innaji da jikin". Murmushi yayi tare da cewa. "Alhamdulillah Adda Shatu duk jikinmu da sauƙin wasuma duk an sallamesu, yanzu nida Hamidu da Adamune kaɗai muka rage, kuma jikin da sauƙi sosai. Sai dan Baba Madune yana shan wuya, Satin daya wucema an sake yi mishi aiki". Cikin sanyi tace. "To yanzu su waye ke kula daku". Kanshi ya rausayar tare da cewa. "Uhumm mufa yanzu bamu da matsalar komai Adda Shatu kwantar da hankalinki, mun samu gata da kulawar wani babban likita mai mutunci. An canza mana asibiti ma an kawomu wani asibiti kamar na ƙasar woje". Cike da jin daɗi tace. "Alhamdulillah, dama dukkan tsanani yana tare da sauƙi". Dogon numfashi Junaidu yaja tare da cewa. "Adda Shatu, ashe mun samu nasara, an kora mana mugun babarbarenen nan,". Uhum tace a taƙaice. Shi kuwa Junaidu cigaba da mgna yayi. "Adda Shatu Ya Salmanu ba lfy, yazo dubamu da jiki shima an kamashi gado. Shi yake cemin wai su Bappa sun tafi Lardi. Ayyah Adda Shatu yanzu sai yaushe zasu dawo? Kina mgna dasu ne?". Cikin dariya tace. "Faɗi gsky dai Junainah kake son tambaya dai. Junaidu. Suna lfy ina mgna dasu. Sai bayan salla zasu dawo." Da sauri yace. "Dan Allah Adda Shatu turo min number su". To tace tare da gyara konciyarta. Nan dai suka ɗan yi hira, kana sukayi sallama. Sannan ta tura mushi number su ɗin. Suna gamawa ta kira Number Bappa. Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga. Cikin jin daɗin jin muryarshi tace. "Ina kwana Bappa na". "Lfy lau Alhamdulillah Shatu ya Azumi, da baƙon wuri". Cikin sanyi tace. "Alhamdulillah, Bappa yaushe zaku dawo". Dariya yayi mai ɗan sauti kana yace. "Bayan salla". Cikin lumshe ido hawaye na zuba tace. "Bappa ina jin kewarku, bani da kowa nawa kusa dani. In na tuno su ya Giɗi hankalina na tashi Bappa inyi ta kuka babu mai sanin irin ciwon da nakeji a raina". Cikin sanyi yace. "Kwantar da hankalinki Shatu, su Ya Giɗi suna raye, sai dai suna cikin mawuyacin hali, suna buƙatar addu'o'in ki musamman a cikin wannan mata mai alfarma, na sanki bakya wasa da riƙo da ibada, amman ki ƙara kan yadda kike, in sha Allah wata rana zasu dawo garemu, cikin sauƙaƙƙiyar hanya, addu'a itace abinda suke so, shiyasa na gaya miki abinda Allah ya nuna min a mafarki a kansu". Cikin sassanyan kuka murya can ƙasa tace. "Zanyi Bappa zan ƙara zan dage, kuma zan roƙi a tayamu addu'o'in a masallatai da wurin tabsir." Cikin jin daɗi yace. "Yauwa Shatu na, ki kwantar da hankalinki, ki zauna lfy da mutanen da kike tare dasu, kiyiwa mijinki biyayya, kiyiwa mayanshi biyayya bana son musu in babba ya gaya miki abu matukar bai saɓawa shariyar musulunci ba." Cikin sanyi tace. "To". Da sauri yace mata ga Junainah". Cikin jin daɗi tace. "To a bata waya". Tsalle Junainah tayi tare da cewa. "Adda Shatu, kizo Lardi garin da daɗi kullum sai an gasa mana zabbi ko Tattabaru, insha nono da zuma inci naman insha zuma, inci su inabi sai na ƙoshi". Cikin so da ƙauna da shaƙuwar ta da yarinyar tace. "Allah sarki Junnu ke ko kewata bakiyi bako?". Dariya tayi tare da cewa. "Nayi kewarku mana harda Ya Junaidu ma nayi kewarshki". Murmushi tayi tare da cewa. "Na bashi number ku, zai kira ku gaisa". Tsalle tayi tare da nufar ɗakin Ummey. Ita kuwa Shatu cikin dariya tace. "Azuminki nawa". Da sauri tace. "Azumi na ɗaya ranan nayi rabi daga safe zuwa azahar jiya kuma na ƙarisa rabin daga azahar zuwa mangriba". Wani irin dariya ne ya rufe Shatu dariya takeyi sosai. Kewa da bege da son ƙanwar tata ya rufeta. Da Sauri ta tsagaita da dariyar jin Junainah na cewa. "Adda Shatu Bappa yayi aure an samo mana wata Inna mai kirki". Cikin mamaki tace. "Ke Junnu ƙarya ba kyau fa". Da sauri tace. "To ga Ummey ki tambayeta kiji". Ajiyan zuciya ta sauƙe jin muryar Ummey cikin sanyi da jin daɗi tace. "Ina kwana Ummey na ya gida, ya Junnuna nayi kewarku, Ummey wai da gaske Bappa yayi aure". Murmushi mai faɗi Ummey tayi tare da cewa. "To duk Alhamdulillah muna lfy eh Bappa yayi aure an bashi ƙanwar innarku, Indo kin santa ai ita take bin innarku, Bata taɓa haihuwa ba, to ashe mijinta ya rasu. Shine yanzu aka aura mishi ita. Kuma tanada hankali kamar innarku". Cikin sanyin jiki tace. "Eh na san Umma Indo tanada kirki, to Allah ya baku zaman lfy yasa kuyi irin zaman da kukayi da Inna". Amin Amin tace kana tai mata nasiha Sannan sukayi sallama. Daga nan ta miƙa ta nufi ɗaki dan yin salla. Ana idar da salla suka fito, kitchen suka nufa ita da Ummi da Saratu da tun ɗazu tana nan. Suka fara aikin buɗa baki sunayi suna kimtsa komai. Kafin shida ta cikama sun gama komai. Yanzu in sun zo buɗa baki ita da Ummi da Hibba tsakiyar falon suke dawowa. Jalal, Jamil, Imran, Sulaiman, kuma su zauna a dinning table. Ya Jafar kuwa wani lokacin har can falon Sheykh zai wuce suyi buɗa baki a tare. Kana su tafi masallacin. Haka dai komai yaketa wakana cikin aminci da tsari. A wurin al'ummar Annabi kowa ya nitsu ya maida hankali kan ibada domin neman rabauta. Ƙarfe takwas dai-dai suka shiga kitchen dan yin aikin sahur. Cikin kula Ummi ta kalleta tare da cewa. "Ɗauko kwanu kan nashi". Kanta ta ɗan juyo ta kalli Ummi tare da cewa. "Ai bai dawo yaci ba ko?". Kai ta gyaɗa mata tare da cewa. "Baya cin ƙosai, kuma kinga doyan ma jiya baiciba, ya gaji dasu ne, ki ɗauko a juyewa su Saratu shi ki ɗan haɗa mishi wani abu kafin ya dawo". Cikin ɗan kauda kai tace. "Ummi ai ƙoshi yake shiyasa bazai ciba, a barshi kawai in yaji yunwar yacima wani bai saniba, ai yunwa ba Umaymah bace ko ke bare zaku lallaɓashi". Dariya Ummi tayi kana kuma ta haɗe fuska tare da cewa. "Je kiyi abinda nace ko". To tace ganin kamar ran Ummi ya ɓaci. Bayan ta dawo da kwanukan ne, Suka bawa Saratu ta juye, kana ta harhaɗa wonke-wonken ta fara. Ita kuwa Shatu cikin yin miƙa tace. "Ummi me zan dafa mishin?". Juyawa tayi tana haura wurin da Fridge yake tare da ce mata. "Duk abinda kika iya kika san ba mai nauyi bane". Kanta ta gyaɗa tare da cewa. "To". Cikin ranta tace. "Bari inyi Special Arish, in yaga dama yaci in yaso ya bari, mutun sai zaɓe-zaɓe kamar mai ciki. Dankali ta ɗan ɗebo da Nama, kwai, tumatur, kabeji, Bama, maggi, tafarnuwa man gyaɗa, komai dai dai-dai misalin yadda zata buƙata duk ta ajiyesu kusa da ita. Fere dankalin tayi ba tare da ta daddatsashi ba. Ta wonƙeshi fes kana tasa a ƴar tukunya tare da tarfa gishiri da ruwa dai-dai misali, sannan ta tafasashi. Kwan ta ɗauka ta fasa ta kaɗashi da kyau tare dasa yankekken al'basa da Curry da maggi da tafarnuwa ɗan kaɗan. Ganin dankalin yayine ta juyeshi a ɗan kondo ta tsaneshi. Tare da ɗan barinshi yasha iska, kaɗan. Kana ta ɗaura Naman da maggi da gishiri da Curry da tafarnuwa da al'basa. bisa wata a ɗan tukunta. Sannan ɗaura man ta ɗauki dankalin ta tsomawa cikin kwan tana soyashi, saida ta gama ta ajiyeshi gefe. kafin nan naman kuma yayi lugub yayi laushin. saida ruwan ya kusa ƙarewa sai ta ƙara wata al'basar da tumatur suka nuna tare sannan ta kwashesu. Kabejin ta yayyanka ƙanana sannan ta ɗauki dafaffan kwai ta yayyanka shi da ɗan girma. Kana tasa Maggi da al'basa da Bama ta gauraya kana Ummi ta miƙo mata ɗan ƙaramin Foodflaks alamun ta amsa ta saka. Kanta ta jujjuya tare da cewa. "Bari in sa mishi a plate kawai tunda ya dawo". Da mamaki Ummi ta kalleta tare da cewa "Yaushe ya dawo?" Plate ta ɗauko tare da cewa. "Tun ɗazu". Da sauri ta sunkuyar da kanta ganin kamar Ummi na mata kallon Mamaki da tuhuma. Ita kuwa Ummi cikin Binta da ido tace, Ya akayi kika san ya dawo". Kai ta rausayar tare daci gaba da aikin kamar bataji Ummi ba. Plate ɗin ta ajiyeta, ta zuba Arish ɗin gefe kana tasa haɗin naman gefe, ta kuma zuba na Kabejin shima gefe. Ta shiryashi yayi kyau sosai. Ɗaya plate ɗin ta kife kanshi. Kana tasa spoon da Fork a cikin tray'n data ajiye plate ɗin. Ɗan madaidaicin flaks ɗin coffee ta ajiye gefe, kana tasa cup da tea spoon a ciki. Sannan turashi gefe. Zuwa lokacin kuma tuni Ummi da Saratu su gama aikin sahur ɗin har Saratu ta tafi. Sauran ta sako a wani plate ɗin tare da cewa Ummu gashi. Amsa Ummi tayi tare da cewa. "Ɗauki ki kai mishi to". To tace tare da ɗaukan tray'n ta fita. A tsaye ta sameshi cikin wani tattausan jallabiya da alamun wonka ya fito, Sai wani irin masifeffen ƙamshi yakeyi. Cikin nitsuwa ta wuce ta bayanshi, inda yake tsaye yana kunna Tv. Bisa santa table ɗin glass mai garai-garai dake tsakiyar falon ta ajiye mishi. Kana ta juya a hankali ta fita. Kai tsaye ɗakinta ta wuce, nan ta samu Hibba tuni tayi bacci. Wonka tayi da ruwan ɗumi tare da shafa mai kana tasa wata tattausar rigar bacci gajera iya karta guiwa. Hibaji ta zura a jikinta kana ta haura gado ta konta tare da jawo blanket ta duƙunƙune a ciki. Sabida ita bata son sanyi, shiyasa takesa ƙaton hijabi kana ta shiga borgo. Badon Hibba Bama dake masifar son sanyi da kashe AC'n zatayi. Ƙarfe ɗaya dai-dai ta tashi bacci al'wala tayi kana tai ta nafila hakama Ummi. Sheykh Jabeer kuwa tuni ya tashi shima. Ya kira su Jalal ma a waya ya tashesu. Ƙarfe huɗu da rabi dai-dai ta isa falonshi da tray'n abincin sahur ɗin shi. Ta ajiye ta juyo kenan shi kuma yana fitowa falonshi. Tazo tsakiyar falon kenan tana tafiyarta a hankali ba zato ba tsammani taji daram-dam ƙaran bindigar da kullum da asuba sai an saketa sau biyu, ta kuma kasa sabawa dashi bare ta daina tsoronshi. Wani irin tsalle da zabura tayi tare da ficewa a guje tana cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". Bayanta yabi da kallo tare da taɓe baki kana ya nufi Dinnin area. Washe gari da safe yau Jumma'a kuma, yaune azumi na shida. Bayan sun fitone, Ummi ta kalleta cikin dariya dan tuno yadda ta fito falon Sheykh Jabeer a guje da asuba, tana jan Allah ya isanmata ana tsinka mata zuciya, Cikin murmushin tace. "Ummi dariyar me kikeyi ne?". Cikin gimtse dariyar tace. "A babu, yauwa tashi muje ɗazu Gimbiya Aminatu ta aiko, wai tayi kewarki kwana biyu azumi ya ɓoyeki bakije ba". Cikin murmushin tace to muje Ummi". Ta ƙarishe mgnar tanayin gaba Hibba na biye da ita a baya. Cikin sauri Ummi tace. "A haka zaki fita ba al'kyabba". Kai ta ɗan dafe tare da cewa. "Wayyo Allah na, Allah kuwa ni nauyi sukemin wannan tsarabe-tsaraben wuya gareshi". Murmushi Ummi tai tare da miƙewa ta ɗauko al'kyabbar. Tazo tasa kana suka fita. Da Side ɗin Hajia Mama suka fara, A falo suka samesu. Cikin fuskar ba yabo ba fallasa Hajia Mama ta amsa gaisuwar Shatu. Batool kuwa sai auna mata harara takeyi. Hira suka ɗan taɓa kana suka fito. Har sun fito Shatu ta ɗan kalli Ummi cikin sanyi tace. "Ummi jirani anan bari inje in isar da saƙon gaisuwar Ummey na wurin Hajia Mama". Da Mamaki Ummi tace to kana ta juya ta nufi ciki, ganin Hibba za biyota ne tace. "A a jirani ina zuwa". Haka suka tsaya suna jiranta. A hankali ta turo ƙafar falon. Da sauri Hajia Mama ta zuba mata ido fuska cike da tsana. Batool kuwa binta da ido takeyi ganin wani irin takun isa da ƙasaitar da takeyi. Kujerar dake fuskantar wacce Hajia Mama ke zaune a kai ta zauna. Ƙafarta ɗaya ta ɗaura kan ɗaya. Kana ta jingina da kujerar, cikin tsare Hajia Mama da ido tace. "Uhummmm kin sanni sarai, kar tasan karne, duk motsinki a tsakiyar tafin hannuna kike, dan haka gwara kiyiwa kanki gada ki fita harka da rayuwar mijina! Da ƙannenshi da wanshi. In kuwa kikaƙi zakisha mamakin Shatu." Tana faɗin haka ta miƙe, tana kallon Batool da tun randa akace Shatu tazo ta bawa Hajia Mama haƙuri da ta shigo tayi wasu kalaman ya ɗaurewa Batool kai ta kasa tantance tsakanin aya da tsakuwa, shiyasa batayi gigin yin mgn ba, sabida tuno abinda Shatu tace mata a ranar cewa. "Mijina kike so ko, to kizo in ya amince ya kalli inda kike na daƙiƙi biyu rak zan sashi ya aureki". Da sauri Batool ta dawo daga duniyar tunanin da take jin ƙaran rufe ƙofar da Shatu tayi. Ido ta maida kan Hajia Mama dake gurnani kamar macijiya. Jim kaɗan ta fito. Cike da son gano wani abu Ummi ke binta da ido, amman ta kasa gano komai domin Shatu ta iye takunta, ta fito kamar ba itaba gaba tayi. Kana suka nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu. Suna shiga ta miƙowa Shatu da Hibba hannu kusa da ita ta ajiyesu. Bayan sun gaisane ta kallesu tare da cewa. "Azumi ya boyeku da yake ku ragwagene". Murmushi sukayi tare da cewa. "Kai Gimbiya jiya nefa kawai bamu zoba". Cikin kula Lamiɗo dake shigowa yanzu zai sabunta al'wala zai wuce masallaci yace. "Shatu matar malam bauɗeɗɗe". Murmushi tayi tare da sunkuyar da kai. Hibba ce tace. "Sai na gaya mishi". Dariya sukayi kana suka sallamesu suka tafi ganin lokacin sallan yayi. Har sunje bakin ƙofa Gimbiya Aminatu tace. "Yauwa Jakadiya kayan miyanku da saura ko ya ƙare?". Cikin rusunawa tace. "A'a da saura sosaima". Kai ta gyaɗa kana suka tafi. A hanyarsu ba komawane Shatu tace. "Ummi wanne kayan miyan ne?". Cikin sanyi tace. "To ba kince bakya son na Hajia Mama ba, shine ita kuma Gimbiya Aminatu ta haɗo miki komai yanzu dasu muke amfani ai". Cikin gamsuwa tace. "To wancan ɗinfa ya akayi dashi?". "Umaymah ta tafi dashi duka". Hibba ta faɗa mata. Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Ba matsala". Nan suka tafi suna salla suka shiga kitchen yau harda Hibba. Sannu-sannu dai bata hana zuwa sai dai a daɗe ba'a jeba. Yau an cika azumi goma. Gobe za'a shiga goma na wuya, an gama na marmari. Yau kuma makara Shatu tayi. Ganin har su Jalal sun zone yasa Ummi ta nufi ɗakinsu. Ai kuwa kan gado ta hangosu. Tadasu tayi kana ta fito. Tana cewa. "Shatu kiyi sauri kizo ki kaiwa Sheykh nashi". Kusan a tare suka diro ƙasa. Brush kawai sukayi suka fito. Da ƙaton hijabin ta fito. Tana zuwa Dinning area Ummi ta miƙa mata tray'n abincin nasa. Amsa tayi ya juya ta nufi falonshi. Tsaye ta sameshi gaban show glass ɗin dake gefen Fridge ɗinsa dake Dinning area, Cup ne a hannunshi cike da madarar gongoni da molt a haɗe. A hankali ta wuceshi kaɗan ta ajiye tray'n. Kana ta juyo da nufin sauƙowa, taku ɗaya tayi a na biyu ta iso gabanshi kenan. Aka saki bindigar shaidar huɗu da rabi tayi. Wani irin zabura tayi tare da af....! Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276, domin shiga Normal group wanda a wata ɗaya za'a, gama Part one. Ko kima kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank, domin samun shiga Special Group wanda a sati biyu cakal za'a gama Part two da izinin ubangiji, 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853297. Ke mai haushi kin turo ɗarinki uku, kinzo kinata haushi, nace ki turo ac no ɗinki in maida miki kuɗinki kin tsaya yimin tumasanci shiyasa nayi Black ɗinki, a rashin Sa'a na haɗa da number ki na goge. Kuma baki Turo ac na na meda miki shi ba. To Alhamdulillah a take a lokacin nayi miki sadaka da ɗarinki uku, ubangijina shine shaidata, banci kuɗinki ba, nasan zakiga PAGE ɗin sabida akwai waɗanda basu san darajar Allah da Manzonsa da iyayensuba, zasu fitar, to kiji ni Shatu na sauƙe nauyin ɗarinki uku. By *GARKUWAR FULANI*Cikin tsananin firgita, da tsinkewar zuciya da tsoro, tare da kerman jiki, ta juyo ta fuskanci inda yake tsaye tare da abkawa jikinshi. Cikin abinda bai gaza one second ba tamkar gilmawar walƙiya ya janye jikinshi ya kauce gefe. Hakan yasa ta faɗa jikin show glass ta ruggumeshi gam-gam cikin tsuma da karkarwa tare da sa hannunta duka biyu ta riƙe kanta, tana mai cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil, Auzubikalimatillahi ta'ammati minsherri makalaƙa." Tanayi cikin ɗan ɗaga murya mai baiyana firgicin da take ciki. Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin masifeffen dariya ne ya taso masa tun daga ƙasan zuciyarshi har zuwa kan lips ɗinshi dole ya taune lip ɗin shi na ƙasa. Kana sai ya gimtse ya murtuƙe fuska cikin tsare gida yace. "Karki fasamin abuna!". Sai lokacin hankalinta ya dawo jikinta. Janye jikinta tayi daga jikin show glass ɗin da abkawar da tayi kanshi marfinshi ya ɗan tsage. Nannauyan ajiyan zuciya ta sauƙe da ƙarfi. Kana ta tura baki sannan ta juya ta fara tafiya tana ƙunƙunin. "Allah ya isana banzan al'ada a rinƙa razana mutun anasa hanjin cikina na hautsunewa". Baki ya taɓe kana ya zauna bisa kujerar ya jawo tray'n ya ɗibi abincin tuƙeƙen tuwo ne da miyar kase. Tana fitowa sukayi sahur ɗin a gaggauce sabida lokacin ya ɗan ƙara to. Washe garin da rana bayan anyi sallan azahar. Ya shigo kamar ko yaushe. A falo ya samu Ummi da Hibba ita kuwa Shatu tana ɗakinta tana karatu so take ta samu izu uku a wunin yau ɗin. Gefen su ya ratsa kana ya zauna bisa kujerar zamanshi. Bayan sun mishi sannu da zuwa ne, ya kalli Hibba cikin kula yace. "Muhibbat ya azumin". Cikin langwaɓe kai tace. "Da wuya". Kanshi ya jinjina kana yace. "Jeki kira Aunty Juwairiyya". To tace tare da miƙewa da sauri ta fita. Shi kuwa wayarshi ya ciro ya kira Jalal dasu Imaran yace suzo su sameshi a falo. Jim kaɗan duk suka shigo. Key ya zaro daga al'jihun tattausan jallabiyar dake ƙasan al'kyabbar jikinshi ya miƙa wa Jamil tare da cewa. "Ɗauko min briefcase a kan Bedside drower'n." To yace kana ya juya ya tafi. Shi kuwa Ummi ya kalla tare da cewa. "Ummi me dame kuke buƙata ne?". Cikin kulawa tace. "Akwai komai, sai zam-zam ɗin kane ya ƙare saura baifi gora biyarba". Gyara zamanshi yayi tare da cewa. "Ba matsala zai isa". Lokacin Jamil ya iso. Miƙa mishi jakar yayi, tare da zaunawa gefenshi. Shi kuwa buɗe jakar yayi. Murmushi Jamil yayi ganin tana ciƙe maƙil da rafan dubu-dubu sabbi dal-dal. Rafa huɗu ya miƙawa Jamil hakama Jalal da Imran da Sulaiman. Sannan ya kallesu tare da cewa. "Kuje KMC plaza ku zabi kayan sallan. Sai ya kuma kalli Aunty Juwairiyya yace. "Aunty Juwairiyya, kuje tare dasu, da Ya Jafar ayi yadda aka saba. Sannan ku zaɓi abin buƙatar ku." Gyara zamanta tayi tare da cewa. "To mu gode, kuma za'ayi yadda kace." Sai kuma ya kalli Ummi yace. "Ummi kada ki manta da su Saratu". Murmushi tayi tare da cewa. "In Sha Allah babu abinda za'a mance". Kai ya jinjina kana ya zaro rafan guda biyar ya miƙa mata, sannan ya miƙa wa Aunty Juwairiyya wasu rafofin kana ya bawa Hibba biyu. Daga nan sukaci gaba da tattaunawarsu. Washe gari kuwa da safe, suka shirya tsab zasu fita. Aunty Juwairiyya ta Ummi cikin yin ƙasa da murya tace. "Ko zan kirawo Shatu mu tafi tare da ita ne?". Da sauri Ummi tace. "A a mijinta baice muje da itaba mujata mu tafi. Muje dai mu zaɓo mata duk abinda takeso". Cikin gamsuwa da hakan tace to. Hibba kuwa cikin sanyi tace. "Ayyah Ummi muje da ita". Fitowar Shatu ne ta samesu a tsaye cikin shirin tafi yasa ta kalli Ummi cikin sauri tace. "Ummi ina zakuje?". "KMC plaza". Ta Bata amsa a taƙaice cikin sanyi tace. "Nima inzo muje, in samu in fita insha iskan woje". Jalal ne ya ɗan kalleta tare da cewa. "Boss ya hana". Ido ta zuba mishi kana ta juya ta kalli Ummi cikin sanyi tace. "Shike nan Ummi kuje, Allah kiyaye hanya." Amin Amin sukace har sun juya zasu tafi sai kuma tace. "Ayyah Ummi dan Allah karku daɗe". To sukace kana suka fita. Shiru ta zauna a falon ba kowa hakane yasa ta kunna TV tashar Zee world. Wani film mai daɗi ta samu sukeyi, sai dai bata san forkonshiba, bisa alamu duk sabone. Konciya tayi bisa 3 str tana kallo wayarta na hannunta. Tana mgna da Rafi'a. A haka bacci yayi awon gaba da ita. Can Cikin bacci take jin alamun kamar mutun na tsaye a kanta, cikin magagin baccin ta buɗe idonta. Gabann Tv ta ganshi ya kashe TV kana ya juyo ya kalleta a fizge yace. "Ba salla sai kallo da bacci". Jin haka yasa ta miƙe zaune tana gyara mayafin kanta. Shi kuwa tuni ya wuce Side ɗinsa. Tana idar da salla ta fito. Nan ta samu Saratu tazo, kitchen Suka shiga suka fara aikin yamman. Sai gab da la'asar su. Ummi suka dawo da kaya niƙi-niƙi. Nan suka ajiye sukayi salla kana suka shiga kitchen ɗin. Hibba kuwa yashuwa tayi a ƙasa tana birgima kamar bazata kai magriba. Sai bayan sallan isha'i sun gama aikin sahur ɗin ne. Suka dawo falo, nan Ummi ta nuna mata ɗinkunanta da aka bada tun Umaymah bata tafiba. Sosai taji daɗin kayan da ɗinkunan, lallai tana son dogayen riguna Amman tana son surkawa da Shadda, atampa, leshi, musamman Waɗan nan ɗinkunan sunyi masifar kyau. Ko wanne dai-dai jikinta kamar an gwada ta. Daga nan kuma suka nuna mata gellulluka da hibai da takalma da saraƙunan da suka zaɓo mata bayan sun zaɓawa kansu. Sun nuna mata nasun ma. Ummi ta ƙara da cewa. "Duk zannuwan da abun ɗinkawan kuma an bawa Kabir telen suma duk cikin KMC suke. Nanda salla dai komai zaizo dai-dai. Cikin jin daɗi tace. "Ngd matuƙa Ummi Allah ya saka da al'khairi". Amin Amin tace. Kana tace. "Sheykh zakiyiwa godiya". Shiru tayi kamar bataji ba. Hibba kuwa cikin jin daɗi tace. Aunty Shatu na zaɓa mana wani Shadda lace mai masifar kyau iri ɗaya na ɗauka mana Royal blue and white Golding color. Nace a tsantsara mana dogayen riguna". Murmushi tayi tare da cewa. "Kai kinko kyauta mana". Daga nan suka tattara tarkacen suka nufi makoncin baccin su. Zaune take gefen Ummi tana riƙe da waya cikin murmushi tace. "Allah ko Umaymah munyi kewarki". Cikin jin daɗi Umaymah tace. "To ko zaku zomin Barka da sallane". Da sauri tace. "Eh Umaymah Allah in ya yarda zamuzo ki tambayan mana shi". Cikin dariya Umaymah tace. "Yoh mace da mijinta sai wani ne zai tambayar miki". Cikin sanyi tace. "Uhummm". Ita kuwa Umaymah cewa tayi. "Ina Umminku?". Da sauri tace. "Gata ta ƙarishe mgnar da miƙawa Ummi wayar. Cikin fara'a suka gaisa kana Umaymah ta tambayeta ya yaran nata, tace duk suna lfy. Nan take ce musu ta cewa Shatu ai a saudia zasuyi salla. Sosai Shatu ta tayasu Murna. Suna cikin hirar Hadimai guda uku suka shigo da jakukkunan guda uku. Rusunawa sukayi bayan sun gaidasu ne, suka ajiye jakukkunan tare da cewa. "Gashi biyun inji Lamiɗo ɗaya kuma Gimbiya Aminatu ce tace mu kawo miki". Sukarishe mgnar suna kallon Shatu. Godiya tayi musu kana ta kalli Hibba data miƙo mata kuɗi sun kai dubu biyar. Ta gane manufar Hibba shiyasa ta amsa ta basu. Godiya sukayi kana suka tafi. Jim kaɗan Hadiman Hajia Mama sukazo da saƙon Hajia Maman. Sosai Shatu tayi godiya ta mashi kuɗi a hannun Hibba ta basu. Nan Hibba ta tattara kayan ta shigar dasu, zata shigar dana HAJIA MAMA tace "A Hibba barsu zan shiga dasu." Gefe ta nuna mata tace ajiyesu anan. Bayan sunyi sallan azahar sun fito zasu Fara aiki ne ta kalli Ummi tace. "Ummi bari inje inyi godiya wurin Hajia Mama". Cikin tsareta da ido tace. "Ki bari mana sai ansha ruwa sai in rakaki daga nan kiyiwa Lamiɗo ma godiya. Duk dai wannan kyauta da yakeyiwa duk ahlin masarautar Joɗa in lokacin salla ya gabato amman muje kiyi godiyar." Da sauri tace. "No Ummi ba sai an rakani ba, zanje ni ɗaya ma, kinga nasa al'kyabba". Daga nan ta fice, cike da mamaki suka bita da ido. Bayan kamar 37 minute ta dawo cike da fara'a sukaci gaba da aikinsu. Can da suka fito dan yin sallan la'asar, Ba kayan ba dalilinshi. Da sauri Hibba tace. "Aunty Shatu kin shigar da kayan ne?". Ci gaba da tafiya tayi tare da cewa. "Maisu ta aiko an kwashe mata abunta dai". cikin mamaki sukabi bayanta. Yau azumi goma sha huɗu gobe 15 in Allah ya kaimu. Bayan yaci abinci ne ya kira Umaymah nan yake ce mata. "In Allah ya kaimu gobe iwar haka ƙarfe goma na dare zuwa sha ɗaya jirginmu zai tashi Umaymah". "Kai da waye zaku tafi ne?". "Nida Dr Aliyu, da Barrister Kamal, sai kuma Ya Hashim da Galadima, da Wambai da Abba na da cimgan ɗin shi". Da sauri tace. "To wai kana nufin kai bazaka je da taka cingam ɗin bane?". Cikin sanyi yace. "Kiyi haƙuri Umaymah dan Allah na roƙeki kada kice inje da kowa, dan Allah a barni mana in huta in na bar ƙasar kam". Shiru Umaymah tayi saida taji ya kai ayane tace. "Shi kenan Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy, kuma muna nan tafe". Amin Amin yace kana sukayi sallama. Washe gari kab mutanen masarautar Joɗa masu zuwa Umrah sun gama shirin su. Bayan ansha ruwa anyi sallan isha'i ne suka shiga kitchen dan aikin sahur, koda ta ɗauko Foodflaks ɗin da akasa mishi abin buɗa baki ko buɗe su baiba. Hakane yasa Ummi tace to maza ta dafa mishi wani abun. To tace kana ta juya ta ɗauko, kaza, kwai, dankalin turawa kaɗan, maggi, gishiri, tattasai, attaruhu al'basa mai Curry, Duk ta matso dasu kusa. Sai kuma ta ɗebo Kabeji karas. Ta miƙawa Saratu tace. "Yauwa Sara goga min su ƙananan, kada ki haɗasu wuri ɗaya, kana ki yayyaka min al'basa sannan ki jajjaga min wata." Ta faɗin tana tura mata Attaruhu da al'basan. Cikin nitsuwa Saratu tace. "To Aunty ba matsala". Ita kuwa Ummi meda hankali tayi kan girkin sahur ɗin. Wanke rabin kazar tayi, tare da sata a tukunya ta watsa al'basa da maggi da tafarnuwa da citta da kanamfari kaɗan. Sannan ta rufeshi. Tasa wuta yadda ya kamata. Kana ta jawo robar dankalin ta fara ferewa tare da cewa. "Allah aikin nan yana yawa Ummi, kusan wuni muke a kitchen mu kuma kusan kwana shima wai bazaici abuba sai sa mutane aiki". Tayi mgnar cikin gajiya da kuma iya gskyar ta, dan muddin kasha ruwa tafa burinka ka samu ka huta. Juyowa Ummi tayi ta ɗan kalleta tare da cewa. "A'a ai bakya son hutun tunda kikaje kika samu Juwairiyya kikace ta huta taji da aikin gidanta, nan zaki rinƙa yi, sannan in Hajia Maman ta aiko ki kora Hadiman dashi, ko kisa Hibba ta kaiwa bayi shi. Kinga duk sun gaji sun daina kawowa, sai Na Gimbiya Aminatu, shi kuma Sheykh yace a dena kawowa tunda kice zaki iya da aikin. Yanzu da kin bari suna kawowa dai da wata ranama sai munga dama mushiga madafa". Sunkuyar da kanta tayi tare da yin shiru kamar bata nan. Yes ta san duk abinda Ummi ta faɗa hakane. Ƙarisa feree dankalin tayi kana ta wonƙeshi fes ta ɗaurashi a wuta, ya dafu sosai kana ta sauƙeshi a gefe. Zuwa lokacin kazar ma tayi lugub, haka yasa ta sauƙeshi ta juyeshi a plate, zare ƙasusuwan tayi duka, sannan ta ajiyeta gefe kusa da dankalin. Jajjageggen Attaruhu da al'basan da Saratu ke miƙa mata ta amsa. Cikin plate ɗin dafeffen dankalin ta juyeshi kana tasa kazarma a ciki. Sannan ta jujjuyasu ta caƙuɗasu da kyau, kana tasa Maggi gishiri ɗan ƙanƙani, sai kuma Curry. Kwan dake gefe cikin ɗan wani kwanon tangaran ta jawo, ta fasa kwan ta juye cikin haɗin kaza da dankali da jajjagen ta ɗan gwarayasu. Hibba data shigo yanzu ne tace. "Yauwa My Aunty dama kwaɗayi ne ya koroni nazo in shiga kitchen." Murmushi tayi tare da cewa. "To matso ki tayani aikin ɗan zuba min ruwan zafi kan Karas ɗincan. In yayi ɗumi ki juye ruwan cikin kwandon kabejin nan ruwan zafin ya ɗan razana ganyen, sai ki miƙo min shi nan". To tace tare da fara aikin. Ita kuwa Shatu ɗiban haɗin ta rinƙayi tana mul-mulawa kamar Yan boll, saida ta gama sannan, ta ɗaura man gyaɗa. yayi zafi ta fara suyasu, saida ta soyasu duka tasa a Foodflaks kudun kada yayi sanyi ta matsar dashi gefe. Kana ta matso ta ta amshi Kabeji da Karas ɗin. Mai tasa kaɗan a tare da al'basa, kana tasa jajjagen kaɗan, ta soyasu, sannan ta ɗauki sauran murmusheshen kazar tasa a ciki kana ta juye Kabeji ta Karas ɗin, sanna tasa Maggi, mintuna biyu zuwa uku ta sauƙesu. Ta zubawa Hibba da Ummi kana tasawa Sara. Sanin ya dawone yasa ta shirya mishi komai a tray'n. Kana ta nufi Side ɗinshi. Ummi kuwa da Hibba a falon suka zauna suka fara ci suna santi. Ita kuwa Saratu tattare wurin tayi ta kimtsa komai ta goge sauran kwanuka kana ta tafi. Shi kuwa Sheykh Jabeer, tuni ya gama kimtsa komai da zai buƙata in yayi tafiyar. Bai wani ɗauki abu da yawa ba. Komai na ɗauki shi ya kimtsashi bisa tsari. A hankali ya taso daga bakin gadon hannu yasa ya shafa cikinsa, Yunwa yakeji kuma ya gaji da masan shiyasa yau bai kulaba. Folon ya nufo tare dasa kuɗin dake hannunshi a al'jihun jallabiyarsa. A hankali ya tura ƙofar ya fito. A dai-dai lokacin itama ta turo ƙofar shigowa falon . A hankali ta shiga Tsakiyar falon ya nufa, bisa kujera ya zauna, ita kuma kanta a sunkuye ta iso inda yaken. Ɗan sunkuyowa tayi ta ajiye tray'n kan santa table ɗin, gabanshi. Kana a hankali ta fara miƙewa zata tashi. Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta, da yatsarshi ya nuna mata ta zauna. Cikin kwaɓe fuska tace. "In zauna?". Kanshi ya gyaɗa mata alamar eh. Cikin turo baki ta harari gefen fuskarshi, kana ta ɗan rusuno a hankali ta zauna. Bakin kujerar dake bayanta. Cikin muryar ƙunƙuni tace. "Bacci nakeji". Bai kulata ba, sai ma gyara zamanshi da yayi ya nuna mata plate ɗin gabanshi. "Cikin cinna bikin sama tace. "Bana gane kurmanci". Juyowa yayi ya watsa mata narkakkun idanunshi da bata iya gano meke cikinsu cikin nata. Karon forko kenan data ga zahirin yadda kalar ƙwayan idonshi suke, sosai kwarjinshi da haibarshi ya danne tsiwarta, a hankali ta matso kusa da inda yake. Rusunawa tayi har ƙasa a hankali ta buɗe plate ɗin data shirya mishi Chechen balls da ganyen Fork ta ajiyeyi mishi gefen plate ɗin kana tasa hannun zata ɗauki flaks alamun zata samunshi tea a cup ɗin. Yatsarshi manuniya ya ɗan ɗaga tare da kaɗa mata ƴatsar alamun bai sataba. Yamutsa fuska tayi tare da turo baki cikin yin ƙasa da murya can cikin maƙoshinta tace. "Karkaci ma in kaga dama". Ta gefen idonshi ya kalleta ba tare da ya juyoba yana kallon yadda takeyin mamul-mamul da lips ɗinta, Gyara zamanshi yayi tare dasa hannun ya ɗan ɗauki Fork ɗin Chechen ball ya ɗan soka kana ya ɗago alamun zai kai bakinshi sai kuma ya maida cokalin ya ajiye. Ɗago kanshi yayi ya zuba mata ido na 3 second kana ya nuna mata idonshi tare da lumshesu alamun ta rufe idonta tako gane abinda yake nufi. Cikin gunaguni tace. "Nifa zan tafi bacci nakeji, ba sai na rufe idona a nanba zan tafi kaci abinci k". Shiru tayi ganin kallo da yake mata da mayun idanunshi. tura bakin tayi tare da sunkuyar da kai kana ta murguɗa bakin. Shi kuwa Sheykh Jabeer, numfashin ya ɗan fesar kana a hankali ya muskuta ya gyara zamanshi, kaikaicewa ya ɗan yi yasa hannunshi cikin al'jihun jallabiyarsa. rafan dubu-dubu sabbi dal-dal ya fito dasu guda shida. Miƙo mata su yayi. Hannunta ta miƙo a hankali ta amshi kuɗin. Gyara zamanshi ya kumayi kana yasa yatsunshi biyu ya jawo ɗaya plate ɗin ya rufe ɗayan. Tsuke fuskarsa yayi da kyau tare da kafeta da ido cikin kakkausar murya yace. "Yau zanyi tafiya daga yanzu, zuwa ƙarfe biyu. Duk inda naje inada lbrin gidan nan duk abinda zakiyi zan sani, duk motsin masarautar Joɗa. Saboda haka ki kiyayi kanki da yiwa mutane tijara, Bana son fitsara da rashin sanin darajar manya, ki tsaya matsayinki, bana son shishshigi cikin al',amuram rayuwata. Ki kuma kiyayi murguɗa wannan bakin fitsarar in ba hakaba wata rana in kin murguɗa minshi bazai dawo dai-dai ba haka zai zauna a murguɗe a karkace, Allah ya nuna miki matsayi da darajar miji." Ƙasa tayi da kanta tare da cewa. "Kuɗin na meye ne". A daƙile yace. "Na yagawa ne, kije ki yaga ki zubdasu". Kallonshi ta ɗan yi ganin hankalinshi baya kantane, ta miƙe tsaya ta juya ta fita. Shi kuwa bayanta yabi da wani irin kallo. Sosai yaci Chechen balls ɗin dan yayi daɗi sosai, kuma gashi rabanshi da abinci tun jiya iwar hakan, dan haka yaci iya abinda zai iya ci, kana ya miƙe yaje yayi wonka ya fara shiryawa. Ita kuwa Shatu tana fitowa a falo ta samesu gaba ɗayansu harda Ya Jafar da Aunty Juwairiyya da kuma. Su Jalal da Hajia Mama. ganin hakane yasa ta ɗan juya ta nufi falonta bedroom ta wuce taje ta ajiye kuɗin sannan ta fito. Gefen Ummi ta zauna kusa da Hibba suka ɗan fara hira da Hibba ko inda Mama take bata kallaba. Can ya fito cikin shigarsa ta yau da kullum. Da sauri Jalal ya miƙe ya amshi ƴar Kekkyawar jaka ta maza dake hannunshi. Dai-dai lokacin kuma Ya Hashim ya shigo tare da cewa. "Sheykh mu tafi lokacin yana ƙurewa". To yace kana ya kalli Ummi, Mama, Aunty Juwairiyya, Hibba, yace. "To zamu tafi". Kusan haɗa baki sukayi wurin cewa. "Allah ya kiyaye hanya ya kaiku lfy ya dawo daku lfy". Amin Amin sukace. Ƙwayar idanunshi ya ɗan juya ya kalli inda take ba tare da kowa ya gane ya kalletanba, kana suka juya suka tafi nan su Jalal Jamil duk suka fito dan sune zasu kaisu Airport. Daga nan suka tafi sha biyu dai-dai jirginsu ya tashi a international airport Ɓadamaya. Sai kusa ƙarfe ɗaya su Jalal suka dawo, Sosai suka mamakin wannan karon Ya Jafar bai ce zaibi Sheykh ba. Haka dai rayuwa tai-ta juyawa sa'a da wuni yau azumi ashirin ne aka kai wanda bahaushe ke cewa an gama goma na wuya za'a shiga na ɗokin salla. Tunda Sheykh ya tafi baiyi mgnar da kowaba a cikinsu har yau kwanansa biyar. Yana can ƙasa mai tsarki ibada tayi daɗi baya tuna kowa baya tuna komai sai kusanci yake nema da yardar mahalinsa. Ko bacci Allah ya yaye mishi sai yayi baccin awa ɗaya zuwa biyu a wuni daga wannan kuma ya gamsu. Kullum a a masallaci yake kwana. In gari ya waye sai yayi walahanshi yayi karatun awa biyu, sai ya tafi gidan ƙanan Sitti dake nan Madina wanda shidasu Baba Kamal duk nan suka sauƙa. to a nanne zai ɗan yi bacci. To yau kuma shine daren da za'a fara tuhajjudi kuma sannan yaune suka baro Madina suka iso makka. Kai tsaye gidansu Sitti suka wuce. Nan suka samu itama Sitti da ahlinta sun iso, Umaymah ma da Haroon yau suka iso. Kana Ibrahim ma da ahlinshin sun iso daga ƙasar Cairo sosai Sheykh Jabeer yaji daɗin hakan. Yau ɗin kuma Yana ɗaya daga cikin dararen da ake tsammanin laylatul Ƙadir. Kasan cewar babbar zuriya yake. Sheykh Jabeer Ali, ɗane ga Sheykh Ali jikan Sheykh Abdulkareem kenan, Wanda sunanshi aka sawa Jabeer. Yana matuƙar son Jabeer sosai. Hakan yasa tare suke shiga harami tare suke fitowa. A nan gida Kautal kuwa hada-hadan jama'ar musulmai na tafiya bisa tsarin addinin musilunci kowa na shirin salla da kuma tarban wannan kwanaki goma na ƙarshe. Yau miyar shuwaka sukayi da tuwo. Suna gama kimtsa komai ne suka dawo falo. Tv suka kunna suna kallo, suna ɗan hira. Gyara zama Ummi tayi tare da cewa. "Lallai yau in munyi garaje zamu makara". Da sauri Shatu tace. "In sha Allah bazamu makara ba, wannan uban bindigar da kukace in lokacin sallan Tuhajjudi yayi zava bugata ai zata tashemu". Hibba ce ta ɗan gyara kwanciyar ta, tare da cewa. "Kalli lokacin shabiyu saura yanzuma za'a fara, Ummi kai mana Tashar Saudi". Ta ƙarshe mgnar tana kallon Ummi da Rimote ke hannunta. To Ummi tace kana ta. Juya musu tashar. Inda suka samu tuni sun fara sallan Tuhajjudi. Inda ake nuna harami kai tsaye. Shiru sukayi suna kallon yadda haramin ya cika yayi maƙil da al'ummar Annabi. Kab an nitsu bakajin komai sai sautin muryar limamin dake karatun al'ƙur'ani cikin zazzaƙar murya mai daɗin sauraro. Koda aka tafi ruku'u gaba ɗaya a tare aka sunkuya hakan yasa abin yayi wani irin kyau mai ɗaukar hankali. Sun jeru tamkar zanen fefeyi. Hakama da suka tafi sujjada. Musamman da yake cameran ɗaukar sama akayi. Suna ɗagowa kuma aka juya cameran ya fuskanci limamin da sauran mamu na sahun forko wanda duk manyan malamai ne. Cikin wani irin kallo Hibba ta miƙa da ƙarfi tare da...! Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 ko kiyi min TRANSFER din 1k Dan samun Special Group ta asusuna na 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* Tare da cewa. "Lahh Ummi kalli Hamma Jabeer kusa da Uncle Jabir Ali ɗin can". Cikin Murmushin Ummi tace. "La ai kuwa, Allah sarki masha Allah, tabarakallah. Allah ka ƙarawa Annabi daraja, Allah ka ƙara bamu hasken addini da imani a zuƙatanmu." Amin Amin Hibba tace. Tare da juyowa ta kalli Shatu da tayi kamar bata jisu ba, Sai tea ɗinta take zuƙa a hankali. A zahiri zakace idonta kan cup ɗin yake, amman a baɗini kan allon TV'n idonta yake, ta zubawa fuskarshi ido. Duk da bawai kai tsaye shi kaɗai ake ɗaukaba, limamin dake jansu ake ɗauka hakan yasa suma suka fito da yake yana cikin mamun limaman sahun forko. Sosai take ƙare mishin kallo tare da tsarin shigarsa dana mutanen da yake cikinsu. Sam bazaka iya bambance shi da suba, Especially ma Sheish Jabir Ali da yake matuƙar kama dashi. Haka nan taji wasu irin zafafan hawaye masu ɗumi suna tsastsafo mata cikin jijiyoyin idonta. Ta kuma kasa janye ƙwayar idanunta kanshi. Tana kallon tsarin shigarshi da kullum take ganinshi a matsayin takura. Lumshe idonta tayi, kana ta buɗe su. Ummi ta kalla wacce farin cikin ta ya fito fili. Hakama Hibba. Sai murnar abun takeyi tamkar tayi tsalle ta shiga cikin TV'n,. Ganin sun sunkuya kai ruku'uh da zasu tafi sujjada ta biyu ne, kuma an ɗaga camerar an maidata ɗaukar samane. Yasa ta miƙe a hankali bisa santa table dake tsakiyar falon ta ajiye cup ɗin kana ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi kinji masallacin Joɗa ma sun fara sallan kuma muna zaune". Da sauri Ummi ta miƙa tare da cewa. "Farin cikine ya rufeni Shatu,. Muje muyi al'walan mu tafi". Uhum tace ta juya ta nufi falonta tana mai share hawayenta da har yanzu suke zubowa, tanajin zuciyarta na amsar wani nannauyan abu a kan Sheykh, ta yarda ta gamsu cewa mutun me ibada da imani da ilimi abin sone a zuciyar kowane mutum na gari. Bayan sunyi al'wala ne suka fito cikin manyan jihabai ƙatti har ƙasa suka nufi woje. Ananne Shatu tai mamakin ganin yadda kusufa-kusufa matan masarautar ke fitowa, duk suka nufi hanyar zuwa masallacin ta ƙofar dasu Lamiɗo ke bi. Suna fitowa jikin masallacin sai ga wani ƙaton rumfa na ƙara an lailayeshi da wani irin yashi fari ƙal-ƙal kana ga hasken wuta a cikinsa. ko wacce da sallaya a hannunta tuni wasu kuma sunma shimfiɗa sallayunsu sunbi jam'i hakanan matan maƙota da sauran matan bayi da hadimai duk nan suke zuwa. A jeru gaba ɗaya ananne ga kafaɗar matar sarki gata baiwa. Babu matsayi ko milki bare isa ko ƙasaita. Haka dai suka bi jam'i sai ƙarfe uku aka idar akayi addu'o'in kana akashafa aka kai sujjadar ƙarshi ta witirin. Kana akayi taiya akayi sallama duk kowa ya nufi gidanshi. Daga nan kuma aka kama aikin sahur. Suna dawowa Hibba ta kuma kunna TV nan ta samu su tuni su sun idar. Wasu nata ɗawafi ne sai addu'o'in ake jerawa. wanda sai kaji tsikar jikinka na tashi sabida yadda yake ratsa zuciya da jini. Washe gari da bayan sallan isha'i da asham, yanzu Jalal da Jamil ne kaɗai ke zuwa dan Imran da Sulaiman ma dasu aka tafi. Haka yasa yanzu duk suna zama a Dinning table suyi buɗa baki a tare. Jalal ne ya ɗan kalli Ummi cikin cin Beans salad da Shatu tayi musu. Hibba ce keta santi tana cewa. "Alhamdulillah yanzu dai saura mana azumi tara ko takwas". Murmushi sukayi, ita kuwa da sauri tace. "Kai takwas nema in sha Allah". Jamil kam tuni yake dariya tare da cewa. "Tara ne". da sauri ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi wai haka ne?". Cikin dariya tace. "A a ban saniba Hibbat." Plate ɗin data zuba ferfesun jan nama ta jawo tare da fara ci tana lumshe ido tace. "Takwas ɗin nema in Allah ya yarda". Allah yasa haka Shatu tace. Sai yanzu Jalal ya ɗan kallesu tare da cewa. "Ashe dai duk kanwar jace". Murmushi Ummi tayi kana sukaci gaba da cin abinci. Yau dai ana zaton salla saura kwana biyar ko shida. Da hantsi suna zaune dan yau sun tashi da wuri. Aunty Juwairiyya ce tayi sallama tare da shigowa, Bayan Ummi ta amsa mata. Gefen Hibba ta zauna tare da cewa. "Alhamdulillah Ummi ɗinkunan mu sun dawo, yanzu KB ya kawosu ya shigo ko?". "Eh ya shigo mana". Juyawa tayi ta kalli Hibba tare da cewa. "Je kice ya shigo Hibba yana nan zaki kanshi cikin baƙar mota". To tace tare da miƙewa da sauri. Jim kaɗan suka shigo tana gaba da jaka a hannunta yana biye da ita a baya da ƙattin jakunkuna guda biyu da wani yaro shi shima da manyan jakukkunan biyu. A tsakiyar falon bisa carpet suka aniye jakunkunan kana, ɗaya yaron ya juya ya fita. Shi kuwa Kabir ya zauna a ƙasa bisa carpet ɗin tare da cewa. "Barka da hantsi Ummi". "Barka dai Kabiru, munyi Sa'a an cika mana al'ƙawarin ko". Murmushi yayi tare da cewa. "Sosai ma kuwa Ummi aini telane mai amana". Hibba ce ta ɗanyi murmushi tace. "To ka bari a yebeka mana". Cikin dariya ɗan matashin yace. "A a ai duniyar yanzu kawai ka yabi kanka, dan ba lallai bane wani ya yaba maka". Dariya sukayi duka. Kana ya fara firfito da kayayyakin. Ko wanne da sunan maishi a jikinshi. In ya fito dana Ummi sai ya miƙa mata, in ya fito dana Aunty Juwairiyya da yaranta sai ya miƙa mata. Hakama na Hibba yana fitarwa yana miƙa mata. Shatu da yanzu ta fitone, ya kalla tare da cewa. "Barka da safiya Sayyada Shatu". Murmushi tayi Allah ya sani in sun ce mata Sayyada dariya suke bata wato irin ita matar Al Sheykh ko. Cikin nitsuwa da danne dariyarta tace. "Barka dai". Sai kuma ta ƙara so ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi waye ne shi?". "Telan mune". Ta bata amsa a taƙaicd. Cike da mamaki tace. "To ina ya sanni?". Hibba ce ta amshi zancen da cewa. "A hoto ya sanki, da mukaje kai ɗinkunanki hotonki kawai aka nuna mishi, ya ɗinka kuma kinga komai yayi dai-dai ko". Kai ta jinjina tare da cewa. "Lallai kam yayi ƙoƙari". Cikin dariya yace. "Uhum ai na iya aikina sosai Sayyada". Yanzu kam dariya sukayi duka. Kana ya zaro kayanta a ƙalla kala takwas ya miƙa mata. Amsa tayi tare da cewa. "Sannu". Hibba kuwa irga kayan tayi tare da cewa. "Kb saura kala bibbiyu a namu nan gani basu". Kanshi ya ɗan sosa tare da cewa. "Wannan yarinya akwai son kalato laifin mutum to sai jibi zan kawosu ko kuma in bawa Su Jamil in sunje amsar kayansu". Cikin murmushin Aunty Juwairiyya tace. "Yauwa ka bawa su Jalal ɗin ma kawai". To yace, kana ya miƙowa Ummi ƙatuwar jakukkuna guda uku tare da cewa. "To Ummi ga na yaranki". Murmushi tayi tare da cewa. "Ka kyauta min Kabiru ngd matuƙa, Allah yayi al'barka". Amin Amin yace kana ya sallamesu ya fita. Ita kuwa Ummi Saratu ta kwaɗawa kira tana zuwa. Ta tace. Jeki kira duk sauran hadimai suzo duk wadannan Kabiru yazo ya gansu ranar." Da sauri tace. "To kana ta juya ta fita. Ita kuwa Ummi. Inda take zaune ta nunawa Shatu. Tare da cewa. "Zo nan ki zauna, zasuzo, ko wacce zata gaya miki sunanta, sai ki duba sunan jikin kayan sai kibata, su duk kala ur'uku akayi musu. Zaki basu da kuɗi dubu biyar-biyar. Kai ta gyaɗa kana da sauri ta koma ɗalinta. Sabida. Sai yanzu ta gano me zatayi da wannan kuɗin da ya bata kenan. Kuɗin ta kwaso kana tazo ta zauna. Nan suka rinƙa zuwa suna gaidata da gaya mata sunansu. Kana Hibba ta irga dubu biyar, ta ɗaura kan kala bibbiyu sun ta basu. Ummi kuwa jakan gabanta ta buɗe tana basu takalma. Aunty Juwairiyya kuwa jakar hijabai ta buɗe tana basu. Suna godiya suna tafiya. Haka sukayi tayi har kusan awa biyu kafin suka gama, duk kayan sun ƙare sai kuɗin ne ya rage. Ganin lokacin salla yayi ne, suka tafi. Bayan sun idar da salla ne, suka fito. Nan a falon Shatu suka zauna. Suna ɗan hira sabida yau aikinsu baida yawa, kuma Saratu nacan na rage musu. A hankali wayar Ummi ta fara suwa, alamun ana kiranta. Da sauri ta kalli Hibba tare da cewa. "Hibba ɗauko min wayata a ɗaki". Miƙewa tayi tare da cewa to. Jim kaɗan ta fito da wayar da sauri ta miƙa wa Ummi wayar a kunne tare da cewa. "Amshi Ummi kiyi mgna na amsa kiran Hamma Jabeer ne, kin sanshi baya kira biyu." Cikin sauri da tarin jin daɗi Ummi tace. "Assalamu alaikum". Shi kuwa Sheykh Jabeer a can saudia yana tsaye ne a gaban dreesing mirror yana gyara igiyoyin al'kyabbar jikinshi. Tare da saƙala wayar a kunnenshi ya matseta da kafaɗarshi. Alamun sauri yake yana shirin tafiya haramine. Cikin sanyi yace. "Wa alaikissalam. Barka da gida Ummi". Fuska a sake tace. "Barka dai Sheykh, ya ibada?". "Alhamdulillah Ummi, yasu Jalal". "Suna lfy, kuma basa wasa da ibada, yanzu Jamil ya dena zuwa hirama wata ƙil kuma ya ɓata da Khadijah naji yanzu wata Maryam yake kira, Jalal ne dai yake ɗan fita shima ba sosai ba". Gyara tsayuwarshi yayi tare da cewa. "To Alhamdulillah, eh shi Jalal ba matsala fitanshi, nasan dashi. Ya Hibba kuma tana azumi ko batayi?". Cikin murmushin da kallon inda Hibba take tace. "A a Hibba ai an girma yanzu ta rage rakinma". Ɗan karamin mataji ya ɗauka yana kontar da sajenshi yace. "To Ummi na gaisheku, na kira Aunty Juwairiyya kam nani jikin ya Jafar da sauƙi sosai mun gaisa da Hajia Mama, har take cemin Affan ɗina zai dawo a salla". Da sauri tace. "Uhum Sheykh". Ajiye kum ɗin yayi tare da cewa. "Na'am Ummi". Cikin sanyi tace. "Ga Shatu". Shiru yayi baiyi magana ba, kuma bai katse kiranba, jin haka yasa ta kuma cewa. "Sheykh". "Na'am Ummi". Ya kuma cewa. A hankali tace. "Ga Shatu". Still baiyi mgn ba, hakanne yasa a hankali ta mannawa Shatu wayar a kunne ta. Kana ta sa hannunta ta kamo hannun Hibba suka fita babban falon. Shi kuwa Sheykh Jabeer shiru yayi tsaye gaban dreesing mirror, yana kallon gemunshi. A hankali yake jiyo sautin sauƙar numfashin can ƙasa-ƙasa, ɗis ɗas haka yaji ƙasan zuciyarshi na harbawa. Ita kuwa shiru tayi tanajin sautin tasbihi da yakeyi can ƙasan-ƙasan maƙoshinsa, Lips ɗin shi na motsawa a hankali suna fidda sautin can ƙasa. Jin shirun yayi yawane yasa a hankali ta buɗe bakinta tare da cewa. "Assalamu alaikum". Sai kuma tayi shiru ta kasa kunnen dan jiran amsarshi. Gyara zamanta tayi tare da ƙara riƙe wayar, numfashi ta sauƙe a hankali. Hakan yasa yaji sautin iskar. Har ta cire tsammanin zai amsa sai kuma taji muryarshi can ƙasa yana cewa. "Wa alaikissalam. Ashe kin iya sallama?". Ya jefo mata tambayar a gajarce. Cikin juya ido tace. "Ba'a koya min da wuri bane!." Shine mgnar da tayi niyar gaya mishi, sai kuma tayi mgnar a zuci, ta danne abun. Sabida tana son ta nemi al'farman addu'o'in a kaba, aka yayunta da suka bace, shiyasa cikin sanyi tace. "Eh, Ummi ta koya min". Shiru yayi kamar bai jitaba, ita kuwa a hankali tace. "Ina kwana". Kanshi ya ɗan kalla a madubi tare da cewa. "To Kifin rijiya su nan yanzu wunine". Cikin sanyi da sassauta Muryar son isar da buƙatar ta tace. "To ina wuni". "Alhamdulillah". Ya bata amsa. Miƙewa tsaye tayi ta nufi bedroom ɗinta. Tare da cewa. "Ya ibada?". "Alhamdulillah". ya kuma cewa. "Har ya kai hannunshi zai janye wayar sai kuma ya tsaya jin tana cewa. "Uhmm, Ayyah Yah Sheykh..". Sai kuma tayi shiru. Cikin saurin jin an kira salla murya a nitse yace. "Uhumm Ayyah, me ɗin?". Da sauri tace. "Dama.. dama!!...". Gajeren tsaki yaja tare da cewa. "Sauri nakeyi zan tafi masallaci, kada kisa na rasa damata". Cikin rauni da muryar dake nuna cewa tana zubda ƙwalla tace. "Ayyah dan Allah da Manzonsa. In kaje kayi min addu'a a harami mana". Juyowa yayi yana kallon Haroon da Ya Hashim da suka shigo yanzu alamun kiranshi zasuyi. Cikin wata iriyar murya a hankali yace. "Addu'ar me zan miki?". Murya na rawa tace. "Allah ya dawo min dasu Yayana lfy, ya kare minsu a duk inda suke, ya baiyana sucikin gaggawa". Cikin rashin fahimtar zancen nata yace. "To zan miki saboda Allah da Manzonsa da kikace". Cikin jin daɗi tace. "Ngd matuƙa Allah ya biya maka buƙatunka." Wani irin sassanyan numfashi ya sauƙe tare da lumshe ido a hankali yace. "Amin ya rabbil izzati, kema kuma kiyita addu'a ki dage da ambaton Allah zai cika mana dukkan burinmu". Yana faɗin haka ya katse kiran. Ita kuma murmushi tayi tare da share hawayenta. Cikin sanyi tace. "Ya Allah ka dubemu da idon rahama". Hibba dake shigowane tace. "Amin Amin." Daga nan suka fito falo suka kama sabgoginsu. A kwana a tashi asarar mai rai. Yau da gobe kayan Allah. Kamar yau aka kama azumi gashi yau an kai azumi na ashirin da tara. Wanda ake tsammanin tsalla gobe ko jibi. Irinsu Hibba duk sunfi fatan wata ta dawo yau. Gaba ɗaya wunin yau aiki Ummi da Shatu da Saratu suka wuni yi, wanda aikin salla ne. Zabbin da Jalal ya kawo bisa umarnin Hammansun. Da kuma kajin da Lamiɗo yasa aka rabawa al'ummar masarautar Joɗa. Ko wani Side in dai akwai mace kaji goma ake kaiwa. Da tarin kayan miya komi da komi, wanda shi cikin lambun masarautar ake cirewa. Kajin kuma daga gidan Gidan gonar MJ aka kawo, kana zabbin da aka kawo manyan sashin Masarautar Joɗa ma daga gidan gonar MJ aka kwasosu. Haka ƙoyayen kaji. Duk an rarraba ko ina. kuma duk saida aka yanka su aka gyarasu aka rarrabusu, dan haka aiki kawai aka fara babu kama hannun yaro. Hadimai da bayi sunata aiki. Duk sauran ɗinku nan suma sun dawo. Kasan cewar kusan a kitchen ɗin suka wuni ne, yasa Shatu ta ɗauki zabbi uku tun da azahar tayi musu gyara na musamman. Hibba kuwa tana Side ɗin Aunty Juwairiyya anayi mata zanen lalle. Akan sai dare za'ayiwa Shatu shiyasa taketa kimtsa aiyu kanta da wuri. Dama sunje da sassafe an wonke musu kai an gyara musu. Ummi kuwa tayi lallenta na gargajiya tana kwance a falo. Hakane yasa Shatu ta kira Gimbiya Aminatu. Cikin wasa tace. "Gimbiya a ƙaro min mai taya aiki yau Ummi na tasa lalle, Hibba ma tana can ana zana mata, nida Sara ce kaɗai a kitchen." Dariya Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa. "To Sayyadar Sheykh bari Larai tazo". Cikin jin daɗi tace. "To Gimbiyar Lamiɗo". Dariya sukayi duka kana sukayi sallama. Juyowa tayi ta kalli Ummi tare da cewa. "Tace zata turo Larai, Ummi ta iya aiki ko?". Kai ta gyaɗa mata tare da cewa. "Sosai ma kuwa". Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa kana ta miƙa wa Ummi wayarta tare da cewa. "Ummi sai mun nitsu ki bani number Gimbiya Aminatu". To tace kana ta koma kitchen ɗin. Wanke zabbin tayi fes tare da ɗan matsa lemun tsami kaɗan a ciki. Kana ƙara lallaɓeshi. A tukunyar ƙirar ƙasar Cameroon ta zubasu. Kana tasa al'basa, Curry, Maggi, kanamfari, citta, tafarnuwa kaɗan, da gishiri ɗan ƙanƙani. Ta rufe tukunyar da zabbin uku suka cikashi. Bisa gas ta ɗaurashi kana tasa wutan dai-dai. Saratu kuwa sa sauran tayi a babbar tukunta tasa kayan ƙamshi da ɗanɗano. Sannan ta ɗaura. Dai-dai lokacin Larai ta shigo. Bayan sun gaisa ne, ta ɗauki markaɗen waken ƙosan da zasuyi na kaiwa masallaci. Da markaɗen tattasan da taruhu da al'basan. Ita kuwa Shatu yau kunun basise ta dama mai kyau, ta cika kulolin. Kana Ta daura ruwan tea Yana tafasa ta ɗura a flaks. Duk wannan zabbin sunata sulaluwa suna bararraka sai wani irin masifeffen ƙamshi da yake tashi. Har yawunsu na tsinkewa. Fruits ta ɗebo a Fridge ta gyarasu ta shiryasu a tray biyu shiri mai kyau. Kana ta medasu cikin ƙaramin Fridge ɗin data kashe dan sanyi su ya daidaita. Larai na dawowa, suka fara suya. Ita kuma ƙullun waken kaɗan ta ɗiba. Kana tasa dafaffan ƙan data ɓare. Da al'basan da kifin data tafasa ta murmusa a cikin ƙullun ta sa mai da Maggi curry da dai sauran kayan haɗi ta kulla alala. Ta ɗaura a gefen tukunyar zabbin. A ƙalla awa ɗaya zabbin na ɓararraka kana tazo. Tasa jajjagen taruhu da al'basan, A ciki. Sai ta ɗan tarfa soyayyan mai kaɗan a ciki ganin kamar man jikin zabbin bazai mata yadda takeso ba. Kayan ɗanɗano ta kuma sawa, da yankekken al'basa mai yawa ta zuwa a ciki. Kana ta maida marfin tukunyar ta rufe. A hankali danderun zabbin ya fara taushi yana lugub cewa, Ƙasusuwan suna saɓulewa daga jikin naman. Tuni su Sara kuma sun gama soya ƙosan, nan ta ciccika kulolin da za'a fidda kana ta ɗiba musu nasu, daban. Sannan suka tattare mata wurin suka tafi sabida ita ta kusa gama nata aikin. Koda alalan ya nuna ta kwashe tasa a kuloli biyu. Sai kuma ƙaramar kula daya. Ya rage zabbin ne kawai a wuta. Rage wutan tayi sosai yadda zasuke jin wutar na ratsasu da kyau. Tattare wurin tayi ta kimtsa komai. Kana ta fito falo. Ƙarfe biyar da rabi. Tace lokacin data zauna ta ɗauki wayarta Ummi kuwa na cire lallenta. Ya kuwa yi baƙi yayi kyau. Hibba ce ta shigo cikin Langwaɓe kai tace. "Aunty Shatu me ake dafa mana yau tun waje can ake jiyo ƙamshin na fitowa a gidanki". Cikin gajiya tace. "Tuwone miyar taushe". Cikin zumbura baki tace. "Tab wlh bazanci ba, inyi azumi a bani tuwo ta yaya zan haɗiyeshi, yaseen zan koma wurin Aunty Juwairiyya nagama tayi awara, ƙamshin gidanki na jiyo na gudo". Dariya Ummi tayi tare da cewa. "Hibba dai cokali a saki a daɗi ko?". Murmushi sukayi dukansu kana suka konta A kan kujerun. Ganin Ummi ta miƙene yasa Shatu cewa. "Yauwa Ummi duba mana kitchen ɗin kiga ko Danderun yayi". To tace kana ta shiga ta duba. Sannan ta fito tare da cewa. "Yayi sosaima, kai gskyar Hibba nima da bana jin ƙamshi yau naji ƙamshin girkin. Jeki sauƙe kawai kiyi wonka kuzo ki huta kafin a kira salla". To tace kana. Ta miƙa taje ta sauƙe. Binta a baya Hibba tayi tare da cewa. "Wai Aunty Shatu bakuga lallena bane banji kunce yayi kyau ba". Murmushi tayi tare da cewa. "Kayya Hibba ai yanzu kam idanunmu basa gani". Ta ƙarshe mgnar tana sauƙe tukunyar, Kana ta ɗauki Foodflaks guda uku biyu manya ɗaya karami. Gaba ɗaya ƙasusuwan sun saɓule. Romon yayi kaurin diddigin nama. Rabin zabuwa ta sawa Sara da Larai a ƙaramar kular. Kana tasawa Gimbiya Aminatu gudar. Su kuma tasa musu ɗaya da rabin a kularsu. Kular datasa alala data kosai ta jere a babban tray'n. Da tray'n fruits, ɗin a gefe. sannan da flaks ɗin kunu ta bawa Hibba tare da cewa. "Ki kawai Gimbiya Aminatu. Na ƙaramar kular nasu Sara ne". Amsa tayi kana ta fita. A can ta samu Ya Jafar shida Lamiɗo bisa alamu yau tare zasuyi buɗa baki. Ita kuwa Shatu Hibba na fita. Ta sauƙe babbar tukunyar tafashen naman kajin ta ajiye gefe. Dama zabbin duk a freezer'n suka sasu. Ɗan buɗe bakin tukunyar tayi yadda zasu sha iska su kama jikinsu. Jajjageggen Attaruhu da al'basan kuma ta sashi a Fridge. Kana ta fito da komai ta jere musu a dinning table. Sannan ta wuce ɗakinta. Wonka tayi da ruwan sanyi duk da bata son sanyi To amman duk jikinta huruwa yake tamkar wuta. Haka yasa tayi da ruwan sanyi. Tana fitowa ko mai bata shafa ba. Wata atamta mai taushi riga da zani, ɗinkin Borno sitayel yayi masifar yi mata kyau. Ɗan kwalin ta ɗaura a sauƙaƙe sabida duk jikinta rawan yunwa da azaba yakeyi. Cikin falon ta fito nan ta samu Hibba ta dawo. Jalal, Jamil, suma sun zo. Ummi ma ta fito da alamun tayi wonka. Tana isa ana kiran salla. Nan sukayi buɗe baki da fruits kawai sai kunun suka ɗansha, kana kowa yaje yayi sallan. Sannan sukazo sukaci sauran kayan kwalamarsun. Suna tashi sukayi sallan isha. Zuwa lokacin kuma anata raɗe-raɗin ba'aga wata bafa. Wannan lbrin shiya tada hankalin Hibba da sauran mutane irinta, a gefe harma da Jamil Sabida azumi ɗayan nan da za'a ƙara wasu ganinshi suke kamar shekara ɗaya za'ayi ana azumin sai kaji anata gunaguni da cewa wai anƙi a faɗa ne. Shatu kuwa murna tayi dan ita bata samu tayi lalle ba. haka yasa gobe zata ƙarisa aikinta a nitse. Jin an kira salla za'ayi Asham ne yasa Hibba zubda hawaye tare da cewa. "Wlh zan kira Umaymah da Hamma Jabeer ina dai saudi sunyi salla Ni babu ruwana salla zanyi". Ta ƙarishe mgnar tana kiran layin Umaymah yanata ringin ba'a ɗagawa. Hamma Jabeer kuwa data kira baya shiga ma gaba ɗaya. Haroon kuma shima yana shiga baya ɗagawa. Dariya Shatu tayi tare da kunna tv tace. "kalli Hibba suma asham sukeyi". Da sauri tace. "A a kam Isha'i ne". Ganinfa da gaske Hibba keyi yasa suka sherata sukaje sukayi asham kana suka dawo. Kitchen suka shiga, soya kajin sukayi suya mai kyau kana suka ajiye. A gefe. Jalal ne ya leƙo kitchen yace. "Ummi azumi talatin zamuyi bana". Dariya tayi tare da cewa. "Aiko gacan Hibba nata fushi." Shigowa yayi plate ya ɗauka ya miƙawa Shatu tare da cewa. "Aunty a samin nan". Amsa tayi tare da saka mishi soyayyen naman kazan. Dakekken yaji ta saminshi a gefen Fridge ya buɗe ya ɗauki Du-du tare da cewa. "Wannan fa yaushe aka fara kawoshi". Ummi ce ta kalleshi tare da cewa. "Naga Shatu tafi sonshi ne yasa nace akawoshi". Kai ya gyaɗa tare da cewa. "To nima bari in taɓa shi". Nan ya fita falon. Su kuwa suka ƙarisa aikin. Suna ƙoƙarin fitowa ne. Jamil ya leƙo tare da cewa. "To yau kuma meye za'ayi mana na sahur ne". Jalal dake bayanshi ne yace. "Yo azumi ɗaya ai ko tazarce zamuyi". Hararan Jalal yayi tare da cewa. "Hege daka ci kaji kayi tak ba, mutun kamar kura". Murmushi Jalal yayi tare da cewa. "Yes naci in kuma ƙara". Hararanshi Jamil yayi tare da cewa. "Mutun sai son nama kamar ba bafulatani ba sai kace babarbare". Da sauri Jalal yace. "Yo dama aini Arbabarbare ne". Dariya Ummi tayi, Ita kuwa Shatu Jalal ta kalla tare da cewa. "Me zan dafa mana to?". Tsaki ya ɗan ja tare da cewa. "Kiyi mana Coucous da miyar hanta kawai". To tace kana ta juya ta fara aiyin. Cikin sa'a ɗaya ta gama ta fito. A falo ta samesu suna. Waya da Sheykh yana ce musu kadafa suyi sakaci suyi sallan, dan babu lbrin ganin wata. Hakan dai suka haƙura. Bayan yaga waya da sune. Umaymah ta shigo ta sameshi zaune yanacin inabi. Gefenshi ta zauna da wata jakar. Miƙa mishi tayi tare da cewa. "Kace ranar salla da safe in an sauƙo idi dai zaku tafi ko?". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "Haka dai Wannan tsohon Galadiman ya buwayeni da zancen komawar". Murmushi tayi tare da cewa. "Abbanka ma yace min ranar sallan zaku tafi". Kai ya gyaɗa. Ita kuwa gyara zama tayi tare da cewa. "Tsarabar me ka sayawa Shatu da ƴar ɗakinta Hibba". Da sauri ya kalleta tare da cewa. "Umaymah tsaraba kuma. "Yo tsarabar me zanyi sai kace wani sabon zuwa, Ni ibada nazo yi ba tsaraba ba". Jakar ta nuna mishi tare da cewa. "To ni kam ga tsaraba ka kai musu, wannan na Shatune Hibba gobe zan dawo da nata. Kai kuma in kaso ka koma hannu rabbana". Kanshi ya sunkuyar kamar baijiba. Sai kuma tace. "Jazrah tace in gaidaka, wai tunda kazo bata ganka ba". Cikin sanyi yace. "Yoh dama ya zanyi in bari ta ganni yarinya sai kallon masifa". Miƙewa Umaymah tayi ta fita. Tana fita Haroon da Ya Hashim suka shigo. Nan suka ɗanyi hira kafin suka tashi suka tafi masallacin dan shabiyu ta kusa a fara tuhajjudin. Nan suka tafi. Washe gari aka tashi da azumi na talatin. Allah cikin ikonshi aka kaishi lfy. Watan Shawwal ya baiyana Ramadan ya tafi kuma sai mai nisan kwana. Shatu kuwa a wunin ranar Yar aikin Aunty Juwairiyya Sato, ta zana mata jan lalle mai ɗan karen kyau. Koda ta dawo kuma jarakuna madarar shanu data gayawa Gimbiya Aminatu tanaso Aka kawo mata ta tafasashi kana tasashi a manyan kware da ƙananan kwore da kyawawan robobi tasa tsami kaɗan a ko wanne kwarya da roba. Ta rufesh ta jerasu a Fridge a ƙalla sunfi kore goma madaidaitan ƙananan sun kai kore takwas sai robobin su kuma sun kai goma suma. Bayan sallan magriba ansha ruwa anyi nak. Hibba sai tsalle da farin ciki da kiraye-kirayen ƙawaye da yan uwa da abokai sai tsiya Jamil ke mata. Bayan sun gama shirya komai na aikin da zasuyi gobene. Suna zaune a falo Ummi ta kalli Jamil tare da cewa. "Jamil wai sai yaushe zaka share Side ɗin Sheykh ne, munyi waya da Umaymah ɗazu tace min gobe fa zasu dawo. Anayi sallan idi a can zasu taso". Gyara zamanshi yayi tare da cewa. "To naga mutun ga matarsa ace Ni in mishi shara". Ko inda suke Shatu bata kalla ba. Ummi kuwa jingina tayi da jikin kujera tace. "Ai bazata san ƙaidar yadda yakeson a gyara mishi ɗakinshi ba. Dole sai ka nuna mata." Cikin gamsuwa da hakan yace. "To ba matsala sai gobe da sasafe mu hau kan aikin abinda ɗakin ba wani ƙura da tarukucene da shiba". Eh hakane Ummi tace tare da kallon Shatu tace. "Gobe in Allah ya kaimu Shatu ku gyara mishi ɗakin nashi". "To Allah ya kaimu. tace ba tare da ta kalli inda sukeba. A can ƙasa mai tsarki kuwa. Ana idar da sallan isha'i da yawa suka fara ɗawafi. A cikinsu kuwa harda Sheykh Jabeer da mai sunanshi kana da Haroon A nitse bisa tsari suke ɗawafin sunje ƙafa biyu ana uku sun isa dai-dai. Maƙama Ibrahim. Sheykh Jabeer ya juyo kanshi ya kalli gefen damanshi da sauri cikin tarin mamaki al'ajabin Fuskar mutumin da ya ga ya wulgawa a idonshi...! Littafin GARKUWA na kuɗine idan kina buƙatar saya ga number 09097853276 katin mtn na ɗari uku. Normal group in kuma special Group kikeso 1k zakiyi min TRANSFER ta ac ɗina 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *GARKUWA* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 📝🍇🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘 ASSALAMU ALAIKUM. MASOYA NA MAKARANTA LITTAFIN GARKUWA, WAƊANDA SUKA BIYA DA WAƊANDA KE KARANTA NA SATA, INA MUKU FATA ALKYAIRI da fatan muna lfy, kana kuma ina mai bawa dubban mutanen da sukayi min mgn ta kafafan sadarwa kamarsu, WHATSAPP, FACEBOOK, INSTAGRAM, WATTPAD, BAKANƊAMIYA, WASUMA A TIKTOK daga jiya da yamma zuwa safiyar yau haƙurin rashin basu amsar tambaya ɗaya dai da aketa memeta min. GARKUWA WAI KIN SAIDAWA ƳAN HAUSA FILM LBRIN GARKUWA? WAI DA GASKENE BAZAKI ƘARASA MANA LITTAFINBA? TO DUK GA AMSARKU NAN. Alhamdulillah, ngd matuƙa da kulawarku. Kana ina mai baku tabbacin EHHH TABBAS NA SAIDA LITTAFIN GARKUWA GA ƳAN HAUSA FILM KAMAR DAI YADDA KUKAGA YAKETA YAWO, TABBAS NA SAIDASHI WA ƊAYA DAGA CIKIN MANYAN INDOSTIRI. DA IZININ UBANGIJI ZASU JUYASHI ZUWA FILM MAI ZAMAN KANSHI, IN LOKACIN YAYI KUMA ZAN SANAR MUKU. DA FARI NASO IN SIRRANTA ZANCEN NE, SABIDA SEDA MUSU DA NAYI BAWAI YANA NUFIN BAZAN ƘARASA LBRIN GARKUWA BANE, ZAN ƘARASA MUKUSHI HAR ƘARSHE DA IZININ UBANGIJI. TO SAI DAI NAYI MATUƘAR MAMAKIN YADDA AKAYI MGNAR TA FITO FILI TA BAIYANA HAR TA BAZU, domin naso barinta sirrin kai da kaina sabida gudun kada hankalin makaranta na ya tashi. To amman ba komi ku kwantar da hankalinku masoya na zan ƙarasa GARKUWA lfy lau. Kana suma ƴan film zasuyi abunsu lfy lau. Duk wacce ta/ya sayi littafin GARKUWA sun san uzurina da yasa kwana biyu bana Update, so ku kwantar da hankali ku, in sha Allah ni AYSHA ɗiyar ALIYU GARKUWA, Jikar Malam Muhammad Babayo mai Murare. Zan ƙarasa mukushi lafiya in Allah ya aramin rai da lfyar. KUYI HAƘURI WAƊANDA SUKAYI MIN MGN TA PC BABU TABBACIN ZAN BIKU ƊAYA BAYAN ƊAYA IN BAKU AMSA. FATAN AL'KHAIRI MASOYANA MAKARANTA LITTAFIN GARKUWA WAƊANDA SUKA BIYA DA WAƊANDA KE KARANTA NA SATA🤝🏻😘🥰😘🥰😘. Dan naga masu karanta na satan ƙarfin halinsu yawa gareshi, har ƴar guntuwar nasiha sukemin wai kada in zalinci mutane na fara musu ban ƙarasa ba🤣🤣😂. Ɗan Adam kayan Allah ana ɗauke damu muna ɗauke da halayenmu🤗🤗🤗🤗.Cikin sassarfa bisa tsarin addinin yaci gaba da ɗawafin. Yana mai bin bayan tawagar mutanen da yaga fuskar wannan mutumin a cikinsu. Idonshi yaketa karkasawa amman ina ya kasa sake ganinshi. Zuciyarshi nike da mamaki. Haka yaci gaba da ɗawafin. Saida sukayi. Kana suka fito. A hanyarsu ta komawa gidane ya haɗu dasu Jannart da Jazrah da Umaymah da Sitti da kuma Aunty Hafsat ƙanwar Umaymah dake ƙasar Masco. nan Aunty Hafsat tayi ta sayan kayan tsaraba tana bawa Sheykh wai a kaiwa surkarta. Dan dole ya amsa sai kuma Aunty Rahma ƴar autar Sitti itama a gaban Aunty Hafsat ta girma. Kuma sa'ar Sheykh Jabeer ce shiyasa akwai yar tsama a tsakaninsu. Cikin hausarsu data fara basu wuya tace. "Ba dai kayi auren sirri ba, in sha Allah zanzo zamuzo auren Haroon zamuga amaryar, inga surkar tawa ya take" Taɓe baki yayi tare da cewa. "Ke tafi daga nan da Allah ki bar manya suyi mgna ba irinki ba". Murmushi Umaymah da Aunty Hafsat sukayi dan sun san tsamarsu. Kuma suna masifar shiri. Ammi suke kiranta ita Aunty Rahman. Jazrah kuwa hakanan take jin daɗi in ta ganshi. Shiyasa taketa murmushi. Haroon kuwa girarshi ya ɗagawa Jannart tare da cewa. "Wai auren ya kusa ko?". Cikin jin kunyar Umaymah tace. "Ban saniba." Haka dai sukaci gaba da tafiya. Washe gari da safiya. Duk kan al'amur musulmai na duniya suna farin ciki da ranar salla. Manya da yara tsoffi maza da mata duk anata shirin zuwa idi. A dukkan ƙasashen duniya a ko wani saƙon da suke da musulmai. Hakace ta kasance a ƙasashen Afrika ma. Wanda ciki ƙasar Nigeria yake. Tun daga idar da sallan asuba. Saratu da Larai sukazo. Nan suka samu Ummi da Shatu suna kitchen. Its Ummi fura take kirɓawa mai ɗan karen laushi da ƙamshi yaji sugar. Ita kuwa Shatu dakkeren Couscous tayi, dambu inji hausawa. Bayan sun gamane suka killace shi gefe. Kana ita Shatu. Ta haɗa kajin nan tayi Pepper Checken mai ɗan karen kyau yaji jajjagen taruhu da al'basa mai yawa ga kayan ɗan-ɗano dana ƙamshi sunji komai yayi maɗau. Su Sara kuwa robobi ta miƙo musu, suka rinƙa mulmula gumbar nan manya manyan mulmulellen masu kyau sai sheƙi da ƙamshi gumbar keyi, dakkeren kuma a robobi Ummi ta rinƙa zubasu. Hibba ce data shigo tare da kuloli a hannunta tace. "Wow Aunty Shatu lallai yau masarautar Joɗa zata amsa sunanta masarautar Fulɓe zata kuma gane an auro mata cikekkiyar ba fulata, gsky tsarin yayi kyau". Cikin jin daɗi Ummi tace. "Gsky nima naji daɗin wannan abu. Dama ace ko wanne yare ranar salla tayi abincin da yarenta keyi ta rabawa maƙota. Hakan zaisa asan cimar juna, kuma yasa aci abincin salla da marmari, amman kayan haushi duk sai a tafi kan shinkafa taliya masa, da dai ire-iresu. Su kuma akeci kullum". Murmushi Shatu tayi tare da cewa. "Ha Ummi ai yanzuma sai nayiwa su Jalal koda dafadukan taliyace, nasan zasuce wannan ai sai mu". Da sauri Hibba tace. "Tab wlh Aunty Shatu karkiyi komai, kinga yanzuma an kawo abincin gidan Barrister Kamal. Ga kuma na gidan Aunty Juwairiyya. Sannan kuma Gimbiya Aminatu ma zata aiko". Cikin sauri tace. "Allah ko Ummi mu huta kawai kenan?". Da sauri tace sosaima. Dan duk yawanci sai an kawo abinci nan wai tunda ke baƙuwace, wannan karamawar masarautar Joɗa akan bago. Kuma koda kin dade ana aikawa juna abincin salla part 2 part". Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Shike nan mu haɗa wannan a kai ko wanne sashin". Ta ƙarishe mgnar tana rufe ƙatuwar Foodflaks ɗin da ta juye Pepper Checken ɗin. Bayan ta ɗebawa sashin Ya Jafar da kuma Lamiɗo da Hajia Mama. Ƙananan robobin da a ƙalla suma nonon dake cikinsu zai kai kwanon sha ɗaya da rabi ta fara firfitarwa. Kana ta fito da madaidatan ƙoren da zasuci kwanon sha biyu da kaɗan sai manyan da sukaci kwanon sha uku da rabi-rabi. A hankali ta jerasu kan table ɗin dake tsakiyar kitchen ɗin. A hankali ta buɗe ƙwaryar forko dake gabanta. Wani irin murmushi tayi tare da cewa. "Alhamdulillah kunɗirmo ya konta yayi bacci yayi kyau". Leƙowa Ummi tayi tare da buɗe na kusa da ita. Nonon yana konce yayi lib ya daskare yayi fari ƙal-ƙal sai alamun maiƙon man nonon da yayi ɗan yellow-yellow kaɗan. A hankali suka fara bubbuɗe fefeyayen tsakan zaren taburma da aka rufe ƙoren dashi. Gaba ɗaya duk sun konta sunyi kyai Yan madaidai robibin da akasa take ɗauka na fura ɗaya na dakkere ɗaya sai na sugar ɗaya kana da ludayin duma. Sai ta jerasu kan fefeyayen da robobin. Ganin haka yasa Saratu da Laraima suka matso suna taya. Har saida ta jerasu kab. Gwanin sha'awa. Manyan ƙore biyu ta maida cikin Fridge. Kana ta irga sauran tsakanin manya da ƙananan Ƙoren da robobin su Talatin da tara Juyowa tayi ta kalli Ummi tare da cewa. "To Ummi gashi mun gama ki gaya musu duk inda zasu kai. Zasu isar ko". Cikin jin daɗi Ummi tace sosaima kuwa harma da sashin bayi zai isa sabida part-part talatin garemu a cikin masarautar Joɗa. Sai sashin bayi part takwas. Cikin jin gamsuwa da tsarin Shatu tace. "Yanzu a kai ƙore biyu sashin Lamiɗo kana duk manyan iyayen Sheykh akai musu kwarya ɗaɗɗaya, sai sashin Ya Jafar kinga manyan ƙoren sun ƙare sai abin na tsakiyan a kai sauran sashin ƴaƴansu robobin kuma akai sashin bayi". Haka kuwa akayi su Sara suka fara rabawa. Ita kuwa Ummi ita da kanta da Hibba suka kai na sashin Gimbiya Aminatu. Kana suka dawo da kuloli har uku na abincin sallan da Gimbiya Aminatu ta basu. Kana ɗaya daga cikin tace na Sheykh ne a ajiye mishi. Koda suka dawo samu sukayi su Saratu sun gama rabawa kab. Kamar yadda Ummi ta tsara. Har sun tattare ko ina sun gyara sun share sun goge sun tafi. Zuwa lokacin kuwa gaba ɗaya kan dinning table ɗinsu cike yake da Foodflaks iri da kala abinci kala-kala. Wani irin kallo Shatu tayiwa kulolin kana tayi murmushin da ita kaɗai tasan ma'anarsa ta juya ta nufi tsakiyar falon. A gaggauce sukayi wonka kowa yayi shirin idi. Ƙarfe tara saura kwata duk suka fito falo. Tuni lokacin kuma liman har ya fara huɗuba. Su Jalal, Jamil Ya Jafar suna tsaye cikin shiga ta al'farma. Karon forko dataga manyan kaya a jikin Jalal. Sai kamanninshi da Hamma Jabeer ɗin nasu ya fito sak-sak kamar an tsaga kara hatta rashin yawan dariyarsu iri ɗaya ne. Sai dai shi Sheykh ko yaushe zakaga lips ɗinshi na motsawa yana tasbihi saɓanin Jalal da zaka ganshi baki a tsuke. Hibba ce ta fito cikin tarin farin ciki da son Jalal yayi murmushi tare da cewa. "Masha Allah ya Jalal kayi kyau kafisu duka". Ya Jafar dake karatu kamar ko yaushene ya kalli Shatu da Hibba da sukayi shigar atampa iri ɗaya da manyan hijabai har ƙasa ga sallaya da carbi a hannunsu sunyi matuƙar kyau, murmushi yayi musu kana ya juya yayi gaba. Jamil ne yace. "Aunty Shatu sai mun dawo, in munci abinci sai mu sharewa. Oga, Dr, Garkuwa, Malam, akarmakallahu, Sheykh, mijin Sayyada, ɗin ɗakinshi". Dariya sukayi dukansu yadda ya jero masa sunayen nashi. Ummi dake cikin shiga ta al'farma ta miƙa tare da cewa mu tafi. Suna fita suka rufe ƙofar. Suka tafi masallacin. Masarautar Joɗa ɗan yin sallan idi. Suna fita su mata sukayi gefen mata su kuwa maza sukayi gefen maza. Bayan an idar da sallane kuma sai suka zagaya suka shigo ta asalin ƙofar sukayi yadda sunna ta koyar. Suna dawowa kuwa a falo suka zube nan sukaci suka sha sukayi haniƙan. A dai-dai lokacin kuma su Sheykh dama sauran al'ummar Annabi duk an sauƙo sallan idi. Suna ɗawafin ban kwana. Sosai Sheykh ke baza ido ko zai sake ganin wancan mutumin amman ina hakan bai samuba. Koda suka fito daga ɗawafin ban kwana. Kai tsaye gidan Sheykh Abdulkareem suka wuce. Nan yayi musu addu'o'in komawa lfy. Kusan duk baƙin gidan a ranar suka bar gidan. Da su Aunty Hafsat ma ranar suka juya Masco hakama Ibrahim. Koda suka iso Airport kowa da inda ya nufa. A nan Ibrahim ya ruggume Sheykh tare da ɗan dukan bayanshi yace. "In Sha Allah Auren Haroon dani za'ayi". Shima Sheykh ruggumeshi yayi gam-gam tare da cewa. "Allah yasa, ina kewar rashinka a ƙasar mu". Aunty Rahma ne tace. "Kai jirgifa ba jiranku zaiba oga Sheykh". Sakin juna sukayi kana kowa ya nufi inda jirgin ƙasarsa yake. Bayan duk matafiya sun shiga, jirgin ƙasar Nigeria wanda zai sauƙa jihar Ɓadamaya. A hankali ya zauna. Ya Hashim na gefenshi. Kasan cewar yana kusa da window ne, ya ɗan juya yana kallon mutanen daketa hada-hadar nufar inda jiragan ƙasar su jihohinsu suke. Can cikin wasu ayarin mutane maza da mata ya hango wannan fuskar da ya gani. Sun nufi can ciki suna tafiya yankin da jiragen ƙasar Cameroon suke. Cikin tarin mamaki ya bishi da kallo tabbas badon jirginsu ya fara ƙugin tashiba da ya fita yaje ya tabbatar da fuskar dattijon da yake hangowa. A haka dai suka ɓacewa ganinshi. Kana jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasarmu ta haihuwa. Ana gida Nigeria kuwa cikin Jihar Ɓadamaya a Masarautar Joɗa. Zaune suke a falon. Shatu na waya da Junaidu nan yake ce mata, Sun samu sauƙi dukansu. Ance za'a sallamesu bayan salla. Kuma harda ɗinkunan kayan salla akayi musu. Bayan sun gama waya da shine ta kira Rafi'a. Nan suka gaisa har ta bawa Ummi su gaisa. Bayan ta bawa Ummi wayarne. Jamil ya ɗan kalli agogon hannunshi a hankali ya miƙe tare da kallon Shatu yace. "Muje mu gyara Side din boss kar ya dawo ya samu da datti". Kai ta gyaɗa mishi kana ta amshi wayarta da Ummi ke miƙa mata. tare da ce mata. "Eh dan Allah Shatu tashi maza-maza kuje share wurin da kyau". A hankali ta miƙe tare da cewa. "To." Hibba ce ta bisu a baya. Jamil na gaba ita Shatu'n tana tsakiya. Hibba na bayanta. A haka suka shigo falon. Da komai na ciki yake fes-fes babu wani daddi ko ƙura ko hargitsewa, sabida an share falon safiyar yau, sai ƙamshi da sanyi ke tashi. A hankali Jamil ya ɗan sa hannunshi tsakanin ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu sheƙin Daimond dake matsayin labulen Dinning area ɗin shi. Ita dai Shatu ido ta zuba mushi, ganin ya zaro key ɗin a cikinsu. Ƙofar bedroom ɗin ya nufa tare da cewa. "Muje." To sukace kana suka biyo bayanshi. Tana nazarin wurin da suke ajiye key ɗin. Key ɗin ya saka cikin raminshi tare da murzawa. Da sauri Shatu ta rumtse idanunta. A hankali take jin zuciyarta na harbawa da sauri-sauri. Shi kuwa Jamil tura ƙofar yayi bayan ya murɗa key ɗin ya buɗe. Wani irin masifeffen harbawa da azaban ƙarfi zuciyar Shatu tayi. Kutsa kai cikin Jamil yayi. Tare dasa hannunshi jikin ginin a hankali ya kunna wutan ɗakin hasken ya gauraye ko ina, jikin window ya wuce ya yaye labulen tare da buɗeglass ɗin. Iskam cikin Garden ɗin dake bayan window wanda ɗawisu yake ciki. Ya buso ɗakin. Juyowa yayi ya kalli Shatu da ke tsaye bakin ƙofar. "Ku shigo, in nuna miki yadda zakiyi mishi". A hankali Hibba ta ratsa gefenta tare da cewa. "Aunty Shatu mushiga". Ido ta buɗe a hankali tare da bin bayan Hibba da kallo. Kana ta ɗaga ƙafarta da kyar ta. Taka cikin ɗakin, wani irin azabebben sarawa kanta yayi tamkar ana buga mata guduma a tsakiyar kan. Cikin rawan ƙafa ta ɗaga ƙafafuwan ta, Tayi taku huɗu zuwa biyar. Ta kusa isa tsakiyar ɗakin. Kenan. Wani irin jujjuyawa taga kanta nayi. Wasu irin ababe masu ban tsoro ta fara gani suna gilmawa cikin ƙwayar idanunta, shiyasa taketa jujjuya kanta. Ta kalli gabas ta kalli yamma ta kalli kudu ta kalli arewa. Hibba ce ta juyo tana kallonta jin Jamil nata mgna bata bashi amsaba. Cikin sauri ta matso kusa da ita ganin yadda taketa jujjuya kai, ga idanunta da suka juye suka zama kamar harari garke, kana sai Rollin ball eyes ɗin ta take da sauri-sauri. Cikin Mamaki Hibba tace. "Aunty Shatu! Aunty Shatu!!". Shiru ba amsa hakane yasa. Jamil juyo kanshi ya kalli inda suke, da sauri ya juyo gaba ɗaya jikinshi ganin. Wani irin karkarwa da jikin Shatu keyi. Hibba kuwa da ƙarfi cikin tsoro tace. "Aunty Shatu lfy kuwa?". Ita kuwa Shatu, zuwa yanzu bata jinsu bata kuma fahimtar me suke faɗa hankalinta ya juye. Cikin wani irin layi da rawan jiki tamkar mazari ta nufi tsakiyar ɗakin. A nan ta tsaya gis gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi. Cikin tsananin tsoro da firgita. "Hibba ta juya a guje tana cewa. "Wayyo Ummi! Ummi!! Ummi!!! Kizo zakiga yadda Aunty Shatu keyi." Ummi dake falo ita da Aunty Juwairiyya, Kamar daga sama suke jiyo muryar Hibba tana rabka musu kira cikin firgici da razani. Haka yasa Ummi da Aunty Juwairiyya miƙewa da sauri suka nufi corridor'n da suke jiyo muryar Hibba na fitowa. Kiciɓis sukayi a bakin ƙofar falon. Cikin sauri Ummi ta ture Hibba ta wuce da gudu ta nufi cikin ɗakin. Sabida jiyo muryar Jamil na cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahuwani'imal wakil. Ummi! Ummi!! Kizoooo". Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka shigo. "Dai-dai lokacin kuma rawan da jikin Shatu keyi ya tsananta. Wani irin kuka tasa tare da tafiya ƙasa luuu zata faɗi Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka tarota. Bisa jikin Ummi ta faɗi hakan yasa itama Ummi tayi ƙasa ta zauna. Babu abinda suke maimaitawa sai innalillahi wa innailaihi rajiun. A kiɗime cikin tsananin gigita Jamil yace. "Subahanallahi Ummi ta sumafa". Jiki na rawa Aunty Juwairiyya ta juya da gudu babban falon ta fito tare da ɗauko goran ruwan sanyi. Kana ta juyo a da sassarfa ta nufi can. Hibba kuwa a gigice take gayawa Jalal da Ya Jafar abinda ke faru. Da sauri ya Jafar ya tashi ya nufi can. Jalal kuwa ya zauna dan ya lura Hibba tayi masifar tsorita. A ɗakin nashi kuwa, Shiru ta lafe jikin Ummi kamar babu rai koda. Ummi ta yayyafa mata ruwan sanyi a fuskarta, a banza saida ta kuma watsa mata a karo na uku ne. Kafin taja wani dogon numfashi cikin sanyi da tsoro Ummi tace. "Alhamdulillah". Sai kuma ta sunkuyo kanta tana ɗan kiranta. "Shatu! Shatu!! Shatu!!!". Ba amsawa kuma bata buɗe ido ba, A hankali ya Jafar ya zauna gefensu, karatun da yakeyi yaci gaba dayi. Cikin sanyi ta buɗe idanunta. Sai kuma ta yunƙura a hankali ta tashi zaune. Da sauri Ummi ta zaro ido ganin yadda idanunta suka juye a murɗe. Ita kuwa Shatu miƙewa tsaye tayi, cikin rawan sanyi da karkarwa, ta fara zagaya ɗakin a hankali taje baki Bathroom nanma buɗe ƙofar tayi ta shiga. Jim kaɗan ta fito. Idanun suna yadda suke sai dai. Yanzu hawayene keta shatata babu ƙaƙƙautawa. A hankali tazo bakin gadon. Sai kuma kawai sukaga ta faɗa kan gadon a sune! Wannan shine tashin hankali da ba'a samishi rana. Da gudu suka kumayi kanta, cikin firgici da tsananin tsoro Ummi ta ƙara yayyafa mata ruwan. Amman shiru, haka suka tsaya cirko-cirko, shi kuwa Ya Jafar sai gashi yana karatu yana kuka kamar dai yadda yakeyi kafin a auro Shatu a masarautar Joɗa in Sheykh baya nan. Gaba ɗaya sun birkice sunma rasa me zasuyi. Aunty Juwairiyya kuwa itama kuka ta farayi. Jiyo kukanta da na Ya Jafar ne yasa, su Jalal da Hibba shigowa. Ganin tana can yashe kan gado a sumene yasa Hibba ma kuka. Cikin ƙarfin hali Jamil yace. "Aunty Juwairiyya Hibba kada kuyi kuka, kuja hankalin mutane nan. Gashi yau salla ba mamaki akwai mutane a cikin Garden." Cikin tashin hankali Ummi tace. "Bari inje in sanarwa Gimbiya Aminatu abinda ke faruwa, ta sanarwa Lamiɗo, sai in biya in sanarwa Hajia Mama." Da sauri Aunty Juwairiyya tace. "Eh yafi kam". Ta juya zata fita kenan sai sukaji tayi wani irin nakasheshen dogon numfashi mai sassanyan sauti. Da sauri Ummi ta juyo ta dawo jikin sanyi tace. "Shatu! Shatu!! Shatu!!!". Shiru babu amsa sai binsu da ido tayi ɗaya bayan ɗaya. Ganin hakane Jamil ya matso. Tofi ya farayi mata. Ummi kuwa ci gaba da kiran sunanta tayi. Cikin tsoro Hibba tace. "Ummi kinga idonta ya koma dai-dai." A tare sukace Alhamdulillah. Sai kuma Ummi ta kuma kiranta. "Shatu!". A hankali tace. "Na'am Ummi". Sai kuma ta kalli inda take, kana ta juya ta kallesu baki ɗayansu, cikin mutuwar jiki ta yunƙura ta tashi. Murya a sanyaye tace. "Jamil sharan kenan ka tsaya kanata kallona. Gaya min ya za'ayi sharar". Cikin sauƙe tagwayen numfarfashi suka kalli juna, Cikin mamaki Jamil yace. "No ki huta kawai my Aunty zan share". Bata da ƙarfi a jikinta ko ta dage tace sai tayi sharar. Bazata iyaba jikinta duk a mace. Hakane yasa tace to. Hannu ta miƙa Ummi tare da cewa. "Ummi ɗan jamin hannuna mana". To tace tare da kamo hannun. Ta tsaida ita, cikin tafiyar sanɗa ta juya ta nufi hanyar fita. Binta sukayi a baya gaba ɗayansu. Jamil kuwa dube-dube yayi a cikin ɗakin kana. Ya fara tattarewa da kimtsawa da sherawa, ya canza mishi beshit and blanket, da rigunan pillows. Kana ya goge ko ina fes Sannan ya shiga bathroom ya wonke ya goge mishi. Su kuwa suna biye da ita har falonta. Ganin ta wuce bedroom ɗinta ne yasa Hibba da Juwairiyya suka tsaya. Ita kuma Ummi tabi bayanta. Ganin tana shiga ta hau gado ta kwanta ne a take sai bacci yasa Ummi ta juyo ta fito. Can babban falon suka koma suka zauna. "Ikon Allah sai kallo wannan abu da ban tsoro da ban mamaki". Ummi ta faɗa cikin al'hini. Jiki a mace Aunty Juwairiyya tace. "Sosai kam wannan al'amari ya firgitani". Hibba dai sai zuru-zuru tayi da ido. Nan sukayi ta mamakin wannan abin. Jamil na fito shida Jalal suka tafi. Shi kuwa Ya Jafar bayan matarsa yabi suka tafi. Hibba kuwa da Ummi nan suka zauna. Ummi ce ta kalli Hibba tare da cewa. "Sai anjima zan kira Umaymah na sanar mata abinda ya faru". Kai kawai Hibba ta kaɗan mata. Ita kuwa Shatu baccin tayi mai nauyi sai kiran sallan azahar ne ya tasheta. Su Sheykh Jabeer kuwa suna can sunata keta hazo. Tafiya awa huɗu ne zai kawosu ƙasar mun. A hankali ta buɗe idonta, miƙa tayi tare da yin salati. Kana ta tashi zaune. Bathroom ta shiga, wonka tayi da ruwan ɗumi. Kana tayi al'wa tana fitowa. Ta zura Hijabi tayi salla. Bayan ta idarne, ta zauna gaban dreesing mirror. Simple makeup tayiwa fuskarta. Sannan ta sauya shiga, wani tattausan lace mai ɗan karen kyau da tsada tasaka duguwar rigace tayi cib-cib da jikinta. Kasan cewarta kalar pink guava da ɗigo-ɗigin mint green ne yasa tayi masifar dacewa da kalar jikinta. Gyara gashin kanta tayi ta tubƙeshi tare da kitsen jelar. Ta saketa bisa kafaɗunta. Ɗaurin asseta tayi ya zauna ɗas a kanta, tattausan gyale minti green color ta yafa a kafaɗunta. Kana ta fesa turarukan ta masu daddaɗan ƙamshi. Sosai jan lallen gargajiya dake kan ƴan fararen yatsun hannunta yayi masifar kyau. Ga kuma zanen da akayi a saman hannun hakama ƙafafun ta, suma sun sha zanen jan lalle tayi kyau sosai, Ta fito ras da ita. Baki ɗauke da sallama ta foto falon. Cikin murmushi Ummi ta amsa sallamar tana mai kallonta, Hakama Hibba da Ummi ta kokkontar mata da hankali taji tsoron ya ragu. Gefen Ummi ta zauna, tana kallon Hibba na ɗaukarta hoto tana cewa. "My Happiness Aunty kinyi kyau". Murmushi tayi tare da cewa. "Na kaiki ne?". Da sauri Hibba tace. "Kin fini ma". Murmushi ta kumayi tare da cewa. "Ngd matuƙa". Sai kuma ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi me zamuyi abincin dare". Cikin jin tausayinta Ummi tace. "A a akwai abinci harda na gobe da safe ma, yanzu kam ki huta, sai dai in akwai abinda kikeso ki gaya min in yi miki". Kai ta jujjuya alamar a a kana tace. "To Ummi a kaiwa Hadimai wani abincin kada ya lalace a banza ko". Cikin gamsuwa Ummi tace to. A can Airport kuwa ƙarfe uku dai-dai jirgin Ahlin masarautar Joɗa ta sauƙa. Nan motoci suka kwatsosu. Suna isa masarautar ana kiran sallan la'asar hakane yasa matan cikine kawai suka shiga cikin gida su mazan. Masallaci suka wuce. Ana idar da salla kuwa fada suka wuce baki ɗayansu. A sashin Gimbiya Saudatu kuwa wani irin dariya mai cike da masifar jin daɗi tayi tare da cewa. "Dai-dai kenan yaro zai dawo ya taradda da mummunan lbrin matarsa ta zama zautacciyar mata...! By *GARKUWAR FULANI* "Mummunam labarin amarya ta haukace. Ai kaɗan ma kenan, kowa yaci tuwo dani miya yasha. Hegen yaro mai jajayen kunnuwan da shegen baki mutun nace masa cuta zai ce ajali, kana ce mishi cas zaice maka kulle, wannan bakin nashi mai zaro zance da inada hali dana rufeshi kirib". Hadimarta dake zaune gabanta wacce taji cikekken bayanin abinda ya faru da Shatu a sashin Hajia Mama da itama yar rahotontace ta kamo mata. Shiyasa itama ta kawo mata rahoto. Cikin jin daɗi ta kalli Laminu dake gefe yanata murmushin jin daɗi tace. "Shiga ɗaki zaka samu kuɗi a kan gadona, kazo ka bata tukuicin wannan daddaɗan labari mai armashi". To yace kana ya miƙa ya ɗauki kuɗin yazo ya bata, tayi godiya kana ta miƙe ta fita. Ita kuwa Gimbiya Saudatu Baba Basiru da Baba Nasiru ta kira ta shaida musu abinda ya faru. Nan sukayi ta murnar abun, da shirya yadda abin zai ɗunguzuma yaci gaba. A can su Sheykh kuwa saida aka idar da sallan isha'i kana kowa ya nufi Side ɗinsa kamar yadda sukeyi duk shekara in sunje umrah sun dawo. A Babban falon sashin Jabeer kuwa. Ummi ce zaune bisa kujera Hibba na gefenta. suna mgn da Umaymah a wayar Hibbab nan Ummi ke sanarwa Umaymah abinda ya faru ɗazu da hantsi na firgitarwa. Cikin tarin mamaki da al'ajabi da tsoro tace. "Ummin Jabeer to yanzu ina take? Kuma ya jikin nata? Meya jawo hakan ne?". Juyawa Ummi tayi ta kalli bayanta a hankali tace. "Tana ɗakinta tunda tayi sallan isha'i ta konta, yau ko abinci babu abinda taci, tunda gari ya waye, dan koda muka dawo idi munci dukanmu amman ita ko ruwa bata shaba, kuma har yanzu babu abinda taci". Cikin fargaba Umaymah tace. "Jazlaan ɗin ya shigo wurinku ne? Ya sanine ko bai saniba?". "A a bai shigoba, eh gsky babu wanda yasan da wannan zancen duk Masarautar Joɗa, saini, da Jamil, Jalal, Hibba, Juwairiyya, Jafar. Mune kaɗai muka san da zancen". Ajiyar zuciya mai ƙarfi Umaymah ta sauƙe cikin sanyi tace. "Kada ku damu zanyi mgna da Jazlaan, kada ku gaya mishi, in lokacin saninshi yayi zai iya sani". Ta tace tare cewa. "Masha Allah gashi ma sai yanzu ya shigo". Tana faɗin haka ta katse kiran. Ta miƙe da sauri hakama Hibba cikin jin daɗi suke cewa. "Oyoyo mutanen saudia garin Manzon Allah, Barka da zuwa lfy da dawowa lfy". Ɗan gajeren. Murmushi yayi tare da ƙarasowa cikin falon. Jalal, Jamil, Ya Jafar na biye dashi a baya. Bisa kujera ya zauna tare da kallon Ummi fuska ƙunshe da annuri yace. "Barka dai Ummi na sameku lfy!?". "Lfy lau Alhamdulillah Sheykh ya kuka baro Sheykh Abdulkareem da ahlinshin. Ina mai sunanka Sheykh Jabir Ali". Cikin jin daɗin kulawarta ga yan uwan mahaifiyarshi yace. "Alhamdulillah suna lfy, Sheykh Jabir Ali yace in gaidaku gaba ɗaya". Cikin jin daɗi tace. "Ina amsawa kuwa ngd matuƙa". Jamil dake riƙe da jakukkunan da Sheykh yace ya ɗauko a motarsa ne ya wuce dasu. Yaje ya ajiyesu a bedroom ɗin shi kana ya dawo falon. Hibba kuwa ruwa ta kawo mishi. Murmushi yayi tare da amsar goran zam-zam ɗin yace. "Baku shanye tsohon ba Ummi ni gashi na samo sabo". Hibba ce ta ɗan kalleshi tare da cewa. "Hamma Jabeer, su Sitti ma sun dawo ne?". Kai ya gyaɗa mata alamar eh. Kana ya miƙe tare da cewa. "Ummi bari inje in ɗan huta". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Ai dole kam saida hutu dan gajiya da rashin bacci kam ka kwasosu dole kayi ramuwar bacci". Ta ƙarishe mgnar tana kollonshi tuni ya shiga corridor'n shiga cikin falonshi. Dama kuma tuni ita da kanta ta kai mishi abinci a Dinning table ɗinshi. Nan sukaci gaba da hira. Hibba na cewa. "Umaymah na ta dawo na kusa komawa". Cikin taɓe fuska Jalal ya kalleta a fakaice. Jamil kuwa dariya yayi tare da cewa. "Za dai ki gudu yarinya faɗi gskyarki". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Ba wani tsoro ai na gaya mata ta kontar da hankalinta." Jafar kuwa karatunshi yakeyi. A hankali saɓanin baya da in zai karatun da ɗan ƙarfi yakeyi. Sosai suka ɗan yi hira kana suka watse kowa ya tafi makoncinsa. Shi kuwa Sheykh yana shiga. Ya rinƙa sauƙe numfashin gajiya tare da rage kayan jikinshi. Wonka ya shiga yayi kana yasa wasu riga da wondo masu taushi yazo ya konta. Ba tare da yasha ko ruwaba, sabida tarin gajiya da bacci. Gaba ɗaya wunin yau a zaune yayi yishi ko a ɗan tsaye. Gashi rabonsa da bacci tun jiya da safe da ya ɗanyi kaɗan kafin ya tafi harami sallan walaha. Yana konciya kuwa yayi addu'o'in ya shafa jikinsa. Kana ya fuskanci allon majigi dake liƙe a bongon ɗakin wanda yake ɗauke da full ƙura'an. Karatu ya farayi daga ƙasa zuwa sama wato nasi. Ɗaga nan bacci yayi awon gaba dashi ko inna'alzzan bai jeba. Ummi da Hibba kuwa suna isa falon Shatu cikin kula Ummi tace. "Kije ku kwana kinji ko Hibba babu abinda zai sameki, Bazata miki komaiba, bata da lfy bai dace mu barta ita ɗaya ba". Cikin sanyi Hibba tace. "Gsky Ummi bazan iyaba wlh ina tsoro". Cikin hikima Ummi tace. "To muje ki hau gado ku kwanta ni kuma sai in kwanta a ƙasa kam carpet ɗin. Gyada tayi cikin gamsuwa da hakan. Haka sukayi Ummi ta kwanta a ƙasa ita kuma Hibba ta konta gefenta a ɗan tsorace. Ita kam Shatu batama san sunayi ba, domin bacci mai nauyi takeyi. Haka dai Ummi tai shiru saida ta tabbatar Hibba tayi bacci kana ta koma ɗakinta. Washe gari da safe bayan Ummi, Saratu, da Hibba sun gama karyawa ne. Shatu da tunda tai sallan asuba ta koma ta konta kan sallayar sai yanzu ta fito. Tayi wonkanta fes ta ƙenƙesa ado da kolliyar ta ba irin mai ramɓatsau ɗin nan ba. Komai dai-dai tayi abunta. Riga da siket ne na Mateyal mai taushin gaske, White Coffee mai kyau. sai ɗan ƙaramin gyale ta yafa a kanta, cikin nitsuwa ta fito. A falo ta zauna tare da juyowa ta kalli Ummi dake shirya abinci a Dinning table. "Ina kwana Ummi". Tace cikin muryarta Normal. Cikin kulawa Ummi ta juyo tare da cewa. "Lafiya lau Shatu. Kin taso kenan". Murmushi ta ɗan yi tare da cewa. "Ummi meyasa baki tadani ba, kika shiga kitchen da kanki". Kai ta jinjina tare da ɗaukan cup mai ɗan girma, Tea mai kauri ta haɗa a ciki kana, ta taho inda take miƙa mata cup ɗin tayi tare da cewa. "Gashi amshi kisha, aiki kam ai saida lfy". Amsa tayi tana murmushi a hankali tace. "Lfyata lau ai Ummi kawai dai baccin ne ban san meyasa nake ta yinshi ba". Kai kawai Ummi ta gyaɗa mata, Kana ta juyo tace. "Hibba kawo mana namu abincin nan muci. Najiyo Muryar Jamil suna zuwa, kuwa wata ƙil dasu Imran zasu zo". To tace kana ta ɗauko musu nasu Foodflaks ɗin da plate and spoons da ta kawo musu. Jolof ɗin taliyace da kifin banɗa dasu Kabeji da karas da green beans da dai sauran kayan haɗin. Sai kuma, ferfesun kayan ciki. A plate ɗaya Hibba tasa musu, da ita kana ta sawa Ummi. Kana tasa musu fork, tare da cewa. "Bismillah Aunty Shatu sauƙo muci ko". To tace kana ta sauƙo, suka fara cin abincin. Amman ina tayi loma ɗaya sai ta kusan 4 minute bata kuma sawa a bakiba. Sai dai ta shanye tea ɗin ganin hakane yasa Ummi ta ƙara haɗa mata wani shayin. Shima ta shanye abinta fes, taliyar kuma baifi cokali biyar ba tayi. Su Jalal kuwa suna shiga suka wuce Dinning area suma sukayi breakfast ɗin kana suka fita, sabida hidimomin salla. Domin yau za'ayi hawan daba, Jalal kuma mayene mai zaman kanshi a kan sarrafa, doki, ɗan daga Affan sai shi. Bayan Sheykh a iya sarrafa doki kab Masarautar Joɗa . Amman shi Sheykh ya daɗe da cewa shi ya girma da yin wannan sakarcin. Su Ummi kuwa, kitchen Suka kuma shiga. Sanin yau tabbas akwai baƙi masu ɗimbin yawa da masarautar Joɗa zata amshi baƙoncinsu. Domun ƙananan sarakunan wasu garuruwanma duk zasu zo da tawagar su. Haka yasa suka shiryawa taron haiƙan ƙadaran ko wani Side dake gidan za'ayi abinci a ciccika manyan kuloli a kai fadar Lamiɗo, wani a kai sashin bayi. Kana kuma ko wani Side da baƙin su. Haka yasa su Ummi da Saratu da Larai zagewa. Sukayi abinci kala-kala kana suka ciccika kulolin aka kai fada akai wurin bayi. Sannan sukayi nasu kuma suka sassaka a Foodflaks masu ɗan karen kyau suka jera a Dinning table, tare da plate, spoons, and forks. Kana sun cika Fridge kuma da drinks kala-kala. Sun kuma yi Pepper Checken mai zafi na zabbi. Sai kusan ƙarfe ɗaya suka gama komai, Su Saratu suka kimtsa komai kana suka tafi. Su kuma duk suka shiga ɗaki da nufin yin wonka. Tuni zuwa lokacin Masarautar Joɗa ta fara ɗinkewa da baƙi tako wani sashin. Sheykh Jabeer kuwa, tunda ya tashi. Ya nufi cikin Garden ɗin nan da ababen tarihin masarautar Joɗa yake. Zazzagayawa yakeyi yana dubawa, dan tabbatar da babu wani abun da zai cutar da wani ko wata. Sabida yasan yau manyan baƙi zasu shigo ciki. A nuna musu ababen tarihi da dai sauransu. Gefen da curin da macijiyar nan yake ya nufa. Ya dudduba ƙofofin ba hayaƙi ba komai. Sai dai in mutun ya kasa kunne zaiji sautin numfashin macijiyar ka da ƴan ƙanana kuka irin na ƙananan macizai. A hankali ya ƙara matsowa bakin curin. Cikin nitsuwa yayi gyaran murya. sai kuma yaji sautin kukansu da kuma numfashin uwar ya ƙaru sosai. A hankali yace. "Assalamu alaikum, ya ke wannan halittar Ubangijin sammai da ƙasai". Gyara tsayuwarshi yayi jin numfashin na ƙara matsowa. A hankali yace. "Ba cewa nayi ki fitoba, nazo in roƙeki ne kamar yadda Manzon Allah ya sanar mana, dukkan halitta tanaji. Kuma ina kaga wani abun cutarwa a gidanka ka haɗashi da Allah da Manzonsa kace ya fita. Manzon Allah ya bamu tabbacin. Muddin ba mai cutarwa bane zai fita. In yaƙi fita kuwa ka kasheshi". Ɗan zagaitawa yayi jin kukansu ya kuma tsananta, cikin sanyi yace. "Ni bazan roƙeku kan ku fita ku bar muhallin zamanku da ban san tsawon shekara nawa kuke rayuwa a wurinba. Kuma bansan dalilin zamanku a wurinba. Shiyasa bazance ku bar Masarautar Joɗa ba. Kuma bazan kasheku ba, Sai dai roƙana garemu. Munada baƙi a Masarautar Joɗa kuma yau zasu shigo, dan Allah da Manzonsa, kada ku fito ku baiyana kanku ga baƙinmu kada ku razana mana baƙi kada ku cutar mana da mutanenmu. Kuyi zamanku a muhallin ku". Shiru sukayi tsit alamun sun jishi kuma sun gamsu". Fahimtar hakane yasashi cewa. "Na barku lfy". Yana faɗin haka ya juya, Lamiɗo da Galadima ya gani tsaye a bayanshi. Murmushi sukayi tare da matsowa inda suke. Galadima ne yace. "Kada ka damu da fitarshi da zamanshi da yaranshi Domin kai ke ganinshi a nan, amman duk in da wani mugu ya shigo masarautar Joɗa da nufin yiwa Lamiɗo wani abun zai ganta da yaranta a gabanshi. Amman wanda yake jinin wannan gidan bazai ganshiba. In kaga mutun ya ganshi saida sahalewar Lamiɗo". Shiru yayi yana kallonsu. Shi kuwa Lamiɗo a hankali yace. "A ƙalla yafi shekaru ɗari biyu da arba'in a cikin wannan curi a wannan Masarautar tun zamanin baban kakana Joɗo yake nan, ba kuma tsafi bane, ba sihiri bane, kamar yadda kowa ya sani shi maciji curi gidan zamansa ne, to bulalin caɗin masarautar Joɗa kuwa suma asali nan suke da zama curin ne ya binnesu, kana macijiyar ta shiga ciki, shine ma dalilin hana shaɗi to sai dai lokaci zuwa lokaci in an sarki maici yazo wurin yayi sallama macijiyar kan fito, in zata fito takan fito da balalin a binɗinta. Sai daga baya ta fara fita ita da ƴaƴanta suna yawo cikin masarautar Joɗa ne, muka gane yunwa ke sata fitowa, sai ta shiga cikin kaji tasha kwayaye ta haɗi ƙananan kaji. Lokacin da muka fuskanci haka sai muka fara kawo mata kwai a matsayin abincinta. Daga baya muka fahimci in mutun ya shigo da mugun nufi tana razanashi". Taɓa bakinshi yayi cikin rashin yarda bare gamsuwa yace. "Ni dai ban tambayeka ba, inma tsafine kaidashi Ni nan Muhammad Jabeer bani dalaifi a ciki nayi-iya yina in rabaku da wannan tsarabe-tsaraben na masarauta kun ƙiya". Ya ƙarishe mgnar yana juyawa ya nufi wurin da tsuntsayen wurin suke. Gefenda aku yake ya nufa. Tana ganinshi ta kaɗan fiffigenta tare da cewa. "Sheykh Jabeer ya dawo". Murmushi yayi tare da shafa kan akun yace. "Ya dai tsuntsuwa mai daraja ya gida". Cikin irin mgnarsu na Ali tace. "Lfy Sheykh ya madina garin Manzon Allah". Ta ƙarishe mgnar tana kaɗa kanta da jelarta alamun yiwa sauran tsuntsaye rigimar ance mata tsuntsuwa mai daraja. Murmushi mai faɗin Sheykh yayi ganin. Ɗawisun nan tazo gabanshi ta tsaya ta buɗe dogon jelanta ta kaɗashi tayi sama dashi. har yana taɓa gemunshi cikin sanyi yace. "A a kekyawar tsuntsuwa mai kyan ado da tafiya". A hankali ta karkaɗa jelan kana ta fara zagayashi. Tana nuna mishi kyan tafiyar. Su kuwa sauran tsuntsaye kuka suka farayi. Murmushi mai faɗi ya kumayi tare da cewa. "Tsuntsaye masu zaƙin murya da sauƙin firewa". Aifa nan suka tashi sama suna shawagi a wurin. A hankali ya juyo ya kalli tarin tattabarun dake gabanshi mazan ciki suna ƙotowa wa matansu. Kai ya rausayar tare da cewa. "Iyayen soyayya duk cikin tsuntsaye bayaku a soyayya". Ai sai suka fara irin kukansu nan guggdu-gudduu guuu". A hankali ya fita yankin tsuntsayen bakin ƙoramar dake gudana a tsakiyar Garden ɗin ya nufa. Inda agwagin ruwa keta shawagi a bakin wurin. Zama yayi yana nazartan lamuran halittun ɗan adam. Ko wanne halitta akwai mace akwai na miji. Kuma ko wanne halitta namiji baya iya rayuwa saida macce. To shi menene matsalarsa da duk manyan likitocin duniya suka kasa ganowa, kowa sai yace mishi lafiyarshi lau. Shi kuma yasan baida lfyar maza, tunda bai taɓa jin wani abu ya motsa a zuciyarshi bare yasa wani sashi na jikinsa motsawa ba yana dai jin shi wasu lokutan a namiji jim kadan lbri zai sauya. Gefenshi Lamiɗo da Galadima sukazo suka zauna. Bisa wani carpet da hadimin da ya shigo yanzu ya shimfiɗa musu. Yana fita wani ya shigo da kayan abinci. Cikin kula Lamiɗo yace. "Taho nan muci abinci Ustazu". Hannunshi yasa ya shafa cikinsa. Sosai yakejin yunwa hakane ya sashi gyara zama nan sukaci abinci su ukum su. Gani. Ƙarfe ɗaya tayine, lokacin salla ya ƙara to. Ga ɓaki nata shigowa masarautar Joɗa. Yasa suka tafi. Shi yana shigowa bathroom ya wuce. Wonka ya fesa mai rai da lfy kana yayi al'wala. Kana ya fito ya kimtsa cikin wasu tattausan riga da gajeren wondo 3 qtr yasaka kana yasa tattausar rigar mai guntun hannun. Duk kalarsu Royal blue ne, sai ya ɗauka farar jallabiya. Fara mai ɗan karen kyau. Kana yasa baƙar al'kyabbar jikinshi tare, dasa hirami mai fari da ja, yayinda hakama takalmanshi fari da ja. Wasu sabbin turaran da ya seyo ya fesa a kan sabbin kayan da ya saka masu ɗan karen kyau. Wani irin ƙamshi yakeyi mai daɗin shaƙa. A hankali ya fito falonshi, kallon abinci dake jere kan Dinnin yayi kana ya wuce ya fita. A falon ya samu su Jalal da alamun da al'wala a jikinsu. Can falon Shatu yajiyo muryarta tana kiran Hibba dake ɗakin Mama. Sai yanzu da yaji muryarta ne ma shi ya tuno da ita a gidan. Kai ya kaɗa yasa ƙannenshi a gaba suka tafi. Suna isa masallacin akayi sallan azahar. Ƙarfe ɗaya da mintu arba'in suka firfito masallacin da ya cika yayi maƙil mafi akasarin matasa suna cikin shigar sukuwane. Yana fitowa gida ya nufa sabida bai son yawan hayaniya, kuma zaiyi baccinsa da ya saba dashi, baccin tsakanin azahar da la'asar. Su Jalal kuma cikin abokansu suka nufa. Yana dawowa Falon Hibba kaɗai ya samu ta kunna tv tana kallon Film ɗin India kamar zai hanata kuma dai sai ya wuce. Bayan tayi mishi sannu da dawowa. Yana shiga ɗakin ya tura ƙofar ɗakin ya rufe ba tare dasa key ba. Kana yasa hannunshi ya kashe fankar, tare da kashe wutan ɗakin. A hankali ya iso bakin gadon. Zare Al'kyabbar ajikinshi yayi ya ajiyeshi bisa gadon. Kana ya zare jallabiyar jikinshi itama ya ajeta kan gadon ya rage dagashi sai 3 qtr da ƙaramar rigar. Dan sosai yake jin bacci, sanadin ɗan zafin hadarin dake haɗuwa yayi yawane yasa ya ƙara gudun AC kana. A hankali yayi taku zuwa, gefen gadon agogon hannunshi ya cire ya ajiye a kan Bedside drower'n dake kusa dashi. Konciya yayi a nan a ƙasa bisa tayis babu shimfiɗan komai bare pillow. Wannan tsarinshi ne da yakeyi, wanda yanayin hakane dan tuna konciyar ƙabarin da wata rana zai riskeshi. Wani lokacin ma, harda AC'n yake kashewa. Yana konciya ya fara tasbihi yanayi a hankali idonshi na rufuwa, wannene yasa yakeyin bacci a lokacin da yaso. A can cikin masarautar Joɗa kuwa. Cikin wani irin farin ciki Jalal Jamil suka nufi Side ɗin Hajia Mama jin labarin Ya Affan ya dawo daren jiya karfe biyun dare, a bakin Imran A falo suka samu Hajia Mama cikin tarin bege da kewar ɗan uwan nasu Jalal yace. "Mama wai Yah Affan ya dawo?". Cikin murmushin tace. "Eh ya dawo". Da sauri Jamil yace. "Yesss Jalal zomu tafi tafi Side ɗinshi Aunty Mami an shawo turai an dawo". Da sauri suka tsaya jin Mama na ce musu. "Basa nan tunda safe Aunty Mamin naku ta matsa ya kaita gida wai Abban Yusuf ba lfy, to sun tafi can, Aryan ma yazo bai sameshi ba shima ya tafi can duk sun haɗe a can". Da sauri Jalal yace. "Muje mu ɗauko shi dan wlh su Hamma Yusuf da Ya Aryan bazasu barshi ya dawo da wuriba". Cikin murmushin Jin yadda yaran ke son Juna tace. "Yanzu kuwa zasu dawo, dan kunsansu duka uku da son daba, sun girmama su basu bar hawa doki da tsereba kuma kasan Yusuf zaice suzo wurin uban gidansa Malam Jabeer". To da hakane suka ɗan gamsu suka nitsu. A can Dou Gire kuwa samun jikin Abban Yusuf da sauƙine yasa. Suka shirya suka nufo Masarautar Joɗa. Ummi ma tayi kolliyar sallanta tayi kyau ta fito falon, inda Hibba take. Shatu kuwa tana ɗakinta lokacin ta gama yin kolliya tasa wani damdatsen Shadda lace mai masifar kyau, Royal blue ne mai kyau da ɗaukar hankali sai zaren lace-lace ɗin da akayi da red and pink guava mai masifar kyau, sai wani irin sheƙin shaddar takeyi tana fidda maiƙon kyau. Doguwar rigace inrin fitet ɗin nan na zamani mai ɗan karen kai duk inda sirin yanken fisis ɗin yake an bishi da jerin duwasun shuwa riski masu sheƙin Daimond, cib-cib rigar tayi a jikinta. Murza ɗauri ɗan kwali tayi irin mai stpes ɗin nan Kana ta tura ɗan kwalin kaɗan wannan tattausan saje da suman dake konce a goshinta ya fito ras. Sai ta baya kuma ta tsakiyar ɗan kwalin ta bar rami ta fito da jelan gashinta ya konto har kafaɗanta ba tare da ta kitseshi ba. Wasu ƴan kunne da sarka na azurfa ta saka a wuyanta, sai wani kekyawan agogon fata rea ƙirar Gucci ta manna a tsintsiyar farin hannunta da yake, ɗanɗase da zanen jan lalle mai kyau. Gyale rea color mai masifar kyau ta ɗan yafa a kafaɗunta. Wasu turaruka kala biyu ta fesa, kana ta kalli muskarta da jikinta a madubin. Wayarta ta ɗauka ta ɗan kaikaice ta ɗauki kanta hoto ta cikin madubin tayi kyau sosai. Wasu takalma marasa tudu tasa suma rea color ne. Tana riƙe da wayarta ta fito falon. Da sauri Hibba ta miƙe tare da cewa. "Wow! Wow!! Wow!!! masha Allah Aunty Shatu kin ganki kuwa masha Allah." Murmushi Aunty Juwairiyya tayi tare da cewa. "Kai gsky amaryar Sheykh ta fito da madarar kyau masha ALLAH". Ita dai sai murmushi takeyi dace musu. "Ngd". Cikin jin kunya. Hibba kuwa duk takun da motsin da zatayi sai ta ɗauke ta hoto. Daga ƙarshe ta rinƙa yi musu selfi su duka huɗu. Saida suka gajine kana suka zauna suna hira. Nan suka kira Umaymah suka sha hira. Suna cikin hira Ummi ta juyo da sauri jin muryar Affan yana sallama tare da cewa. "Assalamu alaikum. Ina Umminmu ina amaryar Hamma tuzuru". Miƙewa da sauri Ummi da Aunty Juwairiyya sukayi tare da cewa. "La Affan yaushe ka dawo". Murmushi yayi tare da cewa. "Jiya da tsakiyar dare, ina Auntyn nawa". Ya ƙarishe mgnar yana shigowa cikin tsakiyar falon. Tafa hannu Ummi tayi tare da cewa. "Suwa nake gani kamar Yusuf da Aryan". Cikin dariya sukace. "Muɗin ne dai Ummi". Cike da jin daɗi Ummi da Aunty Juwairiyya ke cewa. "Kai maraba lale lallai yau munada manyan baƙi , oh duniya Yusuf da Aryan kamar ba kuba". Dariya sukayi tare da zama a kujeru. Hibba kuwa tuni ta isa gaban Affan lakace hancinta yayi tare da cewa. "Sakaliyar Umaymah ashe kina nan bana zakiga shagalin sallan Masarautar Joɗa". Cikin sauri ya kalli Shatu dake ce musu. "Sannunku da zuwa". Da sauri ya juyo ya kalli Ummi kana ya kalli Aunty Juwairiyya tare da cewa. "Wannan ce Auntyn nawa amaryar Sheykh Ustaz Malam Dr Jabeer akarmakallu". Murmushi Ummi tai tare da cewa. "Eh itace". Cikin dariya ya kalli Yusuf da Aryan da suke gaisawa da ita yace. "Kan bala'i ashe dama Sheykh Hamma Jabeer yana kallon mata kalli yadda ya zaƙulo zankaɗediyar sarauniya". Yusuf ne ya daki kafaɗarshi tare da cewa. "Kaifa Affan ɗan iskane baka da mutunci, baiyi aureba kace mishi. Shugaban tuzuran Afirka. Yanzu yayi auren kuma zakace yana kallon to dama ce maka akayi shi makaho ne?". Dariya sukayi baki ɗayansu, Aryan ne yace. "Bar Affan da shegiyar surutu". Dariya suka kumayi kana duk suka zauna. Suka gaisa cikin tsokana Affan ya kalli Shatu dake danna wayarta tana kallon hotunan da sukayi yanzu yace. "Aunty Amarya Hamman namu yana nan ne, ayi mana iso wurin shi mu kwashi gaisuwa". Shiru ta ɗanyi tare da kallon Ummi. Da sauri Hibba tace. "Eh yana nan yanzu ya shiga". Kai ya gyaɗa tare da cewa. "To Aunty Sayyada ayi mana sallama dashi ace ɗaliban shi ne, Affan, Yusuf, Arya,". Cikin tsoron kada Shatu ta kuma zuwa ɗakin abun da ya faru jiya ya sake faruwa Ummi tace. "Ai yana bacci ne yanzu ko". Da sauri Affan yace. "No ba matsala in ance masa Yusuf ne, tashi kice muna sallama dashi." Cikin murmushin jin Yusuf da Aryan sunce. "Eh gsky gwara mu gaidashi kada ya gammu a wurin sukuwa yace bamu nemi izininshi ba". A hankali tace. "To bari a gaya mishi". Ta yunƙura zata tashine Ummi ta riƙe hannunta tare da cewa. "Shatu kadafa". A hankali tacewa Ummi. "Ba komai fa Ummi". Ganin hakane yasa Ummi ta sake mata hannun tare da cewa. "To Allah yasa". Amin Amin Juwairiyya da Hibba sukace. Shi kuwa Affan cewa yayi. "Allah bazaiyi faɗaba in yaji mune". Kai Ummi ta gyaɗa sabida basu san me take tsoron ba. Ita kuwa Shatu a hankali ta nufi Side ɗinsa. Su kuwa hirarnsu sukaci gaba dayi a falon. A hankali ta tura ƙofar falon nashi ta shiga. Shiru babu kowa babu komai sai sautin ac dake tashi fuuuhhh. A hankali ta lumshe idonta kana cikin sanyi ta nufi ƙofar ɗakin nashi. Tare da cewa. "Salamu alaikum! Salamu alaikum!! Salamu alaikum!!!". Shiru babu motsin komai, hakane yasa a hankali tasa hannun hagun ta dafa ƙirjinta dake bugawa. Kana tasa hannun damanta ta tura ƙofar Bedroom ɗin. Sai kuma gashi ta buɗu ƙofar. Wani sassanyan ajiyan zuciya ta sauƙe jin wani irin masifeffen ƙamshi da sanyi daya ratsa mata jiki da zuciya. Sallama ta kumayi shiru ba amsa. A hankali ta cusa kanta cikin ɗakinta da yake duhu. Wani irin bugawa ƙirjinta keyi kana. Kanta na sarawa da masifan ƙarfi. A hankali ta juya gefen mashigar ɗakin hannun tasa ta lalubi abin kuna wutan ɗakin danna ɗaya daga ciki tayi, hakan yasa ƙoyin wutan ɗaya mai kalar Sky blue ya kawo wuta. Sanadin hakane ɗakin ya kawo wani irin haske mai ƙayatarwa. Yanayin wutan ɗakin labulayen da kayan jikinta dana jikinshi sukazo iri ɗaya. Juye- juye tayi tare da cewa. "To ina yak". Shiru tayi bata ƙarisa rogowar mgnar ba hangoshi can ƙasa yana konce rigingine yayi pillow'n da tafukan hannunshin. A hankali tayi taku uku zuwa biyar ta matso kusa dashi cikin sanyin da ya fara yimata yawa ga cikinta dake tsuma a hankali tace. "Salamu alaikum". Ko motsi baiyiba bare tayi zaton zai amsa. Sallama ta kumayi shiru ba amsa. Ganin hakane ta matso a hankali take takun saɗab-saɗab take taka sawunta a hankali har ta isa kusa dashi. Da sauri ta zubawa ƙafar damanshi ido. Ajiyan zuciya tayi mai sanyi tare da mgnar zuciya. "Uhumm ashe dama yana komciya a ƙasa haka babu shimfiɗan komai ba pillow, da kuma ƙaramar riga da wondo iya guiwa." A hankali ta iso gab da kanshi, Cikin yin numfashi a hankali wai karya jita, ta rusuna ta zauna bisa sawunta irin zaman yin tahiyan salla. Cikin ƙurawa babbar yatsar ƙafar damanshi inda ta rinƙa biyo wannan zanen macijin dake kwance lib a ƙafarshi. Da ido tabi zanen har kan guiwarshi inda iya nan wondon 3 qtr ya rufe. A hankali ta ƙara sunkuyowa ta kurawa wurin ido, tare da mgnar zuciya. "To iya ina wannan zanen tafiyar macijin ya tsaya ne a jikinshi?". Jim kaɗan tayi kana a hankali. Ta miƙa hannunta, cikin sanɗa a hankali hankali tasa yatsunta biyu ta kamo bakin ƙafan wonɗon ta ɗan jawoshi a hankali tayi sama das...! Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 in Kuma special Group kikeso wanda a mako biyu ake gaba part 1 kuma abiyu za'a gama Part two da izinin Ubangiji yimin TRANSFER ɗin 1k ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. sai ki turo screenshot shaidar biyanki ta wannan number 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* Ta ɗan ja tayi sama da bakin ƙafan wonɗon wanda yake na robane bakin a tsuke yake. Da sauri cikin tsoro da rawan jiki ta saki robar. Pat ya fetti a jikinshi. Ganin ya motsa. Shi kuwa Sheykh Jabeer wani sassanyan numfashi ya ja mai tsawo tare da fesoshi a hankali kana, ya mirgina a hankali ya juya ya kifu cikin kasalan nauyin bacci ya ɗaura kanshi bisa cinyarta, Kana ya ware hannayenshi da sukayi ɗan tsami sabida pillow'n da yayi dasu. Ware hannayen yayi tare da miƙarar dasu. Ya zama tana tsakiyar hannunshi kana kanshi na kan cinyoyinta. Haɗe hannuyen nashi yayi ya sarƙafe yatsunshi wuri ɗaya, ya zama ya zagayeta tako ina yayi mata ƙawanya. Ya cusa hancinsa cikin mayafinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinta dana kayanta. A hankali ya kuma gyara kwanciyarshi da kyau kana yaci gaba da sauƙe sassauƙan numfashin. Ita kuwa Shatu wani masifeffen tsalle da bugu zuciyarta keyi tamkar zaiyi tsalle ya fito woje. Gaba ɗaya ida nunta kan sumar kanshi ta zubasu. Tare da kallon tattausan sajenshi dake kwance lib-lib a gefen fuskarshi. Wani sassanyan numfashi ta sauƙe tare da lumshe idonta cikin zuciyarta tace. "Allah shi ƙara". Sai kuma tayi sauri ta buɗe idonta tana tambayar kanta. "Allah shi ƙara me ɗin? Ya ƙara ruggumata ko meyeye". Cikin kauda zancen a ranta ta ɗan muskuta dan janye jikinta. Amman sai ta ji ya riƙeta gam-gam, yana ƙara cusa kanshi cikin jikinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren jikinta. Cikin tsoro murya na rawa a hankali tace. "Yah Sheykh!". Karab sautin muryarta ya ratsa kunnuwanshi. Sai dai ko motsi baiyi ba, A hankali ta kuma ce. "Yah Sheykh! Yah Sheykh!!". Shiru babu amsa sai numfashin da yake fiddawa a hankali yana kuma shaƙan ƙamshin jikinta. Cikin sanyi ta ɗan ɗago hannunta a hankali tasa taffin tattausan hannunta, ta ɗan rinƙa buge gefen fuskarshi a hankali a hankali tanayi tana cewa. "Yah Sheykh! Yah Sheykh! ! Tashi wai Affan dasu Yusuf sunzo, shine Affan yace inzo in tasheka". A hankali ya buɗe idonshi, Yanayin yadda take ɗan marin gefen fuskarshi da hannunta wanda ke ɗaure da agogo. A hankali ya ɗago hannunshi ya ɗan kan hannunta ya kamoshi ya riƙe, cikin tsoro ta fara kiciniyar kwace hannunta, Sai kuma tayi zuru, jin ya ja hannun da ɗan ƙarfi ya kawoshi dai-dai saitin fuskarshi. Idonshi ya zubawa yatsun hannunta da kullum in ya gansu da jan lalle yake tuna mishi baya. Da sauri tace. "Wash Allah na". Jin ya murɗa hannun ya juyo da fuskar agogon inda zai gani. Ƙarfe biyu da miti arba'in da ɗaya. Du-du baccin 40 minutes yayi tazo ta tasheshi. "Harda zuba min maruka". Ya faɗa a ransa. Ita kuwa kan tattausan suman ta ajiye sinsiyar hannunta. tana jin kanta na sara Especially in ta kalli saitin ƙasan gadonshi." A hankali ya sake hannunta kana ya yunƙura ya juya rigingine, ya fuskanci sama, ita kuma tana zaune tana kallon ƙasa hakanne yasa suna fuskantar juna, cikin wani irin yanayi ya zuba mata ido na wasu sakanni. Shigarta tayi masifar mishi kyau. Kodan tasa kalan kayan da yafi sone. Cikin muryar bacci yace. "Shine harda dukana? Meyasa ne ku mutanen garincan kuke son dukan mutun da kallon jikinsa?". Cikin tura baki tace. "Cinyana, nagaji kanka nauyi". Bai janye idonshi a kantaba ya yunƙura ya tashi zaune tare da juyowa ya fuskanceta. tanƙwashe sawunshi yayi tare da cewa. "Me zaki kalla a jikina? Woto Kin zama kamar ɓarauniya ko? Me kike son gani? Wani abu kike sone?". Cikin tura baki tace. "Nifa tada kai a bacci kawai nayi". Hannunshi yasa ya riƙo hannunta, yatsunta ya zubawa ido, cikin wata murya mai sanyi yace. "Masha Allah, kinyi kyau." Wani irin sanyi taji kalmar tashi tasa mata a ranta, ido ta ɗan ɗago ta kalleshi. Shima ita yake kallo, ido ya lumshe jin sautin zazzaƙar muryarta a hankali tace. "Nagode". Tonƙoshe kansa yayi bisa kafaɗa kana hankali ya sake hannun nata. Fuskarta ya kalla tare da taɓe baki yace. "Waya koya miki irin sa lalle Mammeyyyyy nah!? Dan tafi ko wacce mace iya lalle". Cikin sanyi da nazartar yadda ya kira sunan Mammeyyyyy da yadda lokacin ɗaya idonshi suka fara sheƙin tsastsafo da zafafan hawayen da ba zubowa zasuyiba. Cikin son gano meke cikin zuciyarsa tace. "Ummeyy nah ce ta koya min tun ina ƙaramar". Yatsunta ya jujjuya kana ya miƙe tsaye. A hankali ya juya ya nufi bathroom sabida baya son ta hango wutar ƙunar dake ransa. Ita kuma binshi da ido tayi, tare da langoɓar da kanta tana kallon sharabansa da gargasa yayi musu ƙawanya. A haka ta shiga wani nazarin tana mai maimaita sunan da taji ya kira da cikekken so shaƙuwa ƙauna tausayi rauni shogoba *Mammeyyyyy.* Ta maimaita sunan a fili. Shi kuwa Sheykh Jabeer al'wala yayi kana ya fito. Yayi mamakin ganinta a zaune bata fita ba. Hararanta yayi ganin yadda taketa kallonshi. Jallabiyar shi ya zura, kana yasa al'kyabbar, tare da sa Hiraminshi. Sannan ya fesa turare. Duk inda yayi tana binshi da ido. Wayarshi da yafi yawan riƙewa ya ɗauka ya zura a al'jihunsa. Sannan ya nufi bakin ƙofa inda takalminshi suke yana cewa. "Wannan kallon maitan fa". Da sauri ta janye idonta. Cikin daƙilewa yace. "Kada ki cinyeni da ido fa. Bana son kallo, ko kina bina bashine?." a hankali ta miƙe tare da lumshe ido ta biyu bayanshi. Tana gyara mayafinta tare da cewa. "Ni ban kalleka ba". "Uhummm." yace a taƙaice. Kusan a tare suka fito. Yana gaba tana bayanshi, Suka fito tsakiyar falonshi. Tsayawa ya ɗanyi ya gyara masaƙalin Al'kyabbar tashi. Shiyasa ya zama a jere suke tafiya tana gefen damanshi. A haka suka fito cikin corridor'n. Suka doshi Falon cikin kwarjini da dacewa da juna sai ƙamshi da sheƙi zallan kyau sukeyi. Da Sallama a bakinshi suka kutsa kai cikin falon. Wani irin dariyar jin daɗi Affan da suke can Dinning area yayi, suna cin abinci da Ummi ta matsa suci. Wani irin murmushi Yusuf da Aryan ma sukayi tare da miƙewa suka nufi inda uban gidan nasu ke tsaye da kekyawar tauraruwarshi mai haskawa. Affan kuwa wayarshi ya zaro yana kekkebta musu hoto tare da cewa. "Ga amarya, ga ango, suna carabki da zallan kyau da ƙamshi". Murmushi sukayi dukansu, ita kuwa Shatu tana tsaye gefenshi. A haka su Affan suka iso. Suna Isa Affan ya ruggumeshi shima Sheykh ruggumeshi yayi tare da make ƙeyarsa. Da sauri ya janye kanshi tare da cewa. "Wayyo Allah na yanzu Hamma Jabeer na girma harda yaran nawama ban wuce dukaba". Murmushi yayi tare da, Ruggume Yusuf da Aryan Allah ya sani yana masifar son yaran nan har gobe bashi da ɗalibai sama dasu yana sonsu so na musamman, duk sanda ya gansu yakan tuna ƙuruciyarsu tun suna yan shekara goma sha biyar-biyar yake tare dasu shi ya horas dasu. Yana tura irin tarin ƙalubale da suka fuskanta a gasar Polo da kuma irin nasarorin da suka samu Especially Yusuf nashi yana tuna yadda yaran suke sheƙiyanci in sun haɗu, yana jinsu tamkar su Jamil. Cikin murmushin ya shafa kansu tare da cewa. "Sannunku da zuwa". Cikin jin daɗi sukace to. Bisa kujera ya zauna su kuma suka zauna a ƙasa a gabanshi kan carpet. Ita kuwa Shatu a hankali ta juya ta nufi kitchen ganin Ummi ta nufi can. Hibba kuwa na gefensu tana gayawa su Jalal ga Ya Affan fa. Da gefen idonshi ya bita da kallo. Har ta ɓacewa ganinsa, Allah ya sani yana son abu blue baya iya cire idonshi kan abu mai kalar shiyasa yake jin baya gajiya da ganinta, da zai samu kada tayi nesa dashi, dan tayi mishi kyau sosai farar fatarta ta fito fes kamar balarabiya ji yake tamkar ya bita duk inda tayi. Cikin murmushin ya kalli Aryan yace. "Aryan Ina su Yusuf ƙaramin". "Alhamdulillah suna lfy Malam". Kai ya jinjina tare da cewa. "Masha Allah". Sai ya kuma kalli Yusuf yace. "Ina mai sunana baka zomin da shiba". Murmushi Yusuf yayi tare da cewa. "Malam baka tambayi Aryan ƙaramin ba da yakeso ya zama kamarka sai ka tambayi mai sunanka". Dariya sukayi kana yace. "Ayyah my Aryan, sun kusa tafiya ai in sha Allah Jami'atul Madina zaiyi karatunshi". Da sauri suka juyo suka kalli Jalal da Jamil da suka shigo da sauri. Ruggume Affan sukayi suna cewa. "Oyoyo ya Affan". Hannu ya basu suka tafa kamar sa'ao',insa ne su. Cikin dariya yace. "Tun ɗazu nake kiranku bakwa ɗagawa. Nace waɗannan ana can cikin hayani ". Murmushi Jamil yayi tare da miƙawa Yusuf hannu wanda ke cewa. "Oh wato Affan kawai kuka gani mu ko oho ko". Cikin ɗan sakin fuska Jalal yace. "Afwan Hamma Yusuf ya Aunty Zahra da Mama". "Suna lfy. Sun gaidaku". yace tare da bashi hannun. Kana suka gaisa da Aryan. Sannan suka miƙe sukace bari suje wurin Aunty Mami. Cikin dariya Affan yace. "Eh kujema kuzo da ita taga matar babban yaya". Da sauri Jamil yace. "A a ka kawota da kanka dai". Ya ƙarshe mgnar suna fita. Su kuwa cikin yin ƙasa da kai Yusuf yace. "Uhum dama Malam zamu ɗan shiga wasan daba ne in batsala". Murmushi mai faɗin Sheykh yayi tare da cewa. "Wato ku dai har yanzu baku girma da batun doki ba". Shiru sukayi sai Affan ne yace. "Tab Yusuf kuma da in ya ga doki bai hauba jikinshi har rawa yakeyi". Murmushi Sheykh yayi kana yace. "To muje muyi salla. Tukun tunda sai anyi sallan la'asar za'a fara ko". To sukace tare da miƙa ganin ya miƙa dan tuni uku da kwata ta wuce. Affan ne ya kira Ummi tare da cewa suzo zasu tafi. A tare suka fito kitchen. Sabbin kuɗi rafa yan dubu-dubu Yusuf ya miƙawa Hibba ƙulli ɗaya dubu ɗari kenan yace. "Gashi miƙa wa Ummi ta raba muku." Affan ma ya basu. Hakama Aryan. Hibba sai tsalle take tana cewa. "Yessss my brother's Allah ya ƙara buɗi Amin Amin sukace kana suka juya zasu fita. Cikin tsare girma Shatu tace. "Mun gode, a gaida gida". Gida zaiji sukace kana suka fita suka tafi. Suma su Ummi wucewa sukayi yin al'wala. Ana idar da salla kuwa aka fara hawan daba, hawan sarki dama duk sauran shagulgula na gidajen masarautun gargaji yayin wurin taron bikin salla. MASARAUTAR Joɗa ta cika tayi maƙil da bani Adam. Haka dai akayi taron lfy aka tashi lfy sai kuma gobe in Allah ya kai rai. Washe garin ranar da sassafe. Sheykh ya tafi asibitinshi. Ko karyawa baiba. Sai kusan sha ɗaya ya dawo da alamun yunwa da gajiya tare dashi. A falon ya zauna suna gaisawa da Ummi dan basu gaisaba ya tafi daga masallacin can ya wuce. Ummi kuwa tasa Shatu ta kai mishi breakfast ɗin shi da yanzu kam in yacima ya zama lunch ne. Hibba kuwa na can ɗauki tana ƙenƙesa ado. Cikin isa da ƙasaita Gimbiya Saudatu ta shigo tsakiyar falon babu ko sallama. Haɗe fuska Sheykh yayi tare da cewa. "Wannan banzan ɗabi'a na arnatakun baya, dan ko arna yanzu suna cewa konkon, mutun kamar shanu ko mahaukaciya". Cikin isa ta iso tsakiyar falon. Dai-dai lokacin kuma Shatu ta fito falonshi. Cikin shigar doguwar riga mai ruɓi biyu. Kanta ta ɗago ta kalli Shatu kana ta kalleshi cikin yin dariyar mugunta tace. "Eh kam tabbas tunda ka auro mahaukaciya dole kasan hali da ɗabi'un mahaukata ai. Zuwa gaba kaɗan kaima zaka fara ihu da kuka da sume-sume irin na wannan al'janar fulanin daji daka auro ɗin". Cikin tarin mamaki Ummi ta kalli Shatu ta kuma kalli Hibba da yanzu ta fito, cike da al'hinin ta yaya taji wannan batun ya fasa Masarautar Joɗa yes in dai Gimbiya Saudatu taji to ai shike nan kowa ma zaiji. Shi kuwa Sheykh ba gane inda soki burutsunta ya nufaba yayi. Ita kuwa cikin watsa musu kallon ku sakarkaru ne tace. "Kuna mamakin ta ina naji, cewar ji shekaran jiya iwar haka dai wannan matar tashin tana yashe a sume da ido a wulkice tana ƙarkarwa farfaɗiya kamar mazari ne. To ai Ni duk wanda yaci tuwo dani miya yasha. Inada tawa a cikinku duk motsinku ina dashi a tafin hannuna. Nan gaba kaɗan zamu samu riƙeƙƙiyar mahaukaciya a masarautar Joɗa". Cikin tsuke fuskarsa yace. "Yanzu ma ai muna da su mahauka ta kam, ke ɗin me banbancin ki da zararrun". Shiru yayi ganin yadda Shatu keyin taku a hankali cikin isa ta nufi gaban Gimbiya Saudatu. Ummi da Hibba kuwa miƙewa tsaye sukayi. Shi kuwa Sheykh gyara zamanshi yayi tare da ɗaura ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya. Ita kuwa Shatu a hankali ta isa gabanta. Ido ta zuba mata tare da yi mata kallon tara saura kwata. Cikin dakkeyar Muryar rashin tsoro tace. "Toh *Bushiya* mai mugun baya, Bushiya mai bayan ƙayoyi masu kama da allurai, ki buɗe idonki da kyau ki kalleni Ni AYSHA ALIYU GARKUWA ba sa'ar yinki bace uwar mahassadan duniya, in kina cin ƙasa to tabbas ki kiyayi ta curi, ki bar min mijina ya sarara ki far masa rayuwa, ɗan shi ba sa'an yinki bane ki bar min mijina ya huta baya son ihun nan da kikeyi mishi, zan kuma iyan komai dan ganin na kauda dukkan abinda baya so." Wani irin daɗi ne ya rufe zuciyar Ummi da Hibba Sheykh kuwa ƙafarshi kawai yake kaɗawa yana mai binta da wani irin kallo mai tarin ma'anoni kalmarta ta *Mijina* yake ji tana sa duk wani hudan gashin jikinsa na amsa amon kalmar yana ratsa jikinshi da zuciyarsa haka yasa bai san sanda wani yalwataccen murmushi ya subce mishiba, tabbas Shatu akwai ƙarfin hali. Ita kuwa Gimbiya Saudatu tsuru tai da ido. Itako Aysha cikin karsashi tace. "Na lura ke dabbace, sam bakya gane yarukan mgna na bani Adam, kinfi son sai an miki irin yarukanku na dabbobi. Kina tsaye da farin yawu a bakinki kina zubda jini. Yayinda wasu ke bayanki da jini a bakinsu suna fidda farin yawu. Sokuwar rama mai tsami. Ni nan da kike ganina da idona tar a buɗe na shigo Masarautar Joɗa, kada ki ganni haka Ni ɗan hakine da zaki iya renawa amman tabbas zan tsole idanun magauta ruwanshi ya tsiyaye. In kin san fullanci to. *MIN MI KURORI CITTA NFAMƊA NHEYAH* NI ```DAKKEN YAJIN BORKONE INYI KAƊAN IN KUMA ISHI MUTUN``` Ki tsumayeni tabbas zanyi daka inyi tankaɗe inyi rairaya a masarautar Joɗa!. Ke ko kallo baki isheni ba domin bata ke akeyi ba da manyan Magauta nakeyi. Ja mugun bakinki ki fice min a gidana!". Rab-Rab. Jalal da Jamil dake da Jafar shigowa ne, suka tafa mata da hannu bibbiyu. Hakama Hibba. Ummi kuwa ƙasa tayi da kanta. Shi kuwa Sheykh ƙanƙance idonsa yayi yana kallonsu yana kaɗa ƙafa ya watsa idanunshi cikin na Gimbiya Saudatu yana mata kallon itama ta isheki. Aunty Juwairiyya kuma da tun ɗazu tana bakin ƙofar shigowa da sauri ta juya ta koma Side ɗin ta. Ya Jafar kuwa sai murmushi yake tare da dunƙulawa Shatu hannunshi kamar haka👍🏻 Wani irin juyawa Gimbiya Saudatu tayi tare da jan al'kyabbar ta ta fita. Har taje bakin ƙofa Shatu tace. "Ki riƙe kalmar mahaukaciya tabbas zakiga mahaukata a masarautar Joɗa zasu baiyana bila'adadin." Daga nan ta juya ta nufi Dinning area ɗin babban falon. Ita kuwa Gimbiya Saudatu ta juya ta fita. Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya sauƙe ƙafafunshi kana ya miƙa ya nufi falonshi. Haka nan yaji murmushi na tsubce mishi. Tabbas ya gamsu da ƙarfin halin Shatu da rashin tsoronta, sai dai yana jiye mata tuggun mutanen da bata san halinsu ba. Yana shiga yaci abinci kana ya shiga yayi wonka. Kana ya ɗauki wayarsa. Jalal, Jamil, Hibba, Ya Jafar, Shatu kuwa zama sukayi a falon cikin mamaki Ummi tace. "To wacece yar leƙen asirin Gimbiya Saudatu a wannan sashin? Ya akayi tasan abinda ya faru da Shatu? Waya gaya mata? Bayan in banda muyamu. Ni Juwairiyya, Hibba, Jalal, Jamil, Jafar. Wanda shi baya mgna, ita kanta Shatu bata san meya faruba batasan ya akayi ba. To waya fitar da wannan zancen a cikinmu?." Cikin gsky da gsky duk suka ce wlh babu wanda suka taɗawa mgnar Hibba harda ƙollarta tace. "Wlh ita ko Umaymah ma bata gayawa ba". To lallai kam akwai buƙatar bincike a tsakanin mu." Ummi ta faɗa tana mai cike da al'hinin abin. Ita kuwa Shatu uhummm. Kawai ta iya cewa tayi shiru bata ce komaiba. Haka dai suka tashi taron. Sheykh kuwa, number Umaymah ya kira bayan sun gaisa ne yace. "Uhumm Umaymah wai me kika sani ne ya faru da wannan yariyar shekaran jiya?". Cikin tsoro da son kauda batun Umaymah tace. "Wacce yarinyar kuma?". Fuska ya ɗan tsuke yace. "Waccar yarinyar dai". "To bata da sunane ita". Ta kuma ce mishi. Cikin gajiya da batun yace. "To ni ba sanin sunanta nayiba, baku gaya min sunanta ba." Wani irin murmushi Umaymah tayi tare da cewa. "Ban gane bafa Jazlaan". Hannunshi yasa ya ɗan shafi sajenshi. Yana mai son yasan meya sameta, meya faru da ita, shiyasa a hankali yace. "Yarinyar dai da kike cewa ɗiyarki!." Kai Umaymah ta jinjina tare da cewa. "Laah ni nama mance bamuyi mgnarba, ran sallane tayi aiki ta gaji tunda safe bataci komaiba to ashe tanada olsa shine fa, ta shiga ɗakinka zatayi maka shara ta faɗi ta suma, da kyar aka samu ta farfaɗo suanta kuma Aysha". Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa. "Shirme in banda sakarci da raki mutun ya bar kansa da yunwa da gajiyan aiki mutun har ya suma". Ya ƙarashe mgnar yana jinjina darajar sunanta a ranshi. Cikin jin daɗin bai tsananta bincike ba tace. "Akwai wani abune?". Gyara zamanshi yayi tare da cewa. "Wannan mahaukaciyar Gimbiya Saudatunce tazo take cewa wai taji lbrin ta haukace". Daga nan ya kauda zancen. A hankali ya miƙe yana riƙe da wayar a kunne shi. Dinning area ya nufa. Murmushi yayi gano tabbas akwai abinda Umaymah ke ɓoye mishi. Hannunshi yasa cikin zirin zirin igiyoyi masu duwatsu masu daraja sheƙin Daimond da sukayi Dinning area ɗinshi a madadin labule. A hankali yasa hannunshin kan na'urar CCTV camera dake liƙe a gefen inda yake ajiye key, wanda duk abinda za'ayi a falon zai gani. Cikin sanyi yace. "Uhummm Umaymah kiyi mata faɗafa, ta dena hawan ƙawara kan mutanen masarautar Joɗa, ta kiyayi kanta da faɗa da magautana zasu ilatata. Bata san komaiba a kaina ta tsaya matsayin baƙuwa Umaymah zafa suyi mata illa". Ya ƙare mgnar a hankali. System ɗinshi dake kan Dinning table ɗin ya jawo. kana yaja kujera ya zauna ya fara haɗa na'urar. Ita kuwa Umaymah a hankali tace. "To ya zatayi tunda ƙaddara ta kasantar da ita matsayin matarka, ko ita kurmace dole sai sun nemi yi mata illa sun sabautata. Dole kasata cikin jerin mutanen da ka zame musu GARKUWA a masarautar Joɗa, tunda ita dai matarka ce, amanarka kuma". Shiru yayi yana jinta yana mai kallon fuskar System ɗinshi date ɗin shekaran jiya ya shiga. ai kuwa Shatu ya fara cin karo da ita tana share falon da goge ko ina. Sai kuma lokacin da suka shigo ita da Jamil da Hibba suka nufi bedroom ɗin sa. A hankali yace. "Uhmmm Umaymah sai anjima zan kiraki". To tace kana ya katse kiran. Ido ya zuwa System ɗinshi. tsaki yaja karo na forko da yaji da ya haɗa na'urar da cikin ɗakinshi. Gashi yanzu baya ganinsu sai dai ihun Hibba, da fitowa da tayi da gudu ta kira Ummi da yadda suka shigo da Aunty Juwairiyya. Kanshi ya gyaɗa lokacin da yaga sun fito a hankali ya rufe System ɗinshi. Dafe kanshi yayi yana nazari. Ya dade a nan sosai kana ya koma ɗakin shi. Da dare misalin karfe sha ɗaya na dare saura. Shatu ta kalli Hibba dake konce tuni tayi bacci. Yasa ta miƙa a hankali ta nufi ɗakin Ummi. A bakin ƙofar ta tsaya a hankali tayi sallama. Cikin mamaki Ummi dake zaune bisa sallaya ta idar da shafa'i da wutri kenan taji sallamarta. Juyowa tayi tare da amsawa tace. "Shatu". A hankali tace. "Na'am Ummi". Cikin mamaki tace. "Lfy kuwa shigo mana". A hankali ta shigo tare da cewa. "Lfy lau Ummi, nazo wurinki ne." "To". tace tare da nuna mata wurin zama bakin gadonta. A hankali ta ƙaraso kusa da ita, Gabanta ta zauna kan sallayan cikin nitsuwa tace. "Ummi kiyi haƙuri ko zakiyi bacci na hanaki". Da sauri ta girgiza mata kai alamar a a. Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "To Alhamdulillah". Sai kuma tayi shiru. A hankali Ummi tace. "Kina buƙatar wani abune?". Cikin nitsuwa tace. "Uhum Ummi dama tambayarki nake son yi". Gyara zama Ummi tayi kana tace. "Ina jinki". Itama zamanta ta gyara a hankali tace. "Dan Allah Ummi in ba damuwa, dan Allah da Manzonsa ki sanar dani abinda Allah ya sanar dake a kan masarautar Joɗa mana. Ummi kaina na kullewa da mutanen masarautar Joɗa, ban gane banbanci su da dankantakarsu da kuma. Alaƙarsu ba". Wani irin dogon ajiyan zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa. "To Shatu ai kin gama komai tunda kika haɗani da Allah da Manzonsa. Kuma dama nace miki ki tambayeni duk abinda baki gane ba, zan gaya miki. To amman akwai wani abun sirrine garesu masarautar in na faɗa kamar cin amarsu ne, wani abun kuma nima kaina ban sanshi ba. Hannun Ummi ta riƙe tare da zubda hawaye tace. "Ummi gaya min yadda masarautar Joɗa take ko zan san irin zama da takun da zanyi da mutane da ɗaukar mataki kan abinda ke faruwa". A hankali Ummi ta gyara zamanta. Ta jingina da jikin gado. Kana itama Shatu ta gyara zamanta ya zama suna fuskantar juna da kyau. Cikin sanyi Ummi ta fara bata lbrin. *Masarautar Joɗa* tsohuwar masarautace. wacce tun kafin zuwan Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ƙasashen Afrika tana kafe da ƙafanta. Kuma masarautar Fulɓe ce tun a wancan lokacin. Lokacin da Shehu Usman Ɗanfodiyi ya iso nan ƙasashen hausa ya basu musulunci ya kafa tutocinsa tako ina tako wacce masarauta. A lokacin Masarautar Joɗa sunanta masarautar Fulɓe. Kuma lokacin Sarki Sule ne a kan karagar mulki. Baban Joɗa kenan wanda yake shi Joɗa shine kakan sarkinmu na yanzu wato Lamiɗo. A lokacin sarki Sule yanada ƙarfin mulki yana da mata huɗu ƙwar-ƙwara biyar. Allah ya azurtashi da arzikin yara a ƙalla sunfi hamsin a cikin matansa huɗu na aure. Akwai wata ɗaya da ake kira Gimbiya sumaye ƴar sarkin kal'anace. Gimbiya Sumaye inrin matannane da Allah ke jarabta da haihuwar wabi. Bima'ana tana haihuwa kuma yaran na rasuwa. A haka har ta haifi yara kusa goma kuma bata da rayeyye ko ɗaya. Cikin ƙwar-ƙwaran sarki Sule ne ɗaya ta ɗauki ɗanta na miji ta bata halak malak kwanan yaron uku a hannunta ya rasu. Wata cikinsu ta kuma bata still shima kwananshi uku ya rasu. A haka duk ƙwar-ƙwaran sarki Sule saida suka bata yara suna rasuwa. Daga nan uwar gidan Sarki Sule wacce take babarbariya ce. Tasa mata suna cikin wasa na tsakanin Fulani da bare-bari amman a zahiri da gaske takeyi. Gsky mai tafiya da wasa kenan. Sai ta sawa Gimbiya Sumaye suna da fillanci wai *Ɓadamaya* ma'ana wai duk wanda ya matso kusa da ita zai mutu, ko wanda ya bata riƙon ɗa kowa kwana uku ne mutuwa zaiyi. Kamar da wasa sunanta ya zama Gimbiya Ɓadamaya. Mutanen masarautar akayi ta mata izgili da habaici. Takan zauna tayi ta kuka. babu mai rarrashi dan ita masarautarsu nada nisa a lokacin kuma babu ko Radio bare waya. Anan Allah ya bata wani ciki ta haifi ɗan ta namiji. Akasa mishi suna Umar faruq. Sai Gimbiya Sumaye take kiranshi da Joɗa ma'anar Joɗa shine zauna. Da haka sai aka maida abun ba'a aka rinƙa kiran yaro da Joɗa. Allah cikin ikonsa ta yaye yaro lfy lau. Ta kuma haihuwa na goma sha biyu. Yariyar watanta biyar ta rasu, sai aka rinƙa mata dariya ana cewa saura *Joɗa* shima ya *Dilli.* Wato wai saura Joɗa shima ya *tafi.* Cikin ikon Allah kuwa ya raya Joɗa ya girma. Ya zama shine ƙarami cikin ƴaƴan sarki Sule kenan. Bayan wasu shekaru, sai Sarki Sule yace to shi zaiyi murabus, a cikin yayanshi yace zai naɗa babban ɗanshi Madu. Ɗan Gimbiya Falmata. Sai ko sauran ƴan uba duk suka tashi akece to sai ayi zaɓen manyan. To akwai ɗan Madu wanda yake mai ilimin addini dana zamani sunanshi Bala, sai ya shiga cikin masu neman mulkin ya kafa hujja da cewa. "Babanshi Madu jahiline dan haka a bashi shine ya dace da mulkar garin. Haka kuwa akayi aka ba Bala mulkin masarautar Fulɓe. Dole babanshi Madu wanda shine Magajin gari ya ƙaura ya bar garin. Tunda kinga bazai yiwuba ace yana mahaifinshi ya rinƙa serving ɗan shiba da baƙinsa ba. Haka dai Bala yayi mulki tsawon shekaru arba'in inda Joɗa kuma yake matsayin Galadima tunda ɗan tsohon sarki ne. To shi kuma Sarki Bala sai Allah ya azirtashi da tarin ya'ya mata ɗan shi na miji daya ne, Sadik. Ya bawa Sadik sarautan Sardaun. Bayan wani lokacin sai tsoro ke rufe Sarki Bala kada fa abinda ya samu babanshi ya sameshi. Wato kar ɗanshi bai gaji mulkiba kamar yadda sarautar ta tsallake babanshi ta dawo kanshi. To shinefa ya tura ɗan shi Sadik wuraren sauran sarakunan ƙasar, cewa zaiyi murabus zai bawa Sadik mulkin. To dama bisa ƙaida dole sai sarakunan sun yarda. Cikin Sa'a kuwa duk sarakunan suka yarda sukasa hatimin amincewa a takardun. To a kan hanyar dawowanshi ne kuma Allah yayi mishi rasuwa. Wannan abu yayi masifar tada hankalin Sarki Bala. Da mahaifiyarsa Gimbiya Salame, da kakarsa Gimbiya Falmata. Saboda wannan pain ɗin mutuwar ɗan nasa, shene ya tattara yaranshi mata kab ya Aurar dasu. Harda ƴar shekara takwas duk ya kwashesu ya aurar. Sabida wai baya son ya mutu baiga aurensu ba. Ya musu aure ya kuma basu sarauta. Suka zama hakimai." Cikin sanyi Shatu tace. "Tirƙashi duk wannan don son mulki ne?". Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Uhum ai akan sarauta babu abinda ba'ayi sabida matsalar sai kowa yace shi ɗan sarkine zai gada. Sabida in basu gadaba sarautar tabar hannunsu, Shatu Sarauta masiface a zuciyar masoyansa da zasu iya komai a kanta." Kai Shatu ta gyaɗa tare da cewa. "To Ummi ina jinki". Gyara zama tayi tare daci gaba da cewa. "To in takai ce miki a ƙarshe dai Joɗa shiya zama sarki wanda shine ɗan ƙaramin a ahlin Sule. A lokacin ne kuma sunan jihar nan ya dawo Ɓadawaya sabida. Nunawa duniya ba haka bane duniya Allah zai iya baka zai iya hanaka. Masarautar Fulɓe kuma ta zama masarautar *JOƊA.* Sabida sunan sarkin kenan. Kuna ya zama adalin sarki mai son baƙi duk inda baƙo yazo zai wuce. Sai Sarki Joɗa ya bashi wurin zama yace mushi Joɗa wato zauna ga wurin zama kayi kasuwanci kayi kiwo ki ciya ka ciyar kasha ka shayar." Shiyasa Jihar Ɓadamaya tayi zarra da tarin ƙabilu sabida son baƙi da basu muhallin zama a wancan lokacin kawai fili za'a yanka a baka ka zauna in Kai baƙone To babban ɗan Joɗa shine Bubayero wato kakan Lamiɗo. Bayan Joɗa ya rasune Bubayero ya hau kan karagar mulki masarautar Joɗa. Ahlin Gimbiya Falmata kuma suna yaɗuwa suma buri da kwaɗayin sarauta na jiƙa a ransu duk burinsu suga yadda sarauta zata dawo ɗakinsu. To koda Bubayero zaiyi murabus ya bawa ɗansa Nuruddeen mulki sai ya aurawa ɗansa yar bappan shi jikar Madu ɗanshi. Sukayi aure aka naɗa Sarki Nuruddeen da matarsa yakura. Bayan anyi aurene da shekara biyu. Ya auro wata ƴar masarautar su Gimbiya Sumaye. To itace tazo ta haifi Lamiɗo. Ita waccar bata taɓa haihuwa ba. To shima Lamiɗo sai ya auro yar masarautarsun Gimbiya Sumaye, wato Gimbiya Aminatu a matsayin matarsa ta biyu. To Galadima da kike gani yanzu bappan Lamiɗo ne ɗan autan su marigayi sarki Nuruddeen. To shi kuma Lamiɗo da aka bashi mulki sai aka aura mishi yar zuriyar Gimbiya Falmata itace uwar gida. Ta haifi Baba Basiru da Baba Nasiru da kuma Baba Kamal da kuma babban yayansu Marigayi Auwalu. Sai Dr Aliyu shi kuwa mamanshi daban itama ta rasu su biyu ta haifa da Gimbiya Surayyah. To Mamansu Baba Nasiru. Yanzu haka tana raye amman ta haukace babu mai shiga Side ɗinta, sai Lamiɗo da yaranta. Duk wanda yaje sai tace zatayi duka, ita da bakinta take bayanin Abbansu Sheykh da Gimbiya Aminatu da Gimbiya Aisha tayiwa asiri ya dawo kanta. Galadima da yaga ya tsufane kuma baida ɗa namiji da zai gajeshi shine. Yacewa Lamiɗo ya naɗan babban ɗan shi Auwalu mijin Gimbiya Saudatu a matsayin Galadima. To bayan ya naɗa shi da shekara biyu ne, ya rasu. To sai ya naɗa Ya Jafar ɗin nan da kike gani a matsayin Galadiman Masarautar Joɗa. Lokacin lafiyarsa lau yadda kikaga Sheykh haka yake da ibada addini ilimi nitsuwa tausayi. Kwananshi goma a kan mulkin washe gari za'a naɗa shi ne, ya dawo haka babu mgna sabida wani babban ibtila'i da tashin hankalin ɗaya samemu. Kuma a lokacin an kusa amishi aure sabida sarautar da za'a bashi. To wannan shine babban mafarin hargitsi da kitimurmurar dake masarautar Joɗa a yanzu. Dan ranar da Jafar ya zama haka akwai babbar masifar data fi wannan muni daya faru a masarautar Joɗa. Shine abunda yayi masifar girgiza mutane. Lokacin Sheykh yana saudia yana karatu a jami'atul Madina. Hankalin Hajia Mama yayi masifar tashi tayi ta suma tana sakewa Umaymah kuwa da Sitti mutuwace kawai da basuyi ba, dan baƙin ciki da tashin hankalin ɗaya samemu. To kuma tun daga nan sai duk magautan suka dena kiyayyarsu kansu Jafar da ƙannensa. Koda Jabeer yayi karatunshi a can yayi digirinsa na biyu da PHD dinsa duk a can. Wani sabon tashin hankalin da Jabeer ya dawo Lamiɗo yabashi mulkin GARKUWAn FULANI, nanfa Magauta sukace zasu mutu. Dan ma mulkin na gefen yaya mata aka bashi shine abin ya ɗanyi sanyi. To kuma ingiza gabar sunga ɗawisun masarautar Joɗa tayiwa Jabeer abinda sai sarki takeyiwa. To kinji lbrin a taƙaice sai a hankali zaki gane komai in kina bin komai a hankali." Numfashi mai sanyi Shatu ta sauƙe tare da cewa. "Ummi wacece Gimbiya Aisha?". Da sauri Ummi tace. "Baki santaba". Da sauri Shatu tace. "Toh ina take?". "Bata nan". Ummi ta bata amsa a gajarce. Da sauri Shatu tace. "Ta rasu ne?". Cikin zubda hawaye Ummi tace. "Bamu san halin da take cikiba shine babban burin Sheykh a duniya, sanin inda take". Cikin sanyi Shatu ta kauda waccar tambayar dan ko Ummi bata amsa mataba ita ta gane matsayin Gimbiya Aisha. Haka yasa a hankali tace. "Allah ya baiyana ta. Ya cika mishi burinsa." Amin Amin Ummi tace tana sharce hawaye. Cikin nitsuwa Shatu tace. "To Ummi mene kuma banbancin mulkin gefen yaya mata dana maza". Cikin jin bacci tace. "Da safe ki tambayi Hibba ko Jamil zasu gaya miki, yanzu jeki shiga dare yayi bacci nakeji". Da haka tatashi taje ta shiga ta fahimci a duddunƙule Ummi ta bata lbrin Sarkin yanzu da matsalar dake faruwa. Washe gari da safe, bayan sunci abinci. Ummi ta miƙe dan taje tayi walaha, Hibba kuma ta tafi sashin Juwairiyya da tun jiya da safe bata sake shigowa ba. Jamil ne ya shigo neman Jalal da sauri tace. "Uhum yauwa Jamil zo mana". To yace kana ya dawo ya zauna. Cikin nitsuwa tace. "Dan Allah in ɗan tambayeka mana". Jingina yayi da jikin kujera tare da cewa. "To ba matsala Allah yasa na sani". Wayarta ta ajiye kana tace. "In sha Allah ka sanima. Wai menene banbanci sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa mata, dana gefen ƴaƴan ƴaƴa maza". Dariya yayi mai sauti tare da cewa. "Uhumm kema kin shiga Masarautar Joɗa cikin kitimurmuran yanayi ko kin ratso cikin ahlin da ba'a sonmu, kin fara fuskantar ƙalubale ko". Tashi yayi yaje ya sha ruwa kana ya dawo ya zauna ya fuskanceta da kyau a hankali yace. "Banbancin tsakanin sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa maza da gefen ƴaƴan ƴaƴa mata. Shine kamar haka. 1 Galadima (must be a prince ) 2 Chiroma (crown prince)first born to the king 3 Tafida ( most be a prince ) 4 Santuraki (must be a prince ) 5 Sarkin dawaki ( prince) 6 Ɗan buram 7 Ɗan isa 8 Ɗan lawan 9 Durbi 10 Wambai 11 Turaki 12 Ɗan maje 13 Yarima 14 Ɗan iya 15 Majidadi. Dan ɗagowa yayi ya kalleta tare da saƙe yatsunshi da yake naɗewa yana irga mata yace. "Wannan duk royal family ne mostly biological sons din sarki ne wasu kuma jikokin sarki kuma kunne biyu sukeyi a rawunansu sabida su ƴaƴan sarki ne ko kuma iyayensu ƴaƴan sarki ne. Kanta ta jinjina mishi alamun ta gamsu tana kuma ganewa. Shi kuwa a nitse yaci ga da ce mata. "Anan ake samin chief of staff da kuma senior councillor kamar galadima mostly shine senior councillor shine elders in royal bloodline ana samun galadima yapi sarki a shekaru kuma shi ake bama riqon gari in sarki bayanan. Sannan duka anan sunayen dana irga miki da fari kowa zai iya yin sarki tunda daga ɗan sarki sai jikokinsa na gegen ƴaƴa maza, shiyasa su kunne biyu sukeyi a rawanunsu. A hankali ya kalli Ummi data fito da Hijabi a jikinta ta zauna kusa da Shatu. Tare da cewa. "To kinji bayanin ƴaƴan ƴaƴa maza na sarki." Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Na gane kuwa Ummi, yanzu gaya min na ƴaƴan yaran sarki mata kuma inji". Gyara zama Jamil yayi tare da cewa. "To sukuma sarautar gefen yaya mata sune. 1 Madawaki 2 Garkuwa 3 Makama 4 Majidadi 4 Waziri 5 Matawalle 6 Sarkin yaki 7 Magayaki 8 Jarma 9 Talba 10 Shatima 11 Ubandoma 12 Ɗan kadai 13 Magajin gari 14 Ɗan masani 15 Barma. Ɗan sauƙe numfashi yayi tare da ci gaba da cewa. All of these hakimai ne wanda sukeyin kunne daya a rawunansu. Kuma wasu a cikinsu jikokin sarki ne ta bangaren mamansu, mum dinsu ce yar sarki kamar dai mu a Masarautar su Sitti ko za'a bamu mulki iya waɗannan za'a bamu kinga baza suyi kunne biyu ba shiyasa suke kunne daya amma suma hakimai ne manya kuma yan majalissar sarki also akwai kin makers a cikinsu. Sai dai su cikin jerinsu babu wanda zai gaji sarautar sarki kamar dai mu yanzu bazamu gaji Jadda ba da masarautar gargajiyace sai dai da yake nasu na musulcine, in Kuma a masarautar Joɗa ne sunayen da na ƙirga miki na forko cikinsu za'a iya bamu, domin yanzu GARKUWA da aka bawa Hamma Jabeer matsayinsa yafi ƙarfin hakan shiyasa Magauta basu damuba." Ya ƙarishe mgnar da cewa kin gane ko Aunty Shatu, Kinga shiyasa da aka bawa Ya Jafar Galadima cikin kwana goma aka sabauta manashi. Ana tsoron kada tarihin Sarki Bala da mahaifinshi Madu ɗan Sarki Sule ya maimaita kanshi a kan ƴaƴan ɗakinmu. Shiyasa da aka bawa Hamma Jabeer Garkuwa mu bamu soba. To sauƙin abin ma ɗaya ne da suga sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa mata aka bashi duk da shi jikan ɗan ɗan ɗansa namiji ne". Ajiyan numfashin tayi kana a hankali tasa hannunta ta tallaɓe habarta, cikin alamun nisan zango na tunani da nazari. A hankali Ummi ta matso kusa da ita cikin sanyi da kuma yin ƙasa da murya tace. "Shatu ni kuma in tambayeki wani abu mana". Kanta ta jujjuya a hankali ta buɗe baki tace. "Na sani! Ummi nasan abinda zaki tambayeni! Zakimin tambaya ne kan menene yasa da na shiga ɗakin Yah Sheykh na suma na fita haiyacina, ko?". Ta ƙarishe mgnar wasu hawaye masu ɗumi suna kwaranyo mata a fuskarta. Cikin sanyin jiki ganin Ummi ta gyaɗa mata kai alamar eh. Jamil ma jiki a mace ya zuba mata ido. Tafin hannunta tasa ta sharce hawayenta murya na rawa alamun tana son danne kukanta tace. "Ummi ɗakin Yan Sheykh ɗakine mai cike da hatsara a rayuwarshi. Tabbas dan Allah yayi shi mutun ne mai ibada da imani da kekyawar zuciya, da yawan ambaton sunan Allah da zama da al'wala wlh da badan wannan nagartar da Addu'o'in da suka zame mishi abokan rayuwa suka zame mishi GARKUWA ba, kamar yadda Manzon Allah yace. "Addu'a'u saiful muminin da tuni sun kasheshi sun sabauta rayuwarshi. Ummi ban san komai ba kan masarautar Joɗa. Amman dan al'farma Annabi da darajar Umaymah. Zan taimaki Yah Sheykh iyakar iyawata. Zan taimake shi akan abinda Allah ya bani ikon gani". A hankali Jamil ya zamo ya zauna a ƙasa. Yana mai jin tsikar jikinshi na tashi. Itama Ummi zamowa tayi ta zauna ƙasa. Hakama Shatu a hankali ta zauna gaban Ummi hannunta tasa. Ta kamo hannun Ummi cikin muryar kuka tace. "Ummi ku yarda dani, ku bani haɗin kai, zan tone duk abun cutarwa dake ɗakin Yah Sheykh. Bazan cutar dashi ba, zan taimake shi kamar yadda Bappa na yake bani umarni duk sanda mukayi mgn dashi. Ummi keda Jamil ina buƙatar taimakon ku. Amman kafin nan ki gayawa Umaymah in ta amince, sai inyi aikin amman kada a gayawa Yah Sheykh dan bazai yarda ba." Cikin tsoro ido cike da hawaye Ummi tace. "To Shatu me zancewa Umaymah, me kika gani a ɗakin har ya firgitaki yasaki suma?". Cikin kuka tace. "Ummi kada ku tsaya bincike a kaina. Ni dai ku yarda dani bazan cutar da kowaba na cikin Masarautar Joɗa sai wanda ya cutar da kanshi Ummi bamu da sauran lokaci mai tsawo fa, komai zai iya faruwa da Yah Sheykh". Cikin tsoro da firgici Jamil yace. "Ba matsala mun yarda dake, ni yanzu taimakon me zan miki?". Cikin sauri ta share hawayenta tare da juyowa ta kalli shi kana tace. "Yauwa Jamilu zaka samo mana mai saka tayis, yazo da katon ɗaya na tayis ɗin irin na bedroom ɗin Yah Sheykh sak da sak. Sai kuma kayi ƙoƙarin mu samu ya Sheykh in ya fita ya wuni sai dare zai dawo". Cikin sauri yace. "Tayis da mai sawa ba matsala, batun in ya fita sai dare ya dawo kuma inaga. Sai zuwa jibi ranar ne zaije asibitin gwamnatin Genaral Hospital. To in yaje can wuni yakeyi wani lokacin sai dare zai dawo". Cikin gamsuwa da hakan tace. "To ba matsala. Ummi ke kuma ki kira mana Umaymah ki sanar mata, muyi abun da saninta." To Ummi tace kana a wurin ta kira Umaymah tayi mata bayani. Ba wani neman ba'asi tace. "A barta Ummin Jabeer na amince, tayi duk abinda ya dace a kan mijinta da yayanshi da ƙannenshi dama duk wani abu nashi". Cikin jin daɗi ta jinjina kai lokacin da take jin mgnar Umaymah. Wani irin dogon numfashi taja mai ƙarfi sai gata ta tafi luuuh kan...! Wasa farin girki? Shatu kadafa allura ta tono garma. By *GARKUWAR FULANI* Ta ɗan ja tayi sama da bakin ƙafan wonɗon wanda yake na robane bakin a tsuke yake. Da sauri cikin tsoro da rawan jiki ta saki robar. Pat ya fetti a jikinshi. Ganin ya motsa. Shi kuwa Sheykh Jabeer wani sassanyan numfashi ya ja mai tsawo tare da fesoshi a hankali kana, ya mirgina a hankali ya juya ya kifu cikin kasalan nauyin bacci ya ɗaura kanshi bisa cinyarta, Kana ya ware hannayenshi da sukayi ɗan tsami sabida pillow'n da yayi dasu. Ware hannayen yayi tare da miƙarar dasu. Ya zama tana tsakiyar hannunshi kana kanshi na kan cinyoyinta. Haɗe hannuyen nashi yayi ya sarƙafe yatsunshi wuri ɗaya, ya zama ya zagayeta tako ina yayi mata ƙawanya. Ya cusa hancinsa cikin mayafinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinta dana kayanta. A hankali ya kuma gyara kwanciyarshi da kyau kana yaci gaba da sauƙe sassauƙan numfashin. Ita kuwa Shatu wani masifeffen tsalle da bugu zuciyarta keyi tamkar zaiyi tsalle ya fito woje. Gaba ɗaya ida nunta kan sumar kanshi ta zubasu. Tare da kallon tattausan sajenshi dake kwance lib-lib a gefen fuskarshi. Wani sassanyan numfashi ta sauƙe tare da lumshe idonta cikin zuciyarta tace. "Allah shi ƙara". Sai kuma tayi sauri ta buɗe idonta tana tambayar kanta. "Allah shi ƙara me ɗin? Ya ƙara ruggumata ko meyeye". Cikin kauda zancen a ranta ta ɗan muskuta dan janye jikinta. Amman sai ta ji ya riƙeta gam-gam, yana ƙara cusa kanshi cikin jikinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren jikinta. Cikin tsoro murya na rawa a hankali tace. "Yah Sheykh!". Karab sautin muryarta ya ratsa kunnuwanshi. Sai dai ko motsi baiyi ba, A hankali ta kuma ce. "Yah Sheykh! Yah Sheykh!!". Shiru babu amsa sai numfashin da yake fiddawa a hankali yana kuma shaƙan ƙamshin jikinta. Cikin sanyi ta ɗan ɗago hannunta a hankali tasa taffin tattausan hannunta, ta ɗan rinƙa buge gefen fuskarshi a hankali a hankali tanayi tana cewa. "Yah Sheykh! Yah Sheykh! ! Tashi wai Affan dasu Yusuf sunzo, shine Affan yace inzo in tasheka". A hankali ya buɗe idonshi, Yanayin yadda take ɗan marin gefen fuskarshi da hannunta wanda ke ɗaure da agogo. A hankali ya ɗago hannunshi ya ɗan kan hannunta ya kamoshi ya riƙe, cikin tsoro ta fara kiciniyar kwace hannunta, Sai kuma tayi zuru, jin ya ja hannun da ɗan ƙarfi ya kawoshi dai-dai saitin fuskarshi. Idonshi ya zubawa yatsun hannunta da kullum in ya gansu da jan lalle yake tuna mishi baya. Da sauri tace. "Wash Allah na". Jin ya murɗa hannun ya juyo da fuskar agogon inda zai gani. Ƙarfe biyu da miti arba'in da ɗaya. Du-du baccin 40 minutes yayi tazo ta tasheshi. "Harda zuba min maruka". Ya faɗa a ransa. Ita kuwa kan tattausan suman ta ajiye sinsiyar hannunta. tana jin kanta na sara Especially in ta kalli saitin ƙasan gadonshi." A hankali ya sake hannunta kana ya yunƙura ya juya rigingine, ya fuskanci sama, ita kuma tana zaune tana kallon ƙasa hakanne yasa suna fuskantar juna, cikin wani irin yanayi ya zuba mata ido na wasu sakanni. Shigarta tayi masifar mishi kyau. Kodan tasa kalan kayan da yafi sone. Cikin muryar bacci yace. "Shine harda dukana? Meyasa ne ku mutanen garincan kuke son dukan mutun da kallon jikinsa?". Cikin tura baki tace. "Cinyana, nagaji kanka nauyi". Bai janye idonshi a kantaba ya yunƙura ya tashi zaune tare da juyowa ya fuskanceta. tanƙwashe sawunshi yayi tare da cewa. "Me zaki kalla a jikina? Woto Kin zama kamar ɓarauniya ko? Me kike son gani? Wani abu kike sone?". Cikin tura baki tace. "Nifa tada kai a bacci kawai nayi". Hannunshi yasa ya riƙo hannunta, yatsunta ya zubawa ido, cikin wata murya mai sanyi yace. "Masha Allah, kinyi kyau." Wani irin sanyi taji kalmar tashi tasa mata a ranta, ido ta ɗan ɗago ta kalleshi. Shima ita yake kallo, ido ya lumshe jin sautin zazzaƙar muryarta a hankali tace. "Nagode". Tonƙoshe kansa yayi bisa kafaɗa kana hankali ya sake hannun nata. Fuskarta ya kalla tare da taɓe baki yace. "Waya koya miki irin sa lalle Mammeyyyyy nah!? Dan tafi ko wacce mace iya lalle". Cikin sanyi da nazartar yadda ya kira sunan Mammeyyyyy da yadda lokacin ɗaya idonshi suka fara sheƙin tsastsafo da zafafan hawayen da ba zubowa zasuyiba. Cikin son gano meke cikin zuciyarsa tace. "Ummeyy nah ce ta koya min tun ina ƙaramar". Yatsunta ya jujjuya kana ya miƙe tsaye. A hankali ya juya ya nufi bathroom sabida baya son ta hango wutar ƙunar dake ransa. Ita kuma binshi da ido tayi, tare da langoɓar da kanta tana kallon sharabansa da gargasa yayi musu ƙawanya. A haka ta shiga wani nazarin tana mai maimaita sunan da taji ya kira da cikekken so shaƙuwa ƙauna tausayi rauni shogoba *Mammeyyyyy.* Ta maimaita sunan a fili. Shi kuwa Sheykh Jabeer al'wala yayi kana ya fito. Yayi mamakin ganinta a zaune bata fita ba. Hararanta yayi ganin yadda taketa kallonshi. Jallabiyar shi ya zura, kana yasa al'kyabbar, tare da sa Hiraminshi. Sannan ya fesa turare. Duk inda yayi tana binshi da ido. Wayarshi da yafi yawan riƙewa ya ɗauka ya zura a al'jihunsa. Sannan ya nufi bakin ƙofa inda takalminshi suke yana cewa. "Wannan kallon maitan fa". Da sauri ta janye idonta. Cikin daƙilewa yace. "Kada ki cinyeni da ido fa. Bana son kallo, ko kina bina bashine?." a hankali ta miƙe tare da lumshe ido ta biyu bayanshi. Tana gyara mayafinta tare da cewa. "Ni ban kalleka ba". "Uhummm." yace a taƙaice. Kusan a tare suka fito. Yana gaba tana bayanshi, Suka fito tsakiyar falonshi. Tsayawa ya ɗanyi ya gyara masaƙalin Al'kyabbar tashi. Shiyasa ya zama a jere suke tafiya tana gefen damanshi. A haka suka fito cikin corridor'n. Suka doshi Falon cikin kwarjini da dacewa da juna sai ƙamshi da sheƙi zallan kyau sukeyi. Da Sallama a bakinshi suka kutsa kai cikin falon. Wani irin dariyar jin daɗi Affan da suke can Dinning area yayi, suna cin abinci da Ummi ta matsa suci. Wani irin murmushi Yusuf da Aryan ma sukayi tare da miƙewa suka nufi inda uban gidan nasu ke tsaye da kekyawar tauraruwarshi mai haskawa. Affan kuwa wayarshi ya zaro yana kekkebta musu hoto tare da cewa. "Ga amarya, ga ango, suna carabki da zallan kyau da ƙamshi". Murmushi sukayi dukansu, ita kuwa Shatu tana tsaye gefenshi. A haka su Affan suka iso. Suna Isa Affan ya ruggumeshi shima Sheykh ruggumeshi yayi tare da make ƙeyarsa. Da sauri ya janye kanshi tare da cewa. "Wayyo Allah na yanzu Hamma Jabeer na girma harda yaran nawama ban wuce dukaba". Murmushi yayi tare da, Ruggume Yusuf da Aryan Allah ya sani yana masifar son yaran nan har gobe bashi da ɗalibai sama dasu yana sonsu so na musamman, duk sanda ya gansu yakan tuna ƙuruciyarsu tun suna yan shekara goma sha biyar-biyar yake tare dasu shi ya horas dasu. Yana tura irin tarin ƙalubale da suka fuskanta a gasar Polo da kuma irin nasarorin da suka samu Especially Yusuf nashi yana tuna yadda yaran suke sheƙiyanci in sun haɗu, yana jinsu tamkar su Jamil. Cikin murmushin ya shafa kansu tare da cewa. "Sannunku da zuwa". Cikin jin daɗi sukace to. Bisa kujera ya zauna su kuma suka zauna a ƙasa a gabanshi kan carpet. Ita kuwa Shatu a hankali ta juya ta nufi kitchen ganin Ummi ta nufi can. Hibba kuwa na gefensu tana gayawa su Jalal ga Ya Affan fa. Da gefen idonshi ya bita da kallo. Har ta ɓacewa ganinsa, Allah ya sani yana son abu blue baya iya cire idonshi kan abu mai kalar shiyasa yake jin baya gajiya da ganinta, da zai samu kada tayi nesa dashi, dan tayi mishi kyau sosai farar fatarta ta fito fes kamar balarabiya ji yake tamkar ya bita duk inda tayi. Cikin murmushin ya kalli Aryan yace. "Aryan Ina su Yusuf ƙaramin". "Alhamdulillah suna lfy Malam". Kai ya jinjina tare da cewa. "Masha Allah". Sai ya kuma kalli Yusuf yace. "Ina mai sunana baka zomin da shiba". Murmushi Yusuf yayi tare da cewa. "Malam baka tambayi Aryan ƙaramin ba da yakeso ya zama kamarka sai ka tambayi mai sunanka". Dariya sukayi kana yace. "Ayyah my Aryan, sun kusa tafiya ai in sha Allah Jami'atul Madina zaiyi karatunshi". Da sauri suka juyo suka kalli Jalal da Jamil da suka shigo da sauri. Ruggume Affan sukayi suna cewa. "Oyoyo ya Affan". Hannu ya basu suka tafa kamar sa'ao',insa ne su. Cikin dariya yace. "Tun ɗazu nake kiranku bakwa ɗagawa. Nace waɗannan ana can cikin hayani ". Murmushi Jamil yayi tare da miƙawa Yusuf hannu wanda ke cewa. "Oh wato Affan kawai kuka gani mu ko oho ko". Cikin ɗan sakin fuska Jalal yace. "Afwan Hamma Yusuf ya Aunty Zahra da Mama". "Suna lfy. Sun gaidaku". yace tare da bashi hannun. Kana suka gaisa da Aryan. Sannan suka miƙe sukace bari suje wurin Aunty Mami. Cikin dariya Affan yace. "Eh kujema kuzo da ita taga matar babban yaya". Da sauri Jamil yace. "A a ka kawota da kanka dai". Ya ƙarshe mgnar suna fita. Su kuwa cikin yin ƙasa da kai Yusuf yace. "Uhum dama Malam zamu ɗan shiga wasan daba ne in batsala". Murmushi mai faɗin Sheykh yayi tare da cewa. "Wato ku dai har yanzu baku girma da batun doki ba". Shiru sukayi sai Affan ne yace. "Tab Yusuf kuma da in ya ga doki bai hauba jikinshi har rawa yakeyi". Murmushi Sheykh yayi kana yace. "To muje muyi salla. Tukun tunda sai anyi sallan la'asar za'a fara ko". To sukace tare da miƙa ganin ya miƙa dan tuni uku da kwata ta wuce. Affan ne ya kira Ummi tare da cewa suzo zasu tafi. A tare suka fito kitchen. Sabbin kuɗi rafa yan dubu-dubu Yusuf ya miƙawa Hibba ƙulli ɗaya dubu ɗari kenan yace. "Gashi miƙa wa Ummi ta raba muku." Affan ma ya basu. Hakama Aryan. Hibba sai tsalle take tana cewa. "Yessss my brother's Allah ya ƙara buɗi Amin Amin sukace kana suka juya zasu fita. Cikin tsare girma Shatu tace. "Mun gode, a gaida gida". Gida zaiji sukace kana suka fita suka tafi. Suma su Ummi wucewa sukayi yin al'wala. Ana idar da salla kuwa aka fara hawan daba, hawan sarki dama duk sauran shagulgula na gidajen masarautun gargaji yayin wurin taron bikin salla. MASARAUTAR Joɗa ta cika tayi maƙil da bani Adam. Haka dai akayi taron lfy aka tashi lfy sai kuma gobe in Allah ya kai rai. Washe garin ranar da sassafe. Sheykh ya tafi asibitinshi. Ko karyawa baiba. Sai kusan sha ɗaya ya dawo da alamun yunwa da gajiya tare dashi. A falon ya zauna suna gaisawa da Ummi dan basu gaisaba ya tafi daga masallacin can ya wuce. Ummi kuwa tasa Shatu ta kai mishi breakfast ɗin shi da yanzu kam in yacima ya zama lunch ne. Hibba kuwa na can ɗauki tana ƙenƙesa ado. Cikin isa da ƙasaita Gimbiya Saudatu ta shigo tsakiyar falon babu ko sallama. Haɗe fuska Sheykh yayi tare da cewa. "Wannan banzan ɗabi'a na arnatakun baya, dan ko arna yanzu suna cewa konkon, mutun kamar shanu ko mahaukaciya". Cikin isa ta iso tsakiyar falon. Dai-dai lokacin kuma Shatu ta fito falonshi. Cikin shigar doguwar riga mai ruɓi biyu. Kanta ta ɗago ta kalli Shatu kana ta kalleshi cikin yin dariyar mugunta tace. "Eh kam tabbas tunda ka auro mahaukaciya dole kasan hali da ɗabi'un mahaukata ai. Zuwa gaba kaɗan kaima zaka fara ihu da kuka da sume-sume irin na wannan al'janar fulanin daji daka auro ɗin". Cikin tarin mamaki Ummi ta kalli Shatu ta kuma kalli Hibba da yanzu ta fito, cike da al'hinin ta yaya taji wannan batun ya fasa Masarautar Joɗa yes in dai Gimbiya Saudatu taji to ai shike nan kowa ma zaiji. Shi kuwa Sheykh ba gane inda soki burutsunta ya nufaba yayi. Ita kuwa cikin watsa musu kallon ku sakarkaru ne tace. "Kuna mamakin ta ina naji, cewar ji shekaran jiya iwar haka dai wannan matar tashin tana yashe a sume da ido a wulkice tana ƙarkarwa farfaɗiya kamar mazari ne. To ai Ni duk wanda yaci tuwo dani miya yasha. Inada tawa a cikinku duk motsinku ina dashi a tafin hannuna. Nan gaba kaɗan zamu samu riƙeƙƙiyar mahaukaciya a masarautar Joɗa". Cikin tsuke fuskarsa yace. "Yanzu ma ai muna da su mahauka ta kam, ke ɗin me banbancin ki da zararrun". Shiru yayi ganin yadda Shatu keyin taku a hankali cikin isa ta nufi gaban Gimbiya Saudatu. Ummi da Hibba kuwa miƙewa tsaye sukayi. Shi kuwa Sheykh gyara zamanshi yayi tare da ɗaura ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya. Ita kuwa Shatu a hankali ta isa gabanta. Ido ta zuba mata tare da yi mata kallon tara saura kwata. Cikin dakkeyar Muryar rashin tsoro tace. "Toh *Bushiya* mai mugun baya, Bushiya mai bayan ƙayoyi masu kama da allurai, ki buɗe idonki da kyau ki kalleni Ni AYSHA ALIYU GARKUWA ba sa'ar yinki bace uwar mahassadan duniya, in kina cin ƙasa to tabbas ki kiyayi ta curi, ki bar min mijina ya sarara ki far masa rayuwa, ɗan shi ba sa'an yinki bane ki bar min mijina ya huta baya son ihun nan da kikeyi mishi, zan kuma iyan komai dan ganin na kauda dukkan abinda baya so." Wani irin daɗi ne ya rufe zuciyar Ummi da Hibba Sheykh kuwa ƙafarshi kawai yake kaɗawa yana mai binta da wani irin kallo mai tarin ma'anoni kalmarta ta *Mijina* yake ji tana sa duk wani hudan gashin jikinsa na amsa amon kalmar yana ratsa jikinshi da zuciyarsa haka yasa bai san sanda wani yalwataccen murmushi ya subce mishiba, tabbas Shatu akwai ƙarfin hali. Ita kuwa Gimbiya Saudatu tsuru tai da ido. Itako Aysha cikin karsashi tace. "Na lura ke dabbace, sam bakya gane yarukan mgna na bani Adam, kinfi son sai an miki irin yarukanku na dabbobi. Kina tsaye da farin yawu a bakinki kina zubda jini. Yayinda wasu ke bayanki da jini a bakinsu suna fidda farin yawu. Sokuwar rama mai tsami. Ni nan da kike ganina da idona tar a buɗe na shigo Masarautar Joɗa, kada ki ganni haka Ni ɗan hakine da zaki iya renawa amman tabbas zan tsole idanun magauta ruwanshi ya tsiyaye. In kin san fullanci to. *MIN MI KURORI CITTA NFAMƊA NHEYAH* NI ```DAKKEN YAJIN BORKONE INYI KAƊAN IN KUMA ISHI MUTUN``` Ki tsumayeni tabbas zanyi daka inyi tankaɗe inyi rairaya a masarautar Joɗa!. Ke ko kallo baki isheni ba domin bata ke akeyi ba da manyan Magauta nakeyi. Ja mugun bakinki ki fice min a gidana!". Rab-Rab. Jalal da Jamil dake da Jafar shigowa ne, suka tafa mata da hannu bibbiyu. Hakama Hibba. Ummi kuwa ƙasa tayi da kanta. Shi kuwa Sheykh ƙanƙance idonsa yayi yana kallonsu yana kaɗa ƙafa ya watsa idanunshi cikin na Gimbiya Saudatu yana mata kallon itama ta isheki. Aunty Juwairiyya kuma da tun ɗazu tana bakin ƙofar shigowa da sauri ta juya ta koma Side ɗin ta. Ya Jafar kuwa sai murmushi yake tare da dunƙulawa Shatu hannunshi kamar haka👍🏻 Wani irin juyawa Gimbiya Saudatu tayi tare da jan al'kyabbar ta ta fita. Har taje bakin ƙofa Shatu tace. "Ki riƙe kalmar mahaukaciya tabbas zakiga mahaukata a masarautar Joɗa zasu baiyana bila'adadin." Daga nan ta juya ta nufi Dinning area ɗin babban falon. Ita kuwa Gimbiya Saudatu ta juya ta fita. Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya sauƙe ƙafafunshi kana ya miƙa ya nufi falonshi. Haka nan yaji murmushi na tsubce mishi. Tabbas ya gamsu da ƙarfin halin Shatu da rashin tsoronta, sai dai yana jiye mata tuggun mutanen da bata san halinsu ba. Yana shiga yaci abinci kana ya shiga yayi wonka. Kana ya ɗauki wayarsa. Jalal, Jamil, Hibba, Ya Jafar, Shatu kuwa zama sukayi a falon cikin mamaki Ummi tace. "To wacece yar leƙen asirin Gimbiya Saudatu a wannan sashin? Ya akayi tasan abinda ya faru da Shatu? Waya gaya mata? Bayan in banda muyamu. Ni Juwairiyya, Hibba, Jalal, Jamil, Jafar. Wanda shi baya mgna, ita kanta Shatu bata san meya faruba batasan ya akayi ba. To waya fitar da wannan zancen a cikinmu?." Cikin gsky da gsky duk suka ce wlh babu wanda suka taɗawa mgnar Hibba harda ƙollarta tace. "Wlh ita ko Umaymah ma bata gayawa ba". To lallai kam akwai buƙatar bincike a tsakanin mu." Ummi ta faɗa tana mai cike da al'hinin abin. Ita kuwa Shatu uhummm. Kawai ta iya cewa tayi shiru bata ce komaiba. Haka dai suka tashi taron. Sheykh kuwa, number Umaymah ya kira bayan sun gaisa ne yace. "Uhumm Umaymah wai me kika sani ne ya faru da wannan yariyar shekaran jiya?". Cikin tsoro da son kauda batun Umaymah tace. "Wacce yarinyar kuma?". Fuska ya ɗan tsuke yace. "Waccar yarinyar dai". "To bata da sunane ita". Ta kuma ce mishi. Cikin gajiya da batun yace. "To ni ba sanin sunanta nayiba, baku gaya min sunanta ba." Wani irin murmushi Umaymah tayi tare da cewa. "Ban gane bafa Jazlaan". Hannunshi yasa ya ɗan shafi sajenshi. Yana mai son yasan meya sameta, meya faru da ita, shiyasa a hankali yace. "Yarinyar dai da kike cewa ɗiyarki!." Kai Umaymah ta jinjina tare da cewa. "Laah ni nama mance bamuyi mgnarba, ran sallane tayi aiki ta gaji tunda safe bataci komaiba to ashe tanada olsa shine fa, ta shiga ɗakinka zatayi maka shara ta faɗi ta suma, da kyar aka samu ta farfaɗo suanta kuma Aysha". Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa. "Shirme in banda sakarci da raki mutun ya bar kansa da yunwa da gajiyan aiki mutun har ya suma". Ya ƙarashe mgnar yana jinjina darajar sunanta a ranshi. Cikin jin daɗin bai tsananta bincike ba tace. "Akwai wani abune?". Gyara zamanshi yayi tare da cewa. "Wannan mahaukaciyar Gimbiya Saudatunce tazo take cewa wai taji lbrin ta haukace". Daga nan ya kauda zancen. A hankali ya miƙe yana riƙe da wayar a kunne shi. Dinning area ya nufa. Murmushi yayi gano tabbas akwai abinda Umaymah ke ɓoye mishi. Hannunshi yasa cikin zirin zirin igiyoyi masu duwatsu masu daraja sheƙin Daimond da sukayi Dinning area ɗinshi a madadin labule. A hankali yasa hannunshin kan na'urar CCTV camera dake liƙe a gefen inda yake ajiye key, wanda duk abinda za'ayi a falon zai gani. Cikin sanyi yace. "Uhummm Umaymah kiyi mata faɗafa, ta dena hawan ƙawara kan mutanen masarautar Joɗa, ta kiyayi kanta da faɗa da magautana zasu ilatata. Bata san komaiba a kaina ta tsaya matsayin baƙuwa Umaymah zafa suyi mata illa". Ya ƙare mgnar a hankali. System ɗinshi dake kan Dinning table ɗin ya jawo. kana yaja kujera ya zauna ya fara haɗa na'urar. Ita kuwa Umaymah a hankali tace. "To ya zatayi tunda ƙaddara ta kasantar da ita matsayin matarka, ko ita kurmace dole sai sun nemi yi mata illa sun sabautata. Dole kasata cikin jerin mutanen da ka zame musu GARKUWA a masarautar Joɗa, tunda ita dai matarka ce, amanarka kuma". Shiru yayi yana jinta yana mai kallon fuskar System ɗinshi date ɗin shekaran jiya ya shiga. ai kuwa Shatu ya fara cin karo da ita tana share falon da goge ko ina. Sai kuma lokacin da suka shigo ita da Jamil da Hibba suka nufi bedroom ɗin sa. A hankali yace. "Uhmmm Umaymah sai anjima zan kiraki". To tace kana ya katse kiran. Ido ya zuwa System ɗinshi. tsaki yaja karo na forko da yaji da ya haɗa na'urar da cikin ɗakinshi. Gashi yanzu baya ganinsu sai dai ihun Hibba, da fitowa da tayi da gudu ta kira Ummi da yadda suka shigo da Aunty Juwairiyya. Kanshi ya gyaɗa lokacin da yaga sun fito a hankali ya rufe System ɗinshi. Dafe kanshi yayi yana nazari. Ya dade a nan sosai kana ya koma ɗakin shi. Da dare misalin karfe sha ɗaya na dare saura. Shatu ta kalli Hibba dake konce tuni tayi bacci. Yasa ta miƙa a hankali ta nufi ɗakin Ummi. A bakin ƙofar ta tsaya a hankali tayi sallama. Cikin mamaki Ummi dake zaune bisa sallaya ta idar da shafa'i da wutri kenan taji sallamarta. Juyowa tayi tare da amsawa tace. "Shatu". A hankali tace. "Na'am Ummi". Cikin mamaki tace. "Lfy kuwa shigo mana". A hankali ta shigo tare da cewa. "Lfy lau Ummi, nazo wurinki ne." "To". tace tare da nuna mata wurin zama bakin gadonta. A hankali ta ƙaraso kusa da ita, Gabanta ta zauna kan sallayan cikin nitsuwa tace. "Ummi kiyi haƙuri ko zakiyi bacci na hanaki". Da sauri ta girgiza mata kai alamar a a. Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "To Alhamdulillah". Sai kuma tayi shiru. A hankali Ummi tace. "Kina buƙatar wani abune?". Cikin nitsuwa tace. "Uhum Ummi dama tambayarki nake son yi". Gyara zama Ummi tayi kana tace. "Ina jinki". Itama zamanta ta gyara a hankali tace. "Dan Allah Ummi in ba damuwa, dan Allah da Manzonsa ki sanar dani abinda Allah ya sanar dake a kan masarautar Joɗa mana. Ummi kaina na kullewa da mutanen masarautar Joɗa, ban gane banbanci su da dankantakarsu da kuma. Alaƙarsu ba". Wani irin dogon ajiyan zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa. "To Shatu ai kin gama komai tunda kika haɗani da Allah da Manzonsa. Kuma dama nace miki ki tambayeni duk abinda baki gane ba, zan gaya miki. To amman akwai wani abun sirrine garesu masarautar in na faɗa kamar cin amarsu ne, wani abun kuma nima kaina ban sanshi ba. Hannun Ummi ta riƙe tare da zubda hawaye tace. "Ummi gaya min yadda masarautar Joɗa take ko zan san irin zama da takun da zanyi da mutane da ɗaukar mataki kan abinda ke faruwa". A hankali Ummi ta gyara zamanta. Ta jingina da jikin gado. Kana itama Shatu ta gyara zamanta ya zama suna fuskantar juna da kyau. Cikin sanyi Ummi ta fara bata lbrin. *Masarautar Joɗa* tsohuwar masarautace. wacce tun kafin zuwan Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ƙasashen Afrika tana kafe da ƙafanta. Kuma masarautar Fulɓe ce tun a wancan lokacin. Lokacin da Shehu Usman Ɗanfodiyi ya iso nan ƙasashen hausa ya basu musulunci ya kafa tutocinsa tako ina tako wacce masarauta. A lokacin Masarautar Joɗa sunanta masarautar Fulɓe. Kuma lokacin Sarki Sule ne a kan karagar mulki. Baban Joɗa kenan wanda yake shi Joɗa shine kakan sarkinmu na yanzu wato Lamiɗo. A lokacin sarki Sule yanada ƙarfin mulki yana da mata huɗu ƙwar-ƙwara biyar. Allah ya azurtashi da arzikin yara a ƙalla sunfi hamsin a cikin matansa huɗu na aure. Akwai wata ɗaya da ake kira Gimbiya sumaye ƴar sarkin kal'anace. Gimbiya Sumaye inrin matannane da Allah ke jarabta da haihuwar wabi. Bima'ana tana haihuwa kuma yaran na rasuwa. A haka har ta haifi yara kusa goma kuma bata da rayeyye ko ɗaya. Cikin ƙwar-ƙwaran sarki Sule ne ɗaya ta ɗauki ɗanta na miji ta bata halak malak kwanan yaron uku a hannunta ya rasu. Wata cikinsu ta kuma bata still shima kwananshi uku ya rasu. A haka duk ƙwar-ƙwaran sarki Sule saida suka bata yara suna rasuwa. Daga nan uwar gidan Sarki Sule wacce take babarbariya ce. Tasa mata suna cikin wasa na tsakanin Fulani da bare-bari amman a zahiri da gaske takeyi. Gsky mai tafiya da wasa kenan. Sai ta sawa Gimbiya Sumaye suna da fillanci wai *Ɓadamaya* ma'ana wai duk wanda ya matso kusa da ita zai mutu, ko wanda ya bata riƙon ɗa kowa kwana uku ne mutuwa zaiyi. Kamar da wasa sunanta ya zama Gimbiya Ɓadamaya. Mutanen masarautar akayi ta mata izgili da habaici. Takan zauna tayi ta kuka. babu mai rarrashi dan ita masarautarsu nada nisa a lokacin kuma babu ko Radio bare waya. Anan Allah ya bata wani ciki ta haifi ɗan ta namiji. Akasa mishi suna Umar faruq. Sai Gimbiya Sumaye take kiranshi da Joɗa ma'anar Joɗa shine zauna. Da haka sai aka maida abun ba'a aka rinƙa kiran yaro da Joɗa. Allah cikin ikonsa ta yaye yaro lfy lau. Ta kuma haihuwa na goma sha biyu. Yariyar watanta biyar ta rasu, sai aka rinƙa mata dariya ana cewa saura *Joɗa* shima ya *Dilli.* Wato wai saura Joɗa shima ya *tafi.* Cikin ikon Allah kuwa ya raya Joɗa ya girma. Ya zama shine ƙarami cikin ƴaƴan sarki Sule kenan. Bayan wasu shekaru, sai Sarki Sule yace to shi zaiyi murabus, a cikin yayanshi yace zai naɗa babban ɗanshi Madu. Ɗan Gimbiya Falmata. Sai ko sauran ƴan uba duk suka tashi akece to sai ayi zaɓen manyan. To akwai ɗan Madu wanda yake mai ilimin addini dana zamani sunanshi Bala, sai ya shiga cikin masu neman mulkin ya kafa hujja da cewa. "Babanshi Madu jahiline dan haka a bashi shine ya dace da mulkar garin. Haka kuwa akayi aka ba Bala mulkin masarautar Fulɓe. Dole babanshi Madu wanda shine Magajin gari ya ƙaura ya bar garin. Tunda kinga bazai yiwuba ace yana mahaifinshi ya rinƙa serving ɗan shiba da baƙinsa ba. Haka dai Bala yayi mulki tsawon shekaru arba'in inda Joɗa kuma yake matsayin Galadima tunda ɗan tsohon sarki ne. To shi kuma Sarki Bala sai Allah ya azirtashi da tarin ya'ya mata ɗan shi na miji daya ne, Sadik. Ya bawa Sadik sarautan Sardaun. Bayan wani lokacin sai tsoro ke rufe Sarki Bala kada fa abinda ya samu babanshi ya sameshi. Wato kar ɗanshi bai gaji mulkiba kamar yadda sarautar ta tsallake babanshi ta dawo kanshi. To shinefa ya tura ɗan shi Sadik wuraren sauran sarakunan ƙasar, cewa zaiyi murabus zai bawa Sadik mulkin. To dama bisa ƙaida dole sai sarakunan sun yarda. Cikin Sa'a kuwa duk sarakunan suka yarda sukasa hatimin amincewa a takardun. To a kan hanyar dawowanshi ne kuma Allah yayi mishi rasuwa. Wannan abu yayi masifar tada hankalin Sarki Bala. Da mahaifiyarsa Gimbiya Salame, da kakarsa Gimbiya Falmata. Saboda wannan pain ɗin mutuwar ɗan nasa, shene ya tattara yaranshi mata kab ya Aurar dasu. Harda ƴar shekara takwas duk ya kwashesu ya aurar. Sabida wai baya son ya mutu baiga aurensu ba. Ya musu aure ya kuma basu sarauta. Suka zama hakimai." Cikin sanyi Shatu tace. "Tirƙashi duk wannan don son mulki ne?". Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Uhum ai akan sarauta babu abinda ba'ayi sabida matsalar sai kowa yace shi ɗan sarkine zai gada. Sabida in basu gadaba sarautar tabar hannunsu, Shatu Sarauta masiface a zuciyar masoyansa da zasu iya komai a kanta." Kai Shatu ta gyaɗa tare da cewa. "To Ummi ina jinki". Gyara zama tayi tare daci gaba da cewa. "To in takai ce miki a ƙarshe dai Joɗa shiya zama sarki wanda shine ɗan ƙaramin a ahlin Sule. A lokacin ne kuma sunan jihar nan ya dawo Ɓadawaya sabida. Nunawa duniya ba haka bane duniya Allah zai iya baka zai iya hanaka. Masarautar Fulɓe kuma ta zama masarautar *JOƊA.* Sabida sunan sarkin kenan. Kuna ya zama adalin sarki mai son baƙi duk inda baƙo yazo zai wuce. Sai Sarki Joɗa ya bashi wurin zama yace mushi Joɗa wato zauna ga wurin zama kayi kasuwanci kayi kiwo ki ciya ka ciyar kasha ka shayar." Shiyasa Jihar Ɓadamaya tayi zarra da tarin ƙabilu sabida son baƙi da basu muhallin zama a wancan lokacin kawai fili za'a yanka a baka ka zauna in Kai baƙone To babban ɗan Joɗa shine Bubayero wato kakan Lamiɗo. Bayan Joɗa ya rasune Bubayero ya hau kan karagar mulki masarautar Joɗa. Ahlin Gimbiya Falmata kuma suna yaɗuwa suma buri da kwaɗayin sarauta na jiƙa a ransu duk burinsu suga yadda sarauta zata dawo ɗakinsu. To koda Bubayero zaiyi murabus ya bawa ɗansa Nuruddeen mulki sai ya aurawa ɗansa yar bappan shi jikar Madu ɗanshi. Sukayi aure aka naɗa Sarki Nuruddeen da matarsa yakura. Bayan anyi aurene da shekara biyu. Ya auro wata ƴar masarautar su Gimbiya Sumaye. To itace tazo ta haifi Lamiɗo. Ita waccar bata taɓa haihuwa ba. To shima Lamiɗo sai ya auro yar masarautarsun Gimbiya Sumaye, wato Gimbiya Aminatu a matsayin matarsa ta biyu. To Galadima da kike gani yanzu bappan Lamiɗo ne ɗan autan su marigayi sarki Nuruddeen. To shi kuma Lamiɗo da aka bashi mulki sai aka aura mishi yar zuriyar Gimbiya Falmata itace uwar gida. Ta haifi Baba Basiru da Baba Nasiru da kuma Baba Kamal da kuma babban yayansu Marigayi Auwalu. Sai Dr Aliyu shi kuwa mamanshi daban itama ta rasu su biyu ta haifa da Gimbiya Surayyah. To Mamansu Baba Nasiru. Yanzu haka tana raye amman ta haukace babu mai shiga Side ɗinta, sai Lamiɗo da yaranta. Duk wanda yaje sai tace zatayi duka, ita da bakinta take bayanin Abbansu Sheykh da Gimbiya Aminatu da Gimbiya Aisha tayiwa asiri ya dawo kanta. Galadima da yaga ya tsufane kuma baida ɗa namiji da zai gajeshi shine. Yacewa Lamiɗo ya naɗan babban ɗan shi Auwalu mijin Gimbiya Saudatu a matsayin Galadima. To bayan ya naɗa shi da shekara biyu ne, ya rasu. To sai ya naɗa Ya Jafar ɗin nan da kike gani a matsayin Galadiman Masarautar Joɗa. Lokacin lafiyarsa lau yadda kikaga Sheykh haka yake da ibada addini ilimi nitsuwa tausayi. Kwananshi goma a kan mulkin washe gari za'a naɗa shi ne, ya dawo haka babu mgna sabida wani babban ibtila'i da tashin hankalin ɗaya samemu. Kuma a lokacin an kusa amishi aure sabida sarautar da za'a bashi. To wannan shine babban mafarin hargitsi da kitimurmurar dake masarautar Joɗa a yanzu. Dan ranar da Jafar ya zama haka akwai babbar masifar data fi wannan muni daya faru a masarautar Joɗa. Shine abunda yayi masifar girgiza mutane. Lokacin Sheykh yana saudia yana karatu a jami'atul Madina. Hankalin Hajia Mama yayi masifar tashi tayi ta suma tana sakewa Umaymah kuwa da Sitti mutuwace kawai da basuyi ba, dan baƙin ciki da tashin hankalin ɗaya samemu. To kuma tun daga nan sai duk magautan suka dena kiyayyarsu kansu Jafar da ƙannensa. Koda Jabeer yayi karatunshi a can yayi digirinsa na biyu da PHD dinsa duk a can. Wani sabon tashin hankalin da Jabeer ya dawo Lamiɗo yabashi mulkin GARKUWAn FULANI, nanfa Magauta sukace zasu mutu. Dan ma mulkin na gefen yaya mata aka bashi shine abin ya ɗanyi sanyi. To kuma ingiza gabar sunga ɗawisun masarautar Joɗa tayiwa Jabeer abinda sai sarki takeyiwa. To kinji lbrin a taƙaice sai a hankali zaki gane komai in kina bin komai a hankali." Numfashi mai sanyi Shatu ta sauƙe tare da cewa. "Ummi wacece Gimbiya Aisha?". Da sauri Ummi tace. "Baki santaba". Da sauri Shatu tace. "Toh ina take?". "Bata nan". Ummi ta bata amsa a gajarce. Da sauri Shatu tace. "Ta rasu ne?". Cikin zubda hawaye Ummi tace. "Bamu san halin da take cikiba shine babban burin Sheykh a duniya, sanin inda take". Cikin sanyi Shatu ta kauda waccar tambayar dan ko Ummi bata amsa mataba ita ta gane matsayin Gimbiya Aisha. Haka yasa a hankali tace. "Allah ya baiyana ta. Ya cika mishi burinsa." Amin Amin Ummi tace tana sharce hawaye. Cikin nitsuwa Shatu tace. "To Ummi mene kuma banbancin mulkin gefen yaya mata dana maza". Cikin jin bacci tace. "Da safe ki tambayi Hibba ko Jamil zasu gaya miki, yanzu jeki shiga dare yayi bacci nakeji". Da haka tatashi taje ta shiga ta fahimci a duddunƙule Ummi ta bata lbrin Sarkin yanzu da matsalar dake faruwa. Washe gari da safe, bayan sunci abinci. Ummi ta miƙe dan taje tayi walaha, Hibba kuma ta tafi sashin Juwairiyya da tun jiya da safe bata sake shigowa ba. Jamil ne ya shigo neman Jalal da sauri tace. "Uhum yauwa Jamil zo mana". To yace kana ya dawo ya zauna. Cikin nitsuwa tace. "Dan Allah in ɗan tambayeka mana". Jingina yayi da jikin kujera tare da cewa. "To ba matsala Allah yasa na sani". Wayarta ta ajiye kana tace. "In sha Allah ka sanima. Wai menene banbanci sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa mata, dana gefen ƴaƴan ƴaƴa maza". Dariya yayi mai sauti tare da cewa. "Uhumm kema kin shiga Masarautar Joɗa cikin kitimurmuran yanayi ko kin ratso cikin ahlin da ba'a sonmu, kin fara fuskantar ƙalubale ko". Tashi yayi yaje ya sha ruwa kana ya dawo ya zauna ya fuskanceta da kyau a hankali yace. "Banbancin tsakanin sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa maza da gefen ƴaƴan ƴaƴa mata. Shine kamar haka. 1 Galadima (must be a prince ) 2 Chiroma (crown prince)first born to the king 3 Tafida ( most be a prince ) 4 Santuraki (must be a prince ) 5 Sarkin dawaki ( prince) 6 Ɗan buram 7 Ɗan isa 8 Ɗan lawan 9 Durbi 10 Wambai 11 Turaki 12 Ɗan maje 13 Yarima 14 Ɗan iya 15 Majidadi. Dan ɗagowa yayi ya kalleta tare da saƙe yatsunshi da yake naɗewa yana irga mata yace. "Wannan duk royal family ne mostly biological sons din sarki ne wasu kuma jikokin sarki kuma kunne biyu sukeyi a rawunansu sabida su ƴaƴan sarki ne ko kuma iyayensu ƴaƴan sarki ne. Kanta ta jinjina mishi alamun ta gamsu tana kuma ganewa. Shi kuwa a nitse yaci ga da ce mata. "Anan ake samin chief of staff da kuma senior councillor kamar galadima mostly shine senior councillor shine elders in royal bloodline ana samun galadima yapi sarki a shekaru kuma shi ake bama riqon gari in sarki bayanan. Sannan duka anan sunayen dana irga miki da fari kowa zai iya yin sarki tunda daga ɗan sarki sai jikokinsa na gegen ƴaƴa maza, shiyasa su kunne biyu sukeyi a rawanunsu. A hankali ya kalli Ummi data fito da Hijabi a jikinta ta zauna kusa da Shatu. Tare da cewa. "To kinji bayanin ƴaƴan ƴaƴa maza na sarki." Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Na gane kuwa Ummi, yanzu gaya min na ƴaƴan yaran sarki mata kuma inji". Gyara zama Jamil yayi tare da cewa. "To sukuma sarautar gefen yaya mata sune. 1 Madawaki 2 Garkuwa 3 Makama 4 Majidadi 4 Waziri 5 Matawalle 6 Sarkin yaki 7 Magayaki 8 Jarma 9 Talba 10 Shatima 11 Ubandoma 12 Ɗan kadai 13 Magajin gari 14 Ɗan masani 15 Barma. Ɗan sauƙe numfashi yayi tare da ci gaba da cewa. All of these hakimai ne wanda sukeyin kunne daya a rawunansu. Kuma wasu a cikinsu jikokin sarki ne ta bangaren mamansu, mum dinsu ce yar sarki kamar dai mu a Masarautar su Sitti ko za'a bamu mulki iya waɗannan za'a bamu kinga baza suyi kunne biyu ba shiyasa suke kunne daya amma suma hakimai ne manya kuma yan majalissar sarki also akwai kin makers a cikinsu. Sai dai su cikin jerinsu babu wanda zai gaji sarautar sarki kamar dai mu yanzu bazamu gaji Jadda ba da masarautar gargajiyace sai dai da yake nasu na musulcine, in Kuma a masarautar Joɗa ne sunayen da na ƙirga miki na forko cikinsu za'a iya bamu, domin yanzu GARKUWA da aka bawa Hamma Jabeer matsayinsa yafi ƙarfin hakan shiyasa Magauta basu damuba." Ya ƙarishe mgnar da cewa kin gane ko Aunty Shatu, Kinga shiyasa da aka bawa Ya Jafar Galadima cikin kwana goma aka sabauta manashi. Ana tsoron kada tarihin Sarki Bala da mahaifinshi Madu ɗan Sarki Sule ya maimaita kanshi a kan ƴaƴan ɗakinmu. Shiyasa da aka bawa Hamma Jabeer Garkuwa mu bamu soba. To sauƙin abin ma ɗaya ne da suga sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa mata aka bashi duk da shi jikan ɗan ɗan ɗansa namiji ne". Ajiyan numfashin tayi kana a hankali tasa hannunta ta tallaɓe habarta, cikin alamun nisan zango na tunani da nazari. A hankali Ummi ta matso kusa da ita cikin sanyi da kuma yin ƙasa da murya tace. "Shatu ni kuma in tambayeki wani abu mana". Kanta ta jujjuya a hankali ta buɗe baki tace. "Na sani! Ummi nasan abinda zaki tambayeni! Zakimin tambaya ne kan menene yasa da na shiga ɗakin Yah Sheykh na suma na fita haiyacina, ko?". Ta ƙarishe mgnar wasu hawaye masu ɗumi suna kwaranyo mata a fuskarta. Cikin sanyin jiki ganin Ummi ta gyaɗa mata kai alamar eh. Jamil ma jiki a mace ya zuba mata ido. Tafin hannunta tasa ta sharce hawayenta murya na rawa alamun tana son danne kukanta tace. "Ummi ɗakin Yan Sheykh ɗakine mai cike da hatsara a rayuwarshi. Tabbas dan Allah yayi shi mutun ne mai ibada da imani da kekyawar zuciya, da yawan ambaton sunan Allah da zama da al'wala wlh da badan wannan nagartar da Addu'o'in da suka zame mishi abokan rayuwa suka zame mishi GARKUWA ba, kamar yadda Manzon Allah yace. "Addu'a'u saiful muminin da tuni sun kasheshi sun sabauta rayuwarshi. Ummi ban san komai ba kan masarautar Joɗa. Amman dan al'farma Annabi da darajar Umaymah. Zan taimaki Yah Sheykh iyakar iyawata. Zan taimake shi akan abinda Allah ya bani ikon gani". A hankali Jamil ya zamo ya zauna a ƙasa. Yana mai jin tsikar jikinshi na tashi. Itama Ummi zamowa tayi ta zauna ƙasa. Hakama Shatu a hankali ta zauna gaban Ummi hannunta tasa. Ta kamo hannun Ummi cikin muryar kuka tace. "Ummi ku yarda dani, ku bani haɗin kai, zan tone duk abun cutarwa dake ɗakin Yah Sheykh. Bazan cutar dashi ba, zan taimake shi kamar yadda Bappa na yake bani umarni duk sanda mukayi mgn dashi. Ummi keda Jamil ina buƙatar taimakon ku. Amman kafin nan ki gayawa Umaymah in ta amince, sai inyi aikin amman kada a gayawa Yah Sheykh dan bazai yarda ba." Cikin tsoro ido cike da hawaye Ummi tace. "To Shatu me zancewa Umaymah, me kika gani a ɗakin har ya firgitaki yasaki suma?". Cikin kuka tace. "Ummi kada ku tsaya bincike a kaina. Ni dai ku yarda dani bazan cutar da kowaba na cikin Masarautar Joɗa sai wanda ya cutar da kanshi Ummi bamu da sauran lokaci mai tsawo fa, komai zai iya faruwa da Yah Sheykh". Cikin tsoro da firgici Jamil yace. "Ba matsala mun yarda dake, ni yanzu taimakon me zan miki?". Cikin sauri ta share hawayenta tare da juyowa ta kalli shi kana tace. "Yauwa Jamilu zaka samo mana mai saka tayis, yazo da katon ɗaya na tayis ɗin irin na bedroom ɗin Yah Sheykh sak da sak. Sai kuma kayi ƙoƙarin mu samu ya Sheykh in ya fita ya wuni sai dare zai dawo". Cikin sauri yace. "Tayis da mai sawa ba matsala, batun in ya fita sai dare ya dawo kuma inaga. Sai zuwa jibi ranar ne zaije asibitin gwamnatin Genaral Hospital. To in yaje can wuni yakeyi wani lokacin sai dare zai dawo". Cikin gamsuwa da hakan tace. "To ba matsala. Ummi ke kuma ki kira mana Umaymah ki sanar mata, muyi abun da saninta." To Ummi tace kana a wurin ta kira Umaymah tayi mata bayani. Ba wani neman ba'asi tace. "A barta Ummin Jabeer na amince, tayi duk abinda ya dace a kan mijinta da yayanshi da ƙannenshi dama duk wani abu nashi". Cikin jin daɗi ta jinjina kai lokacin da take jin mgnar Umaymah. Wani irin dogon numfashi taja mai ƙarfi sai gata ta tafi luuuh kan...! Wasa farin girki? Shatu kadafa allura ta tono garma. By *GARKUWAR FULANI* Ta konta, kamar maiyin bacci kamar wacce ta suma. Cikin mamaki suka bita da ido kana suka juya suka kalli juna, Cikin mamaki Jamil yace. "Ummi suma ta kumayi ne?". Kai ta jijjiga mishi alamar a a. Kana tasa hannun damanta ta gyarawa Shatu'n. Kwanciyarta. Tare da cewa. "Bacci ne tayi". Kai ya kuma gyaɗawa cike da mamaki yace. "Wannan baiwar Allah'n, itama da akwai abin al'ajabi tare da ita. Da akwai abinda yake a duhu wanda bamu sanshi ba a kanta." Cikin gamsuwa da bayan shi Ummi ta gyaɗa kai tare da cewa. "Na daɗe da dasa ayar tambaya a kanta, sai dai bani da mai bani amsar dole sai zaman yauda kullum zai ƙara fahimtar dani ko wacece ita. Yanzu dai Jamil wannan mgnar ta zama sirri tsakaninmu. Da Allah kada kowa yaji!". Cikin nitsuwa yace. "In Sha Allah Ummi babu wanda zaiji". To da haka dai sukaci gaba da hira a wurin. Cikin Sa'a baccin nata baiyi nisaba ta farka. Lokacin sallan azahar nayi suka watse. Bayan sunyi salla da jimawa ne, ta miƙe a hankali ta nufi ɗakinshi. A falo ta tsaya, tana nazarin to in ta shiga ta sameshi idonshi biyu fa? Akwai abinda take son idonta ya ƙara gani dan ta tabbatar. Shi kuwa Sheykh yana ciki, a kwance kamar mafi akasarin lokuta, waya yakeyi da Aunty Hafsat. Tana ce mishi ya haɗata da amryar zasuyi mgna. Cikin sanyi yace. "Bacci, Aunty Hafsat Bacci fa zanyi, afwan ki bari sai anjima mana". Cikin sanyinta tace. "Oho Jazlaan, nace ka haɗani da ita shine wannan magiyar yanzu Yezeed yazo ya nuna min hotunanta wai Hibba ce ta turo mishi. Tamin kyau sosai, ina son yarinyar. Zakiya ma tana amshi number ta, wurin Hibba tana kira kuma bata ɗagawa. Jazlaan haɗani da ita nace ko!". A hankali ya yunƙura ya tashi zaune. Cikin sanyin baccin daya fara yi yace. "To ɗan katse kiran in naje zan kiraki." A hankali ya miƙe tsaye. Al'kyabbar sa ya ɗauka, tare da nufar bakin ƙofar. Yana mai sa hannunshi cikin rigar al'kyabbar. Har yazo bakin ƙofar bai gama sa hannun rigar ba ya buɗata da faɗi. Ita kuma Shatu a hankali ta tura ƙofar. Ta sako kai ciki dai-dai lokacin kuma shima ya sako kai waje. Ba zato ba tsammani sukaji sunyi kiciɓis da juna ta faɗa cikin faffaɗan ƙirjinshi. Cikin sauri ya sauƙo da hannayeshi dake buɗe kuma al'kyabbar na buɗe da faɗinta sanadin sauƙo da hannun da yayine sai ya zama ya sauƙe hannunshi kanta, yayi mata ƙawanya da faffaɗan al'kyabbar jikinshi ya haɗasu wuri ɗaya ya rufesu. Wani irin harbawa zuƙatansu suka farayi da ƙarfi-ƙarfi, suna jam junansu i ziwa jikin juna tamkar mayen ƙarfe. A hankali Shatu taji jikinta na macewa. Kanta ta manna a ƙirjinta kunnenta na dai-dai kan ƙahon zuciyarshi. Lumshe idonta tayi tanajin wani irin masifeffen ƙamshi turare mai daɗin shaƙa dasa baccin daɗi cikin ƙanƙanin lokaci, koda yake baccin nata baya rasa nasaba da abinda ke wujijjigata. Shi kuwa Sheykh Jabeer, shiru yayi yanajin yadda tasa hannunta, ta zagayo ƙugunshi ta riƙe gam-gam da iya ƙarfin ta. Sai kuma ya ɗan sunkuyo cike da mamaki yakkali fuskarta, tuni tayi bacci cikin ƴan second nin nan. Cike da mamaki ya zubawa fuskarta kallon tuhuma. A hankali yasa yatsunshi ya fara ɓanɓaro hannunta, yanayi yana ja da baya-baya yana komawa cikin ɗakin. Ita kuwa binshi take amman ba bi irin na takuba, Cike da mamaki ya ƙara leƙa fuskarta. Tabbas bacci tayi. Janyeta yayi daga jikinshi kana ya saketa a hankali ta tafi zata faɗi, bai tareta ba, sai dai yasa ƙafarshi ya tare dai-dai inda yaga kanta zai bugu. Cikin Sa'a kanta ya sauƙa kan rumfar ƙafarshi. A hankali ya ajiye ƙafar tashi a ƙasa. Kana ya janye ƙafarsa, kanta ya konta a ƙasa. Cike da mamaki, ya juya ya koma can inda yake konciyar. Bai cire al'kyabbar ba ya konta yana mgnar zuciya. "Mutun kamar mayya, wannan baccin kuma na meye to". A haka shima yayi baccin da yasan in bai yishiba, zaiji ciwon kai. Kiran sallane ya tadashi. Tanan konce har yanzu. Al'wala yaje yayi kana ya fito ya kimtsa ya fesa turare. A hankali yazo kusa da ita. Ɗan sauran ruwan dake tafin hannunshi ya yarfa mata a fuska. A hankali ta buɗe idonta, kana ta kuma lumshesu haka tayi kusan sau uku ganin hakane a hankali yace. "Ke kasa uwar bacci tashi kiyi salla". Miƙa tayi a hankali tare da cewa. "To". Shiru yayi yana nazarin muryarta, ba haka muryarta yakeba. Wannan shine abinda su Ummi basu ganeba, shi gashi ya gane a take, Su kuwa basu gane cewa muryarna ba tata bace. Kanshi ya ɗan juya tare da cewa. "Uhummmm". Daga nan ya fita, ita kuma Shatu da ido ta bishi. Yana fita ta miƙe kalle-kalle tayi a ɗakin nashi sosai har ƙarƙashin gado ta leƙe. Tana gamawa ta shiga Bathroom nashi. Wani irin murmushi tayi tare da cewa. "Komai nashi mai kyau da tsabta". Al'wala tayi kana ta fito, a falo ta samu Ummi da Hibba da alamun a nan sukayi salla. Sosai Ummi tayi mamakin kenan, tana ɗakin Sheykh ne, murmushin jin daɗi tayi a ranta tace. "Ikon Allah kenan". Ita kuwa Shatu hijabin Hibba ta amsa tayi salla. Suna zaune a nan ya shigo. Wayarshi na kunne cikin nitsuwa yace. "To Aunty Hafsat gata nan ɗazu bacci takeyi". Cikin murmushin tace. "To bata". A hankali ya iso tsakiyar falon wayar ya miƙo mata tare da cewa. "Aunty Hafsat ce ƙanwar Umaymah saura kiyi mata rashin ta ido". Ya ƙarishe mgnar a hankali yadda ita Aunty Hafsat bazata jishiba. Ita kuwa amsa tayi tare da karawa a kunne cikin nitsuwa tace. "Assalamu alaikum". Fuska a sake tace wa alaikissalam ɗiyata, ya gida ya sanyi". Muryar matar sak irin ta Umaymah shiyasa cikin jin daɗi tace. "Lfy lau Alhamdulillah Aunty ya gida da aiyuka". "Alhamdulillah". Tace kana ta ɗora da cewa. "Sunana Hafsat Jalaluddin Muhammad Sultan". Cikin jin daɗi tace. "Eh Aunty na sanki ai Umaymah ta gaya min sunanki ta nuna min hotonki da Aunty Rahma da Zakiya da Yezeed dama duk sauran". Cikin jin daɗi tace. "Masha Allah, to ki amshi number ta data Rahma da Zakiya a wurin Hibba, ɗazuma Zakiya taita kiranki ashe kina bacci ne". Cikin nitsuwa tace. "To Aunty yanzu kuwa, ngd matuƙa". Cikin jin daɗi Aunty Hafsat tace. "Allah ya muku al'barka ya baku zaman lafiya. In Sha Allah zamuzo auren Haroon zaki gammu mu ganki". "Amin Amin. Aunty Allah ya kaimu lokacin ya kawoku lfy". Tace kana sukayi sallama. Daga nan suka shiga kitchen. Jamil kuwa tuni yaje yayiwa wani mai musu aikin gidansu. Yasa ya nemi irin wannan tayis ɗin. Yace gobe da safe misalin sha ɗaya zaizo ya ɗauke shi. Washe gari da safe. Misalin karfe tara, Sheykh ya fito cikin shiga ta al'farma, yau ba al'kyabba a jikinshi riga da wondone sai malum-malum gariya mai kyau. Getzner ce mai masifar kyau Brownish red color mai ɗan karen kyau da sheƙi, gariyar tasha aiki mai ɗan karen kyau da zaren surfani mai sheƙin piash color. Hular kanshi da red and piash color, takalmin shi kuwa fatar ta kifa kalar red ɗin. Yayi kyau sosai ya kafa hular nan cas a kanshi. Kekyawan suman kanshi ya konto gefe da gefe da ƙeyarshi sai sheƙi da ƙelli yakeyi. Sajenshi ya kwanta lib, gashin girarsa dana gemunshi ɗan cas dashi misalin kamu ɗaya, sai sheƙi suke zubawa. Ɗan madai-daicin bakinshi mai jajayen laɓɓa sai sheƙi sukeyi. Yar ƙaramar jakar na'urar System ya riƙe a hannunshi, sai wani ƙamshi mai daɗin ji yake fiddawa, ɗan farin siririn Glass irin na manyan Doctors ya manna a fuskarshi kana ya fito. A falonshi ya sameta, tana jera mishi breakfast. Ganin zai wucene ta ɗan biyoshi a hankali ya zama suna tafe a jere. Cikin kallon suman ƙeyarshi tace. "You are breakfast is ready". Bai kulata ba yaci gaba da tafiya. Ita kuma ƙeyanshi ta mannawa harara. A haka suka fito. Ya sallami Ummi da Jamil da tunda suka karya bai tafiba. Da sauri Jamil yabi bayanshi yana cewa. "Uhum Dakta sai yaushe zaka dawo ne?". Juyowa yayi ya kalli Jamil sai kuma yace. "Kanada matsala ne?". Da sauri ya jujjuya kanshi tare da cewa. "No. I'm very fine". yayi mgnar yana jijjiga jikinsa. Kai ya kaɗa ya juya zai fita, Da sauri Jamil ya kuma tambayarsa. "Dakta yaushe zai dawone". Cikin tsuke fuskarsa yace. "Ban sani ba". Daga nan ya fita, shi kuwa Jamil tsalle yayi tare da cewa. "Yesss, Dakta Allah ya kiyaye hanya, a wuni lfy a asibiti". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Yi maza to ka ɗauki shi". To yace kana ya miƙe ya fita. Sanin cewa yanzu Sheykh yana sashin Hajia Mama ne. Haka yasa ya rigashi fita. Ummi kuwa miƙewa tayi taje ta rufe ƙofar sabida bata son wani yazo ya shigo. Kiran Jamil tayi a waya tace in sun isoma ya kirata a wayane zata buɗe mishi. Tana katse kiran ta juyo ta kalli Shatu dake zaune gefenta tana ce mata. "Yauwa to Ummi muje mu fara aikin kafin ya iso mun kusa cimma aikin." Cikin mamaki tace. "A a keda kikace sai an matsar da gadonshi sannan aikin tono ai bazamu iyaba. Dole sai mazan". Cikin muryar da har yau Ummi ta kasa banbance shi da asalin muryarta tace. "A a ba matsala Ummi muje zamu iya". Ta ƙarishe mgnar tana yin gaba, ganin hakane yasa Ummi Binta a baya. A hankali suka shiga falon. Tana mai cewa Ummi. "A nan ma an mishi wani aikin amman shi bai shiga jikinsa ba, sabida yanada Garkuwar addu'o'in da yakeyi yau da kullum. Shiyasa duk sabbin sihirurruka basa shigarsa. Sai dai waɗanda akayi mishi tun bai gama girma ba." To kawai Ummi ke ce mata sabida jin kamar muryarta na canza mata. A haka ta kuma nuna mata wani wurin. Tare da cewa. "Uhumm Ya Jafar suke nema, su maida majanunin kan bola sai kuma sharrinsu ya zame mishi al'khairi, Tsawon shekaru baya mgn sai ambaton Allah. Bashi ba zunibi sai tarin lada da yake samu na karatun al'ƙur'ani da ya zame mishi abokin hira. To ita kuma me take nema a duniya da zata cutar da baiwar Allah da ahlinta duka haka. In banda lalaci da son duniya na miji ya lalace da bin matsafa yana sawa ana sabauta ɗan uwanshi da yayanshi." Ita dai Ummi binta takeyi da ido da ƙafa har suka isa bedroom ɗin shi. Ɗan lungun da ɗaya Bedside drower'n take ta shiga. Kana ta kalli Ummi fuska a juye tace. "Naɗe min carpet ɗin nan. To Ummi tace da sauri ta fara naɗe carpet ɗin. Bayan ta janyeshi da kyar ne, ita kuma Shatu. A hankali tasa hannun damanta bisa jikin gadon ba tare da ta ɓallashi ba ko, ta cire wani abu a jikinshi ba, ta yunƙura ta tura gadon tare da cewa. "Bismillahirahamanirahim". Da sauri Ummi taja da baya cike da mamaki da tsoron ganin yadda take tura tamfatsetsen gadon mai ɗirkekiyar katifa da ko tura katifar kawai aikine. Guuuuuuh haka sautin tura gadon yake badawa. Saida ta turashi har jikin Waldurob. Kana ta tsaya a tsakiyar inda gadon yake kafin ta turashi. Dai-dai lokacin kiran Jamil ya shigo wayarta. Da sauri taje ta buɗe mushi. Kana suka shigo,. A falon suka bar Ɗalha mai tayis, kana Jamil ya amshi kayan aikin yabi bayan Ummi yana cewa. "Yauwa ɗalha ɗan jirani bari inzo mu isa kaga wurin". To ɗalha yace kana ya fara cin abincin da Ummi ta saka mishi. Suna shiga suka maida ƙofar falon suka rufe. A inda Ummi ta barta a han suka sameta. Da sauri ta miƙawa Jamil hannun tare da cewa. "Bani gudumar da ma'ɓamɓarin." Cikin sauri ya iso tare da ajiye ɗan buhun ya fito da gudumar da Maɓamɓarin yana mai mamakin yadda aka tura gadon yace. "Bari Aunty Shatu nuna min ina zan fasa". Da sauri tace a a, ku ɗan matsa gefe, musamman ma kai koma can". Ta nuna mishi gefe. Sake mata gudumar yayi jin ta fizgeshi. A hankali ya tashi sabida cewa da tayi ya tashi. Ido suka zuba mata, ita kuwa, gudumar tasa ta rinƙa buga tayis ɗin dake wurin saida ta fasa uku lafiyeyyu. Kana ta ture fasassun tasa maɓamɓari tana ɓalle sauran, saida ta ciresu kab. Sannan ta fara fasa fulon simintin dake ƙasan. Da mamaki Ummi ke kallon wurin sabida tasan babu wani fulo da akayi kafin asa tayis ɗin. Fasashi tayi kana ta fara caccaka ƙasan wurin da matonin, tanayi yana fito da ƙasa. Shiru sukayi ganin ramin yayi zurfi kuma ba komai. A haka taci gaba da tono tana kuma faɗaɗa ramin ta ƙasa. Wani irin zabura Jamil da Ummi sukayi lokacin da suka ga wani baƙin hayaƙi yana fitowa cikin ramin. Ita kuwa Shatu da sauri tasa hannun damanta taci gaba da tonon. Tare da yin mgna da sauri tace. "Jamilu buɗe windows da sauri hayaƙin nan ya fita". Cikin rawan jiki yace to. Kana ya fara buɗe wa da sauri sabida, hayaƙin ya fara cika ɗakin. Yana buɗe windows ɗin kuwa hayaƙin ya fara fita. Tonon taci gaba dayi tare da cewa. "Inama da akwai wani yardajjen mu a kusa, bayan ku biyun nan da yabi hayaƙin nan zaigane mana ina zai shiga cikin sashukan mutanen gidannan shaidar aiki ya koma kan wanda ya yishi." Da sauri Jamil yace. "To ko in fitane inbi hayaƙin". Cikin sauri tace. "A a kada ka fita ku tsaya kaida Ummi." Numfashi suka fara sauƙewa, a hankali lokacin da sukaga duk hayaƙin ya gama fita. Sai kuma suka fara takowa suna zuwa inda take ganin yadda hannunta dake cikin ramin yake karkarwa. Ga wata zufa dake keto mata kamar da bakin kwarya. Wani marfin tukunyar ƙasa ta ɗago. Kana a hankali ta ɗago tukunyar. Ta ajiyeta gefe kana ta koma ta jingina tana mai jan numfashin. Cikin sauri Ummi taje ta kunna sauran wutan ɗakin duka, ya zama kamar farin wata. Jamil ne ya fara leƙa cikin tukunyar. Da sauri yace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun. Ummi zo ki gani". Ya ƙarishe mgnar yana sunkuyowa da kai hannunshi zai kama tukunyar ƙasan cikin sauri da ƙarfi Shatu ta buge hannunshi da hannunta na hagu tare da cewa. "Jininka ɗaya da Yah Sheykh in ka taɓa duk abun zai iya dawowa jikinka." Ta ƙarishe mgnar da ɗago hannun ta na dama tasa a ciki. Tukunyar da sauri ta rumtse idanunta sabida wani irin masifeffen tsikara da taji an mata a hannunta. A can ƙasar Cameroon kuwa cikin Rugar Duno dake, kusa da Rugar Malam Babayo. Ba'ana ne zaune bisa buzun aikinshi. Da kasko a gabanshi yana kallon cikin kaskon gaba ɗaya jikinshi rawa yakeyi cikin tashin hankali da fargaba yace. "A'a A a Mata kada ki taɓa, baki amince na baki mgnin kariyar tonar sihiriba, iya ganin idan a zuba sihiri a abinci yake na shayar dake shi nanma a bisa dole baki saniba. Kada ki taɓa zai cutar dake". Ya ƙarishe mgnar hawaye na zubo mishi, Allah ya sani baya son abinda zai cutar da Shatu ko kaɗan. Ita kuwa Shatu a hankali ta fara fito da wasu irin tabka-tabkan layu wanda aka liƙesu da yadin al'kyabba daga gani kasan na Sheykh ne sabida shi ɗaya kesa irinsu a masarautar Joɗa tun yana ɗan yaro matashinsa. Wani dogon ajiyan zuciya taja tare da fizgo wani dogon maciji a cikin tukunyar ƙasar. Da sauri Ummi taja da baya, shi kuwa Jamil sai leƙowa yakeyi. A dai-dai lokacin kuma Sheykh dake cikin Office dinshi na cikin Genaral Hospital Ɓadawaya shi ɗaya, dan yau ba mutane sosai dudu mutun biyar ne kuma ya gama dubasu ya musu komai, yana zaune ko za'a turo wasu. Wani irin zabura yayi ya miƙe tsaye da ƙarfi tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". Sai kuma ya sunkuyo yana kallon yadda babbar yatsarshi ta ƙafar dama wacce zanen maci ke kanta take rawa kar-kar. Da sauri ya juya ya nufi bathroom ɗin cikin Office dinshi. Cikin sauri ya zare malum-malum ɗin jikinshi juyowa yayi ya ajiyeta saman kujerarshi. Kana da sauri ya nufi Bathroom sabida yadda yakejin ana fizgo wani abu kamar jijiya a jikinshi tun daga saman cikinsa kusa da ƙirjinsa, har zuwa kan ɗan yatsarshi. Da sauri ya cire rigarshi da snglet ɗin, da ido yabi zanen dake jikinshi wanda samanshi zanen kan macijine. Gaba ɗaya jikinshi rawa ya farayi tamkar mazari. Duk wata jijiya dake jikinsa saida ta tashi tsaye. Cikin tashin hankali yake ambaton sunayen Allah da duk addu'o'in da sukazo bakinsa. Hannunshi yasa ya damƙi bnnarshi data miƙe tayi wani irin harbawa da masifar ƙarfi, riƙeta yayi da kyau jin yadda take tashi tana kumbura da cika tana tsawo tamkar zata faso boxes ɗin shi ta fito woje. Wannan shine babban tashin hankalinshi dan tsawon shekaru kusan ashirin bai sake ji ko ganin bnnarshi ta miƙe kamar hakaba sai yau. Karkarwa duk jikinshi keyi, hatta jijiyoyin kanshi dana damatsan hannunshi tasowa sukayi ruɗu-ruɗu jijiyar goshinsa har harbawa takeyi". Innalillahi wa innailaihi rajiun yaketa maimaitawa, yanajin kamar ana jan jijiyoyin jikinsa. A haka ya maida kayanshi kana ya fito. Sai dai bai samu damar maida gariyar ba, zama kawai yayi bisa kujerar yana rawan sanyi. A haka abokinshi Dr Arabi ya shigo ya sameshi cikin mamakin ganin yadda yake karkarwa yace. "Dakta Jabeer lfy kuwa meya sameka". Cikin muryar alamun zazzaɓi yace. "Zazzaɓi ne Arabi. Sanyi nakeji". Da sauri ya iso inda yake taimaka mishi yayi ya saka mishi gariyar. Kana ya kamoshi ya kawoshi bisa tattausan kujerar 3 str dadake cikin Office ɗin ya kwantar dashi. Aunashi yayi tare da kiran wata Nurse ya gaya mata magungunan da zata amsa musu a Pharmacyn nasu, cewa Dr Jabeer ba lfy. Ai lokacin ɗaya sai gata da manyan likitoci har uku. Cikin tarin kulawa, suka fara dubashi ganin yana gab da fita haiyacinsa ne, yasa suka mishi allurar bacci. Da sauri Dr Arabi kuma ya kira, Jalal ya sanar mishi. Jalal kuwa dake falon Hajia Mama ba tare da ya gaya mata ba ya miƙe da sauri ya fita. Tana tambayarshi lfy. Yace lfy sabida baison tayar mata da hankali. A bakin ƙofar fita ya haɗu da Ya Affan da sauri ya kamo hanunshi suka juya yana cewa. "Ya Affan Hamma Jabeer ba lfy, yana Genaral Hospital Ɓadawaya, yanzu Yayan abokina Umar Dr Arabi abokinshi ya kirani ya gaya min yace baida lfy sosai fa". Ai da sauri Affan ya fara lalubo car key dake cikin al'jihunsa cikin kiɗima da tashin hankali yace. "Muje, muje da sauri mu tafi a maidashi Valli Hospital yafi kwararrun likitoci". Kusan a tare suka shiga motar Affan suka tafi. Kafin suje kuwa tuni bacci ya ɗauke shi, an ɗaura mishi ruwa da allurai. Sauran Doctors ɗin sun fita. Sai Dr Arabi da yake zaune gabanshi. Da sauri Affan yasa hannun shi ya taɓa jikinshi tamkar wuta. Jalal kuma yatsarshi daketa karkarwa yake kallo tare da rauni a fuskarshi yace. "Yah Arabi meya sameshi ne?". Cikin sanyi Dr Arabi yace. "To wlh nima shigowa kawai nayi na sameshi yanata karkarwa, yace min zazzaɓi yakeji sanyi na damunshi. Na kira Nurse ta kawo min injections and drip kafin muyi mishi allurar ma tuni ya kusa suma, abun yafa bani tsoro. Amman Alhamdulillah kunga yanzu kuma da sauƙi". Ajiyan zuciya sukayi kana suka zauna a nan, ba tare da sun gayawa kowa ba. A can masarautar Joɗa kuwa. Cikin tarin firgici da al'ajabi Jamil da Ummi ke kallon Shatu. Data fizgo macijin da ƙarfi cikin tukunyar. wurgar dashi tayi a ƙasa sai gashi yayi wutsul-wutsul sau biyu, shike nan ya mutu." Mazargin mondo ta fitar da kuma hula wanda duk na Sheykh ne. Cikin murya mai rauni tace. "Yanzu Jamil zaka iya taɓasu. Haɗasu kaje in akwai inda zaka wurgar dasu ka wurgar dasu, ka fasa tulun. Kada ka binne macijin ya bushe akeso. Ummi ɗauki Hular Yah Sheykh da zariyarshi a wonkesu. Da sauri Jamil yace. "Eh akwai inda zan wurgar dasu". Nan ya tattare macijin da da layun ya saka cikin tulun ya fita. Key ɗin ƙofar baya ya ɗauka ya buɗe ya tafi cikin Garden ɗin. Tafiya yayi sosai saida yaje can cikin dajin ya fasa tulun macijin da layun suka watse kana ya juyo ya dawo ba tare da ko waiwaya ba sabida tsoro. Ita kuwa Ummi bathroom ɗin shi ta shiga a take ta wonkesu kana ta fito dasu. Cikin sanyi Shatu tace. "Wai hannuna Ummi yi sauri ki wonko gero ki kawo min ruwan tsarin." Da sauri Ummi ta fita. Murmushi tayi ganin Ɗalha mai gyaran tayis yaci yayi haniƙan yana kallon tv. Cikin sauri tace. "Yi haƙuri dan Allah Ɗalha muna tattare ɗakin ne da yake tayis ɗin ƙasan gadone ya fashe". Cikin shan iskar yace. "Ba komai Ummi". To tace kana taje ta wonke gero, sannan ta fito da ruwan tsarin tazo. Tana zuwa ta bawa Shatu cikin ramin ta watsa ruwan. Kana ta fara tura ƙasar da kuma fashesshe-fashesshen tayis da fulo ɗin tanayi tana yayyafa ruwan. Dai-dai lokacin Jamil kuma ya shigo. Ganin yadda hannunta yaketa karkarwane yasa ya tayata tura ƙasar saida suka gyara komai fes kamar ba fasawan ganganci akayiba. Kana ta miƙe tare dasa hannun hagunta ta riƙo na damanta tana cewa. "Shima Yah Sheykh dole zaiji wani abu a jikinshi duk inada yake". Sai kuma tayi shiru tare da rumtse idanunta tace. "Wash hannuna". Cikin sauri Ummi tace. "Sannu hannun ya gaji ko". Kai kawai ta gyaɗa mata. A haka suka fito falon. Kai tsaye bedroom ɗin ta ta nufa. Shi kuwa Jamil yayiwa Ɗalha jagoro, Suka shiga suka gyara wurin da aka fasa ɗin fes. Kana Ummi ta share wurin ta goge, sannan suka tura gadon suka maidashi. Nanma ta ƙara gyara ɗakin Jamil kuwa ya ɗauki Ɗalha ya maidashi wurin aikinshi. Ummi na gamawa taja ƙofar ta rufe tana al'ajabin wannan abu da ta gani da idonta. Kitchen ta wuce ta ɗaura musu Lunch tana kiran Umaymah ta gaya mata duk abinda ya faru. "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Kaɗan daga cikin mafarkan da nakeyi kan Sheykh ya auro ba fulatar daji sun fara tabbata. Ya Allah kasa abinda zai faru a sanadin shigowar Shatu masarautar Joɗa ne kake nunamin a mafarkaina". Umaymah ta faɗi lokacin da Ummi ta mata bayanin abinda ya faru. "Amin Amin, Ummi tace kana ta katse kiran jin muryar Aunty Juwairiyya da Hibba." Umaymah kuwa da sauri ta kira Lamiɗo ta gaya mishi abinda ya faru. Murmushi yayi irin nasu na manyan sarakuna yace. "Alhamdulillah warakafa nan shigowa masarautar Joɗa baki ɗayanmu zamu rabu da mugun iri a cikinmu, kada ki gayawa kowa Khadijatu kinji ko". Cikin jin daɗi Umaymah tace. "In sha Allah kuwa ko Jadda bazan gaya mishi ba". Murmushi yayi tare da cewa. "Masha Allah, Allah ya miki al'barka Khadijatu da ace duk ƴan uwa haka suke riƙe ƴaƴan yar uwarsu da zumunci ya ƙara ƙarfi kin musu abinda mahaifiyarsu bazata iya musuba". Amin Amin tace kana ya katse kiran. A cikin ɗakin Shatu kuwa. Wani irin...! By *GARKUWAR FULANI* Ya ruggumeta da kyau a jikinshi. Jinyadda taketa fizge-fizgen zata kwance kanta. Wani irin tsuma jikinshi ya rinƙayi can cikin naman jikinshi yake jin tsuman. A hankali ya manna kanta, kan faffaɗan ƙirjinshi, hannunta mai ciwon data ɗaura a tsakiyar kan natane ya zubawa ido. Sosai hannun yayi jazir sai kelli yaki, alamun kumburin da yayi. A hankali yasa hannunshin ya tallabo hannun. Wani irin ihu tasaka da ƙarfi. Sai dai bai bari ihun ya fito daga bakinta ba, yayi maza ya rufe mata baki da tattausan tafin hannunshi yana ta mai-maita. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". Tabbas da in ya barta ta kurma ihun shike nan ta tabbata zautacciya, yin ihun da take son yi dai-dai yake da sihirin ya gama shiga jikinta ya ratsa zai kuma haukatata. Shiru tayi tana zazzare idanunta da hawaye ke zuba babu ƙaƙƙautawa, shi kuwa Sheykh a hankali ya janye hannun nata data aza a kai ya tallabeshi da tafin hannunshi. Sannan ya manna ƙirjinshi da nata ƙirjin da kyau. Har suna iya juyo bugun zuciyar juna. Sunkuyo da kanshi yayi tsakanin kafaɗarta da wuyatan Bakinshi ya saita cikin kunnenta. Hure gashin daya baje kan kunnen yayi ya matsa, sannan ya kawo bakinshi gab da kunnenta har tattausan lips ɗinshi na taɓa tattausan kunnenta. Lumshe idonshi yayi tare da gyara tsayuwar nasu da kyau. Ita kuma sai fiffizgewa take sonshi jikinta duk yana karkarwa ga zufar dake tsiyayo mata. Hannunta dake cikin hannunshi ya kalla yadda yaketa rawa, gashi zafi jau kamar wuta. A hankali yayi gyaran murya tare da yin bisimilla. Cikin ɗan-ɗaga sauti ya fara karanta Suratul Baqra cikin kunnenta cikin fidda harrufan da karsashin yadda zai ratsa kunnuwanta. Yanashi yana cire tafin hannunshi dake bakinta, wani irin manna kanta tayi da ƙirjinsa, ta lumshe idonta wasu hawaye masu ɗumi suka fara kwaranya. hannunta na hagu dake da lfyar tasa bisa kafaɗanshi ta zagayo wuyanshi da kyau. Shi kuma hannunshi da ya janye daga kan bakinta ya maida kan ƙugunta ya ruggumeta tsam a jikinshi. A haka yaci gaba da karatu, in yazo wasu ayoyin yakan maimaita karshensu kafin ya kuma kama forkon na gaba. A hankali ta fara sauƙe wasu tagwayen numfarfashi, ji takeyi azaba da raɗaɗin yana ɗan lafawa. *Al'farma Annabi da Alqur'ani kenan.* A hankali ta daina duk fizge-fizgen ta dawo sai kukan da takeyi mai sauti amman sautin a hankali ne. Kuka take sosai ganin hakane, ya gyara tsayuwar tasu. Kana ya tallabo kanta ya kalleta. A hankali ya girgiza kanshi tare da jawota suka nufi bakin gado. Yana cewa. "Uhummm baku samu wurin zamaba a kanta in Sha Allah bazamu zauna inuwa ɗaya dani da kuba, zaku bar jikinta." Ajiyeta yayi kan gadon kana shima ya hau ya zauna. da sauri ya riƙo hannunta da take son maidashi tsakiyar kanta ɗin. Karatu ya fara yanayi yana ɗan hura mata sassanyan iskan bakinshi. Tub, tub, tub, haka yake ɗanyi tare da fesa iskar, kana ya zuba mata ido cikin idanunta. A hankali tayi ƙasa da kanta. Shi kuwa haɗe fuska yayi tare da cewa. "Ɗago ki kalleni mana". Kai ta girgiza alamun a a. Shikuwa hannunshi ɗaya yasa ya tallabo haɓarta, dan ta kalleshi da sauri ta rumtse idanunta. Cikin kausasa murya yace. "Buɗe idon ki kalleni!". A hankali ta buɗi baki cikin irin Muryar da yaji tayi mgna kwanaki dashi tace. "Bazan iyaba, kunyarka nakeji!". Watsa mata wani kallo yayi tare da cewa. "Ƙarya ne, bakiji kunyan Allah'n daya haliccemu ya halicceku ya kuma yi mana iyaka a tsakaninmu ya hanaku cutar damu, ta hanyar mazonsa ya ƙaiyade muku dukkan motsinku, ya hanaku cutar da bani Adam. Duk bakiji kunyarsu ba, kika shiga jikin yarinya ƙarama, kina sata yin wasu abun da ba halinta ba, bakiji tsoron Allah daya hanakuba. Bakiji kunyar iyayenta ba, kina cutar musu da ɗiyarsu sai ni?". Cikin sanyi murya cike da alamun tsufa, tace. "Ni bana cutar da ita, Ni ba muguwa bace, ban taɓata cutar da ita ko wani nataba duk tsawon shekarun da nake tare da ita". Da sauri cikin faɗa yace. "To meyasa zaki shiga jikinta". A hankali cikin zubda hawaye tace. "Ni tun tana jaririya nake jikinta, kuma ni makaran gadone na ahlinsu daga wurin kakarta mahaifiyar mahaifinta". Da sauri yace. "Rufe min baki, makaran gado, Ku kuɗine ko wata kadara ce, ku cikin kadarorin da Allah (S.W.A) ya lissafa cikin jerin jadawalin abinda za'a gada?. Ko dan kinga ina binki a hankali ne yasa zakiyi min zancen banza na mutanen banza". A hankali tace. "Jikana ka kontar da hankalinka muyi mgna". A fusace yace. "Waye jikan naki, kina Jinnu ina bani Adam ta ina na zama jikanki. An ƙi a kontar da hankali tsohuwa dake kinzo kin liƙewa yarinya kina ƙoƙarin sata tana yaye suturar jikinta tana shirin yin ihu. Ko baki san cewa matar aure bace, baki san daraja da kimar dake cikin aure bako?". Cikin fushi itama tace. "Ni bani nasata yarda kallabin kanta ba, zafin ciwo da takeji ne ya gigitata yasata yarda kalkabinta. Sannan batun ihu da kakeyi kuwa. Aikin da mugayen Masarautar Joɗa sukayi data taɓane yake shiga jikinta. Ni kuwa na zone sanadin karatun Rugyan da kayi ta mata, amman duk wancan abun da takeyi ni bana kusa ma. Kuma ni ba mai cutarwa bace. Batun darajar aure kuma na fika sani. Kai kama tsaya inda takene bare ka raya auren ka tabbatar da ita matarka ce kai mijinta ne?. Kasa sabgogi a gabanka, kana sane da magautanka sun saka a tsakiya kayi, burus dasu, suna neman rabaka da rayuwarka. Ita kuma dole in taimaketa sannan dama Aysha in dai bata da lfy ko zazzaɓi ne tana kuka haka ciwonta yake." Cikin haɗe fuska yace. "Eh wato da ban ƙonaki bane, kikemin baki ko. T taimako bana son taimakonki ki fitamin a jikin matata, bana so, zakisa tayi ihu ta fita tsakiyar masarauta bayan kin san inada magautan to meyasa zaki nemin abinda zaisa magautana farin ciki. Tai mako kuma bama so, muda mukeda ubangijin taliƙai wanda yasan zahiri da baɗinin shi yake taimaka min, ba tare da yasa mana ciwon kai ko fita haiyaci ko kukaba dan haka fice min a jikin matata". Murmushi tayi tare da jinjina kai kana tace. "Matarka kuma yau". A hatsale yace. "A a matarki ce, in ba matata ba?." Sai kuma yayi bisimilla zai fara karatu da sauri tace. "Tsaya Muhammad Jabeer ɗan Habibullah jikan Nuruddee, Bubayero, Joɗa, Sule Usmanu jinin sarki Muhammad Bello, ni bazanyi faɗa da kaiba kafi ƙarfin haka duk da ni ba cutar daku nakeyi ba. Naga ranka ya ɓaci ina jinin. Wai matarka kace ko?". Wani irin kallo yayi mata tare da ɗago hannun shi zai shararamata mari yana cewa. "Wai ne ma ko?". Da sauri tayi murmushi tare da cewa. "Kamar gibtawar ido zan gudu jikinta, ka kwaɗa marin a kanta". Ai fa a kufule ya kai marin. Hannunshi na isa fuskarta tana yin atishawa. Zafin marin ya sauƙa kan fuskarta cikin azaba ta ɓare baki tare dasa kuka tana mai shafa haɓarta ido na zubda hawaye a gigice idonta na ganin duhu sabida zafin marin bata gama dawowa haiyacinta ba murya na rawa tace. "Wayyo Allah na me nayi maka zaka mareni, ka barni inji da ciwo ɗaya mana". Hararanta yayi tare da miƙewa ya sauƙa gadon yana cewa. "Mutun jiki duk al'janu, sai hegen bakin rashin kunya mutun in ba lfy bazaiyi addu'a ba sai kuka". Ya ƙarishe mgnar da juyawa ya nufi falo. Ita kuwa Aysha wani irin bacci ne yayi awon gaba da ita, tana mai jin zafin hannun ya ɗan lafa sai kuma raɗaɗin marin. A can falon kuwa, wayar Aysha ne dake hannun Hibba yayi ringi. Bappa am. Shine sunan da ta gani a rubuce. Da sauri ta nunawa Ummi shi tare da cewa. "Ummi ana kiranta". A hankali tace ki ɗaga. Kai ta gyaɗa tare da amsa kiran ta kara wayar a kunnenta. Cikin nitsuwa tace. "Wa alaikassalam". Sai kuma tace. "A a Bappa ba Aysha bace. Hibba ce, Aunty Ayshan tana ɗakin Hamma Jabeer". Cikin dattaku Bappa yace. "To Hibba ya jikin nata?". A hankali tace. "Bappa hannunta kam yana ciwo sosai, ya kumbura yayi ja, in an taɓashi zafi kamar wuta, bata iya bacci". Da sauri tayi shiru ganin Ummi na girgiza mata kai alamu. Ta daina faɗa mishi hankalinsa zai tashi. Ila kuwa hakane, cikin tashin hankali da kiɗima yace. "Yanzu kai mata wayar maza, kai mata inji muryarta". A hankali ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi wai in Kai mata wayar". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Jekiyi sallama ki kai wayar". To tace kana ta juya ta nufi falonshi. Tana jin Bappa na cewa. Yi sauri". A falo ta samu Hamma Jabeer ɗin cikin sanyi tace. "Hamma Jabeer gashi Bappa am, na son yin mgna da Aunty Aysha". Hannunshi ya miƙa ya amshi wayar ba tare da yace komaiba. Ganin kiran bai yanke bane. Yasa ya zubawa number ido cike da mamaki ganin code number ɗin bana ƙasar Nigeria bane, na ƙasar Cameroon ne. a hankali ya kai wayar kunnenshi tare da cewa. "Assalamu alaikum". "Wa alaikassalam Jabeer ne?". A hankali cikin nitsuwa yace. "Eh Bappa nine, ina kwana ya gida". Cikin jin sanyi yace. "Lafiya lau Alhamdulillah. Ya jikin Shatu?". A hankali yace. "Alhamdulillah Bappa jiki da sauƙi sosai ma yanzu hakama tana bacci ne". Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah to Allah ya ƙara lfy, amman me yake faruwa da hannun ne?". Cikin sanyi ya miƙe ya nufi bedroom. A gaban gadon ya tsaya tare da cewa. "Hannun ya ɗan kumbura amman ba sosai ba, sai kuma yayi ja, sannan jikin hannun yayi zafi sosai". Cikin tausayawa ɗiyar tasa yace. "Amman kada ayi mata allura, sannan a nunawa masu maganin gargajiya hannun, ko dajine". A hankali yace. "Bappa ba daji bane an gwadata babu wani ciwo a jikinta. Kuma inma dajin ne yanzu akwai alluran shi. Matsalar hannun yana ɗan lafawa ya kuma tashi ne. In ya tashi kuma ihu take son yi. Kuma sai tayi ta kuka. To kukan ne ke sa mata zazzaɓi da ciwon kai". Cikin sanyi yace. "Allah sarki Shatu, haka take in bata da lfy. Zan zo jibi in sha Allah." Cikin hikimar nuna mishi ya fahimci inda yake tace. "To Bappa Allah ya kawoka lfy, daga gobe zaka taso ko?". Cikin nitsuwa yace. "In sha Allah". Kontar mishi hankali yayi kana suka katse kiran. Ba'ana kuwa duk abinda ke faruwa da Aysha yana gani a ƙwaryar tsafinshi. Amman muddin Sheykh yana wurin sai yaga wani haske ya rufe ƙwaryar gaba ɗaya sai ya kasa ganin komai a kanta. Yanzuma zaune yake yasa yaranshi a gaba. Da kuma sabon uban gida daya samu. Cikin fargaba da tausayawa Mata abinda ke damunta ya kalli ɗaya daga cikin yaransa wanda ɗan ƙabilar ɓachama ne, cikin waɗanda suka koro shanayen Bappa ne da Alhaji Haro. Cikin Ɓacamancin yace. "Barun zaka tafi ƙasar Nigeria ka wuce jihar Ɓadamaya kai tsaye har cikin masarautar Joɗa". Cikin tsoro Barun yace. "Masarautar Joɗa kuma, ta yaya to?." Numfashi ya fesar tare da cewa. "Duk magungunan da Sarkin bakan masarautar Joɗa yake saka mata da wanda zai sa mata nan gaba, duk na ruruta ciwon ne, sabida shi magautan Jabeer yakewa aiki, to kasan cewar bawai sihiri bane shiyasa Mata bazata ganeba, kawai maganin ingiza ciwon yake shafa mata. Sannan makarin ciwon Ni kaɗai nake dashi. To zan kira Bappa da layinka. In mishi jawabin ciwon da mgnin sannan zance mishi kai yau zaka kama hanya, dan taimaka mata, amman fa sai in zasu biya kuɗin jinyar da shanu hamsin". Cikin mamaki Barun yace. "Shanu hamsin mutumin da muka kwashewa komai ko ɗan tinkiya bamu bar mishiba, ina zai bada shanu hamsin". Murmushi Ba'ana yayi tare da cewa. "Uhumm baka san waye Malam Liman ba kenan Bappa baka san da waye yake tareba, baka san komai game da shiba. Kai dai bani inkirashi yanzu kaji." Da sauri ya miƙa masa wayar. Shi kuma ya dannawa Bappa kira. Yana katse kiranshi da Sheykh yaji wani kiran ya shiga wayarshi. Amsa kiran yayi tare da kara wayar a kunne. Sauya murya ba'ana yayi tare da cewa. "Ina mgn da Malam Liman ko baban Aysha mai ciwon hannu". Da mamaki Bappa yace. "Waye ne?". Ciki kaurara muryarshi yace. "Sarkin bakan nufe ne, bincike nane ya nuna min ciwon hannun yarka tana can masarautar Joɗa. An kawo wani sarkin baka yana mata mgni sai dai mugune magautansu yakewa aiki. In har zaku biyani ni Shanu hamsin zan je kuma zan mata aiki a take zataji sauƙin". Cikin sanyi Bappa yace. "To yanzu kai ina kake". A nitse yace. "Ni yanzu haka ina bakin iyakar ƙasar Nufe da Nigeria ne. Yau zuwa gobe zan shiga ƙasar". A hankali cikin sanyi Bappa yace. "To ba matsala, nima jibi zan shigo. Mu haɗu a can in dai kayi mata mgnin ta warke a take zan biyaka da abunda kace". Cikin jin daɗi yace. "To sai mun haɗu." Katse wayar yayi tare da cewa. "Alhamdulillah Shatuna zata samu lfy. Zan kuma samu shanu hamsin. Sannan zanji lbrinta, zaka kuma isarmin da manufata. Kunga na jefi tsuntsu biyar da dutse ɗaya." Jinjina mishi sukayi kana ya shiryawa Burun komai nagnin ya nuna mishi yadda zaiyi da yadda zai isar mishi da saƙonshi wurin Aysha. Bappa kuwa Murmushi yayi dan ya gane Muryar Ba'ana. Dama ya sani bazai rabu dasu haka a sauƙaƙeba yasani yanzu duk motsin Aysha yana tafin hannunshi. Abinda yasa ya yarda su haɗu kuma yasan ba shi da kanshi zai jeba. Sai dai ya wakilta wani. Ya kuma sani tabbas yanada makarin ciwon taɓen sihiri wato ƙetare. Yakuma san bazai cutar da Aysha ba yasan tabbas taimaka mata zaiyi dan baya son abinda zai cutar da ita. A haka shima ya kira Arɗo Bani suka tattauna kana ya fara shirin tahowa. Ko Ummey bai gaya mata abinda ke faruwa ba. A can jihar Tsinako kuwa sha ɗaya dai-dai jirginsu Umaymah ya tashi ya nufi jihar Ɓadamaya. A cikin Rugar Bani kuwa. Tun shekaran jiya su Junaidu suka dawo gida. Alhamdulillah duk sun worke kuma har gida aka dawo dasu. Sosai Arɗo Bani da sauran dattawan sukayi mamakin jin Sheykh ne ya kaisu sibitinshi ya kuma kula dasu har suka samu lfy. Kana yayi musu komai ya dawo dasu lfy. Alhamdulillah kuma yanzu Rugar Bani basu da matsalar komai. dan ya rigada Allah yasa tsoron fulanin a zuƙatan Ɓacamawan. Yanzu kowa harkar shi yake ba kare bin damo. Suyi kiwonsu lfyta shanayensu nata habaƙa. Yanzu kuma sun maida hankali kan shuke-shuke amfanin gonakin su. Sabida shigowar damuna. A cikin masarautar Joɗa kuwa. Sheykh yana gama mgna da Bappa ya shiga bathroom. Cike da mamaki ya ɗan sunkuyo ya kalli boxes dake jikinsa, wanda dashi zaiyi wonka. hannunshi yasa ya damƙi bnnarshi da tun jiya da safe data harba ta miƙe ta tsaya ta rinƙa kumbura da cika da miƙewa tayi tsawo. Har yau har yanzu harbawa takeyi babu ƙaƙƙautawa yadda zuciyarshi ke harbawa haka itama. Kuma tana tsaye gam tamkar zata faso boxes ɗin ta fito woje. Shiyasa yake jin tsikar jikinshi yana zubawa. A hankali ya sakarwa kanshi ruwan sanyi, wanka yayi kana, ya fito ya kimtsa ya shirya jikinsa cikin manyan kayan. A falon kuwa Lamiɗo da Galadima da Sarkin bakan. Ne suka shigo bayan. Sallama yayi musu jagora. A bisa kujera Lamiɗo da suka zauna sarkin baka kuma a ƙasa. Hakama Ummi da Hibba. Jalal da Jamil kuwa tun ɗazu suka fita, suka tafi Side ɗin Mama. A can suka samu Ya Affan. Cikin girmamawa Ummi ta ɗan rusunar da kanta tare da cewa. "Barka da isowa Lamiɗo shugaba mai adalci". Kanshi ya jinjina tare da cewa. "Barka dai Jakadiya mai gsky, ya jikin ɗiyar taki, ina take". Cikin ƙara rusunar da kai tace. "To jiki dai da asuba da sauƙi amman kwana mukayi babu bacci. To rana na fitowa kuma ciwo ya harzuƙa ya zarta na baya". A hankali Lamiɗo da Galadima sukace "Subahanallahi". Sarkin baka kuwa. sunkuyar da kanshi yayi tare da sakin murmushin mugunta, kana ya gyara riƙon da yayiwa wayarshi yadda, waɗanda suka sashi aikin zasuji bayanin komai da kunnensu. da kiransu da ya haɗa. A can kuwa magautan dariyar jin daɗin lbrin. Sukayi. A hankali ya kalli Ummi yace. "Sauƙi a hankali yake samuwa, zai nayi yana lafawa har yazo ya bari gaba ɗaya". Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa. A hankali ta miƙe bayan Lamiɗo yace mata. "Jeki kira min ita tazo". To tace kana ta nufi shashin Sheykh. Shi kuwa Sheykh yana cikin fesa turare kenan. Ya juyo ya kalli Aysha da ta tashi zaune da sauri tasa hannu a kanta tana yarfa ɗaya tare da cewa. "Wash! Wash! Wayyoooooooo Allah na!'. A hankali ya ajiye kwalban turaren kana yazo gaban gadon. Tare da cewa. "Sauƙo". Cikin rawan jiki ta sauƙo tana yarfa hannunta. Cikin haɗe fuska yace. "In zakiyi kuka fice min a ɗaki". Cikin rauni tace. "Yah Sheykh zafi! zafi!! zafin nakeji yana dawowa". Da sauri ya juyo ya kalli ƙofar ɗakin jin ana bugawa. Jiyo muryar Ummi ne yasa ya juya ya nufi ƙofar. Yana buɗewa tace. "Sheykh, Lamiɗo ne yazo yana son ganin hannun nata". Kanshi ya ɗan gyaɗa kana yace. "Fito kije, Ummi a kawo mata ɗan kwali ta ɗaure wannan dogon gashin da kitseshi ma aikine shiyasa ko yaushe kai a tsefe ai kuwa al'janu kam sayi ta shiga lodi-lodi". Da sauri Ummi ta miƙo mishi ɗan kwalin doguwar rigarta dake hannunta tun sanda ta wurgar dashi. Kanshi ya juya tare da cewa. "Fito". Cikin zubda hawaye ta fito. Gaban Ummi ta tsaya tana cewa. "Wayyo Ummey na". Cikin tausaya mata Ummi tace. "Sannu ko". Ta ƙarishe mgnar tana yafa mata ɗan gyalen. Kana ta kama hannunta na hagu suka nufi falon. Shi kuwa Sheykh hiraminshi yasa ya dai-dai-ta komai. Sai dai abin da ya sashi jin kunyan kanshi da kanshi ganin. Har yanzu bnnarshi a tsaye ƙiƙam duk da danneta da yayi da boxes. shi da kanshi in ya sunkuyo yana ganin tudunta kaɗan danma manyan kayane a jikinsa. matseta yayi kana ya buɗe al'kyabbar da kyau, sannan ya fito ya nufi falon yanajin yadda take harbawa duk da kai tsaye bawai sha'awa yakeji ko makamancin hakaba. Wayarshi ce kaɗai a hannunshi ya fito. A falon ya samesu tana zaune gaban Lamiɗo da Galadima. Gefensu ya zauna. Sarkin bakan dake gabanta yana kwaɓa mgnine ya kalla tare da cewa. "A bar wannan mgin haka, kada a sake shafawa". Cike da mamaki Sarkin bakan ya ɗago ya kalleshi tare da cewa. "Sabida me?". Idonshi na kan wayarshi yace. "Nace kada a shafa ko". Lamiɗo ne ya juyo ya kalleshi tare da cewa. "Za'a shafa". Shi kuwa Sarkin baka ido ya zura musu. Shi kuwa Sheykh miƙewa tsaye yayi tare da cewa. "Shike nan!". Ya ƙarishe mgnar da kallon hannun Aysha mai ciwon. Kana ya juya ya kalli Ummi tare da cewa. "Bari in ɗauko Umaymah ta iso". Da sauri Hibba ta miƙa tare da bin bayanshi tana cewa. "Hamma Jabeer inzo muje". Kai ya gyaɗa mata, kana suka fita. Ummi na ce musu. "Allah ya kiyaye hanya". Amin Amin sukace sannan suka fice. Ita kuwa Aysha zuwa yanzu ta fara gigicewa. Sai mutsu-mutsu takeyi, tare da shishita. Galadima ne ya kalli Sarkin baka yace. "Kayi aikinka!". To yace kana ya fuskanceta da kyau yace. "Kawo hannunki". Jiki na rawa ta miƙa mishi hannun tana mai lumshe idonta hawaye na zubowa. "Sannu ko Mamana". Lamiɗo ya faɗa cikin tausayawa sabida sunan mahaifiyarshi Aysha. Ummi ma sannu ta mata. Shi kuwa Sarkin bakan da yawa ya daƙumo maganin ya labta a kan hannun. Sannan ya fara shafawa. Wani irin zillo tayi tare da sunkuyar da kanta ta kifeshi kan hannun kujerar da Lamiɗo ke kai. Gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi tamkar mazari. A haka ya gama shafe magungunan sannan ya bata wani yace sai dare ta shanye shi. Ummi ce ta amsa tare da yi mishi godiya. Kana Lamiɗo da Galadima sukayi mata sannu da jiki suka tafi. Suna fita, ta miƙe da sauri ta nufi falon ta. Da sauri Ummi ma tabi bayanta tana cewa. "Lafiya kuwa." Babu mgna tana shiga kan gado ta faɗa ta kife kanta a filo murya na rawa alamun sanyin zazzaɓi tace. "Ummi rufeni rufeni sanyi zai kasheni a kashe min AC." Da sauri ta ajiye maganin kana ta rufeta da jibgegen blanket ɗin sannan ta juya ta kashe AC'n. Ta dawo gefenta ta tsaya. Cikin al'hini take cewa. "Sannu! Sannu ko Aysha". Ina babu mgna sai karkarwa takeyi tamkar zata faɗo ƙasa. Haka yasa hankalin Ummi tashi. Shigowar Aunty Juwairiyya ce da ta kawo musu abincin rana. Dana tarban Umaymah ne. Cikin mamaki tace. "Ummi ko dai in kira. Sheykh yazo muje asibitine gafa yadda take rawan sanyi". Ummi kam tama rasa bakin mgn, shiru kawai tayi tana riƙe da haɓa. Suna cikin hakane Hajia Mama ta iso. Cikin tashin hankali tace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun. Ummin Jabeer ya za'ayi da wannan yariyar ne? Mu tafi asibiti fa, da sauri ta juya ta fita zata kirawo Affan. Tana fita da miti bakwai. Su Umaymah suka shigo. Kai tsaye suka wuce har cikin ɗakin jiyo mgnar su Ummi a can. Shi kuwa Sheykh, asibitin Valli ya wuce. Umaymah na shiga ta isa bakin gadon. Zama tayi a gefe tare dasa hannu ta buɗe borgon. Ganin yadda taketa karkarwa ne, yasa Umaymah ɗagota ta ɗaura kanta bisa cinyarta. Tana cewa. "Innalillahi wannan wane irin sabon al'amari ne mai firgitarwa". Da sauri tace. "Hibba kiyi gudu ki kirawo min Jazlaan kada ya fita." Da sauri Hibba ta juya ta nufi waje. Ita kuwa Ummi da Aunty Juwairiyya ko sannu da zuwa Allah bai basu ikon yiwa Umaymah ba sabida ruɗani. Wani irin numfarfashi ta fara fiddawa a jere-a jere sai ga jikinta ya fara lafawa da rawan da yakeyi. Wani irin zufa ya fara tsastsafo mata duk ta inda hudar gashi yake a jikinta. Cikin sanyi suka fara sauƙe ajiyan zuciya. Suna cewa. "Alhamdulillah". Gyara mata konciya Umaymah tayi ganin tayi bacci. Buɗe mata borgon tayi kana ta kalli Juwairiyya tare da cewa. "Kunna AC". To tace kana ta kunna. Ajiyan zuciya ta sauƙe da ƙarfi. Haka yasa Umaymah ta sauƙo kan gadon. Cike da al'hinin abin suka fito falonta suka zauna. Juwairiyya ce taja jakar Umaymah ta kai ɗakin Ummi. Kana ta fito. Cikin sanyi Ummi tace. "Umaymah sannu da zuwa ya hanya". Tallaɓe habarta tayi tare da cewa. "Uhummmm Alhamdulillah Ummi ya mai jiki". Cikin sanyi tace. "To jiki kam dai babu daɗi. Sai dai godiyar Allah". Cikin sanyi tace. "Dukkan tsanani yana tare da sauƙin. Ya iyayenta sunji ko?". Kai ta gyaɗa alamun eh. Juwairiyya ce taje falon ta kawo mata ruwa da abinci. A hankali tace. "Juwairiyya ajiye abin cinnan bazai ciwuba". Dai-dai lokacin Hajia Mama ta shigo da Affan yana cikin kiɗima. Ganin Umaymah ne yasa suka zaune kusa da ita tare da cewa. "Ya jikin nata". "Alhamdulillah ta samu tayi bacci." Umaymah ta basu amsa. Cikin kula Hajia Mama tace. "Sannunki da zuwa, ya hanya". Yauwa sannu Alhamdulillah tace. Hibba ce ta dawo tacewa Umaymah kafin ta fitama ya tafi. To kawai tace. Daga nan suka zauna suna al'hinin abin. Har azahar tayi nan suka watse kowa taje tayi salla. Ita Umaymah a ɗakin Aysha tayi salla. Bayan sunyi sallan ne Ummi ta kawo musu abinci suka ɗan ci. A nan suka zauna Ummi da Umaymah a ɗakin Aysha. Juwairiyya kuma taja Hibba suka tafi dan yin girkin dare. Haka suka zauna har la'asar bata tashiba. Sheykh kuwa sai ƙarfe biyar na yamma ya dawo gida daga asibitinshi. Nasa falone ya wuce Side ɗinsa kai tsaye. Biyar da miti bakwai dai-dai ta farka daga nannauyan baccin azabar. Da sauri Umaymah tayi kanta. Ganin tana ƙoƙarin tashine yasa Umaymah taimaka mata. Cikin disashewar muryar tace. "Lah Umaymah yaushe kikazo? Sannu da zuwa". Cikin tausaya mata tace. "Sannu Aysha ai ke za'a cewa sannu. Ya jikin naki". Cikin sanyi tace Alhamdulillah". Sai kuma ta zuro ƙafafuwan ƙasa tare da cewa. "Umaymah zanyi salla zanyi wonka". To tace da sauri kana ta juya zata shiga bathroom ɗin. Da sauri Ummi tace bari in haɗa mata ruwan wonka." Umaymah kuwa kamota tayi ta tsayar da ita. Dai-dai lokacin Ummi ta fito hannun ta zubawa ido cikin sanyi tace. "Ya naga kamar hannun ya ƙara kumɓura ne?". Kallon hannun sukayi a tare. Cikin sanyi tace. "Eh kamar ya ƙara kumɓura". Umaymah ce ta ɗan kalli hannun kana tace. "Je kiyi wonka ki fito kizo kiyi salla kici abinci, in baki mgnin da nazo miki dashi." To tace kana ta nufi Bathroom ɗin tana cewa. "Bana iya gogo sosa a jikina sai sabulu kawai. Shiyasa nakeji kamar ba wonka nakeyi ba". Cikin tausayawa Ummi tace. "Allah sarki in kin samu lfy dai shike nan". A haka ta shiga bathroom ɗin yau ko sabulun bata iya gogashi da kyauba. Ita kuma Ummi kaya ta fito mata dashi kamar kullum. Ita kuwa Umaymah Dinning area taje. Ta ɗauko Foodflaks ɗin da plate ta dawo nan. A hankali ta fito bathroom ɗin. Cikin ɗaga hannun sama ta kalli rigar da aka fito mata dashi a hankali tace. "Ummi bazan iya sashi ba, matsastsene a bani mai faɗi". To Ummi tace ta sauya mata wani. Mai faɗin ita kuwa dogon wondon dake kan gado ta ɗauka ta koma bathroom ta saka da kyar sannan ta fito. Koda Ummi ta bata rigar sai ta gaza sata. Ido cike da hawaye tace. "Ummi samun hannun rigar a hannu mai ciwon a hankali kada ya taɓa shi, sai kin buɗashi da hannu biyu. Cikin sanyi Umaymah tace. "Bakisa bra ɗinba". Kanta ta sunkuyar tare da cewa. "Bazan iyaba". Shiru Umaymah tayi tana tunanin dole jinyar hannu sai da mataimaki. Ita da Ummi kuma surkaine Hibba ƙaramace. Shiru dai tayi tana nazari. Bayan Ummi ta taimaka mata tasa rigar ne. Ta saka hijabi tayi sallan a daddafe da taimakon lafiyayyan hannun. Tana idarwa Umaymah tasa mata abinci a plate kasan cewar tuwone da miyar ganye da ɗan tsami. Sai ya zama gaba ɗaya a kaikaice take sa spoon ɗin da niyar gutsuro tuwon. Kuma taji tana son cin miyar. Da kyar ta gutsuro gaya ta ɗan ɗebi miya ta ɗaya zata kaishi bakinta kenan ya faɗi a jikinta. A hankali ta kallesu cikin sanyi tace. "Umaymah a bani tea kawai bazan iya cin wannan ba, zai tazubewa." Da sauri Ummi ta gyara zama tare da cewa. "To matso in baki". Ɗan gajeren murmushi tayi cikin jin kunya tace. "A a bari in sake gwadawa to". Dai-dai lokacin Sheykh da Umaymah ta kirashi a waya ya shigo yanata buɗe al'kyabbar jikinshi gudun kada a iya ganin tudun abinda yake ɓoyewa. A bakin ƙofar ya tsaya tare da yin sallama. Cikin ɗan ɗaga murya Umaymah tace. "Shigo". A hankali ya tura ƙofar ya shigo. Tunda tazo gidan tsawon watanni biyu kenan yanzu bai taɓa tako ƙafarsa nan ba sai yanzu. Ta gefen ido ya kalleta ta sake ɗaukan loma a karo na uku kafin ta kaishi bakinta ya ɓare. Ture plate ɗin tayi tare da cewa. "Bana iya cin abu da hagu gwara tea zan iya kafa kofin insha wani wani ya ɗan zube". Ta ƙarishe mgnar tana shere hawayen da suka zuba mata. A hankali Ummi taja flaks ta fara haɗa mata tea. Umaymah kuwa. Gefenta kan Bedside drower'n ta nuna mishi tare da cewa. "Zauna". fuska ya ɗan kauda kana ya zauna. A hankali tace. "Me zamuyi kan hannun yarinyar nanne?". Cikin jin haushi yace. "Sai abinda su Lamiɗo sukace ai. Ni Ko nayi mgna sai sun musamin ya rigada sun maidani kamar sa'ansu, bani da ancin mgn kan komai nawa sai yadda suka tsara min in naƙi bin unarninsu keda Abba kuyi faɗa, to ya zanyi?". Murmushi Ummi tayi ganin yadda yayi mgnar a tsare kamar shine babba a kansu ba suba wai sun ɗauke shi sa'ansu. Ita kuwa Umaymah cikin sanyi tace. "Kaga bata iya ko cin abinci tana bukatar kulawa ta musamman. Wonka ma wuya yake bata haka al'wala ko kaya sai an saka mata". A hankali yace. "Toh lallai kam Allah ya baku ladan jinya". Kai ta jinjina tare da cewa. "Amin". A ranta kuma tace. "Zanyi mgninka". Ganin tayi shiru ne ya sashi miƙewa tare da cewa. "Allah ya sauwaƙa kana ya fita." Yana mai jin zafin katsalandar dasu Lamiɗo ke mishi a kan lamuran rayuwarshi, komai nashi sai sun saka mishi baki. Yace kar asa mgnin amman dan rainin wayo sunce dole sai an saka. Su Umaymah kuwa nan suka zauna har akayi sallan magriba. Su Jalal Jamil Affan sukazo suka ci abinci aka ɗanyi hira dasu. Har zuwa ƙarfe goma na dare hannun shiru ba ciwon sosai. Haka kowa ya shiga yana cemata saida safe Allah ƙara sauƙin. Umaymah tace Ummi ta tafi da Hibba ɗakinta ita zasu kwana tare. Haka kuwa akayi, har sun fara bacci. Habawa sha ɗaya dai-dai, Ciwo yace salamu alaikum. Tashin hankali iya tashin hankali Umaymah ta ganshi a ranan. Domin har gabanin asuba basu rintsaba kamar dai yadda ta kwana jiya da Ummi abinma har yafi haka yau. Sau biyar Umaymah na kiran layukanshi duka basa shiga. Kuma Aysha guduwa kawai take nufa. Haka yasa dole tai ta riƙe ta. Asuba na ƙaratowa tayi bacci kamar na jiya. Sai da akayi sallan Umaymah ta tada ita. Tayi salla lfy tasha tea. ta koma bacci rana na fitowa ciwo ya dawo. Gaba ɗayansu sun gigice sun tsorita da lamarin Umaymah ta tura Ummi taje ta gayawa Lamiɗo yazo yaga yadda take. Hibba kuwa da Saratu sun kasa yin aikin da aka sasu sai kuka. Hannun kuma yau yayi biyun na jiya. Idanunta sun kaɗa sunyi jazir. tana zaune kan kujera Umaymah na tsaye gefenta gudun kadda ta arce. Ta ɗaura hannun a kai tana kuka iya kuka, kukan azaba haɗe da salati. A haka Sheykh ya shigo ya samesu. Cikin takaici Umaymah ta juya ta nufi falon Ayshan tana kallonshi tana cewa. "Gata ka barta kada ka kula da jinyarta da haƙƙinta ne Allah ya rataya a kan wuyanka ai ka fini sani. Ka sani kana take sani". Ta ƙarishe mgnar tana zubda hawaye sabida duk wanda yaji kukan da Aysha keyi yasan na wahala ne. Ita kuwa Aysha da sauri ta miƙe ta kife kanta jikin gini tana mai ci gaba da kuka. Jamil, Jalal, Affan, sunata yi mata sannu. A hankali yabi bayan Umaymah da kallo tabbas ranta yayi matuƙar ɓaci, ga tashin hankali ga rashin bacci. A hankali ya isa inda take. Hannunshi yasa ya kamo nata. Da sauri ta ɗago jajayen idanunta ta kalleshi, cikin zubda zafafan hawaye tare da cewa. "Yah Sheykh zafi, hannuna zai tsinke." Wani irin masifeffen rauni da tausayinta ne yaji sun rufeshi, kanshi ya juya cikin sanyi, yaja hannuntan. Suka nufi ɗakishi. Ita dai binshi a baya takeyi tana tafiya kamar a sama takejin kanta. Kai tsaye har bedroom ya wuce da ita. Kan gadonshi ya ajiyeta yanajin kukanta na hawa kanshi. Bakin gadon ya zauna ya bata baya tare da cewa. "Ki kwanta kiyi addu'a zakiji sauƙi." Ba jinshi takeyi ba bare ta gane abinda yake nufi. Da sauri ta yunƙura zata sauƙa. Juyowa yayi ya kamata ya ajiyeta kusa dashi kana ya juyo suna fuskantar juna. Cikin kuka ta faɗa jikinshi tana cewa. "Umaymah hannu zai tsinke. Zafi zai kasheni". A hankali ya ruggumeta tare dasa hannunshi ya kamo hannun dake ciwon. Da sauri tayi tsalle zata zille hakan ne yasa ya ƙara ruggumeta gama ya haɗa jikinsu wuri ɗaya. cikin sanyi ya fara mata karatu a kunne yana hura mata iskar bakinshi kan hannun Ajiyan zuciya mai ƙarfi da numfarfashi ta fara sauƙewa da ƙarfi-ƙarfi. Umaymah kuwa jin shirune yasa, ta nufo Side ɗinsa. Ganin baya falone. Tace. "To ina suke ina ya kaita?". Ta ƙarishe mgnar tana tura ƙofar Bedroom. Tana tura ƙofar sai kuma tayi sauri taja da baya sabida hangosu da tayi yana konce lib yayi rigingine ya ɗan jingina da allon kan gadon. Kana ita kuma ya kontar da ita kan jikinshi, ya ɗaura kanta bisa ƙirjinshi hannunshi na kan...! Jinyar Sheykh ta musamman ce. To ya zata kaya ne in ɗan gidan ba'ana yazo. Hege Sarkin baka wa yakewa aikin. By *GARKUWAR FULANI* Ya ruggumeta da kyau a jikinshi. Jinyadda taketa fizge-fizgen zata kwance kanta. Wani irin tsuma jikinshi ya rinƙayi can cikin naman jikinshi yake jin tsuman. A hankali ya manna kanta, kan faffaɗan ƙirjinshi, hannunta mai ciwon data ɗaura a tsakiyar kan natane ya zubawa ido. Sosai hannun yayi jazir sai kelli yaki, alamun kumburin da yayi. A hankali yasa hannunshin ya tallabo hannun. Wani irin ihu tasaka da ƙarfi. Sai dai bai bari ihun ya fito daga bakinta ba, yayi maza ya rufe mata baki da tattausan tafin hannunshi yana ta mai-maita. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". Tabbas da in ya barta ta kurma ihun shike nan ta tabbata zautacciya, yin ihun da take son yi dai-dai yake da sihirin ya gama shiga jikinta ya ratsa zai kuma haukatata. Shiru tayi tana zazzare idanunta da hawaye ke zuba babu ƙaƙƙautawa, shi kuwa Sheykh a hankali ya janye hannun nata data aza a kai ya tallabeshi da tafin hannunshi. Sannan ya manna ƙirjinshi da nata ƙirjin da kyau. Har suna iya juyo bugun zuciyar juna. Sunkuyo da kanshi yayi tsakanin kafaɗarta da wuyatan Bakinshi ya saita cikin kunnenta. Hure gashin daya baje kan kunnen yayi ya matsa, sannan ya kawo bakinshi gab da kunnenta har tattausan lips ɗinshi na taɓa tattausan kunnenta. Lumshe idonshi yayi tare da gyara tsayuwar nasu da kyau. Ita kuma sai fiffizgewa take sonshi jikinta duk yana karkarwa ga zufar dake tsiyayo mata. Hannunta dake cikin hannunshi ya kalla yadda yaketa rawa, gashi zafi jau kamar wuta. A hankali yayi gyaran murya tare da yin bisimilla. Cikin ɗan-ɗaga sauti ya fara karanta Suratul Baqra cikin kunnenta cikin fidda harrufan da karsashin yadda zai ratsa kunnuwanta. Yanashi yana cire tafin hannunshi dake bakinta, wani irin manna kanta tayi da ƙirjinsa, ta lumshe idonta wasu hawaye masu ɗumi suka fara kwaranya. hannunta na hagu dake da lfyar tasa bisa kafaɗanshi ta zagayo wuyanshi da kyau. Shi kuma hannunshi da ya janye daga kan bakinta ya maida kan ƙugunta ya ruggumeta tsam a jikinshi. A haka yaci gaba da karatu, in yazo wasu ayoyin yakan maimaita karshensu kafin ya kuma kama forkon na gaba. A hankali ta fara sauƙe wasu tagwayen numfarfashi, ji takeyi azaba da raɗaɗin yana ɗan lafawa. *Al'farma Annabi da Alqur'ani kenan.* A hankali ta daina duk fizge-fizgen ta dawo sai kukan da takeyi mai sauti amman sautin a hankali ne. Kuka take sosai ganin hakane, ya gyara tsayuwar tasu. Kana ya tallabo kanta ya kalleta. A hankali ya girgiza kanshi tare da jawota suka nufi bakin gado. Yana cewa. "Uhummm baku samu wurin zamaba a kanta in Sha Allah bazamu zauna inuwa ɗaya dani da kuba, zaku bar jikinta." Ajiyeta yayi kan gadon kana shima ya hau ya zauna. da sauri ya riƙo hannunta da take son maidashi tsakiyar kanta ɗin. Karatu ya fara yanayi yana ɗan hura mata sassanyan iskan bakinshi. Tub, tub, tub, haka yake ɗanyi tare da fesa iskar, kana ya zuba mata ido cikin idanunta. A hankali tayi ƙasa da kanta. Shi kuwa haɗe fuska yayi tare da cewa. "Ɗago ki kalleni mana". Kai ta girgiza alamun a a. Shikuwa hannunshi ɗaya yasa ya tallabo haɓarta, dan ta kalleshi da sauri ta rumtse idanunta. Cikin kausasa murya yace. "Buɗe idon ki kalleni!". A hankali ta buɗi baki cikin irin Muryar da yaji tayi mgna kwanaki dashi tace. "Bazan iyaba, kunyarka nakeji!". Watsa mata wani kallo yayi tare da cewa. "Ƙarya ne, bakiji kunyan Allah'n daya haliccemu ya halicceku ya kuma yi mana iyaka a tsakaninmu ya hanaku cutar damu, ta hanyar mazonsa ya ƙaiyade muku dukkan motsinku, ya hanaku cutar da bani Adam. Duk bakiji kunyarsu ba, kika shiga jikin yarinya ƙarama, kina sata yin wasu abun da ba halinta ba, bakiji tsoron Allah daya hanakuba. Bakiji kunyar iyayenta ba, kina cutar musu da ɗiyarsu sai ni?". Cikin sanyi murya cike da alamun tsufa, tace. "Ni bana cutar da ita, Ni ba muguwa bace, ban taɓata cutar da ita ko wani nataba duk tsawon shekarun da nake tare da ita". Da sauri cikin faɗa yace. "To meyasa zaki shiga jikinta". A hankali cikin zubda hawaye tace. "Ni tun tana jaririya nake jikinta, kuma ni makaran gadone na ahlinsu daga wurin kakarta mahaifiyar mahaifinta". Da sauri yace. "Rufe min baki, makaran gado, Ku kuɗine ko wata kadara ce, ku cikin kadarorin da Allah (S.W.A) ya lissafa cikin jerin jadawalin abinda za'a gada?. Ko dan kinga ina binki a hankali ne yasa zakiyi min zancen banza na mutanen banza". A hankali tace. "Jikana ka kontar da hankalinka muyi mgna". A fusace yace. "Waye jikan naki, kina Jinnu ina bani Adam ta ina na zama jikanki. An ƙi a kontar da hankali tsohuwa dake kinzo kin liƙewa yarinya kina ƙoƙarin sata tana yaye suturar jikinta tana shirin yin ihu. Ko baki san cewa matar aure bace, baki san daraja da kimar dake cikin aure bako?". Cikin fushi itama tace. "Ni bani nasata yarda kallabin kanta ba, zafin ciwo da takeji ne ya gigitata yasata yarda kalkabinta. Sannan batun ihu da kakeyi kuwa. Aikin da mugayen Masarautar Joɗa sukayi data taɓane yake shiga jikinta. Ni kuwa na zone sanadin karatun Rugyan da kayi ta mata, amman duk wancan abun da takeyi ni bana kusa ma. Kuma ni ba mai cutarwa bace. Batun darajar aure kuma na fika sani. Kai kama tsaya inda takene bare ka raya auren ka tabbatar da ita matarka ce kai mijinta ne?. Kasa sabgogi a gabanka, kana sane da magautanka sun saka a tsakiya kayi, burus dasu, suna neman rabaka da rayuwarka. Ita kuma dole in taimaketa sannan dama Aysha in dai bata da lfy ko zazzaɓi ne tana kuka haka ciwonta yake." Cikin haɗe fuska yace. "Eh wato da ban ƙonaki bane, kikemin baki ko. T taimako bana son taimakonki ki fitamin a jikin matata, bana so, zakisa tayi ihu ta fita tsakiyar masarauta bayan kin san inada magautan to meyasa zaki nemin abinda zaisa magautana farin ciki. Tai mako kuma bama so, muda mukeda ubangijin taliƙai wanda yasan zahiri da baɗinin shi yake taimaka min, ba tare da yasa mana ciwon kai ko fita haiyaci ko kukaba dan haka fice min a jikin matata". Murmushi tayi tare da jinjina kai kana tace. "Matarka kuma yau". A hatsale yace. "A a matarki ce, in ba matata ba?." Sai kuma yayi bisimilla zai fara karatu da sauri tace. "Tsaya Muhammad Jabeer ɗan Habibullah jikan Nuruddee, Bubayero, Joɗa, Sule Usmanu jinin sarki Muhammad Bello, ni bazanyi faɗa da kaiba kafi ƙarfin haka duk da ni ba cutar daku nakeyi ba. Naga ranka ya ɓaci ina jinin. Wai matarka kace ko?". Wani irin kallo yayi mata tare da ɗago hannun shi zai shararamata mari yana cewa. "Wai ne ma ko?". Da sauri tayi murmushi tare da cewa. "Kamar gibtawar ido zan gudu jikinta, ka kwaɗa marin a kanta". Ai fa a kufule ya kai marin. Hannunshi na isa fuskarta tana yin atishawa. Zafin marin ya sauƙa kan fuskarta cikin azaba ta ɓare baki tare dasa kuka tana mai shafa haɓarta ido na zubda hawaye a gigice idonta na ganin duhu sabida zafin marin bata gama dawowa haiyacinta ba murya na rawa tace. "Wayyo Allah na me nayi maka zaka mareni, ka barni inji da ciwo ɗaya mana". Hararanta yayi tare da miƙewa ya sauƙa gadon yana cewa. "Mutun jiki duk al'janu, sai hegen bakin rashin kunya mutun in ba lfy bazaiyi addu'a ba sai kuka". Ya ƙarishe mgnar da juyawa ya nufi falo. Ita kuwa Aysha wani irin bacci ne yayi awon gaba da ita, tana mai jin zafin hannun ya ɗan lafa sai kuma raɗaɗin marin. A can falon kuwa, wayar Aysha ne dake hannun Hibba yayi ringi. Bappa am. Shine sunan da ta gani a rubuce. Da sauri ta nunawa Ummi shi tare da cewa. "Ummi ana kiranta". A hankali tace ki ɗaga. Kai ta gyaɗa tare da amsa kiran ta kara wayar a kunnenta. Cikin nitsuwa tace. "Wa alaikassalam". Sai kuma tace. "A a Bappa ba Aysha bace. Hibba ce, Aunty Ayshan tana ɗakin Hamma Jabeer". Cikin dattaku Bappa yace. "To Hibba ya jikin nata?". A hankali tace. "Bappa hannunta kam yana ciwo sosai, ya kumbura yayi ja, in an taɓashi zafi kamar wuta, bata iya bacci". Da sauri tayi shiru ganin Ummi na girgiza mata kai alamu. Ta daina faɗa mishi hankalinsa zai tashi. Ila kuwa hakane, cikin tashin hankali da kiɗima yace. "Yanzu kai mata wayar maza, kai mata inji muryarta". A hankali ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi wai in Kai mata wayar". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Jekiyi sallama ki kai wayar". To tace kana ta juya ta nufi falonshi. Tana jin Bappa na cewa. Yi sauri". A falo ta samu Hamma Jabeer ɗin cikin sanyi tace. "Hamma Jabeer gashi Bappa am, na son yin mgna da Aunty Aysha". Hannunshi ya miƙa ya amshi wayar ba tare da yace komaiba. Ganin kiran bai yanke bane. Yasa ya zubawa number ido cike da mamaki ganin code number ɗin bana ƙasar Nigeria bane, na ƙasar Cameroon ne. a hankali ya kai wayar kunnenshi tare da cewa. "Assalamu alaikum". "Wa alaikassalam Jabeer ne?". A hankali cikin nitsuwa yace. "Eh Bappa nine, ina kwana ya gida". Cikin jin sanyi yace. "Lafiya lau Alhamdulillah. Ya jikin Shatu?". A hankali yace. "Alhamdulillah Bappa jiki da sauƙi sosai ma yanzu hakama tana bacci ne". Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah to Allah ya ƙara lfy, amman me yake faruwa da hannun ne?". Cikin sanyi ya miƙe ya nufi bedroom. A gaban gadon ya tsaya tare da cewa. "Hannun ya ɗan kumbura amman ba sosai ba, sai kuma yayi ja, sannan jikin hannun yayi zafi sosai". Cikin tausayawa ɗiyar tasa yace. "Amman kada ayi mata allura, sannan a nunawa masu maganin gargajiya hannun, ko dajine". A hankali yace. "Bappa ba daji bane an gwadata babu wani ciwo a jikinta. Kuma inma dajin ne yanzu akwai alluran shi. Matsalar hannun yana ɗan lafawa ya kuma tashi ne. In ya tashi kuma ihu take son yi. Kuma sai tayi ta kuka. To kukan ne ke sa mata zazzaɓi da ciwon kai". Cikin sanyi yace. "Allah sarki Shatu, haka take in bata da lfy. Zan zo jibi in sha Allah." Cikin hikimar nuna mishi ya fahimci inda yake tace. "To Bappa Allah ya kawoka lfy, daga gobe zaka taso ko?". Cikin nitsuwa yace. "In sha Allah". Kontar mishi hankali yayi kana suka katse kiran. Ba'ana kuwa duk abinda ke faruwa da Aysha yana gani a ƙwaryar tsafinshi. Amman muddin Sheykh yana wurin sai yaga wani haske ya rufe ƙwaryar gaba ɗaya sai ya kasa ganin komai a kanta. Yanzuma zaune yake yasa yaranshi a gaba. Da kuma sabon uban gida daya samu. Cikin fargaba da tausayawa Mata abinda ke damunta ya kalli ɗaya daga cikin yaransa wanda ɗan ƙabilar ɓachama ne, cikin waɗanda suka koro shanayen Bappa ne da Alhaji Haro. Cikin Ɓacamancin yace. "Barun zaka tafi ƙasar Nigeria ka wuce jihar Ɓadamaya kai tsaye har cikin masarautar Joɗa". Cikin tsoro Barun yace. "Masarautar Joɗa kuma, ta yaya to?." Numfashi ya fesar tare da cewa. "Duk magungunan da Sarkin bakan masarautar Joɗa yake saka mata da wanda zai sa mata nan gaba, duk na ruruta ciwon ne, sabida shi magautan Jabeer yakewa aiki, to kasan cewar bawai sihiri bane shiyasa Mata bazata ganeba, kawai maganin ingiza ciwon yake shafa mata. Sannan makarin ciwon Ni kaɗai nake dashi. To zan kira Bappa da layinka. In mishi jawabin ciwon da mgnin sannan zance mishi kai yau zaka kama hanya, dan taimaka mata, amman fa sai in zasu biya kuɗin jinyar da shanu hamsin". Cikin mamaki Barun yace. "Shanu hamsin mutumin da muka kwashewa komai ko ɗan tinkiya bamu bar mishiba, ina zai bada shanu hamsin". Murmushi Ba'ana yayi tare da cewa. "Uhumm baka san waye Malam Liman ba kenan Bappa baka san da waye yake tareba, baka san komai game da shiba. Kai dai bani inkirashi yanzu kaji." Da sauri ya miƙa masa wayar. Shi kuma ya dannawa Bappa kira. Yana katse kiranshi da Sheykh yaji wani kiran ya shiga wayarshi. Amsa kiran yayi tare da kara wayar a kunne. Sauya murya ba'ana yayi tare da cewa. "Ina mgn da Malam Liman ko baban Aysha mai ciwon hannu". Da mamaki Bappa yace. "Waye ne?". Ciki kaurara muryarshi yace. "Sarkin bakan nufe ne, bincike nane ya nuna min ciwon hannun yarka tana can masarautar Joɗa. An kawo wani sarkin baka yana mata mgni sai dai mugune magautansu yakewa aiki. In har zaku biyani ni Shanu hamsin zan je kuma zan mata aiki a take zataji sauƙin". Cikin sanyi Bappa yace. "To yanzu kai ina kake". A nitse yace. "Ni yanzu haka ina bakin iyakar ƙasar Nufe da Nigeria ne. Yau zuwa gobe zan shiga ƙasar". A hankali cikin sanyi Bappa yace. "To ba matsala, nima jibi zan shigo. Mu haɗu a can in dai kayi mata mgnin ta warke a take zan biyaka da abunda kace". Cikin jin daɗi yace. "To sai mun haɗu." Katse wayar yayi tare da cewa. "Alhamdulillah Shatuna zata samu lfy. Zan kuma samu shanu hamsin. Sannan zanji lbrinta, zaka kuma isarmin da manufata. Kunga na jefi tsuntsu biyar da dutse ɗaya." Jinjina mishi sukayi kana ya shiryawa Burun komai nagnin ya nuna mishi yadda zaiyi da yadda zai isar mishi da saƙonshi wurin Aysha. Bappa kuwa Murmushi yayi dan ya gane Muryar Ba'ana. Dama ya sani bazai rabu dasu haka a sauƙaƙeba yasani yanzu duk motsin Aysha yana tafin hannunshi. Abinda yasa ya yarda su haɗu kuma yasan ba shi da kanshi zai jeba. Sai dai ya wakilta wani. Ya kuma sani tabbas yanada makarin ciwon taɓen sihiri wato ƙetare. Yakuma san bazai cutar da Aysha ba yasan tabbas taimaka mata zaiyi dan baya son abinda zai cutar da ita. A haka shima ya kira Arɗo Bani suka tattauna kana ya fara shirin tahowa. Ko Ummey bai gaya mata abinda ke faruwa ba. A can jihar Tsinako kuwa sha ɗaya dai-dai jirginsu Umaymah ya tashi ya nufi jihar Ɓadamaya. A cikin Rugar Bani kuwa. Tun shekaran jiya su Junaidu suka dawo gida. Alhamdulillah duk sun worke kuma har gida aka dawo dasu. Sosai Arɗo Bani da sauran dattawan sukayi mamakin jin Sheykh ne ya kaisu sibitinshi ya kuma kula dasu har suka samu lfy. Kana yayi musu komai ya dawo dasu lfy. Alhamdulillah kuma yanzu Rugar Bani basu da matsalar komai. dan ya rigada Allah yasa tsoron fulanin a zuƙatan Ɓacamawan. Yanzu kowa harkar shi yake ba kare bin damo. Suyi kiwonsu lfyta shanayensu nata habaƙa. Yanzu kuma sun maida hankali kan shuke-shuke amfanin gonakin su. Sabida shigowar damuna. A cikin masarautar Joɗa kuwa. Sheykh yana gama mgna da Bappa ya shiga bathroom. Cike da mamaki ya ɗan sunkuyo ya kalli boxes dake jikinsa, wanda dashi zaiyi wonka. hannunshi yasa ya damƙi bnnarshi da tun jiya da safe data harba ta miƙe ta tsaya ta rinƙa kumbura da cika da miƙewa tayi tsawo. Har yau har yanzu harbawa takeyi babu ƙaƙƙautawa yadda zuciyarshi ke harbawa haka itama. Kuma tana tsaye gam tamkar zata faso boxes ɗin ta fito woje. Shiyasa yake jin tsikar jikinshi yana zubawa. A hankali ya sakarwa kanshi ruwan sanyi, wanka yayi kana, ya fito ya kimtsa ya shirya jikinsa cikin manyan kayan. A falon kuwa Lamiɗo da Galadima da Sarkin bakan. Ne suka shigo bayan. Sallama yayi musu jagora. A bisa kujera Lamiɗo da suka zauna sarkin baka kuma a ƙasa. Hakama Ummi da Hibba. Jalal da Jamil kuwa tun ɗazu suka fita, suka tafi Side ɗin Mama. A can suka samu Ya Affan. Cikin girmamawa Ummi ta ɗan rusunar da kanta tare da cewa. "Barka da isowa Lamiɗo shugaba mai adalci". Kanshi ya jinjina tare da cewa. "Barka dai Jakadiya mai gsky, ya jikin ɗiyar taki, ina take". Cikin ƙara rusunar da kai tace. "To jiki dai da asuba da sauƙi amman kwana mukayi babu bacci. To rana na fitowa kuma ciwo ya harzuƙa ya zarta na baya". A hankali Lamiɗo da Galadima sukace "Subahanallahi". Sarkin baka kuwa. sunkuyar da kanshi yayi tare da sakin murmushin mugunta, kana ya gyara riƙon da yayiwa wayarshi yadda, waɗanda suka sashi aikin zasuji bayanin komai da kunnensu. da kiransu da ya haɗa. A can kuwa magautan dariyar jin daɗin lbrin. Sukayi. A hankali ya kalli Ummi yace. "Sauƙi a hankali yake samuwa, zai nayi yana lafawa har yazo ya bari gaba ɗaya". Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa. A hankali ta miƙe bayan Lamiɗo yace mata. "Jeki kira min ita tazo". To tace kana ta nufi shashin Sheykh. Shi kuwa Sheykh yana cikin fesa turare kenan. Ya juyo ya kalli Aysha da ta tashi zaune da sauri tasa hannu a kanta tana yarfa ɗaya tare da cewa. "Wash! Wash! Wayyoooooooo Allah na!'. A hankali ya ajiye kwalban turaren kana yazo gaban gadon. Tare da cewa. "Sauƙo". Cikin rawan jiki ta sauƙo tana yarfa hannunta. Cikin haɗe fuska yace. "In zakiyi kuka fice min a ɗaki". Cikin rauni tace. "Yah Sheykh zafi! zafi!! zafin nakeji yana dawowa". Da sauri ya juyo ya kalli ƙofar ɗakin jin ana bugawa. Jiyo muryar Ummi ne yasa ya juya ya nufi ƙofar. Yana buɗewa tace. "Sheykh, Lamiɗo ne yazo yana son ganin hannun nata". Kanshi ya ɗan gyaɗa kana yace. "Fito kije, Ummi a kawo mata ɗan kwali ta ɗaure wannan dogon gashin da kitseshi ma aikine shiyasa ko yaushe kai a tsefe ai kuwa al'janu kam sayi ta shiga lodi-lodi". Da sauri Ummi ta miƙo mishi ɗan kwalin doguwar rigarta dake hannunta tun sanda ta wurgar dashi. Kanshi ya juya tare da cewa. "Fito". Cikin zubda hawaye ta fito. Gaban Ummi ta tsaya tana cewa. "Wayyo Ummey na". Cikin tausaya mata Ummi tace. "Sannu ko". Ta ƙarishe mgnar tana yafa mata ɗan gyalen. Kana ta kama hannunta na hagu suka nufi falon. Shi kuwa Sheykh hiraminshi yasa ya dai-dai-ta komai. Sai dai abin da ya sashi jin kunyan kanshi da kanshi ganin. Har yanzu bnnarshi a tsaye ƙiƙam duk da danneta da yayi da boxes. shi da kanshi in ya sunkuyo yana ganin tudunta kaɗan danma manyan kayane a jikinsa. matseta yayi kana ya buɗe al'kyabbar da kyau, sannan ya fito ya nufi falon yanajin yadda take harbawa duk da kai tsaye bawai sha'awa yakeji ko makamancin hakaba. Wayarshi ce kaɗai a hannunshi ya fito. A falon ya samesu tana zaune gaban Lamiɗo da Galadima. Gefensu ya zauna. Sarkin bakan dake gabanta yana kwaɓa mgnine ya kalla tare da cewa. "A bar wannan mgin haka, kada a sake shafawa". Cike da mamaki Sarkin bakan ya ɗago ya kalleshi tare da cewa. "Sabida me?". Idonshi na kan wayarshi yace. "Nace kada a shafa ko". Lamiɗo ne ya juyo ya kalleshi tare da cewa. "Za'a shafa". Shi kuwa Sarkin baka ido ya zura musu. Shi kuwa Sheykh miƙewa tsaye yayi tare da cewa. "Shike nan!". Ya ƙarishe mgnar da kallon hannun Aysha mai ciwon. Kana ya juya ya kalli Ummi tare da cewa. "Bari in ɗauko Umaymah ta iso". Da sauri Hibba ta miƙa tare da bin bayanshi tana cewa. "Hamma Jabeer inzo muje". Kai ya gyaɗa mata, kana suka fita. Ummi na ce musu. "Allah ya kiyaye hanya". Amin Amin sukace sannan suka fice. Ita kuwa Aysha zuwa yanzu ta fara gigicewa. Sai mutsu-mutsu takeyi, tare da shishita. Galadima ne ya kalli Sarkin baka yace. "Kayi aikinka!". To yace kana ya fuskanceta da kyau yace. "Kawo hannunki". Jiki na rawa ta miƙa mishi hannun tana mai lumshe idonta hawaye na zubowa. "Sannu ko Mamana". Lamiɗo ya faɗa cikin tausayawa sabida sunan mahaifiyarshi Aysha. Ummi ma sannu ta mata. Shi kuwa Sarkin bakan da yawa ya daƙumo maganin ya labta a kan hannun. Sannan ya fara shafawa. Wani irin zillo tayi tare da sunkuyar da kanta ta kifeshi kan hannun kujerar da Lamiɗo ke kai. Gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi tamkar mazari. A haka ya gama shafe magungunan sannan ya bata wani yace sai dare ta shanye shi. Ummi ce ta amsa tare da yi mishi godiya. Kana Lamiɗo da Galadima sukayi mata sannu da jiki suka tafi. Suna fita, ta miƙe da sauri ta nufi falon ta. Da sauri Ummi ma tabi bayanta tana cewa. "Lafiya kuwa." Babu mgna tana shiga kan gado ta faɗa ta kife kanta a filo murya na rawa alamun sanyin zazzaɓi tace. "Ummi rufeni rufeni sanyi zai kasheni a kashe min AC." Da sauri ta ajiye maganin kana ta rufeta da jibgegen blanket ɗin sannan ta juya ta kashe AC'n. Ta dawo gefenta ta tsaya. Cikin al'hini take cewa. "Sannu! Sannu ko Aysha". Ina babu mgna sai karkarwa takeyi tamkar zata faɗo ƙasa. Haka yasa hankalin Ummi tashi. Shigowar Aunty Juwairiyya ce da ta kawo musu abincin rana. Dana tarban Umaymah ne. Cikin mamaki tace. "Ummi ko dai in kira. Sheykh yazo muje asibitine gafa yadda take rawan sanyi". Ummi kam tama rasa bakin mgn, shiru kawai tayi tana riƙe da haɓa. Suna cikin hakane Hajia Mama ta iso. Cikin tashin hankali tace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun. Ummin Jabeer ya za'ayi da wannan yariyar ne? Mu tafi asibiti fa, da sauri ta juya ta fita zata kirawo Affan. Tana fita da miti bakwai. Su Umaymah suka shigo. Kai tsaye suka wuce har cikin ɗakin jiyo mgnar su Ummi a can. Shi kuwa Sheykh, asibitin Valli ya wuce. Umaymah na shiga ta isa bakin gadon. Zama tayi a gefe tare dasa hannu ta buɗe borgon. Ganin yadda taketa karkarwa ne, yasa Umaymah ɗagota ta ɗaura kanta bisa cinyarta. Tana cewa. "Innalillahi wannan wane irin sabon al'amari ne mai firgitarwa". Da sauri tace. "Hibba kiyi gudu ki kirawo min Jazlaan kada ya fita." Da sauri Hibba ta juya ta nufi waje. Ita kuwa Ummi da Aunty Juwairiyya ko sannu da zuwa Allah bai basu ikon yiwa Umaymah ba sabida ruɗani. Wani irin numfarfashi ta fara fiddawa a jere-a jere sai ga jikinta ya fara lafawa da rawan da yakeyi. Wani irin zufa ya fara tsastsafo mata duk ta inda hudar gashi yake a jikinta. Cikin sanyi suka fara sauƙe ajiyan zuciya. Suna cewa. "Alhamdulillah". Gyara mata konciya Umaymah tayi ganin tayi bacci. Buɗe mata borgon tayi kana ta kalli Juwairiyya tare da cewa. "Kunna AC". To tace kana ta kunna. Ajiyan zuciya ta sauƙe da ƙarfi. Haka yasa Umaymah ta sauƙo kan gadon. Cike da al'hinin abin suka fito falonta suka zauna. Juwairiyya ce taja jakar Umaymah ta kai ɗakin Ummi. Kana ta fito. Cikin sanyi Ummi tace. "Umaymah sannu da zuwa ya hanya". Tallaɓe habarta tayi tare da cewa. "Uhummmm Alhamdulillah Ummi ya mai jiki". Cikin sanyi tace. "To jiki kam dai babu daɗi. Sai dai godiyar Allah". Cikin sanyi tace. "Dukkan tsanani yana tare da sauƙin. Ya iyayenta sunji ko?". Kai ta gyaɗa alamun eh. Juwairiyya ce taje falon ta kawo mata ruwa da abinci. A hankali tace. "Juwairiyya ajiye abin cinnan bazai ciwuba". Dai-dai lokacin Hajia Mama ta shigo da Affan yana cikin kiɗima. Ganin Umaymah ne yasa suka zaune kusa da ita tare da cewa. "Ya jikin nata". "Alhamdulillah ta samu tayi bacci." Umaymah ta basu amsa. Cikin kula Hajia Mama tace. "Sannunki da zuwa, ya hanya". Yauwa sannu Alhamdulillah tace. Hibba ce ta dawo tacewa Umaymah kafin ta fitama ya tafi. To kawai tace. Daga nan suka zauna suna al'hinin abin. Har azahar tayi nan suka watse kowa taje tayi salla. Ita Umaymah a ɗakin Aysha tayi salla. Bayan sunyi sallan ne Ummi ta kawo musu abinci suka ɗan ci. A nan suka zauna Ummi da Umaymah a ɗakin Aysha. Juwairiyya kuma taja Hibba suka tafi dan yin girkin dare. Haka suka zauna har la'asar bata tashiba. Sheykh kuwa sai ƙarfe biyar na yamma ya dawo gida daga asibitinshi. Nasa falone ya wuce Side ɗinsa kai tsaye. Biyar da miti bakwai dai-dai ta farka daga nannauyan baccin azabar. Da sauri Umaymah tayi kanta. Ganin tana ƙoƙarin tashine yasa Umaymah taimaka mata. Cikin disashewar muryar tace. "Lah Umaymah yaushe kikazo? Sannu da zuwa". Cikin tausaya mata tace. "Sannu Aysha ai ke za'a cewa sannu. Ya jikin naki". Cikin sanyi tace Alhamdulillah". Sai kuma ta zuro ƙafafuwan ƙasa tare da cewa. "Umaymah zanyi salla zanyi wonka". To tace da sauri kana ta juya zata shiga bathroom ɗin. Da sauri Ummi tace bari in haɗa mata ruwan wonka." Umaymah kuwa kamota tayi ta tsayar da ita. Dai-dai lokacin Ummi ta fito hannun ta zubawa ido cikin sanyi tace. "Ya naga kamar hannun ya ƙara kumɓura ne?". Kallon hannun sukayi a tare. Cikin sanyi tace. "Eh kamar ya ƙara kumɓura". Umaymah ce ta ɗan kalli hannun kana tace. "Je kiyi wonka ki fito kizo kiyi salla kici abinci, in baki mgnin da nazo miki dashi." To tace kana ta nufi Bathroom ɗin tana cewa. "Bana iya gogo sosa a jikina sai sabulu kawai. Shiyasa nakeji kamar ba wonka nakeyi ba". Cikin tausayawa Ummi tace. "Allah sarki in kin samu lfy dai shike nan". A haka ta shiga bathroom ɗin yau ko sabulun bata iya gogashi da kyauba. Ita kuma Ummi kaya ta fito mata dashi kamar kullum. Ita kuwa Umaymah Dinning area taje. Ta ɗauko Foodflaks ɗin da plate ta dawo nan. A hankali ta fito bathroom ɗin. Cikin ɗaga hannun sama ta kalli rigar da aka fito mata dashi a hankali tace. "Ummi bazan iya sashi ba, matsastsene a bani mai faɗi". To Ummi tace ta sauya mata wani. Mai faɗin ita kuwa dogon wondon dake kan gado ta ɗauka ta koma bathroom ta saka da kyar sannan ta fito. Koda Ummi ta bata rigar sai ta gaza sata. Ido cike da hawaye tace. "Ummi samun hannun rigar a hannu mai ciwon a hankali kada ya taɓa shi, sai kin buɗashi da hannu biyu. Cikin sanyi Umaymah tace. "Bakisa bra ɗinba". Kanta ta sunkuyar tare da cewa. "Bazan iyaba". Shiru Umaymah tayi tana tunanin dole jinyar hannu sai da mataimaki. Ita da Ummi kuma surkaine Hibba ƙaramace. Shiru dai tayi tana nazari. Bayan Ummi ta taimaka mata tasa rigar ne. Ta saka hijabi tayi sallan a daddafe da taimakon lafiyayyan hannun. Tana idarwa Umaymah tasa mata abinci a plate kasan cewar tuwone da miyar ganye da ɗan tsami. Sai ya zama gaba ɗaya a kaikaice take sa spoon ɗin da niyar gutsuro tuwon. Kuma taji tana son cin miyar. Da kyar ta gutsuro gaya ta ɗan ɗebi miya ta ɗaya zata kaishi bakinta kenan ya faɗi a jikinta. A hankali ta kallesu cikin sanyi tace. "Umaymah a bani tea kawai bazan iya cin wannan ba, zai tazubewa." Da sauri Ummi ta gyara zama tare da cewa. "To matso in baki". Ɗan gajeren murmushi tayi cikin jin kunya tace. "A a bari in sake gwadawa to". Dai-dai lokacin Sheykh da Umaymah ta kirashi a waya ya shigo yanata buɗe al'kyabbar jikinshi gudun kada a iya ganin tudun abinda yake ɓoyewa. A bakin ƙofar ya tsaya tare da yin sallama. Cikin ɗan ɗaga murya Umaymah tace. "Shigo". A hankali ya tura ƙofar ya shigo. Tunda tazo gidan tsawon watanni biyu kenan yanzu bai taɓa tako ƙafarsa nan ba sai yanzu. Ta gefen ido ya kalleta ta sake ɗaukan loma a karo na uku kafin ta kaishi bakinta ya ɓare. Ture plate ɗin tayi tare da cewa. "Bana iya cin abu da hagu gwara tea zan iya kafa kofin insha wani wani ya ɗan zube". Ta ƙarishe mgnar tana shere hawayen da suka zuba mata. A hankali Ummi taja flaks ta fara haɗa mata tea. Umaymah kuwa. Gefenta kan Bedside drower'n ta nuna mishi tare da cewa. "Zauna". fuska ya ɗan kauda kana ya zauna. A hankali tace. "Me zamuyi kan hannun yarinyar nanne?". Cikin jin haushi yace. "Sai abinda su Lamiɗo sukace ai. Ni Ko nayi mgna sai sun musamin ya rigada sun maidani kamar sa'ansu, bani da ancin mgn kan komai nawa sai yadda suka tsara min in naƙi bin unarninsu keda Abba kuyi faɗa, to ya zanyi?". Murmushi Ummi tayi ganin yadda yayi mgnar a tsare kamar shine babba a kansu ba suba wai sun ɗauke shi sa'ansu. Ita kuwa Umaymah cikin sanyi tace. "Kaga bata iya ko cin abinci tana bukatar kulawa ta musamman. Wonka ma wuya yake bata haka al'wala ko kaya sai an saka mata". A hankali yace. "Toh lallai kam Allah ya baku ladan jinya". Kai ta jinjina tare da cewa. "Amin". A ranta kuma tace. "Zanyi mgninka". Ganin tayi shiru ne ya sashi miƙewa tare da cewa. "Allah ya sauwaƙa kana ya fita." Yana mai jin zafin katsalandar dasu Lamiɗo ke mishi a kan lamuran rayuwarshi, komai nashi sai sun saka mishi baki. Yace kar asa mgnin amman dan rainin wayo sunce dole sai an saka. Su Umaymah kuwa nan suka zauna har akayi sallan magriba. Su Jalal Jamil Affan sukazo suka ci abinci aka ɗanyi hira dasu. Har zuwa ƙarfe goma na dare hannun shiru ba ciwon sosai. Haka kowa ya shiga yana cemata saida safe Allah ƙara sauƙin. Umaymah tace Ummi ta tafi da Hibba ɗakinta ita zasu kwana tare. Haka kuwa akayi, har sun fara bacci. Habawa sha ɗaya dai-dai, Ciwo yace salamu alaikum. Tashin hankali iya tashin hankali Umaymah ta ganshi a ranan. Domin har gabanin asuba basu rintsaba kamar dai yadda ta kwana jiya da Ummi abinma har yafi haka yau. Sau biyar Umaymah na kiran layukanshi duka basa shiga. Kuma Aysha guduwa kawai take nufa. Haka yasa dole tai ta riƙe ta. Asuba na ƙaratowa tayi bacci kamar na jiya. Sai da akayi sallan Umaymah ta tada ita. Tayi salla lfy tasha tea. ta koma bacci rana na fitowa ciwo ya dawo. Gaba ɗayansu sun gigice sun tsorita da lamarin Umaymah ta tura Ummi taje ta gayawa Lamiɗo yazo yaga yadda take. Hibba kuwa da Saratu sun kasa yin aikin da aka sasu sai kuka. Hannun kuma yau yayi biyun na jiya. Idanunta sun kaɗa sunyi jazir. tana zaune kan kujera Umaymah na tsaye gefenta gudun kadda ta arce. Ta ɗaura hannun a kai tana kuka iya kuka, kukan azaba haɗe da salati. A haka Sheykh ya shigo ya samesu. Cikin takaici Umaymah ta juya ta nufi falon Ayshan tana kallonshi tana cewa. "Gata ka barta kada ka kula da jinyarta da haƙƙinta ne Allah ya rataya a kan wuyanka ai ka fini sani. Ka sani kana take sani". Ta ƙarishe mgnar tana zubda hawaye sabida duk wanda yaji kukan da Aysha keyi yasan na wahala ne. Ita kuwa Aysha da sauri ta miƙe ta kife kanta jikin gini tana mai ci gaba da kuka. Jamil, Jalal, Affan, sunata yi mata sannu. A hankali yabi bayan Umaymah da kallo tabbas ranta yayi matuƙar ɓaci, ga tashin hankali ga rashin bacci. A hankali ya isa inda take. Hannunshi yasa ya kamo nata. Da sauri ta ɗago jajayen idanunta ta kalleshi, cikin zubda zafafan hawaye tare da cewa. "Yah Sheykh zafi, hannuna zai tsinke." Wani irin masifeffen rauni da tausayinta ne yaji sun rufeshi, kanshi ya juya cikin sanyi, yaja hannuntan. Suka nufi ɗakishi. Ita dai binshi a baya takeyi tana tafiya kamar a sama takejin kanta. Kai tsaye har bedroom ya wuce da ita. Kan gadonshi ya ajiyeta yanajin kukanta na hawa kanshi. Bakin gadon ya zauna ya bata baya tare da cewa. "Ki kwanta kiyi addu'a zakiji sauƙi." Ba jinshi takeyi ba bare ta gane abinda yake nufi. Da sauri ta yunƙura zata sauƙa. Juyowa yayi ya kamata ya ajiyeta kusa dashi kana ya juyo suna fuskantar juna. Cikin kuka ta faɗa jikinshi tana cewa. "Umaymah hannu zai tsinke. Zafi zai kasheni". A hankali ya ruggumeta tare dasa hannunshi ya kamo hannun dake ciwon. Da sauri tayi tsalle zata zille hakan ne yasa ya ƙara ruggumeta gama ya haɗa jikinsu wuri ɗaya. cikin sanyi ya fara mata karatu a kunne yana hura mata iskar bakinshi kan hannun Ajiyan zuciya mai ƙarfi da numfarfashi ta fara sauƙewa da ƙarfi-ƙarfi. Umaymah kuwa jin shirune yasa, ta nufo Side ɗinsa. Ganin baya falone. Tace. "To ina suke ina ya kaita?". Ta ƙarishe mgnar tana tura ƙofar Bedroom. Tana tura ƙofar sai kuma tayi sauri taja da baya sabida hangosu da tayi yana konce lib yayi rigingine ya ɗan jingina da allon kan gadon. Kana ita kuma ya kontar da ita kan jikinshi, ya ɗaura kanta bisa ƙirjinshi hannunshi na kan...! Jinyar Sheykh ta musamman ce. To ya zata kaya ne in ɗan gidan ba'ana yazo. Hege Sarkin baka wa yakewa aikin. By *GARKUWAR FULANI* Cikin tsuke fuskarsa da muryar dake nuna zafin abinda ke zuciyarshi yace. "Ummi in ya fito kiyi mishi jagora zuwa wurin sarkin ƙofa ki nunashi kada a sake barin yazo ko kusa da katangar masarautar Joɗa ne, a korashi ya bar jihar Ɓadamaya." Da sauri Ummi tace. "Toh". Kana tayi gaba tare da cewa. "Mu tafi". Da sauri Barun yabi bayanta. A can falon Sheykh kuwa komawa yayi ya zauna gaban Bappa cikin sanyi yace. "Bappa kayi haƙuri, ka gafarceni, bisa korarshi da nayi. Wannan sunada manufar data kawoshi, ni zan ji da ciwon hannunta, in sha Allah zata samu lfy. Ka kwantar da hankalinka." Ido Aysha ta zuba mishi cike da mamakin ta ina ta yaya ya gane meke tafe da Barun har ya gane sunada wata manufa, ta yaya ya gano kuramen bakin da Barun ya karanta mata, ta yaya yayi musu wasali har ya basu cikekkiyar jimla ya karancesu da fassararsu, meya sani a kanta. Hakama Bappan kallon Mamaki yakeyi mishi amman sai ya gyara zamanshi tare da cewa. "Ba komai Muhammad Allah ya bamu sa'a ya kuma bata lfy". Amin Amin yace shida Umaymah. Al'amin ne ya ɗan gyara zama tare da cewa. "To Allah yasa a dace. Amman ko za'a gwada asibiti ne?." Kai ya jujjuya tare da cewa. "Kada ka damu, in sha Allah ba damuwa". Kai ya ɗan gyaɗa cikin gamsuwa. A hankali Umaymah ta miƙe ta fita. Shi kuwa Sheykh Aysha ya kalla tare da cewa. "Tashi ki barsu suci abinci mana". Da sauri Bappa da Al'amin sukayi mgna kusan a tare sukace. "Alhamdulillah mun ƙoshi". Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Al'ameen da kyau kana a hankali yace. "Ba'a zuwa masarautar Joɗa a fita ba'aci komaiba". Murmushi mai cike da gamsuwa Bappa yayi kana yace. "Eh Alhamdulillah munci a wurin Lamiɗo ai". Kanshi ya gyaɗa cikin gamsuwa da hakan yace. "Toh Bappa". Cikin sanyi ita kuma Aysha tace. "Ya Al'amin bani zanci". Murmushi Al'amin yayi kana ya jawo Foodflaks ɗin, a plate ya zuba mata Couscous da biyar hanta. gyara zamanshi yayi ya fuskanceta da kyau itama gyara zamanta tayi. Bappa kuwa Murmushi yayi yana kallonsu. Shi kuwa Sheykh ido ya zuba musu zaiga dai iya gudun ruwansu duk da zuciyarshi ta gama gano mishi nasabarsu. Shi kuwa Al'ameen. A hankali yasa spoon ya ɗan ɗibo, kana ya nufi bakinta da spoon ɗin tare da cewa. "Ha, buɗe bakin". To tace kana ta buɗe bakin ya saka mata. lumshe idonta tayi tare da tauna abincin dan ya mata daɗi. Sake dibowa yayi ya bata, still ta buɗe baki yasa mata. Cire kanshi yayi a kansu, ya maida dubanshi kan Bappa dake mishi mgna. Umaymah da Ummi ne suka shigo a tare ita Ummi cewa. Sheykh tayi an fidda Barun. Ita kuwa Umaymah ƙwaryar fura da nono ta kawo musu. Murmushi sukayi ganin yadda Aysha ta zage tana cin abinci. Shi kuwa Al'amin ya dage yana bata. "Ya Al'amin zan sha ruwa". Tace mishi tana taunar sokar naman da yasa mata a baki. Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Umaymah tare da cewa. "Allah rene a sammin ruwa in bata". To Umaymah tace ta miƙo mishi ruwa. Tana kallon kamanninshi da Aysha ba sai an gaya maka cewar ɗan uwanta jininta bane. Bata ruwan yayi har baki. Tasha sosai. Kana ya kalleta tare da cewa. "In ƙara miki abincin ne?". Kai ta gyaɗa mishi. murmushi yayi tare da cewa. "Bubbuga rumbun Abboi". Murmushi tayi itama tana mai share hawayen da suka silalo mata. Ƙara mata yayi tare da ci gaba da bata. Sosai kuwa taci tayi haniƙan. Sheykh kuwa da wutsiyar idonshi yake kallon dukkan motsinsu. Bayan tayi gyatsa ne, Ummi ta matsar da kwanukan. Babu yadda Sheykh da Umaymah basuyiba, amman Al'amin da Bappa sunƙi suci abinci. Kiran sallan azahar ne, Yasa duk suka miƙe. Cikin sanyi Al'amin ya kalli ogogon hannunshi da yaketa sheƙi yace. "Bappa muyi salla mu tafi kada lokacin ya ƙure mana". Cikin kula Umaymah tace. "Ba kwana zamuyi ba". Murmushi Bappa yayi tare da cewa. "A'a zamu koma tunda jiki da sauƙin gata taci ta ƙoshi tana hira." A hankali Ummi tace. "Eh ai dama haka takeyi, anjima kuma in ciwon ya tashi zakace kamar zata shiɗe, sai an mata tofi take ɗan samun sauƙin". Murmushi Al'amin yayi tare da kallon Sheykh cikin nitsuwa da gogewar cikar wayewar dake nuni ba makiyayin daji bane yace. "Sheykh ka samu sabuwar wayar hannu, kenan tunda sai kayi tofi akejin sauki. Dan Allah duk inda kake ta kasance a nan a ƙara kulan mana da Boɗɗin Abbai". Murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "In Sha Allah". Cikin karrama Sheykh ya nuna musu wata ƙofar dake gefen ɗakinshi yace. "Ga wuri kuyi al'wala mu tafi masallacin". kai Al'amin ya gyaɗa kana yace. "Bappa je kayi al'wala kazo mu tafi. Cikin nitsuwa Bappa yace da al'wala ta". Shima Al'amin gyara tsayuwarshi yayi tare da cewa. "Nima inada al'wala". Cikin gamsuwa Sheykh yace. "To bisimilla muje nima da al'wala". To sukace kana duk suka nufi babban falon. Suna isa tsakiyar falon. Al'amin ya ɗan tsaya tare da cewa. "Parvina zo". Da sauri ta ƙaraso gabanshi. Shiru sukayi jin Al'amin ya juya harshe zuwa wani Yaren ba larabciba ba Turanciba ba hausaba ba fillanciba. Mgna yakeyi riƙe da hannunta. Ita kuwa Aysha kai taketa gyaɗa mishi ido cike da kwalla. Hannunshi yasa ya share mata hawayen kana yasa hannunshi ya shafa kanta tare da juyawa ya fita. Ita kuwa Aysha cikin sanyi tace. "Bappa dan Allah a kawo min Junainah". Kanshi ya gyaɗa kana shima ya fita. Binsu a baya Sheykh yayi. Ita kuwa hannunta mai lfyar tasa ta share siraran hawayen da suka zubo mata. Kana ta juya ta nufi ɗakinta. Ummi da Umaymah kuwa kallon juna sukayi suma suka wuce ɗakin su. Bayan an idar da sallan ne, Sheykh da kanshi ya ɗauki su Bappa ya kaisu tasha kamar yadda sukace. Bayan ya kaisune. Yayi musu fatan isa lfy ne, yaja motarsa kamar ya tafi. Ya koma can baya ya ajiye motar kana ya kira Ado drevernshi da yake cikin but ya fito. Sannan yace. "Bisu". Da sauri Ado yabi bayansu. Shi kuma yayi gida. A hankali Ado yake binsu. Ga mamakinshi sai yaga sun tari taxi sun shiga. Shima taxi ya tsaida ya shiga, tare da cewa. "Bisu duk inda suka nufa." To yace, kana yabi bayansu kai tsaye international airport Ɓadamaya suka shiga. Suna shiga. Kuwa suka fito. Suka biya mai taxi ɗin da kuɗin ma da bana ƙasar Nigeria bane kuɗin ƙasar Cameroon ne. Cikin sanyi Al'amin yace. "Yi haƙuri bamu da canji ne, kaje wurin yan canji za'a canza maka su zuwa Naira". Cikin jin daɗi mai taxi ɗin ya tafi. Shima Ado ya sallami nasa mai taxi ɗin. Kana yabi bayansu tafiya kaɗan sukayi yaga wasu mutane a ƙalla su shida, sunbi bayansu duk suna cikin shigar sut. Al'amin dake gefen Bappa ne ya miƙo wa ɗaya na kusa dashi hannu. Wayar iPhone ƙirar wannan shekarar ya miƙa mishi. Sai kuma system ɗinshi. Daga nan kan tsaye sukaje suka shiga jirgi. Dole Ado ya rakasu da ido. Su kuma jirgi ya ɗaga dasu. Tun kafin Ado ya koma gida ya kira Sheykh ya labarta mishi. Murmushi Yayi jin abinda Ado yace mishi. Kai ya jinjina tare da danna wasu ababe a wayarsa. " ?+? ". Murmushi yayi kana ya jefa woyar a al'jihunsa. Bai shiga gidaba sai bayan sallan isha'i. Yana shiga kuwa ya samu su Ummi a falo. Aysha da hannunta ya ɗan fara zogin. ta bishi da ido. ganin kamar bazata tashi bane yasa. "Umaymah cewa tashi kije ya miki tofin." To tace kana ta miƙe, ta nufi Side ɗin nashi. Babu kowa a falon sai dai ta hango shigarsa ɗakin. A hankali tabi bayanshi tura ƙofar Bedroom tayi tare da sallama. Kana ta kutsa kai cikin ɗakin. A hankali ta isa tsakiyar ɗakin babu kowa. cikin sanyi tace. "Ina jiranka dan Allah kamin tofin". Shiru taji ba mgna ba kuma motsin komai a ɗakin. Cikin sanyi ta ɗan fara hurawa hannunta iskan bakinta. Tana kallon ƙofar Bathroom ɗin. A hankali kuma ta miƙe tana cewa. "Shyyyuuu hahjjyyyyyyyt". Sai kuma ta matso bakin ƙofar Bathroom ɗin da niyar ta bubbuga ƙofar. Tana sa hannu bisa ƙofar ta buɗu. Da sauri ta ɗan ja da baya. A hankali tace. "Yi haƙuri bansan a buɗe yakeba". Still ba mgn kuma ba motsin ruwa. Hakane yasa ta ɗan leƙa. Ganin ba kowane a ciki ta kutsa kai ciki tare da cewa. "To ina kake ina ka shiga". Shiru wayam ba kowa, komai na bathroom ɗin yana nan fes-fes a kimtse. Da sauri ta fito bedroom ɗin. Waige-waige tayi ba kowa. Haka yasa ta fito falon da sauri tana cewa. "Umaymah ban ganshi bafa, kuma na hangoshi yana shiga ɗakin. Na shiga kuma ban ganshiba." Ummi ce ta amshi zance da cewa. "Ko ya shiga wonka ne". Da sauri tace. "A a baya cikin bathroom". Umaymah ce ta ɗan kalleta tare da cewa. "Ki duba Dinning area ko yana can". Da sauri ta juya tana cewa. "Ɗakin fa ya shiga, kuma ban ganshi ba." Ummi ce tace. "To kije dai ki ƙara dubawa". Dube-duben tayi a falon kana ta koma cikin bedroom ɗin wayam fa A hankali ta ƙarewa wodurob ɗin shi kallo, buɗesu tayi duka, tana cike da mamakin to ina ya shiga, dan tabbas taga shigarsa ya kuma za'ayi baya ciki to ina ya shiga?. A haka duk ta bubbuɗe durowowin babushi babu alamarshi. Falon ta sake fitowa tana mai jin zohin hannun yana tsananta. Ɗaura hannun tayi a kanta tana jin idonta na kawo ruwa. Umaymah ce ta shigo. Ƙofar shiga cikin Garden ɗin su ta duba. A rufe take babu alamun an taɓata ma. Ƙofar ɗaya ɗakin ta nufa zata buɗe. "Aysha tace. "Allah ko Umaymah bai shiga nanba ɗauki shi ya shiga. Kuma na duba baya ciki tako ina kuma banga fitanshi ba." "Ikon Allah to ina ya shiga?". Umaymah ta faɗa tana. Shiga ɗakin. Jim kaɗan ta fito. A gefe ta tsaya tana mamaki tabbas dai sunga ya wuce. Da sauri suka miƙe ganin ya buɗe ƙofar ɗakinshi ya leƙo yana cewa. "Umaymah lfy kuwa? Naji kunata salati". Da sauri tace. "Kai muke nema bamu ganka ba, ina ka shiga Aysha tace baka cikin ɗakin." Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta tare da cewa. "Uhumm to dama ya za'ayi ta ganni tanata kuka ta gigita kanta ba dole ta makanceba". Cikin gamsuwa da hakan dan Umaymah ta yarda wata ƙil ciwone ya gigita Aysha shiyasa Bata ganshi ba. Ita kuwa Aysha cikin zafin tace. "Wlh Umaymah ba ciwo bane na duba ko ina ban ganshi ba". Kai Umaymah ta gyaɗa kana tace. "To kije ya miƙi tofin". Miƙewa tayi ta nufi cikin ɗakin. Ita kuma Umaymah ta koma falon. Raɓawa gefe tayi ta shigo. Shi kuwa maida ƙofar yayi tare da cewa. "Zo nan". Matsowa tayi ya fara yi mata tofin tana jingine da ƙofar yanayi yana hura mata iska. A hankali ta fara lumshe ido, ganin zatayi bacci ne yace. "To jeki". Har zata fita sa kuma ya ɗan sha gabanta ido ya zuba mata kana a hankali yace. "Ke komai kika gani sai kinyi mgn ne?". Kai ya jujjuya alamun a a. Gashin girarta ya zubawa ido tare da cewa. "Bubbuga Rumbun Abboi". Baki ta ɗan tura tare da cewa. "Ni dai ba bubbuga Rumbun bace". Matsota ya farayi ganin hakane ta ɗan ja da baya ta jingina da ƙofar, kusa da ita ya kuma matsowa kana a hankali yace. "To ke meyece in ba bubbuga Rumbun ba, ko kunya babu kin zauna gaban wanda ba mijinkiba, yana baki abinci har baki". Gashin tattausan gemshi ta ɗan kalla tare da cewa. "To nida Yayana ɗan uwana, tunda mai bani Allah ya kawoshi ai sai ya bani kada yunwa ta kasheni". Murmushi mai sanyi yayi sabida tambaya ɗaya ya mata cikin amsa tambaya ɗayan kuma ta amsa mishi tarin tambayoyinshi. iskar bakinshi ya ɗan hura mata tare da cewa. "Kince in baki ban baki bane?". Da sauri tace. "Toh sai nace ne?". Ƙara matsowa kusa da ita yayi tare da ɗada mata girarshi ɗaya a hankali yace. "Na'am sai kin ce mana shima ai ce masa kikayi ya bakin". Mutsu-mutsu ta farayi jin ƙirjjinshi na danne nata a hankali tace. "Toh ai shi ɗan uwanane". Ba zato yaji mgnar ta subce mishi. "Toh ai Ni kuma mijinki ne". Sai kuma yayi sauri ya matsa, tare da juya mata baya. Ita kuwa sumar ƙeyarshi ta zuba ido kana a hankali ta juya. Cikin lumshe ido ta fita. Shi kuwa Sheykh wata iriyar sassayar ajiyar zuciya ya sauƙe mai nauyi. Kana ys cire kayan jikinshi. Sannan ya shiga wonka. Bayan ya fitone yayi shirin baccinsa. Kana ya kwanta. Ita kuwa Aysha tana shiga ɗakinta ta kwanta sai bacci. Umaymah kuwa na ɗakin Ummi suna tattauna wata mahimmiyae mgna, sai ƙarfe sha biyu ta shigo. Tayi mamakin ganin Aysha konce tana baccin. A hankali tace, uhum tana tashi zan kai maka ita tunda ka iya kora masu maganin ka kora sarkin bakan masarautar Joɗa kana ka kora wanda iyayenta suka zo dashi. Daga nan taje tayi al'wala tazo ta kwanta. A can wani yankin kuma. Sarkin baka ne da Ɗalhatu mai sa tayis ne, zaune su, suna musu bayanin duk abinda ya faru. Dariya tayi mai cike da jin daɗi tace. "Uhumm ai zanyi maganin ƴan iska watan cin uwarsune ya kama. Wannan shegen yaro Jabeer Allah ya sani bana ko son ganin fuskarshi. Duk sanda na ganshi sai inji zuciyata ta tsinke hankalina ya tashi. Ɗaya dake gefenta ne, yace. "Aini da inada dama da a daran nan zan kashe shegu gaba ɗayansu." Kai ta juya tare da cewa. "Uhum baka san rashin kunya da tijara da magangun da wannan matar tashi mai kama da aljana tayi minba ne. Shiyasa dole in taka mata birki zanci uwarta zata gane bata da wayo." Daya na gefenta ne yace. "Uhummm ni wlh da zan samu wutan zan bunkawa shegu duk su babbake". Nan dai sukaci gaba da yiwa Ahlin Sheykh tanadin mugunta. A can cikin dajin kuwa zaune yake gaban bokanshi shi. Cikin hatsala yace. "Kace min abubuwa suna gabda nasara amman akwai tsaiko menene tsaikon gaya min shi in kaudashi". Dariya bokan yayi tare da zazzare idanu kana yace. "To ka dai san babban abunda ya hanamu nasara kan yaron nan, shine addu'o'in da yakeyi da yawan zama da al'wala da karatun al'ƙur'ani. To yanzu kuma na gano wannan matar tashi da aka aura mishi idonta a buɗe suke. "Akwai makaran gado, wanda sukeda ƙarfin iko, ko jiya wata cikinsu tazo tajamin kunnen kada in kuskura in cutar da ita. Sannan kuma akwai saurayi ta da ya raineta ya shirya mata jiki, kana tana iya gane sihiri a wuri duk ƙanƙantarshi. To in dai ba rabashi mukayi da itaba ko a kasheta ba tsira zamuyi ba. Kuma tana iya tona asirin kowa". Cikin tashin hankali yace. "Uhumm zata kuwa bar Masarautar Joɗa nan kusa. In kuwa ta nuna taurin kai tabbas zata bar duniyar nanda bada jimawa ba, bazan bar duk wani abun da zai shiga tsakanina da sarautar masarautar Joɗa ba". Daga nan sukaci gaba da tattaunawarsu. Barun kuwa ana korashi ya nufi ƙasar Cameroon, Ba'ana bai iya jiranshi ba, tahowa yayi suka haɗu ya gaya mishi duk yadda sukayi da Sheykh. Nan suka sake komawa cikin Rugar tasu can inda ya samu sabon uban gida. Yanaji kamar ya mutu dan baƙin ciki. Nan yaci gaba da shirya yaƙan Sheykh. A nan kuwa ɗakin Aysha. Ƙarfe ɗaya da rabi Aysha ta farka da salati a bakinta. Cikin sauri ta buɗe idonta. Tare da miƙewa a hankali ta nufi falon. Domin taji zogin na dawowa. Tazo falon kenan ta hango mutun da irin shigar ranan cikin tsoro tace. "Waye ne kai me kakeyi mana a nan?". Juyowa yayi ya kalleta cikin isa ya fara takowa zuwa gabanta. Da sauri ta fara jan baya-baya tana cewa. "Me hakan? Me kake nema damu?". Cikin Tsuke fuskarsa yace. "Me na samu dai. Ai Jahan tun kafin ya nemi abu yake samun abun a hannunshi". Da ƙarfi ta buɗe bakinta zata zurma ihu. Taku biyu yayi ana uku ya isota. Tafin hannunshi yasa ya rufe mata baki tare da cewa. "Kada ki razana wancan mataccen mijin naki". Wani irin zazzaro ido tayi tare da jujjuyasu cikin alamun firgici da tsoro da kiɗima. Kanshi ya jujjuya mata tare da cewa. "Kada kisa zuciyarki ta buga a banza dan nace wancan mataccen mijin naki. Ban kasheshi ba, amman dai ke a wurinki dashi da mace yar uwarki ba sauyi". Hannunta mai lfyar ta fara kiciniyar ɗagawa zata ture hannunshi da ya ɗaura kan bakinta, ya rufe, ya haɗa kanta kuma da jikin gini. Juyota yayi da ƙarfi ya manna bayanta da ƙirjinshi still hannunshi na kan bakinta. Ɗaya hannun kuma, bisa ƙirjinta ya ɗaura. Taku ya farayi yana janta ya nufi hanyar fita woje. Wani irin bugu zuciyarta keyi tamkar zai faso ƙirjinta ya faɗo woje. Zuface ta tsananin firgita da tsoro ta karyo mata tako ina na jikinta. Tuni tsoro yasa numfashin ta ya fara subce mata. Kiciniyar kwace kanta takeyi ta samu damar yin ihun amman ta kasa. Sabida ba ƙaramin riƙo yayi mataba. Hannunshi dake kan ƙirjinta ya cusa cikin rigar ta saman wuyan rigar tata. Wani irin azabebben cizo ta dartsawa tafin hannunshi, amman duk da haka bai janye hannun nashi ba. Sai ma lumshe idonshi yayi tare da jan dogon numfashi mai fitar da ɗimaucewar da yake ciki. Wani irin shafa yayiwa breast ɗinta, wanda yasashi rawan jiki bnnarsa tayi wani irin azabebben zabura da miƙewa gal. wani kiciniya ta fara da iya karfinta dai-dai lokacin kuma suka iso bakin ƙofar fitan Hannunshi dake cikin rigarta ya zaro bayan ya burza nimple ɗin ta. Murza key ɗin ƙofar yayi ya kana ya jawo ƙofar ya buɗe. Wani irin karkarwa jikinta ya fara, Garin son kwace kanta da neman taimakon kanta, ta buge hannunta mai ciwon jikin ƙofar. Dai-dai lokacin kuma ya janye hannuunshi kan bakinta. Wani irin razanenne kuma gigitaccen ihu tasa mai sauti. Shi kuwa Jahan da gudu ya fice kamar walƙiya. Ita kuwa cikin karkarwa da tsoro da gigita ta juya ta nufi cikin falon tare da zurma wani ihun mai cike da kiɗima da azaba gaba ɗaya jikinta karkarwa yake. Cikin bacci Umaymah da Ummi suka jiyo ihunta da rabka musu kiran da takeyi. A guje suka fito cikin ɗakunan suka nufo inda suke jin ihunta. A bakin ƙofar suka haɗu cikin karkarwa ta faɗa jikin Umaymah tare da Ruggume ta da hannu ɗaya. Cikin kuka da fitan haiyaci take cewa. "Umaymah wani, Ummi yau ma ya sake shigowa, zai saceni ya jani har bakin ƙofa, kunga can ƙofar a buɗe ko. Wayyo Allah na, wayyo hannuna". Da sauri Umaymah ta ruggumeta gab zamewa tayi suka zauna a nan. Ummi kuwa hannunta mai ciwon da taga yana rawa tamkar mazari ne ta rinƙa hurawa iska tana cewa. "Sannu Aysha innalillahi sannu". Sai ta kuma fara kiran Sheykh. "Sheykh! Sheykh!! Sheykh!!!". A gigice ya buɗe ƙofarshi ya fito, ya nufi inda suke yana cewa. "Na'am! Na'am Ummi meya faru ne". Cikin gigita tace kalli fa. Dai-dai lokacin kuma numfashin ta ya tafi cak ta sume tana cewa. "Jahan wai zai saceni". Cikin gigita Umaymah tace. "Jazlaan ta suma, ta sumafa. Waye ne Jahan kagafa can ƙofar a buɗe". Hannunshi yasa ya amsheta jikin Umaymah dan yaga itama jikinta karkarwa yakeyi. Ruwan sanyin da Ummi ta miƙo mishi ya amsa, kana ya kurba a bakinshi ya fesa mata ruwan a fuska. Cikin wani irin jan dogon numfashi ta sa hannunta mai lfyar ta saƙalo wuyanshi, tare da ɓoye fuskarta cikin jikinshi tana cewa. "Zai saceni, ɗan iska ne shi". Ummi ce ta miƙe taje ta rufe ƙofar. Shi kuwa Sheykh a hankali ya kalli Umaymah dake gigice yace. "Umaymah ki kontar da hankalinki, babu abinda zai samemu da izinin ubangiji. Kije ku kwanta. Ummi kuje, kwana kima tayi haka cikin Ramadan inaga al'janunta ne ke rikitata. Dan ranar da tace ta ganshi ya shiga Side na ba inda bamu dubaba ba kowa". Cikin kiɗima Umaymah tace. "Yau dai kam tabbas akwai abinda ta gani tunda harda suma kuma ga ƙofar a buɗe, Jazlaan na gaji wlh zaku bar Masarautar Joɗa ko zamu samu kwanciyar hankali a rayuwar mu". Cikin son kontar mata da hankali ya ɗan dafe kanshi kana yace. "To Umaymah zamu barta jeki kiyi al'wala kiyi addu'a Allah ya kare mu". Ya ƙareshe mgnar yana miƙewa tsaye da ita a jikinshi. Dan tayi mishi riƙon ɗaurin goro da hannunta mai lafiya. A hankali Umaymah da Ummi suka juya suka tafi. Shi kuwa Side ɗinsa ya nufa, kai tsaye. Har cikin Bedroom, maida ƙofar yayi ya rufe. Kana yazo kan gado ya sunkuyo ya kwantar da ita. Jin yadda ta riƙe mishi wuya ƙam-ƙam ne ya sashi cewa. "Zafa ki kasheni da shaƙa". Shiru tayi tana ƙanƙame da wuyanshi, hannunta sai karkarwa yake amman bata kuka alamun zafin yayi zafi tsananin yayi tsanani domin wani zafin ya wuce inda hawaye suke. Dole a hankali ya zame wuyanshi kana ya zauna gefenta. Idonta suna buɗe amman sunyi masifar ja, goshinta sai zufa yake tsastsafowa. Numfashin ta wani na korar wani. A hankali ya gyara zamanshi ya fara yi mata tofi yana karanta duk surar da tazo bakinshi. A hankali hannun ya fara rage karkarwan. Tsawon miti talatin yana mata tofi yana jin tausayinta har cikin ransa ya dade yana mata tofin. Sannan ta iya juyowa ta kalleshi cikin rauni da zubda hawaye tace. "Yah Sheykh ka yanke min hannunan mana ko zan huta da azabar da nakeji in ya tashi". Ido ya ɗan zuba mata tare da cewa. "Kiyi bacci kinji ko?". A hankali tace. "Ina tsoronshi kar ya dawo". Cikin sunkuyowa yana kallon hannun yace. "Bazai shigo ɗakina ba. Ki dena tsoronshi babu abinda ya isa ya miki! Ki dena tsoronshi ko yaushe yana tare dake bai cutar da keba ki yarda dani". Cikin zubda hawaye tace. "Ɗan iska ne mugu ne". Cike da mamaki ya yamutsa fuska tare da cewa. "Ɗan iska kuma to me yayi miki na iskanci?". yunƙura tayi ta konta kan gefenta na hagu ya zama fuskarta na kusa da cinyarshi a hankali tace. "Tattaɓani yayi, yasa hannunshi har cikin". Sai kuma tayi shiru, cikin rumtse idonshi yace. "Cikin me?". A hankali murya na rawa tace. "Cikin rigata yana taɓa min". Fuskarshi a murtuƙe kamar zaiyi ruwan jini yace. "Meyasa kika tsaya har ya taɓa ki, kema iskancin kikeso ayi da keɗin inba iskanciba, ai hannunki ne ke ciwo ba ƙafarki ba, ki gudu mana". Juyowa yayi ya fuskanceta tare da ciwa. "Tukunma wanne iskancin ne ke fito dake da dare, in ba bikinku ba ɗaya ba, zakizo kina mana ihu da suman ƙarya ai so kike ayi ta taɓe-taɓe ko?. In tattaɓakin kikeso anayi ki gaya min mana ba sai in tattaɓakin ba hankalinki ya kwanta in miki abin da kikeso duka har sai kince ya isheki". Cikin zubda hawaye tace. "Ina gudu ya kamoni kuma na fitone zanzo kamin tofi a hannuna na haɗu dashi. Wlh ni dai ba yar iska bace. Inata ihu har na fame hannuna Ina kafin kukaji kuka fito". Wani irin kallo ya watsa mata ƙasa-ƙasa kana. Ya juya ya kwanta, a haka sukayi bacci. Washe gari da asuba kuwa. Ta koma ɗakinta tayi baccinta. Shi kuma yana dawowa masallaci, yayi Azkar ɗinsa. Kana ya ɗauko gorar zam-zam. sannan ya ɗauki ganyen magarya guda bakwai, cikin wanda ya amsa wurin Gimbiya Aminatu tun jiya da yamma. Sa ganyen yayi a cikin gorar bayan ya ɗan sha ruwan ya rageshi. Kasancewar bakin gorar nada ɗan faɗi. Haka yasa ya zauna dashi bisa kan sallayarshi. Ayatul shifa ya fara karantawa yana tofawa cikin ruwan zam-zam da ganyen magarya guda bakwan. Kulhuwa Falaƙi Nasi Ƙuluhiya Ayatul-kursiy Amanar-rasuulu Attaba'u ma tatlush-shayaɗeenu ala mulki Sulayman. Ita kuwa Aysha a hankali taje tayi wonka bayan Umaymah ta haɗa mata komai na wonka. Koda ta fito kasa saka rigar tayi sai dogon wondon kawai ta saka. Ganin hakane yasa Umaymah ta miƙo mata rigar dama da ɗan madaidacin hijabi a jikinta. Da hannun hagu ta amshi rigar, ta tsaya tana kallon Umaymah. Ita kuwa Umaymah cikin bada umarni tace. "Kije Jazlaan ya saka miki rigar". Cikin sanyi tace. "Umaymah Hibba tazo ta saka min". Fuska ta haɗe tace. "Kije ya saka miki nace ko". Cikin sanyi tace to. Kana ta juya ta funi Side ɗinsa. Ummi da Hibba da Saratu kuma suna Kitchen. A hankali ta shiga falon. Shiru tayi tana tunanin ta yaya zataje tace mishi ya saka mata riga. Hakan yasa a hankali ta warware karin gugar rigar. Sannan tasa hannunta na hagun ta riƙe wurin zip ɗin, sannan tasa bakinta kuma ta riƙo wuyan rigar. Zut taja zip ɗin ta buɗe shi. Hannunta na hagu ta zura cikin hannun rigar. Sai kuma ta cireshi a hankali tasa hannun damanta mai ciwon a hankali. Ya zama rigar na kan kafaɗar hannun damar Tata. Shi kuwa Sheykh ya gama yin tofin, ya ɗauko goran ruwan ya nufi falon don zai maidashi cikin Fridge. A hankali ya turo ƙofar. Dai-dai lokacin ita kuma tasa hannun hagun nata mai lafiyar ta kamo hijabin jikinta ta ɗagoshi ta gaba zata cireshi. Ya zama daga ita sai dogon wondon, daga ƙugunta zuwa shafeffen cikinta da ƙirjinta dake cike tab-tab da jajayen Caɓɓule duk suna fili. Wani irin ƙara tayi a hankali jin hijabin ya riƙo ɗan kunnenta yaja da ƙarfi. Da sauri tace. "Wayyo Allah na ya zanyi hannu mai ciwo hijabi ya riƙe ɗan kunne, riga bata shigaba". A hankali ta fara juyi tana kiran Ummi Ummi. sabida duk yadda ta motsa hijabin sai taji ya ƙara jan hujin kunnenta. Yadda take taku tana juyi ne yasa jikinta keyin wani irin kaɗawa. Shi kuwa Sheykh, wani irin masifeffen numfashin ya fixga da azaban ƙarfi. Rumtse idonshi yayi da sauri. Tare da juyawa ya fuskanci Dinning area idonshi a rufe. Yana jin tsikar jikinshi yana zubawa yana mummiƙewa. Zuciyarshi na harbawa a dubu. Yana isa ya ajiye goran kan Fridge ɗinsa. Sannan ya juyo da sauri. Juyowar da zaiyi kenan yaji yayi karo da ita. Ta manna bayanta a ƙ....! By *GARKUWAR FULANI*Bayanta da ƙirjinshi. Da sauri ta ɗan koma gaba tare da cewa. "Innalillahi". Sai kuma ta tsaya ta juyo ta fuskanceshi da kyau. Idonshi ya rumtse da sauri, Allah yasani bazai iya jurarar ganin waɗannan ababen ba masu masifar tada hankalin da gigita kwakwalwar ɗan adam. Ido a rufe ya buɗi baki murya can ƙasan maƙoshi yace. "Me hakan?". Da sauri ta fara ja da baya tana cewa. "Ka tafi! Ka tafi!". Buɗe idon yayi a hankali kana yayi taku biyu zuwa uku ya kamota, a hankali yace. "Ke meyasa bakya nitsuwa ne akan komai! Yanzu a hakan ina zakije a tsiraranki". Ya ƙareshe mgnar yana sa hannunshi ya janye rigarta dake cikin hannun ta. A hankali hannunta na hagun ta zaro tare da rufe ƙirjinta da ko rabinsu bai rufuba. Cikin sanyi ya matsota da kyau, a hankali yace. "Me zakiyi ne?". Murya a kunyace tace. "Zan saka rigatace kuma na kasa shine. Umaymah tace inzo in baka kasamin." "Uhummmm". Shine abinda ya iya furtawa sabida ji yake kamar bazai iya mgna ba. Ita kuwa cikin sauri tace. "Wash". Jin ya fara jan hijabin. Da sauri tace. "Kayi min a hankali kunnena". Ba tare da ya sunkuyo ya kalleta ba yace. "Meya samu kunnen?". Cike da kunya tace. "Hijabin ya sarƙafe min ɗan kunne". Bai tanka mata ba, sai hannunshi yasa ya buɗa hijabin. Ya maidashi a hankali yasa yatsunshi biyu, yana cire ɗan kunnen. Matsota ya kumayi, kana ya samu ya warware garkuwan ɗan kunnen daga jikin yadin hijabin. Sai kuma yasa hannunshi ya cire mata hijabin duka. Ya zama daga ita sai wondon dake manne a jikinta. A hankali ya sunkuyo ya ɗauki rigar tata, sannan ya juyo ya zama tanata cikin falon shi yanata baƙin ƙofar shiga, Yayi mata ƙawanya da jikinshi. Idonta a sunkuye, hannunta na saman caɓɓullenta. Zura mata rigar yayi a wuyanta. Cikin nitsuwa ya buɗe hannun rigar na dama ya sakamata cike da takatsantsan. Sannan a hankali yasa hannunshi ya kamo hannunta na hagun ya saka mata hannun rigar. Cikin hikima ya sake rigar tayi ƙasa, sannan a hankali ya juyo bayanta, dai-dai ta wuyan rigar yayi kana yaja mata zip ɗin. Ɗan sunkuyowa yayi ta kafaɗanta, ganin gaban rigar bai dai-dai-ta yadda ya kamata bane yasa a hankali yasa hannunshin cikin wuyan rigar. ciki da mamaki da tsoro ta rumtse idanunta. Shi kuwa hannunshi yasa ya dai-dai-ta caɓɓullenta cikin breastcub ɗin. Kana ya dauki ɗan kwalin ya ɗaura mata a kanta kamar mayafi kana ya juya ya nufi. Dinning area yana maijin wani irin yam-yam da tafin hannunshi ke mishi tun sanda ya taɓa caɓɓullenta, hannunshi yasa ya ɗauki goran zam-zam ɗin da ya mata addu'o'in karya sammu. Gabanta ya dawo, ita kuma tana ta son ɗaura ɗan kwalinta. Goran ya miƙa mata tare da cewa. "Gashi wannan shi zakisha duk sanda kikaji ƙishi. In kinsha kuma ki ɗan shafawa hannun ki mai ciwon". Cikin yin ƙasa da idonta ta amshi goran tare da cewa. "Ngd". Bai tanka mata ita kuma ta juya ta tafi. A falo ta samu Ummi da Umaymah da Hajia Mama, suna zaune. Cikin wani irin yanayi ta kalli Hajia Mama kana tace. "Ina kwana". Fuska cike da fara'a tace. "Lfy lau. Alhamdulillah yau jiki da sauƙi ko?". A taƙaice tace. "E". Daga nan ta wuce. Hajia Mama kuwa Umaymah ta kalla tare da cewa. "Khadijah ya lbrin Auren Haroon ne Kam?". Ajiyan zuciya tayi tare da cewa. "To aure kam yazo ga mai nisan kwana". Bayan sallan layya da kwana goma za'a fara bikin". "A lallai aure kam yazo ga mai nisan kwana". Hajia Mama ta faɗa. Ita kuwa Ummi murmushi tayi tare da cewa. "Lallai jihar tsinako zata kwashi baƙi". Nan dai sukayi ta hira. Sheykh Jabeer kuwa. A hautsune ya koma bedroom, kan gado ya kwanta tare da yin rubd ciki. Idonshi ya rumtse da ƙarfi wai ko zasu dena harsasho mishi hoton abinda ya gani. Kiran da akewa wayarshi ne ya sashi jan tsaki Karo na uku yanajin kiran yana shiga. Ya sani babu mai mishi wannan kiran mafarautan sai mutun biyu. Haroon ko Ahmad wani babban abokinshi ɗan kasar Cameroon. Hannunshi yasa ya amsa kiran tare da danna amsa kuwa. Tsaki yaja jin Haroon na cewa. "Kai kace baka son yawan kira, in an kiraka sau ɗaya kuma baka ɗagawa dan wulaƙanci. Ni kuma gani Sitti ce ta buwayeni da in Kira mata kai taji lbrin jikin amarya." Cikin sanyi yace. "Yaushe kaje lamorde julɓe?". "Yau kwana biyar". A hankali yace. "Anya kuwa Haroon in kayi aure bazaka dena aiki ba". Taɓe fuska yayi tare da cewa. "Babu mamaki in bar aikin ma inji da amaryata". Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa. "Bawa Sitti wayar". Miƙa wa Sitti wayar yayi. Cike da kulawa da so tace. "Muhammad". "Na'am Sitti ya gida". Cikin kulawa tace. "Gida lfy lau. Ya jikin iyalin naka?". A hankali yace. "Alhamdulillah". Da sauri tace. "Muhammad yaushe zaka kawo min itane?". "Nima ban sani ba". Ya bata amsa a gyatsine. Murmushi tayi kana tace. "Shike nan zan zo ai". Da sauri yace. "A a bance ba, ki bari in ta samu lfy zata zo". To tace tana murmushi tasan yasan in tazo tofa. sa'idonta yafi na akowa. Duk motsinshi zata gayawa Lamiɗo. Nan dai suka ɗan yi hira kana suka ƙatse kiran. Da daren ranar kuwa koda suka zo konciya Umaymah tace. "Aysha tafi ɗakin mijinki kar hannun ya tashi dare-dare ya zama kina fita." A hankali tace. "Umaymah yau hannun da sauƙi tunda nasha ruwan addu'o'in nan bana jin zogin sosai". Cikin jin daɗi tace. "To Allah yasa mu kwana lfy ba tashi". Amin Amin tace kana suka kwanta. Allah cikin ikonsa da buwayarsa da al'farmar Annabi da al'ƙur'ani a daren sau biyu kawai ta ɗan tashi. Shima in Umaymah ta shafa mata ruwan dai sai ta koma bacci a take. Washe gari da safe kuwa, Cikin mamaki ta kalli Umaymah dake shafa mata ruwan tace. "Umaymah bakiga kamar kumburin ya raguba". Siyayan ruwan tayi a tafin hannunta tare da cewa. "Sosai ma kuwa Aysha hannufa Alhamdulillah da sauƙi sosai. Ga mgni kusa dake a bakin mijinki muje anyi ta wahala". Uhumm tace tare da sunkuyar da kanta. Ummi kuwa Murmushi tayi. Koda aka gama breakfast. Ranar a haka a kaikacen ta daure taci. Kafin azahar sosai hannun ya lafa. Yau kuma tunda safe ko inda hanyar Side ɗinsa yake bata kallaba, in taji zogin ta ɗauko ruwan tasha a shafa mata. Shi kuwa Sheykh ranar tunda safe ya fita bai dawoba sai tara da rabi na dare. Still yauma an kwana hannun da sauƙin. Washe gari da safe. Sheykh ya kuma ɗauko wani zam-zam ɗin da ganyen magarya guda bakwai, Yazo yana mata tofin cikin ruwan. Yana mgnar zuci. "Uhum jiki yayi sauƙi zamu huta da koken masifa da shogoɓar tsiya". Koda ya gama yaje ya ajiye a Fridge kana yazo. Ya shiga wonka kasan cewar yau Monday ne tushen aiki ko nasara na tsoronta. Ya fara kimtsawa. Ita kuwa a falon bayan sunyi breakfast, suka dawo nan cikin falon, juyowa tayi ta ɗan kalli Umaymah dake shigowa falon tace. "Uhum Umaymah ruwan fa ya ƙare". Shigowa tayi ta zauna gefenta kana ta kalli hannun ya saɓe sosai. "To kije ki gaya mishi mana, ai bai fitaba, tashi kije da sauri kada ya fita baki gaya mishi ba". To tace kana ta miƙe ta nufi can. Tana shiga yana fitowa. A hankali ta koma gefe ta tsaya. "Ina kwana". Tace mishi ido a ƙasa Ta gefen idonshi ya kalleta tare da cewa "Lfy ya jikin?." "Da sauki". Tace kana ta ɗan kalleshi tare da cewa. "Yah Sheykh!". Ido ya ɗan zuba mata kana yace. "Na'am!". hannunta ta ɗan sa ta shafi fuskarta kana tace. "Uhum dama maganin nawa ya ƙarene shiyasa nace bari in gaya maka". Hannunshi ya miƙo tare da cewa. "Inga hannun". Ɗago hannun tayi ta miƙa mishi. Amsar hannun yayi kana ya juyo ya nufi tsakiyar falon. Tana biye dashi abaya. Bisa kujera ya zauna tare da nuna mata gefenshi. Zama tayi, duk yana riƙe da hannun, ɗan sunkuyowa yayi ya fara karanta Suratul Baqra yana tofa mata, yana sa yatsunshi biyu yana ɗan murza hannun a hankali-hankali, ido ta ɗan rumtse tare da motsoshi jin yana ɗan jan hannun. Wash tace a hankali. Ɗan ƙara murza hannun yakeyi yana tofa mata. Hannun hagunta tasa ta damƙi damtsen hannunshi na dama. bai kulata ba yaci gaba da jujjuya mata hannun dan ya lura tana barin hannun a ƙage wuri ɗaya ko yaushe tana naɗe dashi. Murza hannun yakeyi da ɗan janshi yana miƙar dashi da ɗan ƙarfi. Wani irin bubbuga sawunta tayi tare motsoshi da kyau. Tsakanin sawunshi tasa cinyarta ta dama. kana tasa hannun hagun nata ta maƙaleshi. duk ta kanainayeshi tako ina. zuface ta fara keto mata tako ina na jikinta, Ajiyan zuciya ta fara sauƙewa jin ya sake mata hannun. Kanta ta manna a damtsen hannunshi tana maida numfashi. Shi kuwa shiru yayi yana jin yadda take maida numfashi. Kusa 6 minute kana a hankali yace. "To ɗan sakeni in kin gama hutawa ko". A kunyace ta ɗan zame jikinta ta janye cinyarta. Miƙewa tsaye yayi yana gyara al'kyabbar jikinshi. goran ya ɗauko a Fridge ɗinsa kana ya miƙa mata. Amsa tayi kana suka fito a tare. Affan suka samu da matarsa Mami. Suna fitowa Affan ya miƙa tare da miƙa wa Hamman nashi hannu bayan sun gaisane yace. "Ya mai jikin dai?". "Alhamdulillah jiki da sauƙi". ya bashi amsa Mami kuwa a hankali ta zame ta ɗan rusuna cikin girmamawa tace. "Barka da safiya Hamma ya mai jiki". Hannunshi ya kai ya ɗan shafi kan ɗansu Karami Aliyu tare da cewa. "Lfy lau Alhamdulillah jiki da sauƙi. ya yaran?". Suna lfy tace tare da kallon Aysha dake murmushi jin Affan na cewa. "Aunty Aysha ya jikin dai yanzu kam hannun bazai faɗi bako". Murmushi tayi tare da cewa. "Alhamdulillah da sauƙi". Sallaman su Umaymah Sheykh yayi ya tafi. Murmushi Mami tayi cikin son matar Hamman nasu tace. "Ina kwana Aunty Aysha". "Lfy lau". "Ya jikin naki". Tace tana kallon hannunta. "Alhamdulillah jiki da sauƙi sosai ma". Ta bata amsa. Tana zama kusa da ita, tasa hannun hagun ta amshi Aliyu wanda Dr Aliyu sukayiwa mai suna. Affan ne ya ɗan kalleta tare da cewa. "My Aunty ga iyalin nawa. Ƙanwar Yusuf aboki nane yayar matarshi Zahra ce kuma." Cikin fara'a da son Mami tace. "Ayyah yayi kyau Allah ya ƙara zaman lfy da zuriya mai Al'barka". Murmushi yayi tare da cewa. "Amin tare daku, mu yanzu wannan na uku fa, ai munyi ƙoƙari ko Umaymah". Cikin dariya Hibba tace. "Kai Ya Affan abinma ƙoƙari ne kenan". Dariya sukayi duka kana sukaci gaba da hira. Aysha tana jin gamsuwa da gskyar Mami fiye data Aunty Juwairiyya. Ranan dai anan Mami ta wuni. Haka dai taci gaba da amfanin da ayatul shifa da zam-zam da ganyen magarya. Cikin ikon Allah da izininshi. Cikin kwanaki goma sha biyar hannun nan ya warke ya koma garau. Har tana shiga kitchen ayi aiki da ita. Hakane yasa Umaymah ta fara shirye-shiryen komawa tana mai jin sanyi kaɗan a ranta. Yau kwananta ashirin da zuwa, kuma yaune zata koma. To fa batun ƙomar da zatayi da Hibba ne yasa. Aysha taji babu daɗi. Allah yasani ta saba da Hibba sosai. Ganin yadda ta koma ne yasa Umaymah ta ɗan zauna kusa da ita cikin lallami tace. "Kiyi haƙuri Aysha kinga badon makarantar Hibba ba dana bar miki ita. Yanzuma duk an gama mata komai na karatun zata tafi SS1 harma yan uwanta sun fara zuwa. Kuma kema an kusa janye yajin aikin da University's Suka tafi, nayiwa Jazlaan mgna ana komawa kena zaki koma kici gaba da karatunki kewan zai ragun miki. Rafi'anki zata dawo itama". Cikin sanyi tace. "To Umaymah ki bar mana ita mana, sai in gayawa Yah Sheykh ya sama mata wata makarantar a nan". Murmushi Umaymah tayi tare da cewa. "Abbansu bazai yarda ba Aysha". Cikin sanyi tace. "Uhumm Allah sarki to shikenan Umaymah. Amman wlh gidan zai mana babu daɗi ko Ummi". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Gsky kam Aysha zamuji kewar Hibba". Ita kuwa Hibba tana tsaye gefen Jalal ne. Da alamu wani abun yake nuna mata a wayarshi. Jamil kuwa murmushi yayi tare da cewa. "Uhum in tayi tsami dai maji". Hararanshi Jalal yayi tare da cewa. "Namu ƙamshi zaiyi ba tsamiba, ko Hibba". Murmushi ta ɗanyi tana share hawayenta, duk da rarrashinta da yakeyi kan kada tayi kuka. Har yake nuna mata text message ɗin daya turawa Hamma Jabeer ɗin su cewa. "Yana son Hibba". Kowa yasan Hibba na masifar son Ya Jalal ɗin. Duk abinda yakeyi burgeta yakeyi. Tun yana kaucewa har dai shima ya gane yana sonta ne. Shi kuma Jamil sarkin latsi yaje can yace, i love You yaje can ya kuma cewa haka har yau bai tsaida matsaya ɗaya ba. Kuma soyayya ta hanashi maida hankali kan aikinshi. A hankali Aysha ta sunkuyar da kanta ganin hawayen Hibba na zuba. Shi kuwa Sheykh Jabeer ido ya zuba mata. Lokacin da taga Umaymah ta miƙe tace. "To Ummin Jabeer Allah ya sadamu da al'khairi". Amin Amin Ummi tace cikin kewarta tun kafin ta tafi. Hibba kuma ruggume Aysha tayi tare da cewa. "Aunty Aysha zanyi kewarki sosai". Ta ƙarashe mgnar murya na rawa. Tuni hawaye suka tsinkowa Aysha. Aunty Juwairiyya ma sai ga hawaye. cikin danne zuciya Umaymah tace. "Ha Juwairiyya harda ke a kukan so kuke in tafi nima ina kukan ko". Kai Juwairiyya ta jujjuya. Ya Jafar kuwa shiru yayi yana kallonsu. Shi kuwa Sheykh idonshi ya maida kan tab ɗin shi dake hannunshi. Aysha kuwa. Cikin son danne kukanta tace. "Nima haka Hibba zanyi rashinki sosai. Sai yaushe zaki zo kuma". Cikin zubda hawaye tace. "Aunty Aysha auren Ya Haroon ya kusa, ai zaki zo, bai cika wata biyu ya rage bama". Cikin sanyi tace. "Allah ya kaimu". Amin Amin sukace kana suka fita suka tafi. Suna fita Aysha ta koma ɗakinta. Tana kuka. Ummi da Aunty Juwairiyya da ya Jafar kuwa a falon suka zauna. Sauran kuma duk yan rakiya ne sun fita. Daga Side ɗinsa, sashin Hajia Mama taje ta sallameta kana ta wuce sashin Lamiɗo suma ta sallamesu sukayi mata fatan isa lfy kana ta tafi. Ummi da Saratu suka shiga kitchen. Ita kuwa Aunty Juwairiyya ta koma sashinta itama. Koda suka dawo rakiyar bata fitoba. Kasan cewar magriba tayi ne, sukayi al-wala suka tafi masallacin. Itama Ummi taje ɗakinta. Ita kuwa Aysha yau tana hutun sallan. Dan haka taci gaba da konciya. Har akayi isha'i tana konce. Koda suka dawo kai tsaye Side ɗinsa ya wuce. Jim kaɗan ya fito yacewa Ummi. "Bari inje Lamiɗo na nemana". "To sai ka dawo". To yace ya fita. Ita kuwa Aysha, kiran da akayi mata a wayane yasa ta ɗanyi murmushi. Muryar Junainah taji tana cewa. "Adda na ya hannunki". Cikin jin daɗi tace. "Alhamdulillah ƙanwali ya worke yanzu kam ina Ummey na". Cikin jin daɗi tace. "Gata nan". A hankali tace. "Ummey na nayi kewarku, ina jina kamar bani da kowa nawa a duniya. Gashi Hibba ma yau ta koma". Murmushi Ummey tayi tare da cewa. "Ke kuwa kikeda kowa naki a duniya, gaki ga salihin mijinki da Al'amin ya dawo yana yaba mana kamalarsa kowa naki sun gamsu da zaɓin da Bappanki ya miƙi. Gani ga Bappanki ga Abboi ga Ninnanki gasu ya Ahmad sannan ga dengin mijinki masu sonki Gashi kuwa munji lbrin su Ya Gaini". Ta ƙareshe mgnar dan son kontar mata da hankali. sabida basu wani ji lbrin su Gaini ba. Cikin jin daɗi ta gyara konciyarta tare da share hawayenta. "Alhamdulillah Ummey na godewa Allah. Ina suke?". Cikin sanyi tace. "Suna wata rugar FULANI dake ƙasar Senegal, yanzu ana ƙoƙarin a tabbatar ki cire damuwa a ranki ki sasu a addu'a kinji ko". Cikin sanyi tace. "To Ummey na ina sha Allah zan sasu. Kuma zan roƙi Yan Sheykh ma ya samin su a addu'o'in shi". Cikin jin daɗi tace. "Yauwa to yafi. Ga Bappanki". Murmushi tayi tare da cewa. "Bappa na ina wuni". "Lfy lau Shatuna ya jikinki". "Alhamdulillah Bappa na worke". "Masha Allah, to Allah ya ƙara mana lfy". "Amin Amin tace." Kana sukayi saida safe. Tana katse kiran Ummi dake zaune gefenta tace. "Taso muje kici abinci kinji ko kije ki gayawa Sheykh damuwarki ya saki a addu'o'in shi. Domin addu'ar miji ga matarsa bata da hijabi". Kanta ta gyaɗa cikin gamsuwa kana ta miƙe ta fito. Kaɗan taci abincin. Sannan taje tayi wonka, tasa doguwar rigar bacci kana ta zurma hijabin ta. Ta nufi falonshi. Shi kuwa Sheykh lokacin ya dawo daga wurin a Lamiɗo Inda yake gaya mishi, akwai zagayen rangadin da zaiyi rugagen Fulanin ƙasar gaba ɗaya. A cikin wata mai kamawa. Koda ya dawo wonka ya shiga, Ya fito ɗaure da towel a ƙirjinshi zuwa saman guiwarshi. Mai ya shafa tare da fesa turare. Kana yasa wani tattausan gajeren wonɗo mai ɗan faɗi amman ƙasamshi robar a tsuke take. Yana riƙe da rigar bai saba. Yaga kiran Umaymah ya shigo. Wayar ya ɗaga bayan sun gaisa ne take ce mishi sun isa lfy. A hankali ita kuma Aysha ta turo ƙafar bedroom ɗin ta shigo. Ido ta zuba mishi sama da ƙasa a karo na forko kenan da ta ganshi babu riga a jikinsa. Damatsan hannunshi ta zubawa ido zuwa kan ƙirjinshi da tattausan gargasa tsilli-tsilli ya mishi ƙawanya a farar fatarshi. Shi kuwa ido ya zuba mata dan rabonta da shigowa ɗakinshi yafi kwana goma. Umaymah kuwa cikin murmushi mai sauti tace. "Ina ɗiyata, tanata kuka ko?". A hankali yace. "Gata". Wani irin farin cikine ya rufe zuciyar Umaymah tasan burinsu bazai tabbataba muddin babu shaƙuwa da kusanci tsakanin Sheykh da matarsa. Cikin jin daɗi tace. "Bata wayar". Uhum yace kana ya miƙo mata wayar. A hankali ta iso gabanshi kusa dashi gab-gab ta tsaya. wayar ya miƙa mata yana kallon yadda take matsoshi. Amsar wayar tayi ta kara a kunne tare da yin sallama. Kana idonta kuma yana kan zanen macijiyar dake konce har kan cikinsa zuwa saman haƙar-ƙarinshi. Da Ido yabi wurin da take kallon. Fuskarshi ya haɗe tare da ɗaga ƙafarshi zai ja da baya. Sai kuma ya tsaya cike da mamaki ya kalli hannunta da tasaka ta kamo bakin robar gajeren wondon dake ƙugunshi. Hannunshi yasa ya bugi hannunta, Amman sai ta ƙara matsoshi. Cikin sanyi ta....! Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta number nan da nake whatsapp da ita, 09097853276 ba hoton katin zaki turoba, ba kuma TRANSFER ɗin katin zakiyi minba, ba kuma BTU ba, numbers ɗin katin zaki rubuto ki turomin. In kuwa special Group kikeso kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo min screenshort na shaidar biyanki ta wannan number tawa ta whatsapp 09097853276. Kada kiyi min TRANSFER ko BTU na kati wlh in kinyi ba ruwana. By *GARKUWAR FULANI* Ta ƙara matsowa gabanshi. A hankali tasa ƴar yatsarta ma nuniya dai-dai inda taga kan macijin. Wurinda shi kuma yake masifar yimishi ƙaiƙayi. Hannunta ɗayan kuma ta maidashi ta riƙe bakin robar gajeren wondon dake ƙugunshi. Ido ya zuba mata, cike da mamaki da kaɗuwa, da al'ajabi to me hakan me zatayi. A hankali ta fara bin zanen kan macijiyar tana danna yatsarta, tanayi ƙasa da yatsar. Wani irin yam-yam haka tsikar jikinshi ke tashi tana zubawa wani irin abu yakeji yana zir-zir-zirrrrr cikin jikinshi gaba ɗaya, abune da bai taɓa jin makamancinsa ba a rayuwarsa. Cikin wani irin masifeffen da kasala daya diro mishi ya buɗi bakinshi a hankali yace. "M.. me h hakan.". Manna kanta tayi da ƙirjinshi ta kife kunnenta dai-dai kan ƙahon zuciyarshi dake harbawa da sauri-sauri dib-dib dib-dib. Cikin wata muryar data ganar dashi, ba ita bace, bata haiyacinta mutanenta ne a kusa tace. "Kayi shiru da Allah". Kanshi ya sunkuyar a hankali. Idonta a lumshe hawaye na zuba. Cikin raunin muryar tace. "Wurin yanayi maka ƙaiƙayi wasu lokutan ne?". "Uhummmmmm". shine abinda kawai ya iya furtawa. Ita kuwa ƙara shigewa jikinshi tayi. tare da cewa. "To kayi wa kanka jinyar wurin mana. wannan zanen yana daga kan babbar yatsarka har zuwa nan. Yana bin jikinka, kayi ma kanka aikin irin wanda kayi wa Aysha a ciwon hannunta. Kana sha kana shafawa a wurin. Zai bar jikinka zai ɓace duka. Yanzu dai baya ci gaba da tafiya, tunda Aysha ta tone aikin". A hankali yace. "Yau kuma zuwa kika sakeyi kenan? Bazaki bar jikinta ba kenan kike nufi? Sai ki biyota har ɗakina dan baki da tsoron Allah". A hankali tace. "Inada tsoron Allah wlh nima musulmace Kamarku. Kafurun iska ko mugu bazai taɓa iya ratso cikin sashin kaba. Sabida ka wadata wurin da ambaton Allah. Ko yaushe madadin kallace- kallacen tv na banza da wofi karatun al'ƙur'ani kake sawa. Duk sashin gidanka majigine na ƙura'an. Ni ba muguwar iska bace. Bana sata faɗuwa, ko kuka bare ihu. Bana samata koda ciwon kai. Ina kuma kareta ne ga wasu ababen cutarwa wasu lokutan idonta kan iya ganin abinda ba kowa ke ganiba. Wanda wannan baiwar tace tun tana ƴar ƙaramarta" Cikin dakekkiyar murya yace. "Ki bar jikinta bana so. Kina sata yin abinda in tana haiyacinta ba yinshi zatayi ba." Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Shike nan na tafi, amman in buƙatar zuwana yayi zaka gane nazo. abinda ma babu wanda ya taɓa gane ina jikinta sai kai daga nayi mgn sai ka gane. Zan tafi, amman tanada buƙatar daya kawota wurinka. Zata roƙekasa yayunta a addu'o'in kane. sabida sun ɓata tsawon lokaci har yau babu lbrinsu." Cikin haɗe fuskarshi yace. "Na sani ai, ba sai kin gaya minba, Ni nan nasan komai a kan matata, nasan abinda ya faru da yayunta jeki kawai". Atishawa tayi a hankali. Sai gashi ta narke a jikinshi tayi lib ido a lumshe alamun tayi bacci. A hankali ya gyara tsayuwarshi. Tallabeta yayi da kyau. Hannunshi yasa ya cire hijabin jikinta. A ranshi yake mgna. "Na fahimta kenan iyayenta ma, basuma san tanada wata iska a jikinta ba. Shiyasa basu sanarba kafin a ɗaura auren". Ido ya lumshe yana goge wannan ayar tambayar da ya bugawa Bappa cikin ƙoƙolwarshi na ya aurar da yarshi ba tare daya sanar musu tanada al'matsutsaiba kamar yadda shariya tace. A hankali ya zauna bakin gadon da ita. Yana nazartan abubuwa da dama. Ya fara fahimtar wasu ababen a kanta musamman da yake Junaidu ya labarta mishi komai abinda ya sani a kan Shatu da Ba'ana lokacin da suke asibitinshi Valli. konciya yayi a gefen daya kwantar da ita. Kana yasa hannunshi ya kashe wutan ɗakin. Ido ya lumshe ba tare da yayi baccinba. Ita kuwa Aysha a hankali ta farka daga baccin, ido ta ɗan buɗe. tabbas kam tasan tazo ɗakin shi kuma tasan ta ganshi babu riga daga nan kuma bata kuma sanin meke wakana ba. cikin sanyi take juya kwayar idonta. A hankali ta kalleshi yana konce yayi rigingine, cikin sanyin murya alamun baccin tace. "Yah Sheykh! Yah Sheykh!". A hankali ya ɗan juya kwayar idonshi ya kalleta. cikin sanyi yasa hannunshi ya jawota jikinshi. Kan ƙirjinshi ya kwantar da ita. Yana mai jin wani irin baƙon yanayi yana game dukkanin sasan jikinsa gaba ɗaya. Shiru tayi jikinta na wani irin sassanyan tsuma can ciki-ciki. Cikin sanyi tace. "Zan kwanta". Cikin sanyi murya can ƙasa yace. "Yanzu a tsaye kike ai". Ya bata amsa a daƙile, shirun ta kumayi. Shi kuwa gyara kwanciyar tasu yayi. Tare da jawo blanket ya rufesu. kana ya fara Addu'o'in yanayi yana tofawa a tafin hannunshi yana shafawa a fuskarta da sassan jikinta. Idanunta ta lumshe yanaji sanyin tattausar fatar hannunshi. A haka sukayi bacci, ɗaki ɗaya gado ɗaya borgo ɗaya pillow ɗaya a liƙe a jikin juna. Karo na forko kenan da wannan kusancin ya samu tsakaninsu. Washe gari kuwa. Lamiɗo ya ƙara neman Sheykh akan batun tafiyar da dole zaiyita. Shi kam yace zai tura wasu. Dan yana son zuwa aikin haji, Amman fir tsohon nan yaƙi. Ya haɗashi da Abbanshi dole ya haƙura. Washe gari da safe. Mami matar Affan tazo, ita da Zahra'n Hamma Yusuf. Bayan sun gaisane tace. "Ga ƙanwata Zahra matar Yusuf". Murmushi Aysha tayi tare da cewa. "Ayyah ai kuna kama fa". Da sauri Mami tace. "A a na fita kyau duk gidanmu itace mummunar mu fa". Dariya Zahra tayi tare da cewa. "A daba". Nan Aunty Juwairiyya ta shigo sukaci gaba da hira, Ummi da Saratu suna kitchen. To haka dai mafi akasarin lokuta Mami kanzo susha hira. Tofa nan kewar ke ɗan raguwar mata, wani lokacin kuma ta kira Bappa susha hira ko ta kira Rafi'a ko Junaidu taji lbrin Rugar Bani. Yau sallan layya saura sati biyu. Kuma gobene Sheykh zai fita. dole kuma tafiyar da motace bazai yiwu ta jirgiba. Tunda rugogin manyan Arɗaɓe zai ziyarta wanda cikin dazuka suke. Yana zaune a falon Lamiɗo shida Abbanshi da Galadima. "Ka gama shiryawa ko Muhammad?". Abba ya tambayeshi cikin kula. Kanshi ya ɗan gyaɗa tare da cewa. "Eh". Lamiɗo ne ya ɗan shafi kan shi tare da cewa. "Itama iyalin taka ta gama kimtsawa ko?". Da sauri ya kalli Lamiɗo tare da cewa. "Ta kimtsa taje ina ɗin?". Abba ne ya bashi amsa cikin bada umarni yace. "Ta kimtsa ku tafi tare, dole tare zakuje". A hankali yayi ƙasa da kanshi tare da cewa. "Dan Allah Abba tafiyar da nima ba sonta nakeyi ba, a kuma sake haɗani da wani jidalin". Fuska a haɗe Abba yace. "A bayanka akace ka goyeta ku tafi ne?". A hankali ya jujjuya kai. Cikin yanke hukunci yace. "To ku tafi tare Muhammad bana son musu a kan yarinyar nan duk abinda akace kayi dan Allah kayi tunda ba wanda ya saɓawa shariyar musulunci za'ace kayi ba. Baka san abinda muke zaton samu ta sanadinta ba. Muna ganin nasarori kan matsalarmu. Kaje da matarka kaji ko Muhammad na". A hankali yace. "To Abba ba komai in dai zakayi farin cikin hakan zanje da itan". Kanshi ya shafa tare da cewa. "Allah yayi maka al'barka". Amin Amin yace cikin jin daɗi. Kana ya sallamesu ya fita. A falo ya samu Ummi ita ɗaya tana kallon wata tashar da aka saka wa'azin shi. Cikin sanyi yace. "Ummi gani gaki sai kin kalleni a tv". Murmushi tayi tare da cewa. "Ina ƙaruwa ne ai". Kanshi ya jinjina tare da ɗan kallon gefe da gefe kana yace. "Ummi ina take?". Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa. "Tana ɗakinta". Kanshi ya gyaɗa kana yace. "To Ummi Lamiɗo yace wai dole da ita zamuyi tafiyar zaga rugar Arɗabe. A gaya mata ta shirya gobe sammako zamuyi inga ko zamu gama cikin kwana huɗun". Cikin murmushin Ummi tace. "To bari in gaya mata". To yace shi ya nufi sashinsa. Ita kuma ta nufi ɗakinta. A gaban mirror ta sameta tanayiwa kanta kitson kalba manya-manya. "Kitso kikeyi ne?". Juyowa tayi tare da cewa. "Har na gama ma!". "Kuma yayi kyau sosai fa". Dariya tayi tare da cewa. "Allah ko Ummi". Kai ta gyaɗa alamun eh. Kana tace. "Sheykh yace in gaya miki ki shirya gobe zaku tafi tare yawon ziyartan Arɗaɓen inda dama na gaya miki zaiyi tafi, duk an turawa Arɗaɓen saƙon zuwanshi ma". Cikin jin daɗi tace. "Kai naji daɗi na, zan fita in zagaya inga makiyayan in huta da zaman wuri ɗaya". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Wato zakije kiga fulani yan uwanki ko". "Sosai ma kuwa Ummi yanzu tayani shiryawa". Ta faɗa tana buɗe drower'n. Nan kuwa Ummi ta tayata ta kimtsa ababen buƙatar ta. Sannan suka fito falon inda suka samu Jamil ya dawo aiki Jalal kuma dama yana sashin Hajia Mama ne. Sai yanzu ya dawo nan ɗin nan suka zauna sukaci gaba da hira. Washe gari da safe suka fito cikin shirin tafiyar. Motoci guda bakwai ne uku a gaban ta Sheykh uku a bayan tashi. Biyu na gaba fadawa sai ta ukun Jalal ne da wasu mutane su biyu. Sai motar Sheykh shida Aysha suna baya Ado na jan motar. Sai wacce take binsu Affan ne da Ya Hashim sai Sulaiman kana Laminu ɗan jaridar, da zai ɗauki komai. Sai biyu kuma na baya kuma Galadima ne. Sai fadawa da godarai sai hadimai mata biyu da zasuyiwa Aysha hidima. Tafiya mai ɗan nisa sukayi. Kana suka ratsa wata babbar hanyar birji, suka fara tafiya suna kutsawa cikin daji. A ƙalla awa ɗaya suna tafiya. Sunata wuce ƙananan rugagen Fulani makiyaya, da dabbobinsu. Kasan cewar manyan motocine masu inganci yasa. Basu jin wannan gargada ta buwayesu. Jalal da abokanshi sunata hira, sosai Jamil yayi mamakin sakin fuskar Jalal cikin abokanshi. Sannan sukanyi mgna da wani salo na musamman. Shi kuwa Jamil waya yakeyi da Khairat sabuwar budurwarshi. A can baya kuwa Affan ne liƙe da waya a kunne yana mgna da Yusuf. A motar Sheykh kuwa, shiru kakeji kowa da sabgar da yakeyi. Shi zaune yake da kyau ya buɗe system ɗinshi yana wani aiki a ciki. Hankalinshi duk yana kanta. Ita kuwa Aysha wani irin farin ciki mai zaman kashi takeyi. Shiyasa hankalinta kab yana kan rugagen Fulani da suke wucewa. Murmushi mai baiyana shauƙinta da begen irin wuraren takeyi, yana tuno mata Rugar Bani, da sauran inda suka zauna. Kana tana farin cikin bin wannan tafiyar ne ko zataga wani abin da ya shafi su Ya Gaini. Ɗan juya kwayar idonshi yayi ya kalli inda take. Hankalinta duk yana kan window. Taɓe baki yayi kana ya maida idonshi kan fuskar na'urar tashi. Wani babban rugar Jafun suka fara isa. Rugar a cike take maƙil da maza da mata matasa da sofaffi Bisa alumun sun san da wannan ziyar shiyasa basu fita kiwo ba. Bayan sunyi parking ne. Fadawan suka fara fitowa. Sukazo sukayi buɗe wa sauran motocinsu. Galadima ne ya fara fita kana gaba ɗaya su Jamil Jalal dasu Affan suka fito. Ita kuwa Aysha da sauri ta yunƙura zata fita kasan cewar ta gefen da take aka buɗe. Hannunshi yasa ya riƙo nata. Da sauri ta juyo ta kalleshi cikin sanyi tace. "Ba fita zamuyi ba?". Ido ya zubawa fuskarta yana kallon yadda take mgn da alamun tsiwa da tura baki. Uhum wato yanzu ta worke tsiwar zata dawo. Ya raya a ransa, a zahiri kuma kai ya jujjuya mata, tare da ronƙofowa, kan cinyoyinta. Hannunshi ya miƙa ya jawo marfin ya rufe. Su Galadima kuwa kan zuwa sukayi suka zagaye motar tashi, suna jiran fitowarshi. A hankali ya buɗe marfin dake kusa dashi. Kana yasa ƙafarshi ta dama, ya fita. Meda ƙofar yayi ya rufe ganin tana shirin fitowa. Buɗe al'kyabbar jikinshi yayi kana ya gyara zamanta. Bayanshi Galadima ya koma. Sannan Jalal da abokanshi suka koma gefe-gefenshi. Sauran ayari kuma suka rufa mishi baya. Su kuwa can cikin taron fulanin da sauri Arɗo Maru ya miƙe da sauran ƙananan Arɗo na gefenshi, kasan cewar shine Arɗon araɗabe na yankin gaba ɗaya. Da sauri suka nufosu cikin mutumtaka da fara'a suka iso. Hannu ya bawa Sheykh tare da nuna mishi hanyar shiga inda sukayi musu shimfiɗa can cikin manyan rufuna. "Bismillah GARKUWAn mu, gatanmu a idon gwamnatin jiha data ƙasa, bismillah gacan wurin zama". Kanshi ya jinjina kana yabi bayanshi sauransu suka biyo bayanshi. Bayan suna zauna ne, duk Arɗo's ɗin suka zagayeshi ta gaba su Galadima da sauran tawagar kuma suna baya. Kana dogorai kuma na tsaye. Arɗon araɗabe kuwa, yana gabanshi. Gyara zamanshi yayi ya fuskanci Arɗon araɗabe cikin tattausan lafazi yayi ɗan murmushi tare da cewa. "Kuna lfy ko? ba wata matsalar ko?". Murmushi Arɗon araɗabe yayi tare da cewa. "Lfy lau Alhamdulillah". Kanshi ya ɗan ɗago ya kallesu baki ɗayansu kana yace. "Masha Allah. To Allah ya taimaka". Amin Amin sukace cike da jin daɗi, shi kuwa fuskantarsu yayi dukansu tare da cewa. "Na kawo wannan ziyarar ne dan samar da Kekkyawar alaƙa da kauda fitina tsakanin makiyaya da manoma da sauran al',lummar gari. Ina al'fahari da dukanku biyu uku makiyaya manoma jama'ar gari. Bana son wani sashin ya cutar da wani sashin. Ina neman al'farma daku zauna lfy da manoma banda yi musu ɓarna akan haƙinsu. su wahala su noma kusa dabobbin ku suci su taka kunsa ya tabbata baku da gskya duniya zata ɗaukemu masu tada zaune tsaye. Amman ina kuka bari manoma suka tattara kayan amfaninsu sai ku nemi izinisu ku shiga kuyi kiwo a gona kinsu". Cikin gamsuwa da bayaninshi suka haɗa baki wurin cewa. "In Sha Allahu zamu kiyaye, bazaka samemu a layin masu tsokana ba mu nan Jafuna". Kanshi ya gyaɗa cikin gamsuwa kana yace. "Muddin manomi ya neme ku da fitina ko wasu sauran gama gari kada ku tanka musu. Ga number wayata zan baku koda yaushe kuka kira zata shiga. Zan sanar da ƙungiyar *MI YETTI ALLAH* itace ƙungiyar dake kula da matsalolin makiyaya da manoma. Sannan duk inda kuke akwai mambobinmu a garuruwan dake kusa daku zasu shiga lamarin. Duk wanda aka samu da rashin gsky zai fuskaci Hukunci. Kana Ƙungiyar *TABITAL POOLAKU* tana tare daku a cikin dukkan al'amuran ku. Kiyaye shigar banza kamar dai yadda na ganku yanzu cikin manyan suturu shine abinda yafi dacewa damu a matsayinmu na musulmai". Cikin murmushin Arɗon araɗabe yace. "Zamu kiyaye, kuma dama mu Jafunawa bamu ɗaya daga cikin ƙabilun dake yawo a daji da kiwo masu yaɗa barna. Mu Jafunawa ko suturarmu ta banbanta data sauran makiyaya". Hannu ya bashi bayan ya basu number miƙewa sukayi tare. Da musu godiya Kana suka rakasu har wurin motocinsu, nan Galadima ya miƙa musu kyautan kuɗin taimakon da Sheykh ya ware musu. Nan suka shiga suka tafi a jere kamar dai yadda sukazo. Tafiya mai ɗan nisa sukayi kana suka dawo kan hanya. Jihar Jigawa suka nufa, Dan yana so a ƙalla dai a yau ya zauna da Arɗaɓen jihohi uku Kamar yadda ya tattauna da Rugar forko hakama ta biyu. Sun amshesu a mutunce. Daga nan suka nufi jihar (Tsinako) Katsina. Daji suka nausa karfe biyar dai-dai suka isa Rugar da Arɗon araɗabe nasu yake. Dai-dai lokacin kuma gaba ɗaya makiyayan sunata dawowa kiwo. Bayan sun fitone, suka nufi inda suke. Cike da mamaki Sheykh da tawagarsa duk ke kallon mutanen wannan Rugar. Gaba ɗayansu maza garin kitsone a kawunansu reras har kafaɗunsu. Ga wasu irin guntayen wondunan yadin atampa na mata, kana rigunan tashi kabi shanu a jikinsu. Kowa ka gani da sanda a wuyanshi. Ba yabo ba Fallasa suka marab cesu. Bayan sun gaisa ne yayi musu jawabin abinda ya kawosu. Ɗaya daga cikin Arɗo's ɗin ne yace. "To wannan shiga dai itace muka samu wurin iyaye da kakanni babu kuma abinda take mana mu ba a takure mikeba kamar yadda kace. Sannan batun manoma kuma infa suka tsokanemu mu bazamu jira wata hukumar. MI YETTI ALLAH da TABITAL POOLAKU ba. Zamu rama". Murmushi Jalal yayi tare da cewa. "In kunfi ƙarfin kungiyar ku ta mi YETTI ALLAH da TABITAL POOLAKU. Tabbas bazakufi ƙarfi mu mu rundunar tawagar sojojin ƙasar ba. Ku iye harshenku tabbatar da zaman lfy ne ya kawomu nan ba musuba kuma umarnine." Cike da mamaki Ya Hashim da Laminu da Sulaiman harma da Jamil suka zubawa Jalal ido. Mgnarshi ta nuna cewa, shi sojane mai ƙarfin iko kenan. Rigar dake jikinshi ta sama ya cire. Sai ga rigar sojojin ƙasar Nigeria ta baiyana a jikinshi a saman kafaɗunshi. Taurari biyu da kuma alamar Shaho colonel ne kenan. Suma sauran abokanshi biyu rigunansu na sama suka cire. Ganin hakane yasa waɗannan makiyayan sukayi ƙasa da kawunansu. Shi kuwa Sheykh. Gyara zamanshi tare da cewa. "Zama lfy yafi zama ɗan sarki, inji bahaushe to, tabbas mu zauna lfy shine ci gabanmu." Sai kuma ya kalli Galadima dake gefenshi yace. "Waɗannan mutanen a dasawa Rugarsu ayar tambaya. Ku tashi mu tafi, in naji wani kuskure ko tsokana daga gareku tabbas zaku fuskanci fushin ƙungiyar mu, zamu kuma miƙaku hannun hukumar ƙasa. In kuwa wasune suka tsokaneku ga number ta ku gaya min haƙiƙa zamubi kadunku bazan lamunci a cutar daku ba." Da sauri Arɗon Arɗaɓen ya biyo bayansu da sauran wasu dattawansu. Haƙuri suka bashi tare da al'warin zaman lfy. Kana bazasu bari ayi husumaba. Da haka dai sukayi sallama suka tafi. Madadin su kwana cikin jihar Tsinako indama sukeda cikekken ikon a masarautarsu Haroon ga uwa mai daraja Umaymah sai suka wuce jihar Noka bayan sunyi sallan mangriba da isha'i. Suka ɗau Hanya. Gajiya iya gajiya sunyishi. Gaba ɗaya kowa jikinsa yayi nuƙui sabida ba ƙaramar tafiya sukayi ba. Wuni a zaune tun karfe bakwai na safe har yanzu takwas na dare kan tafiya suke kuma babu alamun sun kusa jihar Nokan. A cikin motarsu Jalal da abokanshi sunata hirarsu. Laminu kuwa tuni ya sanarwa Gimbiya Saudatu ashe Jalal sojane. Ta girgiza da jin lbrin sosai. A motarsu Galadima kuwa shiru duk sukayi dan gajiya ga jikin tsufa. Ita kuwa Aysha dama tunda aka hanata fita, ta kumbura ta cika tayi tib bata sake kulashiba, shima ko inda take bai kuma kallonba. Bare yanzu aikin tura rahoton tsarin Rugar da suka fito yake turawa Haroon. Ta E-mail address ɗin shi sabida shi baya whatsapp. Bayani yake mishi ya isar da saƙon ga masarautarsu dan a sawa mutanen wannan yankin ido sosai, ya lura basu da nitsuwa. Haroon kuwa Umaymah ya kalla cike da mamaki yace. "Kinaji Umaymah Sheykh fa yau jihar nan ya wuni. Wai yanzu madadin ya kwana a nan shine ya wuce Nokan a daren nan". Murmushi tayi tare da cewa. "Na sani ai munyi mgna da Aysha. Tare da ita suke shiyasa bazai iso nanba". Murmushi Haroon yayi kana sukaci gaba da hirarsu. Sai ƙarfe Goma da rabi suka isa Nokan state. Wani tamfatsetsen hotel mai zaman kanshi suka nufa. A cikin motar ya rufeta. Kana ya fita. Su Jamil duk na biye dasu a baya. Ɗakuna ya kama musu gaba ɗayansu sannan ya juyo ya dawo shi ɗaya. Motar yazo ya buɗe tare da cewa. "Bismillah". Tura baki tayi tare da cewa. "A barni zan kwana cikin motar". Kanshi ya sunkuyar tare da kaurara muryarshi yace. "Ki fito". A hankali ta zuro ƙafafuwan ta woje, sun ɗan kumbura alamun dadewa a zaune. Sabida ko abinci saya sukeyi a cikin mota sukeci. Sai dai shi wunin duka dabino yakeci. Miƙewa tayi ta fito. Hannunshi yasa ya ɗauki jakar kayanshi. A hankali yayi gaba tana biye dashi a baya. Hotel ɗin babbane mai matuƙar kyau. Wani Side shi wai VIP can suka nufa. Suna shiga cikin falon, ta zauna bisa kujera. Shi kuwa ajiye jakar yayi kana, ya miƙe tsaye, Jikin ƙofar ɗakin ya koma ya rufe kana ya zubawa ƙofor ido. Tsawon mituna biyar, kana ya dawo wurin abun kunna fankan daga nan kuma ya dawo tsakiyar falon saman jikin fanka ya tsurawa ido. Ita kuma tana binshi da ido, ne ganin kamar wani abu yake nema. Bedroom ya wuce. Ya fara bincikar ɗakin. A jikin masaƙalin Rimot ɗin AC yaga wani ɗan ƙaramin abu. Hannunshi yasa ya cire abun. Kana ya fito jakar ya ɗauka tare da cewa. "Mu tafi". Cikin gajiya da wani irin nannauyan masifeffen baccin daya cika mata ido ya kashe mata jiki da gajiya tace. "Ina kuma zamu je? ni bacci nakeji! Ni na gaji". Hannunshi yasa ya kamo nata hannun. Wani ɗakin suka kuma komawa aka basu key tare da bashi haƙurin da ita dai bata san kanme suketa bashi haƙurinba sunata rantsawar basu sani bane. Ma'aikatan hotel ɗin da kansune suka bi bincika ɗakin kana suka fita, suna cewa. "In sha Allah zamu kula zamu kuma kiyaye gaba". Rufe ƙofar yayi kana ya wuce bedroom. Ita kuwa bisa kujerar ta kwanta tana sauƙe numfashin gajiya da bacci a take bacci ya saceta. Shi kuwa Sheykh wonka yayi kana ya fito yayi shirin baccinsa. Leƙowa falon yayi. Tuni tayi bacci bisa kujera sai numfashin gajiya take sauƙewa a hankali baccin kuma mai nauyi takeyi. A hankali ya iso inda take, "Ke Tashi kije kiyi wonka". Yace yana kallonta. Shiru kamar bata da rai ko motsi batayi ba. Karo na uku ya kuma cewa. "Ke tashi kije kiyi wonka ki kwanta". Still ko mitsin batayi ba. A hankali ya ɗan sunkuyo kanta. Hannunshi yasa ya ɗan kamo hannun ta tare da cewa. "Tashi kije kiyi wonka zakiji sauƙin gajiyar". Cikin bacci tace. "Uhum-Uhum. Ni na gaji ka barni bazanyi wonka bacci zanyi". Kanshi ya juya tare da cewa. "Uhummm yanzuma tsami kikeyi, Ni in bakiyi wonkaba bazan kwana dake ɗaki ɗaya ba". Cikin baccin ta ɗan kalleshi tare da lumshe ido tace. "Ni Ko sati nayi banyi wonkaba bana tsami, kuma ni zan kwana a nan kaje can ɗakin". Da sauri yace. "Rufe baki yarinya ko yaushe bakinki baya shiru. Muje kiyi wonka". Komawa tayi ta konta, tare da lumshe idanunta, da suke cike da bacci mai nauyi da gajiya tuni ta meda baccinta". Juyawa yayi ya koma Bathroom ruwan ɗumi mai ɗan zafi sosai ya cika baf ɗin kana, ya fito. Gefenta ya zauna. A hankali yasa hannunshin ya fara zuge zip ɗin rigarta, shiru tayi tana baccinta. Ƙarasa zuge zip ɗin rigar yayi tare da cewa. "Tashi! Tashi!! Zan tuɓeki fa". Shiru kakeji kamar bata da rai". Kanshi ya jingina da kujerar. Kana ya fara yin ƙasa dashi tare da ɗan ɗagota ya jinginata da jikinshi. Still tana baccinta. Ƙasa yayi da rigar ya cire mata hannayen ya rage bra ne a ƙirjinta, ɗan jawota yayi ya kifeta kan cinyarshi ya ɓalle masaƙalin yayi kana ya ɗan ɗagota ya cireshi a hankali. Yana cewa. "Tashi to! Tashi kinji!". Shiru abinta, ɗan gajeren tsaki yayi tare da. Manna bayanta da ƙirjinshi. Shiru yayi tare da zuro kanshi tsakanin wuyanta da kafaɗanta, Caɓɓullenta da suke tamfatse a cike tab a ƙirjinta ya ɗan kalla. Da sauri ya rumtse idanunshi, tare da ƙara mannata a ƙirjinshi. Hannunshi yasa a hankali ya fara murza rigar yanayin ƙasa da ita, shiru yayi jin ta ɗan riƙe hannunshi. Sai kuma ya sauƙe ajiyan zuciya cin ta sake hannunshi ta koma tayi lib alamun ta koma nannauyan baccin gajiyar data kwasa ɗin. Ƙafarshi yasa tsakanin cinyoyinta tura rigar yayi ƙasa gaba ɗaya. A hankali yaji idonshi na mishi rawa, buɗesu yayi ya zubasu kan surar jikinta. Wani irin harbawa da azaban ƙarfi yaji Sheykh ɗin shi tayi. A hankali yasa hannunshin kan santala-santalan cinyoyinta, yana kallon yadda gajeren wodon dake iya guiwarta yayi lib a jikinta. a hankali ya sonkuyo sosai ya kai bakinshi saitin kunnenta cikin wata iriyar raunatacciysr murya mai cike da gajiya, Feeling, da sanyi yace. "Aish! Aish!! Tashi muje kiyi wonka". Ɗan buɗe idonta tayi jin ɗumin numfashinsa a kunnenta da ɗan sautin mgn da taji can cikin baccinta. Mirginawa tayi a jikinshi da kyau, sabida, wani irin masifeffen sanyin ac da taji yana ratsa ta sabida cire kayan jikinta da yayi. A hankali tasa hannunta ta kamo hannayenshi duka biyu ta mannasu kan ƙirjinta. Tare da duƙun-ƙunewa a jikinshi. Wani irin tsalle yayi lokacin da yaji ta manna tafin hannunshi kan C...! Littafina GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 numbers ɗin jikin katin zaki rubuto ki turo min ba hoton katinba. Bana son VTU bana son transfer. In Kuma special Group kikeso kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo shaidar ta number ta da nake whatsapp dashi 09097853276. Banda VTN banda transfern kati. By *GARKUWAR FULANI* Caɓɓullenta. Wani irin abu yaji zir-zir-zir-zirrrrr yana tafiya daga cikin tafin hannunshi har zuwa tsakiyar maɗigan kanshi. Da sauri ya rumtse idanunshi tare da matseta a jikinshi sabida wani irin abu da yaji yana sokin sashin jikinshi har zuwa cikin tafin ƙafarshi har kan manyan yatsun sawunshi dukansu biyu. Wani irin karkarwa lips ɗinshi Suka farayi kamar zasu tsinko suyi ƙasa. wani irin ja sukayi suna sheƙi kamar an shafa musu mai, suka zama tamkar tattausan kunnen fure. Tsikar jikinshi gaba ɗaya tashi tayi saye, har tsakiyan kanshi. Idanunshi ya buɗe cikin yanayin sauyin fitar numfashin. Kasa buɗe su gaba ɗaya yayi, sabida wani irin masifeffen abu da yakeji kamar hawayen da yakeji suna tsastsafo mishi kuma ba hawayen bane. Yaune karo na forko a rayuwarshi lokaci na forko da hannunshi ya taɓa Caɓɓulle da ganinsu ziraran miraran a kundin tarihin rayuwarsa, shiyasa abun yazo mishi a bazata ya hautsina mishi kwanya. A hankali ya ƙara haɗe ta da jikinshi. Ya buɗe lips ɗinshi a hankali murya na rawa magana can ƙasan maƙoshinsa yake cewa. "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yah Subahanallah. Tsarki ya tabbata ga Ubangijin talikai." Gaba ɗaya muryarshi sai ta kuma narkewa ta koma can ƙasan maƙoshinsa cikin wani irin yanayi mai wuyar misaltuwa yace. "A'ich! Ahhhh'i! chhhhh!!!". sai kuma yayi shiru jin numfashin sa na shirin fiffizgewa. Ita kuwa Aysha cikin baccin. Ta mirgina ta juyo jikinshi ta ruggumeshi gam-gam cikin magagin baccin ta fara rawan sanyin. Karkarwan da jikinshi keyi ya tsananta. Hannunshi yasa ya tallabeta da kyau, tattaro sauran kuzari shi yayi. Ya cicciɓeta ya nufi bedroom da ita. Kan gado ya kontar da ita kana ya kashe wutan ɗakin. Sannan ya kwanta gefenta, borgon ya jawo ya rimufesu. Jawota jikinshi yayi, jin ɗumin jikinshi yasata manne mishi da kyau. hannunshi yasa a tsakiyar bayanta, a hankali ya zura yatsarshi tsakiyan kormin bayanta, daga ƙasa kan ƙugunta, a hankali yake jawo yatsar zuwa sama yanayi yana tafiyar tsutsa. A hankali ta fara gantsarewa tana ƙara turo mishi ƙirjinta cikin jikinsa, tare dasa hannunta ta saƙalo wuyan gam-gam. A hankali yace. "Wash Allah na Mamey zata shaƙe miki ni". Sai kuma ya mirginata, tayi ƙasa shi kuma ya zama yana samanta. Sake mata nauyinshi yayi kaɗan. Da sauri ta buɗe idonta tare da cewa. "Wayyo Yah Sheykh". Da sauri ya haɗe goshinsu wuri ɗaya, haƙoranshi yasa ya ɗan kama lips ɗinta duka biyu ya ɗan ciza a hankali. Zilllo ta kumayi tare da janye kanta kana tace. "Wayyo Ummey na bakina". Kanshi ya manna kan ƙirjinta, bada saninshi ba kuma bada niyarshiba ba kuma da sonshi ba, ba kuma da zatonshi ba. hakanan yaji ya manna bakinshi kan Nipples ɗinta. Zillo tayi da ƙarfi. shi kuwa danneta yayi da kyau, kana ya liƙa tattausan harshensa ƙan Nimple ɗinta. ya kamashi tamkar wanda ya samo tom-tom. Wani irin fitinenne numfarfashi suka sauƙe a tare. da ƙarfi tasa tafin hannunta cikin sunan kanshi murya a daburce can ƙasa tace. "Washhhhh Yahhh Sheykh!". Karkarwa jikinsu ya farayi a tare, wani irin kukan da bata san na menene ba ta sake. tare da yayyarfa hannunta. Hakane ya sashi mirginawa ya konta gefe kana ya jata ya ruggumeta tsam a jikinshi hancinshi ya cusa a wuyanta tare da shaƙan dogon numfashi mai cike da zallan wutar fitina. hankali murya can ƙasa maƙoshi ya fizgo mgnar murya can ƙasa yace. "Tsami kikeyi bakiyi wonkaba". Ya ƙareshe mgnar yana cusa hancisa cikin wuyanta da kyau, tare dasa hannunshi bisa breast ɗinta. Maƙe kafaɗarta tayi tare da yin lib a jikinshi. shi kuwa ɗan ɗaga ƙafarshi yayi ya ɗaura kanta. kana ya lumshe idonshi yana kanainaye da ita. A haka bacci ya kwasheta. Shi kuwa Sheykh al'amarin ya zarce zaton mai zato abun ya wuce tunaninku, haka nan yake jin wani irin yelwatacce kuma mashahurin sanyi na ratsa zuciyarshi. Washe gari da Asuba su Galadima da sauran tawagar duk kowa ya fito. A falon ɗakin da Galadima yake suka haɗu suna jiran Sheykh ya iso ya limamcesu. Shi kuwa Sheykh, karo na forko kenan da ya makara, sallan asuba sabida wani irin baccin da yayi mai cike da ma'anoni. A hankali ya buɗe idonshi. Ganin yadda suke kwance liƙe jikin junane ya sashi tuno abinda ya faru tsakanin su, daren jiya. Fuskarshi ya haɗe tare da hararanta. Kana ya miƙe da sauri ya shiga, bathroom, wonka yayi kana yayi al'wala. Sannan ya fito. Wata al'kyabbar da jallabiyar ya fidda. Ya saka kana ya ninke waɗanda ya cire da kuma kayan baccinsa. Ya maida cikin jakar. Yana fisa turare a jikinshi ya ɗan matso bakin gadon yana cewa. "Aich! Aich tashi kiyi salla zamu tafi". Miƙa tayi tare da ƙara jan borgon. Ganin haka ne, ya juya ya fita. Ita kuwa ganin ya fitane ta koma ta kwanta abinta. Shi kuwa yana zuwa ya limancesu suka tada salla. Bayan sun idarne sukayi Azkar kana yace, duk su shirya suci gaba da tafiya da abinda ya fito dasu. Miƙewa Galadima yayi tare da cewa. "Duk a shirye muke ai, mu tafi kawai". To sukace kana suka fito. Su duka suka nufi parking lot da yan jakukkunan kayansu a hannunsu. Shi kuma ya nufi ɗakinsu. A kwance ya sameta kamar yadda ya barta. Fuska ya haɗe tare da matsota yana cewa. "Ke kin tashi kinyi sallan ne ko yaya?". Da sauri ta tashi zaune, jin muryarshi a sama. Tama mance babu riga a jikinta. Ido ya zubawa ƙirjinta. a da sauri ta kalli inda yake kallo. Da sauri taja borgon ta rufe ƙirjinta. Shi kuwa tsaki ya ɗanja tare da cewa. "Tashi daga nan kije kiyi wonka kizo kiyi salla". Ya faɗi mgnar yana bata baya. Da sauri ta juya ta shiga bathroom. Wonka tayi da ruwan zafi. Haka yasa ta ɗanji daɗin jikinta gajiyar ta ragu. Shi kuwa rigarta da bra ɗin ta dake falon ya ɗauko. Yana isowa ya ninkesu. Ita kuwa kai ta ɗan leƙo tare da cewa. "Yah Sheykh!". Ido ya lumshe tare da jin wani sanyi a ranshi Allah ya sani sunan yana mishi daɗi, ko dan salon yadda take fidda sunanne. cikin wani irin yanayi yace. "Na'am". Ƙeyarshi ta zubawa ido tare da cewa. "Ayyah jakata na cikin mota, a ɗauko min". A hankali ya ɗan juyo tare da cewa. "Nine ɗan aikenki kenan?". Da sauri ta jujjuya mishi kai. Shi kuwa jakarshi ya buɗe yasa rigarta da bra daya ninke a gefen da yasa nashi daya cire. Wata doguwar riga ya ciro sabuwa fil da gyalenta babba. Juyowa yayi tare da cewa. "Fito min da towel na". A hankali ta fito ɗaure da tattausan towel. Da wondonta a hannunta. Motsata yayi ya miƙa mata rigar tare da cewa. "Gashi inji Aunty Hafsat itace ta saya miki, zuwanmu Umrah". Da sauri ta amsa tare da cewa. "Ngd matuƙa Allah ya ƙara girma ya biya mata bukatarta". Da sauri yace. "Amin". Ta lura ta kuma fahimta yana matukar son tayiwa Ya Jafar addu'o'in samun lfy, tana ganin farin cikinsa a kan haka. Kuma ta gane yanajin daɗin ta mishi addu'o'in Allah ya biya mishi buƙatar sa dasu Umaymah. Hakane yasa take zaton sunada wata babbar buƙata a duniya a wurin mahalinmu." Cikin sanyi tace. "Yah Sheykh". Juyowa yayi yana kallonta. Allah ya sani yana jin wani abu na dukan zuciyarshi duk sanda ta kirashi Yah Sheykh. A hankali tace. "Bra ɗina". Baki ya ɗan taɓe tare da cewa. "Yana tsami". Ya juya yana rufe jakar. Tura baki tayi tare, da zura rigar. Yane gyalen tayi a kanta kana, ta kabbarta sallah. Bisa sallayar daya shimfiɗa mata. Gefenta ya zauna yana kallon yadda take sallan. Bayan ta idarne, ta ninke sallayar. Kana ta miƙe tsaye sallayar ta miƙa masa. Kana ya riƙe jakar yace. "To mu tafi tun ɗazu ke ake jira". Su Jalal kuwa Affan dariya yayi hangosu suna tahowa. A ranshi yace. "Uhumm Hamma Jabeer ai duk saurinka a tafiya in dai da macece sai ta jaza maka tsaikon. Yana zuwa suka shiga Mota, dama su duk suna cikin. Jan motar Ado yayi suka tafi. Bakwai dai-dai ta ɗan kalleshi ganin zasu fita subar cikin gari a hankali tace. "Yunwa fa nakeji". Juyowa yayi ya ɗan kalleta tare da taɓe baki yace. "Bubbuga rumbun Abboi". Da sauri ta juyo ta kalleshi cikin mamakin sunan daya kirata. Shi kuwa kauda kanshi yayi. Tafiya kaɗan sukayi taga sun tsaya a gaban wani katafaren Restaurant mai masifar kyau da tsaruwa. Jim kaɗan Affan da Jalal da Sulaiman da Laminu suka fita. Suka shiga ciki. Jim kaɗan suka fito da ma'aikatan ciki da ledodin masu kyau a hannunsu. Affan ne ya nufi motar Sheykh da leda biyu ɗaya babba ɗayar kuma yar dai-dai. Ado ya miƙawa ɗayar kana ya buɗe baya gefen Aysha yace. "Aunty Aysha ga breakfast". Murmushi tayi tare da cewa. "Sannu". Yauwa yace kana ya juya ya nufi motarsu. Dan tuni Jalal Laminu da Sulaiman sun mimmiƙawa sauran nasu. Nan sukaci gaba da tafiya. Juyowa yayi ya ɗan kalleta tare da cewa. "Sai kici kada ki cinyeni ɗanye". Ya ƙarashe mgnar yana kallon gefen fuskarta Gyara zamanta tayi kana ta buɗe ladar ta fara cin abinda ya mata. Shi kuma yaci gaba da wayar da yakeyi da Umaymah. Haka dai wunin ranarma suka wuni, sunje rugagen Arɗon Arɗaɓen uku a ranar. Yayinda Duniya ke ganin ziyar GARKUWAN FULANI, zuwa ga dajukan da fulanin ke rayuwa, ta sanadin ɗaukar Laminu da Jamil. Suna turawa ma aikatarsu a jaridu da kuma tv da gidajen rediyo. Yau kwanansu hudu yau wunin na biyar kenan. Tunda sanyin safiyar suka tashi daga masauƙinsu na Barata state. Wanda yanzu sun zagoyo. Sun dawo kusa da gida daga Barata zuwa jihar Ɓadamaya ba wani State ɗin. Sai dai tafiyar mai nisace sosai hakane yasa. suka tashi da wuri dan gefe zasu kuma nufa kafin su dawo hanyarsu. Ƙarfe takwas dai-dai suka isa Rugar Arɗon Arɗaɓen na Rugar Bugem . Dai-dai lokacin kuma makiyayan wurin keta sake dabobbi su dan tafiya kiwo. Cike da mamaki gaba ɗaya su Sheykh suke kallon dabobbin mutanen wannan yanki da suke masu jajayen shanu babu shanu ko ɗaya da zaka gani mai farar fata. Duk jajaye ne gaba ɗaya iya ganinka. Koda suka isa, bayan sun gaisa Sheykh ya musu bayani kamar yadda suka san da zuwansu. Buɗan bakin Arɗon Arɗaɓen sai cewa yayi. "To in bamu ciyar da dabbobinmu da ciyawar manoba to da mi zamu cidasu?. Ai dole mu shiga muyi kiwo du inda mukaga dama, dan aradun Allah da dabbobinmu su kwana da yunwa gwara mu bamuci ba". Ya ƙareshe mgnar da gurɓata ciyar hausarshi. "Cikin fushi Sheykh yace. "To ku gwada ku gani". Cikin tijara ta wasu daga cikin ƙabilun fulanin daji Arɗo yace. "Ba mu gwada ba zakaceba GARKUWA. ai munayi, mu ƙara dai mu gani zakashe! Kuma babu abinda zamu gani, mu ko ina garinmu ne". Jamil ne yayi dariya tare da ɗaukar duk wani motsinsu yana turawa kai, tsaye. Jalal kuwa tuni ya kira het kotan Sojoji na jihar ya sanar musu. Dasu zo su binciki mutanen. Domin gaba ɗaya kowa ka gani da wuka ko arda a jikinsu. Sun tara wani shegen gashin da babu gyara. Daga nan suka miƙe suka nufi inda motocinsu suke. Ƙarfe biyar suka fito cikin dajin suka dawo cikin birnin Barata. Nan sukayi salla. Kana sukaci abinci kafin suka kama hanyar jihar Ɓadamaya. Wanda zasuyi isan dare duk gudun da zasuyi. Suna shiga Mota sukaci gaba da tafiya. Ta gefen idonshi ya kalli Aysha, da tayi shiru tana kallon gefen titi tana murmushi. Hankalinshi ya ɗan maida kan System ɗinshi dake kan cinyarsa. "Murmushin me kikeyi?". Yayi mgnar tamkar ba shi yayi mgnar ba. Juyowa tayi ta ɗan kalleshi tare da cewa. "Ba murmushi nakeyi ba!". Cike da mamaki ya juyo ya ɗan kalleta a fizge kana yace. "Kuka kikeyi kenan?". Kanta ta ɗan sunkuyar cikin tura baki tace. "A a kam". Ajiyan zuciya mai tsawo ya sauƙe tare da lumshe idonsa. Kana ya koma ya jingina bayanshi da kujerar yana lissafi yau sallan layya saura kwana takwas. Ita kuwa Aysha shiru tayi tana nazarin. Toshi wannan wanne irin mutum ne? Taya zata iya fahimtar harshensa? Yanada iya sarrafa harshe duk dagiyarka sai ya kureka. Ba'a gane ina alƙibilarsa ta dosa. Cikin sanyi ta juyo ta kalleshi. Jin ya matso kusa da ita sosai. Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta. Sannan ya kalli madubin motar Ado bazai ganshiba kuma bazai jisuba. Cikin fidda sassanyan numfashi yasa hannunshi ya kamo hannun ta. Zamewa yayi susai bisa kujerar ya zama tsawonsa dai-dai dana juna sajenshi ya manna a fuskarta. A hankali ya ɗan goga mata sajen. Tare dasa hannun shi. Ya ɗan tallabo haɓarta ya ɗan juyo fuskarta kusa da tashi fuskarshin. Al'amarin Yah Sheykh na dabanne komai nashi na dabanne. Shiyasa gaba ɗaya ta gaza yin komai sai zuciyarta dake harbawa. Shi kuwa Yah Sheykh hannunshi na kusa da ita yasa ya zagayo ƙugunta. Kana hannunshi ɗayan kuma. Ya kamo ɗaya hannun ta. Ya matse a kafaɗarshi. Ita kam Aysha shiru tayi, tana ji da ganin ikon Allah. jikinta kuma karkarwa yakeyi a hankali amman can cikin naman jikinta takejin rawan. Tattausan lips ɗinshi ya manna da kunnenta, a hankali murya can ƙasan maƙoshinsa yace. "Aish!". Cikin sanyi taji sautin muryarsa. Idonta ta juya tana. maimaita sunan a bakinta. "Aish!". Taji ya kuma kiranta, a hankali tace. "Na'am". Hannunta ya murza a wuyanshi tare da cewa. "In tambayeki wani abu mana?". Kanta ta gyaɗa a hankali al'amar eh. Gyara zamanshi yayi tare da cewa. "Naga fulanin nan duk ko wani yanki da sashin da mukaje yanayinsu zai banbanta dana saura. Wasuma basa fulataci. Wasu kuma hausa sukeyi wasuma wani yare sukeyi. Kuma duk fulanine?". Cikin sanyi tace. "A a ba duka fulani bane, akwai ƙabilu mabanbanta a cikin daji da dabobbin a gabansu. Yayinda in mutane gama gari suka gansu sukeyi musu kuɗin gorowa wato sai ace duk fulanin ne". Lips ɗinshi ya ɗan goga a kunnenta. Yana shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinta. ita kuwa da sauri ta ɗan maƙe kafaɗarta jin yadda ya goga mata tattausan laɓɓansa. kana ya hura mata isa a kunnenta. A hankali yace. "To menene babbancin gayamin inji". Haka nan taji kasala tarufeta. Shi kuwa cire tafin hannunta yayi a wuyanshi ya manneshi da nashi tafin hannun. Kana ya sauƙeshi kan System ɗinshi. A hankali yace. "Ina jinki gaya min a hankali, kada kimin ihu a kunne kinji ko Aish kiyi hankali". Numfashin ta fesar a hankali kana tace. "Ka tuna Rugar forko da mukaje?". Dan matse hannunta yayi tare da cewa. "Muhammad Jabeer baya mantuwa, gaya min kawai, kaina ba irin naki bane, da wasu ke birki tashi". Ɗan hararanshi tayi tare da tura bakinta kaɗan. "Karon forko a iya tsawon watannin da ta zauna dashi da taga yayi murmushi, kuma murmushi yayi masifar mishi kyau. Cikin murmushin yace. "To ni dai gaya min ba tsiwa nace kimin ba". Ya ƙarashe mgnar yana haɗe fuskarshi da gefen fuskarta. A hankali tace. "To a cikin fulanin ko ince makiyayan dake cikin daji da kiwon dabobbi akwaisu daban-daban. Akwai. 1 JAFUNAWA, 2 UDAWA, AKWAI 3 KASINAWA, AKWAI KUMA 4 KASINALLE, AKWAI 5 SULLUƁAWA, AKWAI 6 DAƊA WOGGA, AKWAI 7 YAN JAJAYE, AKWAI 8 JOTTAN MA'EN AKWAI 9 TEMA'EN akwai Kuma 10 ƳAN BOKOLOJI." Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "To menene babbancinsu." Kanta ta ɗan ɗago ta kalleshi, tattausan gemunshi na gogan goshinta. Shi kuwa idonshi ya ɗan rage tare da cewa. "Na'am Yah Aish". A hankali taci gaba da cewa. "JAFUNAWA, sune masu sa manyan kaya jomfofinsu masu faɗi da zurfi. Asalin fulanine basa son fitina ko kaɗan, sune wanda muka fara zuwa wurinsu. Akwai Katsinalle su kuma sune masuyin kitso mazansu da matansu Hausawa ne makiyaya ashar a bakinsu kamar ruwa. Basu da kunya sai dai sunada tsoro, yanzu zasu fetsare ido zuwa mutun rashin kunya barazana kaɗan zaka musu su tsorita. Kana sai SULLUƁAWA sune, masu yin kitso da man shanu. In Suka wuceka zakaji suna ƙarni kaga maiƙon man shanu na bin wuyansu, basu fiye yin fillanci ba sai hausa. Sai kuma UDAWA sune masu tasowa daga wata ƙasar su zo nan sunfi zama ƙasar Chadi. Sam ma ba funin ƙasarnan bane, kuma bama Fulani bane, su kashe mutun bai zame musu abin tsoroba, mugayen. Sai kuma BOƊEJIN masu Ƴan JAJAYEN shunu. Suma zuwa sukeyi mafi akasari daga kasashen Arewa suke zuwa. Shanayensu duk jajayene, babu wata ƙabila cikin masu bin daji da suka kaisu jaraba da son mata. Mazansu basa gajiya da mata. Matansu basa gajiya da maza. Suna iya tare mace a daji suyi mata fyaɗe su wuce ta ba damuwarsu bane mafi akasari daga Senegal, Chadi, suke tahowa duk sanda suka san damuna ta ɗauke anyi amfanin gona ba'a gama tattateshi ba." Ɗan ɗagowa tayi ta kalleshi jin ya ruggumeta tsam a jikinshi tare da cewa. "Ashe Allah ya rufa min asiri yamin gata". A hankali tace. "Kamar yaya?". Cikin taɓe baki yace. "Da basu cinye min hadiman Gimbiya Aminatu na data haɗomu dasu dan yi miki hidima ba". Uhum tace tare da yin mgnar zuci. "Lallai ma Yah Sheykh watoma shi Hadiman gidansu ya jiwa tsoro ni Ko oho ko?". Sassauta riƙon da yayi mata yayi tare da cewa. "Ina jinki Yah Aish sauran fa?". Kanta ta manna a damtsen hannunshi tare da cewa. "Sai ƴan BBOKOLOJI sune zakaga shanayensu basu da ƙaho, ɗaɗɗaya zaka samu cikin shanayensu masu ƙaho, shima sai ka samu ƙahon ɗan ƙanƙanine kuma, in ka ɗan taɓashi sai kaji yana girgiza. Kuma a haka sunfi shanaye masu ƙaho masifa da zafi. Kuma duk cikin shanaye babu shanun daya kaisu ƙiba in an kiwatasu, makiyayan BOKOLOJI asalin fulanine kuma na ƙasar nan. Su in suje gari, to sarakunan garin suke zuwa su samu, su biyasu kuɗi su saida musu dajukan manoma su. Daga nan Duk gonar wanda suka samu sai su shiga su kiwata abunsu su fita. In mai gona yayi mgna sai suce. "Mufa sayan gonakinku mukayi sarkinku shiua saida mana". Cike da mamaki ya kalleta tare da cewa. "Kenan ɓarnan da wasu ma kiyaye sukeyi dasa hannun sarakunan?". Kai ta jinjina tare dace mishi. "Tabbas kuwa". Idonta ta ɗan zubawa hannunshi daya cusa ta tsakanin bayanta da kujerar motar. Ya ruggume ƙugunta, hannun ya dawo har cikinta, a hankali ta lumshi idonta jin yana cusa hannunshin cikin rigarta kasancewar yau riga da zanine a jikinta. Sajenshi ya ɗan goga mata tare da cewa. "Kalli nan baki gamaba ai su waye JOTTAN MA'EN?". Ɗan matsowa jikinshi tayi jin yadda ya cusa hannunshi ya zira yatsarshi cikin hudar cibiyar ta. A hankali tace. "Hhhhh washhh". Idonshi ya ɗan zuba mata kana yasa bakinshi saitin kunnenta a hankali yace. "Yah dai Aish. Ci gaba mana". Wani irin masifeffen abu taji yana yawo a dukkanin jikinta, cikin sanyi kamar raɗa taci gaba da cewa. "JOTTAN MA'EN sune, Fulani mazauna wuri ɗaya, a ƙalla su shekara ashirin ko talatin zuwa sama kuma su basa ƙaura to sune JOTTAN MA'EN kamar dai fulanin Rugar Bani". Shiru tayi jin yadda ya liƙa lips ɗinshi a kunnenta a hankali yace. "Shhhhhhyyyy Yah Aishhhhhhhh. To kuma su waye TEMA'EN?". Murmushi tayi tare da cewa. "Ku mana!". Da sauri yayi sama da hannunshi, Caɓɓullenta ya ɗan cafke tare da cewa. "Mu kuma?". Hannunta dake cikin hannunshi ta fara ƙoƙarin ja, dan janye hannunshi dake cikin rigarta. Ƙara rumtse hannuntan yayi cikin nashi yanajin yadda Shey ɗinsa ke amsa amo da tsallen neman agaji. Dan ma ya samu System ɗinshi ta danneshi ta hanashi harbawa yadda take son tona mishi asiri. A hankali tace. "Eh mana fulanin cikin birni. Sune TEMA'EN dan in kunyi mgna kune kuke cewa Tema. Ma'anar tema (wata ƙil) shine Tema." Kanshi ya sunkuyar Sosai Yana sunsuna wuyanta, kallonshi tayi, shi kuwa a hankali yayi mata wani irin kallon dake nunida yana gab da fita haiyacinsa yace. "To ke kuma wanne babin kike?". A hankali tace. "Ni dai Aysha Aliyu Garkuwa Fulata marace. Da kuma JOTTAN MA'EN.". Cikin sanyi yace. "Menene fulata mare". "Fulata mare shuwa Arab kenan, Babana su fulata marane, asalin fulanin tsatson Shuwa'arab ne. Mamata kuwa JOTTAN MA'EN ne, Wuitin'en." Kanta ya manna kan ƙahon zuciyarshi dake harbawa. Shiru tayi tanajin yadda sautin bugawar keyi. A hankali yace. "Ngd da wannan bayani Shatu Bororiyar daji mai tallan nono da kiwo". Cikin jin daɗi tace. "Asalina kenan tushena bana ɓoyeshi. Ina al'faharin kasancewata bafulatanar daji makiyayiya yar Fulani makiyaya kuma manoma". Idonshi ɗaya ya lumshe tare da buɗe mata ɗayan. Ita kuwa a hankali. Bacci ya fara surarta sabida jin yana hura mata sassanyar iskar bakinshi. Da sauri yace. "Kada kiyi bacci Tashi muyi salla, sai mu wuce." Buɗe idonta tayi a hankali, kana suka fito. Su suka shiga wani gida dake kan hanya sukayi salla. Su kuma maza suka shiga Masallacin. Bayan sun idar sun fitone. Sukaci gaba da tafiya. Baifi awa ukuba su isaba aka kira sallan magriba. A wani ɗan kekyawan ƙauye suka tsaya sukayi sallan magriba da isha'i. Kana suka shiga Mota sukaci gaba da tafiya. Kasan cewar dare yayi kuma ga garin hadari ya ɗauro Haka yasa cikin motocin yin duhu. A hankali ya jawota jikinshi da kyau. Ruggume ta yayi gam a jikinshi. Lafewar tayi a jikinshi dan ba abinda takeson yi sama da bacci. Dan taci gaseshen naman da Affan ya saya mata. Tayi haniƙan tasha Dudunta mai sanyi. Tayi salla ga gajiya ga kuma. Bacci. Numfashin gajiya taja a hankali tare da shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinshi. A haka tayi baccinta kana sukaci gaba da tafiya. Ƙarfe goma da rabi tayi musu cikin masarautar Joɗa. A hankali aka nufi bakin part ɗin kowa. Har bakin mashigar hawa barandar falonshi motar ta ajiyesu. Ya sani Ummi bata nan tana sashin Gimbiya Aminatu shi yasa. Yace. "Alhamdulillah Ado fita jeka kawai, saida safe kazo ka ɗauke motar a nan". Cikin girmamawa Ado yace. "To". Daga nan ya fita ya juya ya tafi. Shi kuwa a hankali ya ɗan ɗagota tare da cewa. "Aish tashi mun isa gida". Ido ta ɗan lumshe tare da cewa. "Yah Sheykh Na gaji". Buɗe marfin motar yayi kana ya fito. Tallabe da ita. a bakin ƙofar falon ya direta, kana ya kalli inda Ummi ke ajiye mishi key ya ɗauka. Buɗe wa yayi ya shiga, riƙe da hannunta. Binshi kawai takeyi idonta, a lumshe alamun tana baccinta. Shiru Side ɗin. Sai dai komai yana share yana goge ko ina fes-fes sai ƙamshi yakeyi. Side ɗinsa ya wuce da ita. Tana dai biye dashi kamar yar yaye. Har cikin Bedroom ya wuce da ita. Tana ƙoƙarin konciya kan gado, ya jawota suka nufi Bathroom. Har cikin wurin wonkan ya shiga da ita. Kamar daga sama kamar mafarki taji sauƙan ruwan sanyi a jikinta. Wani irin zaro ido tayi tare da firgici tace. "Innalillahi". Sai kuma ta kalleshi ya karkata kai ya tsura mata kyawawan idonshi. Cikin tsiwa tace. "Nifa bazanyi wonkaba". Juyawa yayi ya fita tare da cewa. "Ashe kuwa yau a ciki zaki kwana". Yana fita ya maids marfin ya rufe. Da sauri tasa hannu ta rufe ruwan sanyin. Kana ta buɗe na ɗamin. Dole ta cire wannan kayan ta saƙalasu gefe. Kana tayi wonka fes. Sannan ta fito a zatonta yabar cikin bathroom ɗin bata san yana cikiba. Ta fito ɗaure da ɗankalinta daga gugunta zuwa guiwarta ta fito da niyar ta ɗauka towel. Tana fitowa ta ganshi tsaye a gefen wurin da al'kyabbar jikinshi yana brush. Da sauri ta juya. Shi kuwa bayanta yabi. Ya kamota buɗa al'kyabbar shi yayi gaba ɗaya kana ya haɗa da ita ya rufe kirif tare da cewa. "Ina zaki je?". "Zan ɗauko zaninane in ɓoye jikina". Ɗan taɓe baki yayi tare da cewa. "Meme za'a gani a nan?." Ya ƙareshe mgnar da ware al'kyabbar, da sauri tasa tafin hannunta ta tare ƙirjinta. Juyawa bayanta yayi ya cire al'kyabbar tashi. Kana ya zura mata a jikinta tare da rufeta kirib yace. "To jeki kwanta". Da sauri ta ware hannayenta ta sasu cikin hannun al'kyabbar kana ta haɗa bakinshi ta riƙe ta juyo ta fito. Kan gadonshi ta hau ta shiga borgon ba tare da ta cire al'kyabbar ba. Shi kuma wonka yayi kana ya shirya cikin kayan baccinsa. Sannan ya fito. Yanata zuba ƙamshi. Ita kuwa cikin ɗan baccin data farajin yana fizgarta ta ɗan buɗe idonta a hankali ta kalleshi sai kuma ta maidasu ta lumshe. Wutan ɗakin ya kashe kana yazo ya zauna gefen gadon. Hannunshi yasa ya lalubo wata yar mitsitsiyar waya dake kan Bedside drower'n dake gefenshi. Wasu yan danne-danne na 5 minute yayi. Kana ya juyo ya hau gadon ya kwanta yana fuskantarta. A hankali yasa hannunshin ya kamo hannunta ya jawota jikinshi. A tare suka sauƙe numfashin, Murya can ƙasan maƙoshinsa yace. "K....! Uhummm wani kayan sai amale. Wata soyayyar sai malamai ma gada annabawa. Wannan shafin nakune matan malamai da ustazai Dan ku kaɗai ne kuka san irin salon Sheykh. Littafin GARKUWA na kuɗine akwai Normal group da a wata ɗaya za'a gama Part two, ki sayi katin mtn ki kofi numbobin ki turomin ta wannan number da nakeyin whatsApp da ita 09097853276. Akwai kuma Special Group wanda a sati biyu kacal za'a gama Part two da izin Ubangiji a shiga Part 3 Shi Special Group 1k ne zakiyin min transfer'n ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turomin shaidar biyanki ta wannan number ta WhatsApp 09097853276. Dan Allah kada kiyi min VTU kada kiyi min TRANSFER ɗin katin waya bana so. In kinyi min VTU wlh ba ruwana. Uhummm Ya Allah ka bani sa'a mu gama littafin nan kafin azumi al'farmar Annabi da al'ƙur'ani. By *GARKUWAR FULANI* Yajuyo daita yace ketadabance my shatu samunki gareni alkhairi Ina godema Allah dayamallakamanke wani dadine ya lullubeni nasunkuyar dakaina na lalubo hannumsa nasaka abakina Ina Dan lasa ahankali hakan danakeyi yasa yaa shekh yafara tsuma atsaye take yagangaro da hannunsa Saman wuyana yanamun wata shafa wadda atare mukafara Mika baitsaya ko inaba sai naji bakinsa saman lallausan bakina Yana wani irin gurnani Wanda yatsoratani babu abunda jikina yakeyi Banda kyarma lokacin danaji yafara sakin layi tun inamaidamasa martani har nafara tsorata da salonsa ban ankaraba naji shekh dinsa tafara ratsa jikina shekh baimun dawasaba adaren babu Wanda bankiraba Amma shekh baisauraramunba harsaida yaga bana lumfashi alokacinne hankalinsa yadawo jikinsa shekh yarude yadinga kirana shatu shatu shiru hakan yasa yayi bandaki Dani dasuri yacika baho daruwan zafi yasakani ruwan dasuka Fara ratsanine yasa nafarfado daga suman danai aikuwa nasaki kuka abunka dama gani darakin ciwo shekh ba abunda yakeyi sai rarrashi albarka kuwa nashata "Ke zo nan, zoki cire min rigata." Da sauri tasa hannunta tattare rigar ta riƙe gam tare da cusa kanta cikin pillow'nshi tana ƙoƙarin juya baya tace. "To ai kai ka samin ita". Da sauri yasa hannunshin ya riƙo hannunta tare da cewa. "To dana sa miki ita ce miki nayi rigar baccice?. Tashi ki cire min riga kar ki yamutsa min ita". "Uuuhmmm ni kam ka barni inyi bacci na". "Anƙi a barki ɗin, cire min rigata sai in barki kiyi baccinki daga nan har safiyar gobe". Cikin baccin daya buwayeta. Ta zare hannunta cikin rigar tare da matsawa gefe, kaɗan zare ɗaya hannunma tayi, sannan ta migirna ta matsa gefen Blanket ɗin ta jawo ta dugungune a jikinta. Shi kuwa Sheykh zare al'kyabbar yayi ya maidata gefe. Kana a hankali ya mirgina ya isa inda take. A bayanta ya kwanta. Kanshi ya ɗan ɗago ya tallabeshi da hannunshi na hagu. Fuskarta ya ɗan leƙa ila kuwa ta lumshe idonta alamun zata maida baccin koma ta medashi. Janye borgon yayi da ƙarfi. Da sauri ta yunƙura ta juyo. Hannunshi ya ɗan buɗe hakan yasa ta faɗa jikinshi. Meda hannunshi yayi ya ruggumeta tsam a jikinshi sabida wani irin kallo da yayiwa ƙirjintan. Lib tayi a jikinshi tana jin ɗumin jikinshi da ƙamshinsa. Shi kuwa Sheykh gyara kwanciyarsa yayi da kyau kana ya jawo musu borgon ya rufesu dukansu kab, daga samansu har ƙasansu. Hannunshi ya ɗaura kan cikinta tare da ɗan taɓa wa a hankali yace. "Yunwa kikeji ko?". Ya faɗa a hankali. Cikin baccin tace. "A a ni a ƙoshe nake". Uhumm yace tare da juyota da kyau ya haɗe ƙirjinta da nashi wuri ɗaya. Lumshe idonshi yayi sabida wani abu da yakeji yana bin dukka jinin jikinshi yana zaga sasan jikinsa gaba ɗaya. Hannunshi yasa kan ƙirjinta. Da sauri ta maƙalƙale shi gam ta hanashi samun hanyar saka hannunshin. Hancinsa yasa yana shaƙar ƙanshin jikinta. A haka sukayi bacci. Washe gari da asuba shiya fara tashi. Bathroom ya shige yaje yayi wonka yayi al'wala. Kasan cewar ko kiran forko ba'ayi bane, yasa ya shimfiɗa sallayarshi ya yayi nafila. Kana ya fara karatu. Har sanda akayi assalatu. Nan ya miƙe yazo bakin gadon. Ɗan sunkuyowa yayi tare da cewa "Aish tashi kiyi salla". tanada nauyin bacci shiyasa ko motsi batayi ba. Hannunshi yasa ya ɗan bugi pillow'n da kanta ke kai, tare da cewa. "Tashi kije kiyi al'wala kizo kiyi sallah Aish". A hankali ta buɗe idonta tare da kuma maidasu ta lumshe. Jin ya ɗan bugi ƙafarta ne yasa ta ɗan buɗe ido tare da yunƙurawa ta tashi zaune. Sam ta mance daga ita sai ɗan kwali iya ƙugunta. shi kuma juyawa yayi ya fita. A hankali ta miƙe taje ta shiga Bathroom tai wonkanta kana tayi al'wala sannan ta fito. Ganin kayanta a shanye a kan wani ɗan ƙarfen da yake shanya ƙananan kayanshi ne, yasa tasa hannu ta ɗauki zaninta. Ta ɗauka kana ta fita. Ɗakinta ta wuce, shiru dai babu motsin kowa a Side ɗin. Haka nan sai taji gidan ya mata girma ita ɗaya. Tsoro ya ɗan ɗarsu a ranta. Gsky in babu Ummi a nan bazata iya zama ba. A hankali cikin ɗan tsoron ta saka kaya. kana ta fesa turare, sannan ta zura hijabi ta shimfiɗa sallayarta. Ta kabbarta sallah. Bayan ta idar kuwa, Azkar tayi kana ta ɗan taɓa karatun al'ƙur'ani. Sai bakwai dai-dai ta miƙe cikin kasala da gajiya. Ta nufi kan gadonta. Ba tare da ta cire hijabin jikinta ba, ta kwanta. Mintu goma sha biyu tsakani tayi bacci. A hankali ya shigo falon. Shiru babu kowa, sashin ya nufa. Nanma shiru bedroom ya shiga da sauri ya kuma fitowa, juyowa yayi ya nufi falonta. Daga nan ya wuce bedroom ɗinta. Yana tura ƙofar kuwa ya jita a buɗe. Wani irin ja'irim murmushi yayi tare da nufar kan gadon a hankali ya hau. Sannan ya motso kusa da ita. Konciya yayi. Tare dasa hannun shi ya jawo hijabin cikin baccin tace. "Uhum". Shiru ya kumayi sai da yaga ta kuma maida baccin. A hankali ya cire hijabin, kana ya ɗan kalleta idonshi ya lumshe tare da lasan lip ɗinshi na ƙasa. Wuyan rigarta irin mai faɗin nanne, haka yasa yadda take konce a rigingine rabin ƙirjinta duk yana woje. Cikin wani irin masifeffen yanayin buƙatar kasantuwa da itane ya sashi. Cusa hannunshi cikin wuyar rigar a hankali. Miƙa tayi tare da gyara konciyarta. Wani irin numfashin yaja a hankali ya sauƙeshi jin. taushin fatarta, da kuma laushin lutsama-lutsaman csɓɓullenta, masu girma dai-dai misali. Hannunshi duka biyu ya cusa, cikin rigar. A iya zatonta na cikin bacci Sheykh ne, dan ta lura ya zama wani irin mutun yanzu. Especially zuwansu rangadin nan, bini-bini ya cusa mata hannunshi cikin riga yayi ta kwance mata lissafin kai. Shi kuwa Jahan yatsunshi yasa ya fara murza modonon caɓɓullenta. Yana wani irin lumshe ido tamakar wanda zai suma. Allah ya sani yana son waɗannan abubuwan masu masifar kyau da tsada da daɗin taɓawa. A hankali ta buɗe idonta jin yana ɗan goga fuskarshi jikin tata fuskar tasan Yah Sheykh nada saje da gyemu wannan fuskar kuma ta jita sulum. Wani irin zabura tayi tare da buga tsalle sai gata a ƙasa a tsakiyar ɗakin jiki na rawa cikin kaɗuwa firgici tsoro tashin hankali ta kurma ihun kiran sunan Jabeer. "Yah Sheykh!. Wayyoooooooo Yan Sheykh". Tanayi tana tsalle a gigice. Kanshi ya ɗan shafs tare da cewa. "Matar liman kiyi ihun a hankali yana can har masallaci ba jinki zaiba, kiyi a hankali kada ki yage wannan ɗan kekyawan ƙaramin bakin naki da nake jin daɗin tsotsa." Da gudu ta juya. Ta nufi hanyar fita. Kai tsaye Side ɗin Yah Sheykh ta nufa tana danna mishi kira. Baya cikin ɗakin ganin hakane yasa ta juyo da sauri. A corridor'n shigowa falonshi sukayi kiciɓis da ƙarfi ta faɗa jikinshi tare da ruggumeshi gam-gam cikin kiɗima jiki na rawa tace. "Yah Sheykh, Jahan ya sake zuwa har cikin ɗakinan. Yah Sheykh har kan gadona ya hau". Tallaɓe kanta yayi cikin mamakin tashin hankali da take cike, danne murmushin sa yayi tare da cewa. "Me ya miki?". Sai kuma ya janyeta a jikinshi tare da juya wa da sauri ya nufi sashinta. Da gudu ta biyo bayanshi tana cewa. "Yana ciki muje wlh yana ciki". Shiru tayi ganin babushi babu dalilinshi. Cikin tashin hankali tace. "Wlh yazo har nan har kan gadona. Da ina ta kiranka yace min wai Matar Liman kiyi a hankali ba jinki zaiba dan yana can masallaci". Gaba ɗaya dariyar mugunta ke cinsa. Sanin in yayi dariyar zata iya fahimtar wani abune yasashi zuba mata ido. Sosai ta gigice, hannunta ya kamo suka nufo babban falon. Suna fitowa Ummi da Saratu na shigowa. Da sauri Saratu ta nufi kitchen. Ummi kuwa ta nufi kansu. Cikin kaɗuwa tace. "Sheykh meya faru?". Yana riƙe da hannunta yace. "Ummi wai cewa tayi yauma Jahan yazo har cikin ɗakinta. Ni kuma tun kwanaki da take cewa, yazoma na bincika akace min baya ƙasar nanma gaba ɗaya. Ya fita UK kuma ance zai kai wata shida kafin ya dawo. To waye Jahan ɗin da take gani, taketa ihu duk jama'ar masarautar Joɗa naji in ba aljanunta ba." Cikin damuwa Ummi tace. "To wake firgitata har hakane". Cikin riƙo hannunta gam ganin yadda taketa fizge-fizgen tana rantsewa wlh ƙarya akeyi yana garin. A hankali yace. "Kawai fa Ummi al'janunta ne ke zuwa da wani sabon salo. Kuma zanci musu mutumci, bazasu medamin gida sansanin ihu da kururuwa ba". Cikin sanyi Ummi tace. "Babu maijin ihunta fa Sheykh, kai dai ka ƙara bincike da kyau akan al'amarin." Sai ta kuma kalli Aysha da har yanzu a gigice take. "Ki nitsu ko Aysha gani gashi ga Saratu. Babu wanda zai shigo nan zamu ganshi". Cikin sanyi ta gyaɗa kai. Jan hannunta yayi suka nufi falonshi. Ummi kuwa wurin Saratu taje suka fara aikinsu. Shi kuwa yana riƙe da hannunta ya zauna bisa kujera kana ya zaunar da ita. System ɗinshi dake hannunshi ya ɗaura kan stoll ɗin dake gabanshi. Tare da buɗe wa, ɗan juyowa yayi ya kalleta. jin har yanzu jikinta rawa yakeyi, a hankali yace. "Ke wai me ya miki". Cikin rawan murya na tsoro tace. "Abunda kakeyi min". Da sauri ya juyo ya fuskanceta tare da zaro idanunshi woje cikin ɗan ɗaga sauti da haɗe fuska yace. "Me nakeyi miki da yayi miki?". Ya ƙarashe mgnar a fakaice. Cikin takaici tace. "Hannunshi yasa a rigata". Jawota yayi jikinshi tare da miƙewa tsaye. Cikin faɗa da zafi rai a ɓace na fatar baki yace. "Zancen banza kenan. Ko iskarki ce, ta isa in haɗa muhalli da itane, bare wani can Jahan da ba'a san asalin menene shiba menene addininshi ba. Ke wacce iriyar yarinyace, da zaki tsaya har ya kalli abinda Muhammad Jabeer ya kalla har ya taɓa min kayana. Lallai ya nemawarwa kansa masifa da yayi gigin kai hannunshi inda hannuna ya kuskura ya taɓa." Juyawa yayi a fusace ya nufi. Bedroom wayarshi ya ɗauka tare, da kiran Jamil wanda ma'akacine a ma'akatar su Jahan. Cikin kausasa murya yace. "Ka binciko min waye Jahan ina yake suwa yakewa aiki nanda rabin sa'a ina son amsoshi na". Da sauri Jamil yace to. Ita kuwa Aysha a inda ya tashi ta kwanta. Bayan wani ɗan lokacin. Jamil ya kira Hamma Jabeer ɗin ya shaida mishi cewa da tabbas Jahan baya nan. Baya ƙasarma gaba ɗaya tsawon watanni biyu. Kuma babu wani Jahan da ya sani." Jin hakane yasa Sheykh, yin wani sihirtaccen murmushi da kyau. Ko Jamil bai san komai kan Jahan ba. Murmushi yayi tuno yadda yake cewa al'janin Aysha ke zuwa da salon iskanci. Ranar dai a gida ya wuni, yana fakewa yaita murmushi lokaci zuwa lokaci. Ita kuwa Aysha wurin Ummi ta koma. Sai da Yamma Sheykh da Galadima sukaje suka samu Lamiɗo sukayi mishi dukkan bayanin tafiyar da sukayi da nasarorin da suka samu a ciki, da alamar matsalar da suka tarar, nan sukayi tattaunawa tamu sannan kan al'amarin. Aysha kuwa sai washe gari Ummi ta mata jagora taje, Sashi Gimbiya Aminatu. A can ta samu, Aunty Juwairiyya da Mamin Affan. Nan suka zauna sunata hira. Sai yamma ko wacce ta nufi Side ɗinta. Yau sallan layya saura kwana uku. Mutane nata shiryawa shirin ƙaramar salla. Yau tunda safe da Sheykh ya fita bai dawoba sai dare. Washe gari da Safe, Junaidun ya kira Aysha bayan sun sha hira yake cemata. "Adda Shatu, jiya Dr Sheykh yazo Rugar Bani, wurinsu Arɗo Bani da Babanmu. Sunata godiya dai sunce ince miki ki ƙara yi mishi godiya kan hidimar da yayi mana." Cikin mamaki tace. "Au dama shine likitan da ya maidaku asibitinshi ya kula daku?". Da sauri yace. "Eh amman nima ban san shine kuma mijinki ba sai. Yau da yazo. Ni nayi zaton wurinmu yazo sai naga su Baba da Arɗo Bani sunata murnar zuwanshi, sai na gane bafa wurinmu yazo ba". Uhum tace tare da cewa. "To ba matsala in sha Allah zan masa godiya". Daga nan sukayi sallama. Konciya tayi tana nazartan takun Yan Sheykh sai dai duk nisan da zurfin tunaninta kafin taje wuri a tunani ko bincike tuni ya wuce ta. Abu ɗaya ta fahimta, yana bin diddigi akan abubuwa da dama shi mutumum ne bauɗaɗde mai algibata tako ina ka buga zaka sameshi. A ranar bata ganshi ba. Hakama washe gari. Sai da asuba Ummi ta tasheta akan ta kai mishi. Abun yin sahur sabida gobe za'a tashi da azumin arfa. A tsaye ta sameshi a falo da waya a hannunshi. Bisa alamu da Aunty Hafsat yake mgn. Gabanshi ta ratsa ta ajiye mishi tray'n a kan stoll dake gabashin. Ba tare da ya kalletaba ya kamo hannunta ya riƙe lokacin da zata juya ta fita. Sai kuma yaci gaba da wayar. "Aunty Hafsat wai har bikin ya isone?". A can ɗaya gefen murmushi tayi tare da cewa. "Sosai ma kuwa Sheykh saura wata ɗaya da kwanaki ne zulhajji na ƙarewa da kwana biyar na sabuwar wata za'a fara bikin". A hankali yace. "To kuma shine zakuzo tun bayan salla da mako ɗaya, yanzu ita Ramatu da wa zata bar mijinta ta taho wata kusan biyu". Hannunta dake cikin nashin hannun ya ɗan ƙara matsewa. Tare da janta jikinshi. sai kuma ya ɗan gyara tsayuwarshi tare da cewa. "A a Aunty Hafsat ku bari in bikin saura mako ɗaya ko biyu sai kuzo". Da sauri tace. "Sai dai biyun". Uhum yace. Ita kuwa cewa tayi ina. "Ya Ɗiyata Aysha kuma yar uwata aborso a rayuwarmu". Murmushi yayi a hankali tare da lumshe idonsa yanaji wasu zafafan hawaye na tashin hankali na tsastsafo mishi yace. "Gata". Yana faɗin haka ya liƙa mata wayar a kunnenta. Da sauri ta ɗago ta kalleshi. Tsareta da ido yayi. Jin muryar Aunty Hafsat ne yasata ɗan murmushi tare da cewa. "Aunty Barka da asuba". Cikin tarin so tace. "Barka dai Aysha yasu. Jalal da Jamil ya kewan Hibba". Cikin murmushi tace. "Suna lfy Aunty ina kewar Hibba kam sosai ma". "Kada ki damu mun kusan haɗuwa ai muma zamu zo ai. Ya Jazlaan yana lfy ko". Cikin jin daɗi tace. "Allah ya kawoku lfy Aunty". Amin Amin tace. Kana tace. "Ya Jazlaan yana lfy ba wata damuwar ko". Ɗago kanta tayi ta kalleshi, Kwaɓe mata fuska yayi tare da mata alamun bata amsa. Cikin sanyi tace. "Uhum Alhamdulillah". "Masha Allah. To sai anjima ko kada in hanaku yin sahur". Ɗaga nan sukayi sallama. Shi kuwa a hankali ya zauna tare da zaunar da ita gefe. Kana yace. "Kinyi niyar yin azumin arfanne?". Kai ta gyaɗa mishi alamar eh. Kauda kanshi yayi tare da cewa. "To kin nemi izinine?". Tura baki tai tare da cewa. "Izinin wa?". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "Ok haka kikace ko baki san izinin wanda zaki nema bama kenan ko?." A hankali ta ɗan kalleshi sai kuma tace. "Kayi haƙuri. Ina son yin azumin, ka amince inyi?. Kanshi ya jinjina tare da cewa. "Uhuumm ai da kinyi ba neman izinin sai da yamma in karyashi". A hankali tace. "Ka karya min shi kuma ɗura zakayi min ne?". Kanshi ya kauda tare da cewa. "Aikin wani ladan zanyi dai in Kauda naki da nawan, Ni na samu lada biyu na niyan azumin da ladan raya Sunnah". Shiru tayi tana jin yadda yake murza yatsarshi ma nuniya cikin tafin hannunta. Ganin lokacin sahur na tafiya ne yace. "To tashi kije kiyi sahur". Miƙewa tayi ta fita. Shi kuwa sahur ɗin ya fara. To Alhamdulillah Azumin Arfa dai yayi zafi sosai kowa ka gani kamar yayi azumi goma. Kuma yaune Lamiɗo ya ware raguna aka bada duk cikin masarautar Joɗa ahilinshi da bayinshi da hadimai kowa da ragonsa. Sheykh Jabeer kuwa shima yasa su Jalal sunje sun raba a cikin gari sadaka. Da yamma suna zaune Aunty Juwairiyya ta shigo gefen Ummi ta zauna. Ita kuwa Aysha tana kwance bisa kujera kamar sumemmiya. Azaban ƙishirwa da yunwa ne suka dabaibaye kuzarinta. Cikin sanyi Aunty Juwairiyya tace. "Aunty Aysha sannu fa, Azumin da daɗi kam yau". A gyatsine ta kalli Aunty Juwairiyya, sabida zuwa yanzu zarginta da takeyi yamafi na baya. Ummi ce ta ɗan kauda zancen da cewa. "Ya shirye-shiryen aiyu kam salla". Murmushi ta ɗanyi tare da cewa. "Alhamdulillah Ummi wannan karon ai aiyukan zasu zo mana da sauƙin. Dan nan za'a kawo ragunan Jamil da Jalal Amarya ta gyara musu." Ni inji dana Ya Jafar da nawa dana Hajia Mama". Cikin murmushin Ummi tace. "A a kada ki mana wayo kinada masu tayaki aiki ga Ladi da Lami duk zasu tayaki." "Ummi kuma ga Saratu ga Larai gaki ga Aunty Aysha". Cewar Aunty Juwairiyya. "Duk da haka aikin da yawafa anan ga na Sheykh ga na Mamey ga ganawa gana Aysha kana ga na Jalal Jamil. Kuma suma su Saratu sunada aikin nasu." A hankali Aysha ta miƙe zaune tare da cewa. "Ummi aiki ai ba abin tsoro bane, ba damuwa". Tana faɗin haka ta juya ta nufi ɗakinta. Tazo gab da bakin ƙofar shiga falonta kenan taga wani irin duhu ya rufe mata ido sai jiri da sauri ta zauna. Sheykh kuwa da yayi al'walan la'asar zai fitone ya ɗan zuba mata ido tare da cewa. "A azumi ɗayan ne kike neman faɗuwa zaki sune min ko". Dariya Ummi tayi tare da cewa. "Azumin fa da zafi Sheykh". Kanshi ya ɗan juyo tare da cewa. "Kaiya Ummi ragwanci dai". Murmushi sukayi ya wuce ya fita. Ita kuma da ido tabi bayanshi ƙeyarshi ta liƙawa wani mayataccen kallo. Kana ta miƙa tsaye ta nufi ɗakinta. Ummi kuwa cikin gyara zama tace. "Gsky Juwairiyya aikin nasu Jamil ayishi a sashinki. Kinfa San na Sheykh ma biyu ne". Dariya Aunty Juwairiyya tayi tare da cewa. "Kai Ummi to shi Sheykh ba a ana tashi sallan idi a wurin ake yanka nashiba, tunda shine liman baza'ayi layya ba sai yayi. Yanayi kuma a wurin ake rabashi sadaka. Daga nan kowa ya dawo gida yayi nashi". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Eh to ai akwai wanda Lamiɗo ke bashi kuma za'a kawoshi nan". Miƙewa tsaye tayi tare da cewa. "To shike nan Ummi a bar na Jamil tunda shi zaima je ya tayamu aikin ku ku gyara na Jalal". "To shike nan". tace kana suka tafi salla. Bayan sun idarne suka fito suka fara aikin buɗa baki. Bayan sunsha ruwa sun hutane. Suka shiga kitchen kimtsa kayan aikin da aka lodo musu sukayi. Kana suka ɗan haɗa aikin da zai iya faruwa a lokacin. Washe gari aka tashi ranar Sallan layya. Yara da manya mata da maza al'ummar Annabi na duniya baki ɗaya anata shiryawa zuwa idi. Babu wanda ya tsaya karyawa sabida duk suna azumi. Wanda sai bayan an sauƙo idi anyi yanka mai layya yayi buɗa baki da hantar dabbarsa. Sauri-sauri yake kimtsawa cikin wata kekyawar al'kyabbar mai taushi baƙa sai farar jallabiya da yasa a ciki. Hiraminshi ya kimtsa kana ya fisa turare. Sannan ya fito da sauri ganin lokacin nata gaba towa. A falo ya samu Ya Jafar. Tare suka fito babban falon. Nan suka samu su Ya Hashim, Jalal, Jamil, Imarn, Affan, Sulaiman. Da sai sauransu. Nan suka rakaya suka nufi masallacin Masarautar Joɗa inda nan yake limancin Sallah idi. Masallacin da ƙaton filin harabar masallacin duk ya cika yayi maƙil tako ina al'ummar Annabi ne keta shigowa. Cikin shiga mai kyau ta al'farma da tsabtar addini. Ita kuwa Aysha a hankali take kimtsawa sabida ciwon da mararta keyi. cikin sanyi ta buɗe wodurob ɗinta. Wani tattausan Boyel mai taushi da sheƙi mai ɗan karen kwai ta zaro, dinkin zani da rigace borno sitayel mai masifar kyau. Kalarshi Sky blue an watsa mishi aiki da zare Pink color mai sheƙi. Bayan tasa bra and pant wani tattausan ondawuya dan guntu iya guiwa tasa, kana tasa. Ɗaura zanin ta dai-dai-ta shi. Rigar ta zura a jikinta tayi mata cib-cib gwanin burgewa ƙirjinta ya zauna daɓas. Ninke ɗan kwalin tayi tare, murza asetta ta ɗan karkatashi kaɗan jelan gashinta da bata kitseshi ba, ta barshi kwance a bayanta. Turare mai masifar ƙamshi ta fesa. Sannan tasa wani sarka da yan kunne masu kyau. Gyale pink color ta yafa. A hankali ta fito falo. kiciɓis sukayi da Ummi tana cewa. "Aysha mu tafi ko". A hankali tace. "Ummi kuje kawai. Bazan jeba". Ɗan jim Ummi tayi sai kuma ta juya kawai ta tafi. Ita kuwa Aysha kitchen ta nufa. "Special Arish". tace a hankali kana ta. Ɗebo dankali da sauran kayan da zata buƙata SPECIAL ARISH 1.dankalin turawa 2.nama, kwai, tumatur 3.kabeji, bama , maggi 4.tafarnuwa ,man gyada. Da farko dankalinki ta fara ferewa ba tare da daddatsashiba ta wanke saita-ta tafasashi da ruwa da gishiri kadan. Sai ta kada kwai da albasa d curry da Maggi Tafarnuwa. Daga nan saita dinga tsoma dankalin tana soyawa. Sai ta kuma tafasa nama da maggi da gishiri da curry da tafarnuwa da al'basa har yayi laushi saida ruwan ya kusa tsotsewa saita kara wata al'basa da timatur suka nuna saita kwashe. Ta yanyanka kabeji kanana sannan ta dafa kwai ta yanyan kasa da. Dan girma sannan ta zuba Maggi da bama ta gaura yeshi . Sai ta samu Foodflaks ta zuba Irish a gefe sannan hadin namanki ta shina ta sashi a wani kulan shi kuma haɗin kabejinki ta sashi a wani kulan shima Kasan cewar da yawa ta ɗan yi shi. Tana gamawa taje ta jerashi a kan Dinning area. Sannan tazo ta kimtsa wurin. Tuni kuma an idar da salla. Affan dake kusa da Sheykh ne ya ɗan matso tare da cewa. "Hamma Jabeer gacan ragon an kawo mutane nata son tafiya gida suna jiran kayi yankan." Da sauri yajuya tare da cewa. "To muje". Bayan yayi yankanne ya juya ya tafi. Yasan na cikin gidanma duk shi ake jira. Affan kuwa a gefen wurin ya tsaya saida aka gama fiɗan dogarin dake raba naman ya yanko hantan yasa a leda ya miƙawa Affan. Daga nan Affan ya juya ya tafi cikin gida shi kuma yayi ta rabawa mutanen wurin naman. Yayinda duk sauran mutane gari kuwa aketa tafiya. A can mayankansu na cikin Masarautar Joɗa nan Sheykh ya nufa shida Lamiɗo da sauran manyan masarautar baki ɗayansu. Daga nan ya fara yanka bayi masu fiɗa suna amsa suna feɗewa ko wanne ana kaishi sashin maishi. Affan kuwa kai tsaye Side ɗin Sheykh ya nufa. A falo ya samu Ummi da Aysha, ledan hantar ya miƙa mata tare da cewa. "Gashi a gasawa Dr Liman Sheykh Akarmakallu Hamma Jabeer kafin ya dawo. Yanacan yanata yanka zai dawo a gajiye a yunwace". Dariya Ummi tayi tare da cewa. "Gsky kam Aysha amshi ki fara da wuri". To tace kana ta amshi ledar. Kitchen ta wuce. Ummi na biye da ita a baya. Juyo naman tayi a roba, ta wonkeshi Sannan tasa wuƙa ta fara yankashi dogo-dogon yanka sala-sala. Kara lallaɓesu tayi, kana ta tasashi a wata robar, al'basa ta yanka mai yawa, dai-dai yadda zaji mata, citta kanamfari Curry da maggi da ɗan gishiri ɗan mitsilili ta tarfa a ciki. Ta gaggaureyasu. Kana ta juye a tukunya sannan ta ɗauka a kan gas, tasa wutan dai-dai misali. Ummi kuwa al'basan taketa gyarawa tana yankawa a wata roba. Attaru da basufa takwas ba ta, gyara kana ta jajjaga matasu. Tuni naman kuwa yana tsilala yanata ƙamshi ya tsastsafo ruwan jikinshi, ya haɗe da kayan ɗan-ɗano dana ƙamshi. Jajjageggen Attaruhu da al'basan da Ummi ta miƙa mata, ta amsa. Kana ta buɗe tukunyar, ta juyeshi ciki ta ɗan motsa naman. Haɗin duk ya shiga ciki. maggi da Curry ta ɗan ƙara. Sannan ta rufe tukunyar nan take tafa bararraka bul-bul sai wani irin ƙamshi yake fesorwa. Jamil da ya shigo da bayi uku ko wanne da roban kayan ciki a ciki an wonkesu fes, hanji an kitsesu gwanin kyau. Shima ajiye robar hannunshi yayi tare da cewa. "Wannan ƙamshi shine ƙungiyar yunwa." "Allah ko Jamil". Ummi ta faɗa tana kallonshi. Shi kuwa, kanshi ya jinjina tare da cewa. "Sosai ma Ummi, gashi wannan nakune Sheyky Aunty Ayshan, Mamey ke, Jalal ya kwautar da nashi wa abokinshi". "To yayi kyau, bari mu fara aikin." Cewar Ummi juyawa yayi ya fita yana cewa. "Afa ajemin wannan gashi na Sheykh da yake ta zuba ƙamshi". "Kaɗan ba". Cewar Aysha dariya yayi tare da cewa. "Kai Aunty Aysha rowa ba kyau fa". Murmushi tayi tare da cewa. "Yoh naji Affan yace Hammanku zai dawo a yunwace". Dariya yayi ya fita. Ummi kuwa tukwane ta ɗauka kana ta kalli Saratu da yanzu ta shigo tace. "Yanka min al'basan da yawa. Ke kuma Larai zoki riƙe min mu yayyanka tunda a gyare suke". To sukace kana duk suka fara aiyukan da tasasu. Aysha kuwa buɗe tukunyar tayi ganin. Yadda yayi kauri romon yayi yadda takeso. Yanata ƙamshi sai ta ɗauko wani kekkeyan ɗan Foodflaks karamin. Ludeyi tasa ta rinƙa korfe romon tana sashi a kular da zafin shi. Saida ta korfeshi kab. Kana ta rufe kular sannan. Ta matso kusa da tukunyar ta fara, motsa naman wuta yanaci daki-daki tana motsashi tana gaurayashi. Yana ɗan kame jikinshi yana ɗan zama kamar gashi wuta. saida taga ya tsane yadda takeso. Ta kwasheshi da zafinshi tasashi a kula kana tasa wani a ɗan madaidaicin kula mai ɗan karen kyau. Rufeshi tayi sannan ta raba romon biyu, a ƙananan kulan. A tray'n ta jera Foodflaks masu ɗan karen kyau ɗin kana tasa plate spoon and fork, sannan ta ajiyesu gefe. Kana ta ajiye mai yawan shima gefe. Inda Ummi take ta matso kana ta fara taya wonkewa tana tsaneshi tana zubawa a tukunya. Tare da turbuɗeshi da al'basan da citta kanamfari Curry da maggi tafarnuwa da a dai sauran kayan ƙamshi dana ɗanɗano, saida suka gama komai cikin ƙanƙanin lokaci kana. Su Sara suka kullace wuri. Sannan Ummi tace to suma suje suyi nasu aikin. Ta basu duk wani kayan haɗin da zasu buƙata duk da tasan ana kaimusu. Falon suka dawo suka zauna. Bayan Ummi ta zubo musu hanta gashin tukunyar ta yarfa musu romon a samanshi. Plate ta miƙa Aysha. Da sauri ta jujjuya mata kai tare da cewa. "Bana cin kayan ciki". Cikin mamaki tace. "Allah sarki Aysha am na manta, da ban haɗaki da aikinshiba". Shiru tayi ganin ta rumtse idanunta tare dasa hannunta ta kama mararta. "Sannu baki da lfy ko?". Ummi ta tabayeta cikin kulawa. Kai ta jinjina tare da cewa. "A a ba komai ai da sauƙin". Jalal, Jamil, Affan, Imran, Sulaiman, Y Jafar ne suka shigo a jere. Kai tsaye Dinning area suka wuce. Da sauri Ummi tabi bayansu tana cewa. "Sannunku an gama yankan ne?". Baki Jalal ya tsuke tare da cewa. "Inafa aka gama gajiya kawai mukayi muka gudo . ALLAH ko Hamma Jabeer har tausayi ya bani mutun kusan awa biyu a sunkuye, ba hutu, fuskarshi kayanshi duk sun cika da jini". Jamil ne yace. "Ummi da Allah zubo mana abin ci". To tace tare da shiga kitchen ɗin gaseshen naman ta ɗauko musu. Ta zuzzuba musu kana Special Arish ta saka musu da haɗin naman da kabejin da Aysha tayi musu. Sannan ta ɗauko Drinks ta jera musu, nan suka faraci. A hankali Aysha tace. "Shine kuka gudo kuka barshi shi ɗaya a can ko?". Murmushi Affan yayi tare da cewa. "No Madam Jabeer ba gudowa mukayi ba shi yace mu dawo da Ya Jafar". Sulaiman ne yayi dariya tare da cewa. "Yo gskyanta taga an bar mata miji shi ɗaya duk mun gudo". Dariya sukayi duka. Sha ɗaya da rabi. Dai-dai ya shigo, cikin tarin gajiya. Da sallama a bakinshi, da sauri ta buɗe idonta dake rumtse dan ciwon da cikinta keyi. Su Jalal kuwa daketa hira suna cin abinci da korawa da Drinks mai sanyi ne suka juyo suka kalleshi tare da cewa. "Sannu Hamma Jabeer sai yanzu kanshi ya ɗan jinjina kana ya wuce. Cikin kula Ummi ke ce mishi sannu. " Sheykh sannu da aiki Allah ya maimaita mana". "Amin Amin". yace kana ya wuce. Ita kuwa da ido ta rakashi. Ɗan juyowa yayi ya kalli bayanshi ko ta biyoshi Ɗan gajeren tsaki yaja tare da kallon duk jikinshi jini ya tsastsalu ga riƙewa da bayanshi yayi sabida dogon sunkuyo. A falon kuwa cikin kula Ummi tace. "Sannu ko Aysha dauki tray'n ki tafin masa dashi". To tace kana ta miƙe a hankali ta nufi cikin kitchen tana jin mararta na kartawa. Shi kuwa Ɗan juyowa yayi tare da ɗan buɗe muryarshi a gajiye yace. "Aish! Aish!!". Juyowa su Affan duk sukayi suna kallon hanyar falonshi, salon yadda ya kira sunan a kan harshenshi da yadda ya fitar da ƙal-ƙalan yasa amon sunan ya fito da daɗin sauraro da armashi na musamman". Murmushi Sukayi baki ɗayansu, wannan salo na manya ne. Ummi kuwa murmushi tayi tana sunkuyar da kanta. Affan da Jamil kuwa kallon juna sukayi tare da yin Murmushi. Ita kuwa Aysha a hankali ta fito da tray'n a hannunta ta nufi falon nashi. Tanasa ƙafarta kan steps ɗin da zai sadata da corridor'n taji muryarshi ta ratsa mata kunne a karo na ukku yace. "Ahh'ishhhhh". Cikin sauri ta haura tare da cewa. "Na'am Yah Sheykh". Kai Affan ya jinjina tare yin dariya yace. "Zuwa gidannan yanzu ɗaukan darasi ne kan sarrafa salon so mai zurfi da inƙanci irin na masana ilimin addini, nasu ba irin namu bane na turawa". Dariya yayi ganin Ummi ta mishi daƙuwa. Shi kuwa Sheykh a hankali ya kwaɓe fuskarshi. Tana shiga ya bita da ido sosai shigar da tayi. Yayi masifar amsarta. Kan dinning table taje ta ajiye tray'n kana ta juyo. Gabanshi ta zo tare da cewa. "Gani". Zo yace a taƙaice ya nufi bedroom tana biye dashi a baya. Kai tsaye ƙofar Bathroom ya tura ya shiga. Juyowa ya ɗanyi ganin ta tsaya tare da ce mata. "Dan Allah kizo nan". A hankali tabiyoshi. Tana shiga ya maida ƙofar ya rufe. Sai kuma yazo ya tsaya gabanta, tare da cewa. "Cire min al'kyabbar". Cike da mamaki ta kalleshi ganin ya tsuke mata fuska ya kuma buɗe hannayeshi ne yasa ta ɗan matso. A hankali tasa hannunta ta buɗe al'kyabbar. Juya mata baya yayi. Ta zare rigar. Sake juyowa yayi ya fuskanceta sunkuyowa ya ɗanyi tare da cewa. "Cire min jallabiyar". Kauda kanta tayi tare dasa hannun ta kan wuyanshi inda masaƙalin jallabiyar suke. Boturan ta ɓalle kana ta janye hannunta. Tsaki ya kuma ja tare da kwaɓe fuskarsa da cewa. "Kiyi sauri ki cire minsu ƙarni nakeji zasu sani amai kuma fitsari nakeji. Bana son hannuna ya sake taɓa jinin." A hankali ta matso gabanshi sunkuyowa ta ɗan yi cike da kunyar wai fitsari nakeji. Ƙasan jallabiyar ta ɗago kana ya sunkuyo ta cire mishi. Ta ajiye gefe. Ƙara matsota yayi dagashi sai fararen tattausan gajeren wondo iya guiwa sai boxes dake can ciki Sai Senegal fara, daya sata cikin ƙugun gajeren wondon. A hankali yace. "Ciremin mana". Yayi mgnar yana matsota, a hankali tace. "Ta yaya?". Ƙugunshi ya nuna mata. Tare da cewa. "Zaro snglet ɗin daga cikin." Cikin sanyi ta motso kauda kanta tayi gefe, sabida nauyinshi da kunyarshi da kwarjinshi sun mata yawa. A hankali ta kai hannunta kan ƙugunshi da nufin ta kamo snglet ɗin ta zaroshi sama. sai kawai yaji sauƙan hannunta kan Sheykh ɗinsa dake ts....! Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 ki sayi katin Mtn ki copy NUMBERS ɗin ki turo min ta number nan da nakeyin whatsApp da ita 09097853276. In Kuma special Group kikeso wanda za'a gama Part two a maƙo biyu, to Kiyi min transfer'n ɗin 1k a susuna na Jaiz bank. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta wannan number din da ta whatsapp 09097853276. Banda VTU bana so in kinyi babu ruwana. By *GARKUWAR FULANI* Ɗinshi, ta ɗan shafa, wani irin Yar-yar haka tsikar jikinshi ta mimmiƙe a take wani abu yaji yana game jikinshi. Ita kuwa ba tare da ta fahimci ina ta taɓa ba, ta kuma yi sama da hannun hakan yasa yaji. Kamar tana mishi wani abune da zai iya tafiya da numfashin sa. A hankali yace. "Ha'ahhhhsshh". Da sauri ta juyo lokacin kuma hannunta ya isa kan gunshin. Zaro snglet ɗin tayi ta gaba. Kana ta tura hannunta ta baya ta jawo, ta fito dashi, tare dasa hannunta biyu ta ɗagoshi tayi sama dashi. Karo na forko kenan da taga surar jikinshi ziraran miraran tana cikin haiyacinta. Domin wacca ranar da har ta riƙe baki robar wondonshi bata cikin haiyacinta. Cikin wani irin yanayi ta zubawa faffaɗan kekyawan ƙirjinshi ido, wanda tattausan gargasa tsilli-tsilli ya yi masa ƙawanya. cire mishi tayi. Kana yace. "To sasu cikin washing machine ki wonkesu." To tace kana ta tattarusu ta juya ta nufi inda washing machine ɗin yake. Shi kuwa sunkuyowa yayi ya cire gajeren wondon ya rage dagashi sai boxes. Ita kuwa buɗewa tayi ta sakasu ciki. Da sauri ta juyo jin yana ce mata. "Amshi wannan ma kisa". Da sauri tayi ƙasa da kanta sabida ganinshi haka yayi matuƙar zuwamata a bazata. Ya razanata. Rumtse idanunta tayi kirib. Ajiyeshi yayi a kafaɗanta kana ya juya ya shiga cikin bath ɗin. Ya fara sakarwa kanshi ruwan ɗumi ya kori duk ƙarnin kana ya fara sa sabulu. Ita kuwa da sauri ta sasu. Ciki ta wonkesu a gaggauce. Ta tsanesu, kana ta shanyasu inda taga ya shanya mata zaninta randa suka dawo, rangadin. Tana gamawa ta fita. Shi kuwa kusan awa ɗaya yayi yana murza jikinshi. Allah yasani baya son ƙazanta ko kaɗan bare ƙarnin jini. Koda ya fito sha biyu tayi, har ta wuce. Kimtsawa yayi cikin wasu manyan kayan yadi Getzner mai masifar kyau da tsada lemon green kalanshi, sai aikin da aka yarfawa babbar rigar da zare Royal blue, mai ɗan karen kyau. Hularshi Royal blue da ratshin lemon green da black blue kaɗan kalanshi mai kyau. Wasu takalma masu taushi da kyau Black blue, wani turare ya fesa mai ɗan karen daɗin shaƙa. A hankali ya fito falon sabida ƙarfe ɗaya dai-dai lokacin. A konce ya sameta bisa 3 str da alamun bata da lfy. Cikin gajiya yace. "Yunwa nakeji". Jin hakane yasa ta taso a hankali. Bayanshi tabi. Kujera yaja ya zauna. Ita kuwa gefenshi ta tsaya, gasesshen naman tasa mishi a plate kana ta tasa mishi daddaɗan romon. Sannan ta ɗan ɗebi haɗin kebeji da nama tasa mishi. Spoon and fork tasa mishi kana ta ajiye mishi a gabanshi. Hannunta ya zubawa ido yana kallon jan lallen da tayiwa yatsunta, sai kuma ya ɗan kauda kanshi. Ita kuwa flaks ɗin tea ta jawo. A hankali tayi taku zuwa jikin show glass ɗin shi. Buɗewa tayi cup and tea spoon ta ɗauka. Zama tayi jin cikinta na kartawa. Tea ta haɗa mishi kana ta miƙo mishi amsa yayi tare da cewa. "Jazakallahu khairan". Tea ɗin ya kurba ba tare da yaci komaiba. Ita kuwa a hankali ta kifa ƙirjinta kan, table ɗin tare da rumtse idanunta. Murya can ƙasa tace. "Amin". Ido ya zuba mata, har saida ya shanye rabin kofin. Sannan ya fara cin naman. Ido ya lumshe jin ɗanɗanon naman ya ratsa mishi jijiyoyin baki, yawunshi sun tsinke. Yana kallonta yana ci, har saida ya cinye na plate ɗin data zuba mishi tas, kana ya shanye tea ɗin gyatsa yayi tare da cewa. "Alhamdulillah". Miƙa wa yayi ya nufi wurin washing hand Baby, wonke hannunshi yayi kana ya kuskure bakinshi. Zuwa lokacin har an kira sallan azahar ana gab da shiga Masallacin. Da sauri ya fito. Ba tare da yace mata komaiba. Ba kowa a falon, sai dai yaji motsin Ummi a kitchen. Da alamun ta fara suya ma. Da sauri ya fita, a can masalacin ya samu su Jalal. Ita kuwa Aysha a hankali ta miƙa ta tattara plete da spoons ɗin da yayi amfani dasu da kofunan, ta fito falon. Tanata haɗa zufa. Kitchen ta shiga. Nan ta samu Ummi da Saratu suna ta aikin suya Larai kuma tana can tanayi musu nasun. A hankali tace. "Ummi kawo in karbeki jekiyi salla kinga har lokacin ya tafi". Cikin kula Ummi tace. "Zaki iya kuwa Aysha nafa lura baki da lfy". A hankali tace. "Zan iya jekiyi salla". To tace kana ta fita ta tafi. Ita kuwa ta amsheta. Tana idar da salla ta dawo tace. "Jeki kwanta ki huta". Batayi musuba sabida tana jin masifeffen ciwon ciki jikinta har rawa yakeyi. Wonka ta farayi wai ko zata denajin zufar. Tana fitowa tasa wata tattausan atampa, riga da siket, kalarta orange mai kyau sai rashin yellow-yellow kaɗan a ciki. Batayi wata kolliya ba, amman tayi kyau sosai kalar kayan yazo kusan iri ɗaya da kalan fatarta, ɗinkin ɗan ɗagos. Ɗaurin ɗankwali mai sauƙin tayi. Kana ta fesa turare. Da sauri ta konta jin cikin ya murɗa ko mayafin bata yafaba. Tana kwanciya kiran Hibba na shiga wayarta. Da sauri ta ɗauka tare da cewa. "I miss you Hibba". Murmushi tayi tare da cewa. "Nanda wata ɗaya dai zakuzo auren Ya Haroon sai kin mana wata uku muma yadda nayi muku". Dariyar ƙarfin hali tayi tare da cewa. "Har biyarma zanyi". A hankali ta juyo ta kalli Ummi dake bakin ƙofa tana sallama. "Wa alaikissalam. Ummi shigo mana". "A a sauri nakeyi ki fito Sheykh ne yace kije". Fuska ta kwaɓe tare da cewa. "To". Hibba ce tace. "Aunty Aysha bawa Ummi wayar". Da sauri tace. "To Ummi ga Hibba zaku gaisa". Murmushi Ummi tayi kana ta juyo tazo ta amshi wayar. Sannan suka fito tare, da mayafin a hannunta. Tana worworeshi ne ta nufi falonshi. A falon ta sameshi, zaune a Dinning area. Kujera ya nuna mata, a hankali ta zauna. Shi kuwa tasowa yayi ya dawo kujerar dake kusa da ita. Foodflaks ɗin ya buɗe, plate ɗin da ya ɗauka a show glass ɗinshi. Yasa mata Special Arish da haɗin naman da kwai. Da kuma na Kabejin. Tura mata gabanta yayi tare da cewa. "Kici". Fuska ta ɗan yamutsa tare da cewa. "Banajin yunwa". Tea ya haɗa mata tare da miƙo mata yace. "Kici ko". Tea ɗin ta amsa sanin ruwan ɗumi ne. Shi kuwa ido ya zuba mata dole yasa taci. Bayan ta ɗanci ne yace. "Meyake miki ciwo". Kai ta girgiza alamun babu. Hularshi ya ɗan tura ya maidashi ƙeyarshi kaɗan tare da cewa. "Kenan ƙarya Ummi tayi cewa baki da lfy kuma tunda gari ya waye bakici komaiba". Da sauri tace. "A a ba ƙarya bane". "Uhumm!". yace tare da tura mata plate ɗin dole taci, kaɗan kana tace ya isheta. Miƙewa yayi tare da cewa. "Meke miki ciwo?". A hankali itama ta miƙa tare da cewa. "Ya bari". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "To muje kiyi min tausa bayana ciwo". Ya ƙarashe mgnar yana kamo hannunta suka nufi bedroom. Da goran zam-zam a hannunshi. Bedside drower'n ya buɗe. wasu magunguna ya fitar, ya ɓalli guda biyu a ciki ya miƙa mata. amsa tayi, "Sha wannan sauran na wancan wotan ne". Yace mata. sashi a baki tayi shi kuma ya miƙo mata goran zam-zam ɗin ta sha ta haɗiye mgnin. Gariyar jikinshi ya zare ya saƙala cikin durowa, kana ya cire rigarma ya saƙala. Hakama dogon Wondon da hularshi. Hannunta yaja suka hau kan gadon. A nitse yace. "Ɗan daddanna min bayan". Ya kwanta a kife. Shiru tayi sabida rawan da jikinta keyi. Juyowa yayi ya ɗan kalleta tare da cewa. "Umarnine fa ba shawaraba". A hankali tace. "Yah Sheykh cikina marata ciwofa". Jawota jikinshi ya kontar da ita, kana ya juyata rigingine. Hannunshi yasa kan cikinta. A hankali ya ture rigarta sama kaɗan. kana yayi ƙasa da siket ɗin. A hankali yake shafa mararta-ta yanayi yana ɗan lallatse wurin da danneshi. Shiru tayi sabida tanajin daɗin yadda yake matan. A hankali ya ɗan manna bakinshi kan goshinta. Kiss ya manna mata tare da cewa. "Na sani ai baki da lfy, ɓoye min kikeyi. Sannu". Kanta ta gyaɗa tare da lumshe ido. Cikin sanyi tayi bacci tare dasa hannunta kan sajenshi lokacin data juyo ta konta a rigingine. Gyara musu kwanciyar yayi. Lokacin ɗaya sukayi baccinsu. Ummi kuwa da Saratu cikin sauƙin suka gama aikin hajji. Jannama sai gobe. Bayan sun gama suyan ne, Ummi ta dama musu kunun shinkafa kyau. tasa manyan flaks. Sannan ta koma ɗakinta itama ta ɗan kwanta. A can jihar Tsinako kuwa, sosai fa shirye-shirye bikin Haroon da Jannart ya kankama. Tuni an haɗa kayan lefe a saura kaiwa kuma sai bikin yazo a kai. Haroon ya shiga ribibi. Yau tunda gari ya waye baiyi waya da Jabeer da Ibrahim ba, sai yakeji kamar shekara yayi baiyi mgna da suba. Kiran Sheykh ya farayi sai kuma ya tuno, yanzu duk inda yake lokacin baccinsa ne, in kuma baiyi baccinba to yana babban uzurin da bazai barshi ya ɗaga wayar Bama. Umaymah kuwa tunda safe tayi mgn da AYSHA data kirata tayi mata barka da salla. Ibrahim ma ya kira Jabeer ba'a ɗagaba. Wayar Aysha kuwa Rafi'a da sauran ƙawayensu duk sun kikkira. Bappa ya kirata. Hakama Junaidun da Binto budurwar ya Gaini. Sannan ƴan uwanta ahlin Abboi duk sun kirata. Wani Ummi ta amsa wani ta bari. Kiran salla ne ya tadashi a bacci. A hankali ya zare jikinshi daga nata. Ya shiga bathroom yayi al'wala kana ya fita sukaje sukayi salla. Ƙarfe huɗu dai-dai ya kuma dawowa. Dasu Jalal a falon suka zauna wurin Ummi suna cin soyayyan naman. Shi kuwa cikin ɗakin nashi ya wuce. Har yanzu tana bacci. Wayarshi ya ɗauka Haroon ya fara kira, sukayi hira kana ya kira Ibrahim. Yana cikin mgna dasune yaga ta tashi da sauri. Sauƙowa tayi tana kallon jikinta, dasa hannun ta shafa bayanta dai-dai mazaunanta. juyowa tayi cikin tsarguwa irin ta macen da takejin alamun jikinta ya ɓaci. Ta gefen ido ya kalleta ganin ta juya zata nufi hanyar fita. Da yatsarshi ya nuna mata jikin sawunta, da jini ke ɗan gangarowa. A hankali alamun yanzu ya samu tsinkowa yadda yakeso. Dan tun lokacin data shiga yin wonkan idi taga zubowanshi kaɗan sai kuma yanzu. Ganin ta tsaya ne ya sashi kwaɓe fuskarshi tare da nuna mata hanyar bathroom nashi yana cewa. "Kiyi sauri ki shiga kada ki samin najasa a tsarkakken ɗakina". Hannu tasa ta tattare bakin siket ɗin kana ta nufi ban ɗakin. Tana shiga ta ɗan leƙo tare da cewa. "Ayyah Yah Sheykh dan Allah a kawo min zani mana". Shiru yayi itama shiru tayi tana leƙenshi. da alamu abu yake rubutawa a wayarshi. Saida ya gama har ta buɗe baki zatayi mgna. Sai taga ya miƙe ya fita. Bai kula su Jamil da Affan ba ya wuce. Yana buɗe durowar, ya shaƙi ƙamshin sabbin kayayyakin dake jere. Wata doguwar rigar material Sky blue ya ɗauko da ɗan kwalinta, ganin akwai rasin fari a jikine yasashi ɗaukar mata farin gyale. Har ya rufe zai juya sai kuma ya dawo. sunkuyowa ya ɗanyi. Inda yaga jerin bra and panties ɗauka mata yayi fara. Sai kuma yaga audugar mata a gefe. Kwaya ɗaya ya zaro kana ya juya ya fita. A kan gado ya ajiyesu. Kana ya juya ya fita ya koma falo bai ce mata komaiba. Sake leƙowan da tayine bayan tayi wonka, taga ya ajiye mata kaya kuma ya juya ya tafi. Da sauri ta fito da towel ɗin shi a jikinta. Sauri-sauri ta kimtsa jikinta, ta shirya tsab, sabida taji sauƙin marar tata sosai. Bathroom ɗin ta koma ta wonke wanda ta ciren ta shanyasu a cikin, kana ta fito. Gaban dreesing mirror ta tsaya, turaren shi ta fesa, kana ta juya ta fito. Hanyar fita ta nufa, shi kuwa yana tsaye ta sameshi da alamun wani wurin ya nufa, har taje bakin ƙofa yace. "Zo". Ɗan juyowa tayi ta kalleshi ganin kamar bashine yayi mgnarba, yasa ta juya ta nufi hanyar fita. "Zo". Ya kuma cewa. A hankali ta juyo, ta nufi inda yake gabanshi ta ɗan tsaya. Kanta a sunkuye. "Waya baki izinin samin turarena?". Da sauri ta ɗan kalleshi tare da girgiza kai alalum a a. Fuskar shi ya tsuke tare da cewa. "Ƙarya nayi miki kenan". Still kanta ta jujjuya, shi kuwa kallonta yayi sama da ƙasa ya kalli iya tsawonta da ɗan jikinta da wuraren da sukafi abki a jikinta welcome and bay-bay ɗinta. "Baki da turaren ne?". "Inada shi". "To meyasa kika samin nawa". Baki ta ɗan zumbura tare da cewa. "Nifa bansa maka tutarenka ba". Tana faɗin haka ta juya ta nufi hanyar fita. Da ido ya rakata, tana fita shi kuma ya buɗe ƙofar da zata sadashi da Garden ɗin da ke bayan sashin nasa. Washe gari kuma ranar suyan jan nama, sosai Aysha ta tsaya kan aikin, dan cikinta yabar ciwon nanda nan sukayi aikinsu suka gama. Haka dai akayi shagulgula bikin ƙaramar salla lafiya. Yau kwana huɗu da yin salla a wuni na biyar ne. Affan da Aunty Juwairiyya kusan a tare suka shigo. Wani roba mai kyau Affan ya miƙa Aysha tare da cewa. "Aunty ƙarama gashi inji, Mami a kawo miki". Murmushi tayi tare da amsar robar. Soyayyan namane yayi kyau ya samu kekyawan aiki sai nason mai yakeyu. "Kai a lallai nako gode sosai". Murmushi yayi tare da cewa. "Wai tasan naku duk muke haɗuwa muna cinyewa, wai kowa ya bar na gidansa yazo ya cinye naku". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Tayi gsky ai haka kuke gaku bakwa gajiya da cin nama kamar ba Fulani ba. Gwara ma Jalal shi bai fiye damuwa da namaba amman Kai Affan Jamil Imran da Sulaiman ko kuraye sai haka". Murmushi sukayi. Kana Aunty Juwairiyya ma ta miƙo mata robar da tazo dashi tare da cewa. "Gashi wannan a bawa Sheykh". Fuska ta ɗan yamutsa tare da cewa. "A a barshi kawai". Shiru Ummi tayi dan tasan za'ayi hakan. Ta rasa dalilin da yasa Aysha batason kyautar komin na wurin Juwairiyya da Hajia Mama. Su kuma basa gajiya da ba amsa takeyin ba sai sun bata. Cikin tsareta da ido Juwairiyya tace. "To aini ba ke na bawaba Sheykh nace a bawa". Fuska a daƙile tace. "Bazan bashi ba, bazai ciba. Kije kici abunki. Baya buƙatar nakin". Da mamaki Affan yace. "To Aunty ƙarama meyasa". Juyowa tayi ta ɗan kalli Affan tare da cewa. "Ita ai tasan dalili". Daga nan ta juya ta nufi ɗakinta. Sosai Affan yayi mamaki. Ita Juwairiyya kuwa, ciki takaici tace. "Uhumm lallai ma yarinyar nan, bansan me take nufi da niba, ban san me nayi mata ba, shiyasa yanzu ni bana ko son shigowa nan". Ta ƙareshe mgnar tana miƙewa zata fita. A hankali Ummi tace. "Kiyi haƙuri JUWAIRIYYA KINSAN abubuwan sai a hankali kada ki damu, kin san mutun in yanada ƴar matsala wasu lokutan ma, ba yin kanta bane". Uhum kawai Juwairiyya tace ta fita. Sukuwa sukaci gaba da hirarsu. Washe gari Hajia Mama ta aiko hadimanta su kawowa Sheykh dambun nama. Suna shiga tace, suje su rabashi an basu. Dama Ummi kam tasan za'ayi hakan. Sheykh dake shigowa kuwa cewa yayi. "Ke aka bawa ne da zaki kyautar dashi". Fuska ta ɗan yamutsa tare da cewa. "Bazaka ci bane". Amsar kwanon yayi a hannun Ummi tare da cewa. "Kuje kuce ngd". Daga nan ya nufi ɗauki shi. Da sauri ta miƙe tabi bayanshi. Yana shiga ya ajiye kwanon kan Bedside drower'n. Ɗauke kwanon tayi tare da cewa. "Dan Allah dan Annabi kada kaci, ka barshi, in dambun kakeso ai nayi maka". Taɓe baki yayi tare da cewa. "Nata yafi daɗi akan naki ai". Da sauri ta kalleshi idonta na cicciko da hawaye. Juyawa tayi ta fita da kwanon. "In kinje kin boye kizo". Yace mata, to tace. Ai kuwa taje ta zubar dashi ta bawa Saratu kwanon tace ta maida mata. A zaune ta sameshi da wata leda a gabanshi. Nuna mata ledar yayi tare da cewa. "Gashi ni na mance tun zuwanmu Umrah Aunty Hafsat da Umaymah suka bada sukace in baki". Sunkuyowa tayi ta ɗauki ledar tare da cewa. "Ngd matuƙa Allah ya biya musu buƙatunsu". "Amin Amin". Yace. Juyawa tayi ta fita. Shi kuwa wayarshi ya zaro yabi bayan kiranda Haroon yaketa mishi. Ita kuwa Aysha tana shiga ɗakinta ta buɗe ledar. Turarukane masu kyau da ƙamshi. Harda setin na miski da manshi da samubulunshi da turaren. Taji daɗin su sosai. Dan dama yanzu take shirin tayi wonkan tsarki. zata ci gaba da salla daga la'asar. Wonkanma ta shiga, ta fitowa tasa ɗaya daga cikin dogayen rigunan da suka turo mata. Yau kwana goma da yin salla ya kama saura kwana sha biyar auren Haroon da Jannart ƙanwar Juwairiyya. Tako ina shirye-shiryen biki ya kankama. Washe gari kuwa su Aunty Hafsat da ahlinta duk suka zo. Kai tsaye masarauta Leddi julɓe suka nufa. Daɗi a wurin Sitti babu bayani. Ga ƴaƴanta ga jikokinta, dan Umaymah ma ta kasa jira su iso wurinta randa sukazo da safe suka iso ita kuma da yamma ta iso. Farin cikin Sitti da Jadda basa faɗuwa. sai dai duk sanda sukayi irin wannan haɗuwar, yana tono musu tabo da damuwarsu da tashin hankali su. Hibba ce ta kira, Aysha, take sanar mata. Su Aunty Hafsat sun iso. Yanzu an fidda ankon aure da tsara duk abubuwan da zasuyi. Kwanan Umaymah uku a can ta koma ita da Hibba da Isha yar Aunty Hafsat budurwa, kamar Hibban komai na biki Umaymah ta shiryawa Aysha shi. Yau auren kwana bakwai bikin. Suna zaune shida Ummi suna tsara tafiyar tasu. Dan dole Juwairiyya zataje, amman zata tafi da Ya Jafar da yaransu da Jalal. Su kuwa zasu tafi da Jamil da Ummin. Sai Hajia Mama da su Ramla da Batool da har yau bata komaba. Kiran Haroon ne ya shigo wayarsa. Bayan sun gaisa ne yake cewa. "Wai kai Sheykh yaushe zaku zone? Dudufa yau saura kwana bakwai ne, kuma daga gobe za'a fara hidimomin". Da sauri yace. "Kai haba Haroon ka nitsu mana kaja numfashi kayi mgna a hankali. Ni dai bazan je duk sauran shagulgula kiɗe-kiɗe da raye-raye kuba bazan ce kada kayi bane, sanin Abun harda Aunty Rahma iyayen bidi'a." Cikin hatsala Haroon yace. "Za dai kazo kayi mana walima kam". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "Eh walimar maza ba, shima dan Abba da kanshi ne yamin mgn da dan ta kaine ba yi zamba sabida, ba amfani da abinda ake faɗa a walimar akeyi ba". Dariya Haroon yayi tare da cewa. "To Ustazu Allah ya kawo ka lfy". "Amin". yace "To yaushe zaku zone?". Jibi ya bashi amsa a taƙaice." Daga nan sukaci gaba da hira. Yau saura kwana biyu bikin kuma yaune zasu tafi. Aunty Juwairiyya da Ya Jafar da Jalal kuwa tun jiya suka tafi. Su kuma yau zasu tafi da dare. Ƙarfe takwas dai-dai jirginsu ya tashi zuwa jihar Tsinako. Tara dai-dai jirginsu ya sauƙa cikin birnin Tsinaku. Bayan sauƙansu da wasu ƴan daƙiƙu, aka buɗe jirgin, kana aka fara fita, daki-daki. Kasan cewar Ummi da Jamil na ta bakin ƙofar sune suka fara fita. Sheykh Jabeer da Aysha kuwa suna can VIP Side. Hakan yasa kusan sune ƙarshen-ƙarshen fitowa. A hankali yake taku cikin nitsuwa da kamala ta nitsastsun malamai magada annabawa. A hankali ya saƙo ƙafarsa kan step ɗin forko na farfin jirgin. ido ya lumshe tare da buɗesu yana son jihar Tsinako so mai tarin yawa sabida, yanada jigo shaƙiƙai masu sonshi fiye da yadda suke son kansu. Su Umaymah, Haroon, ga ƙarinsu Aunty Hafsat, da Aunty Rahma, da ahlinsu. Hannunshi yasa ya tattare bakin faffaɗan al'kyabbar jikinshi mai masifar kyau da taushi tare da sheƙi. Yanayin garin da ɗan hadari, ko ina yayi lib, garin yayi duhu yayi baƙi mai kyau, gajumare masu duhu sunyisa sararin samaniya ƙawanya. Ga wasu kyawawan ciyawi kore shar da suka malale can baya kaɗan, iska mai sanyi ke busowa tana ratsa jiki da jinin mutanen dake wurin. A hankali take biye dashi a baya inda ya taka ƙafarsa ya cire nan take taka tata ƙafar. Tayi shigar larabawa tayi masifar kyau, kasan cewar tasa Niƙabi baka iya ganin komai sai fararen idanunta da take ɗan jujjuyawa. A hankali ya gama sauƙa kan, steps ɗin. Yayinda ita kuma take step ɗin ƙarshe. Kanta ta ɗan juyo jin dirin wani jirgi a bayansu yana tashi, yana keta gajumare. Hannunshi yasa a hankali ya kamo nata, da sauri ta ɗan juyo jin hannunshi cikin nata. Takowa tayi ta sauƙo kana ta fara bin takunshi sabida bai rigaya ya sake mata hannun ba. Suna sauƙa gefen jirgin kaɗan baifi taku bakwai sukayi ba, suka isa gaban wata tsaleliyar mota fara ƙal mai sheƙin sabunta, ganin dogarai guda biyu a gefe da gefen motar sanye da jajayen kaya da surkin kore, sai tabka-tabkan rawuna, ne ya tabbatar mata su akazo ɗauka. Shi kuwa tafin hannunshi ta haɗe da nata ya sarƙafe yatsunshi cikin nata. Wasu dattawane suma sanye da kaya da rawuna amman su ba shigar dogarai sukayi ba, bisa alama suma, sunada ƴar saurata. Da sauri suka nufi gabasu. Suna isa dottawan suka ɗan saki murmushi tare da cewa. "Barka da isa lfy Malam Jabeer". Murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "Barka dai Baba Wambai". Sai kuma ya juya wurin ɗayan tare da cewa. "Barka da yamma Malam Liman". Ya ƙarishe mgnar yana miƙa musu hannunshi na dama, dan dana hagu yake riƙe da hannunta. Cikin kulawa Malam Liman ya amshi hannunshi tare da cewa. "Allah yayi maka al'barka ya bada ladan raya zumunci". Amin Amin yace. Cikin nitsuwa Aysha ta gaidasu, cike da jin daɗi suka amsa, tare da juyawa suka nufi motar, da tuni dogaran nan biyu sun buɗe musu, bayan motar. A hankali suka nufi can yayinda Wambai kuma da Malam Liman suka kama hanyar tafiya dan motarsu na can woje. Shi kuwa Sheykh suna isa ya ɗan ja da baya tare da sakin hannunta, ya nuna mata hanyar shiga da hannunshi. A nitse ta rusuna kana ta shiga. Bayan ta shiga ne, ta gyara zamanta tare da lumshe idonta sabida wani irin masifeffen ƙamshi da sanyi da sukayi mata sannu da zuwa a lokaci ɗaya. Gyara zamanta tayi ganin yana shigowa, can gefe ta matsa, shi kuwa yana shiga ya zauna, da sauri dogarin dake gefenshi ya kamo bakin al'kyabbar jikinshi ya samishi ita, ta ciki. Sannan ya maida ƙofar ya rufe. A hankali motar ta fara juyawa alamar direba na ciki. Su kuwa dogaran suka fara bin motar a hankali, har ta gama juya kanta, ta dai-dai-ta. Sannan suka fara sauri yadda tafiyarsu zaiyi dai-dai dana motar dake tafiya a hankali. A haka suka fito asalin farfajiyar kowa da kowa. Nan Ummi da Jamil suke cikin motar da aka ware musu. Kana Baba Wambai Wanda yake Aminin Abban su Jabeer ne ƙut da ƙut, shida Malam Liman suka shiga motarsu. Suma dogaran suka shiga tasu motar, haka suka jera motoci biyar tasu Sheykh ce a tsakiya, ta fadawa a gaba sai tasu Jamil sannan tasu, sai ta malam Liman sai kuma ta dogarai can baya. A haka suka nufi masarautar Tsinako. Cikin mota da Sheykh da Aysha suke kuwa, waya Aysha keyi bisa alama da wata ƴar uwarta ce. sabida yaga tarin farin ciki a fuskarta. A hankali ta ɗan juyo ta kalleshi lokacin da Junainah tace. "Adda Shatu ina mijin naki baki taɓa bashi waya mun gaisa ba, ko bakice mishi kinada ƙanwaba?". Da sauri ta ɗan janye idonta tare da cewa. "Gashi nan, na gaya mishi mana". Da sauri Junainah tace. "Ayyah Addana dan Allah bashi wayar." Juyowa ta kumayi ta kalleshi cikin raɗa dayin ƙasa da murya tace. "Junainah shi miskiline, yayi fuskar bosawa, baya dariya baya son mutane, kada ki damu dashi badai gani kina gaisawa da yar uwarki ba, mai ruwanki da wani can bare". Da sauri ta juyo ta kalleshi, jin yasa hannunshi ya zare wayar a kunnenta. Ido ta zuba mishi ganin ya manna wayar a kunnenshi. Ita kuwa Junainah baki ta tura tare da cewa. "A a Adda Shatu, shina ɗan uwanane, tunda yana tare dake yar uwata. Kuma ma Bappa yacemin da baki da lfy shi yake miki mgnin har kika samu lfy, Ni dai ko yayi fuskar bosawa bashi mu gaisa ina dai ba dukana zaiyiba". Wani irin bugawa da ƙarfi zuciyarshi tayi jin sautin amon Muryar yarinyar tamkar sautin amon da bazai taɓa mancewa a duniya ba. hakane yasa yayi shiru yana jin muryarta na dukan dodon kunnenshi da zuciyarshi, jin tayi shirune ya sashi yin sassauƙan numfashin tare da cewa. "Ƙarya takeyi miki Baby sherri take min. Ni Bana fuskar bosawa, kuma ina son mutane sabida Allah da kanshi yace. "Walaƙat karram'na bani Adam. Toni waye da zanƙi mutane, bazan dakekiba kinji ko". Ya ƙarishe mgnar yana kallonta tare da tsuke fuskarsa ya ƙanƙance idanunsa ya tsura mata su cikin nata, yana mai son ganin iya tsaurin idonta. Ita kuwa Aysha da sauri ta janye ƙwayar idanunta Allah ya sani batayi zato ko tsammanin zaiji abinda ta faɗa cikin raɗaba. Towai shi wanne irin kunnene dashi a rayuwarsa. Junainah kuwa cikin jin daɗi tace. "Yauwa Ina kwana Hamma". Ido ya lumshe tare da cewa. "Lfy Baby me sunanki". Da sauri tace. "Junainah, wani lokacin Adda Shatu na cemin Junnu ko tace min ƙanwaliya ko tace min Baby Ummey'nmu kuma tace min Mamana ko tace min auta". baisan sanda wani murmushi ya subce mushiba. Lokacin ɗaya yaji son yarinyar a ranshi. cikin nitsuwa yace. "Toni kuma da wanne sunan zan kiraki?". Da sauri ta kuma cewa. "Junainah dan Bappa na yace in dena bari ana ɓata min sunan. Hamma kai me sunanka, yaushe zaka kawo mana Addana". Juyowa yayi ya kalli gefenshi ganin sun isa cikin masarautarsu Haroon. A nitse Suka nufi Side ɗin Umaymah. dasu a cikin motar. Shi kuwa Sheykh Jabeer gyara zamanshi yayi tare da cewa. "To Junainah, Sunana Muhammad Jabeer, yanzu munyi tafiya sai mun dawo zan roƙi Bappa a kawo mana ke mu zauna ko". Cikin jin daɗi tace. "To Hamma Jabeer Allah ya dawo daku lfy, bari in meyarwa Bappa na wayarshi kar ya dawo ya sameni." Kafinma yace wani abun ta katse kiran. Dai-dai lokacin kuma motar su ta isa bakin farfajiyar shiga Big Part ɗin Umaymah, parking akayi. hakama motar Ummi da Jamil. bin wayar yayi da ido yanajin wani abu na musamman a zuciyarshi. Ita kuwa Aysha da sauri tasa hannun ta, zata buɗe marfin motar ganin Umaymah, Hibba, Aunty Hafsat da wasu ƴan mata da samari ƴan saffan-saffa kyawawa masu suffar larabawa sun fito daga wata babbar ƙofar suna tako wani babban steps masu faɗi dake jikin barandar wurin. Zura wayar yayi cikin al'jihunsa. A hankali yasa hannunshin ya kamo nata, jawota yayi kusa dashi tare da ɗan juyawa ya fuskanceta da kyau fuskarshi ya haɗe tare da cewa. "Nine mai fuskar bosawa ko? Ina zaune a gabana kikemin sherri da ƙazafi. Nine bana son mutane ko wato bana dariya". Bakinta ta turo ta cinnnashi sama. Idonshi ya tsurawa tattausan red lips ɗinta masu masifar taushi sai sheƙi sukeyi. mui-mui tayi da bakin alamun zatayi tsiwar Tata. Cikin murza bakin tace. "To kanayin dariyar ne? Ban taɓa ganin k..!" wani irin zaro ido tayi da ƙarfi cike da bugawar zuciya. Lokacin data buɗa lips ɗin ta tare da rabasu biyu zata furta kalmar K. Da sauri ya lumshe idonshi tare da kusanto da fuskarshi kan tata manne gishinsu wuri ɗaya, tattausan lip ɗinshi na na sama yasa cikin bakin ta, tare da kamo lip ɗinta na ƙasa, yasa cikin bakinshi ya zama nashi na sama yana cikin bakinta. Da sauri yasa tafin hannunshi ya tallabo ƙeyarta da kyau. Wani irin gigitaccen rugguma yayi mata. cikin rawan jiki ya c...! Littafina GARKUWA na kuɗine By *GARKUWAR FULANI* Idonshi ya lumshe jin fatar idanun sun mishi nauyi. Wani irin abu yakeji yana yawo a dukka cikin jininshi yana zaga jikinshi, manne lips ɗinshi da nata yayi, suka haɗe tamkar mayen ƙarfe. Hanunshi yasa ya ƙara tallabe kanta da kyau. Ita kuwa Aysha wani irin tsuma jikinta keyi tare da miƙewar tsikar jikinta, a lokaci ɗaya taji wani irin masifeffen mamaki, tsoro, kaɗuwa, domin abun yazo mata a baka-ta-tam ba zato ba tsammanin hakan daga gareshi domin bai taɓa gwada yin hakanba koda a kamace ne. Jin yadda yayiwa lip ɗin ta wani irin lasa da kuma tsotseshi tamkar ya samu tom-tom ne yasata. Yin yunƙuri da kiciniyar ƙwace kanta. Ronƙofawa yayi kanta da kyau jin zata kawo mishi wargi. Nauyin ƙirjinshi ya sakar mata ya danne nata ƙirjin da ƙirjinshi, kana ya buɗa al'kyabbar shi, ya rufesu ruf, wani irin numfarfashi yake fesarwa da sauƙewa a jere-a-jere. Cib tayi jin yadda ya mata ƙawanya da jikinshi kana ya sakar mata nauyinshi da yimata garkuwa da al'kyabbar jikinshi. Buɗe idonta tayi ta zubasu kan kyakkyawan fuskarshi, da take yalwace da. Hasken addini, ta ƙawatu da kyawun sura da hali da nagartacen haiba da imani. Gashin girarsa ta zubawa ido, tana kallo tare da sajenshi. a hankali ta shaƙi ƙamshin turaren OudKareem dake tashi a jikinsa. meda idonta tayi ta lumshe da sauri ganin Umaymah ta iso har gaban motar kusa da ƙofarsu. Mutsu-mutsu ta farayi. Sam ta kasa zillewa. Hakane yasa ta ɗago hannayenta, tasa bisa fuskarshi ta tallabe gefen hagu da damanshi ya zama tafin hannunta na kan sajenshi duka biyu. A hankali ya buɗe kyawawan idanunshi ya zubasu cikin nata. Da sauri ta janye nata, kanshi ya fara janyewa still dai yana liƙe da lip ɗinta kan harshensa. da sauri ta turo kanta jin kamar zai tsinke mata shi. Ɗouhh haka ya saki mata wani sauti mai kashe jiki da zuciya cikin kunnenta lokacin daya saki laɓɓan nata. Da sauri tasa tafin hannunta tana fifita lips ɗin tare dayin rau-rau da ido tace. "Zafi! zafi!! Zafeeeh!!!." Hannunshi yasa ya kama tsinin hancinta da yatsu biyu kana ya ƙanƙance idanunsa, cikin wata iriyar fitinenneyar murya yace. "In kika sake murguɗa min bakin, haka zan miki. In kuma kika sake yimin sherri ko ƙazafi tsinke bakin zanyi". cikin kwaɓe fuska tana fifita laɓɓan tace. "Ka tsinke min baki kamar maye". Kafaɗunshi ya buɗa tare da ɗagasu sama ya taɓe baki kana yace. "Mayen ne ai ni. In na tsinkasu haɗiyesu zanyi sai kije in sa miki na Aku kinji daɗin yin surutu da kyau". Ya ƙareshe mgnar yana janye al'kyabbarshi daga jikinta yana gyara shi. Hannunshi yasa ya jawo niƙabinta daya ɗage ya rufe fuskarta tare da cewa. "Ki rufe fuskarki kar Hibba tayi miki dariya tace kin zama mai dogon baki dengin jaɓa". Yana faɗin haka yasa hannunshi ya buɗe marfin motar tare da saƙo ƙafarshi ta dama waje. Wani irin murmushi mai cike da tarin. So, ƙauna, shaƙuwa, tausayi, da kulawa. Umaymah tayi mishi. Hakama Aunty Hafsat. Ita kuwa Aysha bakin ta ɗan tura tare da cewa. "Allah ko sai na gayawa Umaymah ka cinye min lips ɗin a". Juyowa yayi yana kallonta, tare da murmushi a fuskarshi. Sai kuma ya juyo da sauri jin Umaymah da Aunty Hafsat su ruggumeshi ta baya. Hannunshi ya miƙo mata tare da cewa. "To fito ki faɗa kada in rigaki yin nawa sharhin". Ture hannunshi tayi ta fito. Shi kuwa tana fitowa yasa hannunshi ya kamo nata tare da jawota bayanshi. Da sauri Aunty Hafsat ta sakeshi tare da komawa bayanshi hannunta ta jawo tare da Ruggumeta tana cewa. "Masha Allah diyar kirki". Da sauri tasa hannunta ta yaye niƙabin. Umaymah kuwa murmushi tayi cikin tsananin jin daɗin ganinsu take kallonsu cike da so da kulawa tare da cewa. "Jazlaan naji daɗin ganinku". Murmushi yayi tare da cewa. "Muma haka". Sai kuma ya juyo da sauri ya kalli Haroon da Ibrahim da suka fito can gaban motar bisa alamu duk Ibrahim ne yaja motar. Haroon kuwa yana gefen mai zaman banza. Cikin dariyar tsiya Haroon ya matsoshi tare da ruggumeshi ta gefe, dan su Umaymah duk sun sakeshi sun koma kan Aysha. Cikin tsiya yace. "Ur welcome Mr Jabeer Ustazu ƙalilan iya shege kasiran". wani irin tsare fuska da gira Sheykh yayi tare da watsa Haroon kallon. "Hegen munafurcin sa ido". Ya faɗa tare da Ruggume Haroon da ƙarfi yadda zaiji zafi. Da sauri Haroon yasa ƴar ƙara tare da cewa. "Wayyo Aunty Hafsat zai karyan baya in rasa na amarci". Dariya sukayi dukansu. Shi kuwa Sheykh ture Haroon yayi yana mamakin subutar baki irin na Haroon, kwaffa yayi tare da Ruggume Ibrahim murmushi Ibrahim yayi tare da cewa. "Barka da zuwa Garkuwan Masarautar Joɗa". Shima murmushi yayi tare da cewa. "Barka da zuwa, magajin masarautar Leddi julɓe". Hibba kuwa baki ta tura tare da cewa. "Aunty Aysha wato kinga su Umaymah ni Ko ki kulani ko?". Da sauri ta juyo ta ruggume Hibba tare da cewa. "Oh sorry my Hibba ai ke ta dabance". Da sauri ta juyo ganin wata kekyawar budurwa kamar Hibba ta gane Azeema ce yar Aunty Hafsat. cikin bagwariyar Hausa Azeema tace. "Wato mu bana musamman bane ko Aunty". Da sauri ta jawo hannun Azeema ta haɗa su ta ruggume. Da sauri Umaymah ta juyo ganin Ummi ta fito. Ruggume juna sukayi cikin jin daɗin ganin junasu sun kasa mgn sai murmushi. Jamil kuwa da sauri yaje ya Ruggume Abudul-azeez da Sadiq ta baya. Juyowa sukayi suma suka ruggumeshi suna farin cikin ganin juna. Sheykh kuwa sake Ibrahim yayi ya kalli Sadiq da Abdul-azeez ya shafa kan ƴan matasan. Umaymah ce ta juya ta nufi cikin gidan tare da cewa. "Ku shigo, maza ku taho ko". To sukace kana duk sukabi bayanta. Wani babban falo mai zaman kanshi wanda yake ɗauke da lumtsuma-luntsuman kujeru set biyu da Dinning table a can babban Dinning area da ƙaton fili a tsakiyar falon. Suka zauna. Su Hibba da Azeema sun sa Aysha a gaba. Haroon da Ibrahim dasu Sadiq kuwa suna ɗaya sashin. Umaymah da Aunty Hafsat da kansu suka rinƙa kawo musu abubuwan ci da sha. Bayan sun gaggaisa ne. Suka ɗan zauna suna hirar Yaushe gamo. Ummi ce ta ɗan kalli Umaymah tare da cewa. "Ina Rahma ne ban ganta ba ita". Aunty Hafsat ce ta amshi zancen da cewa. "Tab uhum Rahma taji biki ta zauna. Ɗazu da safe jirginsu ya wuce. Leddi julɓe, kinsan gobene za'ayi kamu, to taje ita da su Isha dasu Farida, sun haɗu dasu Juwairiyya sunacan suna shiryawa hidindimun da za'ayi". Ɗan juyowa sukayi suka kalli Azeema da ke cewa Sheykh. "Hamma Jabeer zamuje da Aunty Ayshan can ko gobe in Allah ya kaimu". Ba tare da ya ɗago kanshi bare ya kalletaba ya ɗan jujjuya kanshi alamun. A a, da sauri Azeema tace. "Ayyah dai". Umaymah ce ta ɗaga mata hannu alamun tayi shiru. Ummi da Aunty Hafsat kuwa murmushi kawai sukayi. Hibba kuwa ƙasa tayi da muryarta tare da cewa Aysha. "Zamuje ai". Kai Aysha ta gyaɗa mata alamun eh. Haroon kuwa juyowa yayi ya kalli Sheykh tare da cewa. "Yaushe kace zamu tsaida lokacin walimar?". Kanshi na sunkuye yana kallon wayarshi yace. "Na gama mgn da Abba, babu wani Dinner'n da za'ayi. Madadin dinan shi zamuyi waliman". Da sauri Haroon yace. "Wannan ai tatsuniya ce". Ibrahim ne ya ɗan kalleshi tare da cewa. "Wlh sun gama mgn da Abba, yace tunima ya gaiyaci manyan mutane duk akan walima za'ayi. An gama shirya komai ma, kuma babban wurine aka kama gefen, maza da matane, za'ayi walima mai kyau da ma'ana. Yafi akan yin wannan bidi'ar nan da zamuje mu gwamutsu maza da mata a wuri ɗaya a rinƙa kiɗe-kiɗen da bushe-bushen da raye-rayen banza da wofi". Murmushi Umaymah tayi ganin yadda Haroon ya haɗe fuska kamar zaiyi kuka cikin takaici yace. "To Ni yau ma zan tafi dan inje mu shiryawa kamun da kyau, duk sauran abokanmu zasu je". Ya faɗa yana kallon Sheykh, kafaɗarshi ya ɗaga tare da buɗawa kana yace. "Ya rage naka, Ni nan Muhammad babu inda zanje walimace da ɗaurin aure ya kawoni. Dan dole in jamaka kunne kasan tsarin zaman aure a musulunci ba a yahudance ba". Dariya sukayi sosai. Aunty Hafsat ce ta ɗan gyara zamanta tare da cewa. "In anyi bikin a can, kana in mun dawo nan anyi walima, washe gari ayi fansan ido da daren ranar Lahadi da dare zamuyi mother's day, dan ranar tamuce kuma biki biyune, tunda bamu samu zuwa na Jazlaan ba. Anyishi babu bikin komai to in sha Allah mu dai iyaye zamuyi namu shagalin wannan umarnine ba shawara ba, bakuma neman iziniba". Ido Sheykh ya zuba mata cikin sanyi yace. "Mom". Hannu ta ɗaga mishi, alamar yayi shiru. Sai ta kuma juyo ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummin Jabeer kunzo da shiri ko?". Cikin murmushin Ummi tace. "Sosai ma kuwa". Nan dai sukayi hirarsu da tsara yadda abin zai kasance. Hibba ce taja hannun Aysha, ɗakin Umaymah Suka shiga. Suna shiga tayi wani irin tsayuwa tana kallon tsarin ɗakin yayi masifar kyau. Wasu ƴan mata da manyan mata suka samu a zaune. Cikin murmushin Hibba tace. "Aunty Rabi'atu ga matar Hamma Jabeer Aunty Aysha da nake faɗa miki". Da sauri duk suka juyo. Masha Allah shine abinda suka faɗa kusan a tare. Ɗan rusunar da kai tayi ta gaidasu. Murmushi tayi ganin Aunty. Kubra ƙawar Umaymah dake Ɓadamaya. Motsowa tayi kusa da ita ganin tana miƙo mata hannu cikin kunya tace. "Aunty Kubra Ina wuni. yaushe kika zo". Murmushi tayi tare da cewa. "Alhamdulillah Aysha. Ni tun jiya nazo, ina ɗan nawa yana lfy ko?". Murmushi tayi a kunyace tace. "Alhamdulillah yana falo". Nuna mata sauran matan tayi tare da cewa. "Kinga nan duk ƙawayen Umaymah ne yawanci daga wasu garuruwan sukazo. Kin san Umaymah taku ta jama'ace". Sannu ta sake yi musu. Ita kuwa Aunty Kubra miƙewa tayi tare da kamo, hannun Aysha. "Zo nan". Tace tare suka fita Hibba na biye dasu a baya. Juyowa tayi ta kalli Hibba tare da cewa. "Jeki kira min Hafsat kice ina ɗakin can". Da sauri Hibba tace to, kana ta juya taje falo. Ta kira Aunty Hafsat kamar yadda Aunty Kubra ta umarceta. Tare suka juya suka tafi. Haroon da Ibrahim da Sheykh kuwa miƙewa sukayi suka nufi wanni babban part dake bayan na Umaymah wanda yake da yalwan ɗakuna babban falo sai 3 bedroom sai ƙaramin falo. Nan suka nufa, wanda akwai wani a gefenshi kuma nanne Haroon zai tare da Amaryarshi Jannart. Suna shiga suka samu abokansu. Hunnu sukayi ta bawa juna suna gaisawa cike da fara'a sukeyiwa Sheykh tsiyar yayi auren sirri wato dan baya son suje susha rawa ko. Murmushi yayi tare da cewa. "Mazarai sarakunan rawa yanzu ai kun samu wurin rawan ko?". Dariya sukayi. Aunty Kubra kuwa suna shiga ɗakin. Ta jawo wani matsakaicin akwati. wasu zafafan ɗinkuna ta fara fitarwa. Ko wanne da mayafinshi da takalminshi da jaka ko fosa. Shigowar Aunty Hafsat ce yasa tace. "Yauwa Hafsat Ni ina anko ɗin su na ƙawaye da a abokai wanda za'asa a kamun. Zama tayi gefenta tare da cewa. "Gashi nan gefenki ɗazu aka dawo dasu daga ɗinki. Harda na Farida shine fa tun ɗazu ta buwayeni da kira kadafa a manceta". Jawo ledar tayi ta firfito dasu, kowa da sunanshi a jikin nashi, shiyasa babu wuyan ganewa. Kala shida Aunty Kubra ta miƙawa Aysha tare da cewa. "Gashi dana kamu dana walima dana Dina na wuni, ne a nan sai waɗannan kuma kyasasu sanda kikeso". Aunty Hafsat ce ta ɗan kalleta tare da cewa. "Dinar dai mijinta ya hana, gacan Haroon kamar yayi kuka, Jazlaan kuwa ya gama karya zancen a wurin Abban su Haroon ɗin". Dariya sukayi kana Hibba tace. "Aunty Aysha zo muje ɗakina, ki gani nida Azeema ce kaɗai a can". Da sauri ta miƙe da tana jin nauyin sun Aunty Hafsat. Suna shiga ta zauna bakin gadon Hibba tare da cewa. "Iye ashe dai my Hibba ba dama wurin tsabta". Murmushi Hibba tayi cike da jin daɗin yaba mata da Aysha tayi. Ita ko Aysha numfashin gajiya ta sauƙe tare da cewa. "Yanzu bari inyi wonka wlh na gaji". Azeema da yanzu ta shigo ne riƙe da ƙaramin yaron Aunty Safiyya wacce itace ƴar farin Aunty Hafsat kuma itace matar Ibrahim. Yaron bai wuce shekara Uku bane. Tace. "My Aunty kamar tafiyar mota kikayi". Hannu tasa ta amshi yaron tare da cewa. "Masha Allah yaron waye wannan mai kama da Jalal". Hibba ce ta ɗan shafo kansa tare da cewa. "Aunty Aysha kice kawai mai kama da Hamma Jabeer ko". Yi tayi kamar bataji Hibba ba. Azeema kuwa cewa tayi. "Yaron Aunty Safiyya ce, kin santa ko". Kai ta jujjuya alamar a a. Da sauri Hibba tace. "Itace matar Ya Ibrahim ƙanin Aunty Juwairiyya". Murmushi ta ɗan yi tare da cewa. "Ok na gane masha ALLAH". Tace tana sumbatar goshin yaron. juyowa suka ɗanyi jin motsin buɗe ƙofa da kukan yaro. Safiyya ce ta shigo mai kama da Azeema sak. murmushi Safiyya tayi tare da cewa. "Iye Aunty Aysha kice kin gane Angon naki kenan". Murmushi tayi tare da cewa. "Angona kuma". Azeema ce tace. "Eh ai mai sunan Hamma Jabeer ne." Kai ta ɗan sunkuyar ta kalli yaron tare da cewa. "Eyeh kai mun gode kuwa". Kallonta Safiyya tayi cikin sakin fuska. gyara riƙon da tayiwa ƙaramin ɗanta, Salim tana bashi nono tace. "Yanzu muka dawo kasuwa akace min kun iso ko ruwa ban shaba. Azeema kawo min abinci tun safe muna kasuwa". Da sauri Azeema ta miƙa taje ta kawo musu abinci. Bayan ta zubane tace. "Aunty Aysha sauƙa kuci kema bakici komaiba tunda kukazo". Zatace a a . Safiyya tace. "A a dan Allah kada muyi haka dake sauƙo muci, Ni fa yar uwarkice kuma matar abokin wasanku kinsan ɗan kawuna aka auramin, ni matar abokin mijinki ne kuma Aminiyarki sannan ƙawar mijinki". Dole Aysha ta sauƙo sukaci abinci tare. Sannan ta miƙa taje tayi wonka. Tana fitowa Hibba na shigowa da jakar data amso a wurin Ummi a can ɗakin dasu Aunty Kubra suke. Fita sukayi Safiyya kuma ta shiga Bathroom ɗin. Nan ta samu ta kimtsa. Wani Shadda lace red color sai ratsin white blue a jiki wanda kamar zanen bakan gizo ta saka doguwar rigace Ta zauna a jikinta ras, tayi masifar kyau, bata wani yi kolliyar azo a ganiba. Gyalen shi farine ta yafa, bayan ta murza ɗaurin ɗan kwalinta. Turarenta mai ƙamshi ta fesa. Kana ta ninke kayan data ciren. Da sauri Hibba da yanzu ta shigo ta amshisu tace. "Yauwa bari in kai a wonkesu agoge kadama su tarun miki." "To". tace, kana ta maida marfin jakarta ta rufe. Safiyyah na fitowa ta kimtsa itama nan suka zauna suna hira har dai aka kira sallan magriba. Bayan anyi magriba anyi ishane. Duk suka fito babban falon. Sai Umaymah dake can cikin ƙawayenta da matan abokan Abbansu HAROON. ita kuwa Aunty Hafsat ta Tara zuriyarsu kab sunata hira. Suna tsara tafiyarsu da za'ayi gobe jumma'a da hantsi, zuwa Leddi julɓe. Da yamma ayi kamu jibi a asabar ɗaura aure da hantsi sannan su dawo da amarya da daren ranar kuwa ayi walimar washe gari Lahadi kuma ranar wuni ce ayi fansan ido da yamma, da dare kuma ayi shagalin mother's day. Duk yadda sukaso ayi bidi'a da yawa, Sheykh ya karya musu logo daya samu Ibrahim da Abbansu Haroon da kawunshi Baban Aunty Juwairiyya dasu Ibrahim da amarya Jannart ɗin. Ya dai tsara yadda yaga dama a bikin. Haroon kamar ya rinka ihu. In ya kufula sai Sheykh ya koma gefe yana kallonsa yana taɓe mishi baki. Shi da Ibrahim dama su sunce sai jibi zasuje asabar zasu sammaka da tawagarsu zuwa ɗaurin aure da ɗaukan amarya. Washe gari ranar Jumma'a da hantsi jirginsu Safiyya, Hibba, Aysha, Azeema, Aunty Kubra, da wasu ƙawayen Umaymah da ƙannen baban Haroon jirgisun ya isa birnin Jalaluddin. Sheykh kuwa shi tunda sukazo idonshi ma bai sake ganin Aysha, duk da tana ɗan faɗo mishi a rai lokaci zuwa lokaci sai dai baya bin ta kanta. Dan hidimomin sun sha kansu. Suna isa masarautar Jalaluddin. Kai tsaye suka wuce Side ɗin kakarsu. Sitti kenan wacce taketa dakon zuwansu dan ganin Aysha matar jikanta mafi soyuwa a ranta. Suna Shuga babban falonta Safiyya ta fara kiranta. "Sitti! Sitti!! Sittin Jadda ko dai kina can wurin tsohon zumanki ne". Dariya tayi ganin Sitti ta fito da sauri. hannu ta buɗe wa Aysha irin dai al'adar su ta larabawa. Cike daso tace. "Iye masha ALLAH Jazlaan ya samu kekyawar mace mai nagarta". A kunyace fuska ɗauke da murmushi Aysha ta isa jikinta. Ruggume ta tayi tare da cewa. "Sannu da zuwa masarautar julɓe, jikata". Cikin sakin jiki da ita Aysha tace. "Yauwa Sitti na sameku lfy?". Alhamdulillah tace. Tana kallon tsohuwar da kyau tana gani wasu kamannin Ummey a fuskarta. Jansu tayi har cikin Bedroom ɗin ta. Duk jikokinta ne. Safiyya ce ta zaro wayarta ta kira Aunty Rahama tace mata sun isofa. Aunty Rahma kuwa dake tsuma Jannart da kayan gyara na al'farma Juwairiyya da Jazrah da Saddiƙa na gefenta. Da sauri tace. "Gani nan zuwa yanzu kuwa, Safiyya". Tana katse kiran tace. "Muje Side ɗin Sittiina. Su Safiyyah sun iso." A tare suka miƙa suka nufi ƙofar Sitti. Tafiyar a kwai yar tazara tsakaninsu. A can Side ɗin Sitti kuwa, Bayan sun zauna Sitti tasa hadimanta sun kawo musu abin ci dana sha. Sunaci suna hira. Ita kuwa Aysha Ishma ƴar Aunty Rahma dake bacci kan gadon Sitti ta zubawa ido. Duk da bata ganin fuskar yarinyar gaba ɗaya amman ta hango wani irin masifeffen kama da takeyi mata da Junainah. Shiyasa gaba ɗaya hankalinta na kan yarinyar. Hibba ce ta ɗan kalleta tare da cewa. "Aunty Aysha kici mana, kin tsaya kallon Ishma". da sauri ta ɗan rusuna ta fara cin Couscous da miyar hanta da Sitti tayi musu da kanta. Suna shigowa Aunty Rahma ta tsaya tana kallonsu cikin sakin fuska tace. "To yau duk kamar takuma ta zama ɗaya ina surkar tawa". Sitti ce ta kalleta cikin son yar autar tata tace. "Gata nan a gabanki". Ta ƙarashe mgnar tana nuna mata Aysha dake zaune tana fuskantar gado. Ɗan juyowa Aysha tayi da murmushi a fuskarta. Da sauri ta juyo gaba ɗayanta tana kallon Aunty Rahma cike da mamakin tsananin kamarta da Ummeynta, hatta muryarsu iri ɗaya. Da sauri tayi ƙasa da kanta, jin ta zauna kusa da ita. Cike da Muryar mamaki tace. "Aunty Rahama ina kwana". "Lfy lau Alhamdulillah my surka ya ɗana, Jazlaan". "Alhamdulillah yana lfy". tace fuska a sake tare da alamun kunya da kuma al'hinin abin da take gani da ji na kamanceceniyar fuska da murya. Sitti ce tayi dariya tare da cewa. "Tab lallai kuwa da yana kusa da kinsha tsuka, kin san baya son kina ce masa ɗanki dan yace ya fiki". Safiyya ce tace. "Tab ai Hamma Jabeer baya son ace ta fishi, sai yace. "Dan wata biyun ne wani abun". Dariya dai sukayi ita kam Aysha. Ta shiga ruɗani kamannin. Ƴarinyar da aka kira da Ishma da Junainah sun bata mamaki, sai kuma ga kamannin da yafi bata tsoro ma yanzu kam ko murya da dariyar Ummey nata irin na Aunty Rahma ne. Ya ilahi ya mujibadda'awati". Ta faɗa cikin ranta. Lokacin da Ishma ta taso zaune daga baccin da takeyi, har kamar zata faɗi. Da sauri tasa hannu ta tare yar yarinyar da bazata gaza shekara biyar ba. Da sauri ƴarinyar ta manna kanta a jikinta tare da cewa. "Mommy zansha ruwa". Da sauri ta sunkuyo kan yarinyar hannunta tasa ta dafa goshinta, cikin sanyi tace. "To ga ruwan buɗe baki". Ta ƙareshe mgnar tare da ɗaukan bottle water mai ɗan sanyi dai-dai misali, tana buɗe marfinshi. Juyowa Ishma tayi jin baƙuwar murya. Cikin sauri ta kalli Azeema tare da cewa. "Laa Aunty Azeema kalli Aunty Ayshan Hamma Jabeer tazo". Tayi mgnar da alamun tasan Aysha a hoto. Murmushi tayi tare da sa mata bakin gorar ruwan a baki. Cikin mussuke ido ta buɗe baki ta fara shan ruwan. Aunty Rahma kuwa, kallon Aysha take cike da ƙauna. Aunty Juwairiyya ce ta ɗan kalli Aysha cikin yanayin da bazaka gane manufarshi ba tace. "Sannuku da zuwa yau kam gaki a masarautarmu tushenmu, gaki ga Sitti kakarmu data haifi babana ta kuma haifi Mamansu Sheykh da Ya Jafar dasu Jamil jininmu ɗaya". Ta ƙareshe mgnar cikin nuna kusanci da dangatakar dasu Sheykh na jinine. Kai Aysha ta ɗan juyo ta kalleta, murmushin gefen baki tayi, dan ta gane manufar Aunty Juwairiyya tana nuna mata cewa su jini ɗaya ne, itace bare a tsakaninsu. Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Eh yau kam gani ga Sitti ga Aunty Rahma". Ta ƙareshe mgnar tana wata mgnar a zuciyarta. "Uhumm Aunty Juwairiyya kenan, ai dama saida ɗan gari akanci gari da yaƙi, kina matsayin yar uwarsu kuma kike cutar dasu, in da zasu sani da bazasu aminta da keba". Muryar Ishma ce ta katse mata mgnar zuci da takeyi. "Aunty Aysha ina Hamma Jabeer". Kanta ta ɗan shafa tare da cewa. "Yana Tsinako". Da sauri tace. "To shi bazai zo bane?". Gyara zamanta tayi tare da cewa. "Zai zo". "Yaushe?". Ta kuma tambayarta a gajarce. murmushi ta ɗan yi tare da cewa. "In Sha Allah gobe zasu zo". Allah ya kaimu ta tafaɗa tana wasa da jelan gashin Aysha dake bisa kafaɗarta. Aunty Rahma ce ta ɗan harareta tare da cewa. "Maza tashi a jikinta ki barta ta huta". da sauri ta ɗan zame ta sauƙa ita kuwa. Aysha kai ta ɗan karya tare da cewa. "Aunty Rahma barta". Safiyya ce tace. "Ahyya baki san Ishma bane da shegen surutu da son jiki". dariya sukayi ganin yadda Ishma ta zumbura baki. Sitti ce ta miƙe tsaye tare da kallon jikokin nata da yar autar tata, tace. "Toh maza ku tashi muyi sallan azahar, in mun idar ku isa wurin Jadda ku gaisa." Kusan a tare suka mimmiƙe, Aunty Rahma ce ta kamo hannun Ishma tare da cewa. "Jadda ya fita, ai ɗazu ya kirani yace in masa abincin dare, wai ya ɗan fita zai kai dare kafin ya dawo". Dariya Sitti tayi tare da cewa. "Uhumm kai Jadda wato ki masa abincin dare. In kun koma kuwa naga wa zai ce ta dafa mishi". Safiyya ce tace. "Oh zai ci girgikin yar autarsa". Ita dai Ramatu murmushi tayi tare da cewa. Aysha Juwairiyya Jazrah Safiyya mu tafi ɗakina". To sukace kana suka bita a baya. Har zasu fitane Sitti tace. "A a Aysha dawo nan, ke kam baƙuwa tace ga masauƙinki". Murmushi Aysha tayi kana ta juyo ta dawo sabida tafi gamsuwa da zama kusa da Sitti akan a tsakiyar Juwairiyya da Jazrah dake mata wani irin mayataccen kallo. Haka dai sukayi sallan azahar, kana suka fara shirin kamu. Wanda tuni ango Haroon da tawagar abokanshi sun iso. Anayin Sallan la'asar suka fara. Sai gab da magriba suka tashi. Ranar kusan kwanan zaunen sukayi anata hirar yan uwantaka. Yayinda Aysha bata gajiya da jin muryar Aunty Ramatu da kallon fuskarta da fuskar Ishma. Basu samu sun isa wurin Jadda ba. Sun bari a akan sai gobe da safe in Allah ya kai rai. A can Tsinako kuwa, gaba ɗaya al'ummar masarautar Tsinako da baƙi abokan Abbansu Haroon dana kakansu Sarki. Da kuma baƙi na nesa dana kusa duk an kwana cikin shirin, tafiya ɗaurin auren. Masu tafiya a jirgi ƙarfe tara jirginsu zai tashi. Masu tafiya a motoci kuma sammako zasuyi. Sabida sha ɗaya na safe za'a ɗaura auren. Haka kuwa akayi washe gari da safe masarautar Jalaluddin, ta fara amsar baƙi tako wani saƙo na ƙasar Nigeria. Fadar masarautar dama farfajiyar ta cika tayi tab da baƙi da ƴan gari, tako ina halarta mutane keyi. Karfe sha ɗaya dai-dai na safe taron al'ummar musulmi suka shaida ɗaurin auren Haroon da Jannart. Bayan an ɗan wawwatse mutane duk sun kama hanyar komawa inda suka fito. Sai Abokan ango da zasu ɗauki ƙawayen Amarya da wasu yan uwa. Dan amarya dasu Aunty Juwairiyya da Jazrah da Aunty Rahma Ishma da ƙannen mamansu Jannart duk sun tafi a jirgi, da ango. Safiyyah da Aysha da Azeema da Hibba ne kaɗai suka rage. Dan Safiyyah ce ta hana Aysha tafiya dasu Auntyr Rahma tace, ita tare zasu tafi. Haka kuma Sitti ma tace haka yasa koda suke ribibin tafiya ita tana bacci a ɗakin Sitti bisa gadon mulkinta, dan kwanan da sukayi ba bacci yasa duk suna cike da bacci. Ibrahim da Sheykh kuwa sune suka tsaya da wasu abokan Haroon biyu, sai sunga duk mai buƙatar zuwa ta tafi. Ƙarfe sha biyu dai-dai Sheykh Jabeer da Ibrahim da Munnir da Mansur abokan Haroon Suka shigo babban falon Sitti. A nan suka samu Jalal da ya Jafar da Ammar ƙanin Aunty Juwairiyya da Ibrahim wanda shine yayan Jannart. Sai kuma Goggo Mairo ƙanwar Jadda da kuma sauran yaran Jadda wanda kishiyoyin Sitti suka haifa. Safiyyah na ganin shigowarsu ta miƙe ta nufi Dinning area fridge ta buɗe ta haɗo musu ya'yan itatuwa masu sanyi, ta gyara kana ta kawo musu. Bayan sun gaggaisa ne, Ibrahim ya ɗan kalleta tare da cewa. "Kun gama shiryawa ko?". Kai ta gyaɗa mishi al'amar eh. Sai ta kuma kalli Sheykh dake miƙawa Ya Jafar nonon inabi yana kuma ce mata. "Sitti fa?". jujjuya kai tayi cikin falon ta kalli gabas da yamma kudu da arewa. Gane wai neman inda Sitti takene yasa Goggo Mairo cewa. "Bata nan ai ta fita". ɗan miƙewa tsaye tayi tare da cewa. "Ikon Allah kuma fa da muna nan tare da ita. To ina tayi". Aunty Salima wacce take itace Babba a yaran Jadda ne tace. "Nima fa ita nake jira". Jalal ne ya ɗan kurɓi ruwan sanyi tare da cewa. "To ko tayi ciki ne". "Ba mamaki". Goggo Mairo tace. Cikin nitsuwa Sheykh ya miƙe tsaye, kekyawar al'kyabbar jikinshi ya ɗan buɗa tare da gyara zamanta jikinshi. Corridor'n da zai sadashi da special Side ɗin Sitti ya nufa, a nitse. A can bedroom ɗin Sitti kuwa. Aysha ce tsaye gaban dreesing mirror bayan ta gama ado da kolliyar ta. Wani dandatsetsen Shadda lace ne mai masifar kyau da taushi tare da sheƙi ne a jikinta, ɗinkin Doguwar rigace. Ta zauna ɗas a jikinta gwanin burgewa da ban sha'awa. Kalan kayan sun taimaka kwarai wurin burgewa, dark red wine mai masifar kyau, sai ratsin zare Royal blue mai azabar kyau da sheƙi da aka zubashi suffar zanen ɗawisu. Turare ta feshe jikinta dashi, kana ta maida kolbar sannan ta dawo gaban dreesing mirror kujerar ta jawo ta zauna. Kasan cewar dreesing mirror babbane mai tudu hakama kujerar. hannu tasa ta fara tsaɓule ribon ɗin da ta tubke himilin gashinta dashi. A nitse ya iso bakin ƙofar Bedroom ɗin Sitti. hannunshi yasa ya tura ƙofar, ɗan wani guntun tsaki yaja tare da sa guiwar yatsunshi biyu ya ɗan ƙonƙosa kofar sau uku. Kana ya ɗan tsaya gefe. A hankali ta juyo kanta ta ɗan kalli bakin ƙofar, har kamar bazata tashi ba. Sai kuma ta tuna ta rufe ƙofar lokacin da Safiyya ta shigo ta tasheta kan ta tashi ta shirya su tafi. To da zata shiga wonka ne ta rufe ƙofar dan tana jin kunya kada ta fito tana shiryawa wasu su shigo su sameta. A hankali ta miƙa tare da juyawa ta nufi ƙofar tana ƙoƙarin warware ɗan kwalinta. Isowarta bakin ƙofar yayi dai-dai da lokacin ɗaya kuma ɗan buga ƙofar. Hakan yasa bata gama warware ɗan kwalinba tasa hannu ta buɗe ƙofar dan a zatonta Sitti ce ko Safiyyah. Tana buɗe ƙofar sai ta ɗan koma da baya, haka yasa bata ganshi ba. Bai ganta ba. Kutsa kanshi yayi cikin ɗakin tare da sallama a bakinshi. kana yasa hannunshi ya maida ƙofar. Kasan cewar dreesing mirror yana fuskantar ƙofar shigowan ne, yasa. Mutun zai iya ganin abinda ke bayansa muddin yana kallon cikin madubin. Kanshi a sunkuye da alamu wayarshi yake ɗan lallatsawa. Haka yasa hankalinshi baya kan madubi. Ita kuwa Aysha, wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe a hankali jin daddaɗan ƙamshin turaren jikinshi. A hankali ta zubawa bayanshi idanu tun daga kan dudduniyar farar kekyawar ƙafarshi, har zuwa kan tattausan suman dake kwance lib a ƙeyanshi. Kasan cewar da yasa hiramin yau yayi irin siririn sakun nanne ya tattare gefe da gefen hiramin. Taku uku yayi ana huɗu ya tsaya cak, ba tare da ya ɗago kanshi ba ko ya juyoba, yace. "Wannan kallon fa?". Cikin tsananin mamaki da tsoron al'amarin Sheykh tayi saurin yin ƙasa da kanta. Shi kuwa Sheykh a hankali ya ɗago kanshi, ya dire idanunshi kan faffaɗan mafubin daya hasko mishi ita ras a ciki. Shigarta surarta yanayin tsayuwarta da yadda take wasa da yatsun hannunta da kuma sumanta dake zube a kafaɗunta sunyi masifar jirkita mishi jiki da jini da kwanya. Tabbas jikinshi ne ya sanar mishi ana kallonshi. Shiyasa yace. "Wannan kallon fa?". A zatonshi ma Aunty Rahma ce, ko Sitti dan yasan sun iya tsura mishi ido duk da sun san baya son kallo a rayuwarsa. Ita kuwa Aysha, Koda tayi ƙasa da kanta digadigin sawunshi ta zubawa ido. Shi kuwa Sheykh a hankali yaja wani nannauyan numfashi ya sauƙe a hankali. A hankali ya ɗan juyo fuskarshi ya haɗe tare da cewa. "Ke da izinin waye kika baro Tsinako kika zo nan?". A hankali ta ɗan ɗago kanta, kana ta ɗan turo baki, sannan ta gyara tsuyawarta, tare da cewa. "Cemin akayi in zo". Ta ƙareshe mgnar da yin taku biyu zuwa na uku da nufin zata koma gaban dreesing mirror ta ƙarisa shirinta. Tana isowa gab dashi, da nufin zata wuce da sauri ta rumtse idanunta. jin ya... Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k a mako biyi huɗu ake gama Part one da two. Normal group Kuma 300 a mako takwas za'a gama Part one da two. Idan kina buƙatar special Group kimin TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta wannan number da nakeyin whatsApp da ita 09097853276. In kuma Normal group kikeso na ɗari ukun, shima kiyi min TRANSFER ta ASUSUNA na Jaiz din in baki da halin turowa ta banki to ki sayi katin Mtn na ɗari uku ki copy numbers ɗin ki turo min ta WhatsApp 09097853276. BANA SON VTU KADA KIYI MIN TRANSFER'N DIN KATI BANA SO. By *GARKUWAR FULANI* Yasa ƙafarshi ya ɗan taɗe mata ƙafa. Da sauri ta rumtse idanunta tare dasa hannunta ta kamo nashi ta riƙe gam. Haka yasa bata ida faɗuwar da ta kusa yiba. Shi kuwa Sheykh fuskarshi ya tsuke tare da sa hannunshi ɗaya ya ɓamɓare hannunta dake ƙamƙame da nashi, kana ya ɗan ture ta. Da sauri ta kuma riƙo hannunshi jin tayi gefe zata faɗi. Wani irin ɗan ihun tsoro tasa, jin ta tafi shi kuma ya biyota, da sauri ta rumtse idanunta jira kawai takeyi taji kanta ya raɗu da ƙasa, sabida tsoro yasa tama mance ta gefen gado take. Jin ta faɗa kan tattausan katifar gadon Sittine yasa tayi wani irin dogon ajiyan zuciya. Sai kuma ta buɗe idonta da sauri jin ya faɗo jikinta. Da sauri ta kuma maida idon ta rufe ganin yadda sukeda kusanci. Fuskarshi na kan fuskarta, hancinshi na gogan mata gemunshi na bisa haɓarta, goshinsa na kan nata, hakan yasa data buɗe idon nata sukayi kiciɓis da nashi idanun masu kwarjini. Cikin jan numfashin tace. "Wayyo Allah na nauyi ƙirjina zai fashe, Babba da kai zaka fasamin ƙirji". Ido ya zubawa lips ɗinta yana ganin yadda take motsasu, sai sheƙi sukeyi. Haka nan yaji yana kusanto da bakinshi ga nata, da sauri kuma ya maida kanshi tsakankanin wuyanta da kafaɗarta, ya cusa hancinshi cikin tattausan suman kanta da ya baje a kafaɗun nata, wani irin sassanyan numfashi ya zuƙa tare da ƙamshin gashin kanta da jikinta, wani irin Yar-yar yaji tsikar jikinshi na zubawa suna miƙewa tsaye. hannunshi ya cusa tsakanin bayanta da katifar, ya ruggumeta gam-gam a jikinshi. Shiru tayi tana jin yadda yaketa sunsunar wuyanta yana ƙara matseta tare dasa harshensa yana ɗan lasar fatan wuyan nata. Tattausan sajenshi na gogar haɓarta, haka yasa tsikar jikinta zubawa. A hankali ta buɗe idonta ta zubasu kan sajen nashi dake kwance lib-lib tamkar ciyawar dake samun yabanyar safe da yamma. sai sheƙi yakeyi da ƙamshi, da sauri ta ɗan maƙe kafaɗarta jin yadda ya manna hancinsa da bakinshi ya manna mata wani irin sihirtaccen kiss mai masifar ratsa jiki da zuciya. Sosai take jin nauyinshi sabida duk jikinshi ya sake gaba ɗaya nauyinshi ya sakarmata. Haka yasa tasa tattausan tafin hannunta ta tallabe gefe da gefen fuskarshi cikin jan numfashin tace. "Ƙirjina kayi nauyi na tuba sauƙa". Ƙara matseta yayi a jikinshi kana ya maida bakinshi cikin kunnenta cikin dafeffiyar murya yace. "Waya ce ki jawoni jikin naki? Kuma da izinin waya kika baro Tsinako kika zo nan?". Cikin fidda nishi tace. "Ni ba jawoka nayiba na riƙeka ne dan kar in faɗi. Zuwa nan kuma ai Umaymah ce tace inzo". ƙara manna ƙirjinshi da nata yayi sannan yace. "Na'am wato Umaymah ce Allah yace kada ki fita in ba izinin ta?". Cikin cinna ɗan bakinta sama tace. "To ba Mamanka bace". kanshi ya maido ya haɗe fuskarshi da tata, on expected taji yasa bakinshi kan nata. Lips ɗin ta na ƙasa ya kama da fararen haƙoranshi na gaba ya ɗan ciza ka ɗan. da sauri tayi zillo tare da buɗe bakinta zatayi ihu, hakan ya bashi damar lalumar tattausan harshenta yayi mata wani irin masifeffen tsotsa mai gigitarwa. Ta kasa gane a zahirine ko a mafarki, wani irin kiss yake mata mai masifar ratsa jiki da zuciya. Tana gaza nazari ko tunanin gane Sheykh wanne iriyar halittace shi a cikin halittun bani Adam komai nashi special ne. Duk da babu wani ɗan adam daya taɓa sumbatarta tanada tabbacin ba ko wani namiji ya iya irin wannan zazzafan sumbatar Ustazan nan ba. A hankali tasa tafin hannunta bisa wuyanshi yatsunta ta cusa cikin sumar ƙeyarshi mai sulɓi. Shi kuwa Sheykh wani irin kanainaye harshenta yayi da nashi ya naɗe nata cikin nashi. A hankali ya fara zaro nashi cikin nata, wanda haka yasa taji wani abu na mata. Zir, zir, zir a cikin dukkan sasan jikinta, cikin baƙon yanayin daya cusata tayi wani irin juya harshenta cikin bakinshi ta lalumo harshenshi ta riƙe ƙam ta fara mishi wani irin shan tom-tom har tana bada wani sautin Douh. Wani irin tsuma da karkarwa jikinshi ya farayi tamkar mazari, hannunshi ɗaya ya zaro ya tallabo kanta da kyau. Dai-dai lokacin kuma Sitti ta fito daga falon Jadda tazo falonta, nan ta samu su Goggo Mairo duk sun tafi sai Ibrahim da Safiyyah da ƙannen iyayensu. So bayan sun gaisa da Ibrahim ne take tambayar. "Ibrahima ina Jazlaan ban ganshi ba tunda kukazo, bai shigoba, ga can jadda ma yace kuje yana nemanku". Shi dai Ibrahim murmushi kawai yayi yaci gaba da wasa da yaronshi. Safiyyah ce tace. "Yana bedroom ɗinki tun ɗazu ma shi muke jira duk kowa ya tafi saura mu. Su Azeema ma sun tafi da abokan Ya Haroon". Da sauri ta miƙe ta nufi special Side ɗinta kai saye bakin ƙofar Bedroom ɗinta ta nufa. Tana isa tasa hannu tana ƙoƙarin buɗewa tare da cewa. "Jazlaan! Jazlaan!! Jazlaan!!!". Kamar a wata duniya ko cikin mafarki haka yake jiyo muryar Sitti. cikin sauyawar tsari ya fara ƙoƙarin janye harshenshi daga gareta, amman ina ta riƙe gam. Cikin sauri ya buɗe idonshi ya zubasu kan fuskarta, wani irin sanyi yaji yana ratsa zuciyarshi. Jin motsin turo ƙofarne ya sashi yunƙurawa da ƙarfi ya janye harshenshi tare da janye jikinshi ya miƙe tsaye cikin tsananin kunyar kada Sitti ta shigo ta sameshi a wannan yanayin. Al'kyabbar ajikinshi ya fara bazawa yana buɗata yana gyarawa. Ita kuwa Aysha jin yadda ya zare harshenshi da yadda ya miƙene yasata dawowa cikin haiyacinta daga gigitar da ya sakata. Jiki na rawa ta mike zaune tare dasa tafin hannunta tana goge damshin bakinta cikin tarin azabebiyar kunyarsa. Sitti kuwa tana shigowa ganinshi tsaye yana murmushi yasata isowa gareshi ruggumeshi tayi cikin tsananin jin daɗi tace. "Masha Allah. Marhababika ya Habibi, ana Uhubbuk". Murmushi yayi tare da janye jikinshi gareta kana yace. "Ana uh hibbuki hubban azeem ya Sitti". Hannunta tasa ta shafa kansa fuska cike da annurin ganin jika mafi soyuwa a gareta tace. "Jazlaan me zan kawo maka? me zakaci? me kake da buƙata?". Murmushi ya kumayi kana ya zauna bisa kujerar sarautar dage gefenshi tare da cewa. "Sitti na samu komai". Sai kuma ya ɗan kalli Aysha ta wutsiyar idonshi. Har yanzu jikinta na tsuma. Safiyyah ce ta shigo da sallama tare da cewa. "Ya Sheykh mu tafi darefa nayi". Kai ya gyaɗa mata alamar to. Ita kuwa juyowa tayi ta kalli Aysha tare da cewa. "Kin gama shiryawa ko". Itama kai ta gyaɗa mata. har ta buɗi baki zata kuma yin mgna sai tayi shiru jin Sitti na cewa. "Yauwa to kuzo taso muje Jadda na son ganinku mu tafi ko". Ta faɗa tana miƙewa tsaye. Safiyyah ce ta fara binta a baya kana Sheykh. Har sunje bakin ƙofar fita ya ɗan juyo ya kalleta a fakaice. Mayafinta take yafawa tare da biyo bayansu. A falon suka samu Ibrahim, nan ya miƙe yabi bayansu. Kai tsaye Side ɗin Jadda suka nufa. Shi kaɗai yake zaune a falon nashi dan ya bar fada yace zai gana da jikokinsa. Cikin murmushi mai cike da kamala da dattaku, yake kallonsu tare da cewa. "Lale marhabin da jikokin Sitti da Jadda." Ya ƙare mgnar yana miƙawa Sheykh da Ibrahim hannunshi, Sheykh ne ya riƙe hannunshi na dama kana Ibrahim ya riƙe na hagu suka zauna suka sashi a tsakiya. Safiyyah ce ta matso gefen mijinta ta zauna. Ita kuwa Aysha a hankali ta rusuna zata zauna a gefe, da sauri Sitti tasa hannunta ta kamo nata tare da cewa. "Matso nan kusa zauna kusa da mijinki shine farin cikinmu. Yau gamu Allah ya nuna mana matar Sheykh." Ta ƙare mgnar tana ajiyeta kusa da Sheykh har jikinsu na gogar na juna. Murmushi mai cike da so da tsammani da zato Jadda yayi tare da cewa. "Amaryar Sheykh jikar Sitti da Jadda". Cikin murmushin tace. "Allah rene Jadda Allah nɓeddu sabbugo". Wani irin murmushi mai cike da masha hurin daɗi Jadda da Sitti sukayi tare da haɗa baki wurin cewa. "Amin Amin, tare dake da mijinki". Cikin tura baki Safiyyah tace. "Ikon Allah wato banda mu". Da sauri Sitti tace. "Wa lakum". murmushi sukayi dukansu, kana Jadda yasa tafin hannunshi bisa tsakiyar kan Sheykh da Ibrahim tare da cewa. "Wannan kawuna biyu duk masu ɗaukan rawanin girmane, hakama na ukunku Haroona shima akwai nauyin rawanin bisa kansa. Ibrahim da Haroon bani da fargaba a kanku. Amman shi Muhammad Jabeer akwai ruɗu a al'amarinsa akwai firgitarwa, yana tsakiyar Magauta. Sun kuma rigayemu sanin rawani na bisa kanshi. Shiyasa sukeyi mishi zagon ƙasa tun yana ƙaramin yaro." Shiru sukayi dukansu suna jin zantu kanshi, shi kuwa ɗan tsagaitawa yayi kana ya kalli Aysha yafi tota yayi da hannu alamun ta ƙara matsoshi. A hankali ta rarrafa ta matsoshi, kanta ya dafa kana yace. "Wata rana kina iya zama a matsayin da Gimbiya Aminatu take a yau. Ban saniba ko kafin lokacin ina raye, ko na amsa kiran Ubangiji na. Ga Muhammad Jabeer mijinki ne, kuma uban ƴaƴan kine, in sha Allah, sannan GARKUWArki. Dan Allah Aysha na baki amanarsa ki zame mishi GARKUWA ki kula da damuwarsa tun kan ta riskeshi. Yanada nauyi a cikin zuciyarshi mafataucine a faɗin duniya yana neman wani abu nasa mafi, ƙololuwar daraja ga ɗan adam daya ɓace matsa tsowon shekaru masu yawa, a hasashen da akayi mana zaki iya haska mishi hanyar da zaibi ya ganoshi". Kai kawai take gyaɗa Dattijan tanajin hawaye na cika mata ido. Da kalmarshi ta ko yana raye ko ya amsa kiran Ubangiji. Shi kuwa Sheykh lokaci ɗaya yanayin fuskarshi ta sauya cikin muryar dake nuna dafin zafi da tiririn da ke cikin zuciyarsa yace. "Uhummm Jadda taimakon Ubangiji na mahaliccina masanin zahiri da baɗini kawai nake nema, shi zai haskamin hanya in riski haskena. Zanyi ta roƙonshi kuma da fatan ya baku aron rai da lfy har sanda burinmu zai cika. Ina addu'o'in Allah ya bawa magautanmu lfy da rai har zuwa lokacin da gsky zatayi halinta". Tuni Safiyyah da Sitti sun fara sakin Shessheƙan kuka. Wanda sam Aysha ta gaza gane dalilinsa kalaman Jadda da Sheykh kuwa sunyi mata ɗaurin talala a ƙoƙolwarta, ta gaza gane bakin zaren haka yasa ta tattare yawun bakinta cikin kukan da taji yana son kubce mata tace. "In sha Allah Jadda zan kula da amanarka iyakar iyawata. Zan kuma tayashi da addu'a koda bana yankin da yake. Tabbas watan-wata-rana gsky zatayi halinta". Sai ta kuma kalli Sitti da Safiyyah tare da cewa. "Sitti kiyi haƙuri du ban san zafin me kikeji a zuciyarki ba, amman kukanki yamin kama da kukan uwar data rasa ɗanta, kiyi haƙuri". Da sauri Sheykh ya miƙe ya fita, hakama Ibrahim. Safiyyah kuwa hawayenta ta share kana ta kamo hannun Aysha tace. "Jadda mu zamu tafi kada dare yayi mana". A hankali Yace. "Bazaku tsaya kuyi sallan la'asar ba". Sitti ce tace. "Sai dai suyi a hanya naga yadda Sheykh ya fita bazai dawo cikiba". Kai ya jinjina kana yace. "To Allah ya kaiku lfy ya tsare hanya. Aysha Allah yayiwa aurenku al'barka". Kusan a tare sukace Amin. Kana suka miƙe suka fita. Shi kuwa Jadda ya kira Sarkin dogarai ya bashi umarnin a haɗa motar dogarai hudu suyiwa jikokinsa rakiya. Biyu a gaba biyu a baya tasu Sheykh a tsakiya. Wacce Sheykh da Aysha suna baya. Ibrahim da Safiyyah suna gaba, Ibrahim ke jan motar. A haka suka bar masarautar Jalaluddin suka nufi jihar Tsinako. Tafiyar mai yar tazara ce. Shiru cikin motar Ba maiyin mgn, Sai sautin Radio da suka kunna. Jingine yake da kujerar yayi shiru, idonshi a lumshe sai lips ɗin shi da yake motsawa alamun yana tasbihi kamar ko yaushe. Ita kuwa Aysha sosai ta faɗa duniyar nazari. Ibrahim kuwa ya maida hankali kan tuƙin. Safiyyah kuwa bacci nema ya saceta a motar. A ƙalla tafiyar awa ɗaya sukayi, kana suka fita jiharsu Jadda suka fara tafiya cikin dajin jiharsu Haroon. A hankali ya buɗe idonshi. Jin Ibrahim na cewa. "Tab lallai Abban Haroon da Sarki Ahmadu suna ji da wannan walimar da za'ayi. Kajifa duk gidajen rediyon Tsinako, gaiyatar walimar akeyi ba ƙaƙƙautawa kaji ko zasu sakeyi." Meda kunnuwansu sukayi kan abinda ake faɗin. "A madadin iyalan mai girma sarki Ahmadu suna farin cikin gaiyatar walimar auren. jikokinkin mai Martaba Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Joɗo da matarsa Aysha Aliyu Garkuwa. Da kuma Haroon Abubakar Ahmadu. Da amaryarsa. Jannart Umar Jalaluddin Za'ayi walimar ne a wurin babban filin taron al'ummar musulmi na Tsinako, ana gaiyatar ɗaukacin al'ummar musulmai wurin walimar wanda za'ayi yau misalin ƙarfe takwas na dare zuwa goma da izinin ubangiji, in da sanan malamin nan Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa wanda shima angone kuma shi zaiyi nasiha ga mauratan. Saƙon gayyata daga Mai martaba Sarkin Ahmadu. Allah ya bada ikon zuwa Amin...". Gajeren tsaki Sheykh ya ɗan ja tare da cewa. "Kai tsoffin nan fa sunada matsala, ji wani dogon sharhi iya sunayemmu ya ishi a gunduri mai sauraro". Murmushi Ibrahim yayi tare da cewa. "Kuma wlh tallatar tayi armashi." "Sosai ma kuwa". Safiyyah tace, cikin jin daɗi. A gogon hannunshi ya kalla kana yace. "Tsaya nan garin muyi salla la'asar tana gab da wucewa". To Ibrahim yace, kana sukaci ga da tafiya. Tafiya kaɗan sukayi suka isa. Wani masallaci mai kyau wanda dama dan matafiya akayishi. Gefen mata da ban gefen maza da ban. Bayan duk sunyi parking ne fadawan, suka fara fitowa. Da sauri sukazo suka buɗe musu mota. Ibrahim ne ya fara fita kana Safiyyah. Juyowa yayi ya ɗan kalleta ganin ta gyara zamanta ta kishin giɗa tare da lumshe idanunta. fuska ya ɗan yamutsa kana yace. "Fitowa zakiyi muje muyi salla. Ba gyara zama zakiyi ba." Shiru batayi mgna ba, haka yasashi haɗe fuska ya kuma maimaita mgnar. Fuska ta kwaɓe tare da cewa. "Ni nayi". Idonshi ya zubawa fuskarta na daƙiƙu biyar. Uhummm yace kana ya sa ƙafarshi ya fita. Bayan sunyi sallan ne kana suka dawo sukaci gaba da tafiya. Ƙarfe biyar dai-dai suna cikin masarautarsu Haroon. Suna shiga fadawan suka wuce masauƙinsu dan sai gobe zasu koma. Su kuwa Sheykh da Ibrahim Side ɗin Abban Haroon Suka nufa sabida kiransu da yayi a woya. Aysha da Safiyyah kuwa Side ɗin Umaymah suka wuce. Suna Shiga Hibba tace. "O oyoyo My Aunty's Umaymah gasu Aunty Aysha sun iso". Da sauri Umaymah da Aunty Hafsat da Rahma suka fito. Cikin kula Umaymah tace. "Allah sarki Ɗiyata sukayi muku wayo suka dawo a jirgi ku suka barku da gajiyar mota ko". Murmushi tayi tare da sunkuyar da kai tace. "Ina wuni Umaymah Aunty Hafsat barka da yamma". Murmushi sukayi suka amsa cike da kulawa. Aunty Rahma ce tace. "Yaseen kuwa Umaymah ba wayo mukayi musuba Ibrahim ne yace mu barsu zasu dawo tare tun randa mukaje hutasa bayi shirin dawowa dasu a jirgiba". Ta ƙare mgnar tana kallon Aunty Juwairiyya da Jazrah da suka shigo yanzu. "A Safiyyah sai yanzu kuka iso". Jazrah ta faɗa tana ƙin kallon inda Aysha take. "Eh ba kun musu wayo ba". Aunty Hafsat ta faɗa. Murmushi suka ɗan yi. Cikin kula Umaymah tace. "To Safiyyah yanzu dai kuje ku ɗan huta, kafin ku fara shirin zuwa walimar." To tace kana suka nufi ɗakin Hibba dan yau Side ɗin Umaymah cike yake maƙil da taron al'ummar Annabi. Suna shiga Aysha ta wuce Bathroom da hand bang nata a hannunta. Meda ƙofar tayi ta rufe tare da sauƙe ajiyan zuciya. Dan tana son kimtsa jikinta sabida larurarmu ta mata da take tare da ita. Allah yasa ma ita in tana fashin salla bata yawan fitsari. A wuni bazai fi sau biyu zata zagaba, dan fitsari sai dan ko kimtsa jikinta, shima kuma baya mata wawan zuba, a bisa tsari yake zubo mata sai dai tana yawan bacci in bata salla. Wonka tayi kana ta kimtsa jikinta da kyau, kana ta fito ba kowa a ɗakin sai ɗan Safiyyah dake bacci. Akwatinta ta buɗe ta zaro wata doguwar riga mara nauyi ta zura. Tana rufe akwatin Hibba da Aunty Rahma Suka shigo da Foodflaks a hannunsu. Ishma biye dasu da plate and spoons. A tsakiyar ɗakin suka ajiyesu bisa carpet. "My surka ina Safiyyah". juyawa sukayi jin muryar Safiyyah a bakin ƙofar shigowa tana cewa. "Gani Aunty Rahma naje nayi wonka a wancan ɗakin ne". "Ok to ga abinci zo kuci". Cewar Rahma to tace kana ta shigo. Aunty Rahma da Hibba kuma suka juya zasu fita Ishma na biye dasu. Cikin yanayin gajiya Aysha tace. "Ishma na zo mu zauna mana". Cikin sanyi tace. "Mommy tace in barki ki huta". Fuskar Rahma ta kalla tare da cewa. "Aunty bar min ita". Sake hannun Ishma tayi tare da cewa. "Ai shike nan gata in ta buwayeku da surutu Safiyyah ta korata". Da sauri ta dawo ta zauna bisa cinyar Aysha kana su kuma suka fita. Safiyyah ce ta zuba musu abincin. Bayan sunci sun shane. Aysha ta koma kan gado sabida har yanzu tana ɗan jin ciwon cikin kaɗan-kaɗan duk da tasha mgnin ta. Kwanciya tayi tare dasa Ishma a gaba. Ganin kamar bacci zatayi ne yasa Safiyyah fita, ta koma can cikin ƴan uwa nan sukaci gaba da hirarsu. Saida aka kira sallan magriba ne duk suka tashi duk sukayi al'wala sukayi sallan magriba da yawa basu tashi bisa abin sallaba saida sukayi sallan isha kafin suka tashi. Nan suka fara shirin tafiya walimar. Aunty Hafsat Maman Safiyyar kenan wacce suke kiranta da Mamma ce ta nufi ɗakin Hibba tana cewa Safiyyah dake bayanta. Yauwa zo ki kaiwa Jannart nata kayan da zatasa a walimar, gana Aysha kuma." Ta ƙarishe mgnar tana tura ƙofar Bedroom ɗin Hibba. A hankali ta ƙarasa cikin ɗakin. Kana a hankali ta juyo ta kalli Safiyyah cikin yin ƙasa da murya tace. "Har tayi bacci ne ma?." "Ai tun dazu ma tayi baccin, bari in tasheta". Safiyyah ta faɗa tana nufar gadon. Da sauri Mamma tace. "A a kada ki tasheta da ƙarfi ba'a son tada mai ciki daga bacci ta sigar da zata firgita". Aunty Rahma dake shigowane tayi saurin ƙarasowa tare da cewa. "Kai Aunty Hafsat haba dama ni na lura kamar ciki take dashi naga tana yawan bacci". Juyowa sukayi suna kallon Safiyyah daketa dariya ƙasa-ƙasa cikin dariyar tace. "Au ku dama kallon mai ciki kukeyi mata ashe. To wannan kam yanzuma bata salla, kuma dama wasu in suna al'ada suna yawan bacci inaga ita hakane". "Kai Safiyyah wannan tsarabe-tsaraben naku na Nurses baya gaya muku gaskiya wasu lokutan". Mamma ta faɗa da iya kar gskyar ta. Ita dai Safiyyah dariya tayi kana ta fara kiran Aysha. Ita kuwa Aysha tun mgnar Mamma na forko ta farka daga baccin ta dai ci gaba da rufe idonta ne kawai sabida karta katse musu hirarsu. A hankali ta buɗe idonta tare da yin salati kana ta miƙe zaune. Cikin kula Mamma tace. "Sannu ko tashi kiyi salla ki shirya dan har an fara kai mutane wurin walimar". Cikin sanyin bacci tace. "To Mamma". Daga nan ta miƙa ta nufi Bathroom. Ita kuwa Mamma miƙawa Safiyyah ledar kayan Jannart tayi kana ta ajiyewa Aysha nata a bakin gado tare da cewa. "In kin fito ga kayan da zakisa a cikin jakar nan a bakin gado". "To ngd Mamma". Tace tana rufe ƙofar Aunty Rahma kuwa hannu tasa ta ɗauki Ishma dan zataje ta kimtsata. Safiyyah kuwa da sauri ta kaiwa Jannart nata kayan ta dawo. Tuni ƙawayen Umaymah manyan mata da matan abokan Abbansu Haroon matan sarakuna Da ƴaƴan sarakuna duk anata kaisu wurin da aka tanada dan yin walimar. Manyan mutane dattawa maza masu karamci da mutunci yan kasuwa da yan siyasa da sarakuna duk sun cika maƙil a babban hall ɗin. Katon hall ne wanda a ƙalla zai iya ɗaukar mutune dari takwas zuwa ɗari dubu ɗaya. An gyara wurin an ƙawatashi. Ansa wani labule mai zaman kanshi an raba wurin biyu, kasan cewar dama ƙofofin shigowan biyune, haka yasa aka tsara wurin yadda mata zasu zauna a gefe ɗaya maza a gefe ɗaya bazama su ga junaba. Sai can sama akayi wani ɗan dandamali wanda sai ka taka steps huɗu ana biyar zaka hau. Shine wuri na musamman wurin zaman malami. Ƙasa kaɗan dashi kuma wani ƙawataccen table ne mai kujeru shida, inda nanne wurin zaman angwaye da amare. Can gefen inda malamin zai zaunama akwai ƙofar da ta nan zai shigo. Tako ina ka cilla idonta haskene ras tamkar rana, wurin yayi kyau gwanin ban sha'awa. Gaba ɗaya wurin mata da mazan ya cika maƙil duk manya-manyan baƙin sun samu isowa. Hatta Sarki Ahmadu da tawagarsa da Abbansu Haroon da tawagar abokanshi duk sun iso. Hakama Umaymah da da mutanenta hakama Mamma ta iso da Hajia Mama da Ummi da Aunty Juwairiyya da Hibba da Azeema. Isowar Sheykh Jabeer da Ango da amaren kawai ake dako. Madadin zama shurun sai akasa, sautin karatun al'ƙur'ani mai girma. A can gida kuwa, Ibrahim, Haroon Sheykh da ne tsaye a harabar farfajiyar Side Umaymah, suna cikin wata iriyar fitinenneyar shiga mai masifar kyau da ban sha'awa. Shigar fararen jallabiyar ƙirar Pakistan irin mai riga da wonɗonan ne kalar Sky blue mai azabar kyau da taushi da sheƙi. Sai wasu tattausan al'kyabbar farare ƙal tamkar madara, al'kyabbar sun irin mai shara-sharan nanne haka ya bawa kolliyar tasu damar zama kamar adon sararin samaniya. Sai hiramin dake kansu ne ya banbanta na kan Haroon da Ibrahim farine tas. Sheykh kuwa nashi farine sai ɗigo-ɗigon Sky blue, hakama takalminshi hafl cover suma fararene sai ɗigon Sky blue. Sai kekyawan zoben Daimond mai ɗigon Royal blue mai masifar kyau sai wal-wal yakeyi. Sai ƙamshi sukeyi da sheƙi. Ibrahim ne ya kira Safiyyah a waya tare da cewa suyi maza su fito mana. To tace kana ta kalli Aysha dake cikin shigar doguwar riga mai masifar kyau da tsada, rigar iri ɗaya ce da Tata data Jannart. sai dai tafi kama jikin Aysha sabida ta fisu faɗin ƙasa da sama. Sunyi kyau sosai sunyi rolling kawunansu da gyalullukan suka fito tamkar yammatan larabawa. Cikin sauri ta fesa turare kana ta kalli Safiyyah tare da cewa. "To na gama mu tafi ko". Murmushi Safiyyah tayi tare da cewa. "Masha Allah kinyi kyau. Mu tafi". Da haka suka fito. A falo suka samu hadiman Umaymah nata gyara gidan. Suna fitowa Aunty Rahma da Jannart suma suka iso. Da sauri Ibrahim ya buɗe motarsa ya shiga, Safiyyah ta shiga gefenshi. Aunty Rahma da Ishma suka shiga baya. Haroon kuwa kama hannun Jannart yayi suka shiga bayan motarsa direbanshi na gaba. Sheykh kuwa a hankali ya buɗe motarshi dasu Sulaiman da Ya Hashim suka zo da ita, kuma su tuni an kaisu can wurin walimar. Kasan cewar babu mai janshi ne yasa ya shiga ya zauna a mazaunin gireban. A hankali tabi bayanshi ganin tuni Ibrahim yaja motarshi hakama motar Haroon. Cikin takun nitsuwa ta iso gab da motar, hannu tasa zata buɗe baya ta shiga. Jin marfin a rufe yake yasa ta ɗan matso kusa da inda yake tare da cewa. "A rufe yake". Ƙwayar idanunshi ya juya mata tare da mata alamun ta zagaya ta shigo can gefenshi. Kasan cewar yana latsa wayarshi haskenta ya haska fuskarshi yasa ta gane manufarshi. Zagayawa tayi ta buɗe ta shiga kana ta maida marfin. A hankali ta juyo ta ɗan kalleshi jin yace. "Bismillah". Kana ya tada motar yaja suka bar harabar wurin. Kasan cewar wurin babu nisa sosai da masarautar. Tuni su Haroon sun isa har sun shiga sun zauna yanzu isowar Sheykh kawai ake jira. Suna isa harabar wurin. Bayan yayi parking, suka fito. Suna isa suka samu tarin fadawa a bakin ƙofar. gaba yayi ya nufi ƙofar da zai shiga ta wurin. Ita ma binshi a baya tayi. Suna shiga, tayi maza ta kange fuskantar da bayanshi sabida. Tarin mutanen da ta gani sun firgitata, sam batayi zaton yawan mutanen ya kai haka ba. Fahimtar hakane, yasashi yin gaba ita kuma tana biye dashi. Har inda su Haroon suke. Kujerar dake gefen Jannart ya nuna mata. Ai da sauri ta zauna. Shi kuwa sunkuyowa ya ɗanyi kan Haroon kana yace. "Ka nitsu da kyau ka saurari abinda Allah da Manzonsa suka ce a tsakanin ma'aurata". Cikin murmushin dake bayyana zallar jin daɗi da zumuɗin amarci Haroon yace. "To Sheykh". Daga nan ya juya ya koma inda aka tanada domin shi. Yana zama wani ɗan agaji ya dawo bayanshi ya tsaya. kana ya miƙo mishi abin mgn. Amsa yayi kana ya saƙalashi a bakin al'kyabbar jikinshi. Gyara zamanshi yayi da kyau kana ya fuskanci taron al'ummar baki ɗaya. Ɗaya daga cikin ƴan agajin ne yasa hannunshi ya katse sautin karatun Alqur'ani dake tashin. Cikin nitsuwa kamala haiba da ilimi ya ɗanyi gyaran murya tare da fara bude taro da bimilla da addu'a da sallama. "Bismillah rahmanirrahim. Assalamu alaikum warahmatullahi wa barka tuhu. Innal hamdalillah nahmaduhu wanasta inuhu wanastagfiru wana uzubillahi min shururi am fusina wa sai'yi ati amalina. Manyahadillahu fala mudillalah, famanyuddul fala hadiyala wa asshahu'alla'ila'ha'illalahu wahdahu lasheri kallah, wa asshahadu annamuhammadan abduhuwarasulu. Ya ayu allazina amanuttaƙullaha haƙƙa tuƙatil wala ta mutunna illah wa antum muslimun ya ayu hannasu taƙu rabbakum. Kalakum min nafsin wahida, wa kalaƙa minha zaujaha wa bassa minhuma rijalan khasiran wa nisa'ah wattaƙullah lazitasa'aluna bihi, wal'arhama innallaha kana alaikum raƙiba, ya aiyu allazina amanutaƙullah wa ƙulu ƙaulan sadidah yuslahlakum amalakum wayagfirlakum zunuba kum, waman yuɗillah wara sulahu, faƙadfaza fauzan azeema ambaduhu fa inna'asdaƙal hadisi kitabullah wa'ahsanal hadi hadiyu Muhammadin (S.A.W) wa sharal umuri muhdasatuha fa innakulla mudasatin bidi'a wa kulla bidi'atin balala wa kulla balaltun finnar." Dogon nufamshi ya sauƙe mai ɗan nauyi sabida jan dogon numfashin da yayi, kana ya kalli Side ɗin dasu Abbansu Haroon suke yace. "Alhamdulillah kamar yadda muka sani, walimace ta farin cikin auren ƴan uwanmu, kana kamar yadda kowa ya sani walima shine aci asha kana a watse. To a madadin muyi zaman da ci da sha kawai ya dace mu haɗa da ambaton sunan Allah, dayiwa ango da amrya taƙaitacciyar nasiha akan tsarin aure a musulunce da haƙƙoƙin ma'aurata ga junansu da addu'an zaman lafiya." A hankali yayi gyaran murya. Kana ya muskuta ya gyara zamanshi da kyau ya fuskanci taro al'ummar Annabi dake gabashin. Manya da yara maza da mata. Especially matasa, yatsarshi manuniya yasa gyara zaman siririn farin gilashin dake manne a fuskarshi. Ɗan sunkuyar da kanshi yayi. Dai-dai inda abin sautin mgnar ke saƙale a wuyan al'kyabbar jikinshi. Gaba ɗaya hall ɗin yayi tsit bakajin motsin kowa sai sautin numfashin mutane dana A/C. Cikin tattausan lafazi muryarshi ta ratsa kunnuwan duk wanda yake wurin inda yace. *AURE* Ma'anar aure a musulunce shine. Sunnan Allah a wojen halittar Allah daya halitta ya haliccemu ne a jinsi guda biyu macce da namiji. Kamar yadda Allah (S.W.A) ya ce, a Suratul Zariyya aya ta 49:- (WA MIN KULLI SHA'I'IN KHALAƘNA ZAUJAINI LA ALLAKUM TAZAKKARUM) "Kan ko wa wane abu Allah ya halice shi namiji da mace don ku yi tunani a kansa. Sannan Allah maɗaukakin sarki a wata ayar ya sake cewa a Suratul yashin aya ta 36:- (SUBHANALLAZII KHALAƘAL AZWAJA KULLAHA MIMMA TUMBITUL ARDU WA MIN AMFUSIHIM WA MIMMA LA YA ALAMUN) "Tsarki ya tabbata ga Allah wanda ya halicci ma'aurata namiji da mace, dukkansu daga abinda ƙasa ke sirarwa, kuma daga ko wannensu kuma da ma abin da basu sani ba!." Kanshi ya ɗan ɗago ya kalli gefen maza, idonshi ya ɗan lumshe sabida gamsuwa da nitsuwarsu data tabbatar mishi, zantukanshi na ratsasu. Idonshi ya ɗan tsaida kan fuskar Haroon ango mai jiran gado. Sai kuma ya janye idonshi yaci gaba da cewa. "Tabbas da wannan tsarin na auratayya ne. Allah ya zaɓa mana ya zama hanyar da zamuyi ta haife-haife muyi ta karuwa a bayan ƙasa. Domin shi aure wata muhimmiyar igiyace wadda idan aka ƙullashi zai bawa ma'aurata daman saduwa tsakaninsu ba tare da wata ƙyama ba, kuma ta hakane ma'aurata zasu zama sutura ga junansu kamar yadda Allah maɗaukakin sarki ya faɗa a Suratul Baƙara aya ta 187:- "Su mata suturane gareku maza, sannan kuma maza sutura ne garesu-su matan. Saboda haka zamu tabbatar lallai akwai al'ƙawari da amana mai ƙarfi a tsakanin ma'aurata, kuma Allah ya al'barkaci aure kuma yana son tabbatarsa , yana kuma ƙin ɓacinsa ba tare kwakkwaran larura ba. Shi aure sunnace daga cikin sunnonin da ɗan Adam ya sami kansa a ciki, sannan kuma larurace daga cikin larurorin rayuwar ɗan Adam domin da aurene mutun zai kiyaye dangantakarsa, kuma ya ƙididdige ƴaƴansa wanda ya haifa kuma da shine zai kiyaye mutuncinsa, martabarsa dama dukkan dangantakarsa ga sauran ƴan uwansa da jama'a baki ɗaya kamar yadda Allah (S.W.A) ya faɗa a Suratul Furƙan aya ta 54:- ( WA HUWALLAZII KHALAƘA MINAL MAA'I BASHARAN FAJA ALUHU NASABAN WA SIRRAN WA KANA RABBUKA ƘADIIRA) "Kusani Allah shine wanda ya halicci mutun daga ruwa kuma mai dangantaka surukuta kuma ka sani Allah mai iko ne akan haka". Sassanyan numfashi ya fesar a hankali, kana yaci gaba da cewa. "Shi Aure sunna ne mai samar da nitsuwa tsakanin ma'aurata. Ɗan Adam bazai samu cikekkiyar nitsuwa ba a gidansa ba, sai in har yanada mata wacce ya aura. Domin zata ɗebe masa kewa ta sashi ya samu nitsuwar hankalinsa. Saboda zamansu tare a inuwar aure zatayi masa maganin kaɗaici kamar yadda Allah (S.W.A) ya faɗi a Suratul Rum aya ta 21:- (WA MIN AYATIHI AN KHALAKA LAKUM MIN AMFUSIKUM AZWAJAN LITASKUNUW ILAIHA WA JA'ALA BAINAKUM MA'WADDATAN WA RAHMA INNA FII ZALIKA LA AAYAATIN LIKAUMIN YATAFAKKARUN) ma'ana. Yana daga cikin ayoyin Allah mai girma da ya halitta mana mataye daga kawunan mu, mataye da muke aure da su. Domin su samu nitsuwa da junansu, sannan kuma ya sama musu soyayya a tsakanin su, tare rahama da tausayawa juna lallai a cikin wannan al'amari akwai ayoyi abin lura ga jama'an da suke masu tunani. Saboda haka idan muka dubi wannan ayar ga ma'aurata zamu gane girman kudirar Allah da hikimarsa mai girma da ya halicci maza da mata kuma ya sanya ko wanne sashi mai karkata ga junansu kuma ya sanya igiya ya ɗaure tsakaninsu, wannan igiyar kuwa itace soyayya da tausayin juna da jinƙai. Kuma Annabi (S.A.W) ya ce, cikin hadisin da Ibnu Majah ya ruwaito cewa. (Babu wata fa'ida da mutun zai samu bayan ya. Takawar da Allah (tsoron Allah) wanda yafi masa al'khairi fiye da ya samu salihar mata ta kwarai wanda idan ya umarceta da tayi masa abu zata yi masa biyayya idan ya dubeta ta faranta masa ransa idan yayi rantsuwa game ita akan zatayi abu kaza ko bazata aikata abu kaza ba, zata kuɓutar dashi akan wannan rantsuwar da yayi, idan baya gida baya tare da ita, zata kiyaye mutuncinsa (Bazata yi fasiƙanci ba) kuma zata kula da dukiyarsa. Ku duba cikin Fikihul Wadi littafin Dr Muhammad B Isma'il shafi na 9 zaku sami wannan hadisin. A hankali Haroon ya ɗan juyo ya kalli fuskar amaryarshi Jannart, hannunshi yasa ta ƙasa table ɗin dake gabansu, tafin hannunta ya haɗe da nashi, tare da ɗan ronƙofowa kaɗan kana yace. "Kina ji da kyau dai ko?". Cikin lumshe ido tace. "Sosai ma kuwa". Aysha dake gefensu Haroon ya kalla tare da cewa. "Al Sheƙiya matar Sheykh, ko zakije ki ja mishi baƙine?". Ido ta ɗan sunkuyar tare da fidda nannauyan numfashi kana a hankali tace. "Ba dan gefen can da tarin maza manya iyaye da kakanni da sarakuna ba, tabbas da naje na zauna gefenshi na ja mishi baƙi". Safiyyah da Ibrahim dake bisa kujerun dake gefensu ne suka kalli juna tare da yin murmushi. Abokan Haroon kuwa gaba ɗaya sun nitsu. Abbansu Haroon da tawagarsa kuwa sai jinjina kai suke alamun gamsu ɗari bisa ɗari. Ita kuwa Aysha a hankali ta ɗago kanta ta kalli inda yake, aikuwa karab idonsu ya haɗe cikin na juna, taɓe laɓɓansa yayi tare dasa hannunshi ya shafi tattausan sajenshi kana a nitse yaci gaba da cewa. "Aure kariya ce, kuma GARKUWA ce ga Musulmi saboda duk wanda yakeda mata, to ba zaka ganshi ya bar gida yana yawace-yawace ba ko ka ganshi yana leƙe-leƙe a woje ba, don yana da irinsa a gidansa, saboda haka mata ta zama GARKUWA a rayuwar ɗan Adam. Saboda haka ne ma Annabi (S.A.W). Ya kwaɗaitar da matasa samari da yin aure a cikin wani hadisin da muka samu a cikin Fiƙhul waɗi littafi na 2 na Dr Muhammad B Isma'il shafi na tara, Annabi (S.A.W) ya ce:- Yaku samari wanda ya samu iko daga cikin ku to yayi aure. Domin shi aure yana kare mutuncin farji da aukuwa cikin haram, (Yin zina) wanda bai sami iko ba to lallai ne ya juri yin azumi. Domin assaumu junnatu, shi azumi GARKUWA ne. Kuma shi aure cikon addini ne, saboda idan muka dubi aure sosai. Zamu fahimci aure yana taimakawa musulmi wajen tsare-tsaren addininsa kuma da wannan ne addininsa yake cika kamar yadda. Dabarani da Hakim suka ruwaito daga Buhari da Muslim inda Manzon Allah (S.A.W) yake bamu labari a kan cewa aure tsari ne wanda yake taimakawa ga mutum ya cika addininsa a in da yake cewa: Yana daga cikin arzikin Allah. Allah ya azurtaka da mace salihan ko salihan mata, haƙiƙa zata taimaka ko wannan auren zai taimaka akan wani yanki na addini ka sai kuma kaji tsoron Allah akan sauran yankin. Aure sunnace ta Annabawa da manzanni, saboda haka idan kayi aure ko yi ne da Annabawa da manzannin Allah. Allah maɗaukakin sarki ya faɗi:- (WA LAKAD ARSALNA RUSULAN MIN ƘABLIKA WAJA'ALNA LAHUM AZWAJAN WA ZURRIYYAH) Haƙiƙa mun aiko manzanni kafin kai, (Muhammad, S.A.W) kuma mun sanya matayen aure da zuriya a garesu. Idan muka duba zamuga cewa yin aure koyi ne da aikin Annabinmu Muhammad (S.A.W) ne in da yace:- (Kuyi aure ku yawaita domin ni zanyi alfahari da yawanku ranar lahira". Juyowa yayi ya fuskanci gefen taron maza, kana yaci gaba da cewa. "Kamar yadda muka sani cewa. Mace abokiyar zama ce kuma shimfiɗa ce ga mijinta kuma mai rainon gidansa ce kuma abokiyar rayuwarsa ce, sannan kuma uwar ƴaƴansa ce sannan mai kula da dukiyarsa ce da mutuncinsa cikin amana saboda haka idan mata-ta zamo salihan ta gari to sai ta zamo kyakkyawan abu na duniya kuma ni'ima daga cikin manya-manyan ni'imomin da Allah ya azurtaka da ita". Gyaran murya yayi tare da gyara zamanshi, kana ya fuskanci Haroon da Jannart da kyau, sannan ya ɗan kalli Aysha da wutsiyar idonshi. Tura bakinta ta ɗanyi fahimtar ita yake kallo, kanshi ya jinjina kana ya buɗe muryarshi da ɗan ƙarfi dai-dai misali yadda amon mgnarsa zata ratsa kunnen kowa yace. HAƘƘOƘIN MA'AURATA GA JUNANSU. bari mu fara da haƙƙin macce akan mijinta. HAƘƘIN MATA A KAN MIJINTA. Haƙƙoƙin mata a kan mijinta suna da tarin yawa. Kuma ya zamo wajibi a kan mai gida ya tsareshi dai-dai gwargwadon hali, kuma wannan haƙƙoƙin Allah da Manzonsa sun tabbatar dashi, ga faɗin Allah madaukakin sarki akan haka inda yayi mgna cikin Suratul Baƙara aya ta 228:- (WALAHUNNA MISLULAZII ALAIHINNA BIL MA'ARUF WA LIRRIJALI ALAIHINNA DARAJAT) Mata sunada haƙki a kan mazansu kamar yadda aka sani. Sannan maza suna da wata daraja akan mata. Haƙƙokin mace a kan mijin ta, suna da yawa amman ga wasu daga cikinsu. (1) Wurin zama ga matar aure wajibi ne a kan mijinta. Miji zai tanadi wurin zaman matarsa gwargwadon ikonsa da samunsa kamar yadda Allah maɗaukakin sarki ya faɗa a cikin Suratul Ɗalak aya ta 6:- (ASKINU HUNNA MIN HAISU SAKANTUM MIN WUJIDIKIM WALA. TUDAARUHUNNA LITUDHAYYIKUM ALAIHIN) Ku zaunar da matanku inda kuke zaune wato gidajenku. Ba mummunan wurin zamaba kada ku cutar dasu don ƙuntata musu. (2) CIYARWA. Ciyarwa yana daga cikin abubuwan dake wajabta kan miji wato wajibi ne miji ya ciyar da matarsa, kuma ciyarwar zai yishi ne gwargwadon ikonsa kamar yadda Allah maɗaukakin sarki yace a cikin Suratul ɗalak aya ta (7). (LIYUN FIƘ ZUU SA'ATIH MIN SA'ATIH, WA MAN ƘUDIRA ALAIKU RIZKUHU FALYUNFIƘ MIMMA AATAHULLAH LAA YU KALLIFULLAHU NAFSAN ILLA MAA AATAHAA SAYAJA ALULLUHU BA'ADA USRIY YUSRAA). Ma'ana. Mawadaci sai ya ciyar da abinda Allah ya bashi na wadata, shi kuma wanda Allah ya ƙaranta masa arziƙinsa to sai ya ciyar daga abinda Allah ya bashi. Domin Allah baya ɗorawa bawa abinda bazai iyaba kuma ka sani Allah zai baka wadata bayan ƙuncin da ka shiga. Dangane da hadisin Annabi (A.S.W) yace a hadisin da a ka ruwaito daga mu'awiyya Bin Haidatu Allah ya ƙara masa yarda yace: Sai muka tambayi Manzon Allah (S.A.W) shin menene haƙƙin mata akan ɗaya daga cikinmu?. Annabi (S.A.W) ya ce. "Idan kaci abinci to ka ciyar da ita, idan ka ɗinka sutura to itama ka ɗin ka mata, sannan kuma in tayi maka laifi zaka bugeta, to kada ka bugeta a fuskarta kada ka munanata, idan zaka ƙaurace mata to kada ka ƙaurace mata a woje sai dai a ɗaki." (3) Kyakkyawan mu'amala. Shi mu'amala mai kyau babban abune ga ma'aurata. Especially shi miji, yana daga cikin haƙƙin mace akan mijinta, yayi mu'amala mai kyau da sakin fuska a tsakaninsu, raha da barkwanci ta yadda zasu shaƙu da junansu. Lallai waɗannan muhimman abubuwane da miji zai kiyaye su, kuma wajibi ne miji ya yawaita nasihi da wa'azi ga matarsa a kan harkar addini da sauran al'amuran yau da kullum sai dai a kula wurin nasihar da wa'azin kada ka tsananta kuma kada ka sake kwarai sabida sani yadda mata suke murɗaɗɗune sai anyi da lura. Duba da wani hadisin da Annabi (S.A.W) yana cewa a cikin hadisin da aka samo daga Abu Huraira inda yake cewa. Manzon Allah (S.A.W) yace: "Mafi cikar mumini a wajen imani shine wanda ya fiku kekkyawan ɗabi'a kuma zaɓaɓɓe a cikinsu shine wanda yafi Kyakkyawar mu'amala da iyalinsa. A wani hadisin kuma yace. Lallai ku sani cewa an halicci ƴa mace da ƙashin haƙarƙari ne bazata taɓa miƙewa gareka ba, wato ka sameta sak ba matsala, wannan kam bazai taɓa samuwaba in ka samu jin daɗinta to zaka samu jin daɗin ta ne a ƙarƙashin yadda take, (kuma ka sani in ka nemi miƙar da ita to tabbas zata karye. Karyewarta kuwa shine SAKINTA saboda haka sai kuyi taka tsan-tsan acikin lamuran." Gyara zamanshi yayi da kyau, kana yasa hannunshi ya gyara gilashin fuskarshi da kyau, Sannan ya sa hannunshi zai ɗauki goran ruwan dake gabanshi. Da sauri ɗan agajin dake bayanshi ya ɗauki gorar kana ya buɗe ya tsiyaya mishi sassayan ruwan cikin kofi, kana ya miƙa mishi sannan ya koma inda yake ya tsaya. Amsa yayi yasha ruwan sosai kana ya ajiye cup ɗin. Sunkuyar da kanshi yayi sosai sannan yasa hannunshi ya gyara hiraminshi ya rufe gefe da gefen fuskarshi. Al'ummar jama'ar dake wurin kuwa kan sun nitsu sunyi shiru maza da mata manya da yara. Kab an zuba mishi idanu alamun ana dakonshi yaci gaba. Domin sosai walimar tayi armishi sabida dace da tayi da fasihin malami. Shiru kakeji sai sauti A\C dana numfarfashi. Aysha kuwa haka nan take jin wani irin mashahurin daɗi. Gaba ɗaya tsikar jikinta tashi takeyi, tana jin Allah yayi mata babban rahama da ni'imar duniya da bata Sheykh Jabeer a matsayin Garkuwan ta mijinta. Da sauri ta ɗago kanta ta kalleshi lokacin da yaji yace. (4) SADUWA DA ITA. Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300. 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa. Ta nan zaki turo kuɗin, sai screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* Littafin nan na kuɗine, akwai Normal group 300 a wata biyu za'a kare Part 1 and 2, kiyi transfer'n dari uku ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276. In Kuma special Group kikeso wanda a wata ɗaya za'a gama Part one, two. 1k zaki turo ta ac no ɗin nan 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number da nake whatsapp dashi 09097853276. Akwai kayan gyaɗa na amareni uwar gidaye sitin hawa-hawa ne, akwai na dedai talaka akwai na masu hannu da shuni, in kina buƙatar saya kimin mgn ta whatsapp 09097853276. Idonshi ya ɗan lumshe kana ya ɗanyi ƙasa da kanshi cikin nitsuwa yaci gaba da cewa. "Anan ana son miji ya dinga yin jima'i (Saduwa) da matarsa ko da sau ɗaya ne a cikin ko wanne tsarki ta, na Al'ada amman ƙaranci kada ya wuce wata huɗu ba tare da ya sadu da itaba kamar yadda wasu malamai suka faɗa, in bazai iya biya mata buƙatarta ba, kuma wannan za'a kauwacewa al'amarin jima'i kamar yadda al'ƙur'ani mai girma yace. (Allah yayi mgna game da mazajen da suke barin matansu basu kula su har tsawon wata huɗu kai harma suna ƙarawa da rantsuwa bazasu tara (Sadu) da suba, to idan daga baya sun dawo ga iyalan nan to shike nan Allah mai gafara ne mai jinƙai. Saboda haka idan muka dubi wannan ayar zamu fahimci cewa, idan miji ya bar matarsa tsawon wata huɗu bai sadu da itaba haka nan kawai ba tare da wani kyakkyawan dalili ba, to ya cuceta, kuma ana iya raba auren, Allah ya kiyaye. Sai na (5) kiyaye mutuncinta kishi a kanta yana daga cikin mu'amala mai kyau tsakanin miji da mata ya zama miji ya kiyaye mutuncin matarsa da yin kishi a kanta, saboda haka wajibi ne ga miji yayi kishin matarsa ya kareta daga dukkan abinda zai taɓa mutuncinta da martabarta da dukkan abinda yayi kama da hakan domin mumini mai kishin gidansa ne, kamar yadda. Dabarani ya ruwaito daga Ammar Ɗan Yasir Allah ya ƙara musu yarda, cewa Manzon Allah (S.A.W) yace. Mutane uku bazasu shiga aljanna ba, 1 wanda baya kishin iyalansa 2 macen da take shigar maza, 3 wanda bai damuwa akan kowa da kowa ya shiga wajen iyalinsa. Sai Sahabbai suka tambayi Annabi (S.A.W) suka ce,. Ya manzon Allah shin dai bugegge sun san shi, to amman (Addayyus) wato mara kishi iyalinsa shine bamu sanshi ba. Sai Manzon Allah (S.A.W) yace musu. Shine wanda bai damuwa kowa da kowa kare da doki su shiga gidansa wato mutumin banza da wofi idan sun shiga gidansa baya damuwa. Shi wannan hadisin ya nuna mana cewa dole mu tsare mutuncin matanmu. Wannan kenan sune kaɗan daga haƙin mata akan mijinta. Sai kuma haƙƙoƙin miji akan matarsa. (1) yin ɗa'a ga mijinta domin Allah ya faɗi a Suratul Baƙara aya ta 228. ( WA LIRRIJALI ALAIHINNA DARAJAH) Su maza sunada wata daraja a kan matansu. (2) Kula da dukiyarsa wajibi ne a kanki haƙƙine wanda ya zama dole mata su kiyayeshi Dole mace ta kula da dukiyar mijinta fiye da yadda shi zai kula dashi. Kamar yadda Allah Mai girma da ɗaukaka ya faɗa a Suratul Nisa'i aya ta 34. (FASSALIHATU ƘAANITAATUN HAAFIZAATUN LILGAIBI BIMA HAFIZALLAH) Allah ya ambaci salihai mata masu ɗa'a ga mazajensu masu tsoron Allah masu kiyaye abinda ke ɓoye na al'amuran mazan aurensu sobada Allah yace su kiyayeshi, kiyayewar kuma ta haɗa da tsare mutuncin kansu dana mijinsu ko yana nan ko baya nan. (3) Yiwa miji hidimar cikin gida kamarsu girki shara kula da yara da dai sauransu duk aikin macene. Kamar yadda Allah maɗaukakin sarki yace. (WALAHUNNA MISLULLAZZI ALAYHINNA BIL MA'ARUF) Mata suna da haƙƙi a kan mazansu kamar yadda suma maza sukeda haƙƙin a kan matansu. (4) ikon canza mata wurin zama daga wannan garin zuwa wancan gari. Kamar yana aiki a jihar Ɓadamaya sai aka canza masa wurin aiki zuwa Tsinako to yana ikon ɗaukarta daga can zuwa nan. Domin musulunci ya bashi dama kamar yadda Allah maɗaukakin sarki yace. (ASKINU HUNNA MIN HAISU SAKANTUM MIN WUJDIKUM WALA TU DARRUWHUNNA LITUDAYYIƘUN ALAIYHIN) ku zauna dasu inda kuke kada ku cucesu ku ƙuntata musu wajen zama. Idan muka dubi wannan ayar tana gargaɗin mazaje ne akan cewa kada ka sauya mata garin zuwa wani garin ya zama cutarwa a gareta. In taga cutarwa ne nan zata iya ƙin zuwa in ya matsa ta gayawa waliyansu. (5) kada mace ta shigo da wani mutun gidansu sai da izinin mijinta, domin wannan haƙƙine kuma damarsa ce. Numfashi ya sauƙe tare da kallon taron mazan kana yaci gaba da cewa. "A gurguje. (6) Neman izinin miji dan yin azumi. Baya halasta ga mace tayi azumi in dai na nafila ne sai tare da izinin mijinta matukar mijinnan yana gida tare da ita. Duba haɗisin daya gabata na haƙƙin maigida saboda haka ya zama dole mace ta nemi izinin mijinta kafin tayi azumi nafila amman banda na farillah". Haroon ne yayi wani irin murmushin jin daɗi kana ya kalli Jannart cikin raɗa yace. "Kinaji kina ɗauka kina fahimta ko?". Longoɓar da kai tayi. Umaymah kuwa sai murmushi takeyi tana ƙara godewa Allah da samun Sheykh a ahlinsu. Mamma ma sai murmushi takeyi. Jamil Jalal Azeez da Sadiq da Imran ne suka ɗan haɗe kansu suna ƴar hira ƙasa-ƙasa. Da sauri suka ɗago kansu jin muryar Sheykh yana cewa. "Jamil ku fita waje kuna toshewa jama'a kunne". Cike da mamaki suka miƙe suna kallonshi suna al'ajabin ya akayi ya gane su kuma har yaji muryarsu. "Ku fita". Suka sake jin muryarsa, cikin tuttura baki suka fita. Aysha kuwa tafin hannunta tasa ta tallabe haɓarta, tare da zuba mishi ido cikin wani abinda bata san sahihancinsa ba, take kallon tattausan lips ɗinshi suna motsawa yana mai ci gaba da cewa. Kanshi ya sunkuyar sosai, babu mai iya ganin kwayar idanunshi cikin tarin al'kunya yace. "Haƙƙin jima'i haƙƙine wanda yake tsakanin miji da mata. Amman ƙarfin haƙƙin yafine gashi mijin, shi yake da haƙƙi mafi girma. Kuma shi wannan jima'in yana daga cikin manufofin aure, domin shi aure shi yake tabbatar da mutane su wanzu, su tabbata akan ma'aunin mutane su ba nau'in dabbobi ba. Domin shi dabba duk lokacin daya buƙaci biyan buƙata yin jima'i zai tare dabba mace ƴar uwarsa ne a hanya nan take ya biya buƙatarsa ya rabu da ita, kamar yadda muke gani a tsakaninsu yana faruwa. Shiyasa duk mazinaci bashi da banbanci da Dabba!. Jima'i babban al'amari ne cikin auratayya, domin biyawa kowa buƙatar sa, kana jima'i wata iriyar sutura ce wadda ma'aurata suke suturce junansu, kamar dai yadda Allah maɗaukakin sarki yace a cikin suratul baƙara aya ta 187:- (UHILLA LAKUM LAILATASSIYAMIRRAFASA ILAA NISA'A IKUM HUNNA LIBAASULLAKUM WA'ANTUM LIBAASULLAKUM) A halasta muku matanyenku kuyi jima'i dasu a dararen Azumi, domin su mata sutura ne a gareku, kuma suturce a garesu." Ɗan ɗago kwayar idanunshi yayi ya fuskanceta Aysha, kollon kwayar idanunta data zuba mishi yayi na ƴan wasu daƙiƙu kana yaci gaba da cewa. "A wata ayar Allah maɗaukakin sarki ya siffanta mata da cewa gonakine a garemu maza, ku zowa gonakinku a duk lokacin da kuke so. Ayar itace. (NISA'UKUM HARSULLAKUM FA'ATUN HARSUKUM ANNAA SHI'ITUM) Matanku gonakinku ne ku zowa gonakinku a duk sanda kuke so". Haroon ne ya ɗan matse hannun Jannart dake cikin nashi kana ya ɗan juyo ya kalleta. yana wani ja'irim murmushi. Shi kuwa Sheykh gyara zamanshi yayi tare da ƙanƙance kwayar idanunshi ya watsasu cikin manyan idanun Aysha ya tsareta dasu. harshenshi ya ɗan turo woje ya ɗan lasi lips ɗin shi kana yaci gaba da cewa. "Kamar yadda aka faɗa shi jima'i Saduwa haƙkine ga kowa wanne ɗaya daga cikin mauratan, hakan ya sanya ya zamo wajibi ga mace lallai ne dole ta bada haɗin kai a duk lokacin da mijinta ya nemeta da jima'i matuƙar dai bata cikin haila ko jinin biƙi ko kuma da rana cikin watan Ramadan. Ko tana cikin wani uzurin wanda zai iya hanata biya mishi buƙatar sa. Uzurin kuma ya zama na Shari'a yardajjen kamar rashin lafiya mai tsanani. To in ba waɗannan uzurorinba babu wani dalilin da zai sa mace taƙi bada haɗin kai ta biyawa mijinta buƙatar sa. In kuwa taƙi bashi haɗin kai da son ranta, to zata haɗu da tsinuwar mala'ikun Allah kamar yadda yazo a hadisin Bukhari da Muslim wanda ke cikin. Minhaju Muslim shafi na 380 sun ruwaito daga Annabi (S.A.W) yace. ( Idan miji ya kira matarsa zuwa shimfiɗarsa don yin buƙatar sa, Saduwa da ita, sai taƙi yarda ta bashi haɗin kai, sakamakon hakan sai mijin ya kwana cikin fushi da baƙin cikin hakan da tayi mishi. To Mala'ikun Allah zasuyi ta sinemata har sai gari ya waye. Lallai ne mace ta sani mijinta yana da ikon biya buƙatarsa da ita a duk lokacin da yaso hakan." Juyowa yayi ya fuskanci mazan da kyau kana kwayar idanunshi a sunkuye yace. "Haƙƙin mace kuwa a kan jima'i malamai sun karkasu kan wannan hukuncin kamar haka. 1 Mafiya yawan malamai suna ganin wajibi ne ga miji ya biyawa matarsa buƙatar ta jima'i a duk sanda ta nema. Domin yin hakan yana cikin kekkyawan zamantakewa kamar yadda Allah maɗaukakin sarki ya yi umarni dashi inda yace. (WA'ASHIRU HUNNA BIL MA'ARUF) Kuyi musu kekkyawan zamantakewa babu cuta ba cutarwa. 2 Su kuma shafi'iyyah suna ganin cewa shi jima'i haƙƙin mijine sabado haka baza'a tilasta shi yayi dole ba. 3 Hanabila kuwa suna ganin cewa. Baya halasta miji yaƙi yin jima'i da matarsa fiye da wata huɗu. Saboda haka wajibi ne miji ya sadu da matarsa cikin ko wanne wata huɗu. 4 Ibn Hamza yana cewa wajibi ne miji ya sadu da matarsa cikin ko wanne tsarkin hailan da tayi. Matuƙar yanada halin yin hakan, domin yin hakan shine mafi ƙarancin tarawa da zaiyi da ita. Amman a karan kaina a fahimtata ni dai Muhammad nafi nitsuwa dana forkon nan wanda mafiya yawan malamai suka yarda dashi matuƙar yana da ikon yin haka, ya biya mata buƙatarta duk sanda ta nemeshi, domin yin hakan shine zai kiyaye mutuncinta da addininta kamar yadda Musulunci ya umarceshi da ya yi". Numfashi ya ɗan fesar kana cikin nitsuwa yace. "A gaggauce ga laduban jima'i. Wasu abubune wanda ake buƙatar aikatasu lokacin da mata da miji sukayi nufin saduwa. Jima'i da junansu, idan ka aikata waɗannan abubuwan zaka ƙara samun lada a wannan ibadar saduwar da zakiyi, amman kuma in baka aikata ba, bakayi zunubi ba,sai dai kayi asarar wannan ladan wanda aka tanada domin waɗanda suka aikata waɗannan abubuwan wojen koyi da sunnar Annabi Sallallahu alaihi Wasallama. Domin su waɗannan laduban Sunnah ce da. Masu yawa amman ga kaɗan daga ciki: (1) Addu'a ana son miji idan zai sadu da matarsa yace. "BISMILLAH ya kuma yi addu'a to idan yayi hakan yayi abinda ake so aiki da ladabi kamar yadda yazo a Hadisin Bukhari da Muslim, Tirmiziy Ibn Majah, Abu Dauda suka ruwaito Hadisin Abdullahi ɗan Abbas cewa. Manzon Allah (S.A.W) yace. Da ace ko wanne ɗayanku lokacin da zai zowa matarsa yin jima'i zai ce. (BISMILLAH ALLAHUMMA JANNIBAL SHAIƊAN WA JANNIBAL SHAIƊANA MARAZAƘTUNA) to idan Allah ya ƙaddara samun ɗa a wannan saduwar to shaiɗan bazai cutar da wannan abinda za'a haifaba har abada. Saboda haka ya kamata duk mijin da zai sadu da matarsa ya kiyaye wannan, in kuma kinga mijinki shagalellene ke mace kike tunasar dashi. Dan samuwa ya'yan da zaku haifa kariyar Allah. 2 Wasanni kafin jima'i. Yin wasanni gabanin jima'i domin samun cikekken jin daɗi, kamar yadda aka ruwaito. Daga Annabi (S.A.W). "Kada ku aukawa iyalanku da gaggawa, har sai wani abu na sha'awa ya fito musu, irin wanda ya fito maka, domin kada ka rigata yin inzali fidda manniyi. Sai wani daga cikin Sahabbai sukayi tammabaya. "Shin wannan jin daɗin mata daga gareni ne? Ma'ana Ni zan sa taji daɗin. Sai yace, Na'am zaka sata taji daɗi ne ta hanyar sumbatarta haɗa baki da baki ruggumarta da abinda yayi kama da haka. Idan kaga wani abu ya zo mata, na ruwan maniyyi irin wanda yazo maka, daga nan sai ka sadu da ita. 3 Tanadar kyalle domin goge maniyyi. 4 Kada ayi jima'i tsirara. 5 Yin al'wala idan zaka sake mai-maita na biyu ko na uku, ko fiye da haka." Ɗan tsagaitawa yayi ya kalli hadimai mata dake ta jere ababen ci da sha akan ko wanne table yawan adadin mutanen dake zagaye da table ɗin yawan abubuwan da ake ajiyewa. Idonshi ya ɗan juyo ya kalli gefen maza. Nanma hadimai mazane keta jera abubuwan cin da na sha, kana. Ta gaba gaba kuma wurin VIP sukuma Jamil, Jalal, Azeez Sadiq sune suke ta jerawa. Kanshi ya gyaɗa alamun gamsuwa da tsarin domin anyi komai cikin tsari da wadata da karamci da girma cikin nitsuwa mutane suka fara ci da sha. Gyaran murya ya ɗan yi kana yace. "Abubuwan da aka haramta game da jima'i. 1 Jinin haila, da biƙi 2 jima'i ta dubura 3 Bayyana sirrin jima'i." Murmushi ya ɗan yi ganin mafi akasarin mutane sun fara hidimar ɗa'amu. Ajiyar zuciya ya sauƙe ganin tuni har goma na dare ta gota, babu wanda ya Ankara, alamun tabsirin walimar yayi zaƙi kenan. Numfashi ya sauƙe kana ya ɗaga hannun alamar addu'an rufe taron yace. "Subahanakallamumma wabi hamdika asshahadu alla'illaha illa anta astagafirukka wa'atubu illaik Allahumma salli ala muhammad wa ala ali Muhammad kama sallaita ala ibrahima wa barik ala muhammad wa ala ali Muhammad kama barakkata ala Ibrahim wa ala ali Ibrahim inna ka hamidul majid. Ya Allah ka meda kowa gidansa lfy yan nesa dana kusa. Allah ka bawa ma'aurata zaman lfy ka sanya al'khairi a rayuwarmu, ka azurta dukkan ɗan uwa Musulmi da ƴaƴa na gari." "Ameeeeeeen". Haka hall ɗin ya ɗauka. Hadimai kuwa tuni sunci gaba da raba jakukkunan kyautar walima. Gefen maza, Sallaya da al'ƙur'ani da carbi da jallabiya da turare akasa a cikin ko wacce jaka da take ɗauke da hoton Haroon, Sheykh, Jannart Aysha. Turaren irin mai tsadar gaskenan ne. Hakama jallabiyar, ko dan sanin taron na manya ne. A gefen mata kuwa, Shima sallaya ce da ƙur'ani da carbi da turare da manya-manya hijabai bibbiyu cikin ko wacce jaka. Haka akayi ta rabawa. Cike da Mamaki Umaymah ta kalli Hibba da Azeema da Safiyyah da Jazrah da suke ta rabawa, kamo hannun Safiyyah tayi tare da cewa. "Ke Safiyyah wannan fa, yanzu na kira hadimai akan suzo su fara raba kyautukan da muka shirya." Murmushi Safiyyah tayi kana tace. "Eh gasu can suma sun fara wannan kuma kyautar Sheykh ne. Dama tun jiya yace mu raba da kanmu mu kuma tabbatar kowa ya samu. Gefen maza ma gacan su Jalal na rabawa". Wani irin murmushi mai cike da jin daɗi tayi kana ta jinjina kai. Ita kuwa Safiyyah sukaci gaba da rabiya. Suma hadimai suka zo suka fara nasu rabiyar. Gyaran muryar da Sheykh yayine ya jawo hankalinsu gareshi. Cikin rauni murya a sanyaye yace. "Ƴan uwana ina neman addu'o'in ku, inada wata buƙata mai girma da nake nema wurin ubangijina kuma mai sauƙine in ya lamunce min. Na roƙeku al'farmar Annabi da Alqur'ani ku sani addu'o'in ku Allah ya biya min buƙatata". Kusan a tare duk hall ya ɗauki. "In sha Allah, Allah ya biya maka buƙatar ka". Amin Amin yace. (Kana nima Aysha Aliyu Garkuwa, inada buƙata wurin ubangijina fans ku tayani roƙo dan Allah, Allah ya cika min buƙata.) Daga nan manyan mutane duk suka mimmiƙe suka fita. Nan kowa da kowa ma ya fara fita. Haka motoci sukayi ta ɗibar mutane suna wucewa dasu gida. Safiyyah, Ibrahim, Haroon Jannart, duk tare suka miƙe suka fita. Bayan suna fita Haroon yaja hannun Jannart suka shiga Mota. Ibrahim ma da Safiyyah motarsu suka nufa, cikin kula Safiyyah ta kalli Aysha dake gefenta tace. "Yah Sheykh bai fito ba ko". Ibrahim ne ya amshi zancen da cewa. "Eh ya tsaya yana gaisawa da Abokan Abbanshi ne. Bari in amso key ɗin motarshi sai ta jirashi a ciki kafin ya fito ko". Eh Safiyyah tace, kana ya juya ya koma ciki. Ita kuwa Aysha ɗan numfashin gajiya ta sauƙe tare da bin motarsu Umaymah da aminanta da ido kana tace. "To wai dole sai dashi zan tafine? Mu tafi kawai mana in dai ba rowar motar taku zakuyi min ba gashi kowa ya tafi sai mu kaɗai". Murmushi Safiyyah tayi tare da kamo hannunta ta ja suka jingina da motar Sheykh cikin raha tace. "Eh gsky rowar motar mu zamuyi miki, haka kawai zaki hanamu sakewa bayan kema ga motar naki mijin. Gsky ki jirashi ya fito ku tafi, dan wlh ya Ibrahim yace haƙurinshi ya ƙare daga nan hotel muka nufa". Ta buɗi baki zatayi mgna kenan Ibrahim ya iso da car key a hannunshi. Sa key ɗin yayi ya murza ƙofar ya buɗe kana yace. "Yauwa shiga nan ki jirashi yana nan fitowa". To tace a sanyaye kana ta juyo ta kalli Safiyyah daketa kerkerar barbara tace. "Allah kuwa tsoro nakeji sai inji zuciyata na tsinkewa". Murmushi Safiyyah tayi kana tace. "Wlh ba komai keda gaki ga GARKUWAR ki to me zai firgitaki". Kai ta jinjina kana tasa kai ta shiga, gefen mai zaman banza. shi kuwa Ibrahim key ɗin ya saka a mazauninshi a cikin motar kana yaja hannun Safiyyah yace. "Kinga mu tafi". To Safiyyah tace kana ta juya tabi bayanshi, tana cewa Aysha saida safe. Murmushi Aysha tayi kana ta bisu da ido, har motarsu ta fita ta bar harabar wurin. A hankali ta sauƙe ajiyan zuciya, kana ta juya ta kalli gefe da gefenta, Sam babu kowa a wurin sai hasken wuta tako ina sai inuwar fulawi da dogayen bishiyoyin namijjn gwanda. Da kuma inuwar motocin da suka ɗan rage wanda basu wuce biyar ba. Dan sam babu motsin kowa da komai. A hankali ta ɗan juya kanta gefe tana jiyo ɗan sautin kukan tsuntsaye su Sheykh da suke ciki kuwa sam ko muryarsu bata iya jiyowa gashi tsaka ninta da masu gadima tafiyace mai zaman kanta, fadawan kuwa suna ciki wurin ubanin gidajen nasu. A hankali yasa hannunshin ya buɗe marfin motar, gefen drever cikin Sa'a kuwa ƙofar ta buɗu. Da sauri Aysha ta juyo jin an buɗe ƙofar, cikin sauri da tsoro ta zaro idonta ta kalleshi tsaye cikin kaɗuwa da tsoro tace. "Waye ne kai?". Cikin wani irin masifeffen murmushi mai cike da ma'anoni yace. "Jahan ɗinki ne". Ya ƙarashe mgnar yana gyara zamanshi bisa kujerar, kana ya jawo marfin motar ya rufe gib. Cikin tsananin azabar tsoro, firgici, kaɗuwa, cike da rawan jiki tasa hannun ta kama ma buɗin marfin motar da niyar zata buɗe motar. Kit kit taji alamun an datse marafen motar gaba ɗaya basu taɓa buɗuwa ba, sai in har an buɗesu daga gaba wurin zaman driver. Cikin tsananin tashin hankali tace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun ka buɗe min ƙofa bana so, wayyo Yah Sheykh! Ya Sheykh!! Ya Shey.." Da sauri ta fizge hannunta da ƙarfi jin yasa hannunshi ya kamo nata hannun, hankali a tashe ta fara bubbuga glass ɗin shegiyar motar da ko bindiga bazai fasashi ba. sam babu mai jinta ko kaɗan. Shi kuwa Jahan cikin wani irin ja'irin murmushi mai tarin manufofi yasa hannunshi ya fizgota, ta abka jikinshi, bisa ƙirjinshi yasata. Cikin muryar kuka da tsoro tace. "Wayyo Allah na! Wayyo Bappa na, Wayyo Ummey na, Jahan kaji tsoron Allah ka sani ni matar aurece, ka rufa min asiri kada ka tozartani ka wulaƙanta min aurena. Kaji tausayina ka barmin mutuncina dana mijina kada ka keta mishi haddin matarshi, bana so!.". Ta ƙarashe mgnar da azaban ƙarfi da kuma kuka mai ƙaƙƙarfan sauti, sai dai babu mai jinta bare ya a gaza mata. Kiciniya takeyi da iya kar ƙarfinta take tuttureshi da fiffizgewa tana kuka hawaye har bisa gemunta. Shi kuwa Jahan wani irin masifeffen dogon ajiyan numfashin ya sauƙe tare dasa hannun yana shafa haɓarta. Wani irin gigitaccen cizo ta datsa mishi a ƙirjinshi. wanda yasa dole ya saketa. Yana cewa. "La la la kika cijeni Allah zai ƙonaki fa Aish". Dabbas da tana cikin nitsuwarta da yaci da fahimci da wanne suna ya kirata, sunan da tasan mutun ɗaya ke kiranta dashi. Muryar kuma ta fito sak muryarshi da yake ɓoye mata. Da sauri ta koma kan kujerar da take tun fari, kana taci gaba da bubbuga glass ɗin motar da iyakar ƙarfinta tana cewa. "Ya Sheykh! Ya Sheykh!! Ya Muhammad!". Cikin tsoro da gigita ta juyo gareshi. Jin ya danna wani abu kujerar ta koma baya ta konta. Itama ta koma baya ta konta bisa kujerar, da sauri ta yunƙura zata taso kenan. Taji yayi mata rumfa da ƙirjinshi ya kwanto kan, tare da cewa. "Ihunki da buge-bugen ki duk na banza ne babu mai jinki. Shi wannan Yah Sheykh da kike ta kira da bai ba gashi ba. Naga kamar bai ɗaukekj ƴa macebanw me ruwanshi dake, ki bari in medaki cikekkiyar mace, kisan me ake nufi da aure kiji daɗin da ma'aurata keji, mutumin da kona kusanceki ba ganewa zaiba." Cikin fiffizgewa tace. "Wa iyazubillah Allah ya tsareni, fasiƙi azzalumi kaji tausayi na ka barni ka bar hurumin mijina". Wani irin masifeffen karkarwa jikinta ya farayi numfashinta na sama da ƙasa lokacin da taji yasa hannunshi ta cikin wuyan rigarta ya damƙi breast ɗinta kana ya gyara zamanshi kan cinyoyinta da kyau, tare da fara kwance igiyoyin dake sarƙafe gefen wuyan rigar ta kaɗanta ta dama. Hannayenta tasa tana kai mishi bugu yagushi. Cikin wani irin yanayi yasa hannunshi ya jawo hannayen nata, ya ajiyesu gefe da gefen cinyoyinta kana yasa guiwowinshi ya ɗan danne hannun nata yadda bazata iya zarosu ba kuma bazata ji zafiba. Wasu gigitattun hawaye masu masifar ɗumi ne suka kwaranyo mata tamkar an ɓalle bakin pampo. Shi kuwa Jahan ƙarasa kunce igiyoyin yayi, sai gashi wuyan rigar ya buɗu yayi faɗi sosai. Da sauri ya jawo wuyun rigar ta gaba ya zama rabin breast nata duk suna fili. Hannunshi na dama yasa cikin rigar ya cirosu cikin bra kana hankaɗosu sama suka fito woje suka tsaya tirsa-tirtsa suna tsaye sunyi tamtsan-tamtsan tamkar zasu tsole mishi kwayar idanunshi, wani irin yar, yar, yar, yaji tsikar jikinshi tana miƙewa tana zubawa. cikin wani irin zir-zir-zirrrrr yaji Jahan ɗinshi tanayi tamkar zata faso suturar dake jikinshi ta fito ta bindiga. Hannunshi yasa ya fara yi musu wani irin masifeffen tausa da murza. Yana sauƙe tagwayen numfarfashi tamkar zai shiɗe ya bar duniya. Yadda jikinta yake rawa hakama nashi yake karkarwa. Ita kuwa kuka takeyi har muryarta ta disashe sai dai duk da tashin hankali da take ciki, tana jiyo ƙamshin turaren jikinshi kamar na Yah Sheykh ne, sai dai tsoron ya hanata tantancewa, asalima sai tayi zaton ko dan a motarshi ne yasa take jin ƙamshinsa. Sai dai shima baya jinta dan ya tafi duniyar da babu kunne. Sunkuyowa yayi cikin buƙatuwa da manufarsa ya saita bakinshi da jajayen Caɓɓulenta cikin wani irin wutar fitina yasa lips ɗinshi kan n...! Littafin GARKUWA na kuɗine in bazaki iya biyan special Group ba a sauƙaƙe akwai Normal group 300 kacal By *GARKUWAR FULANI*[3/15, 9:56 PM] +234 806 559 0880: Cikin tashin, fargaba, tsoro, kiɗima, gigita, ta ɗago kanta da azaban ƙarfi lokacin data ga yana sunkuyo da bakinshi nufin zai mu'alamanceta tamkar mijin aurenta, kuka mai cike da tsaro ta saki, sai disashewar da muryarta tayi ta hana sautin fitowa fili. Wani irin karkarwa da tsuma jikinta ya farayi, wata azabebiyar zufa ta karyo mata lokacin da numfarfashi ya fara korar juna alamun zai ɗauke. Sam har ga Allah bai san takai wannan matakin tsorita da razanaba. Kana ganin ababen marmarinsa yasa ya mance a suffan waye ma yazo mata. Kanshi ya ɗago hango mutun ya fito cikin halla ɗin ya nufo harabar wurin motocin. Da sauri ya saketa, cikin abinda bai gaza second biyu ba, ya buɗe marfin motar ta gefen da take ya fita da sauri kana ya sunkuya, a sunkuye yabi inuwar motocin dake gefenshi. Ita kuwa Aysha ta gama gigicewa ta ɗimauce tana jiran taji ya tozarta mutuncinta da darajar aurenta wanda take fatan ta mutu yafiye mata. Jin an buɗe marfin motar ya kuma sauƙa kan cinyarta ne, yasa ta tashi cikin azama da gigita. Cikin tattaro sauran kuzarinta da buɗe muryarta take cewa. "Ya Sheykh! Ya Sheykh!! Ya Sheykh!!!". Tanayi tana gyara wuyan rigar tare da maida caɓɓullenta ta killacesu, sai dai duk tanayin abin a gigice ne kuma har lau numfashin ta na fuzga. "Ya Sheyyyyykh!." Ta kuma danna kiran da ƙarfi numfashin ta na fizgewa. Dai-dai lokacin kuma taji an buɗe marfin motar ta gefen driver, cikin tsananin zabura da kaɗuwa ta juyo a firgice. Shima Sheykh da yanzu ya iso wurin da sassarfa, da sauri yasa kai ya shiga cikin motar ba tare da ya ida shiga motarba ya zauna. Ita kuwa Aysha. Wani irin yunƙura tayi ta abko jikinsa da ƙarfi. Da sauru yasa hannunshi ya riƙe kujerar kana ya jawo marfin motar ya rufe da ƙarfi sabida jin da yayi yana baya alamun zai koma baya ya faɗi. Cikin mamaki da ɗaga murya yace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun, ke me hakan? Zaki kadamu fa!." Ina gaba ɗaya jikinta rawa tsuma karkarwa yakeyi tamkar mazari, cikin fizgar numfashin ganin tsira tace. "Ya Sheykh Jahan! Jahan!! Jahaaaaan!!!". Ta ƙarashe mgnar tare da shigewa jikinshi da kyau ta cusa kanta cikin ƙirjinshi, wanda yake bugawa dib-dib yana harba sama da sau ɗari a cikin ko wacce daƙiƙa. Yayinda nata ke harbawa samada sau ɗari da hamsin a cikin ko wanne daƙiƙa sabida tsananin tashin hankali da kiɗima da firgici. Cikin wani irin yanayi ya rumtse idanunshi da ƙarfi kana ya buɗesu da sauri, yayinda tuni suke jazir kana shima jikin nashi tsuma yakeyi. Hannunshi yasa ya ruggumeta gam-gam a jikinshi da kyau, al'kyabbar jikinshi ya ware da kyau ya buɗa ta kana ya rufeta dashi rib. Sabida yadda jikinta ke rawa abin ya zarta zaton mutun. Cikin wata iriyar murya mai cike da diriricewa tausayi rauni murya a sarƙafewa yace. "A'ich! A'ish!! Kiyi haƙuri I'm so sorry, in sha Allah bazan sakeba, ki yafe min kinji". Ina babu amsa sai ƙara cusa kanta da takeyi jikinshi bata kuma haiyacinta har yanzu bare ta fahimci me yake faɗin. Cikin taune lip ɗinsa na ƙasa yace. "A'ich ki nitsu ki kwantar da hankalinki babu abinda zai sameki. Kinji ba gani ba. Babu kowa da zai cutar dake da izinin Allah". Ina ita dai sai ƙara ƙwaƙumarshi takeyi. A hankali ya juyo ya kalli gefenshi jin ana ɗan ƙwanƙwas glass ɗin motar, Ƙasa yayi da glass ɗin. Ya Hashim ne da Affan da Jalal Imran da Sulaiman sai Kabir ƙanin su Haroon wanda suka haɗa uba, kuma a motarsa suke da kuma motar ɗaya Haroon dake hannun Jalal, kasan cewar bai sauƙe gilashin sosaiba, basa iya ganin Aysha dake kwance a jikinsa. Affan ne ya ɗan motse kana yace. "Ya Sheykh mufa gobe sammako zamuyi, shiyasa muke son key ɗin motar ya kwana a hannunmu". Kanshi ya jingina da jikin kujera kana ya kalli Ya Hashim da Sulaiman da Imran yace. "Ku bari sai jibi ku tafi, mana kunzo jiya, gobe kuce zaku koma ku dai bari jibi". Kai Sulaiman da Ya Hashim suka gyaɗa alamun yarda. daga nan suka juya suka nufi motar Kabir tare da cewa. "To sai da safe". Allah ya bamu al'khairi yace kana ya ɗaga glass ɗin. Su kuma suka shiga mota sukaja suka tafi. A can gida kuwa bayan duk sun watsa ruwa kowa yayi shirin baccine, sai kuma duk suka firfito falo suka kafa hira irin ta ƴan uwa in an haɗu a biki. Umaymah ce ta kalli Aunty Rahma dake kwance gefenta tayi pillow da cinyarta tace. "Wai ina Safiyyah da Aysha ne, su ban gansuba". Gyara konciyarta tayi tare da cewa. "Safiyyah dai tabi mijinta, ita kuma surkar tawa inaga itama suna tare da ɗan naki". Ummi ce ta ɗan kallesu tare da cewa. "Ai kuwa ni tun ɗazuma naketa kiranta bata ɗaya wayar". Mamma ce tace. "Halan suna can tare". Hajia Mama dake zaune gefen Umaymah ce ta ɗan kishiƙiɗa da tum-tum tace. "Uhummm". Daga nan bata kuma cewa komaiba. Ummi kuwa ci gaba da kiran Aysha tayi, wayar tana shiga amman ba'a ɗagawa. A can kuwa wurin Sheykh da Aysha. Gyara zamanshi yayi da kyau bayan, abokan Abbanshi duk sun tafi. Gyara mata zamanta a jikinshi yayi da kyau yadda bazata takurashi yin tuƙiba gaba ɗaya zuciyarshi a hautsine take, ya rasa gano wake tura mishi wasu pictures ɗin Shatu da mishi zantukan ita yar iskace. Allah ya sani baya zarginta ko wannan abun ya fara faruwa ne dan ta ganshi da kamanninsa na sirri, da fari tsiya yake mata, sai kuma yake jin dadin yanayin yakanyi ta murmushi in ya tuno tsoron da yake gani a kwayar idanunta, yana mmkin yadda take gaza gane muryarsa, to batun hotunanta fa da ake tura mishi da wani yanzu ya gama gamsuwa aiki magautansa ne. Ajiyar zuciya ya sauƙe mai nauyi tare da tada motar, A/C'nta ya kunna, sabida wata iriyar fitinenneyar zufar dake tsastsafo musu su duka biyun. Ƙafarshi ya murza ya kaita kan birki, lokacin da ya iso gab da bakin gate, ɗan tsayawa yayi aka buɗe musu gate ɗin, kana ya cilla hancin motarsa woje. Da hannun ɗaya yake murza siterin motar, hannun damanshi. Kana hannun hagunshi kuma na ruggume da ita. Zuwa yanzu yaji rawanda jikinta keyi ya fara tsagaitawa. Ita kuwa Aysha cib tayi a jikinshi tana jin yadda bugun zuciyarshin ke harbawa da sauri-sauri kana kuma da ƙarfi-ƙarfi. Tafiya mai tsawo sosai, har ya fara fitowa wojen gari. A hankali ya ratsa wani titin ya shiga, tafiya kaɗan yayi ya ratsa cikin wani tamfatsetsen hotel mai masifar kyau wanda yake killace a bayan gari, sabida manyan mutane ba kasafai suke son hotel ɗin dake sarari ba. Bayan ya gyara parking ya kashe motar. Ɗan sunkuyar da kanshi yayi kanta sannan a hankali yasa tafin hannunshi ya tallabo kanta, cikin sanyi ta buɗe idonta. Ta ɗan kalleshi kana ta medasu ta lumshe. Manyan yatsunshi yasa yana ɗan shafa kuma tunta dasu. Kana a hankali yace. "A'ish kiyi haƙuri kinji bazan sake yin nesa da keba". Sai kuma ya ɗanyi shiru kana ya kusanto da fuskarshi gareta sosai, a hankali ya hura mata iskar bakinshi kan idanunta tare da cewa. "Buɗe idon Yah Sheykh ɗinki ne, ba Jahan ba". A hankali ta buɗesu, ta kalleshi. Wani dogon nannauyan ajiyan zuciya ta sauƙe tare meda kanta saman ƙirjinshi". A hankali yace. "Wayyo Mamy zata karya min cinya, sauƙa muje ciki." Bata kulashi ba, ganin hakane yasa ya buɗe ƙofar kana ya ɗan mirginata gefe, sannan ya sauƙo. Gyara tsayuwarshi yayi tare da gyara hiraminshi ya rufe fuskarsa da kyau sannan yace. "Aish fito ko Boɗɗi". Da sauri ta zuro ƙafafuwanta woje sabida gani take yana matsawa Jahan zai zo. Marfin baya ya buɗe. Wasu ledodi masu kyau ya ɗauka kana ya rufe motar tako ina, sannan ya juya, ya nufi ciki da sauri ta bishi a baya. Tafiya kaɗan sukayi suka haɗu da Jamil. cikin sauri ya iso gabansu, key ya miƙa mishi tare da cewa. "Room number 37 VIP Side". Kai ya gyaɗa tare amsar key ɗin. "Sai da safe". Yace yana mai wucewa. "Allah ya bamu al'khairi yace kana. Suka wuce shima ya wuce. Suna shiga, ɗakin. A hankali ya miƙa mata ledodin. Sannan ya juyo ya rufe ƙofar, duk da yasa Jamil ya bincika masa ɗakin saida ya ƙara duba jikin ƙofar da makunnin fanka da A/C da kyau. Kana ya dawo tsakiyar ɗakin ya ɗaga kanshi sama ya kalli sanan sosai hakama ya shiga bathroom ya duba komai saida ya tabbatar ba komai daga cikin ababen da ya kamata duk musulmi in larurar zuwa hotel ya kamashi ya tabbatar da ya bincikesu da kyau Especially in ku mata da miji ne. Ita kuwa Aysha da Ido take binshi, ta rasa me yake nema a duk ɗakunan hotel da suka taɓa zuwa. Bathroom ɗin ya koma, bai daɗe sosai ba, ya fito, bisa alamu ruwa ya watsa, kana dan al'kyabbar shi na hannunshi yanzu dagashi sai jallabiya. ninke al'kyabbar yayi, kana, ya ajeshi gefe, inda ya ajiye hiraminshi da wayoyinshi. Ledodin hannunta ya amsa tare da cewa. "Je kiyi wonka kizo ki kwanta". Cikin sanyi tace. "Ni nayi wonka ɗazu". Kanshi ya gyaɗa dan ya lura har yanzu a tsorace take. Zama yayi bisa sallayar da yasan Jamil ne ya shimfiɗa misa kana yace. "To zauna kici abinci". Da sauri tace na ƙoshi". Ido ya ɗan zuba mata, kana yace. "Uhummm, to kwanta kinga gani nan kusa babu abinda zai sameki da izinin ubangiji". Da sauru tace. "Toh". Ta ƙare mgnar tana nufar kan luntsumemen gadon. Ledodin da Safiyyah ce ta ajiye musu cewa na abincin walimar ne kuma tace mishi Ummi da Umaymah da Mamma ce da kansy sukayi aikin ne yasa, ya gamsu da aikin kuma zaici. Sosai yaci naman zabuwar da Arish ɗin. Ɗan saura kaji akayi na zabbin na musamman ne shiyasa su Umaymah suka yishi da kansu. Ruwa yasha, kana ya gyara zamanshi tare da tattare sauran bakin ledar ya ƙulle. Jingina bayanshi yayi da jikin gadon. Kana ya fara rairai karatun al'ƙur'ani cikin zazzaƙar muryarsa haka yasa yaji sanyi zafin da zuciyarsa keyi na fahimtar sharrin magautanshi har baiwar Allahr da bataji bata ganiba, kawai dan ta kasance matarsa magautansa ke bita da sharri. A hankali Aysha ta sauƙe ajiyan zuciya, tana mai jin daɗin sautin muryarsa da karatun da yakeyi a hankali. Mirginowa tayi bakin gadon. Kana ta kwanta tayi lib ta matso da kanta kusa da kafaɗunshi. Lokacin ɗaya taji bacci na fizgarta. Shi kuwa Sheykh a hankali ya juyo ya kalli wayarshi daketa haske alamun ana kiranshi. kasan cewar yazo ƙarshen suratul Maeda sai yayi addu'a ya shafa. Kana ya miƙa hannunshi ya ɗauki wayar, Ummi ya gani a saman screen ɗin ya kai yatsarsa kenan kiran ya katse. Dama shima katse kiran zaiyi shi zai kuma kiranta. A can gida kuwa Umaymah ce ta ɗan kalli Ummi tare da cewa. "Sake kiranshi ni naji tsoro ita a kirata bata ɗagawa kuma shima a kirashi bai ɗagawa". Cikin gyara zama Ummi tace. "Zai kira, in yaga kiranmu inaga baya kusa da wayane sanda kika kirashin." Shiru suka ɗan yi. da sauri Ummi ta kalli wayarta. "Yauwa gashi ma ya kira". Ta faɗa tana amsa kiran. "Assalamu alaikum, Ummi". Cikin jin daɗi tace. "Wa laikassalam Sheykh kana lfy". "Alhamdulillah". yace Yana gyara zamansa. Da sauri tace. "To Masha Allah. Aysha fa munyi ta kiran wayarta bata ɗagawa, hankalinmu ya tashi tana lfy ko?". Juyowa yayi ya ɗan kalleta kana yace. "Uhummm to ga dai ta nan Ummi, wannan tsoron nata ne yau kuma ya dawo a cikin mota kafin in fito tace, wai Jahan yazo, gaba ɗaya ta gigice shiyasa ma ban kawota nan wurinku ba". Ya ƙarashe mgnar a kunyace wai kada suyi zaton rashin kunyane da jarabar mace ya sashi ɗauketa. Cikin tsoro Ummi tace. "Subahanallahi Jahan kuma, Sheykh ya kamata kasa ido sosai fa a kan abun nan". Juyowa yayi ya ɗan kalleta, tayi shiru ta zuba mishi ido. A hankali yace. "Ummi babu batun wani Jahan fa, Ni inaga Ja Ha N nefa Ummi suka bada Jahan. Kawai dai magautanna ke mata barazana da sunan. Dan suna da wata manufa akanta akayi katari kuma akwai mai suna Jahan sanane a gari aikinsa kuma sirrine, shi kuma an bani tabbacin ma baya ƙasar mafa tun watannin baya kawai mutanenta ne". Da sauri ta tashi zaune cikin rauni tace. "Wallahi mutum ne, ba iska bane, Ni bani da iska ka dena cewa iskokaina, wlh Ummi mutum ne". Ummi da taji muryarta cikin kula tace. "Sheykh ka ƙara kula kan iya linka". "To Ummi". yace Ita kuwa Umaymah ta miƙawa wayar. Jin muryar Umaymah ne ya sashi cewa. "Umaymah ba komai fa ku kwantar da hankalinku". Cikin kula da so tace. "To Jazlaan Allah ya kare mun ku, saida safe ko". Amin Amin yace kana ya katse kira. Miƙewa tsaye yayi, tare da wayar a hannunshi inbox ɗinsa ya ɗan shiga text ɗin da aka turo mishi ɗazu da pravate number, ya Kuma zuwa ido. "Da kyau kayi tabsir mai zafi, sai ka kula da yar iskar bororiyar da aka auro maka, mai son maza. kayi amfanin da wannan damar ko zaka gaskata abinda muke gaya maka, na son maza da binsu." Idonshi ya rumtse da ƙarfi kana ya buɗe su a hankali. Su kuwa can sashin magautan Sheykh sun dade da fara turo mishi irin waɗannan saƙonnin a saninsu dai sun san sun kashe mazakunta Sheykh bazai iya raɓar maceba. Shiyasa suke nuna mishi ita Aysha yar iskace dan su samu su haddasa zargi a tsakaninsu, shiyasa suke cewa ya gwadata duk da su a zatonsu wani zai wakilta ya gwada masa ita. Sabida basu san yanada wani sashi na sirrin aikinshiba. Wanda yake bibiyar komai wanda Shatu kuma ta taɓa yin karo dashi a lokacin da yake fita aikin nashi da dare. So shiyasa yake amfani da wannan damar. Numfashi mai zafi ya fesar. A hankali ya kalleta ganin ta mirgina ta koma can tsakiyar gado tana mgna kaɗan-kaɗan. "Ni bani da iska Allah ma ya sani, koma menene ai a gidanka ne ya fara min, komai sai kayi ta cewa inada iska, har kana gayawa mutane, zakasa ayita min kallon mai iska. Na tambayi Bappa na yace min iya tsawon rayuwata basu sanni da iskaba, kuma ai da sun sani da zasu gayawa Lamiɗo". A hankali yasa hannunshin ya kashe wutan ɗakin. Da sauri ta taso zaune lokacin da duhu ya mamaye ɗakin. "Dan Allah ka kunna wutan". Da sauri ta matso kusa dashi jin yayi mgna kusa da ita yace. "Ni bana iya bacci in haske na kunne. Kwanta gani nan babu wani al'jani Jahan da zaizo da yardar Allah". A hankali ta zame ta kwanta kusa dashi. Yayinda shi kuma yake zaune. "Tashi ki zauna kiyi addu'a kafin ki kwanta". Yace mata lokacin da yaji ta kwanta. Cikin bacci tace. "Na gaji kayi min mana". Kanshi ya jinjina jin wai ai ta gaji. Tafukan hannunsa ya hada ya buɗa, kana ya karanta ƙulhuwa 3 falaƙi 3 nasi 3 Ayatulkursi'u 1 ya tofa, kana ya shafawa jikinsa. Sannan ya kumayi kamar yadda yayi ya tofa kana ya juyo kanta, daga kan fuskarta ya kife tafin hannunshi ya shafa mata har zuwa kan yatsun ƙafarta kana ya shafa kanta, sannan ya kwanta kan gefen damanshi. A hankali yasa hannunshin ya juyata yace. "Kwanta ta gefen dama". To tace ya zama baya ta bashi. Shiru tayi tanajin alamun kamar karatu yakeyi. tsawon lokaci sukayi a haka batayi bacciba shima baiyi baccinba. A hankali ta juyo sabida gajiya da gefen daman yayi mata. Lumshe ido tayi. Shi kuwa Sheykh a hankali ya yunƙuro ya matsota sosai, cikin sanyi tace. "Ka matseni fa". "To ki koma can baya mana." Yace mata. Yana lumshe idonsa. A hankali ta mirgina zata matsa, sai kuma ta ɗan tsaya jin tama isa bakin gado, daga ita sai katanga, juyowa tayi ta fuskanci katangar ta kwanta tayi shiru. Shi kuwa Sheykh shima shirun yayi, yana dogon nazari kan al'amarin Jahan da yake girmama kullum a wurinta, ya lura yau saura kiris ta suma. Numfashi ya ɗan fesar a sanyaye kana ya juyo da kyau ya fuskanceta, sannan ya matsota ya manna bayanta da ƙorjinsa. Da sauri ta buɗe idonta tare da buɗe baki zatayi mgna sai kuma tayi shiru jin ya sunkuyo kanta kanta sosai daga koncen, kanta ya ɗaga kana ya ture pillow'n da kanta yake kai, sannan miƙar da hannunshi a wurin, kanta ya kwantar bisa damtsen hannunshi da ya miƙar, kana ya juyota rigingine, ƙafarshi ya ɗan ɗaura gefen cinyarta kaɗan, kana yaja cinyarta yasa tsakankanin cinyoyinshi. a hankali ya fesar da numfashi kana murya can ƙasa yace. "Shike nan baki da iska. Kiyi haƙuri, Umaymah kawai na gayawa fa." Cikin wani irin masifeffen sanyi da jin daɗin kulawarshi gareta a hankali tace. "Toh, amman Yah Sheykh da gaske inada iska ne wai". Kanta ya shafa kana yasa bakinshi ya sumbaci goshinta cikin son kawar da tambayar tata yace. "Me Jahan ɗinkin yake miki in yazo wurinki? Yana mgna ne? In yanayi me yake ce miki?". Baki ta tura tare da cewa. "Ni dai ba Jahan ɗina bane". hannunshi yasa a hankali ya fara janye dogowar rigar jikinta yanayi sama dashi kana yace. "To na ji, me yake miki?". Cikin takaici tace. "Ba kanaga kamar wai al'januna bane sai kake ɗaukar abin wasa to wata rana sai yamin ciki ai da ƙarfi". Cikin sauri ya rumtse idonshi da ƙarfi tare da yin sama da rigar sosai kana a hankali yace. "Na yarda ai baki da al'janani. To amman ta yaya zai miki ciki". Juyowa tayi ta fuskanceshi da kyau kanta na damtsen hannunshi, tattausan gemunshi na taɓa goshinta, cikin muryar da tafi kama data tsoro da raɗa tace. "Duk fa lokacin da ya zo na ganshi sai yayi kissing lips ɗina. Ɗazu kuma harfa kwance min igiyoyin wuyan rigata yayi, gasuba har yanzu ban ɗauresu ba". Cikin hikima ya zare hannunta ɗaya cikin rigar kana ya zare ɗayanma sannan yace. "To sai kuma yayi me daya kunce igiyoyin?". ya ƙareshe mgnar yana ajiye rigar tata bisa inda ya ajiye al'kyabbar shi. Kana ya zare jallabiyar jikinshi, ya ajeta, sannan ya matso gareta tare da jawo musu blanket yace. "Uhumm". Cikin tsurawa inda yake ido tace. "Harda sa hannunshi cikin rigata, kuma yana mammatse min ƙirj.." Da sauri ya lumshe idanunshi tare da jawota jikinshi ya matseta gam har saida tayi ƙara sabida matsar tayi ƙarfi, shi kuwa Sheykh gaba ɗaya jikinshi tsuma yakeyi ya gama gamsuwa Shatu Mar'atussaliha ce. Ya yarda ita bata da wanda ta yarda dashi a Masarautar Joɗa sama dashi bata ɓoye mishi komai, ya kuma gamsu da son kiyaye lfyarsa da takeyi. Cikin wata iriyar fitinenneyar murya mafi daburcewa yace. "Bana son ji, kuma kodama al'janin nakine, zanyi mgninshi da izinin Allah, bashi da hurimi da mallakin Muhammad, shi kaɗai yake mallakar abunsa, kuma ko gani nai wani bazai yiba in sha Allah a mutum dai babu mahaluƙin da zai min kutse a gidana ma bare a kan iyalina." Ita dai ba jinshi sosai takeyi ba, sabida wasu abubuwan da yakeyi mata sun zarta abinda Jahan ya aikata mata. Dib, dib, dib, haka zuciyarta keyi lokacin da taji ya haɗe lips ɗinshi da nata, kana tattausan tafin hannunshi na yawo a cikin dukkanin sasan jikinta. Gaba ɗaya sai tsoro ya rufeta, a hankali taketa jujjuya kai alamun a a. A hankali ya rabe lips nasu, cikin sanyi tace. "Ya Sheykh bacci nakeji". Uhummm yace kana ya gyara musu kwanciyar. A can ƙasar Cameroon kuwa. Ba'ana ne zaune gaban wani ƙasurƙumin bokanshi mai ƙara buɗa mishi ido, da koya mishi siddabaru iri-iri. Wani ƙaton kaskone a gabansu. Cikin muryar da babu daɗin amo boka Dumba ya cewa Ba'ana. "Leƙa ka gani, gacan ajiyarka tana kwance tana bacci lfy lau babu wani mahluƙin namiji da zai iya taɓa koda farcenta ne bai mutuba, bare har ya shafeta ko ya kai ga taɓa wani sashin sirri na jikinta bare a kai ga ya kusanceta". Tuni Ba'ana ya leƙa kanshi yana ƙarewa fuskar Aysha kallo, cikin jan dogon numfashi yace. "Boka Dumba to shi wannan haskenfa da yake kwance kusa da ita menene shi kuma wane haskene ya zagaye ɗakin da fuskarta?". Cikin yin cacuɓe-cacuɓenshi yace. "Wannan haskene dake wanzu da izinin ubangiji haskene dake kare wanda ke kusa da ita sam bamu da tsumi ko dabarar ganin komai a kanshi, sabida shi mutum ne da bakinshi baya bushewa da ambaton Allah kana baya rabuwa da al'wala a jikinshi. Ita kanta in dai tana kusa dashi ainun jikinta ya taɓa nashi to bazamu ga komai a kanta ba, batun kusanta ne dai tabbas babu mahaluƙin da zai kusanceta ya rayu, domin madadin ɗanɗanon ni'imomin da ko wacce mace take dashi, in namiji ya sadu da ita, to ita dafin kuna da macijiya ne ni'imarta zata shigeshi a sashi mai tsada a jikinshi kan gari ya waye zai mace ya bar duniya". Wata iriyar muguwar dariya suka kece da ita kamar zasu fasa kogon da suke ciki, boka Dumba ne yaci gaba da cewa. "Kai dai ka gama aiyu kan ka hankalinka kwance, shi wannan da yayi sanadin faɗinka gasar Shaɗi har yasa kabar ƙasarku, tuni munsa ajalinshi a jikin matar da yakega matarsa ce, kaga koda baka tare da Shatu zata tayaka yaƙi ba tare da ta sani bama". Cikin jin daɗi da baƙar mugunta Ba'ana yace. "Dole ma ya mutu, sai dai babarsa ta haifi wani hegen bafullatani mai jajayen kunnuwa". Daga nan sukaci gaba da hirarsu da tanadin hana fulanin ƙasar Nigeria da Cameroon zaman lfy. A nan Ɓadamaya kuwa, cikin Masarautar Joɗa, a wannan lokaci na tsakiyar dare. Suka fito cikin masarautar suka nufi gidan boka Tsitaka, garin yayi duhu yayi dim sai azabar zafi da ake tsulawa zafi irin na tsakiyar damuna irin wanda in an kwana biyu ba'ayi ruwan samaba, bisa alamu hadari ke diddigowa daga ƙasa shiyasa garin yayi dim babu alamun iska. Suna shiga Boka Tsitaka ya kwashe da dariya tare da cewa. "Lbri mara daɗin gashi can konce da matarsa bisa gado ɗaya, sai dai kun san ɗan naku ba'a iya ganin sirrinshi, ko matar tashi bana gani sai wani haske daya rufesu. Kuma yana gab da ɗirkawa ƴar fulani ciki hegen yaro dan yanada ƙoyayen haihuwa da ƙenƙesa". Cikin tashin hankali ɗayan yace. "Kusantar mata harda haihuwa, anya kuwa bazan sa a dandatse min wannan yaron ba, shin wai shi wanne irin mutum ne da baya jin sihiri da tuggu da makirci". Ɗayan ne yace. "Ai kuwa koda ya haihu yarane dai bazasu rayuba". Dariyar mugunta Boka Tsitaka yayi tare da cewa. "Ku dai kun iya kawo aiki kun kuma iya faɗin mugunta sai dai tabbas akwai wani wanda yake gefenku, da yake aikata musu fiye da shirinku, kullum in kun tuna yimasa wani abun kafinma kuyi abun zakuga fiye da hakan ya faru tun shekarun baya. To bare kuma yanzu an sake samun wani taƙadirin ma yasa mishi ido". Dariyar jin daɗi sukayi kana sukaci gaba da muhawarar mugunta. Washe gari azahar Gimbiya Aminatu ce zaune gefen Lamiɗo da ya kira Sheykh suna gaisawa, tare da cewa. "Muhammadu Akwai babban uzurin dake buƙatar ka dawo gobe". Gyara zamanshi yayi tare da kallon Aysha dake gefenshi ita da Hibba da Jalal da sune suka kawo musu abinci a hotel ɗin da suke. Maida kanshi yayi ya jingina da kujera kana ya lumshe idonshi tare da cewa. "Eh dama gobe zamu taho, amman sai dare jirginmu zai tashi. Su Ya Hisham da Affan kuwa sunce sammako zasuyi wai tafiyar mota zasuyi". Cikin sauƙe numfashin Lamiɗo yace. "To Allah ya kaimu ya kuma dawo daku lfy, itafa Juwairiyya sai yaushe zata dawo". Kanshi ya ɗan mirgina kana yace. "Zan dai taho da Ya Jafar da Jalal, in bata gama uzurorinta ba, sai ta koma masarautar Jadda ta dawo daga baya." Cikin gamsuwa da hakan Lamiɗo yace. "To hakan yayi Allah ya kawoku lfy". Amin Amin yace kana ya katse kiran. Jalal ne da Hibba suka miƙa tare da cewa. "Mu zamu tafi." Bai kulasu ba, Jalal ne ya ɗan matsoshi tare da cewa. "Umaymah tace ka kai mata Ɗiyarta taga ya ta kwana da jikin". Kai ya gyaɗa alamar to. kana Hibba ta kalleta tare da cewa. "Aunty Aysha sai kin dawo, Allah ya ƙara sauƙin". Amin tace tana gyara zamanta tare da jawo ƴar jakar kayan da Hibba ta kawo mata. Wai na anko ɗin fansan idon da za'ayi. Su kuma nan suka fita. Suna fita, ya miƙe ya rufe ƙofar, kana ya dawo ya hau kan gado ya kwanta. Da ido ta bishi tare da cewa. "Yah Sheykh gado kuma to yaushe zamu tafi ko inbi su Hibba kawai ne?". Lumshe idonshi yayi alamun bacci zaiyi, a hankali tace. "Dole ne kullum sai kayi baccin tsakanin azahar da la'asar ɗin nan". Kanshi ya gyaɗa mata alamar eh. kana ya juya mata baya. Dole itama ɗin ta hau ta kwanta, tana konciya ya jawota jikinshi nan take sukayi bacci. Ƙarfe uku da minti arba'in da biyar ya farka, da sauri ya zareta daga jikinshi kana ya shiga bathroom, wonka yayi fes kana yayi al'wala ya fito. zaune ya sameta bakin gado. "Tashi kiyi wonka mu tafi tunda ke bakya cikin masuyin salla". Cikin sanyi tace. "Ah ina cikin masuyin salla mana". Kai ya gyaɗa yana zura tattausan al'kyabbar shi. Yace. "Eh amman ni dai tun jiya banga kinyi salla ba". Cikin rashin fahimtar wayon da yake mata tace. "In Sha Allah gobe dai da safe ai zan fara". Murmushi yayi tare da cewa. "To tashi kiyi wonka kafin inyi sallan". To tace kana ta miƙe ta shiga Bathroom da ƴar jakar kayanta. Shi kuwa ya kabbarta sallan la'asar. A cikin bathroom ɗin ta canza kayanta bayan ta kimtsa jikinta. Kana ta ninke wanda ta cire ta saka a ciki ta feshe jikinta da turarenta mai sanyin ƙamshi, sannan ta fito. Zaune ta sameshi bisa sallayar yasa System ɗinshi a gaba ya maida hankalinshi kab kanta. Bisa alamun wani abu mai tarin mahimmanci yakeyi. Dan gaba ɗaya yatsun hannunshi aiki sukeyi sai kwayar idanunshi da yake jujjuyawa kan screen ɗin na'ura. Yanayi kuma yana motsa lips ɗinshi alamun still kuma tasbihi yakeyi bincikar number da ake tura masa text a rufe yakeyi yadda zai samu ya buɗe layin yabi diddiginshi. A hankali ta kalleshi da kyau, kana ta kalli kayanshi da ya cire ɗauka tayi ta ninninkesu ninkewa mai kyau, tasa a ƴar jakar ta zuge zip ta rufe. Sannan ta koma gefenshi can ta zauna bayanshi. Cikin sanyi tace. "Ni dai banga wayata ba". Bai kulata ba, domin aikin da yakeyi ya tunzura mishi nitsuwa. Cikin sanyi tace. "Ayyah to dan Allah. Sammin wayarka in yi kira". Tura mata wayarshi dake gefenshi yayi sabida ya samu ta rabu dashi dan tana raba mishi hankali". Ɗaukar wayar tayi sai kuma taga akwai security code a jiki. Matsoshi tayi da mamaki dan tasan akwai woyoyin shi biyu data taɓa riƙewa basa da security, jujjuya yar wayar tayi ganin yar micilace kuma harda liƙa mata matakan tsaro, taɓe baki tayi tare da cewa. "Me code ɗin buɗe shi". "Mamey". Yace mata ba tare da ya kalleta ba. jujjuya yar mitsitsiyar wayar tayi a tafin hannunta, contacts ta danna da nufin ta ɗan duba ko da number sai ta samu nanma a garƙame yake. Ikon Allah tace a hankali kana ta danna. Phone na ma kirib yake, cike da mamaki tace. "Wayarfa tako ina ansa mata kan tsaro". Da sauri ya juyo ya kalli wayar da ke hannunta. Hannunshi yasa ya amshi wayar da sauri tare da zurata a al'jihunsa kana ya yasa kan yatsunshi ya ɗan bugi goshinsa tare da kwaɓe fuska kana ya kalleta cike da alamun damuwa yace. "Kai Alhamdulillah, Allah na gode maka daka jarabceni da wannan fitinenneyar yarinya Aish mata, kinzo kin tasani gaba da surutu, kuma kina gani aiki nakeyi, ko so kike na ki rikitamin tunani ne". Kanta ta langoɓar tare da kwaɓe fuska tace. "A a, Ni kawai wayata zan kira". Cikin zubawa lips ɗinta ido yace. "Ba kin barta a motaba". Da sauri tace. "Laah hakafa ni na manta ma". Kanshi ya gyaɗa kana ya gyara zamanshi ya fuskanci System ɗin nasa. Gefenshi ta ɗan kalla tare da cewa. "Yah Sheykh!". Shiru bai amsa ba yaci gaba da aikinshi. a hankali ta kuma cewa. "Yah Sheykh!!". Bai amsaba bai kalleta ba. A karo na huɗu ta kuma kiranshi. "Yah Sheykhhhh". Ta ƙarashe kiran murya can ƙasa da alamun bacci ya fara kamata, a hankali ya ɗan juyo kwayar idanunshi ya kalli inda take. Cikin lumshe ido tace. "Mu tafi mana, za'ayi fansan ido da bamu jeba". Kanshi ya gyaɗa alamun to, daga nan ya meda kai yaci gaba da aiki. A can gida kuwa, tuni anyi fansan idon amarya da ango gaba ɗaya an gama komi da komai. Har an fara shirya farfajiyar Side ɗin Umaymah wanda anan za'ayi shagalin mother's day ɗin. An gyara wurin an kimtsa an shirya komai yadda ya kamata. Ƙarfe biyar dai-dai duk an gama shirya amarya cikin shiga ta al'farma, hakama ango Haroon ɗan ayi. Aunty Rahma kuwa tasa mabusan masarauta da makaɗa yan kakaki da tambura da al'gaita duk sun shiryawa shagalin tunda abu na jinin sarauta ai dole a gwada iyawar. Safiyyah ce ta shigo bedroom ɗin Umaymah inda ta wuce zugan ƙawayen ta duk suna falo cikin kwalliyar ƙasaitattun mata, matsowa kusa da Umaymah tayi tare da cewa. "Umaymah Aysha fa har yanzu fa Hamma Jabeer bai kawota ba,". Cikin sauri Aunty Juwairiyya tace. "Dan Allah Umaymah kirashi ya kawota Mamma tace su Haroon ma bazasu fitoba sai sun iso". Murmushi ta ɗan yi tare da cewa. "Uhummm Jazlaan fa ba son waɗannan abubuwan yake ba. Bana son tirsasa masa yin abinda baya so ku kuma kun dage, ala dole tunda bikinsa ba shiri ba'a zoba yanzu sai kunyi shagalin". Ummi ce ta ɗanyi murmushi tare da cewa. "To bari ni in kirashi". Cikin sauri Umaymah tace. "Yauwa yama fi min". Ita kuwa Ummi wayarta ta kara a kunne bayan ta danna mishi kira. Bugu biyu ana uku taji ya katse kiran. Jim kaɗan kuwa sai ga kiranshi. Bayan sun gaisane sai kuma ta ɗan yi shiru. Jin hakane ya sashi cewa. "Na'am Ummi meke faruwa ne?". Cikin tausasa murya tace. "Eh dama duk an gama shirine ku kaɗai ake jira". Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Haroon dake ta murmushi kana a hankali yace. "Ummi ai mun dawo, yanzu muka shigo, bata iso wurinku bane?". Da sauri Ummi ta juyo ta kalli bakin ƙofar jin muryar, Aysha tana sallama. "Yauwa gata ta iso". Ta faɗa mishi tare da katse kiran". Safiyyah ce tayi sauri kamo hannun Aysha tare da cewa. "Yauwa zo muje ɗakin Hibba ki shirya". Murmushi tayi tare da cewa. "Safiyyah barni mu gaisa dasu Umaymah mana". Murmushi Mamma da yanzu ta shigo tayi tare da cewa. "Uhumm Safiyyah kuwa da gaggawa". Cikin ladab da biyayya ta rusuna ta gaidasu kana, Safiyyah ta jata suka tafi ɗakin Hibba. A can Side ɗin dasu Haroon suke kuwa, Ibrahim ne ya ɗauko wasu tattausan kaya masu masifar kyau da taushi, yadin Getzner ne mai ɗan karen kyau kalar pink guava mai masifar kyau, riga da wonɗone da babbar riga gariya an watsawa mats aiki da surfani mint green color irin mai sheƙin nan, sai baƙin hula mai ɗan karen kyau shima da ratsin mint green da fari, amsa yayi tare da kallon Haroon da Ibrahim ɗin sosai kayan sukayi masifar musu kyau, kanshi ya ɗan juya ya kalli takalman da Ibrahim ke nuna mishi baƙaƙene irin masu sheƙin fatar nanne. Fita sukayi, dan bashi wuri yasa kayan. Sosai kayan sukayi masifar amsar fatar jikinshi da surarshi ya fito ras balaraben asali. Komai. Hular ta zauna ras a kanshi, gefe da gefen kan nashi duk tattausan sumanshi ya ɗan fito, Especially ƙeyarshi da sumar ta kwanta lib kana farar fatarshi tayi ras ciki sajenshi da girarshi komai tubar kalla masha ALLAH. A hankali ya taƙo ya fito falo. Nan take su Haroon Suka miƙe, kasan cewar duk abokansu sun tafi sun watse tunda bikin maza ya ƙare, sai su uku suka rage sai kuma su Ya Hisham, Affan, Jamil, Jalal, Azeez, Sadiq, imran, Kabir, Kamal, Sulaiman, da dai sauran ƴan uwa da wasu makusanta. Haka suka fito a tare, Tuni harabar wurin ta cika tayi maƙil manyan matane tako ina matan sarakuna da manyan yan kasuwa da siyasa, aminan Umaymah da matan abokon Abbansu Haroon, sabida ranar tasuce ko wacce tasan Umaymah da Jazlaan ɗin ta sun san soyayyarsa a ranta fiye data Haroon ce sun kuwa san biyayyarsa gareta. Shiru wurin babu hayaniya, hakane yasa Sheykh bai damuba dan baiga abun kiɗe-kiɗen da ya tsana ba. Kuma gashi babu wasu taron maza, duk ƙannenshi ne. Sai kuma iyayenshi, duk da har ga Allah har ransa baiso wannan tsarin ba sai dai bisa dole Umaymah'nshi da Abba Hajia Mama da Ummi suka tirsasashi. Kuma suma basu san Aunty Rahma ta tsara kayan kiɗa da bushe-bushen sarewa da al'gaitanba. "To ma in banda su Umaymah ya za'ayi ayi abu salam". inji Aunty Rahma da take tare da mabusan. Hibba ce ta ɗan kalleta tare da cewa. "Ai kuwa Hamma Jabeer zaiyi faɗa". Dariya tayi tare da cewa. "Me ruwana". Sai kuma ta juyo ta kallesu tare da cewa. "Kuna ganin amaren sun fito ku fara buga tambura da kakaki ayi bikin gidajen sarakuna haka Salam". Ai kuwa bata ida rufe baki ba. Aunty Juwairiyya ta buɗe ƙofar babban falon Umaymah ta fito ita da Jazrah. Jannart na bayanta Aysha na bayanta. Sai kuma Safiyyah ta biyosu. Wani irin murmushi da gyaɗa kai Aunty Rahma tayi lokacin da taji an saki sautin tamburan. "Uhum yauwa haka mana asan ana biki kam". Ta ƙarashe mgnar tana tahowo kusa dasu Umaymah cike da mamaki suke kallonta ita kuwa tana musu murmushi Yar autar Sitti kenan. A hankali Aysha ta lumshe idonta sabida wani irin yam da taji tsikar jikinta na badawa. Hannun Safiyyah dake riƙe da nata ta ɗan juya itama ta riƙe. A hankali sukaci gaba da taku cikin irin wasu masifaffun kaya masu masifar kyau, irin dai kayyakin nan da yan gayu ke sawa mai shara-sharan tattausan yadin cikin pink guava ne, kana net ɗin saman kuwa mint green ne. Anyi ɗinkunan dogayen riguna masu kyau cib cib da jikinsu. Sai wasu takalma masu ɗan karen tsini kalar azurfa da yar karamar fosa sai a goggoronsu shina kolon takalman. Sosai sukayi kyau, A hankali suke shigowa cikin taron ana mc ɗin yana mai bin waƙar da ya saki ta. "Ku-martsa-ku-martsa ga amarya ta iso". Wani irin murmushi mai cike da jin daɗi Umaymah tayi kana ta kalli Hajia Mama dake gefenta tace. "Kinga surkanki masha Allah". Uhummmm tace tare da kaɗa ƙafarta. Sheykh kuwa wani irin rumtse idanunshi yayi lokacin da yaji an saki kuɗin badujalan injishi da faɗin. Tsayawa yayi cak ba tare da ya ƙara koda taku ɗaya ba. Haroon da sauran tawagar ma tsayuwa sukayi, Ibrahim ne ya ƙara matsoshi tare da cewa. "Dan Allah kayi haƙuri mu ƙarasa koda 5 minute ne kayi sai ka tashi. Dan Allah muje Umaymah zataji daɗin hakan". Cikin takaici yace. "Bazan jeb..". Bai rufe bakinshi ba yaji an riƙe hannunshi na dama da sauri ya juyo, Aunty Hafsat Mamma kenan Cikin sanyin murya tace. "Dan Allah Muhammad muje na roƙi wannan al'farmar kayiwa Allah da Manzonsa muje, koda zaman daƙiƙu ukune kayi. Kada mu kunyata wurin aminan Umaymah". Ya zaiyi sun gama ɗaureshi da jijiyoyin jikinsa, Wani nannauyan ajiyan zuciya ya sauƙe mai ƙarfi kana ya gyaɗa kanshi yaci gaba da tafiya. Still Mamma na rike da hannunshi a haka har suka iso, farfajiyar wurin. Har gaban kujeru inda aka shirya wurin zamansu taje ta ajiyeshi kusa da Aysha, tuni shi Haroon ya zauna kusa da amaryarsa. Shi kuwa Ibrahim shima ya zauna gefen Safiyyarshi. Kana su Affan kuwa duk suka zauna tare dasu Jazrah da Azeema da Hibba da sauran cousin sisters ɗin su. Mc ne ya fara shelan Amare su fito, surkansu su nuna musu gata. A hankali Jannart ta miƙe tsaye sabida ita duk yan uwanta ne, ita kuwa Aysha gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi Allah ya sani ita dai tana tsoron idon mutane, ganin bata miƙe tsayeba ne, yasa Aunty Rahma yin sauri ta iso garesu sunkuyowa tayi ta kamo hannun Aysha tana miƙar da ita tsaye. Ɗan juyowa tayi ta kalli Sheykh. Cikin tsuke fuskarsa yace. "Zabiya kiyi a hankali dai dan dujal da ganga yake baiyana tsoro nake jiye miki kada ki zama cikin mabiyansa". Murmushi tayi kana taja hannun Aysha suka shiga cikin taron tare da Jannart. Wani sassanyan waƙa aka saki. Kana su Hibba suka taso da sauri suna feffesa turare mai ƙamshi kana da bada wani kala na musamman. Cikin tsananin jin daɗi Umaymah, Mamma Aunty Rahma, Hajia Mama. Suka fito bisa dandamali buɗe bakin jakukkunansu sukayi, wani irin liƙi na musamman sukeyiwa amarenta tamkar babu talauci. Gaba ɗayansu da 1-1k suke liƙi cikin ƙasaita. Kusan 5 minute sukayi suna liƙi kana MC yace su koma su zauna su huta. Wani irin banbaraƙwai Sheykh yake ganin abun sabida shi dai a iya tsawon tarihin rayuwarsa bai taɓa zuwa ba, kuma shi bai taɓa ganin tsarin wannan bidi'o'inba. Ina dalili wannan abun, ai ko basuyi hakaba tabbas an san dai suna cikin farin cikin. Baya zamansu kamar da mintuna 3 MC ya kuma kiran amare dasu fito tsakiyar taron. A hankali suka miƙe tsaye, kana suka fara tafiya a hankali, wani irin masifeffen zubawa tsikar jikin Aysha yayi tare da bugawan ƙirji da ƙarfi. Sabida sarewa da al'gaita da tamburan da kakakin da aka sake gaba ɗaya a lokaci ɗaya. A hankali dai suke takowa, suna nufo tsakiyar taron. Nan MC ya kuma cewa yana buƙatar uwar angwayen Gimbiya Khadijah Umaymah kenan da tawagar ƙawayenta. A nitse Umaymah ta miƙe kana Su Hajia Kubra, Hajia Rakiya, Gimbiya Ruƙayya Hajia Maimunatu sai kuma Ummi da dai sauransu. Suna shigowa Umaymah taci gaba da yin liƙin 1-1k duk sauran kuma 5-500 suka fara miƙa wa. Yadda ake busan sarewa ne yake ta'azzara tashin tsikar jikinta da kuma bugawan zuciya. Busar sarewan yakeyi mai busar cike da iyawa da ƙwarewa da bajinta,. Kana ga tamburan da aketa dokawa, a hankali Aysha ta sunkuyar da kanta tare da rumtse idanunta jin naman jikinta ya fara tsuma da karkarwa. Cikin haka MC ya buɗe muryarshi da azaban ƙarfi tare da cewa. "In kaji tambura sai Babbar fada kakaki da al'gaita mabusar masarauta ne. ai duk daren daɗewar tsuntsu a sararin samani bai kai tala-talaba kaga jefa garma a caɓe sai ɗan gada kiɗan shantu sai mata. Ina angwayen Gimbiya Aysha da Gimbiya Jannart fili dominku ku shigo gaban iyayenku". Wani irin haɗe fuska Sheykh yayi to waima ta yaya ta ina zai fara. Haroon kuwa tuni ya miƙe dan gaba ɗaya tsikar jikinshi tashi yakeyi sabida kirarin da akayi musu. Hannunshi yasa ya kamo hannun Sheykh kana yaja, Ƙin miƙewa yayi. Sai dai kuma ya ɗago kanshi ya kalli can tsakiyar taron tsakanin kafaɗun Ummi da Hajia Kubra ya hango Aysha, Ido ya zuwa fuskarta da kyau, kasan cewar shi a zaune yake ita kuma a tsaye take ta kuma rusunar da kanta yasa yana kallon fuskarta ras. Cike da mamaki Haroon ya kalleshi ganin ya miƙe ya kuma nufi wurin. juyawa yayi kana yabi bayanshi suka fara taku a tare. MC ne ya ɗan dakada daga kirarin da yakeyi kana ya buɗe murya tare da cewa. "Gimbiya Khadijah Umaymah ga yaranki angwayen a bayanki a basu wuri su ƙarasa kusa da amaren. Da sauri Umaymah da Ummi suka ɗan ja da baya suka basu hanya. A hankali Haroon ya matso kusa da Jannart. wani sabon liƙi Umaymah da ƙawayenta suka fara, shi kuwa Sheykh a hankali yake ƙara matso inda Aysha take tsaye. Ita kuwa Aysha wani irin tsuma da karkarwa jikin ta yakeyi tuni numfashinta ya fara fizga. Ido Sheykh ya zubawa goshinta ganin yadda zufa ta tsastsafo mata, har tana kwaranya ta gefen kunnenta. A hankali ya ƙara matsota wanda hakan yasa mutane zaton wani salone kawai nashi. Haka yasa Mamma da Aunty Rahma da Hajia Mama suka shigo suma aka ci gaba da liƙin dasu. Affan, da Jamil kuwa murmushi sukeyi, Jalal kuwa ido ya zuba musu. Hajia Mama kuwa sai wani irin sihirtaccen Murmushi takeyi wanda ita kaɗai tasan ma'anarsa. Shi kuwa Sheykh ƙara matsota yayi da kyau har kamar zai ruggumeta, hannunshi na dama yasa ƙasan haɓarta ya tallaɓeshi tare da cewa. "Aish! Ais.. da sauri ya ida ƙarasowa gareta lokacin da ya ɗago kanta yayi dai-dai da ƙaƙƙafewar da idanunta sukayi, kana numfashinta ya tafi cak ya ɗauke ta sum...! Kiyi haƙuri da typing errors banyi editing ba, abubuwa sunmin yawa. By *GARKUWAR FULANI* [3/16, 11:10 AM] +234 806 559 0880: Luuuh ida nunta suka limshe ta sume. Da sauri yasa hannunsa ya tallabo ta faɗa jikinsa, cike da tsoro Ummi ta matsoshi tare da cewa. "Sheykh lfy kuwa meke faruwa?". Cicciɓota yayi ya ruggumeta tsam a jikinshi kana, ya juya ya fara taku, yana ratsawa gefe. Cikin tsananin tsoro Umaymah, Ummi, Mamma. Suka rufa mishi baya. Yayinda Aunty Rahma kuwa da sauran tawagar ƙawayen Umaymah suke zaton, kawai wani salone hakan sabida abu da Ustazu sai kallo. Hajia Mama kuwa da ido ta bisu tare da yin wani ɓoyeyyen murmushi mai cike da manufofi masu ƙarfi. MC kuwa wani sassanyan ƙiɗan da DJ ya saki yake takawa rawa. Yanayi musu kirari, Affan da Jamil kuwa tafi sukeyi tare da alamun, jinjina dan babu wanda ya gano Aysha a tsume take ko Haroon da Ibrahim da Jannart basu ganeba. Da sauri Jalal ya miƙe shima ya rufa musu baya. Da sauri Ummi ke biye dashi a baya tare da cewa. "Sheykh lfy kuwa". A hankali ya jujjuya kanshi tare da cewa. "Ummi a sume take fa". "Subahanallahi!". Suka faɗa a tare. Da sauri Umaymah tayi gabansu tare da cewa. "Zo nan zo muje part ɗin Abban Haroon." Binta a baya yayi sabida yasan canne kaɗai zasu samu babu taron mutane. Suna shiga part ɗin ta juya gefen da. Wani ɗan madaidaicin Side ne mai kyau. Wanda yake da ƴar tazara tsakaninsa da Side ɗin Abbansu Haroon. Hannu tasa ta tura ƙofar. Cikin wani ƙawataccen falo suka shiga, da sauri ya kontar da ita bisa kujera. Kana ya miƙe tsaye tare da sauƙe numfashi yana ɗan miƙar da hannunsa, cikin ruɗani Mamma tace. "Umaymah ya haka, bata da lfy tana sume kuma mu zauna da ita a gida mu tafi asibiti mana". Ta ƙare zancen a firgice sabida bata san matsalar Aysha ba. Ummi ce ta ɗan sauƙe numfashi tare da cewa. "To meya tayar da jikinta kuma lokaci ɗaya haka". Cikin takaici ya ɗan tauni lip ɗin shi na ƙasa tare da cewa. "Uhummm to Ummi kuma kun sani mutun tana na nan matsala, sannan anzo ansa ƙiɗe-ƙiɗe ga ƙarin al'gaita, sannan kuma aka ƙara da sarewa. Ko wanda baida komai a kan shi sai yaji tsikar jikinai na tashi. To ga irinta nan, in kuma ba'a katse sarewar nanba duk zasuyi ta sumewa masu makaran". Cikin sanyi Umaymah tace. "Wlh duk tsiyar Rahma ce, yanzu kayi wani abu ta farfaɗo yafi". Kanshi ya gyaɗa kana yace. "Da fari aje ace subar wannan bushe-bushen sarewa da kiɗan tambarin, a ma tashi kawai a taron haka ya isa haka kowa yaje yayi al'wala magriba ta gabato." Jalal dake tsaye bakin ƙofar ne yace. "To bari inje in gaya musu". Da sauri Ya juya ya fita. Ita kuwa Ummi a hankali ta matso kusa da Umaymah kana tace. "Muje kawai, ba komai zai kula da komai". To Umaymah tace jiki a mace, hankali a tashe, Mamma tace. "Haka za'a barta". Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Mamma kana a hankali ya ce. "Ba komai Mamma kada ki damu zata dawo dai-dai, kije kuyi salla". Bisa dole dai tabi bayansu suka fita. A can wurin kuwa kai tsaye wurin MC Jalal yaje yace. A tashi taron haka lokacin salla yayi. Dole aka tashi kowa ya kama gabansa, bayan ƙannnen ango su Hibba sunyi liƙinsu. Su Umaymah kuwa wurin suka koma taje ta jagoranci ƙawayenta suka koma cikin Part ɗinta. Ƴan cikin garin Tsinako duk suka koma gidajensu sai ƴan nesa-nesa wanda duk gobe zasu tattafi. Su Ya Hisham da Affan kuwa tare da Haroon da Ibrahim suka koma part ɗin da aka sauƙesu, nan kowa ya fara shirin al'wala dan lokacin ya ƙara to. Sheykh kuwa a can Side ɗin. Su Umaymah na fita, ya maida ƙofar ya rufe, kana ya dawo gaban kujerar da ya kwantar da ita. Tayi lib kamar gawa. A hankali ya sunkuyo hannunshi yasa ya dafe hannun kujerar da kanta yake kai. A hankali ya sunkuyo kanta sosai, yatsunsa yasa tsakiyar goshinta ya ɗan buga da ƙarfi tare da cewa. "BISMILLAH". Kana yaci gaba da ɗan buge goshin nata, a hankali tayi wani irin sassanyan miƙa tamkar wahainiya, fatan idonta ta fara motsawa shi kuwa Sheykh ci gaba yayi da buge goshin nata tare da cewa. "Aeeyshah! Aeeyshah!!." Cikin fizgar numfashin da mgn tace. "Na'am". Haɗe fuska yayi tare da cewa. "Ba ke na kiraba,". Da sauri tace. "Ni ka kira mana kanata dukana a goshin da amton sunan Allah". Fuskarshi ya tsuke tare da cewa. "Goshinki ko goshin matata! sanina dake kince kin tafi, meya kuma kawoki me kike nema?". Kwaɓe fuska tayi murya na rawa hawaye na zuba tace. "Kirana ankayi tunda anka kunna Sarewa da al'gaita dole du inda nake zan taho". Cikin faɗa yace. "Ke tafi daga nan maƙaryaciyar banza". A hankali ta buɗe baki alamun zatayi atishawa cikin tsawa yace. "Tsaya ban gama mgn da keba in kika kuskura kika tafi, to tabbas zan jawoki in kuma ɗaureki in ƙonaki". Cikin rawar murya tace. "Na tsaya, kayi haƙuri". "Maza tashi ki zauna". Yace a faɗace. Da sauri ta tashi ta zauna, Gefenta ya zauna kana ya kamo hannunta ya riƙe gam saida tayi ƙara sannan yace. "Baki san gidan da take bane". Da sauri tace. "Na sani". "To ina take?". Ya kuma tambayarta. "Masarautar Joɗa take". Kanshi ya gyaɗa sannan yace. "Na'am kin san kuma dole duk wanda ke cikin masarautar Joɗa sai yaji kakaki da al'gaita da tambura da sarewa tunda mabusar masarauta ne, ko kina nufin duk sanda taji sai kinzo kin fiddata cikin haiyacinta kin tozarta min aurena a bainal jama'a, in bana kusa ta faɗi har ƙasa a sume ko me kike nufi ace matata tana sume a kwance ƙasa". Da sauri tace. "A a baza'ayi hakaba in sha Allah bazan zoba, in dai dan kiɗane da sarewa nayima al'ƙawarin bazan zoba, na dena zuwa har abadan dan Allah sake min hannuna". Kanshi ya jinjina kana yaci gaba da matse hannun da kuma karantar Baƙara da yakeyi a hankali. Cikin kuka tace. "Dan Allah kada ka cutar dani wlh nima ban taɓa cutar da Shatu ba, Ni makariyace a wurinta, dan Allah kada ka ƙonani, zan tafi dama ko iyayenta basu san in jikinta ba, sai dai sukayi zaton akwai wani abu jikinta tunda sa'i zuwa lokacin takan ga abinda bani adam basa iya gani da yardar ubangiji". Cikin sanyi yace. "Wato dan raini baki taɓa baiyana a jikinta iyayenta suka saniba sai Ni Muhammad kikewa hakan ko?". Da sauri tace. "Wallahi Allah kenan na baiyana a jikinta ne bisa dole da kuma ceton lafiyarta da kuma bata kariya dama kai kanka". Cikin hatsala yace. "Ubangijina shine mai bani kariya, in kika kuskura na ƙara ji ko ganinki to tabbas zan babbakaki, fice min daga jikin mata dan kan babarki". Ai kuwa a take Aysha ta fesa wasu tagwayen atishawa guda uku. Sai gashi ta koma ta konta lib a jikinshi tayi bacci. Kanta dake bisa kafaɗarshi ya dungure tare da cewa. "Jiki duk al'janu sai son bidi'a da sakalcin yin addu'a ma wai kin gajiya, gaba barinsu zanyi su mummurƙusheki zaki gane kurenki, wai Yah Sheykh na gaji kayi min addu'ar". Sai kuma yayi murmushi tuno jiya-jiya nan taketa mitar ya dena ce mata mai al'janu, wai harda cewa yana bazata a gari. Zareta daga jikinshi yayi kana ya miƙe yana cewa. "Zaki bazu yarinya bari ki shiga tarkon Muhammad zaki bazu iya bazuwa". Ya ƙarashe mgnar yana wuce bedroom ɗin yana shiga bathroom ya wuce al'wala yayi kana ya fito. Wayarshi ya zaro a al'jihunsa, kirar arshi mai sauti yasa mata kana ya ajiye mata gefen kanta, sannan ya fita ya tafi masalacin. Bayan sunyi sallan mangriba basu fitoba saida sukayi isha'i, kana suka dawo gida. A falon ya samu Umaymah, Ummi, Mamma, Aunty Rahma, Safiyyah Jannart. Itama Aysha tana zaune, yana ganinsu a cike ya ɗan tsaya kana ya kalli Umaymah dake cewa. "Jazlaan ya jikin nata dai". Matsowa yayi yasa hannunsa ya ɗauki wayarshi dake kusa da ita kana yace. "Uhumm ta worke ai". "Alhamdulillah Allah ya ƙara lfy". sukace a tare, A hankali Aysha tace. "Amin". Safiyya, Jannart, Aunty Rahma, ne suka fita. Hakane yasa ya rage Umaymah, Ummi Mamma. Kanshi ya ɗan juya ya kalli Ummi dake cewa. "Wannan abun fa sai an tsaya mata zata rabu dashi Sheykh". Yana lallatsa wayarshi yace. "Dama ai Ni na sani tun jiya data fara cewa, taga Jahan a a Jahan yazo nasan ba wani Jahan ababaɗenta ne kawai ke mata gizo. Amman ba komai zan juyo kansu ya faɗa yana ɗan guntun murmushi, domin yasan Umaymah dai tasan waye Jahan". Ita kuwa Aysha. Tura baki tayi tana kallonshi kamar tayi kuka. Allah ya sani bata son yana cewa tana da al'jani". Murmushi Umaymah tayi ganin yadda tayi kana a hankali tace. "Kada ki damu, yana raba wasuma da nasu bare ke, in sha Allah zasu bar jikinki juyowa ɗaya zaiyi kansu bazasu sake waiwayarki ba ɗiyata. Kirkiji komai mu mun sani matsalar a masarautarsu ce, da Juwairiyya ma lfya lau muka kaita gidan Jafar bata shekaraba makarai suka shige ta". Da sauri yace. "Amman dai ita wannan da abunta tazo Umaymah ba a masarautarmu ta sameshi ba". Mamma ce tace. "Kada ka kare wancan masarautar taku, mu tayi mana illa mafi muni a rayuwa." Kanshi ya jinjina tare da lumshe idonsa kana yace. "To ya zanyi Mamma tunda jigo nane asalinane, kuma ba kowa na ciki keda mugun dafiba, kada kuyi mana kuɗin goro, Nima inai musu uzuri duk da dai nasan duk duniya babu wanda sukayiwa illa sama dani, sai dai nasan zanen ƙaddaratace suka bi". Kai Ummi ta jinjina kana suka miƙe tsaye. Umaymah ce ta nuna mishi Foodflaks dake tsakiyar falon tace. "Kuci abinci ka kula da ita,sai da safe". Ta ƙare mgnar suna fita. Cikin jin kunya yace. "Allah ya bamu al'khairi". Amin sukace kana suka tafi. Washe gari da asuba, a hankali ta buɗe idonta jin muryarshi yana karatu. Ganin ya bata baya baya ganinta ne, yasa ta yunƙura a hankali, ta zuro ƙafafuwan ta ƙasa. Kana ta miƙe ta nufi Bathroom, ruwan ɗumi ta haɗa cikin bathtub ɗin sabida alamun hadari da sassayan iskan dake busowa. Wonka sabulu tayi, kana tayi na tsarki sabida al'adarta ta ɗauke. Towel ɗin dake bisa masaƙalin ta ɗauka ta tsane jikinta, kana ta meda kayan jikin nata.sannan ta fito. Gefenshi ta ɗan ratsa sannan tace. "Zanyi salla kuma ba hijabi". Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta, kana yaci gaba da karatun. Cikin yin ƙasa da murya tace. "Ni ban san ina mukeba, kuma ba hijabi". Miƙewa tsaye yayi jin masallacin Masarautar suna ƙoƙarin tada kabbara. Al'kyabbar ajikinshi ya zare, kana ya dawo ta bayanta. Hannunshi yasa ya ɗago hannunta ya zura mata hannun al'kyabbar, kana ya ɗago ɗayan ma ya zura mata. Sannan ya saketa. Har ƙasa ta zo mata, kasan cewar irin al'kyabba mai duhu da kaurin nanne yasa tayiwa jikinta ƙawanya. Gabanta ya dawo, jallabiyace a jikinshi fara ƙal. Hiramin kanshi ya cire, kana ya ɗaura mata shi a kanta tare da dai-dai-ta zamanshi ya rufe komai na kanta sai fuskarta kawai. Ido kawai ta zuba mishi tana mai shaƙar ƙamshin jikinshi. "Ni dai ba ɗan aikenki bane, kuma bani nace kisa suturar da bai inƙanta ayi salla da itaba, dan haka babu ruwana. Al'barkacin salla zakiyi ne yasa na baki aron rigata, kina idar da salla ki cire min abuna". Ya gaya mata yana tsareta da ido. Cikin yin mui-mui da baki tace. "Uhummm". Shi kuwa juyawa yayi ya fita. Daga nan Side ɗin da kayansu yake shida Ibrahim yaje. Wata al'kyabbar yasa kana suka nufi masallacin. Bayan an idar da salla sune suka dawo gida. Tuni Umaymah kuma tasa Safiyyah da Aunty Rahma sun shiga kitchen da kansu sun haɗa breakfast. Nan aka kaiwa su Affan da Ya Hashim, Imran Sulaiman. Sukaci abinci kana suka kama hanyar komawa Ɓadamaya. Sheykh, Ummi, Aysha, Hajia Mama da Batool da Jamil, Jalal ya Jafar kuwa su sai bayan sallan isha'i jirginsu zai tashi. Haka kuwa akayi. Bayan sallan isha'i. Su Umaymah Haroon, Ibrahim, Safiyyah, Sadiq, Azeex, Hibba Azima Aunty Rahma Ishma sukayi musu rakiya har Airport. Sunata kewar juna, A cikin mota ne, Aysha ta kalli Safiyyah dake gefen Umaymah da Mamma tace. "Safiyyah ai zaku zo mana kafin ku tafi ko". Aunty Rahma dake jen motarce tace. "In sha Allah kuwa, ai muma duk zamuzo, sabida zamu ɗan kwana biyu kafin mu koma". Cikin jin daɗi tace. "To Aunty Rahma a bamu Ishma mana mu koma da ita sai kunzo ku taho da ita". Cikin dariya Hibba dake can baya ita da Hajia Mama da Ummi tace. "Aunty Aysha wayo ko". Da sauri Aunty Rahma tace. "Kada ki damu in sha Allah zasu dawo tare da Juwairiyya, kinga mu zamuyi ko kwana uku ne nan gaba kafin mu koma wurin Sittinmu, in mun koma kuwa bazai dadeba Juwairiyya zata komo to sai ta taho miki da Ishma'n". Cikin gamsuwa tace. "To Allah ya kaimu Lokacin". Amin Amin sukace, kana dai-dai lokacin suka isa, harabar airport ɗin. Nan suka samu su Aunty Juwairiyya da Azeema da Jazrah ma sun iso. Gefensu Sheykh suka isa. Nan sukayi sallama da juna, cikin bege da kewar juna. Suka rabu. Jin ana cekiyar matafiya. Nan suka nufi cikin jirgi su kuma suka koma baya. Basu dai tafiba saida jirgin ya tashi, kana suka juya suka koma gida. Tsakanin Tsinako da Ɓadamaya tafiyar 40 minutes ne a jirgi. A mota kuwa awa goma sha biyar ne. So takwas dai-dai jirginsu ya tashi. Su Affan kuwa dai-dai lokacin suka isa. Kasan cewar a gajiye suka isa, kowa wonka yayi kawai dama sunyi salollinsu a hanya sun kuma ci abinci sai bacci kawa. 8:40 dai-dai na dare jirginsu ya sauƙa a Airport ɗin Ɓadamaya. Dr Aliyu, da Baba Kamal mahaifin Sulaiman kenan, sai Sarkin fada da Galadima ne sukaje tarbosu tun kafin su iso. Tafiyar 24 minutes ne tsakanin Airport ɗin da masarautar Joɗa. Tara da minti goma dai-dai motar Dr Aliyu ta iso har farfajiyar Side ɗin Sheykh, wanda Sheykh yake gaba kusa dashi, Ummi da Aysha suke baya. Motar Baba Kamal kuwa Hajia Mama ce da Batool, Sai, Motar da Galadima ke ciki kuwa, Nan Ya Jafar da Jalal da Jamil suke ciki. Kai tsaye kuma Side ɗinsu Jalal ɗin aka wuce dasu. Itama Hajia Mama har bakin Part ɗin ta aka sauƙeta. Da sauri Ummi ta buɗe marfin motar gefenta ta fita. Nan Aysha ma tabi ta fita. Shi kuwa Sheykh juyowa yayi ya kalli Dr Aliyu cikin nitsuwa yace. "Baba Aliyu ngd matuƙa". Kai Dr Aliyu ya gyaɗa tare da cewa. "To sai da safe". Allah ya bamu al'khairi yace. Amin Amin yace kana yaja motar ya tafi. A bakin ƙofar shiga falon suka tsaye. Suna rike da jakukkunansu. Gefen Aysha ya ratsa ya wuce, ya isa gaban ƙofar, hannunshi yasa ya ɗan zuge zip ɗin jakar dake hannunshi key ya zaro. Kana ya zuge zip ɗin ya rufe. Cusa key ɗin yayi a ramin kana yayi bismillah tare da murza key ɗin, kat-kat yayi sau uku kana yasa hannunshi ya tura ƙofar sannan ya wuce ciki tare dasa hannunshi ta sama jikin ginin ya kunna wutan falon kana ya juyo ya kallesu tare da cewa. "Bismillah Ummi shigo". "To". tace kana ta nuna Aysha hanya alamun tayi gaba. Kafar dama tasa tare da cewa. "Assalamu alaikum". Ba tare da ya juyoba yace. "Wa laikissalam". Ya amsa sallamar a hankali batama jishi ba. Ummi na biye da ita a baya suka shigo cikin kekkyawan falonsu da sukayi kewarsa. Ajiyan zuciya Aysha ta sauƙe tare da cewa. "Masha Allah komai tsab, Allah sarki HIBBA AZEEMA ina kewarku Safiyyah ina begenki kusa Ayyah my Ishma fuskarki ta tuna min Junainah na, Aunty Rahma ganinki ya tada min begen ganin Ummey na. Ayyah 40 minutes kawai ya nesantamu Umaymah, Mamma Ina kewarku Ina jinku kamar yadda nake jin Ummey na". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Kinga gama Umaymah na kira". Ta ƙare mgnar tana amsa kiran. "Eh Alhamdulillah mun isa lfy gamu nan a tsakiyar falo, ɗiyarki nata kewarsu Hibba da Safiyyah naga harda ƙwalla a idonta". Ummi ta faɗawa Umaymah cikin kewarta. Ita kuwa Aysha da sauri tasa hannunta ta shafi haɓarta sai ma lokacin ta gane ashe harda hawaye take zubdawa. Ita kuwa Umaymah cikin murmushin tace. "Wallahi gamu muma yau duk sai mukaji babu daɗi Safiyyah tace ita fa da Aysha ta tafi gidan ba daɗi". Dariya Ummi tayi tare da cewa. "Sabo kenan". "To ku huta gajiya". Umaymah tace kana ta katse kiran. Ita kuwa Aysha haka nan yau take jin bege da kewar ahlinta ta kasa tsaida hawayenta Especially Ahlin Abboi. Tana tuno Didenta su Yah Al'ameen da Innayinta. Bappa'nta Ummeynta, Ya Giɗi, Ya Seyo, Ya Gaini, da Ya Lado. Shi kuwa Sheykh ido ya zuba mata ganin yadda hawaye keta shatata a fuskarta babu ƙaƙƙautawa. Remote ɗin A/C'n dake hannunshi ya meda a masaƙalinshi kana, bakin ƙofar ya koma ya rufe ƙofar kana yazo ya wuce. Side ɗinsa. Miƙewa Ummi tayi tare da cewa. "To nan dai Side dinmu Sara ta gyara mana komai amman nasan Side ɗin Sheykh ba a share yakeba, tunda tare muka dawo da Jamil, dan haka tashi kije ki ɗan kimtsa mishi bedroom ɗin". Miƙewa tayi itama tare da share hawayenta kana a hankali tace. "Naji kafin jirginmu ya tashi yayi mgn da Affan yana ce mishi ya share mishi ɗakin ya amshi key a wurin Gimbiya Aminatu". Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa. "Eh hakafa ni na mance ai Affan na nan". Falon Aysha suka nufa, suna shiga kowa ta nufi ɗaukinta. Ummi Al'wala tayi kana tazo ta kwanta. Ita kuwa Aysha tana shiga, ta ajiye jakarta gefe kana ta faɗa kan gado ta kwanta a kife, ta kifa kanta bisa pillow kuka mai ƙarfine ya kwabce mata, sabida suya da zafin da zuciyarta keyi na tuno ƴan uwanta da suka ɓace. Duk da kuma kontar mata hankali da Bappa keyi na cewa anji lbrinsu har an gansu. Kuka tayi tayi sosai wanda ita kanta bata san tsawon lokacin da tayi tana kukanba. Sai ƙarfe uku dai-dai ta samu bacci ya saceta. Shi kuwa Sheykh yana shiga, yayi ajiyan numfashin sabida ya samu komai tsab-tsab a gyare a killace ko ina na ƙamshi. Kasan cewar ana zabga zafin da rashin ruwan sama da akayi kwanaki ba'ayi bane yasa, garin ɗinkewa da zafi. Gudun A/C'n ya ƙara kana ya ajiye jakarshi cikin drower'nshi. Rage kayan jikinshi yayi kana ya shiga bathroom wonka yayi tare da al'wala sannan ya kimsa cikin tattausan rigan bacci riga da dogon wondo ne. Yana fitowa ya rage hasken ɗakin kana yazo ya zauna bakin gadon. Ya buɗe hannunshi ya ɗagasu sama alamun zaiyi addu'o'in kwanciya baccine, kiran Haroon ya shiga wayarsa. Yasan idan ba ɗagawa yayiba Haroon ba barinshi zaiba, hakane yasa ya amsa kiran da sauri. "Alhamdulillah mun iso lfy yanzuma bacci zan kwanta". Ya faɗa da sauri. Dariya Haroon yayi tare da cewa. "Ya haka dai malam kamar korata kakeyi, nima sabon ango banma hakaba sai kai tsohon ango, to a huta gajiyar hanya, ni yanzu zan kama hanyar fatauci ne". Wani gajeren tsaki yaja tare da katse kiran. Dariya Haroon yayi kana ya jawo hannun Jannart ɗinshi suka nufi ɗauki shi. Shi kuwa Sheykh addu'a yayi ya tofa a tafin hannunsa ya shafe jikinsa duka kana ya kwanta bisa hannun damanshi. Lumshe ido yayi tare da sauƙe numfashi kana ya fara tasbihi kamar yadda ya saba, lokaci ɗaya bacci ya samu nasarar ɗaukeshi. Haka sukayi bacci a gajiye gaba ɗayansu. Ƙarfe biyar saura kwata, ya fito cikin shirin tafiya masallacin Masarautar Joɗa domin limancin sallan asuba. Da sauri ya buɗe ƙofar kana ya fita sannan yaja ƙofar ya rufe. Dai-dai lokacin Ummi kuwa ta farka daga baccin da ya samu nasarar sata makara, da sauri ta miƙa bathroom ta faɗa al'wala tayi kana ta fito. Aysha kuwa can cikin bacci take cin sautin karatun Alqur'ani da yakeyi na suratul Al-Burooj. Sosai sautin muryarsa ke ratsa ko ina na cikin masarautar Joɗa, a hankali take buɗe kwayar idanunta wadanda bacci da kukan da tayi ya kumburasu suka yi wani ɗan ja haka mai gauraye da farin. meda idon tayi ta lumshe jin yadda yaja tsakiyar aya ta 8. Yadda yaja illahhhhhhhh ɗin cikin taƙib mai ja shida, kana ya maida numfashi. Saida taji tsikar jikinta na tashi yar-yar, da sauri ta buɗe idonta kana miƙa zaune, cikin kasala da yanayin bacci bai isheta ba sam ta miƙe tsaye ta faɗa bathroom. Wonka tayi da ruwan sanyi sabida wani irin zafin da ake zabgawa, kai baka ce tsakiyar damuna bace. Al'wala tayi kana ta fito, wata tattausar doguwar riga ta zura a jikinta, kana tasa hijabi. Sannan ta shimfiɗa sallayarta. Bayan ta idar da sallan ta fara du'a'u Azkar tanayi tana lumshe idonta sabisa sam da baccin bai isheta ba. Koda ta ida addu'o'in ta shafa, a hankali ta miƙa ta ninke sallayar da hijabin kana ta ƙara ƙarfin A/C'n sannan ta kashe wutan ɗakin ta koma ta konta, Mustsuke idon tayi jin har wani yaji-yaji suke mata, gyara kwanciyar ta tayi take kuwa baccin yayi awon gaba da ita. Bakwai dai-dai Ummi ta fito asalin babban falon. Kitchen ta nufa jiyo motsi a ciki alamun Sara tazo kenan. Tana shiga kuwa ta samu Sara na fere Arish ga kuwa ruwan tea ta ɗora ta zuba citta kanamfari sunata ƙamshi. "Ina kwana Ummi". "Lfy lau Alhamdulillah Sara mun sameku lfy". "Alhamdulillah". "Masha Allah". Tace tana haurawa saman steps ɗin da zasu sadata da inda freezer yake. Buɗewa tayi, zabbi uku ta ɗauko kana ta sasu a wata ƴar madai-daiciyar roba. Kana ta dawo jikin sink wuƙa ta ɗauko sannan tazo ta fara gyarawa. Sheykh kuwa karfe bakwai da kwata ya fito cikin wasu tattausan farin yaɗin boyel riga da wondo da malum-malum yadin irin mai gidan dara-daran nanne. An watsa gariyar aiki da surfani Royal blue mai masifar kyau, hular kansa itama farace mai rashin Royal blue. Hakama takalmin shi half cover suma Royal blue ne masu azabar kyau, sajenshi ya kwanta lib gwanin burgewa. Jakar System ɗinshi ya rataya a kafaɗarshi ta dama, kana ya fito ya nufi Valli Hospital ɗinshi. Ƙarfe tara saura kwata Jalal, Jamil, Ya Jafar, Imran suka shigo falon. Jamil ne ya lumshe idanunshi tare dacewa. "Wow Ummi wannan ƙamshin na girki shine ƙungiyar yunwa, duk yawunmu ya tsinke." Dariya Ummi dake Dinning area tana jera Foodflaks bisa table ɗin tayi tare da cewa. "Alhamdulillah kuwa kun iso a Sa'a an gama kenan kun iso, maza ku ƙara so nan." Jalal dake riƙe da hannun Ya Jafar dake karanta Suratul Al-monafiqoon a hankali yake motsa laɓɓansa saɓanin da da yakanyi da ƙarfi. Zama sukayi baki ɗayansu, kana suka fara yin karin kumallon da kekkyawan girkin Ummi. Ita kuwa Ummi kitchen ta koma, ta sawa Sara nasu, kana tace. "Yauwa kije ki ɗan huta sai shabiyu sai kizo mu ɗaura na rana". Ɗaukan kularta tayi kana ta fita ta tafi. Ita kuwa Ummi ɗakin Aysha ta nufa jinta shiru-shiru bata fiton ba. Sallama tayi a bakin ƙofar, shirun da tajine yasata ƙarawa, still ba amsa, Sallama ta uku tayi kana ta tura ƙofar a hankali sannan ta kutsa kai ciki. Can ta hango Aysha konce lib tana sharan bacci cikin salama, murmushi tayi kana ta juya ta koma falon ta ɗebi nata abincin taci kana ta koma ɗakinta dan yin walaha. Su Jalal kuwa sai goma da rabi suka bar falon, ya zama shiru. Bayan fitansun ne Ummi ta fito ta kimtsa Dinning table tsab, sannan ta zauna a falon. Sha ɗaya dai-dai Aysha ta farka daga baccinta mai cike da mafarkai, bathroom ta kuma shiga, ruwa ta watsa sabida zafin da akeyi. Tana fitowa ta zauna gaban dreesing mirror body lotion ɗin ta mai ɗan karen kanshi ta shafa, kana ta ɗanyi light mackup akan Kekkyawar fuskarta tayi kyau sosai kuwa, wata atamfar Super Engla mai kyau, green, red, and white color, yanada zanen tsintsiya a jikinshi ɗinkin doguwar rigace takoyi dabas a jikinta gwanin burgewa, ɗan kwalin ta murza a kanta irin ɗaurin mai stpes ɗinnan sosai fuskarta ta fito ras, ta kitse jelar gashinta ta konto bayanta, gyale ja ta yafa turare ta fesa, sannan ta fito ta nufi falon tana ɗan hamma alamun yunwa. Ummi na ganinta ta mike zaune tare da cewa. "Sai yanzu". Gefen Ummi ta zauna a ƙasa bisa carpet tare da cewa. "Eh Ummi gajiya. Ina kwana". Fuska a sake tace. "Lfy lau Alhamdulillah gsky kam kinsha bacci". Kai ta rausayar tare da yin wata hammar, miƙewa Ummi tayi ba tare da tayi mgna ba, ƴan kananun Foodflaks ɗin da ta zuba mata breakfast ɗin ta jera a tray da flaks ɗin tea da plate spoon and cup. Gabanta ta ajiye kana tace. "Yauwa ga abinci maza kici ki shiga kitchen ki shiryawa Sheykh nasa karin dan inaga ya tafi asibitinshi". Jawo tray'n tayi tare da cewa. "Toh". Soyeyyen dankali da kwai ta zuba a plate kana ta haɗa tea sannan ta ɗan sa ferfesun zabbin kaɗan kana ta faraci suna, hirar bikin haron. A nan Safiyyah ma ta kira nan akayi yar hira da ita. 12:00 Sara ta shigo. "Ina kwana Aunty". Tace tana kallon Aysha, cikin sakin fuska tace. "Lfy lau Alhamdulillah Sara ya gida". Alhamdulillah itama tace. Tray'n ta tura mata gabanta tare da cewa. "Yauwa muje kitchen ki ɗan tayani aiki Arish zaki ɗan fere min kaɗan. Sai ki gyara min kayan miya." To tace tana muƙewa rabi bayanta. Itama Ummi bayansu tabi, ita ta fara aikin Lunch su kuma suna aikin na Sheykh. Jan nama mai kyau ta ɗiba tayi musu yanka yan mitsi-mitsi ta wonkesu kana ta juyesu a tukunya, tasa al'basa da Curry Maggi kanamfari citta tafarnuwa kaɗan da dai sauran kayan ɗan-ɗano ta rufe tukunyar bayan ta ɗaura a wuta, Bayan an fere mata dankalin ne, ta amsheshi tayi mishi ƙananun yanka, sannan ta amshi tattasai, attaruhu da al'basa, da Sara ta jajjaga mata. Ta ajiye a gefe tuni naman nan yaketa sulala yana zuba ƙamshi yayi lugub. juye naman da ruwan tayi a wani ɗan kwano na tangaram kana tasa mai a tukunyar ta meda kan wuta. yankekken al'basa ta watsa a man take ya baza ƙamshi a Side ɗin gaba ɗaya, kayan miyar tasa ta soya ya soyu da kay, sannan tasa ɗauki ruwan naman nan da naman ta juye ciki. Kana ta rufe sannan ta ɗan ɗauko maggi da gishiri ɗan ƙanƙani ta watsa ciki. Sannan ta rufe, wata ƴar ƙaramar tukunya ta ɗaura tasa ruwa kaɗan kana tasa kwai guda bakwai ciki kana ta rufe. Sannan ta ɗauko sufageti rabin ledar ta karya tasa a cikin haɗin tukunyar. tare da watsa dankalin nan a ciki sannan ta maida ta rufe. Tukunyar kwan nan ta buɗe ganin sun dafu ne yasa ta sauƙesu, ta tsanesu kana ta sasu a plate. ɗan motsa taliyar da dankalin tayi kai ta gyaɗa ganin yayi yadda takeso naman ya wadaci girkin sosai, Kwan ta fara ɓarewa, saida ta baresu fes kana, ta rufesu gefe, buɗe tukunyar taliyar tayi ganin yayi dai-dai da Dan ruwa-ruwane yasa ta ɗauki caras da al'basan da ta yanka tare da dafaffan kwai ɗin ta sasu ciki. sannan ta rufe ɓol-ɓol yake wani kekkyawan ɓararraka. Wata kekkyawar Foodflaks mai marfin glass ta ɗauko ta fara ɗiban taliyar gefe-gefe tana sawa a wani kekkyawan kwano gudun kada garin sawa a Foodflaks ɗin ya ɗan ɓata kular, daga cikin kwanon ne ta juye a kular sannan ta dawo ta yaɗe al'basa da caras da kwan da namomin ta jerasu saman kular kana tasa marfin ta rufe. Sosai tsarin yadda tasa abincin yayi masifar kyau. Sauran na tukunyar ta sawa Sara a plate da kwai ɗaya da Nama dasu karas ɗin sauran kuma ta sawa Ummi shi a wata ƴar kula. Cikin Murmushin Ummi tace. "Gsky kam Aysha koda a ƙoshe nake zanci girkin nan". Murmushi tayi tare da ɗauko lfaks ɗinshi da Ummi tasa mishi tea, kasan cewar ɗan ƙaramine yasa ta jerashi kan tray kusa da kular, ferfesun da Ummi tayi ta ɗan ɗuma tasa mishi a ƙaramar kula, kana tasa plate, cup, tea spoon and fork. ta kimtsa komai, kana ta tura tray'n can gefe, sannan ta matso kusa da Ummi tana cewa. "Ummi miyan me zakiyi mana". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Ɗanyar ƙuɓewa". Da sauri tace. "Ummi yaushe zamuyi miyar kase". Cikin dariya tace. "In sha Allah gobe zamuyi". Allah ya kaimu tace cikin jin daɗi. A hankali yayi parking gab da bakin ƙofar falon nasu, Allah ya sani ya gaji ga yunwa. A hankali ya fito, dai-dai lokacin kuma Jamil da Affan suka iso wurin. Affan ne yasa hannun ya amsar mishi jakar system ɗinshi. Tare da ce mishi. "Sannu da dawowa Malam". Kai ya gyaɗa musu, yayi gaba kana suka bishi a baya. Da sallama a bakinshi ya shiga. Suna shiga kai tsaye Side ɗinsa ya wuce, Affan na biye dashi a baya. Jamil kuwa kitchin ya nufa yana cewa. "Salamu alaikum Ummi". Da sauri ya iso kusa da Ummi. "Ummi me kuke dafawa haka naketa jin ƙamshi ya ƙare zancen yana jan kular dake kusa da Ummi. Yana buɗe wa yace. "Kai badon a ƙoshe nakeba da nayi tafiyar ruwa da kular nan". Dariya Ummi tayi shi kuwa cewa yayi. "Dan Allah wa akawa wannan girkin?". Da sauri Ummi tace. "Hammanku". Juyowa yayi ya kalli Aysha tare da cewa. "Uhum son kai. To ya dawo sai a kai mishi tare muka shigo". Murmushi Aysha tayi tare da cewa. "Ba ni naiba Ummi ce ta mishi". Dariya sukayi duka, ita kuwa Ummi kallon Aysha tayi tare da cewa. "To ɗauki ki kai mishi, kinga fa ɗaya tayi". To tace tare da ɗaukan tray'n ta nufi Side ɗinsa. Ummi da Sara kuma sukaci gaba da aiki Jamil na zuba musu surutu. A hankali tayi sallama tare da kutsa kai ciki jin muryar Affan a ciki yana surutu shi ɗaya kai kace zarerrene shi kuwa Sheykh bakace yana falon bama sai dai kaji yana cewa. "Uhmm, uhum, ehh, ko?". Iya amsar kenan. Ganin suna tsakiyar falon ne yasa ta iso tsakiyar falon, a hankali ta sunkuyo ta ajiye tray'n bisa santa table dake tsakiyar falon. A hankali ya ɗago idonshi ya zubasu kanta, da sauri ya juyo ya kalli Affan ajiyan zuciya ya sauƙe ganin Affan ba ita yake kalloba duk da ita yakewa mgn, amman wayarshi yake latsawa. wuyan rigarta da yake mai faɗine ya samu nasarar baiyana raɓin ƙirjinta a woje sabida sulewar da gyalenta yayi. murmushi ta ɗanyi jin Affan na cewa. "Ƙaro plate da spoon Aunty Aysha nima nan yunwa nakeji". Cikin tsokana tace. "Ina Maman Amal". cikin kwaɓe fuska yace. "Uhum ita kuwa yar zuriya tana can wai suna auren ƴar autarsu Zeenart". miƙewa tayi kana ta ɗan kalli Ya Sheykh haɗe fuska yayi tare dasa yatsarshi kan ƙirjinshi yaja kana ya nuna mata ƙirjinta da idonshi sannan ya nuna mata Affan da babbar yatsarshi wanda yayi alamun kamar gashin girarsa yake kwantawa. Da sauri ta janye idonta kanshi kana ta gyara gyalenta. Sannan ta juya ta ɗauko plate sannan tazo ta zuba musu. Kana ta juya ta fita sabida wani irin mayataccen kallo da Ya Sheykh ke cilla mata. A hankali Sheykh ya lumshe idonshi lokacin da yasa abincin a bakinsa taunawar da yayi yaji ɗan-danon ya sashi jin kunnenshi na amsa amo. Affan kuma haɗiye lomar dake bakinshi yayi tare da cewa. "Kai abincin yayi daɗi Malam jolof ɗin kwai ne ko na dankali ko na taliya ko daima jolof ɗin nama ne?". Murmushi Sheykh yayi tare da kurban tea kana yace. "Ko zan riƙe maka takalminka kaje kayi tambaya ne?". Dariya Affan yayi tare da cewa. "Wallahi ba santi bane". hannusa yasa ya ɗan make ƙeyan Affan kana yace. "Kai ana zafi a garin nan ƙara gudun A/C'n nan ɗazu da zan fita na rage." Mikewa yayi tare da cewa. "Gsky ana zafi koda yake naji ɗazu Gimbiya Aminatu na cewa yauwa kwana goma kenan ba'ayi ruwan samaba jiya har roƙon ruwa aka fita". Ya ƙare zancen yana dawowa ya zauna kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "Har kwana goma, to Allah ya bamu mai Al'barka mai cike da ni'imomi". Amin Amin Affan yace kana sukaci gaba da cin abinci. Ita kuwa Aysha kitchin ta koma, nan suka ƙarashe aikin kana suka shirya komai a Dinning table, sannan Sara ta tafi. Ummi kuwa da Jamil suka zauna a falo. Ita kuwa Aysha bedroom ɗinta ta, shiga. Bathroom ta shige sabida, wani shegen fitinenne fitsarin da takeji. Bisa toilet ɗin ta zauna tare da lumshe idanunta, sabida jin daɗin juye nauyin mararta da takeyi. Bayan ta gamane, tayi amfani ruwan ɗumi. Sai kuma ta kwabe dan zafin da takeji tace bari ta ɗan watsa ruwan sanyi lumshe idonta tayi lokacin da ruwan sanyin ya sauƙo jikinta, kana dai-dai lokacin ta tuno mafarkin da tayi da safiyar yau, da sauri ta rumtse idanunta gam sabida a fili take ganin yadda Sheykh yayi ta murzata a mafarkin da kuma irin kukan da tayi sabida azabar da ya azabar da ita da sauri ta ware idon da kyau sabida sai takega kamar zai shigo yanzune ya ritsa da ita haka yasa taci gaba da wonkon da sauri-sauri. Cikin tsananin isa da izza da tsaurin ido, take taku har zuwa tsakiyar falon kana hadimanta na Binta a baya. Tsakiyar falon ta tsaya tare da watsawa Ummi da Jamil ido dogon tsaki taja tare da cewa. "Ina yake ɗan masu fiffigen!?". Da sauri Jamil ya miƙa tsaye tare da watsa mata wani irin mugun kallo mai cike da tsana yace. "Baya buƙatar ganin irinku da ko sallama baku iyaba". Cikin tsawa da ɗaga murya tace. "Rufe min baki ƙaramin kwaro, ka bari inyi da shi jan wuyan naku". Da sauri Sheykh ya miƙe tsaye jiyo muryar Gimbiya Saudatu a tsakiyar falonshi. Affan ma miƙewa yayi da sauri kana yabi bayan Sheykh daya nufi falon da sassarfa. Yana fitowa Gimbiya Saudatu ta gyara tsayuwarta tare da buɗe al'kyabbar jikinta kana tace. "Yauwa al'huda-huda sarkin karatu. Zo nan zo ka gayawa wannan ɗan tayin ƙanin naka cewa. Duk lalacin mutun ya iya sallama amman banda tsuntsaye su sai dai su gani anayi, gwarama tsuntsun da ba zunibi ne ya maidashi tsuntsuwar ba dama haka Allah ya halicc...". Cikin wani irin tsananin tafasan zuciya da tuƙuki da ciwo a rai. Sheykh yayi mata wani razanenne tsawan da saida tayi tsalle ta koma baya kaɗan. Tsawar daya danna matane yasa Aysha fito da sauri tana mai gyara ɗaurin ɗan kwalin doguwar abayar da tasa yanzu. Cikin rawan jiki yake taku har gabanta. Ummi da Affan da Jamil kansu jikinsu kerma yakeyi. Jalal dake Side ɗin su ma yajiyo sautin muryarsa hakane yasa ya nufo falon da sauri. Cikin azabar fushi ya nunata da ƴar yatsarshi manuniya murya na rawa yace. "Duk tsuntsuwar da kika gani Allah yasan da zamanta, ki kuma sanni wannan tsuntsuwar ta fiki daraja har gaban Allah". Cikin jajir cewa da ƙarfin hali ta ɗan ja da baya tare da cewa. "Eh lallai kam ta fini har gaban Allah mana tunda girman zunubanta da jafa'inta yasa Allah ya nuna mana ikonsa da aya a kanta ya sauya mata halitta daga mutun zuwa tsu..". Wani irin zabura Ummi, Affan, Jamil, da hadiman Gimbiya Saudatu Sukayi sabida wani irin azabebben ihu da ta kurma da karfi sabida wasu irin gigitattun tagwayen maruka da Sheykh ya yarfa mata da hannunshi. Wanda sukayi nasarar tafiya da jinta da ganinta. Kanta ya sake nufa da azama alamun zai tabketa da iyakar iyawarsa Cikin rawan jiki Ummi tace. "Sheykh kayi haƙuri barta kasan hannunka". Ina wani marin ya kuma yarfa mata wanda saida taji wani fitsari ya tsarto mata. Ihun data kurma yayi dai-dai da kife kanta da tayi da jikin kujera. Cikin wani irin azama da sauri haɗi da kiɗima Aysha tayi sauri ta nufi gaban Sheykh sabida ganin baya cikin hayyacina. Affan da Jamil da sukayi nufin riƙeshi ne ya yarfawa maruka wanda yasa suka ja da baya. Cikin azama tasha gabanshi tare dasa hannunta ta riƙo hannunshi da ya ɗago zai mari Gimbiya Saudatu, cikin azaban fushi ya juyo ya kalleta da rinannun idanunshi. Da sauri ta kuma ƙara riƙe hannunshi tare da matsoshi kana murya na rawa tace. "Yan Sheykh! Kayi haƙuri". Fusge hannunshi yayi da ƙarfi ya nufi kan Gimbiya Saudatu domin idonshi ya rufe rib baya ji baya gani kamar yadda itama Gimbiya Saudatu idonta da kunnenta suka dena aiki kana fitsari ke tsiyayo mata. Da sauri Aysha ta kuma shan gabansa, kawai sai ta faɗa jikinshi ta ruggumeshi gam-gam a jikinta, cikin rauni take cewa. "Yah Sheykh ka bari, kada ka kulata Please Yah Sheykhhhh kada ka sake barin hannunka mai daraja da kullum yake cikin taɓa al'ƙur'ani mai girma ya taɓa fuskarta kada ka bari fuskarta ta samu darajar da hannunka zai taɓata. Kar-kar haka jikinshi ke rawa da tsuma tamkar mazari, yana mai jiyo amon sautin muryar Aeech cikin kunnuwansu. Ita kuwa Aysha a hankali tasa tafin hannunta ta tallabe gefe da gefen fuskarshi ta karkatoshi gareta, cikin sanyi da tattausan lafazi tace. "Mai hankali keyin mgn ya dami mutane ba, majanuniya irinta ba. Bata da ma dafa, ita fa bushiyace mai baya kamar allurai, Please kada idonka ya sauƙa a kanta". Ta ƙare mgnar tana jan hannun sa na dama tana ja ta nufi Side ɗinsa. Cike da mamaki Ummi, Affan, Jalal, Jamil, Hadiman Gimbiya Saudatu suka bisu da ido ganin ya bita a baya, tuni ta sarrafa fushinsa. Ita kuwa Gimbiya Saudatu har yanzu lalube takeyi wanda yasa Affan da Jamil murmusawa dan sai tafi kyau da makanta. Ita kuwa Aysha Kai tsaye har bedroom nashi ta wuce riƙe da hannunshi suna shiga ta faɗa jikinshi. Wani irin rumtse idanunshi yayi da azaban ƙarfi tare da ruggumeta tsam a j...! Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 zaku turo ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276. Bana son VTU in kinyima ni ba ruwana. In ya kama dole ma baki da damar tura kuɗin ta Account ɗina to katin mtn zaki saya ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsapp 09097853276. Gareku *Murmushi group* ngd da halaccin ku, zumuncin kenan. By *GARKUWAR FULANI* [3/16, 9:48 PM] +234 806 559 0880: A jikinshi, ya matseta da ƙarfi, sabida tsananin fushin da yake ciki da tafasar da zuciyarsa keyi, ji yakeyi tamkar ya matseta ya medata cikin jikinshi kanta ya danni zuciyarsa ko zaiji sassaucin. Ƙuna da ƙuncin da kalaman da Gimbiya Saudatu ke jifarshi dashi da mahaifiyasa dasu. Haƙiƙa ita kaɗaice mutun da ta samu nasarar gano abinda ke ta'azzara fushinsa har ya kasa control ɗin kanshi ta tunzurashi. Wani irin wahaltaccen numfashi Aysha ta fesar a hankali sabida jin wani fitinenne rugguma da yayi mata tamkar zai gamesu ya cure jikinsu wuri ɗaya. Gaba ɗaya jikinshi rawa da kerma yakeyi tamkar mazari. Cikin fizgo numfashin ta kwantar da kanta bisa ƙirjinshi dai-dai kan ƙahon zuciyarsa, Kana tasa hannun ta saƙalo wuyanshi, ta ware yatsunta manya tana yin sama da ƙasa dasu a kan tattausan sajensa Cikin sanyi tare da muryar kwantar da hankali tace. "Indai har ikon Allah kan iya yaye duhun dare da hasken rana ya meye gurbindun. To tabbas yaye baƙin ciki i zuwa farin ciki a zuciyar bawansa al'amarine mai sauƙin gaske. Abin sani kawai shine su mumanai girman jarrabawa ko ƙalubalen rayuwa baya sasu fidda tsammanin samun rahamar ubangijin taliƙai." Murza kanta ta kumayi bisa ƙirjinsa sabida tanajin wuya da zafin ruggumar da ya mata cike da fushi. Cikin sassanyan murya tace. "A shawarce kayi ƙoƙarin jagorantar zuciyarka, kayi baya da lamuran kowa ka ruggumi naka. Sabida kana zagaye da Magauta makusanta yau da gobe ita ce zata ganar da kai abubuwa da yawa, ka fuskanci magautanka ka dena dukan dungu." Mutsu-mutsu ta farayi a jikinshi sabida kalamanta na ratsashi kuma suna sashi zafafa ruggumar da yayi mata. Koda yake hakan baya rasa nasaba da hautsunewar kwanyarsa a kan kalamanta. Cikin ɗan buɗa murya taci gaba da cewa. "Kafin ka yarda da mutane to ka rinƙa morar Kekkyawar ƙwaƙwalwarka mai tarin basira da nazartarsu, ka dena yarda da mutun a bisa fuskarshi ta zahiriya. Kafin ka buɗe musu zuciyarka ba basu kekkyawan mazauni na mutane masu amana. Da yawan mutane dake da kaifin basira da iya tsara zance, har su sanyaya zuciyar mutun su sa mishi yardarsu a ransa. Da idan zaka shiga zukatansu zaka samu dafin guban dake zuƙatansu yafi na baƙin kumurci. Yah Sheykh kada ka damu da sauyin ɗan Adam tunda dama shi halittace mai rauni kan rikon amana da halaccin. Har kullum ka jingina da kanka, duk wanda ya nuna zai zamto tsanine a gareka, koma yake ganin shine tsaninka, nuna mishi tun kafin zuwasa gareka. A tsaye kake da ƙafafunka. Ta hakane zai san ƙaucewarsa bata nufin faɗuwarka." Ɗan tsagaitawa tayi ta ɗago kanta, ta kalleshi sabida jin yadda tattausan gemunshi ke shafa goshinta. Lip ɗinshi na ƙasa ya taune tare da girgiza gemun. Ya kuma rumtse idanunshi sai dai yanzu ya ɗan fara sassauta ruggumar da yayi mata. A hankali taci gaba da cewa. "Gimbiya Saudatu fa, ba belbela bace, Yah Sheykh ka nazarci kalamai na, ita bushiyace ko ince kunkuru. Zanfi son ka ɗauki zancenta dana mai taɓun hankali a ma'auni ɗaya. Ni dai ban san menene tsakaninku ba, sabida bani da damar sanin komai naka, da ace na sani da ni zanji da ita, sai dai batun gsky ka dena yankewa littafi hukunci a bisa bongon bayanshi, ka buɗe littafi ka nazarceshi shafi zuwa shafi kafin ka yanke wa littafin hukunci". A hankali ya buɗe idanunshi. Ya zuba matasu, tabbas yaji wani abu ya ɗarsun masa a zuciya, da zai samu yanzu duk suturan jikinta zai kekketashi ko zaiji sassaucin abinda yakeji. A hankali ya saketa. Kana ya zauna a bakin gado, Kanshi ya dafe da hannunsa duka biyu. Still har yanzu jikinshi kerma yakeyi. Ita kuwa Aysha juyawa tayi da sauri ta nufi falon, da nufin ta ɗauko mishi ruwan sanyi yasha ko zaiji sassaucin abinda yakeji a ransa. Ba ruwa Fridge ɗin nasa. Hakane yasa kai tsaye ta wuce babban falon. A can falon kuwa Affan da Jamil, sai dariya sukeyi ganin yadda har yanzu Gimbiya Saudatu taketa lalube a inda ta faɗi kasa dirsham. Tuni fuskarta ta haye ta kumbura tayi sintim. Hakama bakinta. A hankali ta fara bude idanunta, sai ta kuma rufesu. Ummi ce tayi murmushi mai cike da jin daɗin marukan da Sheykh ya yayyarfa mata. Cikin dakiya ta kalli hadiman Gimbiya Saudatu dake gefe suna murmushi suma tace. "Ku matso kuyi mata jagora". Da sauri Gimbiya Saudatu ta gyara zamanta tare da buɗe jajayen idanun nata, cikin masifewar murya tace. "Ke tafi daga nan Jakadiya mara galihu". Da sauri suka juyo suka kalli inda Aysha ke tsaye wacce ta nuna Gimbiya Saudatu hanyar fita tare da cewa. "Ki ɓace min daga nan, sabida mijina bazai juri jin ihun haukanki ba". Wani mugun kallo ta watsawa Aysha da jajayen idanunta kana tace. "To fitsarerriyar ƙauye, mai gaggawar tsiri da cewa miji Baba, waya kasa dake bare ki zari babban kashi". Jalal ne ya ƙaraso cikin falon, sabida yana son yaga matakin da Aysha zata ɗauka tunda ta iya fesa Hajia Mamansu ma rashin kunya. Ummi, Jamil, Affan, suma gyara zama sukayi. Ya Jafar da yanzu ya shigo ma gefen Jalal ya zaune. Ita kuwa Aysha cikin isa da ƙasaita ta iso gaban Gimbiya Saudatu kujerar dake gabantan ta zauna a kai wacce kujerar zaman Sheykh ne. Kai ta jinjina tare da cewa. "Ƙauye tushen kowa! Duk wanda bashi da ƙauye to bashi da asali kenan, shin baki san cewa da ƙauye akanyi birni ba. Shin ke kinma san me ƙalmar ƙauye take nufi kuwa?". Ƙafarta ɗaya ta ɗaura kan ɗaya, kana taci gaba da cewa. "Da fari Makka itace babban birni sabida Annabi Sallallahu alaihi Wasallama yana cikinta. Da yayi hijira ya koma madina kuwa sa madina ta zama babban birni mai cike da salama sabida addinin da kanshi ya koma can. In kin gane me ƙalmar ƙauye take nufi garin da babu addini ba ilimi garinda kafurai suke, shine ƙauye, domin duk inda hasken addini yake da ilimin da masana ilimin to sun zarta ace musu ƙauyawa, domin kalmar ƙauyawa tana nufin jahilai, niko nan da kike ganina gidanmu tushene na tsanƙaya yara da dattawa. Dan haka janye kalmarki ta fitsarerriyar ƙauye, gorinki bai samu muhalliba." Tsaki taja tare da cewa. "Baki san cewa kunne ya girmi kaka ba ko? To inma baki saniba Ni nan Aysha ina sane da labarin ƙuruciyarki da rashin kunyar da fitsarar da kikayi da taraddadin da kika sawa iyayenki na alamun lalacewa, dan haka kece fitsarerriyar. Kana kuma in kin mance in tuna miki ƙauyenmu ya zarta asalin naku ƙauyen girma da daraja ko dai kin mance inane asalin ƙauyenku. In kin mance in tuna miki, ita kanta masarautar Joɗa kafin a auroki cikinta zata amsa kiran suna ƙauyen da hausawan ke nufi. Yau da gobe shike sauya komi da kowa. Ni nan da kike gani da mgnarki data ɗaurerre a turu basu da maraba." Cikin masifa Gimbiya Saudatu tace. "Sai dai in kece mahaukaciyar". Dariya tayi tare da cewa. "A a akan bola nake". Miƙewa tsaye Gimbiya Saudatu tayi tare da fara gyara al'kyabbar jikinta, tare da cewa. "Zanyi mgninku zaku gane kurenku". Taɓe baki Aysha tayi. Ita kuwa juyawa tayi ta, fice hadimanta na biye da ita a baya. Dariya sosai Ya Jafar yayi wacce saida ta basu mamaki. Sheykh kuwa da tun ɗazu ya fito bayan yayi al'wala ganin azahar tayi, Tsayuwa yayi yana jin yadda Aysha keyi da Gimbiya Saudatu. Ita kuwa Gimbiya Saudatu ganinshi ne yasa ta miƙe maza ta fice. Miƙewa Aysha tayi da sauri jin muryar sa yana cewa. "Ku tashi kuje kuyi al'wala lokacin salla yayi". Juyowa tayi ta zuba mishi ido. Tabbas daga jin muryarsa da yanayin fuskarsa zai iya nunawa mutun cewa har yanzu a zuciye yake. Kallonta yayi a fizge kana yaja idonshi yayi gaba su Affan na biye dashi a baya. Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Dai-dai kenan yau dai Sheykh ya sawa Gimbiya Saudatu tsoron zuwa nan ta baje kolin rashin kunyar ta." Juyowa tayi ta kalli Ummi tare da cewa. "Uhummm Ummi an dukan tenki akefa aka bar jaki a ɗaure" Cikin sauri Ummi tace. "Kamar yaya?". Kai ta jinjina kana tace. "Muje muyi salla, Ummi". To tace tana mai son nazartan kalaman Aysha. Bayan sunyi salla ne suka fito falon. Suna zama Sheykh Jabeer ya shigo. Affan, Jalal, Jamil, Ya Jafar. Na biye dashi a baya. Su duk Dinning table suka nufa. Ummi na biye dasu a baya. Abinci ta fara zuzzuba musu. Shi kuwa Sheykh tuni ya wuce Side ɗinsa. Ita kuwa Aysha waya takeyi da Aminiyarta Rafi'a. Gyara zamanta tayi tare da cewa. "Rafi'a naji kamar an nememu a makaranta ko?". Ɗan gajeren tsaki Rafi'a taja tare da cewa. "Haka dai akayi ta cewa, to amman zancen Babu tushe, ance ƙaryane, gwamnatin ma bata nemi malaman ta zauna dasu ba." Ɗan murmushi tayi tare da cewa. "Alhamdulillah aini wannan yajin aikin da aka shiga yamin rana, kinga da wannan tsarkafeffen auren da aka liƙamin da ya sani a tsaka ba fita. To amman yanzu kinga duk muna a tare, zan kuma dage inyiwa Umaymah batun karatun nawa, kafin a nememu, in tayiwa Yah Sheykh mgna dai nasan zai barni." Tsaki Rafi'a ta kumayi tare da cewa. "Hegiya Aysha wato ke murna kikayi". Dariya tai kana tace. "Sosai ma kuwa". Kauda zancen Rafi'a tayi da cewa. "Yauwa su Ummey sun dawo kuwa? Ɗan na kwana biyu banyi mgn da suba." Jingina kanta tayi da jikin kujera kana ta fesar da numfashi a hankali tace. "Uhummm basu dawoba, Rafi'a bani da kowa nawa a kusa dani, tunda nazo gidan nan ban sake ganin Ummey naba gwara Bappa na da Ya Al'ameen sunzo da bani da lfy, ina kewar Junainah, ina kewarsu Yah Giɗi in na tunosu hankalina na tashi ina masifar kewa da son ganin Dedde na". Cikin tausayawa Rafi'a tace. "Ba komai Aysha kiyi ta musu addu'a in sha Allah zasu baiyana kuma Allah zai karesu. Su Ummey kuwa kwanaki da mukayi mgna da Junnu tace min wai sun kusa dawowa". Cikin sanyi tace. "Wasa sukewa Junnu, sabida ta matsa wai ita zata zo wurina kuma ita ko a gidansu Junaidu zata zauna". Dariya Rafi'a tayi tare da cewa. "Uhmm su Junainah manya wato ita fa da gaske har ranta take son Junaidun fa". "Sosai ma kuwa". Aysha ta faɗa tana kallon Ummi dasu Affan da suka miƙe tsaye alamun sun gama cin abinci. "Yauwa ga Umma wai tayi kewarki kwana biyu baku gaisaba". Rafi'a ta faɗa tana miƙawa Ummanta wayar. Amsa Umma tayi tare da cewa. "Aysha ya gida ya kwana biyu". Cikin jin daɗi tace. "Lfy lau Alhamdulillah Umma yasu Jamila". "Lfy lau suna gaidaki". Tace. Kana ta miƙawa Rafi'a wayar tare da cewa. "Tashi kije kinyi baƙo". To tace kana ta katse kiran sannan ta fita. Ita kuwa Aysha juyowa tayi ta kalli Ummi dake miƙa mata wayarta tare da cewa. "Amshi Umaymah ke son mgna da Sheykh ta kira wayarsa baya ɗagawa ke kuma ta kiraki taji kina waya." Amsa tayi da sauri kana ta kara a kunne tare da cewa. "Assalamu alaikum, Umaymah ina wuni". Umaymah dake kwance kan gado Mamma na gefenta, Murmushi tayi tare da cewa. "Lfy lau Alhamdulillah Aysha, ya gajiyar hanya?". "Alhamdulillah Umaymah inasu Hibba da Safiyyah". "Suna lfy, suna can Side ɗin Jannart". Ayyah tace, ita kuwa Umaymah gyara kwanciyarta tayi tare da cewa. "Yauwa Aysha Kaiwa Jazlaan waya". Da sauri ta miƙe tare da cewa. "To Umaymah bari in Kai mishi". Corridor'n ta shige, tana tafiya tana gaisawa da Mamma data amshi wayar. A hankali ta kutsa kanta cikin falon shiru, babu kowa sai hasken wuta daya karaɗe falon. Ƙofar bedroom ta nufa, tare da kallon wayar da taji kiran ya katse. A hankali tasa hannun ta tura ƙofar Bedroom ɗin tare da sallama a saman lips ɗin ta. A hankali ta meda ƙofar ta rufe, kana ta ɗan tsaya tana kallon yadda ya kunna wutan ɗakin gaba ɗaya hasken ya cika ko ina. Can ta hangoshi konce bisa gadonshi, ya kwanta a kife, kana babu riga ko singilet babu a jikinshi. Dagashi sai gajeren wondon, wanda yazo mishi har guiwarsa. Roban ya zagaye ƙugunshi ya manne gam. A hankali ta fara yin taku, tana matsowa, kusa da gadon. Shiru ta ganshi kwance lib. Ya kwantar da kanshi bisa pillow'nshi yana kallon gefe jikin gini. Cikin nitsuwa ta ƙaraso gabanshi, ido ta zurawa Kekkyawar farar fatar bayanshi, da take tamkar ta Balarabe. Sumar ƙeyanshi ta kalla, ido ta lumshe tare da ɗan sunkuyowa, bakinta ya kusanta da kunnenshi, a hankali ta buɗe baki tare da cewa. "Yah Sheykh!". Idonshi ya kuma lumshe da kyau, jin sautin zazzaƙar muryarta cikin kunnensa. Tun shigowarta idonsa biyu, dan ya gaza samun bacci, yaso ace ya sauyawa Gimbiya Saudatu kamanni ta yadda har abada bazata sake tsayuwa a gabanshi ta ƙalubalanci ƙaddarar mahaifiyarshi ta kalmar sakaiyar zunibinta ne ba. Ƙara manna kanshi da pillow'nshi yayi, jin alamun ta hau kan gadon. Ita kuwa Aysha a hankali ta rarrafo ta matso gareshi. Sunkuyowa tayi ta leƙa fuskarsa, tare da kiranshi. "Yah Sheykh". Shiru bai motsaba bai kuma amsaba, kana bai buɗe idanunshi ba. Idonta ta lumshe tare da buɗesu a hankali. Fatar bayansa ta zubawa idanun, zuwa ƙeyarshi da sajenshi. A hankali tasa tafin hannunta kan kafaɗarsa ta ɗan taɓa a hankali tare da kuma kiranshi. Still bai kulaba, yana dai jin yadda take taɓa kafaɗarsa, tana ɗan jujjuyasa, bai kulaba sabida jin yadda taketa ƙara matsoshi. Ita kuwa Aysha kwarmin bayanshi ta kalla, sai kuma ta ɗan ronƙofo kansa, Dai-dai lokacin kiran Umaymah ya kuma shiga. Da sauri ta amsa kiran wai sabida kada ya tashi daga baccin. "Umaymah nazo kuma yana bacci". Ta faɗa a hankali. "Okay to ba matsala barshi in ya tashi zamuyi mgna". Umaymah ta faɗi tare da katse kiran. Wayar ta ajiye gefen kansa, Cikin lumshe idonta, tasa yatsarta dai-dai bisa ƙugunsa, cikin tsakiyar kormin bayansa, a hankali ta fara yin sama da yatsar, tana jin taushin fatarsa. Shiru yayi tamkar bashi da rai a jikinsa, sabida wani irin masifeffen abu da yaji yana bin duk ta inda hudan gashin jikinsa yake, yana bin jininshi da jijiyoyin jikinsa. Yana aika saƙo zuwa ƙwaƙwalwarsa. Numfasa ne ya fara sauya fitarsa. Amman ita bata ganeba. Saima sa doguwar yatsarta ta tsakiya da tayi ta haɗa da manuniyarta tana yimishi tafiyar tsutsa a tsakiyar banshi. Yar-yar haka tsikar jikinsa ta zuba tare da mimmiƙe". Ɗaya hannun tasa bisa ƙeyarshi, yatsunta ta cusa cikin ƙeyar tasa, tana yamutsawa. So take ya juyo rigingine sabida, wannan zanen macijiyar take son ganin ya yake a jikinsa a yanzu. Wani irin fitinenne numfarfashi ya fesar a sanyaye tare da mirginowa ya juyo rigingine sabida bazai iya jure abinda takeyi mishiba. Wani irin tsalle tayi ta diro ƙasa, lokacin da ya juyo rigingine ya kwanta, tsuma jikinta ya fara sabida, yadda taga Sheykh ɗinsa tayi wani irin kumbura ta taso tayi sama tamkar zata faso boxes ɗin shi ta fito woje. Da sauri ta juya da gudu ta nufi ƙofar fita, sabida ganin yadda abun ya miƙe fiye da yadda ya miƙe na farin. Juya kwayar idanunsa yayi tare da binta da ido. Ganin ta fice a guje. Uhummm yace a bayyane kana cikin zuciyarsa kuma yace. "Zakiyi bayani ne yarinya". Juyawa yayi ya kifu rub da ciki. Daƙiƙu biyu tsakani, ya kuma juyowa rigingine tare da jan dogon tsaki. gefen damansa ya kuma juyowa amman ina duk yadda yayi babu damar kwanciya domin, ya rigada nitsiwarsa ta bar jikinshi. Ta gama hautsuna mishi lissafi. Ta birkitashi, ta tsokano mishi bananarsa ta hanashi salama. Da sauri ya miƙe tsaye, bathroom ya shiga. Yana shiga kuwa ya sakarwa kansa ruwan sanyi wai ko zaiyi ƙasa da fitinenneyar sha'awar data yunƙuro mishi, uwa zata kaishi ƙiyama. Madadin ta kwanta sai ƙara ƙarfi da miƙewa da cika takeyi. "Shehhhhyyt". Ya faɗa cikin hautsunewar kwanyarsa. A hankali ya fito, kana ya sauya boxes ɗin. Sannan ya fito. Komawa yayi ya kwanta amman ina abunfa yama wuce zatonsa. Haka ya rinƙa juye-juye bisa gadon. Kamar zaiyi hauka, to abin ya haɗe masa da yawa ga fushin da bai husheba, muddin ba ya samu ya kekketa wani abunba. Sabida shi in ya fusata koda abincine in zaici zakaga yana taunarshi da ƙarfi kamar dai yana hucewa a kansa. To yau kuma ga fushi ga Sha'awar data addadabeshi wacce yasan Aysha ce ta tsokano mishi ita. Gashi kuma in a fushi yake duk abinda zai yaken mishi da ƙarfi, hakane ya ta'azzara bukatarsan. Aysha kuwa tana fita kai tsaye ta wuce. Ɗakin Ummi sabida ta samu ba kowa a falon alamun su Affan duk kowa ya tafi uzurin gabansa Jalal wurin aikinsa ya wuce, hakama Jamil. Kwance ta samu Ummi a bisa gado tana bacci. A ƙasa ta kwanta, bisa carpet, Tana zazzare idanunta sabida gani take in ta shiga ɗakinta kamar zai biyota, sabida sosai ya firgitata da jarumtarsa. numfashi take fiddawa a hankali tare da lumshe idonta. Duk da bai taɓa nuna zaiyi wani abu da itaba. Taji tana tsoronshi yau, ko dan ganin fusatarsa da fushin da yake cikine. Oho. Ta faɗa a hankali. A haka dai itama bacci yayi gaba da ita. Shi kuwa Sheykh Jabeer karo na forko a rayuwarsa da sha'awar ta gigitashi ta sashi, fita haiyacinsa. Yayi wonka kusan sau huɗu tsakanin azahar da la'asar, sabida masifar da yakeji. Ƙishin da yakeji yasashi fitowa falonshi, Dinning area ya nufa. Fridge ya buɗe, babu ruwa ko ɗaya, sai madarar ruwa ta goggoni, Ɗaya ya ɗauka, mai sanyi kana yazo gaba show glass ɗin da cups da sauran ababen buƙatarsa suke ciki, Ya buɗe. Bula gongonin yayi yasa a cup kana ya ɗauki ɗan galan ɗin zuba dake wurin, ya cika cup ɗin. Spoon ya ɗauka ya jujjuya, kana ya zauna bisa Dinning chair. Kafa kanshi yayi ya shanye shi tas. Sannan ya miƙe ya koma bedroom. Bathroom ya wuce. Al'wala yayi bayan ya kuma watsa ruwan. Yana fitowa ya buɗe drower'rsa wani sabon boxes da yasan zai matseshi ya zaro, ya saka kana yasa wani gajeren wondon a kai sabida su danne mishi Sheykh ɗinsa dake son nunawa duniya a yunwace take. Farar jallabiya ya zura, kana ya ɗauko al'kyabba irin mai shara-sharan nan ita kuma Sky blue ya saka, sannan yasa hiramin ya fesa turare. Kana ya fito. Shiru falon ba kowa, haka yasa ya fice. Da ɗan sauri sabida lokacin yayi. Kiran salla ne ya tada Ummi daga baccin da ta ɗan yin. Da mamaki take kallon Aysha dake kwance itama tana baccin. Sauƙowa tayi ta tsaya kana ta gyara ɗaurin zaninta sannan, ta sunkuyo kan Aysha ta tasheta daga baccin. Da sauri ta tashi zaune tana waige-waige. "Tashi kije kiyi salla lokaci yayi". Ummi ta faɗa tana shiga bathroom. To tace tare da miƙewa ta nufi ɗakinta. Bayan sun idar da salla ne, suka fito a tare. Kitchen Suka nufa. A nan suka samu Sara tana jajjaga kayan miya. Ummi kuwa tukunyar data ɗaura tun kafin taje tayi bacci ta buɗe, bul-bul haka yake bararraka a hankali sabida ta rage wutan sosai yadda ko zata kai magriba ruwan bazai kare ba. Ƙara wutan tayi, tare dasa ludeye ta ɗan motsa ƴan ƙananan mulmulen tunkusa, wanda suketa bararraka da jan nama mai kyau da tantaƙwashi, sai ƙamshi yakeyi tuni saman ruwan ya cika da mai naman kab ya diddige ya marmashe. Juyowa tayi ta kalli Aysha tare da cewa. "Me zaki dafawa Sheykh?". Matso tayi kusa da ita tare da cewa. "Ba miyar kase za'ayi ba, ai yanaci". Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa. "Eh yanaci kam, bare an kwana biyu ba'ayi ba. Yanzu ɗebo nama mai ɗan yawa ki haɗa kifi kizo. Ki saka. Ke kuma Sara gyara min ganyen yakuwar nan." To sukace baki ɗayansu. Sara ta fara gyara yakuwar. Ita kuwa Aysha naman tukunyar dake gabanta ta buɗe wanda sulallen naman ke ciki. Juyewa tayi cikin tukunyar miyar, kana ta juya ya shiga Store bandan kifi ta ɗebo manya masu kyau. Ruwan ɗumi ta zuba a ciki ta wonke ta gyarasu fes. Kana tasa a cikin tukunyar. Ummi kuwa tukunyar tuwo ta ɗaura. A masallacin Masarautar Joɗa kuwa, ana idar da sallan la'asar duk, aka fara fitowa. Affan shi cikin gari ya wuce wurin aminansa Yusuf da Aryan. Jalal kuwa amsa kiran uban gidansu ya tafi. Jamil da Ya Jafar ne suka dawo gida. Suma Side ɗin su Jamil ɗin suka wuce. Ƴan tsirarun mutane ne suka rage a masallacin wanda Sheykh yana cikinsu. Mafiya yawa karatun al'ƙur'ani mai girma sukeyi. Wasu kuma tasbihi sukeyi wasu kuma a kwance suke suna sauraron sautin murya. Sheykh dake Karatun Alqur'ani cikin sassanyan murya. Biyar dai-dai Sheykh ya fito cikin masallacin da sauran mutane. Sabida wani irin duhu da ya fara yiwa illahirin garin Ɓadamaya ƙawanya. Bisa alamu wani babban hadarine ke ketowa tun daga ƙasa. Dimmmmmmm haka garin yayi, koda tsuntsaye baka ganin suna shawagi. Gaba ɗaya kowa hanyar gidansa ya nufa. Cikin nitsuwa bakinshi ɗauke da tasbihi yake tafiya. A Lamiɗo da Galadima suna gabanshi. A haka ya isa farfajiyar Side ɗinsa. Ya kai hannu zai tura ƙofar kenan yaga an buɗe. Gefe ya ɗan koma yana jiran mai fitowa. Sara ce ta fito riƙe da kuloli a hannunta da alamun sun gama girki kenan. Da sauri ta wuce saboda ganin hadarin. Batama lura dashi ba. A nitse ya shiga falon da sallama a bakinshi. Ummi ce ta amsa tare da juyowa ta kalleshi. Windows ya fara rurrufewa yana gyara labulayen. "Hadari ne a garin namu ko?". Ummi ta tambaya tana kallonshi. Kanshi ya jinjina tare da cewa. "Mai ƙarfi ma kuwa Ummi, ku rurrufe windows ɗin falon can da ɗakunan ku. "To". Ummi tace tare da miƙewa ta nufi falon. Gefen Aysha ya ɗan ratsa ya nufi kitchen. Zagayawa baya yayi, ya dudduba ko ina kana ya dawo. A inda ya barta a nan ya sameta. Tana ta danna waya. "Nace kije ki rufe windows ɗinki ko". Ɗan juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa. "A rufe suke". Kanshi ya gyaɗa kana ya wuce ya barta a wurin. Lib-lib haka gari ya ƙara ɗibkewa da duhu. In dai wuri babu hasken ƙwan wuta to ko tafin hannunka bazaka gani ba. Da sauri ta nufi ɗakin Ummi. A zaune ta samu Ummi tana gyara carbinta daya tsinke. Gefe ta zauna ta fara tayata. Shi ko Sheykh Windows ɗinsa ya rurrufe, tare da kashe komai na wuta dake falonshi da Dinning area, hasken wayarshi ya kunna kana ya wuce bedroom. Wutan ya ɗan kunna guda ɗaya hasken yayi dai-dai misali. Umaymah ya kira bayan sun gama mgna ya katse kiran. Sai ya zauna bakin gadonshi tare da jawo system ɗinsa. Gaba ɗaya hankalinsa ya meda kanta, shiyasa baima san lokacin ya tafi ba. Shida dai-dai, hadarin ya gama haɗa gangaminsa tako ina gabas da yamma kudu da arewa da tsakiyar sararin samaniya yayi baƙiƙƙirin Sai wani irin walƙiya mai masifar haske da akeyi tako wani sashin. Wani walƙiyane da a haska yazo tare da wani razanenne tsawa mai firgitarwa ne yasa Aysha wani irin zabura ta takure kanta cikin cinyoyinta tare da cewa. Innalillahi wa innailaihi rajiun". Itama Ummi abinda ta maimaita kenan sabida ta razana matuƙa. Sheykh kuwa hannunshi yasa ya rufe system ɗinsa tare da cewa. "Subhanallazee yusabbihu ra'adu bi hamdihi wal Mala'ikatu min khifateeh". Ya maimaita sau uku. Wani irin kumshe idonsa yayi lokacin aka kece da ruwa tamkar da bakin kwarya. "Allahumma saiyiban nafi'an". Ya kuma fara mai-maita wa. Aysha kuwa da sauran matsorata irinta ajiyan zuciya ta sauƙe, tare da cewa. "Kai ya Allah kasa mucika da imani, wlh Ummi ina tsoron walƙiya da tsawa a rayuwata, ina son yanayin damuna amman ina tsoronshi". Jingina kai da jikin gado Ummi tayi tare da cewa. "Tsawa abin tsorone ƴar nan. Nima kaina naji tsoron". Kai ta gyaɗa jinjina tare da cewa. "Tab Ummi kema kina tsoro". Sosai ma kuwa tace. Dariya suka sa. Ruwane fa ake tsulawa da iya ƙarfin shi. Miƙewa Sheykh yayi tare da kallon time a wayarshi. Shida har ta wuce. Gab ake da kiran sallan magriba. Gashi kuwa ruwa aketa fesawa babu kama hannun yaro. Tsaki ya ɗan ja tare da cewa. "Da ban dawo bama sai nayi salla a masallaci". Bathroom ya wuce. Al'wala yayi kana ya fito. Turare ya fesa, a jikinshi kamar yadda yakeyi koda yaushe. Falonshi ya fito, dai-dai lokacin aka kuma danna wata tsawar da ta kece da ruwa mai ƙarfi. "Ya ilahi". Yace lokacin da ya fito babban falon, shiru ba kowa sai hasken wuta. Sanyin dake ratsa jikinshi ne yake sashi cikin wata fitinar kuma. Baka iya jin sautin komai sai na ruwan shuuuhhhh. Ƙofar falon ya nufa, a hankali ya buɗe. Jingina kanshi yayi da jikin ƙofar yana kallon ikon rabbil samawati. Ruwane tako ina yake kwaranya. Ƙasa tasha ruwa ta ƙoshi. Tabbas in matsoraci zai gani zaiyi zaton ƙasar ma tsastsafo da ruwa takeyi. Magadanan ruwan duk sun cika tambul. Dole ya maida ƙofar ya rufe, sabida. Ruwan yayi yawanda in ya shiga kafin ya isa masallacin zai iya cutar dashi Allah ya sani baya son yayi salla shi ɗaya ba cikin jam'iba, gashi su Jalal ma yau duk basa nan ɗin. A nitse ya juyo. Falon Aysha ya nufa. Shiru ba kowa sai TV'n da suka bari a kunne. Kanshi ya ɗan juya ya kalli ƙofar ɗakinta, TV'n ya kashe sannan ya nufi ɗakin. Da sallama a bakinshi ya shiga, tsayuwa yayi a tsakiyar ɗakin, ganin ba kowa. juyowa ya ɗan yi kana, ya fito falon, ƙofar ɗakin Ummi ya nufa, a bakin ƙofar ya ɗan tsaya tare da cewa. "Assalamu alaikum". Da sauri Ummi tace. "Wa laikassalam, Sheykh ka shigo". Kanshi ya ɗan shafa tare da yin jim kaɗan kana yace. "Umm Aish tana nanne?". Da sauri Ummi tace. "Eh gata nan muna tare". Ta ƙare mgnar tana nunawa Aysha hanyar fita alamun taje. Shi kuwa Sheykh ɗan juyawa yayi tare da cewa. "Ummi magriba ta kusafa". Miƙewa Ummi tayi tare da cewa. "To Sheykh". "Aish". Ya kira sunan a mutunce. A hankali tace. "Na'am". "Kizo". Yace yana mai juyawa. Miƙewa tayi ta fito. Da ɗan sanɗa ta isa gefenshi tare da cewa. "Gani". Juyowa yayi ya ɗan kalleta sama da ƙasa kana yace. "Je kiyi al'wala kizo ɗakina muyi salla, bazan samu zuwa Masallaci ba". Cike da gamsuwa da mgnar sa ta ɗan karya wuya tare da cewa. "To amman zanyi wonka kafin nan". Kanshi ya gyaɗa mata tare da cewa. "To Kiyi sauri kada lokacin yayi baki fitoba". To tace kana ta nufi ɗaukinta. Shima ya wuce ya nufi Side ɗinsa. Kai tsaye bedroom ya wuce. Babban sallayarshi ya shimfiɗa musu a tsakiyar ɗakin kana ya zauna a wurin, tare da lumshe idonsa ya fara bita. Ita kuwa Aysha Kai tsaye bathroom ta wuce. Ruwa mai ɗan zafi sosai ta haɗa, bayan tayi Brosh wonka ta farayi mai rai da lfy. Sosai ta cuccuɗa jikinta lungu da saƙo kamar ko wani lokaci tana gama wonkan tayi al'wala kana ta fito. Tana fitowa ta wuce gaban dreesing mirror, gashin kanta ta taje ta gyarashi ta tubkeshi a ƙeyanta sabida saurin da takeyi bata tsaya kitse jelarba. body lotion mai ɗan karen ƙamshi ta shafa a jikinta, kana ta shafa humranta mai sassanyan ƙamshi. Kasan cewar yanayin Weather'n garin ya sauya ko ina yayi sanyi iska mai sanyi nata busawa tana kaɗawa da sassayan ruwane yasa. Ta saka dogon wondon blue jeans sai kuma tasa wani Baby top fari wanda ya lafe a jikinta yayi mata cib-cib kana ta ɗaura wani pink jacket wuyanshi da tattausan suma fari, sai dai jacket ɗin ba irin ƙattin nan bane ƴar cafalce dai-dai da jikinta kuma ya tare mata sanyin. Gaban dreesing mirror ta koma wasu turaruka masu ƙamshi guda biyu ta fesa. Kana ta zato wani ƙaton hijabinta Black blue mai ɗan karen kyau da sheƙi, ta zurashi har ƙasa ko idon sawunta bazaka iya ganiba. Sallayarta ta ɗauka kana ta fito da ɗan sauri ta nufi Side ɗinsa. Ganin baya falone yasa ta wuce bedroom da sallama a bakinta. "Wa laikissalam". Ya amsa mata lokacin da ta turo ƙofar ta shigo. A gogon hannunshi ya kalla tare da cewa. "Iso muyi lokacin na tafiya." To tace tare da ƙarasowa tsakiyar ɗakin. Sallayan dake hannunta ya kalla tare da taɓe fuska kana yace. "Duk sallayan dake ɗakin nan bazasu isheki bane sai kinzo da naki?". Girgiza kai tayi alamun a a. Hannunshi yasa ya amshi sallayar, kana ya juya ya fuskanci gabas. Ita kuma ta ɗan matso gefenshi ta tsaya daga bayanshi kaɗan. Ganin ta kimtsa ta nitsu yasashi tada kabbara. Masarautar Joɗa kuwa, an dai kira salla amman ba'a samu mutane da yawa ba sabida laruran ruwan sama. Bayan sun idar da sallan ne, sukayi addu'o'in kana sukayi nafila raka'a biyu, sannan suka zauna. Tasbihi ya ɗanyi kana ya gyara zamansa da kyau, Al'ƙur'ani dake kan durowar dake gaban wurin da yake sallan ya dauko, juyowa yayi ya fuskanceta kana ya miƙa mata. Kallonshi tayi tare da amsar ƙura'an ɗin. "Ki karanta inji yadda kira'arki take". Ya faɗa idonshi na kanta. Shiru ta ɗanyi tare da kauda idonta daga kan nashi. Cikin sanyi ta miƙo mishi ƙura'an ɗin". Ba tare da ya amsaba yace. "Bazakiyi ba, inji ki samu lada ba?". Kai ta jujjuya kana a hankali tace. "Zanyi". Cikin kauda kanshi daga kanta yace. "To bismillah". Miƙo mishi ƙura'an ɗin ta kumayi tare da cewa. "Ka riƙe min sai inyi kana duba min haddana yayi ko da gyara". Wani irin sassanyan numfashin da bai shiryawa bane ya subce mishi. Cikin nitsuwa yace. "Ba sai na duba mikiba, kada ki damu kiyi inaji in kin ɓata zan gane ba sai ina duba surar ba". Cikin sanyi ta ɗan ɗago idanunta ta kalleshi kana ta ruggume ƙura'an ɗin a ƙirjinta. Lumshe idonta tayi tare da cewa. "Wacce sura zan karanta?". Kanshi ya jingina da jikin gado kana ya zubawa fuskarta dake zagaye da hijabin ido a hankali yace. "Surar da kikafi jin daɗin haddarsa". Cikin nitsuwa tace. "Suratul Noor". Kanshi ya jinjina mata tare da cewa. "Bismillah". Kai ta rausayar ba tare da ta buɗe idonta ba, ta gyara zamanta kana a hankali tayi gyaran murya tare da cewa. "Aaoozubillahi minashaiɗani rajen. Mismillahi rahmaniraheem. (Suratu anzalnaha wa farad'nahah wa'anzalnaaa fihahhhhhhhhhhh Aayati baiyinati la'allakum tazakarun." Ida nunshi ya lumshe a hankali tare da sauƙe numfashi jin yadda ta bada taƙib a wurin fihahhhhhh, kana ta rufe ƙarshen ayar da bawa Wawun iya damarsa. A hankali ya buɗe idanunshi ya zubawa lips ɗinta su, sabida jin taci gaba da aya ta biyu. Karatun takeyi cikin sanin ƙaidarsa da bawa ko wanne harafi haƙƙinsa tsakanin ɗauri da wasalin sama dana ƙasa da kuma wurin ja mai shida da huɗu da uku. Sosai yake jin sautin zazzaƙar muryarta na ratsa mishi kunnuwa har zuwa ƙahon zuciyarshi. Kanshi ya jingina da gado yana jin yadda take fitar da Tajwid da kyau da fidda Qalqala, iglab, idgham, ikhfa'a Ghunna. A hankali ya ɗan ɗago kanshi lokacin da ta iso aya ta 31 gyaran murya ya ɗan yi, wanda yasa ta buɗe lumsassun idanunta da sauri. Kallon alamun tambaya ta mishi. Kanshi ya jujjuya tare da mata alamun taci gaba. Nannauyan numfashi ta sauƙe tare daci gaba. Kai ya sake ɗagowa lokacin da tazo aya ta 61 still yayi gyaran murya. Ci gaba tayi da karatun dan ta fahimci alama yake mata. Kasan cewar suratul Noor ayoyi 64 gareta. Aya uku ta kara kan na 61 da ya mata gyaran murya tazo ƙarshen ayar. Da sauri ta buɗe idonta jin yace. "Sadakallahul azeem". Kanshi ya jinjina tare dayin murmushi. Ita kuwa cikin sanyi tace. "Ɓata nawa nayi?, Yah Sheykh a gyara min?". Murmushi yayi tare da cewa. "Baki ɓataba kinyi ƙoƙari sosai". Cikin sauri tace. "To kuma naji kayi gyaran murya". Gyara zamanshi yayi ya fuskanceta da kyau kana yace. "A aya ta nawa da ta nawa nayi gyaran murya?". Hannunta tasa ta tallaɓe fuskarta tare da cewa. "Aya ta 31 da 61". Hannunsa yasa ya ɗan shafa gemunsa kana yace. "Ayoyin sun kasance ɗaya daga cikin dogin ayoyin da aka ƙiyasta tsawonsu dake cikin al'ƙur'ani mai girma". Kai ta jinjina alamun gamsuwa kana tace. "Ayyah, wato shiyasa lokacin da nake haddarsa aya ta 31 saida na kusan sati a kanta, bappa yayi ta faɗa wai nasa wasa a gaba". Kanshi ya jinjina kana yace. "Sosai ma kam gskyar Bappa kinyi wasa". Cikin sanyi tace. "Kai a kwana nawa ka haddaceshi?." Murmushi yayi tare da cewa. "A kwana bakwai sati ɗaya na haddace suratul Noor". Cikin ware ido tace. "Kai ai ƙwaƙwalwarka ta musamman ce Yah Sheykh." Miƙe tsaye yayi yana cewa. "Ko?". Eh tace tana kallon dunduniyar ƙafarshi. Wayarshi ya ɗauka, ɗan daddan nawa yayi kana ya kara a kunne jim kaɗan ya fara mgna. "Ayyah Ummi zanci gashinki". Murmushi Ummi dake zaune bisa sallaya tayi tare da cewa. "Kaza ko zabuwa?". Juyowa yayi ya ɗan kalli Aysha kana yace. "Zabuwa, Ummi ta gasu da kyau". Cikin sakin fuska tace. "To Sheykh bari inyi sallan isha'i". To yace kana ya katse kiran. Ya dawo ya zauna. Ummi kuwa har ta zauna sai kuma ta tashi. Ta nufi kitchen a cewarta kafin tayi sallan zabuwar ta sulala. A gudanta haka ta wonketa fese. Kana tasa a tukunta, sannan tasa al'basa, kanamfari citta tafarnuwa kaɗan sai kurry, sannan tasa Maggi da gishiri kaɗan, sannan ta ɗaura a wuta kana ta wonke hannunta ta koma ɗakinta. Ruwa kuwa har yanzu tsugashi akeyi kamar ba gobe. Tana gab da shiga falon ne ta jiyo muryar Jalal. "Ummi". Da sauri ta juyo tare da cewa. "Yauwa Jalal ɗaukar muku abinci tun ɗazu ku nake tunawa". Kanshi ya sunkuyar yana kallon yadda yake ɗigan ruwa. Dinning table suka nufa. Foodflaks ɗin ya ɗauka tare da plate kana ya juya ya fita da sassarfa. Yana fita Ummi ta meda ƙofar ta rufe kana ta koma ɗakinta. A can ɗakin Sheykh kuwa. Kallonta yayi tare da cewa. "Bappa ya baki tabsir a kan surar ne?". Da sauri tace a a. A gogon hannunshi ya kalla kana yace. "Kina son ki san abinda Allah madaukakin sarki yake cewa a Suratul Noor ɗin?". Da sauri tace. "Eh sosai ma." "To tashi muyi sallan isha'i sai in fassara miki ita ko a taƙaice". To tace kana ta miƙe. Bayan sun idar da sallan isha'i sukayi addu'o'in kana ta miƙe tayi shafa'i da wutri". Sannan ta zauna tana tasbihi. Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta kana ya meda kai yaci gaba da Addu'o'in. Ummi kuwa tuni ta fita tazo kitchen. Gashin tukunya mai masifar daɗi da ƙamshi tayiwa zabuwar. Bayan ta kwashe robon, ta sake sata ta hasata da kyau. Gaba ɗaya gidan ya cika da ƙamshi mai tada yunwa. A wani kekyawan Foodflaks tasa dangwaleliyar zabuwar kana tasa, romon mai cike da ɗan-ɗano da kayan ƙamshi a ƙaramar kula. Sassayan madarar shanu, ta haɗa da zuma ta gaureya kana tasa a flaks ɗin riƙe sanyi. Kamar yadda tasa yana son zabuwa da madara da zumar. Plate, cup, spoon, fork, knife, ta jera bisa plate ɗin kana ta kife ɗaya a kai. Sannan ta jerasu a tray. Sannan ta fito tazo ta ajiyesu kan dinning table, ita kuma ta ɗebi tuwo da miyar kasenta taci tayi haniƙan kana ta koma cikin ɗakinta ta ɗauki wayarta, ta kirashi ta shaida mishi ta gama yana kan dinning table. "Sannu Ummi ngd matuƙa Ubangiji ya biyaki da mafi kyawun sakamako". Yace cikin girmamata. Amin Amin tace kana ta katse kiran. Ita kuwa Aysha zaman jiran ya ida addu'o'in sa ne ya fassara mata surar take jira. Kallonta ya ɗanyi, kana yace. "Tashi muyi nafila". A hankali tace. "Nayi ai". Gyara tsayuwarsa yayi ba tare da ya kalleta ba yace. "Na sani ai ƙarawa zamuyi ko bakya son ƙarin lada". Kai ta jujjuya tare da cewa. "Ina so mana". "To taso muyi ba yawa raka'a biyu ne". Yace yana kallonta. To tace kana ta miƙa tsaye. Nafilan sukayi raka'a biyu kamar yadda yace ɗin kana sukayi zaman tahiya. Bayan sun sallame ne, duk suka gyara zamansu. Tasbihi ya ɗanyi kana a hankali yace. "Zo nan". Ya faɗi yana nuna mata gabanshi. A hankali ta ɗan musukata sai dai bata iso inda ya nuna matan ba. Kanshi ya kauda kana ya juyo ya fuskanceta da kyau. da sauri ta ɗan sunkuyar da kanta. ƙara matsota yayi har guiwowinshi na gogan nata. Da sauri yasa hannunsa ya riƙe nata ganin ta yunƙura zata ɗanyi baya. Cikin juya fuska ba wasa kuma ba tsanani yace. "Tsaya mana". Ido kawai ta zuba mishi. Shi kuwa a hankali ya ware tafin hannunsa na dama ya buɗa yatsunshi kana ya kife tafin hannun kan goshinta. "Uhhhmmm". Haka ta fidda wani ɗan sauti na tsoron jin yadda tafin hannunshi ya sauƙa a goshinta. Sama kaɗan yayi da hannun ya zama rabi na kanta rabi na kan goshinta. Babbar yatsarshi na kan babbar jijiyar kanta na gefen dama. Doguwar yatsarsa ta tsakiya tana kan jijiyar kanta na gefen hagu. Cikin ɗan ɗaga sauti kaɗan ya fara karanto addu'ar marabtar amarya ga ango. Addu'ar Neman Zaman lfy ce. *"Allahumma inni As'aluka min khairi ha wa khaira ma jabaltaha alaihi, wa a uuzu bika min sharri ha wa sharra ma jabaltaha alaihi".* Ma'ana "Ya Allah ina roƙon ka Al'khairin ta, da Al'khairin da ka Halicce ta akan shi. Kuma ina neman tsarin ka daga Sharrin ta, da kuma sharrin da ka Halicce ta da shi ko akan shi. Amfanin Addu'ar Idan ka yi ta. Allah zai cike Soyayyar da ke tsakanin ku 100%. Zai tsare Shaiɗanu da Miyagu daga cutar da zaman Auren ka da ita da sauran su... Wani irin nauyinshi mai yawa ta rufeta. Shi kuwa a hankali ya janye tafin hannunsa daga kanta, kana a hankali yaja ba ya koma mazauninsa. Jingina kansa yayi da jikin gado kana murya can ƙasa yace. "Ɗauko min abinci a can falo Ummi ta ajiyeshi bisa Dinning table ki kawo min shi nan ɗinan!". Da sauri ta miƙe kamar dama umarnisa take jira. Ƙofar fita ta nufa. A hankali ya bita da idanu har ta ɓacewa ganinsa. Meda idon yayi ya lumshesu. Yana mai jin zuciyarsa na bugawa. "Meyasa lokaci ɗaya rana ɗaya, zuciyashi da jikisa suka amince da ta zamo sutura a gareshi, shima ya zama sutura a gareta kamar yadda Allah maɗaukakin sarki yace. Ya akayi yakejin yau zai iya haɗa shimfiɗa da ita, meyasa ya yanke wannan hukuncin na tabbatar da ita matsayin matarshi ta sunna suturarsa?". Wani dogon numfashi mai sanyi yaja ya fesar, yana mai jin yadda iska mai sanyi ke ratsa fatarshi. Ita kuwa Aysha a tray'n ta ɗauka ta nufi falonshi da nufin tana ajiye mishi zata juyo. Tana shiga ta sameshi yadda barshi haka ta sameshi. Zaune, ta jiye tray'n a hankali, shi kuwa tuni ya miƙe tsaye. bakin ƙofar ya nufa, tsayawa tayi ta jira ya fita kafin ta fita. Can babban falon ya nufa, tana biye dashi a baya. Ƙofar falon ya rufe, tare da addu'a kamar kullum. Ya juyo kenan sai ya ganta tana ƙoƙarin shiga falonta, Yafitota yayi da hannunsa tare da cewa. "Zo". Yayi mgnar a hankali. juyowa tayi ta nufi inda yake a zatonta ko wani abun zai sa tayi mishi. Tana isa wurin yasa hannunsa a hankali ya kamo nata. Kana ya juya ya nufi Side ɗinsa bayan ya kashe wutan ko ina. Ita dai tana biye dashi kamar raƙumi da akala sai tsoronshi dake ƙara tsananta a zuciyarta. Suna shiga falonshi ma ya meda ƙofar ya rufe, nanne ta kalleshi a hankali tace. "Zanje in kwanta ne bacci nakeji". Kanshi ya gyaɗa mata alamar to. Wutan ya kashe da komi na wuta kana ya nufi bedroom ɗinsa da ita. suna shiga ya meda ƙofar ya rufe da key a hankali tace. "Zan tafi ɗakina". jawo hannunta yayi suka iso gaban tray'n kana a ya zaunar da ita shima ya zauna suka sa tray'n a tsakiya cikin hikima da ɗan sakin fuska yace. "Nawa kika sayi ɗakin ya zama naki?". Cikin kwaɓe fuska tace. "Ban saya ba". Kanshi ya ɗan sunkuyar kana yace. "Shine kuma kike cewa ɗakinki. Rau-rau tayi da ida nunta. Tuni sun ciko da ruwa. Ganin haka ne yasashi ɗan matsowa ta inda take kana a hankali yasa hannunshin ya jaw...! Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 babbancinsu a yawan posting ne. In special Group kikeso kiyi min TRANSFER ɗin 1k ɗin a asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, in kin tura sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276. Kuma yan 300 ta nan accutan ɗin zaku turo, ku turo shaidar biyanku ta whatsapp. In baki da halin turawa ta Account ki sayi katin Mtn na ɗari uku ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp 09097853276 bana son VTU ko transfer'n kati, in kinyi ba ruwana. Yan special Group Please bandaku a kati mtn ɗin ma. Ku ku bada a POS a tura. By *GARKUWAR FULANI* [3/17, 9:03 PM] +234 806 559 0880: Ya jawo hannunta na hagu ya haɗe da nashi hannun. Kana a hankali yace. "Kici abinci sai muje in rakaki, tunda bakya tsoron kwana ke ɗaya ko?". Da sauri tace. "Eh bana tsoro". Foodflaks ɗin ya buɗe tare da cewa. "To kici abinci tukun, ba kyau kwanci da yunwa". A hankali tace. "Na ƙoshi ɗazu da muka gama girki naci abinci". Plate ya ɗauka. Kana ya buɗe kular, yasa Fork ya soko zabuwar ya ɗaura kan plate ɗin kana yace. "Me kuka dafa?". "Tuwo ne". Ta bashi amsa a gajarce da kuma yanayin tsoronshi. "Miyar me". Yace mata yana mai kallon ƙwayar idanunta. "Miyar kase ne". Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta kana yace. "Uhumm shine ko ki kawo min". Shiru tayi, shi kuwa ƙaramar kular ya buɗe. romon ya ɗan sa a gefen plate ɗin. Kana yace. "Uhumm duk wanda yaci shi ɗaya shi ɗaya zai mutu ai". Ya ƙare mgnar yana murmushin gefen baki". Still shiru tayi. shi kuwa, cikin son sama mata nitsuwa dan ya lura ta firgita da shi. A nitse yace. "Rowa ba kyau". Cikin sanyi tace. "Ai nasa maka, yanzuma na sameshi a can, in kawo maka in kana so?". Kanshi ya jujjuya kana yace. "A a, saida na roƙa meyasa tun ɗazu baki kawo min ba". Ɗan kallonshi tayi a fakaice kana tace. "To ai naji kace Ummi ta gasama zabuwa". Kai ya jinjina alamun gamsuwa kana yaci gaba dasa Fork yana saɓule kasusuwan zabuwar yana turesu gefe sai tururi da ƙamshi naman yakeyi. Ruwa kuma har yanzu tsugashi akeyi. Saida ya gama saɓule sokokin ya zare ƙasusuwan ya medasu gefe, kana ya tura mata plate ɗin gabanta, sannan yace. "To muci, sai ki tafi tunda bakya tsoron Jahan yazo ya sameki a ɗakinki ke ɗaya." Cikin sanyi tace na ƙoshi". Kanshi ya ɗan kauda kana, ya fara cin naman da sauri-sauri kuma yana taunan da ɗan ƙarfi kamar dai yadda ko yaushe inda fushi a zuciyarsa haka yake komai. Ta fuskar ibadace kawai fushinsa baya tasiri bare ya sashi yin abu da gaggawa ko da karfi. Duk fushin da yake ciki, in dai ya fuskanci abu na ibada ne to a take nitsuwarsa ke dawowa. Kaɗan yaci kana ya tsiyayi sassanyan madara da zumar nan, cikin kofi, ya kafa kai bai ajiye ba saida ya shanye. Kana ya sake tura mata plate ɗin gabanta, sannan ya cika mata kofin da madarar zuma, kana ya miƙe tsaye tare da cewa. "Zan shiga wonka in kin cinye kafin in fito to na miki al'ƙawarin zan buɗe miki ƙofar ki koma ɗakin naki, in kuma kinƙi cinyewa to dole a nan zaki kwana". Yana faɗin haka ya shiga bathroom. Shiru tayi tana nazartan kalamansa, da kuma abubuwan da suka wakana. Wannan nafila raka'a biyu da addu'arga da yayi ya ɗura mata ruwa a cikinta, ya kuma kaɗa mata hanjin cikinta tsoronshi ya rufeta. Ta lura gaba ɗaya ya sauya komanshi na yau wani sabon al'amari ne. Jawo plate ɗin tayi sabida tasan ya fita sanin girman al'ƙawari da mahimmanci cikashi. Fork ɗin tasa tana sokan naman tana sawa a baki tana tauna tana haɗiyewa, sabida ɗanɗanonsa yayi mata daɗi. Ci takeyi tana kallon ƙofar Bathroom ɗin. A hankali ta ajiye fork ɗin kana tasa hannunta ta ɗauku cup ɗin madarar, tasa a baki. Ido ta lumshe sabida wannan shine haɗin da tafi so. Sabida dashi Ummey ta raineta. Zuƙeshi tayi har kusan rabi. Kana ta janyeshi daga bakinta, tare da buɗe idonta data lumshe cikin sanyi tayi wata gyatsa mai tabbatar da ƙoshi. Dai-dai lokacin kuma ya fito daga bathroom, daga ƙafarshi ta fara kallo har zuwa sama. wasu tattausan riga da wondo masu masifar kyau Sky blue ne mai ɗigo-ɗigon fari. Wondon dogone har ƙasa rigar kuma irin mai hular manne ya kwantar da hulan a bayanshi bisa kafaɗunsa. Hannun rigar yan dadai. Wani irin ƙamshi yakeyi mai masifar daɗin shaƙa. Sejenshi yayi lib sai sheƙi yakeyi. Kanshi ya ɗan jujjuya kana yace. "Kada ma kiyi ta turawa a dole, barshi kawai kin faɗi sharaɗin. Janye plate ɗin yayi kana ya juye naman cikin kular. Cikata mata cup ɗin yayi da madarar zuman kana ya ture tray'n can gefe, sannan yace. "Shanye madarar kizo ki hau gado ki kwanta". Tura baki tayi alamun zatayi mgna, sai kuma tayi shiru ganin ya shimfiɗa sallayarsa can gefe, ya kuma ɗauki al'ƙur'ani, alamun karatu zaiyi. Hakane yasa tayi shirun. Shi kuwa karatu ya fara kamar yadda ta zata. A hankali tasa kofin a baki taci gaba da shan madarar, tanayi tana lumshe idonta, sabida haɗin yayi iri ɗaya sam dana Ummeynta kamar itace ma ta haɗashi. A hankali ta shanyeshi tas, kana ta ajiye cup ɗin kan stoll dake gaban gadon. Zama tayi tana jin ƙira'arsa mai daɗin sauraro. Ƴar ƙaramar wayarshi dake gefenta ta kalla, ƙarfe goma harda rabi. Zuwa yanzu kuma ruwan saman ya tsaya cak sai walƙiya da rugugin da akeyi tako ina wanda haka ke nunin da hadarin bai gama hucewa na zubda ruwanba, ko ma wani hadarin ne ke tasowa daga ƙasa. Wani sassanyan hamma tayi mai cike da bacci. Inda yake ta kalla, sam hankalinsa baya kanta. Hakane yasa ta miƙe a hankali, sabida hankalinta ya ɗan kwanta dashi ganin bai kulata ba. A hankali ta zagaya can gefe, ta zauna bakin gadon. Tana mai lullumshe idanunta. Minti talatin tsakani ta ɗan gyara zamanta ta mirgina ta kwanta, kana ta bashi baya. sannan ta gyara ƙaton hijabinta ta duƙunƙune a ciki. A hankali take jiyo muryarsa yana karatun. Shi kuwa Sheykh duk abinda takeyi yana sane bai kulata bane, dan yana son ta nitsu. Sha biyu dai-dai agogon wayarsa ya nuna masa. A hankali yayi addu'an samun zuriya ta gari da Addu'o'in kariya da kuma cikar burinshi ya shafa sannan ya miƙe ya ninke sallayar, ya ajiye al'ƙur'ani. Kana ya tako ya iso jikin gini, gudun A/C ya dai-dai-ta kana ya kashe wutan ɗakin. Sannan ya kunna hasken wayarsa ya nufo kan gadon. A hankali ya zauna a bakin gadon bakinsa ɗauke da tasbihai. A hankali ya ɗaga hannunshi ya haɗesu kana ya buɗe tafin hannunshi yayi addu'o'in bacci ya tofa, ya shafawa jikinsa. Kana ya hawo saman gadon da kyau. Cikin sanyi da nitsuwa ya isa inda take. A hankali yasa hannunshin ya fara jan ƙaton hijabin dake jikinta. Da sauri tasa hannun ta ta kamo nashi, sabida dama baccin nata ba wani nauyi yayiba. Jin yadda ta riƙe hannunshi ne yasa ya sunkuyo ya kawo bakinshi kusa da kunneta kana yace. "Addu'a zan shafa miki, kuma bazan shafawa hijabiba". Cikin muryar bacci tace. "Sanyi nakeji ai". Ci gaba da janye hibajin yayi tare da cewa. "In na shafa miki sai ki meda". Sake mishi hannun tayi kana, tayi shiru tana jinsa yana karanto addu'o'in yana tofawa a tafin hannunsa. Saida ya gama kana ya sunkuyo ya kife tafin hannunshi kan fuskarta. Ya fara shafawa daga saman kanta har zuwa ƙasa kana har bayanta. A hankali tace. "To bani hijabin". Konciya yayi tare da cewa. "Yayi nisa". Shiru tayi tana jin wani irin fitinenne ƙamshin jikinsa da sanyin ɗakin suna ratsata. A hankali ta fara fidda numfashi. walƙiya kuma in ya haska har cikin ɗaki. Har yana ɗauke ido. Hannunsa yasa ya kamo hannunta na dama ya joyota rigingine. Ɗan sunkuyowa kanta yayi. Hakan yasa suka ɗan fidda numfashi a tare, Cikin nitsuwa taji ya manna mata kiss a goshinta, tare dasa tafin hannunsa bisa nata tafin hannun. Cikin wani irin sassanyan numfashi ya cusa kanshi tsakankanin wuyanta da kafaɗarta hancinshi ya manna kan fatar wuyanta, idonshi ya lumshi tare da ƙara shaƙan ƙamshin jikinta. Iya kuwa Aysha wani irin harbawa zuciyarta ya fara can ƙasa yake. Dib-dib-dib. Shi kuwa Sheykh a hankali ya dawo da kanshi kan fuskarta. ƙasa yayi da bakinshi. Harshensa ya ɗan zaro ya manna da tattausan lips ɗinta, lasarsu yayi tare da fidda wani matacce sauti. "Hiehhhhhhh". shiru tayi kamar mai bacci, sai kuma taji ya zira mata harshensa cikin bakinta, A hankali ya lalimo tong ɗin ta wanda haka yasa jikinta ya fara tsuma rumtse idanunta tayi da ƙarfi jin ya, naɗe tong ɗinta cikin nasa, tare da fara tsotssarshi tamkar ya samu tom-tom mai yaji. Ƙasa yayi da hannunsa cikin wuyan rigarta yasa yatsunshi yana neman inda zip ɗin. gaban rigar tata yake. meda hannunshi yayi ya tallabeta da kyau. Kana yasa yatsunshi biyu kan zib ɗin gaban jacket ɗin. hannunshi yasa cikin gashin dake wuyan jacket ɗin. Zib ɗin ya kamo kana yaja yayi ƙasa dashi, yayinda kuma tong ɗinsa na kanainaye da nata. da sauri ta riƙe hannunsa tare da alamun kada ya cire mata shi. Bai kulata ba kuma bai sake zib ɗin ba. a hankali ta kuma riƙe hannunsa tare da fara jujjuya kanta. Wani kiss ya ƙarayi mata mai cike da sabgogi masu birkitarwa. A hankali ya ture hannunta kana ya zuge zip ɗin da ƙarfi yayi ƙasa dashi. kana ya buɗa rigar tare da wareta. shiru tayi tana jinsa sabida karkarwan da jikinta keyi ya fara yawa. hannunta ya zare cikin hannun rigar, ya zare shi kana ya jefar dashi gefe. Ya rage daga ita sai Baby top da jeans ɗin jikinta. zare bakinshi yayi daga nata. Haka yasa ta juya da sauri ta bashi baya tare da haɗe hannunta a ƙirjinta ta ƙanƙame kanta gam tana jin yadda zuciyarta ke buga lugude. shi kuwa matsowa ya kumayi a hankali ya manna ƙirjinsa da bayanta, Ɗan ronƙofowa yayi kanta ya cusa fuskarshi tsakanin wuyanta da kafaɗunta. yana shaƙan ƙamshin turaren dake jikinta hannunshi ɗaya kuma bisa cikinta ya ɗaurashi a hankali murya can ƙasa yace. "Aish!". Shiru tayi ba amsa mishiba, sai wani tsuma da jikinta keyu. "Aich". Ya kuma kiranta a hankali cikin kunnenta. Murya can ƙasa tace. "Na'am". Kanshi ya ɗan manna da fuskarta kana a hankali yace. "Bana son wanna shigar a irin ya wannan lokacin". Kawai ta tsinci bakinta da cewa. "Kayi haƙuri". Kafaɗarshi ya maƙe tare da cewa. "A a bazanyi haƙuri ba." A hankali murya na rawa tsoro da sanyi tace. "To Yah Sheykh ya zanyi". Ƙara manneta da jikinsa yayi tare da cewa. "Cireshi zanyi". Da sauri tace. "Yah Sheykh". Bai bari taci gaba ba yace. "Na'am Ya Aish". hannunshi yasa ya tura rigar sama, ya zama cikinta ya baiyana woje, tafin hannunsa yasa yana shafa cikin a hankali. wani irin numfarfashi take fiddawa a hankali a hankali, yayinda zuciyarta ke buga dib-dib ya zatayi? Me yake nufi? Me yake so? Me zaiyi? Sune abubuwan da suka taru suka sa mata taraddadi. Shi kuwa Yah Sheykh, na mijin duniya. Yatsarshi manuniya ya zira cikin hudan cibiyarta, yana ɗan zagayeshi ta ciki, kana yayi sama da yatsar kana yayi cikin hudar cibiyar a hankali. cikin raunin murya mai nuni da fargabarta a hankali cikin rauni tace. "Yahhh Sheykhhhh baccccci". A hankali yayi sama da hannayeshi duka biyu. Ya cusa su cikin rigar tata. Ya ɗaurasu bisa mayan Caɓɓullenta. A tare sukayi wani irin nufanshi wanda yake gab da barin gangar jikinsu. A hankali ta ɗago hannunta ta ɗaura kan hannunshi dake murza Caɓɓullenta ta riƙe ba tare da ta janye nashi hannunba. iska ya hura mata cikin hudar cibiyar ta har saida ta maƙe kafaɗarta a hankali yace. "Kiyi mana to, kiyi baccinki, Aich ai ban hanaki ba". ya ƙareshe mgnar yana mai ci gaba da tasbihi kamar yadda ya saba duk abinda yakeyi. Cikin wani irin yanayi ya ɗan sunkuyo da kanshi, dai-dai kan hudar cibijiyarta, yayinda hannunshi kuma suna can sama kan caɓɓullenta, Wata iriyar fitinenneyar miƙa mai kashe dukkan sasan jikinta tayi lokacin da taji ya zira harshensa cikin hudan cibiyarta. Shiru sukayi gaba ɗayansu sai wasu tagwayen numfarfashi masu nauyi suke sauƙewa, kana zuciyoyinsu na bugawa. A hankali ya zira tong ɗinsa cikin hudar cibiyar tata. Wani irin zira hairshen yakeyi yana in and out tare da nitsa hancinsa cikin fatan cikinta. Cikin wata iriyar murya mai cike da rauni tace "Ahhhhhhh Yah Sheykh". haka ta kirashi cikin wata daburtacciyar murya. "Uhummmmmmmm". Ya fidda sautin ba tare da ya zare tong ɗinsa ba. A hankali ya ƙara yin sama da hannunsa dake ƙan ƙirjinta, tare da tura rigar. Har saida ya cireta gaba ɗaya. A hankali tace. "Yah Sheykhhhh sanyi". Zare harshensa yayi kana a hankali yayi ƙasa da kanshi har ya iso inda zib ɗin wondon jikinta yake, Bikinshi yasa ya kamo zip ɗin da fararen haƙoranshi. Zaiyi ƙasa dashi kenan yaji ta yunƙuro da sauri ta tashi zaune, tare da fara jujjuya kai gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi. Da sauri yasa hannunshin ya jawota jikinsa, ya sata tsakiyar cinyoyinsa ya zama bayanta na manne da ƙirjinsa. Rigarsa ya kamo ya fara yin sama da ita ya cireta ya cillata gefe, haɗe bayanta yayi da ƙirjinsa sosai fatarsu ta manne da juna, hannunshi yasa kan ƙirjinta ya fara shafawa tare da murza bakin jajayen nimple ɗin ta. Cikin rauni tace. "Ayyah Yah Sheykh ka bari mana". A hankali murya na rawa ya raɗa mata. " Ay... Ayyah Ai... Aish dan Allah kada kiyi min haka, kada ki bari ki kwana cikin fushin Allah da mala'ikunsa, Please ki zama jaruma a dare ɗaya tak ɗinan dai kada ki baiyana sirrinmu wa kowa." Rau-rau tayi da idanunta tuni hawaye suka fara tsilalo mata sabida ta gama fahimtar abin nashi na yau na gaskene babu irin wasannan ko kauda kai. Ƙara sa cire rigar, yayi ya zama ba komai a jikinta sai wondon. numfashi ya ɗan fesar kana ya gyara zamanshi da kyau ya jingina bayanta da ƙirjinsa. hannunshi yasa kan fatan cikinta yana shafawa har zuwa sama, wani irin sanyi da takeji da yanayin da yake jefata yasa takejin tsikar jikinta na mimmiƙewa. Hannunta tasa ta damƙi cinyoyinsa, Yayinda shi kuwa zuciyarshi ke gab da hautsine ta faso ƙirjinsa ta fito woje. A hankali take jiyo muryarsa can ƙasa cikin rawa yake maimata. "Astagafirullaha Subahanallah Alhamdulillah wa la'ilahaillaha Allahu Akbar." Ta gama sanin duk abinda yakeyi baya barin ambaton sunan Allah, inma kaga bayayi a baki a fili tofa yanayi cikin zuciyarsa. A hankali ya kife tafin hannunsa kam caɓɓullenta yayi musu wani irin gigitaccen shafa da matsa mai cike da fitina da ɗimautarwa. "Uhhhhmmmmmm". Ya fidda sautin cikin kunnenta. yatsunshi yasa ya kama nimples ɗin ta duka biyu yayi musu wani irin sahihin murza mai cike da taka tsantsan yadda bazataji zafiba. Ƙara cutsa yatsunta tayi cikin sumar kansa data meda hannunta ciki. A hankali yaji alamun hawayenta na ɗiga kan hannunshi kana jikinta duk yana tsuma da kerma dib-dib-dib haka yake jin alamun bugun zuciyarta. cikin sanyi yayi ƙasa da hannusa ɗaya, zip ɗin wondon ya kama ya fara yin ƙasa dashi. Zuwa yanzu gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi. Hannunta tasa da nufin kamo hannusa sai taji yasa hannunsa ɗaya ya haɗe hannunta ya riƙe. haka yasa murya na rawa ido na zubda hawaye tsoro tace. "Yeah Sheykhhhh". Kanshi ya sunkuyar dai-dai kunnenta cikin daburtacciyar murya yace. "Na'ahhhm?". Cikin rawan murya tace. "Kayi haƙuri, ka barni mana". Fara murza Wondon ƙasa yayi tare da cewa. "Me zan bari Aish in bar haƙƙina a kanki zaki iya dakon zunubin?". Murya cike da rauni tace. "Ka yafe min". Cikin sanyi da hikimar zare wondon yace. "Bazan iya yafewa ba Aich, sai dai in zakiyi dakon zunubin." Cikin rawan murya tace. "Bazan iyaba". Zameta yayi ya kwantar da ita kana murya can ƙasa yace. "Ni kuma Bappanki ya bani tabbacin nagartarki da biyayyarki, bani da zaton tirjiyar samun haƙƙina a kanki, Aysha ko baki san inada haƙƙi a kanki bane?". Kuka mai cike da rauni da tsoron abinda bata taɓa fuskanta ba ta farayi a hankali, tayu mgna cikin rauni tace. "Na sani". Janye jikinshi yayi baya kana ya kwantar da ita, bisa pillow'nshi sannan ya koma gefe. Gefe ya ɗan janye jikinshi, singilet ɗin jikinshi ya zare ya wurgar gefe, kana yasa saɓule dogon wondon dake jikinsa. A hankali ya miƙo hannunsa, ya kamo hannunta ya jawota jikinsa. Wani irin rugugi akayi mai ƙarfi, tare da walƙi mai jan haske. Cikin tsoro da razana ta faɗa jikinsa tare da ruggumeshi gam-gam, ɓarin da jikinta keyi ya tsananta. Shi kuwa Sheykh wani irin lumshe idonsa yayi kana yasa tafin hannunsa duka biyu ya tallabo fuskarka, goshinsu ya haɗe wuri ɗaya, tsinin hancinsa ya goga kan nata tsinin hancin. A hankali yace. "Na gama gamsu cewa duk duniya, kena sirrina Aish. Dole ki zamo suturata, kamar yadda nima zan zama suturarki, kamar yadda Allah (S.W.A) ya fadi." Ya ƙarashe mgnar yana manna Bakinshi da nata, lips ɗin ta duka biyu ya ɗan kamo ya tsotsa a hankali. sannan ya sake, kiss ya manna mata a goshi kana ya manna mata a tsakanin wuyanta da kafaɗarta, harshensa ya zaro ya manna bisa wuyanta yana ɗan lasawa, tare dasa hannunsa yana murza ƙirjinta da leleye nimple ɗin ta. hannunshi yasa ya kwantar da ita, kar-kar haka yaji jikinta na rawa, hannunshi yasa ya danna wani abu dake jikin gadon. Sai ga wani tattausan labule ya sauƙo daga saman rumfar gadon, yayi wa gadon ƙawanya. A hankali ya ronƙofo kanta, cikin sanyi murya can ƙasa yace. "Aish meyasa jikinki keyin rawa?". Cikin rawan murya tasa hannu ta riƙo damatsan hannunsa a hankali tace. "Tsoro nakeji Yah Sheykh ina jin tsoron". Kanshi ya maida bisa lafeffen cikinta, cikin hudan cibiyarta ya zira harshensa, da sauri ta rumtse idanunta sabida wani irin masifeffen daɗin da taji yana ratsawa cikin hudan cibiyarta sai dai tsoronta kuma ƙara hauhawa yakeyi. Hannunsa ya miƙa ya ɗaurasu kan tamtsan-tamtsan breast ɗin ta. yatsunta ta cusa cikin sumar kanshi, tare da fidda sassanyan sauti. "Ahhhhhhh". Zaro harshensa yayi kana ya fara lasan fatar cikinta tare da kissing cikin. har zuwa sama. A hankali ta buɗe bakinta sai kuma ta kasa yin mgna sabida, yadda ya zura harshensa cikin bakinta. Wani irin fitinenne kiss tongue to tongue yake yi mata mai, rikitarwa. Hannunshi yasa bisa breast ɗin ta yanayi musu wani murza, kanta ta fara jujjuyawa. A hankali ya zare harshensa ya dawo dashi bisa ƙirjinta, harshensa ya manna kan nimple ɗin ta ya, ya fara yi mata wani irin tsotsa mai rikitarwa. Wani irin fitinenne zabura yaji BNN ɗinsa tayi tare da miƙewa zamɓal ta fara harbawa, tamkar zataci babu. Hannunsa ɗaya kuma yana kan ɗaya breast ɗinta. Yana matsawa, gaba ɗaya ya gigitata, ya hautsuna mata lissafi, jikinta yayi weak sai tsuma da yakeyi. A hankali yayi ƙasa da hannunshi yana shafa cikinta har zuwa kan mararta. Cikin wani irin yanayi ya tura yatsunshi cikin pant ɗin ta, wani irin zillo tayi tare da buɗe baki tace. "Washhhhh, haahhyyyy". Da sauri yayi sama da hannunshi yatsarshi ya zira mata cikin bakinta. Wani irin cabke yatsar tayi ta fara tsotsa sabida yadda ya rikita mata, lissafi. A hankali yake murza pant ɗin. Yanayin ƙasa dashi. saida ya cireshi kana yaci gaba da shafa PP ɗin ta, yanayi mata wani irin salo. Kerma jikinta ya fara, a gigice take jan numfashin tare da tsotsan yatsarshi, hannunta kuwa na bisa wuyansa. Zare yatsarshi yayi daga bakinta, kana ya tashi zaune, sabida wani irin masifeffen feelings da yakeji tamkar zai ɗauki ransa, Sheykh ɗin shi sai wani irin miƙewa da cika da kumbura takeyi tana harbawa tamkar zataci babu ta cika tayi tab ta miƙe zamɓal sai harbawa takeyi. Zare boxes ɗinsa yayi ya cillata gefe. Kana ya matsota sosai. Gyara zamanshi yayi ya jingina da kan gado, hannunta ya kama, tare jawota jikinshi. Bnn ɗinsa ya kamo da ɗaya hannun ya cusa mata shi cikin tafin hannunta, wani irin zabura da razani ne da tsoro suka risketa lokacin ɗaya, murya da jiki na rawa tace. "Wayyo Yah Sheykh barni sakeni". Cikin wata irin murya mai rauni yace. "Uhhhahhhhhhhh. Aish riƙeni, ki riƙeshi". hannunsa yasa ya haɗe da nata ya matse bnnarsa da tafin hsnnunta. Da karkarwa hannunta ya farayi, ganin hakane yasa ya sake hannunta, yajawota ya kwantar da ita. rigingine, tsakiyar cinyoyinta ya dawo, hannunsa yasa ya buɗe sawunta, kana a hankali ya sunkuyo da kanshi ƙasanta. Wani irin masifeffen ƙamshi turaren misski ne mai ɗan karen daɗin shaƙa ya bugi hancinsa, cikin rawan jiki ya manna bakinshi bisa pp ɗin ta. wani irin yunƙura tayi tare dasa tafin ta damƙi damatsan hannunsa da ƙarfi. cikin wata iriyar fitinenneyar murya tace. "Ahshhhhhhhhyyy Yan Sheykh. Ka bari marata zata fashe". Hannunshi yayi sama dashi dai-dai kan marar tata, Ya fara ɗan shafawa. Yayinda ɗaya hannun kuma yana can sama yana murza breast ɗinta da mulmula nimple ɗin. Wani tsalle yakeji Sheykh ɗinsa tanayi babu sassauci ji yake tamkar zata tsinke tayi ƙasa dan azabar sha'awa da cika da tayi. Ita kuwa Aysha tuni hawaye keta shatata a fuskarta, murya na rawa jiki na rawa take cewa. "Yah Sheykh ina tsoro ni dai ka barni, bazan iyaba. Ka sakeni zan koma ɗaki na". Cikin rawan jiki da gigita, ya zaro harshensa daga ƙasanta da tuni take tsiyayar da ruwan madara mai ƙamshi da yauƙi. yatsarshi yasa ya ɗan shafa kana ya yi sama da kanshi. Cikin sanyi ya buɗa sawunta kana ya kawo bakinshi dai-dai kunnenta a hankali murya na rawa yace. "Aish buɗe sawunki, zan miki a hankali. Please ki bani hanyata". Cikin kuka tace. "Ina tsoro Yahhh Sheykhhhh ban taɓa yiba ance da zafi". Kanshi ya cusa a wuyanta tare da cewa. "Na sani, nasan baki taɓa yiba Aish na sani, Ba zafi, zan miki a hankali jini ko". Hannunshi yasa ya buɗa sawunta kana yasa hannunshi ya kamo Sheykh ɗinsa da bai taɓa sanin girmanta ya kai hakaba, saita ta yayi da muhallinta. Tare da cewa. BISMILLAH ALLAHUMMA JANNIBNAL SHAIƊAN WA JANNIBAL SHAIƊANA MARAZAƘTUNA. Wani irin rumtse idanunta tayi da ƙarfi jin wannan abu mai kama da maciji yana neman inda zai shiga a cikinta, murya a hargitse tace. "Wayyo Yah Sheykh. fitsari nakeji, zanje inyi fitsari". Ina zuwa yanzu bazai iya sahirta mataba. Cusa kan Sheykh ɗinsa yayi da jikinta, wanda yasa ta zurma wani gigitaccen ihu mai sauti dai-dai lokacin kuma aka saki wani irin razanenne tsawa mai firgitarwa da walƙiya mai masifar haske. Sai kuma aka kece da wani sabon ruwa tamkar da bakin kwarya. Wani irin karkarwa da tsuma jikin Sheykh yakeyi, burinshi ya rabata da budurcinta ya tabbatar da ita mace, ya kusanci duniyarta ya medata cikekkiyar matarsa abar jin daɗinsa ta zama cikekkiyar suturarsa ya zama cikekkiyar sutarta, shiyasa cikin fitta haiyaci ya baƙonci rayuwarta da tashi rayuwar ta da masifar ƙarfi da gigin sha'awa. Ƙanƙameshi tayi da masifar ƙarfi tare da yunƙurowa ta cusa kanta cikin ƙirjinsa sabida wani irin azabebben zafin rabuwa da tantanin budurcin da taji yana shirin ɗauke ranta kar-kar jikinta ke rawa, Wata fitinenneyar zufa ce ta karyo mata duk da tsoron sanyinta ga kuma ac.da sanyin damuna. A gigice tace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun. Wayyoooooooo Allah na Wayyo Deddena Wayyo Abboi, Wayyo Ummey na Wayyo Bappa na, wayyoooooooo Umaymah Yah Sheykh zai kasheni, Ummi kizo ki ceceni, kice ya barni". Jin yadda take zurma ihu da kiraye kirayene yasa ya manne bakinshi da nata lips ɗinta duka biyu ya haɗe ya fara yi musu wani fitinenne tsotsa tamkar zai tsinkesu ya haɗiyesu. Kuka tasa da ƙarfi tare da soma girgiza mashi kanta da takeji tamkar ya kumbura ne. Wani azabebben ihu ta kurma da iya ƙarfinta, wanda badon ruwan da ake sheƙawa ba, da rugugi da rabin masararutar Joɗa duk sai sun jiyota. Cusa kanshi yakeyi cikin jikinta yana buɗa kilatacciyar hanyar yana ratsawa, tare da kekkyawan fatauci da ƙarfin inƙarmansa na cikekken namiji tare da ambaton sunan Allah. "Hhhhhhhhhh, Alhamdulillah, Yah subahanallah! Subahanallah!! Allahu Akbar ohh sorry Im so sorry Yah Aish. Afwan Larki". Sune kalaman da yake iya maimaitawa da alamun a gigice yake. Iskar damuna mai sanyi da sanyin A/C suka haɗe mishi da ƙamshinta suka ƙara zuzuta karfinsa suka hautsunashi suka fiddashi haiyacinsa. Sai haƙilo da fatauci yakeyi babu sassauci. Cusa kanta tayi cikin ƙirjinsa tare da riƙo damatsan hannunsa ta saki kuka mai cike da rauni sabi ta fara gala baita shi kuwa baiji bai gani bare ya sararamata, wani zazzafan cizo ta datsa mishi a ƙirjin saman nononshi kaɗan tare da fara tuttureshi. Hannunshi yasa ya jawo sawunta ya ɗan buɗa da ƙarfi kana ya dannesu, wani irin gigitaccen gamaiya ya kai mata wanda yasa ta shaƙi wani dogon numfashi tare da koma ta kwanta a sume. Sai dai baima san ta sumaba, ci gaba yayi da fatauci sa. ita kuwa Aysha kamar yadda wahala tasa ta suma wahalarce ta kuma farfaɗo da ita abu dama da mai raki. Sama-sama takejinshi har yanzu tare da ita, Sai zufarshi mai ƙamshi dake ɗigowa kanta ba sassauci. Rumtse idanunta tayi da ƙarfi sabida raɗaɗin da takeji tamkar zai kasheta, ƙarfinta ya ƙare duk kuzarinta ya tafi. Cikin wahalar da take cikin take jiyo muryarsa can sama yana mgnar da ƙarfi kamar yadda yake isarta da ƙarfi murya na rawa da alamun kuka yake cikin harshen larabci yake cewa. "Yah Subahanallah, Alhamdulillah Allahu Akbar. "Aish As attu li wajattu xawajiki". Kuka ta kuma sawa tare da ruggumeshi gam-gam a jikinta, tare da cewa. "Wash, wash, Wayyo Yah Sheyyyykh". a kiɗime yayi mata wata iriyar fitinenneyar kuma gigitacciyar rugguwa da azaban ƙarfi tare dasa wani raunataccen muryar kuka dan ji yake kamar daɗin zai kashesa cikin kemar yace. "Wayyo Mamey, hashhhh, Mammey, Mammeyyyyy. zan mutu bamu sake haɗuwa ba". Da karfi ya kuma fara fidda numfashi tare da maimata wata kalma da larabci. "Kuntil lagamee! Kuntil lagamee!! Kuntil lagamee Yah A'ish, kuntil lagamee. Kunti ba'adu jasadi ya A'ish, kunti ba'adu jasadi feeh hayati ana". Wani irin karkarwa ya fara da azaban ƙarfi tare da bada himma can ya saki wani irin masifeffen numfashin tare da kifuwa kanta ya kifa kanshi bisa filo bakinshi na dai-dai cikin kunnenta murya a sake yace. "Hashhhh Wahyyyyy Jazakallahu khairan Yah A'ish. Alhamdulillah! Alhamdulillah!! A'ish kin zama suturata, Ngd kin bani abinda ban taɓa samuba a duniya kin tabbatar dani cikekken mutun magidanci." Ita kam Aysha da ita da matacciya babbancinsu ba yawa, domin ko yatsarta bata iya motsawa, tana dai jin duk abinda yake faɗa, na hausa ko fillanci ta gane duka na larabci da yake zubawa kuwa kaɗan take ganewa tunda ba ji takeba. wani irin numfarfashi tayi mai rauni lokacin da taji yana raba jikinshi daga nata, kana ya faɗa gefenta bakinshi ya manna da kunnenta a hankali yace. "Hazal yaumu huwa a'axamu minna, A'ish Hazal yaumu a'axamu minna." Hannunshi yasa ya jawota jikinshi ya kifeta bisa ƙirjinsa. wani irin masifeffen zafi taji jikinsa yayi har kamar tururi yakeyi, zafine irin mai ratsa jikin nanne. Ruggume ta yayi tare da lumshe idonsa sabida, wani irin fitinenne zazzaɓi mai masifar zafi da suka ƙasusuwan jikin daya rufeshi a take a lokacin ɗaya gaba ɗaya jikinsa karkarwa ya fara. har tanajin hakan, so yake ya tashi da ita a jikinsa ya nufi Bathroom Amman ya kasa sabida abin sai ƙaruwa yakeyi, ji yakeyi tamkar kansa zai rabe gida biyu. Cikin rawan jiki ya jawo blanket ɗin ya rufesu da kyau. sama take jinshi yana sambatu irin na marasa lfy dake jin azabar ciwo da kuma raki. "Mamey! Hahhhhh Mamey kaina, Mamey kaina zai fashe Mamey jikina zazzaɓi Mammeyyyyy". Ya ƙare kiran kamar zaiyi kuka. Itama kukan takeyi gashi taji shima kukan yakeyi da samɓatun da batasan na menene ba. Shi kuwa Sheykh wasu irin abubuwa yakeji suna tafiya cikin jikinshi suna haurawa saman tamkar dafin...! Littafin GARKUWA na kuɗine in kinason ki karanta ba tare da haƙki ba ga number ta 09097853276 special Group 1k ne shi anfi yawan posting ta Account ɗina zaki turo 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276. Normal group Kuma 300 ne, kema ta ac no ɗin zaku turo, in ba halin biya ta ac kuma ki sayi katin Mtn na ɗari uku ki copy numbers ɗin katin ki turo min ta whatsapp 09097853276, kada kiyi min VTU ko transfer'n kati bana so. By *GARKUWAR FULANI* [3/18, 12:40 AM] +234 806 559 0880: Kamar dafin maciji, gaba ɗaya tsikar jikinshi ta fara mimmiƙewa tsaye. Yanajin wasu abubuwa na bin dukkanin sasan jikinsa gaba ɗaya. Matseta yayi gam-gam a jikinshi tare da jawo blanket ya rufesu rib, cikin rawan murya mai baiyana yanayin wahalar zazzafan zazzaɓi da ya rufeshi da yake ji yake cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil. Mamey, Abba, Jadda, Lamiɗo, Umaymah Sitti Ummi." Sai kuma ya kuma ci gaba da Addu'o'in. Cikin abinda bai gaza 2 minute ba yaji abubuwan da yakeji suna sauƙa ƙasa a madadin sama da suke ta haurawa, duk inda yakejin suka da sari sai ya farajin sanyi mai ƙarfi yana ratsashi ciwon na gushewa kasala mai mai tsanani tana rufeshi. Lakaci ɗaya yaji jikinsa na sakewa yana mutuwa ciwon na gushe. Al'farmar Annabi da al'ƙur'ani kenan, sabida dama addu'a'u saiful muminin. Luƙus ya kwantar da kanshi, kana hannayenshi dake bisa bayanta suka sake sukayi nauyi. Karkarwan da jikinsa keyi ya bari a take, sai wani masha'hurin zazzaɓi mai zafi ya mishi rabkar ƙarfi. Ita kuwa Aysha hawaye taketa kwaranyarwa. Tare da Shessheƙan kuka mai cike da rauni da wahala da raɗaɗin ciwon da ko wacce diya mace ke riska yayin rabuwa da tantani wato budurci. A haka tana kukan baccin wuya ya saceta. Ko a baccen shessheƙan kuka takeyi tare da wasu surutai na magayi. A hankali ya juya kwayar idanunsa dake lumshe wanda ko buɗe su ya gaza, muryarta yakeji a hankali tana cewa. "Yah Sheykhhhh na tuba ka barni haka zafi. Ummey zafi, Innayi Yah Sheykh yaji min ciwo, Yeyyeh ciwo". Duk da yanayi da yake ciki. Bai hanashi tafiya duniyar nazartan sunayen da take kira tana kukan wuya haɗida shogoɓa ba. Tabbas akwai ababen dake sarƙafe a kan Aysha. A haka suke kwance cikin borgon ana tsula ruwa kamar da bakin kwarya. Ita dai tayi bacci amman ina shifa zazzaɓi ya hanashi rumtsawa. Yanaji a jikinsa lokacin tashi yayi nafilarshi yayi amman ya gaza koda motsa yatsarsa. Numfashi yake fiddawa hankali yana mai jin fargabar kada fa, har gari ya waye masa a haka. To wai dama duk na miji in ya kusanci iyalanshi haka yakeji, ko dai shine yaji haka?. To ko dai dan bai taɓa yi bane?. Wannan shine nazarin da zuciyarshi keta nazarta masa. Wani nannauyan ajiyan zuciya ya sauƙe mai ƙarfi lokacin da yaji an kwaɗa kiran sallan forko na a masallacin Masarautar Joɗa, wanda haka yake nunin saura awa ɗaya lokacin salla asuba tayi. "Ya ilahi, ya mujibadda'awati". Ya fara maimaitawa a zuciyarsa. Ita kuwa Aysha har lau bacci takeyi tare da sabke ajiyoyin zuciya a jere a jere. Tsawon mintuna talatin yayi yana addu'o'in a zuciyarsa, Kamar a fizge yaji bakinsa ya buɗu ya furta. "La'haulawala ƙuwta illabillah aliyul axeem". A bakinshi, dai-dai lokacin kuma ladanin masalacin matsarautar Joɗa yayi kiran assalatu. Wani irin tsuma yaji jikinsa nayi, zufa mai zafi ta karyo masa. A hankali ya muskuta, kana ya ɗan ɗago hannunsa ya ɗaurasu tsakiyar bayanta, cikin sanyi yace. "A'ish, Ahh'ihch". shiru babu, amsa. Sai shessheƙan, jin kuzarin jikinsa kaɗan yasa a hankali ya mirgina da ita ya kwantar da ita, kana ya ɗan ja baya. sannan ya buɗe borgon ya fita, ita kuma ya rufeta. A hankali yasa hannunshin ya kunna wutan ɗakin. Gajeren wondon sa dake gefe yasa hannunsa ya ɗauka kana ya zira a jikinsa. Miƙewa yayi tsaye. "Waiyyyy, daɗi Alhamdulillah". Yace a saman lips ɗinsa ya ƙare zancen dasa hannun ya shafa mararsa da tayi mishi sakayau ba nauyi ba tauri ba ciwo, taku ya farayi a nitse ya shiga bathroom. Kai tsaye wurin wonka ya shiga. Ruwan ɗumi ya sakarwa kanshi, tare da sunkuyar da kanshi. Cike da mamaki ya zaro kekyawan idanunsa ya zubawa ƙasan baf ɗin ido, inda yaga ruwan nabi sawunshi da kalan ja. Da sauri yasa hannunshin ya rufe shawan. Cike da mamaki ya sunkuyo ya kalli boxes ɗinsa, da sauri ya sunkuyo yayi ƙasa da ita, idonshi ya rumtse da sauri sabida ganin gaba ɗaya matse-matsin cinyoyinsa jini hakama joystick ɗinsa duk jinine a jikinta. ga boxes ɗin ya ɓaci. A hankali yayi ƙasa da baxes ɗin ya cireshi, gefe ya ajiyeshi. Karon farko kenan a rayuwarsa tun bayan girmansa da zaiyi wonka tsirara haihuwar uwarsa. Haka yasa yakejin kunyan kanshi da kanshi. Sabulu da soso ya jawo, wonka ya farayi soso da sabulu ya murje jikinsa tsab ya solle ko ina. Daga nan kuma yayi wonkan tsarki inda yayi suppatul kamal wato wonka tsarki mai haɗe da al'wala. Da sauri ya fito cikin jakkuzin. Drower'nshi dake cikin bathroom ɗin ya nufa. cike da kunya, da sauri ya zaro towel ya ɗaura a ƙugunsa, Sannan ya dauko baby towel ya fara tsane ruwan jikin nasa, yana gama ya ɗan shafa mai kana ya zaro farar jallabiyarsa sabuwa dal ya saka bayan yasa farar boxes da singilet. Wata farar al'kyabba sabuwa dal itama ya zura a jikinsa kana yasa hirami. OudKareem dake cikin drower'n ya fesa tako ina na jikinsa kana ya fito. Yana sako ƙafarshi a bedroom ɗin ana tada iƙama, hakane yasa da sauri yanufi hanyar fita jin jam'i zai wucesa. Juyowa ya kumayi, wayarshi ya ɗauka ya zura a aljihu kana ya iso bakin gado, cikin ya ɗan ɗaga murya yace. "Aish tashi lokacin salla yayi". A hankali ta buɗe kekywawan kwayar manyan idanunta da suka rine sukayi jazir kana suka kumbura. A hankali ya ɗan sunkuyo kan goshinta ya manna lips ɗinshi yayi kissing nata tare da cewa. "Gud gerl, jazakallahu khairan yah Aysha tashi kiyi wonka kiyi salla." Shar-shar haka yaga wasu tafasassun hawaye sun kwaranyo mata, ba tare da ta motsa ko yatsarta ba. Da sauri ya sunkuyo kanta da kyau cikin murya mai cike da kulawa da tausayawa yace. "Sannu Aish kiyi haƙuri kinji kibar, tashi kiyi wonka kiyi salla kinga lokaci yayi". Ya ƙarashe mgnar yana juya ya fita jiyo ana tada kabbara. Kai tsaye masallacin ya nufa. Ita kuwa Aysha da kumburarrun idanunta ta bishi da kallo duk da dishi-dishi take gane. Cikin rauni ta saki raunataccen kuka murya na rawa take kukan tare da cewa. "Gud gerl ko? Ta ina zan iya tashi, kamin fyaɗe kace na tashi, rufe idanun tayi sabida duhun da taga yana meye ganinta, kana ɗakin yayi mata duhu gaba ɗaya. Shi kuwa Sheykh da sauri ya isa tuni an karance fatiha ta raka'ar forko har an fara suratul Al-Burooj, yana isa kuwa ya wuce sahun forko. miti bakwai tsakani aka tafi ruku. A hankali ya sunkuyo dan yin rukun, sai kuma ya rumtse idanunshi da ƙarfi sabida wani irin masifeffen ciwo da yaji cinyoyinsa sunayi, Ciwon da duk na mijin da bai taɓa kusantar maceba kuma yazo yayi katari da yage cikekken (tattani) budurci tofa dole yaji wannan sauyin da ciwon cinyoyi. A hankali ya taso daga ruku'un sabida sosaifa cinyoyinsa da ƙugunsa sukayi sami da fitinar gwatson da yayi daren jiyan wanda bai taɓayi ba. Taune lip ɗinsa na ƙasa yayi lokacin da aka tafi Sujjadar forko. Sabida ciwon yafi na rukun. A haka dai akayi sallan aka idar. Bayan an idarne, kamar koda yaushe ya fara Du'a'u Azkar. Abbansa da Lamiɗo da Galadima suna gefensa. Suma sunayi koda suka ida a hankali ya miƙe tsaye ganin Abbanshi ya yafitoshi da hahhunsa. Bayan Abba da Lamiɗo da Galadima da Baba Kamal yabi. Affan, Jamil, Jalal, Ya Hashim, Imran, Sulaiman, Laminu. Suma suna biye dasu can baya da sauran zaratan jikokin Lamiɗo da sauran ahlin masarautar Joɗa. Kana jan baya kuwa dogaraine. Side ɗin Lamiɗo ya nufa Abbansa da Galadima da Lamiɗo na gabansa. Suna shiga suka wuce can cikin special Side ɗin Lamiɗo. Bayan sun zauna ne ya kalli, Abbansa a hankali yace. "Abba ina kwana". Tsura mishi ido yayi tare da cewa. "Lfy lau Muhammad ya gajiyan hanya". A hankali ya gyara zamanshi ya tonƙoshe sawunshi kana yace. "Alhamdulillah, Jiya naje mu gaisa sa Hajia Mama tace baka nan". Kallonshi Abba yayi tare da jijjiga kai. Shi kuwa Lamiɗo ya ɗan kalla da Galadima kana yace. "Kun kirani kunyi shiru, kunata bina da kallon tuhuma, me yake faruwa in da wani abune ku faɗa kawai mana ku dena min kallon tuhuma". Murmushi sukayi dukansu kana a hankali Galadima yace. "Babu komai, kawai dai yau ɗin ranace da al'amarin auren ka ya tabbatar da nuna kanada damar mulkar masararutar Joɗa". Fuska ya taɓe tare da cewa. "Bafa nason kuna min haka, bani son haka, nace bani da ra'ayin wannan abun ku dena alaƙantani dashi. Me haɗina da sarauta, kuma me ruwanku da lamuran gidana". Cikin Murmushin Lamiɗo yace. "Uhumm toh ai ba mune muka kiraka ba, Abbanka ne ya kiraka. Kuma ba mune muka alakantaka da Masarautar Joɗa da sarautarba Allah ya alaƙamtaka dasu tunda ka fito a jininmu. Mu dai ya nuna mana alamomin dole watan wata rana zaka mulki masarautar Joɗa." Cikin tsuke fuskarsa yace. "Uhum zadai a tarwatsa min rayuwa, tunda kuna sane Galadima kawai aka bawa Yah Jafar cikin mako biyu, aka rabamu da gatanmu aka birkita masa rayuwa. Shin Jalal da Jamil ma sun tsirane, kallon me akeyi musu. Jamil mazinaci mai yawon bin mata, Jalal mashayi ɗan shila, nima ɗin dole ana wani abin, da ƙudurar ubangiji kawai nake tsira, kuma wanda ake nema gabas da yamma kudu da arewa wata ranafa zasu cimmin musamman in suka samu zantukanku". Dafa kafaɗarshi Galadima yayi kana a hankali yace. "Uhum Muhammadu ai sunyi nasara a kanka tun a baya yanzu dai karyewar al'ƙadarinsu ne kawai ya rage. Tashi kaje ka kula da matarka, muna sane da gyallen yarinta, kada kace zaka ɓoyeshi ko zaka wonkeshi, a ma'ajiyin tarihi za'a ajiyeshi shaidar yarinta da tarbiyyar matar sarki uwar wani sarkin kuma a wata rana". Kanshi ya sunkuyar cike da takaici yace. "Wai meyasa kukeyi min hakane? Shin bani da wani sirri a rayuwata da iyalina ne dole sai kunbi diddigin komai kun sani". Haɗe fuska Abbansa yayi kana yace. "Tashi kaje, kada a wonke komai a ka bawa Umminku ta kawoshi. Umarnine ba shawara ba". Cikin sanyi ya miƙe ya tafi. Shiru babban falon ba kowa, sai dai bisa alamu Ummi na Kitchen dan yaji motsinta. A nitse ya wuce Side ɗinsa. Idonshi ya rumtse sabida jin suna mishi wani yaji-yaji dan rashin baccin da baiba tun na yammacin jiya na tsakanin azahar da la'asar ɗin daya zame mishi jiki da kuma na daren da bai samu yayi ba. A hankali ya tura ƙofar Bedroom, da sauri ya ƙarasa bakin gadon cike da mamakin ganin tana kwance, kuma kuka takeyi. Sunkuyowa yayi kanta tare da cewa. "A'ish Ahh'ihch kuka kuma? meya saki kuka. meya sameki?". Ɗago jajayen idanunta tayi ta kalleshi hawaye na kwaranya murya na rawa tace. "Meya sani kuka? Bayan kai, kaji min ciwo, bazan iya tashiba, ƙafafuwana ba ƙarfi, jiri nakeji yunwa nakeji kaina ciwo, kafata ciwo, idona ciwo, komaina ciwo, zogi nakeji". Ta ƙarashe mgnar murya na rawa alamun zazzafan zazzaɓi da zafin ciwo. Cikin wani irin rauni da tsananin tausayinta yace. "Afwan kiyi haƙuri, sannu ko ki gafarceni". Da sauri ya juya ya nufi Bathroom, ruwa mai ɗumi sosai ya cika baf dashi, kana ya fito. Al'kyabbar ajikinshi ya zare tare da hiramin kana ya matso bakin gadon. Hannunshi yasa ya fara janye blanket ɗin. Da sauri tasa hannu ta riƙe hannunsa a raunace tace. "Banda sutura a jikina". Kanshi ya ɗan kauda kana a hankali ya janye borgon tare da cewa. "A'ish gani kuma wanne suturan zaki nema bayan ni, yanzu baki da wata sutura sama dani, kiyi haƙuri ki dena kukan kinji ko bana son jin kukanki". Ya ƙare zancen yana cicciɓota. Da sauri ta rumtse idanunta tare da cusa kanta cikin ƙirjinsa. Bathroom ya wuce. A hankali ya sauƙeta cikin ruwan ɗumin. Wani irin zillo tayi tare da yarfa hannun da kuma sakin ihu mai sautin rauni. "Wash Allah na Yah Sheykh zafi- zafi." Cikin sanyi yace. "Sorry kiyi haƙuri zakiji daɗin hakan, yanzu zaki worke". Ina sai zillewa take son yi. Da sauri yasa hannunshin ya danne ta cikin ruwan ta zauna daɓas. hannunta ta fara yarfawa tare da zubda hawaye, Bakin baf ɗin ya zauna, kanta ya jawo ya manna da jikinsa, kana yayi shiru yana jin yadda jikinta ke karkarwar tamkar mazari. Wata fitinenneyar zuface ta fara karyo mata tako ina na, jikinta, sai kuma ta fara sauƙe ajiyan zuciya. Ummi kuwa, ferfesun zabi tayi, tare da dama kekyawan kunun kanwa mai ɗan karen daɗin yaji citta da kanamfari da kanwa. Kana ta daka mazarƙoila ta zuba a ciki a madadin Sugar. Babban flacks ta cika da kunun. Kana ta juyo ferfesun zabi guda biyu cikin Foodflaks mai kyau. Tuƙeƙƙen tuwon masarar tsari, mai tauri tayi, da kuma miyar ɗanyar kuɓewa da man shanu sai kifi da nama yasha citta da yajin daddawa sai ƙamshi yakeyi. A Foodflaks ta saka, sai kuma gashesshen jan nama, anyi Normal gashi irin na mutanen da. Wanda murhun garwashi ta hura ta gasashi. Sai kuma tea data tafasa ta tsula zuma da citta a ciki. Shi kuma tasa a ƙaramin flacks. Jerasu tayi a manyan tray guda biyu. Sai lokacin kuma Sara ta iso nan suka fara haɗa wani girkin. Sheykh kuwa a hankali ya kamo hannunta ya miƙar da ita tsaye. Tana cikin bathtub ɗin shi kuma yana ta woje. Zubda ruwan yayi tare da ruggumeta a hankali yace. "Zamu ƙara wani ruwan ɗumin kinga wannan duk kinyi masa fitsarin jini a ciki, duk kin ɓatashi raguwa kwai sakaliyar Ummey". Ƙara tsune kanta tayi jikinsa, tare da manne ƙirjinta da nashi wai bata son yaga breast ɗinta. Wani ruwan ɗumi ya kuma sawa, kana ya zaunar da ita ciki. Sannan a hankali yace. "Aha Gud gerl kiyi wonka da kyau, in kin gama jin ɗumin ruwan sai kiyi wonkan tsarki, kin iya ai ko?". Ya ƙare mgnar yana kallonta, cikin sanyi ta gyaɗa mishi kai still hawaye na zuba, a hankali yace. "To niyar wonkan me zakice". Shiru tayi bata kulashi ba kuma bata kalleshiba sai hawayen da takeyi. "Okay to bari in shigo muyi wonkan tare sai in koya miki". Ya faɗa yana sako ƙafarsa cikin bathtub ɗin da sauri tace. "Na'iya". fuskarta ya ɗan tallabo tare da cewa. "Kin iya me?". "Wonkan tsarkin". Ta bashi amsa ido a rufe. shafa fuskarta yayi tare da cewa. "Niyan wonkan me zakiyi". Idonta ta ƙara rumtsew wasu hawayen suka zubo a hankali tace. "Wonkan Janaba". murmushi yayi mai faɗi kana yace. "Eyeh Gud gerl, kin girma yanzu kin zama big gerl ai, tunda har wonkan Janaba ya hau kanki, sannu ko Aish Allah ya miki al'barka". Tafin hannunta tasa ta kare fuskarta. Shi kuwa miƙewa yayi tare da cewa. "Bari inje in ɗauko miki wasu kayan, ko in baki aron al'kyabbata?". A hankali tace. "A a ɗauko min". To yace kana ya fita. Ba kowa a falon, dan haka da sauri ya wuce falonta har bedroom. drower'nta ya buɗe, hannunsa yasa ya zaro wani abu da ya gani Royal blue shi kalan yabi. Sai kuma ya samu ashe doguwar rigace ta shaddar wagambari mai masifar kyau. daga ita bai kuma ɗaukan komaiba ya juya ya fita. A babban falon ya samu Ummi tsaye, cike da tsananin kunya ya sunkuyar da kanshi kana a hankali yace. "Um Uhmm Barka da safiya Ummi". Ganin alamun kunya yasata kauda kanta kana tace. "Barka dai Muhammad". Ci gaba da tafiya yayi. Da ido ta rakashi, tana murmushin jin daɗin. Muhammad ɗinta ya zama cikekken magidanci, daga yawau zasu fara hango nasarorinsu. Tabbas akwai kwan da zai fashe nan kusa a tsakiyar masararutar Joɗa. Shi kuwa yana shiga bathroom ya sameta zaune bakin bathtub ɗin ta ɗaura towel a jikinta. A hankali yasa hannunshin ya kamo nata ya tsaida ita, kana cikin sanyi yace. "Wanne irin wonka kikayi?". A hankali tace. "Da al'wala a haɗe". Na'am yace kana ya zira mata rigar. Saida ya dai-dai-ta mata rigar kana ta kwance towel ɗin ta ɗaura ɗan kwalinta. Sannan ya nuna mata hanyar fita da hannunshi. A hankali ta ɗago ƙafarta ta taka, ido ta ɗan rumtse tare da cije laɓɓanta, kana ta ɗan ware ƙafafuwanta tare dacewa. "Wash". Ido ya ƙurawa yadda take tafiyar. Kanshi ya jinjina sannan a hankali ya biyota cikin kauda kai yace. "Y.M.D.G ko dai kin ƙarune?". Shiru batayi mgna ba, sabida sosai takejin zafin. Buɗe mata ƙofar yayi ta fita. Da sauri yabi bayanta suka fito. Sallaya ya shimfiɗa mata, tare da miƙo mata hijabinta, hannun ta miƙa zata amsa tana mai ɗan kallonshi. yana kallonta yace. "Kiyi salla sai in dubaki inaga ko na buɗa ƙofar da yawa. Gwara in gani da wurin in na buɗata ne in ɗinketa". Hawayenda ya zubo mata sanadin rumtse idanunta ne, ta share da hijabin kana ta juya ta fuskanci al'ƙibila. Shi kuwa Sheykh bakin gadon ya dawo, da nufin gyarawa yana janye blanket ɗin yayi maza ya maidashi tare da cewa. "Subahanallahi har haka ta zubda jini". Gaba ɗaya tausayinta ya rufeshi wani irin abu na musamman yakeyi a kanta yana ratsa dukkan jikinshi da zuciyarsa. Ita kuwa Aysha tana idarwa ta zauna tana sharce hawayenta dake silalowa tana mamakin wasu zantukan Yan Sheykh yana abu ko a jikinsa kamar bashi yayi wannan abun ba. Tana shafa addu'a yace. "Taso zo muje kici abinci in dubaki, tafiyar kin nan batayi minba, akwai matsala". A hankali ta yunƙura ta tashi dan tabbas yunwa ke son hallakata. Da sauri ya isa gareta sabida ganin ta dafe kai ta rumtse idanunta tayi baya alamun zata faɗi. Ruggumeta yayi a jikinsa tare da tallabe kanta. Luuu yaga idanunta na tafiya alamun suma zatayi. Murya can ƙasa tace. "Yah Sheykh duhu nake gani, jiri nakeji kaina ciwoooo". Da sauri ya tallabota jikinshi. Kan gadon babu inda zai ajiyeta dan haka ya wuce falo da ita. Bisa 3 str ya kwantar da ita dai-dai lokacin kuma taja wani dogon numfashi ta fara wani irin karkarwa da rawan sanyi alamun tana gab da sume mishi. Cikin ɗan ɗaga murya yake kiranta yana ɗan marin kumatunta. "A'ish! A'ish!! A'ish!!! Tashi! Ummi! Ummi!!". Ya ƙare kiran Ummi da ƙarfi dan gigice Ummi dake bakin ƙofar falon zata shigo musu da breakfast ɗin su ne, tayi sallama tare da shigowa da sauri, bisa santa table ta ajiye tray'n tare da isowa inda suke a kiɗime tace. "A subahanallahi Sheykh sata a jikinka, sata a jikinka". Da sauri ya jawota jikinshi ya ruggumeta gam-gam. Ita kuwa Ummi gefe ta tsaya tana cewa. "Subahanallahi". Kar-kar haka jikinta ke rawa har nashina na rawa. Da sauri Ummi ta juya falon. Wayarta ta ɗauka da sauri ta kira Dr Kubra tace suna buƙatar taimakon gaggawa. To Dr Kubra tace kana ta fara shirin tahowa. Ita kuwa Ummi falonshin ta koma. Cikin mamaki ta iso kusa dasu. Ganin jikin Aysha ya dena karkarwan ta kuma buɗe idonta. a hankali ya sauƙe numfashi kana ya medata kan kujerar ya ajiyeta, sannan ya gyara zamanshi a hankali yace. "A'ish". Kauda kanta tayi daga kallonshi ta kalli Ummi. Cikin sanyi da disashewar muryar tace. "Ummi yunwa nakeji, kaina ciwo jiri nakeji'. Da sauri Ummi ta ɗauki cup kunun kanwan nan mai haɗin mazarƙwaila da citta kanamfari. Ta zuba a kofin da yakeda da girma saida ta cikashi. Kana ta matso kusa da ita, kofin ta miƙa mata, amsa tayi da sauri takai bakinta. Kafa kanta tayi ta fara sha, tanayi tana ɗan cire kofin dan zafin kunun. Shi kuwa Sheykh matsawa gefe yayi, ya fara daddanan wayarsa idonshi kuma na kanta, kunyar Ummi ya sashi ɗan matsawa. Ita kuwa Ummi sannu take yiwa Aysha. Da sauri ta juyo ta kalli Sheykh jin yana ce mata. "Ummi Abba yace ki kaiwa Lamiɗo beshit". Cikin kauda kai tace to. Ta lura kunyar ta kusa tasashi ya maida kanshi cikin wayar da yake dannawan. Kai tsaye bedroom ɗin ta nufa. Cike da farin ciki take kallon shimfiɗan. Ture blanket ɗin tayi ta haɗe beshit ɗin kana, ta shimfiɗa blanket ɗin, sannan ta fito. A falon ta wucesu yana sunkuye kamar yadda ta barshi yana danna wayarsa, Ita kuwa Aysha kunun take sha, tana mai jin daɗin shi a bakinta. Kai tsaye Side ɗin Sarki Nuruddeen ta wuce. Har cikin ɗakin Gimbiya Aminatu ta wuce. Durƙusawa gaban Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa. "Allah hokke sabbugo Ga tabbacin tantanin Aysha uwar gidan Sheykh." Wani sihirtaccen Murmushi Gimbiya Aminatu tayi kana ta tashi zaune daga kishingidar da take, cike da farin ciki tace. "Alhamdulillah mafarki mu nata dabbata kamar yadda muke dako, yau Allah ya nuna mana dare mai cike da ruwan sama da walƙiya da rugugin tsawa. Kana ga tabbacin kyakkyawan budurcin bafullatanar daji, zantu kan malam Musa na baiyana ɗaya bayan ɗaya." Sai kuma ta kalli zanin gadon da jinin ya ɓatashi sosai. Cikin ƙasaita tace. "Maza a haɗa tukuicin budurci, domin ta bawa Jabeer kyauta mai tsada a bata tukuici mai girma." To Ummi tace kana ta miƙe ta fita ta nufi ɗakin tukuicin. A can Side ɗinsa kuwa, bayan ta shanye kunun sai ta koma ta konta bisa kujerar tayi lib, wani irin zufane yake tsastsafo mata tako ina na jikinta limshe ido tayi tana jin raɗaɗin jikinta. Shi kuwa Sheykh da alamun wani abu mai mahimmanci yakeyi a wayarsa. Koda ya ɗago kai yaga ta lumshe idonta sai yayi zaton ko bacci tayi. Gimbiya Aminatu da Lamiɗo da Galadima ne zaune a falon Lamiɗo, Ummi na zaune a gabanta da wasu manyan ƙore da daro irin nada. Cikin girmamawa ta jawo ƙwaryar dake kusa da ita, A hankali ta fiddo wasu manyan al'kyabba irin na matan sarakuna guda uku. sai kuma ta fiddo wasu kekyawawan yan kunne da sarƙa mai masifar kyau, na gold. Wasu aworworo ta fiddo na asalin azurfan masarautar Joɗa, wanda yake da sirruka, domin matuƙar mutun mayene in ya leshesu zaiyi bayani da kansa. murmushi Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa. "Tun bayan Ayshancan ba, sake danƙawa wata mace sarƙar tamɓarin Masarautar Joɗa ba, gashi da ita dashi duk basu tsira ba. Ina fargabar a sake baiyana wani a ahlinta. kada tarihi ya maimaita kanshi. Murmushi Lamiɗo yayi kana yace. "In Sha Allah babu komai fashe al'kyairin Allah, Magauta sunyi tasu nasarar sun gama, yanzu lokacin masu gaskiya ne". Shiru Abba yayi yana jin kalaman iyayen nashi, suna masu uzzuro mishi ciwon dake zuciyarshi. Galadima kuwa kwalin babban ashanan da Ummi ta buɗe wanda yake cike tab da ƴaƴan ashana ya kalla tare da yin murmushi. Wannan itace babbar shaidar mace in ta kawo budurcinta gidan mijinta a masarautar Joɗa. Shine asa kwalin ashanan a cikashi tab da yayansa, in kuma bata kawo budurcinta ba, sai a zazzage ya'yan ashanar asa fonko haka ba ɗa ko ɗaya a ciki. Kuma za'abi sashi-sashi na Masarautar a nuna kowa shaida to indai anga fonko babu ɗa a ciki to shaidar ta zubda budurcinta a woje. Ci gaba da ɗaga kayayyakin Ummi tayi. tana nuna musu. Ɗaya daro ta jawo shi kuwa, silke ne da sirdi a ciki sai linzamin doki, kana sai takalman hawa doki kala biyu na mace dana miji, sai kuma ɗaya kwaryan cike yake da gero sai citta da kanamfari sai kwalin sugar irin mai ƴaƴan nan. Kai ta ɗan ɗago ta kallesu tare da cewa. "Ga haɗin kayan da dawakai biyu mace da namiji ɗaya macen na Aysha ɗaya namijin na Sheykh. Sai kuma kyautar zabbi ashirin na jinyar Aysha daga Masarautar Joɗa." Cikin jin daɗi Gimbiya Aminatu tace. "Masha Allah. Allah ya sanya al'khairi, kira yan rakiyarki su rakaki ku nunawa kowa dake Masarautar Joɗa. To Ummi tace kana ta miƙe ta fito falon forko dasu. Saratu da Larai ta kira sukazo suka ɗauki kayan. Nan suka fara da sashin Hajia Mama. Koda aka nuna mata kayan shiru tayi cikin wani irin yanayi ta gyaɗa musu kai tare da nuna musu hanyar fita ba tare da tace ko ƙalla ba. Daga nan gidan Galadima da sauran dottawan masarautar suka nufa. Sai da suka gama da gidajen manyan kana suka nufi, Side ɗin Gimbiya Saudatu kasancewar itace matar babban ɗan Lamiɗo. Wani irin masifeffen kallo tabi sarƙar tamɓarin Masarautar Joɗa da akasa cikin kayan kana ta kalli Ummi tare da cewa. "Uhummm za'a kuma kenan, wata sarƙar aka kirkiro ko dai waccar ɗin ce aka gano? Ita dai Ummi kai ta sunkuyar. Ita kuwa Gimbiya Saudatu Baba Basiru dake gefenta ta kalla tare da cewa. "Ashe ɗan naku waliyi ne?". Da sauri yace. "Waliyi kuma". Cikin takaici tace. "Eh to gani nai wata shida kenan da yin aure. Ace bai kusanceta ba sai yauwa ai da gani kasan munafurcine da ƙarya, harda basu dawakai ma'aurata ko meye manufar hakan?". Cikin nuna tsantsar tsana Baba Basiru yace. "Wani salone hakan". Ita dai Ummi dasu Saratu sun gaza tashi. Cikin bala'i Baba Nasiru da yanzu ya shigo yace. "Kai da Allah ku ɓace min da gani". Da sauri suka ɗauki kayayyakin suka fice, sukaci gaba da nunawa. Su kuwa Gimbiya Saudatu da muƙarraba ta suakaci da tattaunawa. A hankali Dr Kubra ta shigo falon ta sallama a bakinta. Su Jalal ta samu suna breakfast kamar kullun. A falon ta zauna bayan sun gaidatane, Jamil yace. "Ummi tayi cikin masarautar Joɗa jirata zata zo". "Okay ba matsala". Dr Kubra ta faɗi tana gyara zamanta. Jim kaɗan sai ga Ummi ta shigo su Saratu na biye da ita a baya da kaya niƙi-niƙi. A ƙa'ida a hannun miji za'a danƙa kayan sai ya haɗa da nasa tukuicin ya miƙawa amaryarsa. Cikin sakin fuska Ummi ta kalli Dr Kubra tare da cewa. "A a lale marhabin da Dr". Murmushi tayi kana tace. "Yauwa Ummin Sheykh ya mai jikin". "Alhamdulillah jiki da sauƙi. tace. Tana amsar kayan hannun Saratu. Tare da cewa. "Yauwa kawosu nan, kije ki kawowa Dr ruwa". To Suratu tace. Ita kuwa Ummi amsar kayan tayi kai tsaye falonshi ta nufa da sallama a bakinta, yadda ta barsu haka ta samesu. kai tsaye bedroom ta wuce da kayan taje ta ajiye kana ta dawo ta wuce ta ɗauko sauran sannan taje ta ajiye, tana fitowa tazo kusa dasu cikin kula tace. "Yauwa Sheykh gacan tukuicin masarautar Joɗa, sai ka da kashi gareta sanda kaso". Kai ya jinjina ba tare daya ɗago kanba. Ita kuwa Ummi Aysha ta kalla tare da cewa. "Aysha tashi muje ga likita tazo". Cikin sanyi ta buɗe idonta kana tace to. Ita kuwa Ummi tuni tayi gaba. Yunƙura tayi a hankali ta miƙe tana mai cewa. "Wash Allah na". Miƙewa tsaye yayi tare da cewa. "Allah'nmu dai". murmushi yayi ganin yadda ta fara tafiya. Cikin yin ƙasa da murya yace. "Dawo ki zauna ba inda zakije kina tafi like ƴar kaciya. ki tsaya zan duba abina da kaina, zanyi gyaran ɓarnar da nayin". Cikin rauni tace. "Ni bana so ita zata dubani". Kanshi ya gyaɗa kana yace. "Okay". Ummi kuwa jin shirune yasa ta dawo, nan yace su shigo nan ɗin. A mutunce Dr Kubra ta gaisa da Sheykh kana ta kalli Aysha cikin kula tace. "Meke damunki?". Ido ya ɗan zuba mata don jira yake yaji me zata ce. Ajiyan numfashin yayi a hankali jin tace. "Kaina ne ke min ciwo sosai, sai kuma zazzaɓi, da jiri nakeji idona na ganin duhu". Juyowa tayi ta kalli Sheykh cikin sanyi tace. "Dr ni ai bansan ka dawoba, da bazanzo ba. Gaka a wuri kuma me amfanin nemana. Yanzu zamu fita da Jamil sai in turo mata mgnin da kaga ya dace". Kai ya jinjina kana yace. "Kin san maganin wanda baka saniba yafi daɗin karɓa a wurin wasu, rubuta mata kawai ba matsala ki bawa Jamil ɗin ya kawo." To tace tana murmushin yadda Aysha ta turo baki. Bayan ta fitane Ummi kuwa ta zauna. Ferfesun zabi ta zuba a plate yana zuba tiriri mai ƙamshi kana tasa mata tea, sannan tace. "Zoki zauna kici kinji ko!". Tana faɗin haka ta fita. Shi kuwa Sheykh kanshi a sunkuye idonshi kuma na kan Aysha, a fakaice yake kallon Ummi bayan Ummi ta fitane, ya ɗan ɗago kanshi kana ya ajiye warshi, kusa da ita ya matso, a hankali ya gyara zamanshi suna fuskantar juna, Fork ɗin ya ɗauka ya riƙe yana dan sa Fork ɗin yana saɓule kasusuwan daga jikin naman kanshi a sunkuye yace. "Ki dena hararata mana, me nayi miki haka kike min mugun kallo?". Tura ɗan bakinta tayi cikin zubda hawaye tace. "Ni ban harareka ba". Kanshi ya gyaɗa ba tare da ya kalleta ba, kana ya sa hannunshi ya ɗauki cup ɗin, miƙa mata yayi har kusa da bakinta. Kana ya gyaɗa mata kai alamun ta sha. Wani irin lumshe ido tayi hakan ya bawa hawayenta daman zubowa. a hankali ta buɗe idonta ta zubasu kan fuskarsa, wani irin masifeffen abu takeji cikin zuciyarta, zirin kwayar idanunshi ta zubawa ido. Tabbas Yah Ba'ana kekyawa ne ajin forko, amman yau data nazarci fuskar Sheykh sai take ganin ko rabin kyanshi Ba'ana bai samuba. A hankali ta buɗe lips ɗinta jin ya manna mata kofin. Lumshe ido tayi lokacin da taji ɗumi da ɗanɗanon team ɗin, wanda yake tamkar Ummey'nta ne ta haɗashi. Kaɗan tashe ya janye kofin, kana yasa Fork din ya soki tattausan soƙan gasashen naman. Bakinta ya nufa sashi tare dasa hannunsa ɗaya ya riƙe hannun damanta ya fara murzawa a hankali kana cikin yin ƙasa da murya yace. "Haa". Ya ƙare abun da alamun ta buɗe bakin. Haka nan taji ta kasa yi mishi musu, cikin sanyi ta buɗe bakin yasa mata tsokar, Ido ta lumshe sabida wani irin masifeffen daɗi da taji naman yayi mata, Allah ya sani bata taɓajin gashin naman da ya mata daɗi irin na yau ba. wani ya kuma bata, still ta amsa taci. Kana ya kuma bata cup ɗin tea ta kurɓa, haka yayi ta bata tanaci yana bata tea kana yana murza tafin hannunta cikin nashi saida tayi gyatsa kana a hankali tace. "Alhamdulillah". Ganin ya kuma miƙo matane yasa ta kauda kanta tare da lumshe idanunta tace. "Yah Sheykh na ƙoshi". Kanshi a sunkuye yace. "Ban yardaba". A hankali tace. "Allah kuwa". Numfashi ya ɗan fesar kana yace. "To muga cikin". A hankali tace. "Gashi". Hannunshi yasa bisa cikin nata, kana a hankali yace. "Ɗaga rigar". Tura baki tayi cikin jin bacci tace. "In ɗaga kuma?." Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. "Na'am ki ɗaga inga in cikin ya cika, sai muje bedroom inga wurin ciwon kuma". Cikin zuba mishi ido tace. "Uhumm". Sai kuma ya ajiye plate da cup ɗin a gefe kana ya miƙe tsaye, hannunsa yasa ya miƙar da ita tare da cewa. "Mu tafi bedroom". Kai ta gyaɗa kana ta juya kamar zatayi bedroom nashi, sai kuma tayi maza ta nufi ƙofar babban falon da sassarfanta tanayi tana buɗa sawunta alamun tana jin ciwon tafiyar. Ganin kamar yana biyo tane yasa ta ɗanyi ƙara tare da cewa. "Wayyo Ummey zai kamani". Sai kuma ta fara sassarfa tanayi tana yarfa hannunta. Ido ya zuba mata yana kallon tafiyarta, cike da wani shauƙi. Murmushi yayi kana ya ɗauki sauran tea ɗin ya shanye. Ajiye cup ɗin yayi ya tsallaka kwanukan ya nufi bedroom ɗinsa dan gaba ɗaya jikinsa ba ƙarfi yakeji ga alamun zazzaɓi ga bacci ga wani masha'hurin farin ciki. Yana shiga ya kwanta lokacin ɗaya kuma bacci yayi gaba da shi. Aysha kuwa a can falonsu ta samu Ummi, riƙe waya da alamu da Umaymah take mgna. Tana ganinta ta mike tsaye tare da kamo hannun ta, bedroom ɗin Ayshan suka nufa tana mai cewa Umaymah. "Alhamdulillah komai ya kusa baiyana da izinin ubangiji. Gata ma". Ta ƙare mgnar tana miƙawa Aysha data zaunar a bakin gadonta waya, cikin sanyi Aysha ta amsa kiran da Umaymah tayi mata. Ido ta lumshe tare da konciya ta juya ta bawa Ummi baya sabida masifar kunya da takeji, da sauri ta kuma rumtse idanunta jin Umaymah na cewa. "Sannu ko Aysha, Allah ya miki al'barka yasa al'barka a taraiyar ku, Allah yasa nanda wata goma masu zuwa inji lbrin haihuwar jika kamar yadda naji lbrin tukuicin masarautar Joɗa." Cike da kunya tayi shiru sai dai a zuciyarta tace. "Amin". Ummi kuwa falo ta fito jin muryar Jamil. Ledan magungunan ta amsa tare da nufar Dinning area fridge ta bude DuDu mai sanyi ta dauko, ta dawo ɗakin Aysha. Magungunan ta bata tasha da sassayan DuDun kana, ta gyara mata rufuwan ta, sannan ta amshi wayar ta juya ta fita tana mai ci gaba da mgna da Umaymah tana gaya mata abubuwan da aka haɗawa Aysha na tukuici. Ita kuwa Aysha tuni bacci yayi awon gaba da ita. A can birnin Yahunde kuwa na ƙasar Cameroon, Ba'ana ne zaune gaban bokanshi sun sa kasko a gabansu. Cikin tuhuma Ba'ana yace. "Tun ɗazu nake cewa ka buga min ƙasa inga Mata inga meke faruwa da ita, sai kayi tamin zanen banza ka gaya min meya faru?." Cikin tsananin tsoro da kaɗuwa Boka yace. "Ba komai ita bacci ma takeyi yanzu haka. Kaje sai jibi mu buga muga meke wakana' dan sam yau abun yaƙi nuna komai sai haske mai kashe ido". Cikin kwaffa Ba'ana yace. "Lallai kwannan zan tafi Nigeria dole zan koma domin amso matata dole zan tafi". Yana faɗin haka ya juya ya fita. Alhamdulillah Aysha kuwa tana farkawa bacci taji komai ya lafa sosai sai abinda ba'a rasa ba. Bathroom ɗinta ta shiga gasa kanta ta kumayi da ruwan ɗumi kana tayi wonka ta fito ta canza kaya, Sosai taji daɗin jikinta, sallaya ta shimfiɗa dan yin salla. Sheykh kuwa tuni ya nufi masallacin Masarautar Joɗa. Bayan ta idar da sallan Ummi ta kirata suka fito falo. Tana gaba Ummin na Binta a baya don so take ta kalli yanayin tafiyarta. Bayan ta zaunane Ummin ta ɗauko tray mai ɗauke da Foodflaks tazo ta ajiye a gabanta. Acan masallaci kuwa ana idar da sallan Sheykh ya nufo gida. Yana shiga falon, ko tsakiyar falon bai isoba yaji Muryar Gimbiya Saudatu a bayanshi tana cewa. "D...!" Littafin GARKUWA na kuɗine in kinason ga number ta 09097853287 kiyi min mgn By *GARKUWAR FULANI* [3/18, 9:19 PM] +234 806 559 0880: Akwai kayyakin gyara masu kyau na amare da uwar gidaye, harma da kayan ƙamshi. Idan kina buƙata kiyi min mgn ta WhatsApp 09097853276, akwai haɗin uwar gidaye da amare, akwai sabulai na gyaran jiki. Kana akwai kayyakin daɗi kan daɗi. Set ɗinsu hawa-hawa ne akwai na manya akwai na saffa-saffa akwai ƙananan robobi masu sauƙin kuɗi. Ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Kimin text ta inbox ko kimin mgna ta whatsApp yafi akan ki kirani dan da wuya in amsa kiran amman in kinmin text ɗin zamufi fahimtar juna.🤝🏻😘 Godiya ta musamman gareku Mommy Niger Mamana ta kaina, da Rafi'a ƙawar Shatu Yah Sheykh ɗina, ngd Matuƙa da taimakon ku Allah ya bar zumunci da ƙauna. Mom Sayyid da Rafi'a Ngd da fama da kurame Allah bar zumunci da ƙauna Ngd Ngd Ngd matuƙa. Jamila mainasara ina godiya da mutuntaka, Allah bar zumunci ina sane da soyayyarki gareni. Mutanen GARKUWA fan's 1 and 2 ina al'fahari daku. Kune mutanen da dukkan iya gskyarku ku gamsu da rubutuna wanda ko ɗigo ɗaya na littafina bakwa jira ku gani kuke saya da dukkan yaƙinin zaiyi muku daɗi, kuma Alhamdulillah kuna samun fiye da zatonku inba soyayya ba ace tun kafin in fara posting kun gamsu har in cika group 2 har a tafi na biyu Ina roƙon Allah ya bani aron rai da lfy da damar ƙarara littafin lfy ba tare da na tsallake muku koda rana ɗaya ba. GAREKU Special Group SPG 1. Kuma kunada cikekkiyar yaƙini kaina, kuma 2, 3, 4, 5 ban manceku ba fatan al'khairi da addu'a Allah yasa ku rage zaƙuwa😂😂😂🤪 masu hana kansu bacci dan jiran posting yaseen ni babu ruwana🤝🏻🥰😘 Ya ruggume ta a hankali. Wani irin juyowa tayi cikin tsaro da zazzaro, ta buɗe baki da ƙarfi tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". Ta ƙarashe addu'ar da ƙarfi tare da kyarma tana kuma juyowa. Da sauri yasa tafin hannunshi na dama ya kife bakinta, cikin tsoron kada ta kunyatashi ya ɗan ronƙofo kanta tare da cewa. "Ahhhhhhh dan Allah kiyi shiru ki nitsu nine". Wuƙi-wuƙi tayi da idanunta sai jujjuya kwayar idanun takeyi tare da sauƙe dogon numfashi. sai kuma tayi shiru tana kallon Kekkyawar fuskarta da matso da ita kusa da tata fuskar. A hankali ta lumshe idonta jin ya cusa kanshi tsakankanin wuyanta da kafaɗarta, hancinshi ya manna bisa fatar wuyanta. Idonshi ya lumshe tare da shaƙan daddaɗan ƙamshi jikinta. a hankali tasa hannunta ta jawo wayarta dake kan pillow'nta, wanda take jiyo muryar Rafi'a nacewa. "Hello! Hello Shatu lfy kuwa meke faru?". sabida ita Rafi'a bataji mgnar Sheykh ba sabida a hankali yayi mgnar. Cikin sanyi ta ɗan maƙe kafaɗarta jin yasa harshensa yana lasar kunnenta. cikin daburtacciyar murya tacewa Rafi'a. "Uhmm ah u uhnn ba... ba komai fa, ina jinki". Ta ƙarashe mgnar tana gyara konciyarta. Shi kuwa Sheykh cikin wani irin baƙon yanayi da baƙon murya yace. "Hirar me kikeyi da tsakiyar dare, ke da waye?". Cikin sanyi tace. "Rafi'a ce". Bai ce komai ba, sai hannunshi yasa, ya jawo wayar katse kiran yayi kana ya cilla wayar kan bed side drower. Ronƙofowa kanta yayi sosai. ya zama bayanta na manne da kirjinsa, a hankali ya cusa hannunshi cikin rigarta. hancinshi ya ɗan goga a haɓarta. Kana ya saita bakinshi cikin kunnenta a hankali ya fesa mata sassayar iskan bakinshi. Yar-yar haka taji duk tsikar jikinta na mimmiƙewa. Wata fitinenneyar kasala ta rufeta. Lumshe idanunta tayi a hankali. sabida wani irin sanyin da taji tafin hannunshi dake kan fatar cikinta. A hankali yake shafa cikinta, tare da zira yatsarshi cikin hudar cibijiyarta, murya can ƙasa cikin maƙoshj yace. "Aieeeeesh". Yada yaja sunan da yadda taji yayi ƙasa da tafin hannunshi yana cusa hannun cikin pant ɗinta yasata yin wani narkekken numfashi tare da cewa. "Uhhhhhhhmmmm". ƙafarshi ya ɗaura kan nata sawun kana murya a narke yace. "Ya ciwonki?". Jikinta na tsuma jin ya cusa hannunsa kan mararta, yana shafawa a hankali yasa cikin tsoro tace. "Yana nan bai worke ba". Tayi mgnar a nufinta zai bar abinda yakeyi. Gaa mamakin ta sai taji yana cewa. "Ohhhh sorry bari yanzu in duba miki shi in sa miki mgni kinji ko?". Ya ƙarashi mgnar ya juyota rigingine. Kana yasa hannunshi ya fara murza pant ɗinta ƙasa. Da sauri ta riƙo hannunshi tare da yarfa hannun ta ɗaya cikin tsoro tace. "A a ka bari zai worke da kanshi". Jin yadda jikinta ke karkarwar ne yasashi zaro hannunshi. Mayatattun idanunshi dake tsume da fitinenneyar sha'awar ya watsa mata cikin nata, wanda su kuma tsoro ya baiyana cikinsu. Harshensa ya ɗan zaro kana a hankali ya sunkuyo kanta, tattausan lips ɗinta ta lasa tare da cusa hannunshi cikin rigarta yayi sama dasu. Da sauri tasa hannu ta riƙe damatsan hannunsa tare dayin zillo ta banƙaro ƙirjin ta sama, jin yadda ya cabko Caɓɓullenta, yayi musu wani irin gigitaccen kamo, tare da furta wani sauti mai haɗe da kiran sunanta. "Shhhhhhhhhhhh Aissssssssh". Cikin wani irin kasala daya sakar mata sabida kiran sunanta da yayi a haka cikin kunnenta yasata kiranshi a raunace. "Yahhhh Sheykhhhh". Bakinshi ya manna kan nata, madadin ya amsa mata. wani irin masifeffen kamu yayi harshenta, wanda saida tayi zillo tasa hannunta duka biyu ta ruggumeshi gam-gam a jikinta. Allah ya sani Yah Sheykh ya iya Kiss da kiss daya yake iya gigitata. Shi kuwa Sheykh wani irin tsotson tom-tom ya fara yi mata. Yayinda gaba ɗaya jikinshi ke tsuma, abin ya haɗun masa biyu. Ga masifeffen feelings da yakeji, ga azabebben zazzaɓin da ya rufeshi. Kana ga shauƙin jin wani irin sahirtaccen rugguma da Aish tayi mishi wanda saida yaji Jabeer ɗinsa ta miƙe tayi sama. Cikin rawan jikin ya zaro harshensa, kana ya juyota rigingine. Jiki na rawa, yasa hannunshi ya kwance igiyoyin dake sarƙafe gaban rigar baccin nata. Ido ta zuba mishi ganin yadda jikinshi ke rawa. ta kasa koda motsi sabida ya gama kashe mata jiki. Jiki na rawa ya zare rigar ya cillata gefe. a hankali tayi wani irin miƙa mai cike da ma'anoni. Lokacin da taji ya manna bakinshi kan breast ɗinta, kana hannunshi ɗaya kuma ya ci gaba da murza pant ɗin ta yana ƙasa dashi, cikin wata iriyar fitinenneyar murya mafi rauni da ɗai-ɗai cewa tace. "Ya! Ya... Yah. Yahh Sheykhhhh, hyyyyhhhh". "Uhhhhhhggmmmmmm". Haka yaja mata wani dogon numfashi tare da cilla pant ɗinta gefe. Ita kuwa Aysha yatsunta ta cusa cikin sumar kanshi tare da rumtse idanunta jin yadda yake lailaye mata nimple ɗinta da harshensa. Kar-kar hakan jikinsa ke rawa, cikin kiɗima ya janye kansa daga gareta. Jiki na rawa ya zare rigarshi ya cillata can ƙasa lungun gado. tallabota yayi jikinshi gaba ɗaya. Gyara mata konciyarta yayi bisa tsakiyar gadon.da sauri ya ɗan ware sawunta. Tsakiyar sawunta ya zauna, tare da rinƙofowa, har zuwa kan cikinta harshensa ya zira cikin hudar cibijiyarta ya rinƙa yi mata wani irin masifeffen abun da yasata, cilla wani ɗan nakashesshen sauti mai haɗe da fitan numfashin kiɗima. Hannunshi kuma duka biyu suna bisa ƙirjinta. wani irin shafawa yakeyiwa breast ɗinta tare da leleyesu, haka yasa, ta buɗe bakinta a hankali murya can ƙasa kamar maiyin raɗa take cewa. "Yah Sheykhhhh, hyyyyhhhh Hamma Jabeeeeeeeeer Yah Sheykhhhh. Da sauri ya meda kanshi duniyarta. Wani irin zillo tayi tare sayi wani irin miƙa kana ta buɗa kekkyawan sawu ta,. Jin ya zira harshensa cikin PP ɗinta. Kar-kar haka takejin illahirin jikinta na karkarwa. wani irin masifeffen kuma azabebben abu takeji mai matuƙar daɗi da gigita ƙoƙolwarta yana game dukkan jikinta da jininta hannunta ta cusa cikin sumar kanshi ta yamutsa suman. Shi kuwa Sheykh hannunshi yasa bisa cikinta nan ƙasa kusa da mararta ya ɗan danne ta famintar zillewa take ta son yin. Da ɗan ƙarfi take fidda numfarfashin gigita. "Auwoooo, hyyyyyyyyhhh ahhhhhhh". Wani irin gigi tacce tsalle tayi tare da faɗawa jikinshi ta rungume shi gam a jikinta, sabida Sheykh yana gab da haukatata. Shi kuwa jin yadda ta abka jikinshi ne yasashi tashi zaune jiki na rawa. hannunshi yasa cikin gajeren wondon shi, Jabeer ɗinsa da ke barazar tsinkewa ya kamo da ƙarfi, ya fito dashi ya cusa mata cikin tafin hannunta. Kar-kar haka duk suka fara karkarwa. Gaba ɗaya da jikinta rawa yakeyi baza iya mishi komaiba. Ita kuwa Aysha jin Jabeer ɗinsa a tafin hannunta yasa kuma gigice. jikinta ta fara janye wa,. tana jujjuya mishi kai. da sauri ya riƙota, ware sawunshi yayi ya ajiyeta tsakiyarshi. sai kuma yasa hannunshi ya tureta ta faɗa ta baya ta konta. a hankali cikin rawan murya kamar mai kuka yake cewa. "Uhhhhhshhhhhh Aishhhhhhhh". Cikin yarfa hannu tace. "Hamma Jabeer kayi haƙuri ban workeba, ciwon bai workeba." Hannunshi yasa ya shafo pp ɗinta da yaga tana tsiyaya. a hankali ya hauro kanta, cikin rawan jiki ya kusanto Jabeer ɗin sa, da Shatunta. Da azaban ƙarfi ta rumtse idanunta tare da buɗa baki tace. "Washhhhh haahhyyyy Washhhhh Allah na, Yah Sheykhhhh zafi". Dai lokacin kuma taji ya kuma ziyartar jikinshi gareta. Da karfi ta yarfa hannunta tare da sakin kara ta buɗa sawunta wai ko zataji sassaucin zafin karɓar bakwancinsa a karo na biyu murya na rawa tace. "Wayyo Allah Wayyo Ummey na. Yah Sheykh zafi.zafi.zafi.zafi zafifa". Cikin gurnani da kasa control ɗin kansa da muryarsa yace. "Wowwwhhhhh Washhhhh Shyyyyyyyyyah Aishhhhhhhh". Dai-dai lokacin kuma Ummi ta tashi daga bacci ɗan fitsari daya matsa mata a hankali ta miƙe zaune. Can ɗakin Shatu kuwa, cikin rauni da zafin da take ɗan ji take jujjuya kanta tare data tafin hannunta ta damƙi damatsan hannunsa, tana mai jujjuya kai take kuka mai cike da raki da shogwaɓa take cewa. "Yah Sheykh zafeeeh zan mutu." Can sama yaji kalmar ta ta karshe, wacce ta daki kahon zuciyashi cikin rawan murya taji yana cewa. "No! Aishhh bazaki mutuba, kunti ba'adu jasadi Yah Aish". Kai take ta jujjuyawa hawaye raki na tsiyaya babu gaggauta wa,. Murya a shogobe ta kuma cewa. "Yah Sheykh zafi na gaji, Wayyo! wayyo! wayyo! Zafee". wani irin kwaƙuma yayi mata wanda yasata, yin ihu mai ɗan ƙarfi. "Wayyoooo ooo Ummeey na zai yagani". Bafaya jinta zuwa yanzu sabida ya tafi duniyar da Hamma saif yaje kuramtarsa ta worke da gurguntakarsa, (NAKASA BA KASAWA BACE) yaje duniyar data faransa Hamma Haydar zama Balarabe,( BANDIRAWO) yaje duniyar datasa Hamma Yusuf yace in yayi shiru baiyi ihuba daɗi zai ƙumemeshi a ciki ya kasheshi (HUKUNCIN ALLAH). Wani irin gurnani da surutai yakeyi tamkar ba Sheykh mai libga-libgan al'kyabbas ba. wani irin masifeffen ƙara tasa lokacin da taji yana wani irin zabura da kamar doki. gaba ɗaya ya jikkatata. Kuka ta farayi sosai tanayi tana yarfa hannu tare da ture ƙirjinsa. Ƙankameta yayi tare da manneta a jikinsa da karfin masifa sabida wani irin azabebben masifeffen daɗi da yakeji yana gab da sumar dashi in yaci gaba da rufe bakinsa cikin rawan murya da karkarwa ya fara cewa. "Subahanallahi! Alhamdulillah la'haulawala ƙuwta illabillah aliyul axeem, Jazakallahu khairan Yah A'ish kuntil lagamee Yah Aishhhhhhhh laisa li misluki abadan Dazakallahu ilman wa fikhran wa yatta ƙi Allahu jami'an". Ummi kuwa cike da tsoro ta miƙe tsaye jiyo kamar muryar Aysha tana kuka da surutai. jiki na rawa ta lalubo kallabinta kana ta sauƙo kan gadon. Shi kuwa Sheykh gaba ɗaya ya gigice sai larabci yake bugawa, da tasbihai tamkar a bakin masallaci yake. Ita kuwa Shatu sosai take zuba taɓara da raki da zallar shigoɓa da kukan zafin da takeji. Cikin wani irin gamsuwa mai cike da jin daɗi ya mirgina gefenta ya kwanta lokacin da ya gama zazzage mata yayyafin shi. Jawota yayi jikinshi ya ruggumeta tsam cikin meda numfashi yasa hannunshi yana shafa kanta zuwa bayanta tare da cewa. "Afwan Yah A'ish, kiyi haƙuri dena kuka kinji ko, boɗɗon Ummeyna na barki haka". Cikin shogoba ta fara tumurmushe da bubbuga kafa still har yanzu kuka takeyi dan gsky taji azaba, kuma har yanzu ji takeyi kamar Jabeeeeeeeeer ɗinsa na cikin jikinta, sabida wani zogi da raɗaɗi da wurin keyi mata cikin kuka da raki da ɗan daga murya tace. "Hiyyhhh Wayyo Ummey na, zafi zai yagani Ummey". Wani irin yalwataccen murmushi mai cike da zallar jin daɗi yayi tare da cewa. "Kiyi haƙuri na tuba, kada ki haɗani da Ummeynki bazan yagaki ba, kinji ko boɗɗon Ummey." Cikin ɗaga murya da ɗan bubbugeshi tace. "Wlh sai na faɗa wa Ummey na kamin mugunta Wayyo Ummey na". Dai dai lokacin kuma Ummi ta fito daga ɗakinta da sauri ta nufo bakin ƙofar ɗakin Shatu. Shi kuwa Sheykh cikin tsoron kada ta jawo hankalin Ummi garesu, ya ɗan saketa tare da jawo gajeren wondoshi ya fara zirawa yana cewa. "Dan Allah kada ki tara min jama'ar masarautar Joɗa, kinga haka kikayi last time ma, Ummi tajimu kafinma inje masallaci ta kira Gimbiya Aminatu ta gaya mata, ita kuwa ta gayawa tsoffin sa'idon nan tun a masallaci suke tamin kallon tuhuma kamar ba matata na raɓaba". Manna kanta tayi da pillow'n tare da zuba mishi ido kana da ƙarfi cikin salon tsokana da raki tace. "Sai na gaya Ummi". Tayi mgnar cikin son ganin ya zaiyi. Ai kuwa cikin tsananin zaro ido ya kalleta sai kuma ya juya da sauri ya nufi ƙofar fita yana cewa. "Ni na tafi bari in bar miki ɗakinki tunda kunya tani kike sonyi". Ya ƙarashe mgnar yana fita. Ita kuwa Aysha haka nan taji murmushi ya tsubce mata. Shi kuwa Sheykh da sauri ya fita, kanshi ya sunkuye yana gyara zaman Jabeer ɗin sa cikin wondon. Yazo tsakiyar falon kenan, Ummi ma ta iso. cikin wani irin azabebben kunya mai tsanani ya juya da tsananin sauri ya fuskanci ɗakin Aysha, gaba ɗaya jikinshi karkarwa yake dan wata iriyar fitinenneyar kunyar data rufeshi. Itama Ummi cikin wani azabebben sauri ta juya a saba'in ta nufi komawa ɗakinta. Shi kuwa Sheykh gani yake baya sauri hakanne yasa ya haɗa da sassarfa. Yana shiga ya maida ƙofar gib ya rufe. Da sauri Aysha ta ɗago kanta ta kallishi, da sauri tace. "Lfy?". Ganin yadda jikinsa ke kerma. Bakin gadon yazo ya zauna, hannunshi yasa duka biyu ya dafe kanshi cikin muryar gsky da gsky cike da kunya yace. "Aishhhhhhhh da wanne idon zan kalli Ummi Aish kinsa ta ganni dagani sai gajeren wondon, a suffar da ke kaɗaice kika dace da ki ganni da ita duk duniya. Aish kin jawo ta fito da wannan rakin naki da kukan banza". Sai kuma ya juyo gareta jin tana mgn cikin shogwaɓa. cikin sanyi tace. "To ai zafi naji, shiyasa nayi ihu". Cikin takaici yace. "A haka zamu tabbata kenan? Duk sanda zan kusanceki sai kinyi tamin ihu kina tara min jama'ar gari". Bakinta ta ɗan tura kana ta koma ta kwanta. Shi kuwa Sheykh miƙewa yayi ya shiga Bathroom ɗinta. Ummi kuwa ai fitsarin da batayi ba kenan, sabida wata iriyar fitinenneyar kunyar Sheykh ɗin data rufeta. Dugungunewa tayi cikin borgon ta, tana tunanin tsawon shekaru ashirin da biyar kenan rabonta data ganshi da gajeren wondon. Oh ni Zainabu meya kaini fita, gidan mata da miji gashi naje nasa yaro jin kunya, da matarsa, ashe shiyasa yaketa zirga-zirga da kora su Jalal oh Jabeer ka yafe mana mun shiga lokacin ka". Haka tai ta surutu har baccin ya kuma kwasheta. Shi kuwa Sheykh yana shiga yayi wonka, towel ɗin ta da ya gani a ciki ya ɗaura. kana yana fitowa ya kalleta cikin alamun tausasawa yace. "Tashi kije kiyi wonka na haɗa miki ruwan ɗumi". Cikin sanyi tace. "To ka tafi tukun". Kanshi ya gyaɗa kana ya fita, da sassarfa ya koma Side ɗinsa. Ita kuwa Aysha a hankali ta miƙe ta shiga bedroom ruwan ɗumi daya haɗa mata ta shiga ta zauna. Kana tayi wonka sannan ta fito, riga kawai ta saka ta koma ta kwanta tanata numfashin gajiya a take tayi bacci. Shi kuwa Sheykh ganin karfe huɗu yayine yasashi. Fara nafilarshi. Cameroon Yahunde. Washe gari da safe. Ba'ana ne zaune gaban bokanshi, cikin tsareshi da ido cike da takaici yace. "Yau kwana biyar kenan in binka ka bincika min lamarin Shatu na, sai kai tamin hanya-hanya. Shekaran jiyan can kace min haske yayi yawa baka ganin komai, jiya nace ka duba kaƙi dubawa me kake nufi da nine wai?". Cikin tsanani tsoro da shakku bokan ya kalli Ba'ana cikin sanyi da tsoro yace. "Batun gsky bazan ɓoye maka komaiba tunda ka matsa ka sani. Sai dai in kayi al'ƙawarin bazaka cutar da niba". Cikin faɗa Ba'ana yace. "Kai ubanane ko uwata ko Shatu ce kai da zanyi maka alƙawarin bazan cutar da kaiba,. Ko ka gaya min ko in nuna maka ainihin waye ni. Dan ubanka dubo min Mata ko inci uwarka". Cikin rawan jiki da sadaukar da rayuwarsa dan yasan ko ya yayi Ba'ana zai kasheshi cikin rawan murya yace. "Koda zaka kasheni zan gaya maka gsky, ko kaso ko ka ƙi, gskya ta binne ƙarya, haske ya kori duhu. mutumin can mijin Shatu shine gsky kaine karya shine haske kaine duhu. Zan gaya maka gsky ko Allah zaisa ka yarda da wuri kada kayi makararran yarda irin nawa. Babu wani makami sama da addu'a, kuma babu wani addini na gsky sama da musulunci, addini mai cike da ni'imomin duniya da lahira, Sheykh yafi ƙarfin ka domin shi Allah da manzasa ya riƙe, bazaka taba iya cutar dashi da komaiba a duniya har sai dai in dama Allah yan ƙaddara zai cutu. Domin duk sihirina da mukayi kan cewa in ya kusanci Shatu yaji zafin dafin cizon kunamai, toshi wannan abun shegen daɗi yaji. Yakusance tun kwana huɗu baya, kuma daren jiyama kwana yayi tare da ita ya kusanceta yayi jima'i da ita babu abin daya sameshi saima lfy da girma da Jabeer ɗinsa ta ƙara dan ta samu gamsuwa da Shat.." Bai ƙarasa zancenba ya kurma wani irin gigitaccen ihu mai azaɓan ƙarfin amo, sabida wani irin zabura da Ba'ana yayi ya caka mishi ƙahon rago a dai-dai kan ƙahon zuciyarshi. Nan ya faɗi kwance jini na zuba cikin rawan murya na magagin fitar rai yace. "Baka da nasara, kada kaje Nigeria in ka koma ka kai kankane, babu abinda zaka iya yiwa wanda yake riƙe da addinin Musulunci da gsky da al'ƙur'ani littafin Allah." Yana faɗin haka ya rai yayi halinsa. Shi kuwa Ba'ana cikin wani irin masifeffen tashin hankali da kiɗima ya kurma wani ƙaƙƙarfan ihu tare da kiran Shatu da karfin kana yace. "Mata ganinan dawowa duk da nasan da wuya in iya shiga masarautar Joɗa, amman dole zan faɗaɗa bincike na, zan zama dodon tsafin kaina zanzo na saceki, dole sai na aureki na kusanceki naji daɗin ni'imomin jikinki na baki ciki kin haifu dani, bazan yi renon banzaba ko nononki ban taɓa taɓawa ba, wani can yazo ya cinye min budurcinki dole zai ɗanɗani azaba mai girma, sai na sake yi mishi ka ciya dan kan uwarsa". Tulun tsafin ya jawo gabansa yafara aikin da kansa. A can gefensu Bappa kuwa. Ummey ce zaune Junainah na gefenta amaryar Bappa nayi mata kitso, cikin sauƙe ajiyan zuciya Ummey ta kalli Bappa dake gefensu yana al'walan yin walaha cikin sanyi tace. "Bappan Shatu yaushe zamu koma Rugar Bani? Ina kewan Shatu, ina yawan mafarki da ita, ina son inje inda take". Murmushi Bappa yayi kana ya kalli Junainah dake cewa. "Bappa ai ni dai Addana tace dan Allah Yah Al'amin ya kai mata ni, ina ka yarda?". Cikin sanyi ya gyaɗa mata kai kana ya juyo ya kalli Ummey cikin tausayawa yace. "In sha Allah zamu koma Rugar Bani, amman da sauran lokacin komawarmu". A hankali Ummi tace. "Zai kai kamar yaushe?". Cikin sanyi yace. "In sha Allah zuwa wani ɗan lokacin". Kai Ummey ta jinjina dan ta fahimci ba rana kenan. A can Masararutar Joɗa kuwa, wunin ranar Sheykh wasan buya yakeyi da Ummi sabida masifar kunyarta da yakejin. Yau kwana biyu kenan da faruwar abin kuma, jikin Shatu yayi sumul yanzu bata jin ciwon komai. Ummi kuwa wani tsumi na musamman ta haɗa mata na masarautar Joɗa tana bata safe da yamma kofi ɗaɗɗaya, ita da kanta ta gamsu da kyan tsumin sabida ita kanta takanji tana tsiyaya duk sanda ta tuna Yah Sheykh. A hankali yake taku, har ya iso bakin corridor'n, kanshi ya ɗan turo, ya leƙa cikin babban falon, da sauri ya dawo da baya, sabida hango Ummi na tsaye tana miƙa wa Shatu wani abu a kofi. Ido ya ɗan lumshe tare da cewa. "Allah ya sani ina jin kunyan Ummi tayaya zan fito". Sai kuma ya ɗan leƙo, da sauri ya sako kai ya fito sabida hango Ummi bata wurin. A hankali ya iso tsakiyar falon. Ido ya ɗan zubawa Shatu dake kallonshi babu ko ƙebta ido. Yayi masifar kyau cikin shigarss, gaba ɗaya ta kasa janye idonta kanshi. Girarshi ɗaya ya ɗaga mata tare da cewa. "Aishhhhhhhh ya dai? Kinada matsala ne?". Cike da mamaki tayi ƙasa da kanta tare da sake gajeren murmushi. Cikin sanyi tace. "Ina kwana". Bakinshi ya ɗan taɓe tare da cewa. "Bana so riƙe gaisuwarki, tunda ban kai aje a gaisheni ba. Na lurama guduna kikeyi ko faloncan bakya son zuwa". Cikin yin ƙasa da murya tace. "To ba kai bane". Da sauri yace. "Nine me?". bakin ta kuma turawa tace. "Kaine kake min". Sai kuma tayi shiru, murmushi yayi kana ya matso kusa da ita. gefenta ya ɗan zauna a hankali ya kamo hannunta ya manna kan wuyanshi tare da cewa. "Aishhh." Cikin kula ta kalleshi jin jikinsa zafi jau-jau a hankali tace. "Yah Sheykh baka da lfy ne". Kanshi ya jinjina kana ya miƙa tsaye dan gudun kada wani ko wata yazo ya samesu a hakan, cikin sanyi yace. "Nima ban saniba Aish amman yau tsawon kwana bakwai kullum da zazzafan zazzaɓi nake kwana. Babu wanda ya sani da yake bani da gata, Umaymah na bata kusa, Mameyna bata kusa da ko ƙuda bazata bari ya sauƙa a kainaba." Ya ƙarashe mgnar jijiyoyin idanunshi na tsastsafo da wasu tafasassun hawaye masu ƙuna a zuciya. sai kuma yayi sauri ya juya ya fita. Cikin wani irin rauni, tausayi, so, shaƙuwa, kaunarsa. ta rakasa da ido, tabbas da Side ɗinsa ya koma da ta bishi a baya, sai dai kuma kash woje ya fita. Da yamma suna zaune a falon Umaymah ta kira Ummi bayan sun gaisa ne tace. "Ummin Jabeer Hajia Kubra na ba lfy tunda ta dawo auren Haroon, jiya mukayi waya da ita tace har an Bata gado. Amman an sallamesu yau da safe. Shine nake so dan Allah keda Juwairiyya kuje ku duba min ita da jiki. Nima kaina in sha Allah na kusa zuwa da zaran baƙinmu sun gama komawa, zanzo da Aunty Hafsat da Rahma". Cikin kula Ummi tace. "Ayyah Allah ya bata lfy. In Sha Allah kuwa zamuje mu dubota da jiki gobe". "Amin Amin, yau dan Allah kuje ku duba min ita". Umaymah ta faɗa cikin jin daɗi. Sai kuma tace. "Ya jikin ɗiyar tawa". Juyowa Ummi tayi ta ɗan kalli Shatu dake shan tsumin data bata tace. "Uhuhh yanzu dai anyi lfy sai kuma tsoro da raki". Dariya sosai Umaymah tayi dan Ummi ta bata lbrin abinda ya faru wancan ranar. Cikin yin ƙasa da murya tace. "Shifa ɗan naki". Miƙewa Ummi tayi ta nufi kitchen tare da yin ƙasa da murya tace. "Uhumm kedai bari ai mun zama surkan juna wlh har yau ɗin nan ban kuma ganinshi ba. Ni ina jin kunyarsa haka shima yana jin kunyata, itako ɗiyar taki sarkin raki ko a jikinta". Murmushi Umaymah tayi tare da cewa. "To yar taki zakiwa faɗa ta kula da mijinta fa bata san irinsu ba in sunji mace basa iya dogon haƙuri". Dariya sukayi kana suka katse kiran. Falon ta dawo dai-dai lokacin kuma Sara ta shigo. Gefe ta zauna jin Ummi na cewa Jamil. "Gobe in Allah ya kaimu zaka kaimu, gidan hajia Kubra aminiyar Umaymah mu dubota da jiki nida Juwairiyya". Kai ya gyaɗa alamar "To". Da sauri Shatu ta kalli Ummi cikin zumuɗin son fita tace. "Yauwa Ummi nima zanje". Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Eh ki tambayi mijinki in ya barki sai muje". Kai ta ɗan kauda tare da cewa. "Kai dai Ummi sai na wani tambayeshi ai bazaiyi faɗaba tunda aiken Umaymah ne". Da sauri Ummi ta jujjuya kai tare da cewa. "A a badani za'ayi hakabs kam gsky ki dai tambaya in ya amince kinje in ya hana ki haƙura muje Salim alim". Kai ta jinjina tare da cewa. "Toh zan gwada Allah yasa ya barni". Amin Amin sukace. Kana Ummi ta ɗan kalli Sara dake takure a gefe cikin kula tace. "Saratu ya dai zazzaɓin ne?". Cikin rawan sanyi ta gyaɗa kai. Shatu ce ta kalleta cike da kulawa tace. "Allah sarki sannu Sara kinsha mgni kuwa?". Cikin rawan murya irin na mai fama da fitinenne masassaran cizon sauro tace. "Naje asibitin mu na cikin masarautar Joɗa an min allurai, to kuma duk jikina rawa yakeyi. Shine nace bari in zo in gaya muku, bazan iya zuwa muyi girkikiba. Amman naje na samu Huwaila zata zo ta tayaku". Cikin tausayawa Shatu tace. "Ba komai Sara Allah ya baki lfy je ki kwanta". Cikin kulawa Ummi tace. "Allah ya sauwaƙa ko kada kice zakizo gobema Huwailan zata ke zuwa tana tayamu sai kinji sauki sosai." To tace kana ta miƙa ta tafi. Huwaila ɗayace daga cikin hadiman Sashin Aunty Juwairiyya wacce asalinta hadimar Hajia Mama ce. Kuma har gobe a sashin Hajia Mama take kwana. Ita da gidan Aunty Juwairiyya sai in zatayi girki tana gamawa take tafiya. Sai Indo ita kuma a sashin Aunty Juwairiyya take, kuma asalinta daga masarautarsu Sitti aka kawota da ita. Huwaila itace idon Hajia Mama a sashin Yan Jafar, shiyasa duk motsinsu ta sani sabida itace yar rahoto ko lokacin ciwon Shatu taji Aunty Juwairiyya na Umaymah a wayene daga nan taje tana fesawa Hajia Mama, dai-dai lokacin kuma yar rahoton gefen Gimbiya Saudatu na jinsu shiyasa mgnar ta isa ga Gimbiya Saudatu. Su kuwa nan sukaci gaba da hirarsu. Yau Sheykh bai dawo da wuriba sai ƙarfe goma na dare ya dawo. Ba kowa a babban falon haka yasa ya rufe ƙofar. Kana ya wuce Side ɗinsa jiki na karkarwa sabida masifeffen zazzaɓin daya zame mishi abokin rayuwa in dare yayi tun randa ya kusanci Shatu na forko yau kusan mako biyu kenan. Sosai zazzaɓin ya shiga jikinsa sabida har ya ɗan faɗa. Jiki na rawa ya ɗan rage kayan jikinshi, a daddafe yayi al'wala kana yazo ya kwanta. Haka ya kwana da masifeffen zazzaɓin ya dai sa a ransa gobe zaije yabinciki lfyarsa. Washe gari da safe. Bayan sun gama aiki. Ummi ta kalli Huwaila cikin kula kamar yadda ta saba da Sara tace. "Yauwa ga naki tafi dashi kije ki huta sai anjima kizo muyi na dare dan zamu fita anguwa yau ɗin". Cikin wani irin kallon ƙasa-ƙasa ta kalli Ummi tare da cewa. "To sai kun dawo". Tana faɗin haka ta fita. Tana fita ba jimawa su Jalal suka shigo. Dinning area suka wuce kai tsaye. Dai-dai lokacin Shatu ma ta fito cikin shigar doguwar riga mai masifar kyau da taushi sai ƙamshi take bazawa. Gefen Ummi ta zauna kana ta kalli Jalal dake cewa. "Adda Shatu Hibba ta kiranki bakya ɗagawa". Kai ta ɗan juyo ta kalleshi tare da cewa. "Fushi nayi da ita ai". Murmushi sukayi baki ɗayansu. Ita kuwa Shatu ido ta zubawa kular soyayyan Arish ɗin da Ummi ta buɗe. da sauri ta rufe idonta cikin sanyi tace. "Ummi wannanfa waya kawo mana shi?". Jamil ne ya amshi zancen da cewa. "Wa kuma zai kawo mana tunda duk wanda ya kawo korarsa da abinsa kikeyi". Cike da mamaki da tsoro ta kalli Ummi tare da cewa. "Ummi waya kawo mana wannan?". Dafe kai Ummi tayi tare da cewa. "Babu wanda ya kawo mana shi Shatu. A nan mukayi girkin nida Huwaila". Shiru Shatu tayi tare da jan dogon numfashi kana tace. "Ohooooooh Allah sarki ba laifi Ummi rufe kular". Cike da mamiki suka haɗa baki wurin cewa "Meyasa?". Miƙewa tsaye tayi tare da tattara kulolin duk tayi cikin kitchen dasu tana mgnar zuciya. "Yah ilahi ya mujibadda'awati meyasa? Me mukayiwa Aunty Juwairiyya?". Ajiye abincin tayi gefe. A take ta fara kiciniyar yi musu wani girkin. Su kuwa a Dinning area da ido suka rakata. A hankali Ummi ta biyo bayanta. Ganin tana jajjaga kayan miya ne, yasa Ummi matsowa kusa da ita kana tace. "Shatu meyasa zargina kikeyi ne nima ɗin?". Cikin sauri tace. "A a Ummi har abadan bazan zargeki ba. Amman naga abinda nake gani a abincin Hajia Mama da Aunty Juwairiyya ko na wasu gidajen in an kawo mana. Ummi akwai mgni a ciki. Ban zargekiba Amman zargina ya ƙara ƙarfi kan Aunty Juwairiyya duk da kareta da wonketa da kikeyi da nunamin ita yar uwarsuce. Tunda kinga dai yar aikinta ce tazo ta tayaki aiki mukaga abin nan" Wani irin dogon nazari da tunani Ummi ta faɗa can kuma sai ta nisa tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil. Shatu anya kuwa matsalar nan Juwairiyya tasan da ita, anya ba zagon ƙasa akeyi mata ba ita kanta da mijinta da ƴaƴan taba". Da sauri ta juyo ta kalli Ummin tare da cewa. "To Ummi ina dai Huwaila yar aikinta ne?". Da sauri ta gyaɗa kai tare da cewa. "Allah sarki Juwairiyya ashe bamu saniba magautan sun samu damar tura wakilai sashinki, sunaci gaba da rarakarmu". Cikin sanyi Shatu tace. "Ummi me kike nufi?". Cikin sanyi da zubda hawaye tace. "Juwairiyya tasha yin kuka tana rantse min da abunda zai kasheta bata san me kike gani a abincin taba. Tace min Ummi inrasa wanda zan cutar sai ƴan uwana. Shatu shiyasa Juwairiyya tayi fushi ta dena zuwa sashinki. Sai yanzu na tuno asali Huwaila hadimar Hajia Mama ce, daga baya ta bawa Juwairiyya ita wai aiyukanta sunyi mata yawa". Wani irin ajiyan zuciya Shatu ta sabƙe tare da cewa. "Uhummm makashinka taburmanka, Ummi ko dai har yanzu baki yarda da wacece Hajia Mama ba, ko baku cemin ba ita mahaifiyar Yah Sheykh ba na sani ba ita ta haifeshi ba kuma nasan kuma kun san ita majirace, sai dai bansan dalilinku na zuba mata ido kuka meda kanku baku saniba, wata ƙil ƙofar rago zakuyi mata." Sai kuma ta juyo taci gaba da aikinta tare da cewa. "Kwantar da hankalinki Ummi barni da ita ai nida aita kar tasan kar. Jeki zauna bari in tafasa mana ko indomei". To Ummi tace kana ta fita. Ita kuwa Shatu cikin hanzarin ta dafa musu indomei. Kana ta kai musu. Tana zuzzuba musu ne ta kalli Ummi tare da cewa. "Yah Sheykh fa wanne abinci aka kai mishi?". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "A a shi Gimbiya Aminatu ce ta aiko mishi nashi karin kumallon. Nama kai na ajiye mishi a falonshi. Kai ta gyaɗa cikin gamsuwa kana sukaci gaba da cin indomein. Bayan sun gamane suka tashi. Jamil ne ya ɗan kalli Ummi tare da cewa. "Ummi ku shirya mu tafi gidan Hajia Kubra ko, dan da yamma inada inda zan je". To Ummi tace kana ta miƙe ta nufi ɗakinta, shi kuwa Jamil fita yayi ya nufi Part ɗin Yah Jafar dan ya cewa Aunty Juwairiyya ta shirya su tafi. Jalal kuwa Part ɗin Affan ya nufa. A can ya samu Imran Sulaiman. Itama Shatu kai tsaye ɗakinta ta wuce. Bathroom ta shiga dan sake yin wanka. Shi kuwa Sheykh kasan cewar zazzaɓi na yawan addabarsa da dare. Shiyasa bai samu isasshen bacci ba. Kasan cewar yau asabar bazai je asibitiba dan yanada zaunanan likita dake zuwa asabar da Lahadi. Shiyasa tunda ya dawo Masallaci ya kwanta yayi bacci sabida zazzaɓin ana kiran sallan asuba zai sakeshi. So sai ƙarfe tara ya tashi daga baccin. Jinshi garau yasashi shiga Bathroom. Wanka ya fesa mai rai da lfya. Kana ya fito ya murje jikinsa da OudKareem ɗinsa mai sasayyan ƙamshi. Wata tattausar jallabiya royal blue ya sake mai ɗan karen taushi da sulɓi ya ɗaura kan boxes ɗin dake jikinshi fara ƙal irin mai taushi nan mai botura biyu a gaba. Jallabiyar kuma hannunta guntaye ne, farin hular taɓa kaji hadisi ya murza a kanshi. Turare ya ƙara fesawa kana ya ɗauki system ɗin shi ya fito falonshi. Ganin tray'n dake kan stoll ɗin dake tsakiyar falon ne ya gane, cewa Gimbiya Aminatu ce ta turo mishi breakfast haka yasa, yazo ya zauna bisa kujerar 2 str da stoll ɗin ke kusa dashi. kasan cewar stoll ɗin nada ɗan faɗi da tutu yasa, ya miƙa ƙafafunshi gefen tray'n sabida ba yanzu zaici abincinba. Wani ɗan aiki ya farayi a system ɗinshin. A can ɗaƙin Aysha kuwa. A hankali take fesa turaren a jikinta. Tayi ɗan karen kyau cikin wata doguwar rigar Getzner mai masifae kyau, rigar tayi cin da jikinta color Getzner Sky blue ne mai masifar kyau kana sai kolliyar pent work pink, green, red, da yellow akayi kwalliyar tamkar zanen ɗawisu, ƙasa duk akayishi kamar zanen ƙirjin ɗawisu saman kuma kamar irin ɗaziwisu ya ɗaga fikafikansa nan. Tayi ɗaurin ɗan kwalintagwanin burgewa. Gyalenta pink color hakama takalmita, Cover'n wayarta ta sauya tasa shima pink. Sosai tayi kyau rigar tayi cib-cib da jikinta sai dai wuyan rigar irin mai faɗin nanne. A hankali ta fito, falo jin Ummi na cewa. "Shatu to mun tafi sai mun dawo". Da sauri ta ƙara so babban falon nasu tare da cewa. "Ummi na gama shirifa nima gani na fito". Cikin mamaki Ummi ta kalleta kai ta jinjina kana ta juyo ta kalli Jamil dake riƙe da hannun Mimi kana tace. "To kin tambayi Sheykh ɗin ne kam?". Kai ta ɗan sunkuyar kana tace. "Yanzu zanje in tambaya". Kai Ummi ta jujjuya kana tace. "Tab amman Shatu yarinta na damunki waya ce miki ana shirin zuwa Anguwa ba tare da an tambayi mijiba, wlh zaiyi wuya ya barki". Da sauri tace. "Dan Allah Ummi ku jirani inje in tambayeshi in sha Allah zai barni". Kai ta gyaɗa mata kana tace. "To kiyi sauri, muna jiranki". Da sauri ta juya ta nufi falon nashi. Tun kafin ta iso ƙamshinta ya sanar masa gata nan zuwa. Kanshi ya ɗan ɗago ya kalli ƙofar falon. Dai-dai lokacin kuma ta shigo bakinta ɗauke da sallama. Wani irin matse cinyoyinsa yayi da ƙarfi sabida jin yadda Sheykh ɗinsa ta harba da masifar ƙarfi sabida ganin amininsa. Lumshe idonshi yayi tare da motsa lips ɗinshi a hankali yace. "Wa alaikassalam". A hankali ta ƙara so gabanshi. cikin sanyi ta ɗan kalleshi tare da cewa. "Barka da safiya Yah Sheykh". Shiru yayi bai ce mata komai ba, sai idanunshi daya buɗe ya zuba mata su. Kai ta ɗan kwantar bisa kafaɗa cikin yin ƙaramar murya tace. "Yah Sheykh ya jikin naka?". Still bai amsa mataba, ganin hakane ta ɗan sunkuyo a hankali ta dafa Stoll ɗin wanda hakan ya bawa wuyan rigarta damar buɗuwa, gaba ɗaya rabin breast nata suka bayyana. Wani irin matse cinyoyinsa ya kuma tare da taune lip ɗinsa na ƙasa. Ita kuwa cikin sanyi da ƙaramar murya irin tamu na mata in muna son a amince mana yin wani abun a hankali tace. "Ayyah Hamma Jabeer kayi mgn mana dan Allah". Tofa ya rigada ta gama dashi tunda tace dan Allah. a hankali ta ɗan zamo ta durƙusa a ƙasa bisa guiwowinta. kanta ta kwantar cikin yin ƙasa da murya tace. "Yah Sheykh ya jikin naka?". Dariya ma ta bashi ganin yadda take ladab sai kuma ya danne dariyar. A hankali ya motsa lips ɗinshi yace. "Ɗazu dai da sauƙi amman yanzu kin famo min ciwon". Da sauri tace. "Allah ya sauwaƙa." Bata jira amsarshi ba ta ɗaura da cewa. "Ayyah Yah Sheykh dama Hajja Kubra ce ba lfy shine Umaymah tace muje mu dabota, shine to yanzu su Ummi zasu tafi Dan Allah in bisu muje?". Ta ƙarashe mgnar a hankali. Shi kuwa ƙirjinta ya zubawa ido ba tare da yace komaiba. A hankali ta kuma matso tare da cewa. "Ayyah Yah Sheykh ka barni inje?". Kanshi ya jingina da jikin kujera kana a hankali yace. "Kina son in barki kije?". Da sauri tace. "Eh Ina so mana". Ba tare da ya ɗago kanshi ba yace. "To kuma gashi kin tsokono Jabeer yana kwance kika sashi tashi tsaya, zaki bashi haƙuri, in barki kije ko bazaki bashi ba?". Da sauri tace. "Zan baka, kayi haƙuri". Ta ƙarashe mgnar ba tare da tasan manufar zancesa ba. Shi kuwa Sheykh na mijin duniya gyara zamanshi yayi tare da cewa. "Ai bani zaki bawa gaƙuri ba, Jabeer na zaki bawa haƙuri, shi kuma baya jin mgn sai dai an yi a aikace." Cike da mamaki da rashin fahimta tace. "Jabeer kuma". Eh yace mata yana ƙara lumushe idanunsa. A hankali tace. "Akwai wanine mai wannan sunan in ba kaiba?". A hankali yace. "Eh akwai mana ai shi kika tsokana ma ba niba." Cikin sanyi tace. "To ina yake?". Ɗan ɗago kanshi yayi ya kalleta, ido cike da masifeffen sha'awa yace. "Dolefa in na nuna miki shi ki bashi haƙuri". Da sauri tace. "Eh zan bashi, in dai zaka barni muje". Ta ƙarashe mgnar tana kallon fuskarshi. Shi kuwa meda kanshi yayi ya jingina da jikin kujerar kana ya lumshe idonshi. Hannunshi na dama yasa ya kamo bakin jallabiyar jikinshi. A hankali ya fara jawota, ba tare da ya kuma buɗe idanunshi ba. Yanajin cikin jiki da zuciyarshi bashi da wani sirri a jikinshi da zai ɓoye mata, sabida ya gamsu cewa yanzu itace suturarsa shine kuma suturarta. Ita kuwa Aysha fuskarshi take kallo Especially sajenshi dake kwance lib da gemunshi. Tattare rigar yayi har sama kana ya medata baya. Fararen kyawawan cinyoyinsa da gargasa yayi musu ƙawanya suka baiyana. A hankali yasa hannunshin bisa mararshi. hannunshi na hagu ya miƙa saitin inda take. bata kulaba taji ya kamo hannunta da hannunshi na daman. Da sauri ta ɗan sunkuyar da kanta tana kallon kyawawan cinyoyinsa. hannunshi na hagu yasa ya ɓalle botura guda biyu dake gaban boxes ɗin nasa. cikin sanyi murya na rawa yace. "Matso ki zakiga yadda yayi fushi ya tashi tsaye, motso ki bashi haƙuri." Ya ƙarashe mgnar yana jawota kusa dashi tsakiyar sawunshi. Ya zama tana fuskarta mararshi. Idonshi ya ɗan buɗe kana ya lumshesu a hankali. Sannan yasa hannunshi ta cikin ramin boturan daya buɗe, ya fito mata da Sheykh ɗin. Da sauri tayi ƙasa da kanta tare da manna kanta da cinyarshi. Cikin jin kunya. Anyah kuwa Yah Sheykh ne. a hankali yaji hannunta dake cikin nashi yana ɗan tsuma kaɗan-kaɗan. A hankali ya kuma yawota. Tsakiyar cinyoyinsa, sakke hannunta yayi ya kamo kanta. ya kusanto tota gareshi. ɗaya hannun kuma ya kama hannunta ya ɗauka kan bnnar kana ya matse da nashi. Cikin wata irin fitinenneyar murya yace. "Hahhh". Ya ƙarashe mgnar da alamun ta buɗe bakinta. idonta ta kuma rumtse jin ya ɗaura mata kan Sheykh ɗin kan lips ɗinta, a hankali ya fara goga mata shi bisa tattausa laɓɓanta kamar dai mai shafa mata jambaki. Ya ilahi ya mujibadda'awati tace cikin ranta ta ɗora da ikon Allah kai maza masu duniya. Shi kuwa Sheykh a hankali ya fesar da wani dogon numfashi tare da cewa. "Shhhhhhyyyyyyyyy buɗe bakin ki Aishhhhhhhh, ki bashi haƙuri". sai kuma tayi sauri ta buɗe idonta, jin wani abu mai ɗan yauƙi-yauƙi kan lips ɗinta da yake gogawa. Da sauri ta buɗe bakinta da nufin yin mgn. Kawai sai taji ya tura mata sh....! By *GARKUWAR FULANI* [3/20, 12:23 PM] +234 806 559 0880: Cikin bakinta. Wani irin lumshe ido yayi tamkar wanda ransa ke shirin barin gaggar jikinsa. hannunta dake cikin nashi wanda ya haɗa ya riƙe Sheykh ɗin nashi, ya matse da ƙarfi tare da isar da kusancinsu, irin isarwar da dole tasa ta buɗe bakinta da kyau. Cikin tsananin Feelings da rauni murya can ƙasan maƙoshi a hankali tamkar maiyin raɗa yace. "Shyyyyuuyyh Aish. lollipop". Tsuma jikinta ya farayi sabida. Abin yazo mata a bazata babu zato babu tsammani. Ko za'a kwana gaya mata Sheykh zai juye ya zama haka har ya aikata wasu abubuwan bazata taɓa yardaba. A hankali ta ƙara matsowa gabanshi da kyau. jin yana jawo ɗaya hannunta. A hankali ta buɗe lumsassun idanunta da suka fara raina fata. Fuskarshi ta zubawa ido, idonshi a lumshe sai dai ya zaro harshensa woje yana ɗan karkakaɗashi tare da fidda wani maraitaccen sauti mai nuna ƙololuwar fitinenne abun da yakeji. A hankali ta manna tsinin harshensa ƙan lollypop ɗin. cikin wani irin yanayi na rashin sabo da tarin kunya ta fara ida mishi muradinsa. Jin yana cewa. "Aish in baki bashi haƙuriba bazaki je bafa". Hakanne yasa ta fara wannan abun, da kawai ta tsinci kanta data iya. Lumshi idanunshi yayi tare dasa tattausan tafin hannunshi yana ɗan marin kumatunta tare da raɗa murya can ƙasan maƙoshi yake cewa. "Oh yessss! Ohhhh yessss my Aish." gaba ɗaya ya fara fita cikin hayaiyacinsa duk jikinshi kerma yakeyi tamkar mazari hannunshi ɗaya yasa ya tallabo kanta ta baya. Yana mai lumshe ido tare da fidda wasu zafafan numfarfashin murya can ƙasa cikin raɗa. "Wash, Ohoo, Hahh Aissssssssh thanks my Y.M.D.G oh yessss Baby". Cikin sauri ta buɗe kwayar idanunta jin yadda ya ƙarashe mgnar da ƙarfi tare da jan numfashi. Da sauri ta janye kanta, tare da cewa. "Ummi na falo tana jirana fa Yah Sheykh zata jika fa". Da sauri ya buɗe siraran idanunshi da suka firfito sukayi girma, kana suka sauya launi daga ruwan zaiba zuwa ja, da alamun hawaye cike a ciki. Da sauri ya ɗan matso bakin kujerar, hannunshi yasa ya riƙe lollypop ɗin. Kan tattausan lips ɗinta data tsuke ta tura ya manna shi, da sauri ya fara yin kamar mai shafa mata jambaki. Ido ya lumshe tare da sauƙe wani masifeffen ajiyan zuciya sabida jin taushi lips ɗinta da ɗan yawu kaɗan, sai yayi ɗan damshi na musamman. da sauri tasa hannu ta riƙe lollypop ɗin ta kaudashi daga kan lips ɗinta. Idonshi ya buɗe ya zuba matasu tamkar zautacce. Ita kuwa Shatu cikin kwaɓe fuska da shogoɓa ta tura baki kamar mai jin ƙyaman abu. Bayan tafin hannunta tasa ta fara goge lips ɗinta zuwa kan haɓarta. Wani irin shu'umin murmushi yayi tare dasa hannun sa, ya kamo hannun nata, kana ya miƙar da ita. Bisa cinyoyinshi ya zaunar da ita, ya zama suna fuskantar juna. Hannayenta ya kamo ya ɗaura kan kafaɗunshi. kana shima ya ɗaura hannayenshi kan kafaɗunta, still dai lollypop ɗin tana woje. A hankali ya matso da fuskarshi gareta sosai, har tsinin hancinsa na gogan nata. murmushin gefen baki yayi tare ɗaga mata girarsa ɗaya, kana a hankali yace. "Me kike gogewa?". Cikin wata iriyar fitinenneyar murya da itama kanta batasan dalilintaba tace. "Abunka". A hankali ya zaro harshensa ya ɗan lashi lips ɗinta tare da kai bakinshi kusa da kunnenta cikin raɗa yace. "Abunki dai, ai naki ne?". Ganin yadda ya tsareta da idone, da yadda ya tura hannunshi cikin rigarta yasa a hankali tace. "A a". idonshi ya lumshe dai-dai lokacin daya fito da breast ɗinta ɗaya ta saman wuyan rigarta da yaja yayi ƙasa da wuyan rigar. Cikin raɗa yace. "Zakisha ko?". Cikin tur baki da shagwaɓe fuska tace. "Yah Sheykh Ummi na jirana, kada su tafi su barni". Kanshi ya sunkuyar ya manna bakinshi kan ƙirjinta, wani irin sahihin murza yyi, wanda saida tayi ɗan zillo tare dasa tafukan hannunta ta tallabe habarshi tare da cewa. "Wash Shyah". Ɗagowa yayi ya zuba mata ido. sai kuma yayi murmushi a hankali kana ya gyara mata wuyan rigar. Cikin kasala da yasa hannunshi ya kamo nata, A hankali yace. "Jabeer baya so kina nesa dashi, bazai iya jurewa ba. Yanzu yaji haƙurin da kika bashi tashi kije?". Ina ai gaba ɗaya ya gama kashe mata jiki tayi luƙus, saima kwantowa kanshi da tayi ta manna kanta a ƙirjinsa. Tana mai jin yadda zuciyarshi ke harbawa. A hankali yace. "Aish". Cikin kasalelliyar murya can ƙasa tace. "Na'aaam". ɗago kanta yayi, kana a hankali ya manna sajenshi kan lips ɗinta ya fara gogawa a hankali har saida ya goge mata ɗan ruwan yauƙi-yauƙin daya shafawa lips ɗinta. a hankali ya yunƙura ganin duk jikinta ya mace. Tsayawa yayi kana ya tsaida ita. rigarshi ya sake ba tare da ya maida Sheykh ɗin nashi cikin boxes ɗinba. Haka yasa tana tsaye cikin jallabiyar har kana iya hango yadda take harbawa, alamun tana matse. A hankali ya gyara mata maya finta cikin kulla da danne azabebben Feeling da yakeji, sanin ya mata al'ƙawarin in tayi mishi abinda tayin zai barta taje, kuma ga yunwar da yakeji shiyasa ya daure, domin yin jima'i da yunwa yana cutar da namiji. Cikin tsareta da ido yace. "Kije ku tafi. Ko dai kin fasa zuwane!?". A hankali tace. "A a zanje". Tai mgnar kanta manne a kafaɗarsa. murmushi yayi kana ya ɗan shafo fuskarta sannan yace. "Uhum Y.M.D.G to kije". A hankali tace. "Jikina ya mutu, ƙafafuna na rawa". Kanshi ya kuma mannawa da nata kana a hankali yace. "Y.M.D.G". Sai kuma yace. "To mu tafi ɗaki mu gaisa, fitinenneyar Baby kawai". Da sauri ta rufe idonta tare da janye jikinta ta nufi hanyar fita. Murmushi yayi tare da cewa. "Kice ina gaida Hajia Kubra da jikin". Tana barin falon nashi tace. "Zataji." Ba kowa ta samu a falon, haka yasa da sauri ta fita. Part ɗin Aunty Juwairiyya ta nufa. Tana gab da shiga sukayi kiciɓis da Jamil. "Allah da baki zoma da tafiya zamuyi." Cikin wani irin masifeffen kasalan da namijin duniyan ya sake mata tace. "Afwan na tsaya bawa Yah Sheykh abinci ne." Sai kuma ta ɗan matsa ganin Ummi da Aunty Juwairiyya suna fitowa. Cikin sakin fuska ta kalli Aunty Juwairiyya tare da cewa. "Aunty Juwairiyya barka da hantsi". Cike da mamakin sakin fuska da Shatu tai mata tace. "Barka dai. Ya jikin naki?". Cike da kunya tace. "Alhamdulillah jiki da sauƙi". "Masha ALLAH Allah ƙara sauƙin". Amin Ummi tace kana suka nufi inda Jamil ke tsaye da mota, nan suka shiga suka tafi. Shi kuwa Sheykh tana fita. Ya bita da ido da wani murmushi mai tarin manufofi. A hankali ya ɗan sunkuyar da kanshi ya kalli jikinsa. Wani dogon numfashi ya fesar kana ya juya a hankali ya shiga ɗakinshi kai tsaye Bathroom ya faɗa. Ruwan sanyi ya sakarwa kansa, wai ko zai samu nitsuwa. Alhamdulillah kuma ya samu nitsuwa, haka yasa yayi al'wala bayan yayi wonkan. Wata jallabiyar ya zura. Yana fitowa yayi walaha. Kana ya kimtsa cikin wani farin yadi mai ɗan karen kyau da taushi yadin farine ƙal ɗinkin riga da wondo da gyariya ne. Gariyar tasha aikin hannu da zare surfani royal blue sosai ya fito ras. Hula damanga ya murza a kanshi itama royal blue. Tattausan sajenshi ya kwanta lib. gashin kansa kuma yi lib ta gefe gefen kanshi da ƙeyarsa. Wasu takalma sau ciki yasa suma royal blue. OudKareem ɗinsa mai sasayyan ƙamshi ya fesa a duk sasan jikinsa, kana ya ɗauki wayarshi dake gefen gado ya zura a al'jihun gariyar. A hankali ya fito falonshi. Cikinsa ya ɗan shafa tare da cewa. "Wayyo Mamey na Yunwa". sai kuma ya zauna bisa kujerar da suka gama bidirinsu shida Shatu. Murmushi yayi ganin wayarta a gefenshi. Kai ya jinjina yana mai jin masifar daɗin wannan yanayin da suka kasance a ciki. Abincin ya zuba, a plate ya faraci yana ɗan kurban kunun nono mai ɗumi wanda yasa a kofi. Sosai yaji daɗin kunun sabida yayi ɗan tsami. Sosai abin ya bashi mmki domin shi dai baya son abu mai tsami ko kaɗan. Amman yau yanajin daɗin tsamin da kunun yayi sosai a bakinsa. Sosai yaci abinci wanda rabonsa da haka, tun kafin su dawo Tsinako auren Haroon". Koda ya gama komai. Sai ya rurrufe ko ina na gidan kana ya fito. Sabida yau ɗin yana son zuwa gidan Malam Abubakar malaminshi kenan?". So amman zai shiga wurin Lamiɗo tukun. Su Ummu kuwa a gidan Hajia Kubra sosai taji daɗin zuwansu matuƙa. har taji jikinta ya ɗan ƙara worwirewa. Hira sosai Ummi da Hajia Kubra da Aunty Juwairiyya keyi. Shatu kuwa da Samira matar ɗan Hajia Kubra suka tafi sashinta, Samira nada saukin kai da saurin sabo da ɗan karen surutu. Haka yasa taja Shatu da zance sosai. Shi kuwa Sheykh yana shiga Part ɗin Lamiɗo kai tsaye har bedroom ɗinsa ya wuce. A bakin ƙofar ya ɗan tsaya tare da yin sallama. "Wa alaikassalam. Jabeer shigo". Yaji Galadima ya amsa mishi tare da bashi umarni". A nitse ya shiga. Zaune ya samesu. da wasu takardu a gabansu. A hankali ya zauna gabansu kana fuskancesu da kyau. cikin nitsuwa yace. "Na'urar CCTV Cameran dake sashin berbelar ya samu matsala." Da sauri Lamiɗo yace. "Tun yaushe." Kanshi ya rausayar kana ya ajiye system ɗinshi a gabansu. Kat rida ya ɗan zaro cikin ɗan wani ƙaramin abu dake hannunshi gefen System ɗin ya soka abun kana ya ɗan danna play sannan ya juya system ɗin ya fuskancesu. Cike da mamaki suka zuwa system ɗinshin ido. Shatu suka gani tsaye tsakiyar falon Hajia Mama. Ita kuwa Hajia Mama, tana zaune bisa kujera. Batool kuwa na can gefe. Wani irin taku na isa da rashin tsoro Shatu takeyi har ta isa gaban Hajia Mama. Da gaba ɗaya jikinta kerma yake dan masifar ɓacin rai. Cikin isasshiyar murya Shatu ta nunata da yatsarta manuniya kana tsuke tace. "Uhummmm in ke Halimace Ni Shatu ce. Ni nan da kike gani wargice dai-dai da ƙugun duk wani mugun Masararutar Joɗa". Da sauri ta ɗagawa Batool hannu jin ta taso zatayi mgn cikin isa tace. "Ke kul kada ki kuskura kice zakiyi mgn a kaina, ki tsaya iya matsayinki. In kin samu mijina ya kalleki koda kallo biyu a wuni ɗaya to Ni kuwa Ni Shatu zan sashi ya aureki ba dai shine burinki ba, to ki kama kanki ki bari sai kin zama matar ahlin masarautar Joɗa kafin kimin mgn". Cikin shakku Batool ta koma ta zauna tare da zuba mata ido. Ita kuwa Shatu yatsunta ta murza kana cikin haɗe fuska tace. "Gsky na jinjina miki kin cika muguwa. Halima, dama mugu bai cika mugu sai ya boye kamanninshi. To ki kula ki fita rayuwar mijina, wlh ki rabu dashi da ƙannenshi da yayanshi. Ki kiyayeni kijin tsoron randa zan miki wankin babban borgo a masarautar Joɗa. Wato ke gaki shegiyar makira munafuka mai fuskoki goma da ashirin ko, kina tare dasu kina cin dunduniyarsu kinata ciyar dasu mganunnukan tsafinki. To a hir ɗinki, wlh ko ciwon farce Mijina yayi ko ƙannenshi nida ke bibbiyu, kin sanni Ni dake kar tasan karne. Kika kuskura kika sake aika min wani abu Part ɗina, babu shakka ubanki zanci. Wato ke a dole kina jiran inzo in baki haƙuri ko? To jira zakisha mmki". Tana faɗin haka ta juya ta fita. Ita kuwa Hajia Mama cikin wani irin tafasan zuciya tace. "Uhummmm yanzu za'a fara wasan". Cike da mmki da rashin sanin manufar zancenta da kalaman da Shatu tayi Batool tace. "Hajia Mama, wai meke faru ne, me tsakaninki da ita, ko dai kawai dan ina son Sheykh ne ta tsaneki". Wani mugun harara Hajia Mama ta watsawa Kubra kana ta juya ta nufi bedroom ɗinta tana huci kamar zakanya. Kusan a tare Sheykh Jabeer da Lamiɗo da Galadima suka sauƙe ajiyan zuciya, cikin murmushin Galadima yace. "Alhamdulillah yarinya ta fara yaƙin kare mijinta". Murmushi Lamiɗo ma yayi kana yace. "Alhamdulillah komai na tafiya yadda muke zato". Cikin taɓe baki Sheykh yace. "To waya sata, ko ce mata akayi ban san waye Hajia Mama bane, ko ta fini saninta ne. Ya za'ayi muna ɓoye abu tsawon lokaci ita zata zo ta nuna ta sani. Ai da bata jira kantaba kuma, tasha ciwon hannu". Murmushi Lamiɗo yayi kana yace. "Koma mene dai a kanka takeyi". Kanshi ya kauda yana mai jin wani sanyi murmushi mai yalwa ne ya subce mishi kana yace. "Uhumm wai mijinta ko kunya babu". Sai kuma ya haɗe abubuwan nashi kana yace. "To nadai sa Jalal ya sake dasa wata Camerar ya kuma sake dasawa, ita kuwa sakarya kallon bugegge takewa Jalal in yana sade ɗinta tana mishi kallon kare da uban gidanshi bata san a tsakiyar tafin hannunmu takeba Jalal ya fita sanin makaman ɓoye abu." Yana faɗin haka ya nufi woje tare da ce musu lokacin salla yayi. Nan masallacin Masarautar Joɗa yayi sallan azahar kana ya wuce gidan Malam Abubakar. Koda yaje ya sameshi da baƙi. Haka yasa suka zauna nan suna tattaunawa saida akayi sallan la'asar kafin baƙin suka tafi. Nan suka samu suka zauna suna tattauna matsalarsu. Har magriba tayi, sukayi salla a masallacin ƙofar gidan Malam Abubakar ɗin, basu fitoba saida sukayi isha'i. Suna fitowa kuwa yace zai tafi. Malam Abubakar ɗin yace a ai dole fa ya tsaya suci abinci. Dole suka koma falonshi. Baici komai ba sai kunun tsamiya da yasha. Sabida sam bakinsa ba daɗi. Gashi yana jin zazzaɓin nan nashi na dare ya fara rufeshi. Suna gama cin abincin kenan wasu mutane biyu mace dana miji suka iso falon bisa jagorancin ɗan Malam Abubakar ɗin. Ya yunƙura zai miƙe ya tashi kenan sai kuma ya koma ya zauna jin Malam Abubakar na cewa. "A a tsaya Muhammad ban gama da kaiba zauna ba matsala". Cikin sanyi yace. "To". Kana ya koma ya zauna. Shi kuwa Malam Abubakar a hankali ya juyo ya fuskanci baƙin nashi bayan sun gaisane sukayi yar mgnarsu kana suka tafi. Gyara zamanshi yayi ya fuskanci Sheykh da kyau cikin nutsuwa irin ta manyan dattijai yace. "Muhammadu wlh wani tsautsayi ne ya ritsa Sulaimanu". Cikin nitsuwa Sheykh ya kalleshi. Domin Sulaiman abokinshi ne, sabida shi ƙanin Umma matar Malam Abubakar ne, tare sukayi karatu da Sulaiman a wurin Malam ɗin shiyasa ya sanshi sosai, suna mutunci kuma. Sulaiman ɗan kasuwane saye da sayarwa yake na golagolai masu tsadar gaske, yana zuwa sari ƙasashen ƙetare da dama yana kawowa Ɓadamaya inda yakeda manyan shagunan shi na saida golagolan. Ya haɓaka yayi ƙarfi sosai. To matsalar rufe boda data shafi duniya baki ɗaya ne, ya sashi fara sari nan cikin ƙasar. Yakanje wasu jihohin ya tsara. A irin hakane ya faɗa hannun mugaye suka sarar mishi golagolan matar gwamnatin wata jihar mafarin matsalarsa kenan. Haka yasa hukuma suka kamashi. To shine damuwar ahlinsu baki ɗayansu. Hankalin kowa ya tashi. Sabida Sulaiman shine jigonsu. Mutun ne mai tausayin yan uwansa. Cikin sanyi Malam Abubakar ya gama yi mishi bayanin ya ƙara da cewa. "Muna barar addu'arka Allah ya kuɓutar dashi ya tsareshi ya fito dashi lfy. Kuma ina akwai taimakon da zakayi mana muna buƙata, yanzu haka ita Ummun taku tana can gida sun." Cikin tausayawa da tabbacin Sulaiman mutumin kirkine ƙaddarace tazo mishi a hakan yace. "In sha Allah zamuyi ta addu'a, kuma da izinin ubangiji zanyi ƙoƙarin ganin ya dawo gidanshi". Cikin jin daɗi Malam Abubakar yace. "Alhamdulillah Ngd matuƙa, Ataimaka Muhammad". Cikin tausayawa yace. "In sha Allah kuwa". Daga nan sukaci gaba da tattauna matsalar. Yayinda sosai yakejin azabebben zazzaɓin yana rufeshi. Sai ƙarfe tara ya sallami Malam ya fita ya tafi. Cikin ƙarfin hali yake tuƙin, sabida gaba ɗaya zazzabin ya rufeshi ji yakeyi duk gabbanshi kamar ana sossoka mishi allurai. A hankali yasa hannunshin ya kashe A/C'n motar sabida sanyin da yakejin har jikinsa na rawa. Cikin ƙarfin hali ya juya akalar motar tasa ya nufi Valli Hospital. Wayarshi ya ɗauka Dr Kabir ya kira. "Assalamu alaikum,". "Wa alaikassalam, Sheykh Barka da yamma". A takaice yace. "Barka dai Dr Kabir kana Valli ko?". Cikin kula tace. "Eh ina nan". "Na'am to gani nan zuwa banda lfy fa". "Subahanallahi, to sai ka iso, ko dai inzo in dubaka a gida?". "A a gani ma na kusa". Yace mishi dai-dai lokacin da ya Iso bakin wani irin tamfatsetsen Hospital mai masifar kyau da girma. Valli Hospital kenan. Da sauri mai gadin ya buɗe mishi gate ɗin. Tare da ɗan matsawa gefe. Cikin rawan sanyi yayi parking cikin rumpar da sunanshi ke rubuce a sama. Da sauri mai gadin ya buɗe mashi marfin motar tare da cewa. "Barka da zuwa mai gida". Cikin sanyi yace Barka dai kana ya fito. A hankali ya ɗan jingina da jikin motar yana kallon farfajiyar asibitin. Wani irin ƙaton filine mai girma. Wanda akayi mishi ƙawanya da bishiyoyin namijin gwanda. Kana ƙasa kuma fulawowine a jere iya ganin mai hange wani faffaɗan titine ke malale, wanda tsakiyarshi dogayon ƙarafunan wuta ke jere iya ganin ka. Can gefen dama wani tamfatsetsen gidan samane mai zaman kashi ya kai hawa uku. Gefen hagu kuwa wata hanyarce ta kuma shiga. Sai wani irin tamfatsetsen gini mai masifar kyau inda marasa lfy ke kwanci gefen mata. Komai kalan kayan asibitin royal blue and white. Can gaba kuwa kuwa jerin Offices ɗin Dictors ne. Sai Side ɗin Nurses. Tsab-tsab cikin asibitin. Sai motoci keta gilmawa. Haske kamar rana. Kai faɗin tsatuwar asibitin sai wanda ya gani. A hankali ya nufi gefen Office ɗin Dr Kabir. Yana shiga Nurses ɗin dake zirga-zirga tsakanin wurin suka rinƙa ɗan bashi hanya suna. "Ur welcome sir". Kai kawai yake jinjina musu kana ya wuce su wuce dan zazzaɓin ya fara damunshi sosai. Yana shiga Office din Dr Kabir da sauri ya miƙe tare da cewa. "Barka da zuwa Sheykh". A hankali ya zauna tare dafe kanshi. Cikin sanyi yace. "Kabir test nake so ayi min yanzu-yanzu gaba ɗaya na rasa meke damuna kullum da zazzaɓi nake kwana". Cikin kula Dr Kabir yace. "Tsawon kwana nawa ya fara maka?". Jingina kanshi yayi da jikin kujerar tare da cewa. "Two weeks ago". A hankali ya gyaɗa kanshi kana ya juya ya koma kan table nashi abubuwan aikinshi ya ɗauko kana yazo ya zauna kusa dashi, cikin kula yace. "To test ɗin me da me za'ayi maka?". Cikin sauƙe numfashi yace. "Widal, Mp, Emergency, fa." Kai Dr Kabir ya jinjina kana ya kamo hannunshi. Ba musu ya miƙa mishi bayan ya tattare gariyar tasane. Ya ɗebi jininsa. Lab ya wuce Direct. shi kuma ya zauna a nan yana jiranshi. Yana zuwa yace, to jinin ogonane da kanshi kuma Emergency ne. ai kuwa cikin awa ɗaya suka gama bicikan jininsa kab. Bayan sunyi ƴan rubuce-rubucen sune. Ya amshi takardar ya koma Office ɗin sa. Inda ya barshi nan ya sameshi sai dai yanzu, yana karatune, ganin ya dawone ya ɗan sahirta. Takardan ya miƙa mishi. A hankali ya gyara zamanshi kana ya meda idonshi kan takardar. Tests result ɗin yake dubawa. Cikin sanyin zazzaɓin yace. "Widal risult ɗin bani da matsala, 40% da 80% kaga kenan bani da Typhoid". Kai Dr Kabir ya gyaɗa tare da cewa. "Eh gsky kam babu matsalar Typhoid wanda ni da fari shi nafi zargi". Kanshi ya sunkuyar tare da buɗe fefa ta gaba yana cewa. "Nima haka naiyi tunani". Rubutun ya zubawa ido ganin. Mp 1+. Kanshi ya ɗago ya kalli Dr Kabir a hankali yace. "Ina da Malaria'n amman ba sosai ba 1+ baici ace ina jin irin wannan zazzafan zazzaɓin ba. To me matsala ta?." Ya ƙarashe mgnar yana kallon Dr Kabir. Cikin kula Dr Kabir yace. "To yanzu dai bari muyi allurar Malaria'n mu gani wata ƙil jininka bazai juri 1+ ɗin ma zai wahal da kai. Gashi dama na biya Pharmacy na amso allurar bari inyi maka kawai muga zuwa gobe ya abun zaiyi". Cikin gamsuwa da hakan yace. "To". Hannunshin ya kuma kamowa ya tsira mishi allurar. Kana ya bashi wasu magunguna a take a nan ya shasu. Nan sukayi sallama ya tafi gida. A gida kuwa tuni su Shatu sun shiga dan basu dawo da wuriba shiyasa suna dawowa basu tsaya hiraba. Shiru ya samu falon babu kowa. A hankali ya wuce Side ɗinsa. Dan wani irin masifeffen karkarwa da jikinsa ya fara. Ga wani irin tsuka da zazzaɓin ke mishi. Da kyar ya rage kayan jikinshi. A daddafe ya shiga yayi fitsari yayi al'walan kwanciya bacci. Yana fitowa ya kwanta. Kar-kar haka yake rawan sanyin masifeffen zazzaɓin nan kamar zai ɗauke ransa. Allurar tamkar ƙara mishi ciwon tayi. Haka ya kwana wannan ranar da masifeffen zazzaɓin. Ana kiran sallan forko, yaji zufa na karyo mishi alamun zazzaɓin zai ɗan sauƙa kamar yadda yake mishi kullum. Ai kuwa lokaci ɗaya zufa ta jiƙashi. Jikin sanyi ya tashi AC ya kunna kana ya dawo bakin gadon ya zauna yana maida numfashin jin daɗin sanyin ac lokacin ɗaya kuma ya jishi garau kamar bashi ba, ƙamshin turaren jikinshi da sanyin ac yasashi jin wani irin sassanyan yanayi yana rufeshi. Kusan 5 minute yayi kana ya miƙa ya shiga Bathroom. Allah ya sani da Shatu na kusa dashi zai raɓeta ko zaiji daɗin rayuwarshi. Ruwan sanyi ya watsa kana ya fito. Da al'walan sa. Nafila ya fara. Kana ɗaya sallame ya fara karatu. Jin anyi asslatune ya sashi fita ya nufi Masallacin masarautar Joɗa. Ƙarfe bakwai dai-dai ya turo ƙofar falon jiki a mace. Wani fitinenne yanayi nata ɗawainiya dashi. Yana zuwa tsakiyar falon Ummi na fitowa cikin kitchen. Da sauri ya sunkuyar da kansa cike da kunya. Domin tun randa Ummi ta ritsashi ya fito ɗakin Shatu bai sake yarda sun haɗa idoba sai yanzu. Cike da kunya yace. "Uhmm Barka da safiya Ummi". Cikin kula da mamaki, ramarsa ita kuma Ummi ta bishi da kallo tare da cewa. "Barka dai Sheykh lfy kuwa, meke damunka". Murmushi yayi cike da kunya yace. "Uhum Ummi me kika gani?". Cikin tausayawa tace. "Sheykh kaga yadda ka rame kuwa, anya kanada lfy kuwa?". Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta kana a hankali yace. "Lfy ta lau Ummi kawai dai ɗan zazzaɓin dare ne ke yawan damuna, in gari ya waye kuma sai inji sauƙi". Da sauri tace. "Ina kuwa sauƙi Sheykh nadai lura sam baka son cin abinci. gashi gaba ɗaya ka faɗa". Ci gaba yayi da tafiya tare da cewa. "Ina ci fa". Da sauri tace. "To kaje kaga likita ne?". Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. "Eh naje. Jiya da dare". Cikin sanyi tace. "To Allah ya sauwaƙa". Amin yace kana ya wuce. Ita kuwa Ummi sosai taji ba daɗin ganin yadda ya ɗan faɗa. Suna cikin yin aikin breakfast ita da Shatu. Huwaila ta shigo kamar yadda Sara take zuwa tayasu aikin. Kai Shatu ta jinjina kana ta nuna mata Arsh tace. "Fere minshi in kin gama kije kawai sai anjima kizo yanzu mun gama". Cikin kallon ƙasa-ƙasa Huwaila tace to. Bayan sun gama komai na aikin breakfast sun shiryashi a Dinning table ta kalli Shatu data nufi ɗauki ta. "Zo ki kaiwa Sheykh abincinsa kinga ba lfy ce da shiba". Cikin gajiya tace. "Ayyah Ummi to bari inje in watsa ruwa wlh zafi nakeji. Watsawa kawai zanyi yanzu zan fito". Kai kawai Ummi ta gyaɗa mata. Bayan tayi wonka, mai kawai ta shafa ta fesa turare. Ta zura doguwar riga ko bra bata saba. Jin Ummi na kiranta tana fitowa ta samu Jalal, Jamil, Affan, Sulaiman Imran duk suna yin karin kumallo su. Tray'n da Ummi ta miƙa mata ta amsa kana ta wuce falonshi. A hankali tayi sallama tare da kutsa kanta cikin falon. Shiru babu motsin komai sai na A/C, bisa Dinning table ta ajiye tray'n kana a hankali ta juyo ta ɗan tsaya tsakiyar falon. Ido ta ɗan zubawa ƙofar ɗakinshi. har kamar zata shiga sai kuma ta juya da nufin fita. da sauri ta ɗan ja da baya ganinshi tsaye a gabanta ya tankwara kanshi bisa kafaɗarsa, a hankali ya ƙara matsota. Batayi yunƙurin matsawa ba, saima idonta data ɗan lumshe. a hankali ta buɗe idonta jin ya kamo hannunta ya riƙe cikin nasa a hankali yace. "Tafiya zakiyi bazaki duba lfyata bako?". Cikin kula tace. "A a nayi tunanin ko kana baccine kada in shiga in tada kai". Murmushin gefen baki yayi kana yace. "Zo in baki saƙonki to". "Toh". Tace mishi kana tabi bayanshi. Har ya nufi Bedroom ɗinsa, sai ya kuma juyo a hankali ya fuskanci ƙofar nan da zata sadashi da Garden ɗin Masarautar Joɗa. Ita dai Shatu ido ta zuba mishi tare da bin bayanshi. Hannunshi yasa ya tura ƙofar tare da juyowa ya ɗan kalleta a hankali yace. "Muje kiga yadda tsuntsayema ke nunawa juna kula". Murmushi tayi tare da cewa. "Yakai rabin kular da nake nuna maka ne". Yatsarshi yasa ya ɗan lakaci tsinin hancinta tare da cewa. "Muje dai kiga yadda sukeyi, ke zaki yanke hukuncin irin kular da kike bani". Wani irin sassanyan numfashi suka sauƙe a tare dai-dai lokacin da suka shigo cikin filin, sanyin iskar da ƙamshi ya'yan itatuwa da kukan tsuntsaye yasasu jin wani irin masifeffen shauƙi na musamman. Ido ta fara jujjuya tana kallon tsarin wurin da kyanshi, sai kuma ta ɗan juyo ta kalli ƙofar da suka shigo ɗin wanda bata taɓa sanin da zamanshi ba, tsawon watanni kusan bakwai da take gidan. Cikin lumshe ido ta juyo ta kalleshi. kanta ta ɗan manna a ƙafaɗarsa, jin haka yasa hannunshi ya ɗan shafi haɓarta, ido ya zuba mata jin tana cewa. "Uhummm Yah Sheykh kenan". Cikin yin sassayan numfashi yace. "Me nayi?". A hankali tace. "Uhumm naga ƙofofin dake sade ɗin kane kamar basu da adadi, ashe shiyasa wasu lokutan kake ɓacewa." Murmushi yayi tare da cewa. "Ɓacewa kuma kamar wani al'jani". Cikin sanyi tace. "Ɗan baiwa dai, dan tabbas dai kam kana ɓacewa tunda dai a Bedroom naka dai kam naga babu wata ƙofo to amman ina gani ka shiga a take in shiga in nemaka in rasa, to gashi kuma yau dai naga wata ƙofar da ban san da itaba." Wani irin ɓoyeyyen murmushi gefen baki yayi tare da ɗan manna mata kiss a goshinta, kana a hankali yace. "Wato bincike kike min a ɗaki". Dai dai lokacin kuma suka iso cikin fagen da tsuntsayen suke, gyaran murya yayi a hankali ai kuwa a take sai ga tsuntsayen wurin kab sun nufoshi. Wani irin narkekken murmushi tayi tare da ƙara manna kanta a damtsen hannunshi a hankali tace. "Ni ɗakin mijina nake bincika". Wani irin yalwataccen murmushi yayi dai-dai lokacin kuma. Ɗawisun nan na tarin masarautar Joɗa ta iso gabanshi. Wani irin taku yakeyi cikin rigima, ya iso garesu a hankali ya fara zagayasu. "Wow masha Allah". Tace dai-dai lokacin daya gama zagayasu kana ya dawo gabansu ya ɗaga binɗinsa sama ya buɗa fikafikinsa, ya baza a gabansu. Wanda ya iso har kan fuskarta shi kuwa Sheykh zuwa kan ƙirjinsa. Wani irin murmushi Sheykh yayi tare da cewa. "Kekkyawar tsuntsa a gaban kekkyawar sarauniya, kiyi haƙuri karon farko dai na kawo miki sarauniyar data fiki kyau, sabida na halittar bani Adam amman dai a cikin tsuntsaye har gobe babu ya kai". Wani irin juyowa tsuntsuwar tayi, ƙuntunta mai cikar blue color ya manna bisa saman rumfar sawun Shatu. Murmushi tayi kana ta sunkuyo ta shafata tare da cewa. "Masha Allah da kekyawar halinta". A hankali ta juya ta fara tafiya cikin rigima. Da sauri Shatu ta ɗago kanta ta kalli sama ganin yadda suntsaye masu masifar kyau sukayi musu ƙawanya suna kukansu mai daɗin ji. Murmushi tayi ta kalli Sheykh dake musu kirarin zaƙin muryarsu. Ruggumeshi tayi ta bayanshi tare da lumshe idonta lalacin daya nuna mata tattabarun daketa yiwa juna ƙoto kana suna kusantar juna. Cikin murmushi da shauƙi yace. "Lallai ke ta musamman ce, kalli ɗawisun nan batama jira na gabatar mata da keba, to ko-dai-ko dai". Da sauri tace. "Ko-dai-ko-dai mefa?". Ido ya lumshe tare da kamo hannun ta ya manna a habarshi tare da cewa. "Kodai jinin masarautar Joɗa ya gauraye da nakine, wanda ba sai an gabatar da keba". Ya ƙarashe mgnar yana sa tafin hannunshi yana shafa lafeffen cikinta". Cikin lumshe ido tace. "Kamar ya". Sunkuyowa ya ɗan yi bisa kunnenta ya kai bakinshi a hankali yace. "Kamar ko mun samu ƙaruwar akwai shigar cikin Muhammad jikin Shatu". Da sauri ta manna kanta da ƙirjinshi dai-dai lokacin kuma suka iso bakin ruwan nan inda agwagin ruwa ke cike murya can ƙasa tace. "A a kam ba wani ƙaruwa". Ƙara jawota jikinshi yayi tare da matseta murya can ƙasa yace. "To muje muyi fatauci Allah yasa muyi dace da katarin ƙaruwa, mu samowa Mamey jikoki masu kama dake in ta dawo ta samu masuyi mata surutu." Da sauri ta ɗan kalleshi dai-dai lokacin kuma ya juyo da ita suka nufi hanyar komawa falonshi murya a nitse tace. "Wacece Mamey Ina take? Yaushe zata dawo". Cikin sanyi ya ɗan kalleta a hankali yace. "Da gaske Aish ina son haihuwa matuƙa gaya, inason inga jinina ina son samawa Mamey na jikoki". Ya kauda zancen tambayar da tayi mishi. Da wannan batun yana kuma mai kai hannunshi kan cikinta. Dai-dai lokacin kuma suka shigo falon. Meda ƙofofin yayi ya rufe kana a hankali yace. "To muje in baki saƙonki". Cikin nazarta zantukanshi tace. "To". daga nan suka nufi bedroom ɗinsa. A hankali suka shiga bedroom ɗinsa, Komai kimtse sai ƙamshi turarukanshi da suka kama ɗakin. A hankali ya iso da ita bisa, carpet zama yayi kana itama ya ajiyeta. Suna fuskantar juna, kwaren da ke gefen gadonshin ya jawo ya ajiyesu tsakiyarsu. Cikin nitsuwa ya janye fefeyin saman. ya ɗaura matashi bisa cinyarta, wasu dandatsa-dandatsan al'kyabba na matan sarakuna ya fidda masu masifar kyau guda uku ya ɗaura mata kan fefeyin dake bisa cinyarta. kanshi a sunkuye yace. "Wannan kyautar tukuicin budurci ne daga tambarin Masarautar Joɗa." Ya ƙarashe mgnar yana fito da wasu takalma da linzamin dawakai biyu, ya ɗora bisa rigunan. kanshi ya ɗan ɗago ya kalleta ido cikin ido. Idonshi ya ɗan lumshe mata ganin yadda take kallon sajenshi. cikin tsokana yace. "Ya dai kin ƙyatsa ne?". cike da kunya tayi murmushi tare da cewa. "Nida abuna." Wani yalwataccen murmushi, sai kuma ya tsareta da ido jin tana cewa. "Ngd matuƙa Allah ya saka da al'khairi". "Amin Amin". yace kana ya jawo ƴar ƙaramar ƙwaryar dake gefen babbar, a hankali ya buɗe hannunshi yasa ya ɗauki wata iriyar fitinenneyar sarƙar ɗanyen gol mai ɗan karen kyau da masifar sheƙi na ɗaukar idanun mutun. da sauri ta waro idanunta woje cikin tsananin mamaki da al'ajabi take kallon sarƙar. Shi kuwa Sheykh miƙo mata sarƙar yayi tare da cewa. "Ga kyautar da ko wacce matar masarautar Joɗa ke harin ya kasance a sashinta. sai dai banda Mamey na, ita batayi harinshi ba, kuma Allah ya ƙaddara aka batashi, wanda kuma batashi bai zame mana al'khairi ba. Tsawon shekaru babu wanda ya sake ganin makamancinsa, sai kuma gashi a karo na biyu ya shigo cikin ahlinta a hannunki." Ya ƙarashe mgnar yana jawota jikinshi. Ba musu ta kwanta cikin ƙirjinsa sabida ƙamshin jikinsa da take son shaƙa. Sarƙar daya saƙala mata a wuyan nata ta kalla, cikin al'ajabi da mamakin ganin irin sarƙar Ummeynta ce. Dan komai nasu iri ɗaya harta tambarin jikin sarƙar to sai dai wannan tafi sabunta da sheƙi. Wannan banbanci na saraƙunan da kuma jin abinda yake matane yasa tayi shiru. Ta gaza cewa komai, ido ta lumshe jin ya manna bakinshi bisa wuyanta, harshensa yasa yana ɗan lasar fatan wuyan nata a hankali. Kana hannunshi na zuge zib ɗin rigarta. batayi yunƙurin hanashi ba, jin yadda yake jan wasu tagwayen numfarfashi masu nauyi. Ido ta ɗan lumshe ta faɗa jikinsa, lokacin daya gama zare mata rigar tata. Jingina bayanshi yayi da jikin gado, kana a hankali yasa hannunshin ya jawo jallabiyar jikinshi daga ƙasa yayi sama da ita, ya cireta ya rage dagashi sai gajeren wondon iya guiwa wanda ƙasan shi kuma akwai boxes. Ita kuwa Shatu manne jikinta tayi da nashi kana tasa hannun ta zagayo bayanshi tayi lib a jikinshi. Ƙugunta ya zubawa ido cikin tsananin Feeling dake ɗawainiya dashi, yasa yatsunshi biyu ya kama bakin robar gajeren wondon dake jikinta wanda yayi cib da jikinta. da sauri ta mirgino kanshi tare da tashi zaune bisa cinyarshi ya zama suna fuskantar juna, hannayenta ta meda ta saƙale wuyanshi, tare da kai bakinta kusa da kunnenshi a hankali tace. "Na gode Yah Sheykh, Allah ya cika maka burinka Allah ya kare min kai da kariyarsa yayi maka rahama da rahamominsa, ya albarkaci ahlinka da albarkarsa yasa ka gama da duniya lfy". Hannunshi yasa ya mata wani irin masifeffen rugguma ya matse Caɓɓullenta da ƙirjinshi murya can ƙasa yace. "Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati. Yah Aish Mar'atussaliha." Sai kuma yasa hannunshi ya tallabo kanta ya haɗe goshinsu, tsinin hancinsa ya goga kan nata, a hankali kuma yasa harshensa ya fara lasar lips ɗinta kamar mai lasar askirim. ido ta lumshe jin wani irin masifeffen abu ɗaya taso mata daga ƙan babbar yatsar ƙafarta har zuwa maɗigan kanta. sabida yadda ya cusa harshensa a bakinta ya kamo nata, yanayi mata sahihin kiss mai lankwasa tunanin. Yatsunta ta cusa cikin sumar kanshi tana yamutsawa wanda hakan ya zuzuta fitinar dake cinsa. Hannunshi yasa ya murza gajeren wondon dake guguunshi yayi ƙasa dashi ya rage dagashi sai boxes. Cikin rawan jiki yasa hannunshi yayi ƙasa ya ɗan nata. Cikin ɗimuwar daya sata. ta ruggumeshi gam-gam a jikinta tamkar zata game jikinsu. da sauri ya yunƙura ya miƙe tsaye da ita. taku biyu yayi da ita zuwa uku yasa hannunshi ya ɗauki al'kyabbar shi dake gefen gado. Wore al'kyabbar yayi ya rufesu gaba ɗaya. Kana ya juyo ruggume da ita sukazo bakin ƙofar. Rufe ƙofar yayi kana yasa hannunshi ya kashe wutan ɗakin gaba ɗaya. Duhu ya gama ɗakin, Kasancewar duk labulayen wondons ɗin a rufe suke. Ga yanayin ɗan hadarin. Bakin gadon ya dawo da ita. zama yayi kana ya jawota gareshi. wani irin maraitaccen sauti ya sake lokacin da yaji ta fara mishi zazzafan darasin daya koya mata. "Hyyyuu, Aishhh". wani irin fitinenne salo mai gigitarwa ta fara mishi wanda yasa gaba ɗaya jikinshi karkarwa da amsa amon aiken da takeyi mishi. Hannunshi yasa bisa kanta yana mai ɗan shafa kanta da ɗan marin kumatunta a hankali da sauri-sauri. Da sauri ta janye kanta jin yadda ya saki wani irin sauti da ɗan ƙarfi. "Ohh yess, Na'am Yah Subahanallah Alhamdulillah". jawota yayi ta faɗa jikinsa bakinsu ya haɗe, ya fara yi mata wani irin tsadajjen kiss mai wuyar samu. hannunshi na yawo a jikinta, yanayi mata wani irin sahihin murza mai cike da kwarewa. cikin rawan jiki take shafa dukkanin sasan jikinsa gaba ɗaya da son nuna mishi kulawarta da tsantsar farin cikin kyautukan daya damƙa mata. a hankali ya zame bakinshi daga nata. yana mai laso fatarta yakeyin ƙasa, har zuwa ƙirjinta nan ya ƙara susucewa. da ɗan ƙarfi tace. "Shhhhhhhhwhhhh". gaba ɗaya jikinshi da nata karkarwa sukeyi. wani irin gigitaccen abu yayi mata mai wuyar a dannewa, kar-kar haka jikinta ya fara karkarwa cikin gigicewa ta yunƙuro ta tashi zaune. hannunta tasa bisa kanshi. Murya na rawa alamun kuka takeyi tace. "Washhhhh Shyyyyyyyyyah Yah Sheykhhhh hyyyyhhhh". sai kuma ta miƙe tsaye tare da ɗora hannun ta saman kanta, ji takeyi kamar tayi ta surfa ihu sabida wani fitinenne tsotsan da yasata jin tamkar shauƙi zai kasheta, da sauri shima ya miƙe tsaye, stiil al'kyabbarshi na jikinsa. ganin yadda jikinta ke karkarwar ne, ya ruggumeta gam-gam ta bayanta. A hankali ya sunkuyar da ita, ta dafa jikin gadon, shi kuwa ya matso kusa da ita ta bayanta. Ware al'kyabbar yayi ya rufesu da kyau tana sunkuyen yana tsaye. Kanta ta cusa cikin gadon tare da jawo blanket ta cusa bakinta ciki lokacin da ta amshi baƙoncinsa. Sabida tabbas in ta bar bakinta a buɗe ji take in numfashin in ya fita bazai dawoba. Wani irin masifeffen karkarwa yakeyi tamkar mazari hannunshi ɗaya dafe da ƙugunshi ɗaya kuma yasa ya danne nata ƙugugun. wasu irin gigitattun hawaye yaji suna silalo mishi murya na rawa yake wasu irin gigitattun surutai da yaruka mabanbanta. "Yah Salam Yah Subahanallah Alhamdulillah. Wayyo Y.M.D.G belɗum. Oh yessss my dear so sweet. Na'am yah Aishhhhhhhh laisa limisluki abadan. Aish! Aish!! Allah ya miki al'barka ya saka miki da jannatul fiedausi ya jiƙan iyayenki yasa ki gama da duniya lfy." Wani irin kukane ya kubce musu Dukansu biyu. Ita tana kukan farin cikin addu'o'in da al'barkar da yake sakamata tabbacin ta bashi dukkan jin daɗi da farin cikin duniya. wanda duk mace ta gari takeso ta bawa mijinta. Shi kuwa Yah Sheykh yarukan da yake gwamutsawa. Fullanci, hausa, larabci, turanci, Indianci harda barbarci." Sosai yake yin abunda yakega zai iya sama mishi nitsuwar juye fitinar manyan tunzura dake cinsa. Wani irin maraitaccen sauti yayi tare da matsawa gareta. Ya faɗa kan gado. kana yasa hannunshi ya jawota jikinshi ya ɗaurata kan ruwan cikinsa. Ya ruggumeta gam-gam a jikinshi yana maida wani dogon numfashi cikin fizgo numfashin da mgnar yace. "Jazakallahu khairan *Mar'atussaliha*". Kanta ya fara shafawa jin har yanzu kuka takeyi a hankali yace. "Kiyi haƙuri Mar'atussaliha dena kuka kinji ko? Kin samu lada mai tarin yawa. Allah ya miki al'barka kinji Nana Aysha Allah miki al'barka yasa ki gama da duniya lfy." Cikin rauni da gajiya murya na rawa tace. "Ahhuhh Amin ya Allah". Ya sani dole ta gaji kuma taji jiki dan sam bai bita a hankali ba, dan ta gama gigitashi. gashi duk jikinta yayi laƙwas sabida dole akwai rashin sabo tunda du-du yaune karonta dashi na uku". Sunkuyowa yayi tare da kunna hasken wayarshi daya ɗauka ƙasan pillow'nshi fuskarta ya haska, sosai idonta suka ɗan kumbura sukayi jazir. tafin hannunshi yasa ya share mata hawayenta, kana ya miƙe zaune ya jingina da kan gadon. Jawota jikinshi ya kumayi cikin sanyi da tausasawa da lallashi yace. "I'm very sorry Aish, kiyi haƙuri daga yau bazaki sake jin wahala ba. kiyi haƙuri gaya min me kike son inyi miki?". Gyara kwanciyarta tayi a jikinshi murya can ƙasa tace. "Kayi ta samin al'barka, kana roƙa min Allah ya azurtani da aljanna ya bamu ƴaƴa nagari salihan bayi da musulunci zaiyi alfahari dasu kamar yadda musulmai ke alfahari da kai Abbansu". Da sauri ya rufe mata bakinta da hannunshi tare da cewa. "Wannan ai na dade ina miki ita kuma in sha Allah har gaban abadan zanyi ta miki ita dan ko a aljanna kece' kece' kece! uwar gidan Yah Sheykh. gaya min wani abun da kike so?". Wani irin murmushi na jin daɗi tayi kana a hankali tace. "Ka dena zuwa part ɗin Hajia Mama, in ta baka abu ko menene kada kaci kazo ka gaya min ni zan maka abun". Cusa kanshi yayi a wuyanta. Ya sani ya yarda yanzu dai Shatu ta zama wani sashi na jikinsa yasan irin duk abunda takeyi dan lfyarsa da farin cikinsa hankali yace. "Me ma zata bani Aish? Ai babu wata mace da takeda abunda zata bani sai ke". Da sauri tace. "Ka cemin bazaka sake ciba kuma ka dena yarda da ita kawai". Murmushi yayi tare da cewa. "To Bazan sake ciba shike nan ko yarda kuma ai dama bbushi". Da sauri tace. "Yauwa Noor Hayat".. A hankali ya miƙe tsaye al'kyabbar jikinshi ya gyara kana a hankali ya jawo blanket ya rufe mata jikinta. Wonka yaje yayi kana, ya fito yace itama taje tayi. Bayan ta fitone. ya zura mata wata tattausar jallabiyarsa. kana ya kamo hannunta suka fito falo. Tare sukaci abinci kana ya jata suka koma ɗaki sukayi baccin liƙe da juna. A hankali a haka dai rayuwa tayi ta tafiya, lokacin nata shuɗewa. Zazzaɓin dare kuwa kullum Sheykh kwana yakeyi dashi, asuban fari ya worke. Shatu na kawo mishi breakfast zai tsareta da salonshi mai gigitarwa. Sai ya zama in ma bai sameta da safe ba. Tofa bayan azahar sai ya ritsata. Zuwa yanzu ya dena bata mamaki sai al'ajabi yake bata sabida ta lura in dai akan wannan fanninne to malamine mai zaman kanshi kullum da salon darussan da yake koyar da ita. Ya ɗan rame alamun baida cikekkiyar lfy ga kuma aikin fatauci. Zuwa yanzu kuwa Shatu ta gama gane cewa Huwaila munafukar Hajia Mama ce. Ita takeyiwa aiki ta gano sam Aunty Juwairiyya Bata san komaiba zagon ƙasa akeyi mata. Yanzu kusan wata biyu kenan Da Sheykh yake fama da wannan zazzaɓin da yasha mishi mgnin ya binciki kansa har ya gaji bai gano meke damunsa ba. Yau jumma'a ne, bayan an taso sallan Jumma'a ne yana kwance a ƙasa bisa carpet. Ita kuwa Aisha tana kwance gabanshi. A hankali ya kamo hannunta ya manna da bakinshi kiss ya sake mata a hankali yace. "Gobe Umaymah da Aunty Hafsat da Rahma zasu zo, jirgin magriba zasu biyo." Cikin jin daɗi tace. "Eh haka Umaymah tace min, zasu zo da Ishma ko?." Cikin wani irin sauri. Ya Tashi zaune y da sauri ya kamo hannunta tafin hannun nata ya zubawa ido cikin mamaki ya ɗago idanunshi ya kalleta cike da al'ajabi da kaɗuwa ya kuma kallon tafin hannunta na hagu. Ita kuwa ido ta zuba mishi ganin yadda yake kallonta. Cikin son tabbatarwa yace. "Aish cik...!? Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k zaki turo ta 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta whatsapp 09097853276. In normal group kikeso na 300 ma ta nan zaki turo, in baki da damar turawa ta ac kuma to nayi miki uzuri ki sayi katin Mtn na ɗari uku kacal ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsapp 09097853276 bana son VTU KADA KIYI min bana so. By *GARKUWAR FULANI*[3/31, 9:24 PM] +234 806 559 0880: "Ta Suma ne!". Da sauri Sheykh ɗin ya taso, tare da sa hannunshi ya amsheta, da sauri ya juya. Itama Umaymah da sauri tabi bayanshi. Side ɗinsa ya koma da sauri key ɗin motarsa ya ɗauka Umaymah na biye dashi a baya kana Haroon ma na biye dasu a baya. Shatu kuwa cikin wani irin kuka mai rauni daya kubce mata ta koma bakin gado ta zauna gaba ɗaya jikinta kerma yakeyi. Shi kuwa Sarkin al'adun suna, da rarrafe ya fita ya bar ɗakin yana fita falon ya miƙe a guje ya bar Part ɗin da sauri Jalal ya mara mishi baya, kafinma ya bar Part ɗin ya damƙeshi Part ɗinsu ya wuce dashi. Mamma kuwa da Gimbiya Aminatu gefen Shatu suka zauna. Hannunta tasa bisa kafaɗarta a hankali tace. "Kiyi haƙuri Aysha in sha Allah babu abinda zai samu ƴarki da izinin ubangiji, zata samu lfy". Cikin rauni murya na rawa ta juyo ta kalli Mamma ido cike da hawaye tace. "Mamma me tayi musu, da zasu cutar da ita ba tare da haƙƙinta ba, shike nan yanzu duk magautan Yah Sheykh sai su dawo kanta, kawai dan ta kasance ƴarsa, Mamma ya zamuyi". Da sauri Gimbiya Aminatu tace. "Babu komai Shatu da izin Ubangiji baza suci nasara a kankuba". Aunty Rahma da Aunty Juwairiyya da Jannart kuwa jiki a mace suka koma falon Shatu suka zauna. Gaba ɗaya jikin kowa yayi sanyi. Khadija da Aunty Amin kuwa tsoron al'amarin masarautar Joɗa ne ya rufesu. Da sauri Mamma ta miƙa ganin Shatu ta zabura ta miƙe tsaye da sauri tare da tallabe breast ɗinta. "Aysha zauna". Murya na rawa tace. "Mamma maman Afreen na tsastsafo da ruwa, Ina Yah Sheykh ya tafi da ita? Ni kam zanje inga halin da take ciki". Ajiyan zuciya mai nauyi Hajia Kubra dake tsaye gefen Mamma tace. "Asibiti suka tafi, kuma insha Allah zataji sauƙi". Kai Gimbiya Aminatu ta gyaɗa tare da cewa. "Sosai ma kuwa tunda har kikaji haka to ta farfaɗo ne". Dai-dai lokacin kuma Umaymah dake tsaye bakin ƙofar ɗakin da Sheykh da wasu manyan likitocin su na Valli Hospital Suka shiga da Afreen a sume. Ta sauƙe wata ƙaƙkarfan ajiyan zuciya jin kukan da Afreen ta cillara da ƙarfi. A cikin ɗakin kuwa. Kusan a tare sauran likitocin suka sauƙe ajiyan zuciya tare da ɗagowa suna kallon Sheykh daya ruggumeta jikinshi tare da cewa. "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!". Sai kuma ya juyo da sauri ya kalli Dr Lukman Ibrahim babban likitan yara kenan na asibitin na cewa. "Ina Maman baby a yi maza a bata mama tasha shi zai taimaka wurin ƙara ƙarya ƙarfin gubar". Da sauri Sheykh yace. "To". Kana ya juya. Yana fitowa Umaymah tabi bayanshi. Tana tambayarshi. "Ta farfaɗo ko?". Cikin ƙara saurin tafiyarsa yace. "Eh Umaymah". Suna shiga motar yaja da sauri ya nufi masarautar Joɗa a guje. A can part ɗinsu Jalal kuwa. Wani irin gigitaccen mari Jalal ya yarfawa Sarkin al'adun suna. Wanda yasa shi jin fitsari ya kubce mishi. Ba tare daya gama dawowa hayyacisa ba ya kuma jin saukan wasu tagwayen maruka a gigice ya kurma ihu tare da cewa. "Wayyoooooooo Allah na na shiga uku ni ilu Jalaluddin kayi haƙuri". A fusace Jalal yasa ƙafarshi ya taɗe sawunshi har saida ya faɗi tib! A ƙasa hannunshi yasa ya tallabe ƙeyarsa tare da sakin wani gigitaccen ihu. Da sauri Jalal yasa ƙafarshi ya taƙa yatsun hannunshi tare da cewa. "Sheeeyyt rufe min baki, uban me kuka sa a cikin fatar ragon sunan?". Cikin kerma da zare ido yace. "Wlh bani ne na sakaba". Ƙara taka yatsun yayi tare da murjesu da ƙarfi yace. "Me akasa a cikin fatar ragon? kuma waya saka? Nawa kuma aka biyaka?". Cikin sakin fitsarin azaba yace. "Madarar fiyafiya ce aka saka cikin fatar. Hajia Mama ce ta saka! Dubu ɗari bakwai ta biyani". Wani irin murza yasun yayi da ƙarfi tare da cewa. "Okay bari in daddage yatsun hannun da zaiyi kisan kai da amsar kuɗin yin kisan kai ɗin". Zuwa yanzu ya gigice ihu kawai yakeyi, shi kuwa Jalal rufe Windows ɗinsa yayi ya mishi ɗan karen duka. Kana ya kira ɗaya daga cikin ma'akatansu na jami'an sirri na soja yazo ya tafi dashi. A nan falon Shatu kuwa, a hankali Jamil da Yah Jafar Suka koma suka zauna. Yana gaba Umaymah na binshi a baya a haka suka shigo. "Aish Aish Aysha!". Ya ɗan ƙare kiran da ƙarfi. Da sauri Shatu ta miƙe da sauri ta nufo falon. Ummi da sauran na biye da ita a baya. Aunty Amina da Khadijah kuma suna zaune. Da sauri ya kamo hannunta bisa kujera ya ajiyeta gefen Aunty Rahma da sauri yace. "Bata nono yi sauri". Da sauri tace to tare da fara kiciniyar ɗago rigarta. Ina gani yake bata sauri shiyasa cikin sauri ya ɗaura mata ita kan cinyarta. Kana yasa hannunshi ta baya ya zuge zip ɗin rigar yayi ƙasa da ita. Hannunshi yasa ya fito da breast ɗinta na dama. Tare da ɗago kan Afreen daketa fidda wani irin numfarfashi alamun har yanzu numfashin bai dai-dai taba. Da sauri kuwa ta damƙi nonon tare da fara zuƙa. Wani irin dogon ajiyan zuciya mai nauyi suka sauƙe a tare shi da ita. Lokaci ɗaya kuma hawayensu ya kwaranyo bisa fuskokinsu. Cikin sanyin murya yace. "Alhamdulillah Aish kada kiyi kuka kiyi mata addu'o'in samun lfy ke wuce addu'aki gareta bata da hijabi". Hannunta tasa tana ƙara tallaɓe kan Babyn murya na rawa tace. "Yah Allah ka bawa wannan baiwa taka lfy ka yaye mata wahalar shaƙar numfashi ka sauƙaƙa mata shi al'farmar Annabi da al'ƙur'ani." "Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati my Dear". Ya faɗa yana share mata hawayen fuskarta da hannunshi na hagu. Su kuwa saura kab ajiyan zuciya sukayi tare da cewa. "Alhamdulillah".. Sai lokacin ya ɗan kalli Aunty Rahma dake gefen Shatu tana zubda hawaye a hankali yace. "So sorry my Aunty in Sha Allah babu komai likita yace, da shayar da ita shi akayi zaifi mata illa yanzu kuma shaƙane an mata duk wani taimakon gaggawa daya kamata". Cikin gamsuwa ta gyada kai. Sai kuma ya ɗan taso tsaye sai lokacin yaga yawansu. A hankali ya ɗan sunkuyar da kanshi cikin sanyi yace. "Gimbiya Aminatu in sha Allah daga yau wannan al'adar zata kau a masarautar Joɗa dama duk wasu tarkacen al'adun daba addiniba ki gayawa Lamiɗo". Cikin jin daɗi tace. "Ai ba ita kaɗai ba in dai ka yarda ka mulki masarautar Joɗa duk wata al'ada na masarautun gargajiya kana da damar datsesu ka wanzar da Sunnah". Wani irin dogon ajiyan zuciya mai nauyi ya sauƙe. Tabbas masarautar Joɗa tana buƙatar sabon Sarki sabon tsari sabon zubi bisa koyarwar musulunci da sunnar manzon Allah a kauda bidi'a a kawo sunna. To amman shi baida ra'ayin mulki. Cikin sanyi yace. "Gyaran ba lallai sai ni ɗaya zan yi shi ba ai, kuma ko bani ke mulkiba zan iya bada shawara in an yarda a amsa". Cikin sauri Umaymah tace. "Idan dai har kana son kauda al'adun a wanzar da sunna to dole ka mulki masarautar Joɗa da kanka". Kanshi kawai ya jingina jikin kujerar kana a hankali ya sunkuyo yana kallon Shatu dake cewa. "Baiyi mulki Bama Umaymah ana neman ransa da na ahlinsa". Lamiɗo da Galadima dake shigowa ne dan jin lbrin abinda ya faru a bakin Jalal ne. Suka haɗa baki wurin cewa. "Ƙi gudu sa gudu, Shatu ke muke zaton zaki bashi ƙarfin guiwa kuma sai ki karaya da wuri haka." Da sauri su Umaymah kab suka ja da baya suka basu wurin zama. Suna zama dai-dai lokacin kuma Shatu ta zare mamanta daga bakin Afreen ɗin cikin tsoron ganin yadda ta ke ɗan yunƙuri tana kwaro amai. Da sauri Sheykh ya matso tare da cewa. "Innalillahi". Ita kuwa Shatu ɗagota tayi da sauri ganin yadda taketa yunƙirin kakarin amai ba ƙaƙƙautawa. Da sauri Gimbiya Aminatu ta matso tana cewa. "Subahanallahi" Shi kuwa Sheykh wayarshi dake cikin al'jihun rigarsa ya zaro da sauri ya kira Dr Lukman Ibrahim yana ɗagawa yace. "Dr Baby fa sai amai takeyi ba tsayawa". Da sauri Dr Lukman Ibrahim yace. "Alhamdulillah tasha Mamanta ko?". "Eh tasha, tana shane ma ta fara aman". Ya bashi amsa. "Yauwa haka akeso Sheykh ba komai yanzu duk kaifin gubar ya karye ta harar dashi yanzu zatayi bacci kuyi mata wonka da ruwan sanyi. Tana farkawa kuyi mata wonka da ruwan sanyi kuma zata dawo dai-dai da izin Ubangiji". Da sauri ya katse kiran bayan yace. "Ok thanks Dr". Ita kuwa Shatu ajiyan zuciya ta sauƙe tare da meda kanta ta jingina da kujera ganin ta bar aman. Shi kuwa Umaymah ya kalla tare dayi mata bayanin da Dr yayi mishi. Da sauri ta iso garesu ta amshi ƴar kana ta wuce Bathroom. Wonka tai mata da ruwan sanyi ɗan kwalinta ta wore ta naɗeta a ciki. Tuni tayi bacci kafinma ta fito da ita. A hankali ta zauna bakin gadon Shatu gefen Aunty Amina da Khadijah dake waya da Abboi Appansu kenan tanai mishi bayanin duk abinda ya faru. Cikin tashin hankali da mamaki Abboi yace. "Subahanallahi, kai wannan gida nasu akwai sarƙaƙiya. yanzu ina Parvina?". A hankali tace. "Tana falo can naji kamar harda Lamiɗo ma yazo da kanshi, amman yanzu yarinyar gata nan ta farfaɗo harma tayi bacci". Cikin kula da son ahlinshi especially Parvina a hankali yace. "In sha Allah nida Dedden ku da Al'ameen zumu zo gobe gobe da izinin ubangiji, dama tun tuni ma shiryawa hakan, in Parvina ta shigo kice ta kirani". Da sauri tace. "Toh Appa". Guntun murmushi Umaymah tayi tare da cewa. "Babanku kika gayawa ne?". Cikin alamun karaya da lamarin gidajen sarauta tace. "Eh Umaymah". Kai kawai ta gyaɗa tare da gyarawa jaririyar kwanciya. Aunty Amina kuwa sunkuyowa tayi tana kallon fuskar Babyn. A falon Shatu kuwa sosai Lamiɗo ya kwantar mata da hankali kana suka tafi Gimbiya Aminatu na biye dasu a baya. Bayan ta shiga ta ƙara duba Babyn. Umaymah kuwa fitowa falon tayi suka zauna a nan. Ita kuwa Shatu bedroom ta koma ta konta tasa yarta a gaba tofi takeyi mata tana kallon fuskarta Allah ya sani ji takeyi kamar bata tsiraba shiyasa har yanzu hanjin cikinta ke kaɗawa. A hankali ta jawo wayarta. Abboi ta kira, bayan sun gama gaisa ya alhinta abinda ya faru ya ɗaura da cewa. "Dama can gobe zamu zo ko ba komai zanzo inga amryata, inga mummunace ko kekyawa". Ya ƙare mgnar da ƴar raha da son kontar mata sa hankali. Murmushi tayi tare da cewa. "Allah ya kawomku lfy Appa na, da Ummey na da Junainah take kamafa". Tayi mgnar cikin jin kunya duk da yawan shaƙuwa dake tsakaninsu. Murmushi yayi tare da kallon Dedde dake jin duk tattaunawar da sukeyi yace. "Ato kekkyawace sadaki ta garken shanun Bappa zai bata". Dariya sukayi baki ɗayansu kana sukayi sallama da juna. Daga nan kuma Bappa ta kira, wanda tun ɗazu Abboi ya shaida masa abinda ya faru yana ɗagawa yace. "Shatu na ya jikin Aisha ƙaramar dai?". A hankali ta ɗan shafa kan Afreen tare da cewa. "Alhamdulillah Bappa na ba komai ta samu lfy gatama tana bacci". Cikin jin daɗi yace. "Alhamdulillah ga Ummeynki tun ɗazu hankalinta a tashe yake". Amsa Ummey tayi cikin kula tace. "Boɗɗo na me sukayi miki?". Cikin yin ƙasa da murya tace. "Ummey na so sukayi su kashe miki jikarki tun baki ganta ba, dan Allah da Manzonsa Ummey na kizo gobe". Cikin kaɗuwa da begen son ganin Shatu da ƴar tata tace. "In Sha Allah Gobe za muzo tare da Abboi da izin Ubangiji". Cikin jin daɗi tace. "Alhamdulillah naji daɗi na, Gobe ina cikin gatana". Su kuma ta kalli Umaymah da ta shigo yanzu tare da cewa. "Alhamdulillah Umaymah na Gobe Ummey na zatazo da Bappa na da Deddena da Abboi". Cikin wani irin masha'hurin farin cikin alamun son tabbatuwar wani abu Umaymah tace. "Alhamdulillah Allah ya kawo mana su lfy". Amin Amin sukace baki ɗayansu. Haka dai akayi wunin sunan jiki a mace da abinda ya faru. Sai can da yamma ne da Afreen ɗin ta farka daga baccin suka ganta lfy lau kafin hankalin kowa ya kwanta. Nan Umaymah suka fito da kayan suna na gani na burgewa, da aka haɗawa mai jego da Ɗiyarta. Kayan da Sheykh yayi musu kuwa abin sai dai ace son barka. Gaba ɗaya wunin yau shima ya kasa fita ko nan da can tunda akayi sallan Jumma'a ya shigo ya wuce Side ɗinsa. Bini-bini ya kira Shatu ko Umaymah ya tambayi jikin yarinya. Bayan sun dawo sallan la'asar ne. Jalal ya biyoshi har cikin falonshi, gefen Haroon ya zauna kana a hankali yace. "Shima sarkin al'adun sunan harda shi a sahun Magauta sai dai biya shi Hajia Mama tayi da dubu ɗari bakwai daga baya yace min tace in ƴar ta rasu zata cikata mishi dubu ɗari uku ya zama one million". Cikin mamaki Haroon yace. "Ikon Allah ikon gaske, wai ita wannan shegiyar matar meyasa bazamu fito mata a fili bane mu nuna mata mun san komai mu kuma juyo kanta". Cikin taune lips Sheykh yace. "Uhumm bazaku gane bane,". Da sauri Umaymah dake shigowa tace. "Ni na gaji bazamu gane me ɗin ba kuma". Cikin wani irin yanayi mai rauni cikin sanyi murya na rawa yace. "Affan ina ɗagawa Hajia Mama kafane sabida Affan ina jin takaici in na tuno a cikinta Affan ya fito, ku kun san waye Affan kun kuma san asalin zahirin gskyar so da ƙaunar da yake mana, kunsan yadda yake faman faɗa da yaƙin sauya mahaifiyarshi daga mummunan ɗabi'a eh zuwa kekkyawan ɗabi'a. Ta yaya zanci zarafin ta al'halin Affan ya ɗaukeni matsayin Uba ya ɗaukeni ciki ɗaya muka fito,kada ku manta son da Affan kewa Mameynmu Jalal ka duba tarin son da Affan yakeyi muku kaida Jamil. Ko a lahira wani kanci al'barkacin wani. Ina barine sabida ko Affan zai samu nasarar juya halinta". Ya ƙarashe mgnar hawaye na zubo mishi. Gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi tabbas sun san waye Affan ko su Jalal basa so da shaƙuwa dashi kamar Affan. A hankali yace. "Duk abinda nasa Affan zaiyi minshi babu musu koda baya son abin duk inda na aikeshi zaije min duk abinda na bashi zaɓi zaɓina yake bi, Affan da kanshi ya fara nuna min baya son inci abincin Hajia Mama wacce take uwace a garesa, yayi hakane sabida zargin tana samin abu a cikin abinci. Yasha yin kuka yana mgiya in ya tareta tana wani abun me zanyiwa Affan in nuna mishi halaccin ɗan uwantaka banda in rufawa mahaifiyarshi asiri". Shiru yayi ganin kiran Affan daya shigo wayarshi. Jiki a mace itama Umaymah ta zauna. A hankali ya kara wayar a kunne bayan a amsa kiran. "Assalamu alaikum Hamma Jabeer". Affan ya faɗa cikin tsananin so da ladabi ga ɗan uwan nasa. "Wa alaikassalam Affan kana lfy". Sheykh yayi mgn yana mai jin wasu zafafan hawaye na tsastsafo mishi. Murmushi Affan yayi cikin yanayin shi na Happy mood yace. "Alhamdulillah Hamma Dr Akarmakallu Yah Sheykh, mun sauƙo lfy". Jingina bayan sa yayi da kujera tare da cewa. "Alhamdulillah Affan Allah yayi ma al'baka". Da sauri yace. "Amin Hammana". Sai kuma yace. "Jamil ne yazo ya daukomu a airport to yanzu mun biya mun sauƙe Yah Sulaiman da Malam Abubakar. To gani tare dasu Giɗi ɗin yanzu su ina zamu kaisu, umarni nake jira Hamma?". Cikin sanyi yace. "Alhamdulillah Affan ku dawo dasu masarautar Joɗa ku wuce dasu Part ɗinsu Jalal a sauƙesu a can. Bawa Jamil wayar". Da sauri yace. "An gama sir yadda kace haka za'ayi ga Jamil ɗin". Ya kare mgnar yana miƙawa Jamil wayar. Saƙale wayar yayi da kafaɗarsa tare da cewa. "Assalamu alaikum Yah Sheykh". Gyaɗa al'kyabbar jikinshi yayi tare da cewa. "Wa alaikassalam Jamil ka kaisu part ɗinku ɗakinka ka nuna musu Bathroom suyi wonka. Aunty Rahma zata kawo musu abinci ka tabbatar sunci sun ƙoshi. Sannan Jalal zai ɗauki Dr Kabir zaizo ya dubasu in sunada matsalar lfy zai kula da komai". Cikin gamsuwa Jamil yace to yana kallon kekyawar fuskar Giɗi ta madubin motar. Shi kuwa Sheykh a hankali yace. "Toh Umaymah a hakan ta yaya zan tozarta mahaifiyar Affan wanda duk munin halinta uwa dai uwace." Cikin rauni Umaymah tace. "Wannan hakane Jazlaan amman Hajia Mama tanayi mana illa a rayuwa". Sosai jikin Haroon yayi sanyi. Shi kuwa Sheykh Jalal ya kalla tare da cewa. "Kaje Valli ka taho da Dr Kabir". Jiki a mace Jalal yace to kana ya miƙe ya fita. Umaymah na biye dashi a baya, har taje bakin ƙofar fita a hankali yace. "Ayyah Umaymah Ɗiyar taki ta kawo min ɗiyar tawa mana in ganta". Murmushi tayi tare da cewa. "Toh". Shi kuwa Haroon da sauri yace. "To bari in baka wuri dan nasan dai uwar ɗiya za'a gani ba ɗiyaba". A hankali yace. "Mutun da abinsa". Dariya Haroon yayi kana ya nufi ƙofar da zata sadashi da Garden. A hankali ta turo ƙofar Bedroom ɗinsa. Tare da cewa. "Assalamu alaikum". Cikin wani irin happy yace. "Wa alaikissalam". sai kuma ya juyo ya fuskanceta tare da buɗe mata hannunshi. Cikin sauri ta faɗa jikinshi ruggume da Afreen haɗe su yayi ya ruggume tare da cewa. "Alhamdulillah ya Allah ka tsare min ahlinna ka cika mana farin cikinmu". "Amin ya Allah". Ta faɗa a hankali sai kuma ya jawo hannunta suka zauna a bakin gadon. Cikin narke fuska yace. "Nayi fushi Aish tun ɗazufa na aika kizo baki zoba sai yanzu". Cikin sanyi tace. "Ayyah Malam sallan la'asar nakeyi". Cikin sauri ya kalleta tare da cewa. "Kai haba dai Aish da gaske shine baki gaya minba yaushe kika fara salla". Murmushi tayi tare da cewa. "Yoh ai dama ina salla". Lakace hancinta yayi tare da cewa. "Batun gsky dai my dear yaushe kika samu tsarki?". Cikin nitsuwa tace. "Yau da safe, nai wonka naci gaba da salla tunda naga jinin biƙin ya ɗauke na samu tsarki". Kanshi ya gyaɗa tare da cewa. "Masha Allah, jego yayi kyau kenan Boɗɗo na, dama wasu matan kafin satin sunama sun samu tsarki sun fara salla, kinga kema kina ɗaya daga cikinsu wasu kuma sai anyi arba'in ma, wasu har hamsin suna likin. Koda yake ke dama al'adarma kwana uku kikeyi ko". Kai ta gyaɗa mishi. Hannunshi ya cusa ƙasan pillow'nshi tare da zaro key ɗin sabuwar mota dal a leda. Kamo hannun ta yayi ya danƙa mata key ɗin tare da cewa. "Al'ada kwana uku baƙi kwana bakwai kai naji daɗi na, na more". Da sauri ta buɗe tafin hannunta tare da kallon key ɗin sai kuma ta lumshe idonta jin ya manna mata tattausan lips ɗinsa a goshi ya sake mata sassayan kiss. Tare da cewa. "Taki ce motar sai dai bani son kiyi tuƙi nafi son a jamin ke, sai daifa bana miji zai jamin keba. Sara taki zata zama yar rakiyarki mai jan mota da tayaki kula da Babynmu, duk inda kuke in bana kusa daku. Gimbiya Aminatu zata bamu wata mai girki". Cikin wani irin farin cikin ta ruggumeshi gam-gam a jikinta. Da sauri yace. "Wayyo Aish zaki danne Mimi na". Da sauri ta kwantar da Afreen gefe, kana ta faɗa jikinshi ta rungume shi. Murmushi yayi mai cike da farin ciki cikin wasa yace. "Zaki bani abin daɗi?". Da sauri tace. "Ban workeba". Dariya mai ɗan sauti yayi tare da haɗe bakinsu wuri guda. A part ɗinsu Jalal kuwa. Yah Giɗi Seyo Gaini ne zaune bayan duk sunyi wonka, sun saka sabbin kayan da Jamil ya zaro musu cikin durowarsa. Cikin wani irin yanayin jin daɗin duniya da kuma bege da kewar iyaye da ƴan uwa wanda da sun cire tsammani. A hankali Yah Giɗi ya kalli Jamil dake miƙo mishi turare yana cewa. "Kai masha Allah sai kunga yadda kukayi kyau, farinku ya ƙara fitowa". Cikin rauni Giɗi yace. "Dan Allah bawan Allah, nan ina muke ne? Kuma ina wanda muka dawo dashi? Sannan ina za'a kaimu? Wayasa aka fito damu?". Da sauri Jamil ya zauna gabanshi kamo hannun shi yayi a hankali yace. "Nan kuna cikin Ɓadamaya ne, cikin masarautar Joɗa, wanda kuka dawo dashi kuma Yayana ne Affan ya tafi ƙofar matarshi. Wanda ya taimake ku yasa aka fitar daku kuma babban Yayanane Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa. Yana nan matarsa ta haihu yau akeyin suna. Sai in ya nitsu zaizo wurinku shi zai gaya muku ina za'a kaiku". Wasu irin hawaye ne suka tsunkowa Gaini murya na rawa yace. "Alhamdulillah kowa yace yaya zaiyi ya manta da Allahu wahidun ƙahharar sarki buwayi gagara misali mai badawa mai hanawa mai raya mai kashewa mai kawo sauƙi cikin tsanani mai yaye tsananin duhu ya wanzar da haske". Ido Jamil ya zuba musu cike da so da ƙaunar su, sai kuma ya kalli Seyo da yake zubda hawaye cikin sanyi yace. "Ko wanne hali ahlinmu ke ciki". Da sauri Jamil yace. "Yanzu muje falo kuci abinci kunji dan Allah ku bar kukan". Kasan cewar ya haɗa su da Allah yasa ba musu suka tashi. Amman badon hakaba farin cikin da suke ciki ya kori yunwa bare ƙishi. A tsakiyar falon suka zauna. Jamil da kanshi ya zuba musu abincin da Aunty Rahma ta kawo musu. Sukaci suka sha. Dai-dai lokacin kuma aka kira sallan magriba. Nan sukayi al'wala kana Jamil ya jasu sukayi jam'i. Shatu kuwa bata bar ɗakin Sheykh ba saida ya tafi masallaci. Ta fito cike da farin ciki. Aunty Amina da Khadijah da Umaymah da Hibba ta samu a falonta Umaymah ta miƙa wa key ɗin tare da cewa. "Umaymah Yah Sheykh ya saya min mota". Cikin jin daɗi Umaymah tace. "Masha Allah. Allah ya sanya al'khairi". Amin Amin sukace baki ɗayansu. Kana duk sukayi al'wala haramar salla. Ƙarfe goma da rabi. Duk baƙi sun watse. Sai su Umaymah da su Aunty Amina. A falon Shatu suke suna hirarsu cikin salama Ummi na ruggumi da Afreen. Umaymah kuwa na haɗawa Shatu tea da fifitashi da kyau. Aunty Rahma kuwa kitso Khadija keyi mata. Junainah da Ishma kuwa suna can babban falon da Hibba da Jalal. Sara da Larai da indo hadimar Aunty Juwairiyya kuwa tattare kitchin sukeyi da kimtsa ko ina na gidan. Sheykh kuwa a hankali ya jawo wayarshi daya tattare wacce yake waya da Hajia Mama da ita. Kiranta yayi. Tana amsawa yace. "Ƴar ta mutu ko?". Wani irin gigitaccen tsaki taja tare da cewa. "Inafa ta mutu na dai ji ta suma amman wannan Shegen yaron duk abinda nayi a kanshi ko matarsa yanzu dama yar tashi abun baya tasiri. Sannan babban tashin hankali na, shima Sarkin al'adun suna bai dawoba. Kuma wayarshi na shiga baya ɗagawa, tsorona kada dai sun ganeshi". Cikin sauya muryarsa ih zuwa muryar Jahan yace. "A a ba dai kamashi ba kam, sai dai ko in yana jin tsoron amsa kiran nakine sabida kada kiyi mishi faɗa tunda ƴar bata rasuba kada kice bai iya aikinsa bane a ganina fa shine yasa baya amsa kiran naki". Cikin tashin hankali tace. "Ni babbar matsala ma yau tunda gari ya waye hankalina yake a tashi zuciyata na tsinkewa gaba ɗaya tsoro ya rufeni ji nakeyi wani mugun abu yana tunkaro rayuwata, naje gidan boka kuma ya koroni shima sai tsalle yakeyi yana kaɗe jikinsa Wai komai na gab da dawo mana". Murmushi mai cike da jin daɗi yayi a ransa yake zaton ko shiryace zata zo mata, haka yasa yace. "Sai gobe zanzo muyi mgn in kaiki gidan wani sabon boka". Da sauri tace. "To". Daga nan ya katse kiran. Kana ya miƙe ya fito falo, a hankali ya kalli Jalal da Hibba tare da cewa. "Jamil fa". "Yana Part ɗin mu". Jalal ya bashi amsa". To yace kana ya juyo ya kalli Yah Jafar da yanzu ya shigo kenan. A hankali ya tsaya gaban Sheykh. A hankali suka lumshe idonsu a tare, da sauri Sheykh da Jalal da Hibba suka matso kusa dashi sosai jin yana cewa. "Jabeer zuciyata na tsinkewa tun jiya sai inji kamar wani abu zai faru". Cike da mamaki Jalal yace. "Wlh nima tun jiya zuciyata ke tsinke kirjina yaita bugawa". Wani irin rumtse ido Sheykh yayi tare da cewa. "Nima abinda naketa fama dashi kenan tun jiya, to da Aisha ta suma sai nai zaton ko abinne ke samin tsinkewar zuciya. To kuwa still abin bai bariba saima ƙaruwar da yakeyi yana tsananta". Cikin sanyi Hibba tace. "To kuyi ta addu'a hakama Umaymah da Mamma da Aunty Rahma sukace suna ji". Kai suka gyaɗa gaba ɗaya. Hannun Yah Jafar ɗin Sheykh yaja suka nufi Part ɗin su Jamil. Su kuwa su Jalal zama sukayi suna kallon Ishma da Junainah daketa sabgoginsu. A hankali Sheykh ya zauna tare da kallon Jamil dake zaune tsakiyarsu Giɗi a hankali yace. "Ka barsu su huta mana". Cikin sanyi Jamil yace. "Allah ko Hamma Jabeer ina so in tafi wurin Khadijah ma sai inji zuciyata na tsinkewa kamar dai zan samu wani abu". Cikin kula Sheykh yace. "Uhmm duk haka mukeyi kaita mai-maita innalillahi wa innailaihi rajiun". To yace. Shi kuwa Sheykh nitse ya kalli Gaini da zai kai sa'an Affan. Cikin kula yace. "Sannunku da hanya". A tare sukace sannu. Jamil ne ya ɗan kallesu tare da cewa. "Shine babban yayanmu Sheykh da yasa aka fito daku". Da sauri suka ɗan gyara zama suka matsoshi tare da cewa. "Allah sarki bawan Allah mun gode Matuƙa Allah ya saka da al'khairi ya kula da ahlinka fiye da yadda ka kula damu". Cikin jin daɗi yace. "Amin ya rabbil izzati, amman kuma duk haka ya farune sanadin Sulaiman da aka rufeshi tare daku". Cikin gamsuwa sakace. "Ayyah". Sai kuma Giɗi ya ɗan share hawayen da suka zubo mishi tare da cewa. "Ayyah bawan Allah yaushe zamu koma Rugar Bani muga Bappa da Inna da Ummey da Shatu da Junnu". Cikin gamsuwa da tausayinsu Sheykh yace. "In sha Allah nan kusa amman nafi son sai naga kunyi aski kun ƙara hutawa, gobe zuwa jibi da kaina zan medaku". Cikin wani irin masifeffen jin daɗi sukace. "Allah ya kaimu". "Amin Amin". Yace kana ya musu sai da safe. Daga nan wurin Abbanshi da Lamiɗo da Galadima yaje suka ɗan yi wata mgnar kana ya dawo. Ranar dai haka suka kwana gaba dayansu babu wanda yayi isasshen bacci sabida masifar bugawa da ƙirazansu keyi. A can Rugar Bani kuwa. Ko abincin dare Ummey bata iya ciba. Haka nan sai taji zuciyarta na tsinkewa yana bugawa. Tun abun bai damunta har ta gayawa Bappa, so ya bata ƙarfin guiwa da yin addu'a. *Ba'ana* Zaune yake gaban yaransa cikin rauni da yanayin damuwa yace. "Nanda wata uku masu zuwa zan koma ƙasar Nigeria zanyi yaƙin neman Shatu koda zan rasa rainane, zan koma gareta. Zan gaya mata ko mutuwa nayi sonta ne ajali na". Cikin bashi ƙarfin guiwa ɗaya daga cikinsu yace. "Zama kayi nasara". A hankali yace. "Babu tabbas, domin tunda na rasa Shatu nakega nayi rashin babbar nasara". Sai kuma ya miƙe ya shiga cikin ƴar ƙaramar bukkarsa. Murmushi Baron yayi tare da katse kiran da yayi Sheykh yana jin duk bayanan Ba'ana. Dan shi Baroon yanzu ya zama ɗan aikin Sheykh dan tun zuwansa lokacin ciwon hannun Shatu. Da fari har yasa a kirasa daga baya yasa aka dawo dashi. Ya biyashi kuɗi masu tarin yawa, yayi mishi duk bayanin ɗaya nema, kana yasashi ya koma wurin Ba'ana kuma ya naɗo mishi rahoto da duk wani motsin Ba'ana yana turo mishi. Alhamdulillah kuma yanzu duk shirin kama Ba'ana yakeyi. Washe gari ranar asabar yau babu aiki. Da misalin ƙarfe goma na safe jirginsu Abboi ya sauƙa cikin birnin Ɓadamaya. Kai tsaye Salmanu yayi musu jagora zuwa Rugar Bani dan a take suna sauƙa wasu tsala-tsalan motoci guda biyar suka iso wanda dama su tun jiya suka iso. A ƙasan plate number motocin akwai tambarin hatimin kan shanu a ƙasa ansa Abboi, irin tambarin dake jikin jiragen Abboi kenan. Suna zuwa kuwa babu ɓata lokacin suka isa har cikin gida. Inda nan Arɗo Bani da kanshi da sauran dattawan sukazo. Bayan sun gaggaisane Abboi ya ɗan yi gyaran murya tare da cewa. "Toh Alhamdulillah lallai komai yayi forko to tabbas yana da ƙarshe, to bayan bincike da bin diddigi dai mun gama fahimtar inane asalin wannan baiwar Allah'n kuma munada yaƙinin daga masararutar Joɗa ta fito. To yau dai kam ranar data kamata mu shiga da ita ciki da yardar ubangiji tazo. Kamar yadda muka tsara, yanzu zamu tafi". Cikin tsananin jin daɗi da kuma fargabar ko ya al'amarin zai kasance Bappa yace. "Alhamdulillah mu duk a shirye muke, fatanmu Allah yasa ina munje ta tuna baya, ta tuno ita wacece". Da sauri Arɗo Bani yace. "In Sha Allah ma zata tuna Malam Babayo". "Allah yasa haka". Al'ameen ya faɗa. Amin Amin sukace kana duk suka miƙe suka fito. Kana Bappa yazo yacewa Ummey da Dedde su fito. Nan suka mara musu baya. Mota ɗaya Bappa da Abboi da Arɗo Bani suka shiga. Ummey da Dadde da Al'ameen kuwa suma mota ɗaya suka shiga. Sauran kuma ƴan tsaronsu ne a ciki sai motar Yah Salmanu da Hafsi ƙanwar Shatu a haka suka fito daga Rugar Bani suka nufi Masarautar Joɗa. A hankali Ummey ta jingine kanta da jikin kujera tare da dafe ƙahon zuciyarta a hankali ta furta innalillahi wa innailaihi rajiun". Sabida tsananin tsinkewar da zuciyarta keyi Dedde kuwa hankalinta naga makiyayan dake zirya. A nan cikin birnin Ɓadamaya a tsakiyar Masarautar Joɗa kuwa. Gaba ɗaya su Umaymah suna falon Shatu. Aunty Rahma ce da su Sara a kitchin, Aunty Juwairiyya tana part ɗinta da Hibba. Junainah da Ishma kuwa suna kitchen tare da Aunty Rahma. Kowa sabgar gabansa keyi. A hankali Shatu ta miƙe ta nufi ƙofar falon Sheykh da sallama a bakinta. Shiru ba kowa a falon tray'n breakfast ɗinshi shida Haroon ta ajiye bisa Dinning table. Ganin ba kowane yasa ta turo kanta cikin bedroom ɗin. Shiru ba kowa a hankali ta ƙara so ciki tana cewa. "Salam Yah Sheykh". Ƙofar bathroom ta matso a hankali ta tura ba kowa a ciki komai yana kimtse tsab-tsab. "Toh ina yaje kuma yau Lahadi kuma ai babu inda zaije". Shiru tayi tare da juyowa ta matso tsakiyar ɗakin jujjuya kanta tayi ba mutun ba alaman mutun a ɗaki. Har ta juya zata fita, sai kuma tayi sauri ta juyo tazo bakin gadonshi, abun data hanƙo ƙasan pillow'nshi ne yasa ta sunkuyowa da sauri hannunta tasa ta zaronshi. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". Ta faɗa jiki na rawa tare da sakin fuskar robar da Sheykh ake amfani da ita a matsayin Jahan. Da sauri ta juyo da nufin zata fita, sabida tsoron daya rufeta. Sai kuma tayi sauri taja da baya tare da zare idanunta dai-dai lokacin da ta iso jikin marfin wodurob ɗin sa Wanda yayi dai-dai da lokacin da Sheykh ya turo marfi ya fito. A gigice take jujjuya kai tare da zaro ido. Sai kuma ta juya da sauri ta kalli fuskarnar da ƙarfi ta buɗe baki tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun Yah Sheykh". Da sauri yasa hannunshi ya kamo nata ya fizgota jikinshi cikin haɗe fuskarsu wuri ɗaya yace. "Na'am Aysha please kada kiyi ihu tsaya nitsu nine Muhammad Jabeer Yah Sheykh mijinki Abu Afreen". Cikin yanayi kaɗuwa tace. "Yah Sheykh kai mutum ne ko al'jan". Da sauri ya kamo hannunta suka iso gaba durowar. Buɗe ƙofar yayi, kana a hankali yasa hannunshin ya ture, al'kyabbas ɗin shi dake jere a hanga a saƙale, sai ga wani ƙofa mai kamar glass. A hankali yace. "Aysha nitsu ki jini kinji ko". Cikin sauƙe numfashi tace. "Toh". Kanshi ya gyaɗa kana a hankali yace. "Kinga wannan wurin ko?". Da sauri tace. "Eh naga kamar ƙofa ne". Jawota yayi suka ɗan matso hannunshi yasa ya tura ƙofar da sauri tace. "Lahh". Sabida ganin wata ƴar siririyar hanya mai tsawo. A hankali yace. "Ni mutum ne Aish yanayin tsarin masararutar Joɗa ne yasa dole nake amfani da wasu ababen. Kinga wanan hanyar har cikin bedroom ɗin Lamiɗo da Abba na duk akwai su. Muna haɗuwa dasu a ɗakin Lamiɗo lokuta da dama. In kina so anjima zan nuna miki, dan yanzu Lamiɗo ya rufe ƙofarsa ne da yanzu zamuje". Da sauri tace. "Me kukeyi a ɓoyen". Jawo ƙofar yayi ya rufe kana a hankali yace. "Ina wani aikine Aish Kuma aikin sirrine, tsawon shekaru inayi babu wanda ya sani sai Lamiɗo da Abba na da Umaymah sai yau kuma da kika zama ta uku". Ya ƙarashe mgnar yana jawota suka zauna bakin gado. A hankali ta sauƙe numfashi ido ta zuba mishi a hankali tace. "Kai SS ne ko Yah Sheykh?". Murmushi yayi tare da cewa. "Ba'a faɗa kiyi shiru kada wani yaji kinji ko sirri ne Boɗɗo na". Murmushi mai cike da jijjina tayi mishi. Shi kuwa ruggume ta yayi ya koma baya ya kwanta. Dai-dai lokacin kuwa motar Salmanu dake gaban motocin su Abboi ta kusa kai cikin matsarautar Joɗa bayan an wangale musu gate. Wani irin rumtse ido da ƙarfi Ummey tayi tare dasa kanta bisa guiwowinta sabida wani irin masifeffen tsarawa da kanta yayi da azaban ƙarfi. Kai tsaye bakin part ɗin su Sheykh Salmanu ya nufa dasu sai dai Motar Abboi da sauran duk a can baya bakin fada suka tsaya inda Bappa ya nuna musu. Yadda suke ƙara kusanto Part ɗin su haka sarawa da bugun zuciyar da Ummey keyi yake ƙaruwa. A can cikin falon Shatu ma, da sauri Umaymah da Mamma Suka kalli juna sabida masifar bugawa da ƙirazansu sukayi. Sheykh kuwa da ƙarfi ya ruggume Shatu sabida ji yayi tamkar zuciyarsa zata faso ƙirjinsa ta fito woje. Jalal da ke Part ɗin Yah Jafar da sauri ya rumtse idanunshi shida Yah Jafar ɗin. Hakama Jamil dake tare dasu Gaini. A hankali motocin sukayi parking. Ummey kuwa wani irin ƙara rumtse idanunta tayi da masifan karfi. Dedde kuwa a hankali ta buɗe ƙofar. Ta sako ƙafarsa cikin shigarta ta al'farma. Shi kuwa Al'ameen da sauri ya zagayo ya buɗe wa Ummey kofar tare da cewa. "Ummey mun iso bismillah". Cikin tsananin danne sarawar da kanta keyi ta ɗago jajayen idanunta a hankali ta zuro ƙafafuwan woje. Ras ras Din dab din dab haka zuciyarta ta bada wasu tagwayen bugu. Da sauri tasa hannunta ta dafe ƙirjinta. Dedde kuwa a hankali ta zagayo inda take. Shi kuwa Al'ameen a hankali yace. "Bismillah ku shiga ga ƙofar". A hankali Dedde tace to kana ta nufi ƙofar. Ita kuwa Ummey cikin rawan jiki ta ɗaga ƙafarta ta dama ta ɗaura kan barandar tare da ƙara dafe ƙirjinta da rumtse idanunta sabida jujjuyawan da kanta ya fara. Shi kuwa Al'ameeen bayansu yabi. Shi kuwa Salmanu a hankali ya kalli Hafsi ƙanwar Shatu dake bin Khadijah. Cikin yin ƙasa da murya yace. "Ko in ɗagaki ne in kaiki". Cikin jin kunya tace. "A a Yah Salmanu zan shiga da ƙafata". Su Bappa kuwa Sarkin ƙofa ne yayi musu iso zuwa cikin fada. A hankali Dedde ta kai hannunta ta kama handil ɗin ƙofar falon ta murɗa tare da turawa kana tasa ƙafarta ta dama ciki bakinta ɗauke da sallama. Aunty Rahma dake fitowa daga kitchen Junainah na biye da ita da sauri ta ɗan juyo ta kalli Dedde tare da cewa. "Wa alaikassalam". Ta ƙarashe amsa sallamar tana matsowa dan ganin wani irin fitinenne kama da Dedde keyi da Shatu. Da sauri ta juyo bayanta jin Junainah na cewa. "Lah Oyoyo Dedde". Dai-dai lokacin kuma Ummey ta ƙarasa shigowa ciki wanda hakan yayi dai-dai da bugawar da kanta yayi wanda saida tayi sauri sa hannunta duka y ta damƙe kanta da masifan karfi tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun". Da ƙarfi wanda haka yasa Dedde juyowa ta fuskanceta sanadin juyawar da Dedde tayi kuma ya bawa Aunty Rahma da Junainah damar ganin fuskar Ummey da kyau. Wani irin sauri Junainah tayi ta nufi inda suke ganin yadda gaba ɗaya jikin Ummeynta yake karkarwa da tsuma. Aunty Rahma kuwa cikin wani irin tsananin firgita da kaɗuwa ta zazzaro idanunta waje har kamar zasu faɗo. Wani irin taku mai cike da firgici tayi tana matsowa gaban Ummey dake jujjuyawa tana mai-mai-ta. "Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil". Wani irin matsowa kusa da ita Aunty Rahma tayi tare da buɗe baki da ƙarfi tace. "La ha ila ha illahu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallama. Aunty Mamey!." Ta ƙarashe kiran da azaban ƙarfi da rakaɗi. Ummey kuwa. Kiranta da Aunty Rahma tayi yasata ƙara gigicewa. Karkar haka jikinta ke rawa. Cikin wani irin gigitaccen murya Aunty Rahma ta fara rabkawa ahlinta kira. "Umaymah! Mamma Jazlaan ga Aunty Mamey ta dawo da izinin ubangiji Jazlaan, Jafar, Jalal, Jamil, Umaymah. Kuzo ga Aunty Mamey...". Wani irin azabebben zabura...! Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k ne kacal zaki turo ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Normal group Kuma 300 zaki turo ta asusuna ɗin sai kuyi screenshort na Debit Alert din ku turo min ta whatsApp 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* [4/2, 7:40 AM] +234 806 559 0880: Cikin tarin kaɗuwa Umaymah, Mamma, Ummi, suka kalli juna tare da yunƙura suka tashi a tare. Sabida jin kalmar da Aunty Rahma ke mai-maita wa, da tsananin ƙarfi da karaɗi. A guje suka nufo falon sabida jin yadda take ƙara auna musu kira babu ƙaƙƙautawa. Jalal da Yah Jafar da Aunty Juwairiyya dake Part ɗin su kuwa, suma da ƙarfi suku mimmiƙe tsaye, tare da juyowa suka nufo Part ɗin Sheykhhhh. Dedde kuwa da sauri ta matso kusa da Ummey da nufin sa hannunta ta tallabeta, cike da al'hini al'amarin. Junainah kuwa da gudu ta iso gareta tare da da faɗa wa jikinta ta ruggume sawunta tare da sakin kuka da ƙarfi sabida ganin yadda gaba ɗaya jikinta ke karkarwar. Sheykh kuwa da Shatu kafin kiran Aunty Rahma tayi mgnarta ta forko ruggume da ita yayi da kyau tare da cewa. "Uhmmm kin san ko wanni sirri nawa, har na aikina da yake sirri amman ni kin gaza fitowa fili ki nuna min waye Bappa a wurinki waye Abboi a gareki". Hannun tasa ta ɗan shafa sajenshi ta buɗe baki da nufin yin mgn kenan suka tsinkayo. Muryar Aunty Rahma. Wani irin tsinkewa da bugawa zuciyar Sheykh tayi da masifar ƙarfi wanda hakan ya haddasa wata iriyar fitinenneyar karkarwar zuciya da jiki, da ƙarfi ya sake rumtse idanunshi tare da sa yatsunshi cikin kunnuwanshi ya jijjiga sabida jin abin yakeyi kamar gizo. Junainah kuwa wani irin masifeffen kuka tasa mai cike da rauni tare da yayyarfa hannunta murya a hargitse tace. "Wayyo Adda Shatu! Adda Shatu zo kiga Ummeyn mu bata da lfy Adda Shatuuuu". Tayi kiran da masifan ƙarfin. Ganin yadda Ummeyn ta tureta tare da jujjuyawa a tsakiyar falon kamar irin wacce hajijiya ke juyawa haka take tafiya tangal-tangal. Wani irin zabura Shatu tayi wanda yayi dai-dai da lokacin da Mamma da Umaymah da Ummi da suka fito yanzu suka haɗa baki wurin cewa. "La ha ila ha illahu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallam". Sai kuma gaba ɗaya jikinsu ya saki wani irin masifeffen karkarwa da sakewa ya rufesu. Suka kasa koda ɗaga sawunsu bare su matsa inda suke. Sabida tsananin kaɗuwa. Ita kuwa Shatu tsalle ɗaya tayi ana biyu sai gata a bakin ƙofar Bedroom ɗinsa. Cikin gigita shima ya yunƙuro da ƙarfi ya mara mata baya, sabida yadda yake jiyo falon a hargitse. Gudu ya farayi ganin yadda Shatu ta fice a guje sabida ihun Junainah da take jiyowa. Da sauri Yah Al'ameen ya sako kansa cikin falon jin muryar Junainah da abinda take cewa. Yah Jafar da Jalal da Aunty Juwairiyya na biye dashi a baya. Cikin matsanancin tashin hankali Shatu ke kallon Ummey dake tsaye acikin tsakiyar falon, tana me riƙe da kanta dake juya mata sosai, ko mai bibbiyu take ganinsa, hakan yasa numfashinta soma ƙoƙarin ɗaukewa, take kuma idanunta suka rufe rub, hakan yasa ta-ta-fi luuu zata faɗi. Da wani irin sauri mai haɗe da gudu Shatu da hankalinta yakai ƙololuwa wajen tashi ta ƙarasa wajen da Ummeynta ke tsaye, hakanne kuma yasa Ummeyn ta faɗa jikinta. Hannayenta duka biyu tasa ta rungume Ummeyn tare da fara jinjigata cikin kiɗima da gigita, cikin muryar kukan da yazo mata lokaci ɗaya ta shiga faɗin. “Innalillahi Wa’inna ilahirraju’un. Ummeyna Ummeyna maiya sameki? Ummey ki tashi dan Allah, ki buɗe idanunki!!!”. Ta ƙare maganar nata cikin matsanancin kuka, tare kuma da sanya hannayenta ta shiga girgiza Ummeyn da ƙarfi. Sheykh kuwa dake tsaye ganin fuskar matar da Shatu’n nasa ke kira da sunan Ummey ne yasa shi, jin wani irin abu ya daki zuciyarsa da ƙarfi, wanda hakan yasanya shi jin ƙafafunsa sunyi masa nauyi, lokaci ɗaya kuma wani irin rauni ya cika zuciyarsa, wanda har hakan yasa yaji wasu irin ƙwalla masu ƙuna suka bayyana acikin idanunsa. Ahankali ya ɗan soma taka ƙafafunsa tare da ƙarasawa wajen da Shatu da kuma Ummey'n suke. Durƙusa guiwowinsa yayi aƙasa a dai-dai lokacin daya iso wajen da suke, cikin wani irin yanayin dake fusgansa, ya shiga ambaton sunan Allah, a dai-dai lokacin daya sanya duka hannayensa biyu ya rungumo Shatu da kuma Ummey’n jikinsa. Cikin wata irin sassanyar muryarsa wanda amo da kuma sautinta baya bayyana ya shiga faɗin. “Subahanallah!. Alhamdulillah!! Hasbunallahu wani’imal wakil, innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un, la haula wala k’uwwata illa billahil aliyil azim!!” Sune tasbihan da yaketa mai-mai-tawa Shatu dake kuka kuwa jin ya sakasu ajikinsa ne, yasa ta ɗago jajayen idanunta dake tsiyayar da hawaye, cikin matsanancin damuwa da kuma ruɗewa haɗi da tashin hankalin da ta samu kanta aciki tace. “Hamma Jabeer Ummeyna bata numfashi. Dan Allah kace ta-tashi, kace ta buɗe idanunta, banason wani abu ya samu Ummey na, ka taimakamin, wayyo Dedde na Umaymah kuzo Ummeyna ...” Kasa ƙarasa maganar nata tayi, saboda sosai kuka yaci ƙarfinta, sai-dai kuma amma duk da haka bata daina jijjiga Ummeyn nata ba. Su Yah Jafar Jalal Ummi Mamma Aunty Juwairiyya Aunty Rahma Khadiya Aunty Amina Ishma, Hafsi Yah Al'ameen kuwa gaba ɗayansu zobe sukayi musu, cike da tarin al'ajabi al'hini kaɗuwa da tarin farin ciki. Junainah kuwa da ta ƙara ruɗewa saboda ganin kukan da Shatu keyi, ƙarasowa jikin Shatu’n tayi ta raɓa jikinta, cikin muryar kuka take cewa. “Adda Shatu Ummeynmu. Adda Shatu Ummyen kice ta tashu mukaita asibiti kada wani abu ya sameta!”. Sauran jama'ar kuwa. Kowannensu fuskarsa ɗauke da hawaye suka ƙaraso garisu sosai kusa dasu Shatu, Sheykh, da Ummey’n suke. Sautin kukan Aunty Rahma ne mai nuna tsantsar farin ciki da na Umaymah da Mamma ne suka fito fili, a dai-dai lokacin da sukayiwa Ummey’n zobe, Kowannensu kuka yake, sai-dai kallo daya zakayiwa kukan nasu ka fahimci cewar ba kukan baƙin ciki bane kukane na tsantsar farin cikin da yiwa Allah godiya, domin kuwa acikin muryar kukan nasu suke ambaton sunan Allah, suna me faɗin. “Alhamdulillah! Alhamdulillah ya Allah!! Alhamdulillahil lazi bi ni’imati hi ala tatimussalihat!!!” Umaymah kuwa da matsanancin farin cikin mara misaltuwa da take jin kanta aciki ya kasa ɓuya, durƙushewa tayi bisa guiwowinta tare da kifa goshinta aƙasa tayi Soujjadar nuna, matsanancin godia ga Allah daya dawo mata da ƴar uwarta. Ummey kuwa wani irin Numfarfashi taja sai gata a sume. Dai-dai lokacin kuma Jamil da jiyo hayaniyarsu ya sashi tahowa a guje, ganinsu cike a falon kowa fuska cike da hawaye kuma sai kalmar Alhamdulillah suke maimaitawa. Duk sun kasa bin ta kan kalaman Shatu. Ganin Jamil ne yasata mgn cikin rauni tace. "Jamil dan Allah taimaka min Ummey na ta suma". Jin hakane yasa ba tare da ya iso inda sukeba ya nufi kitchen da sauri mai kama da gudu ruwa ya ɗebo kana ya dawo. Yana isowa gab dasu, ya zaro idonsa baki ɗaya murya can sama yace. "Mammeyyyyy". Sai ga ruwan ya kwaɓe a hannunshi shima ya faɗi bisa jikin Yah Jafar a sume. Gaba ɗaya sun gaza cewa komai sai ambaton Allah. Da gudu Affan da tun jiya daya dawo dasu Giɗi bai gana da Hamman nasu ba sai yanzu ya nufo Part ɗin. Jin ƙaran muryar Jamil ne ya sashi shigowa falon da sauri yana cewa. "Me haka Jamil lfyarka kuwa?". Turus yayi a bakin ƙofar ganin duk suna cike a falon sun taru wuri ɗaya kowa da irin addu'ar da yakeyi. Cikin tsaro da fargabar kardai wani abune ya samesu ya nufosu. Cikin kaɗuwa yace. "Mamey". Ya kira sunanta da ƙarfi lokacin da idanunshi suka sauƙa bisa fuskar Ummey. Jiki na rawa ya juyo ya kalli Sheykh dake mgn cikin rawan murya da rauni yake cewa. "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Yah Allah na gode maka bisa wannan rahama da kaimin ko yau ka ɗauki raina burina ya cika, yau gani ga Mameyna a cikin masarautar Joɗa a suffar mutun bani Adam ba tsuntsuwar Boleru ba". Wani irin kuka ne mai rauni ya kwabce mishi. Yah Jafar ma kuka yakeyi tare da cewa. "Alhamdulillah al'ƙadarin Magauta ya karye". Ummi kuwa da rarrafe ta rusuna gaban Ummey tare dayin ƙasa da kanta cikin rauni tace. "Barka da dawowa Adalar Uwar gijiyata". Umaymah kuwa da sauri ta jawo wayar da ta gani kusa da ita. Saida ta danna sai taga ashema wayar Hibba ce da ta bawa Junainah nayi Game. Jadda ta dannawa kira. Yana ɗagawa tace. "Assalamu alaikum Alhamdulillah Allahu Akbar Jadda! Jadda!! Jadda!!!". Cike da kaɗuwa Jadda dake kishinƙiɗe ya miƙe zaune tare da kallon Sitti dake yanka mishi lemu wanda tana iya jiyo abinda Umaymah ke faɗa sabida yadda take mgn da ƙarfi. Wani irin dogon numfashi suka sauƙe a tare jin Umaymah na cewa. "Alhamdulillah Jadda Aunty Mamey ta dawo Jadda zatonmu da tsammanin mu ya zama gsky Aunty Mameyna ta dawo gata gabanbu Jadda kace Alhamdulillah". A tare Jadda da Sitti suka fara maimaita kalmar hamdala. Affan kuwa cikin wani irin sauri ya juya a guje tamkar ƙaramin yaro ya nufi Part ɗin Abbansu. Yana shiga da gudu yana mai cewa. "Abba Abbanmu Abbana Mamey Mamey". Da sauri Gimbiya Samira amaryar Abban ta fito tare da cewa. "Affan lfy kuwa Abbanku yana fada". Ai bai kuma bin ta kanta ba ya fito. Kiciɓis yayi da Hajia Mama tana cewa. "Kai lfy kuwa kake gudu kamar yaro?". Ba tare da ya tsaya ba yace. "Abba nake nema ina yaje Mamye." Daga nan ya nufi fada. Ita kuwa Hajia Mama cikin wani irin masifeffen tsinkewar zuciya da fargaban jin sunan da bata ko son jin an kira ta juya ta nufi ɗakinta. A can fada kuwa bayan sarkin ƙofa yayiwa su Bappa iso cikin ƙaton falon. Abboi na gaba Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro suna biye dashi a baya kana sai masu tsaronshi da suka tsaya can bakin ƙofar shiga sabida dakatar dasu da yayi. Suna shigowa Lamiɗo dake fuskantar Kofar shiga fuska cike da annuri da haiba yace. "A a a Masha Allah lalle marhabin da Alhaji Abbo lale da zuwa masarautar Joɗa Fulle bandu fullo". Da sauri Wambai, Dirankadi, Ɗan isa, Ɗan buram, Sarkin fada, Ɗan kade, Galadima Ɗan maliki Chiroma Durbi Ma'aji. Duk suka miƙe tsaye cikin tsananin sakin fuska da alamun sanayya na mutuntaka suka kalli Abboi tare da haɗa baki wurin cewa. "Marhababika da zuwa masarautar Joɗa". Sai kuma ɗan zagi ya fara baza rigarsa tare da cewa. "Sarki ya gaisheka. Sarki yace ayi maka sannu da zuwa fullo Nbandu fullo manyan fada na farin ciki da zuwa ka". Wani irin murmushi Abboi yakeyi mai cike da kamala ya nufi gaban Lamiɗo. Har kusa dashi ya isa kana ya rusuna, yayinda Bappa da sauran ke biye dashi a baya. A hankali ya sunkuyar da kanshi tare da ture hularshi yayi baya da ita. Cikin alamun shaƙuwa Lamiɗo yasa hannunsa tsakiyar kansa tare da cewa. "Allah yayi muku al'barka". Murmushi Abboi yayi tare da cewa. "Amin ya Allah Baba". Sabida Lamiɗo yasan Abboi a matsayin ɗansa yake zuwa gareshi yana jin daɗin abokin mahaifin nashi ya sanya mishi albarka". A hankali ya koma ya zauna ya tanƙwashe sawunshi tare da cewa. "Barka da hatsi". "Barka dai". Lamiɗo yace. Abba dake gefenshi ne ya kalli Abboi tare da bashi hannu suka gaisa. Sarkin fada kuwa da sauri ya fito ya umarci hadimai maza da su kawowa baƙin abin taɓawa ai kuwa nan da nan aka cika gabansu Abboi da abubuwan ci da na sha. Cikin tarin kula Lamiɗo ya kalli Bappa tare da cewa. "A a Malam liman tafe kuke tare da shine?". Cikin nitsuwa Bappa yace. "Na'am tare muke". Kai Lamiɗo ya jinjina tare da kallon Abboi gyara zama Abboi yayi fahimtar tambayarsa Lamiɗo yayi a hankali yace. "Ai mutumin ƙasar mu ne zamane da wani babban dalili ya dawo dashi nan ƙasar ku". Cikin gamsuwa Lamiɗo yace. "Makiyayinka ne shi?". Cikin mutuntaka da kunya Abboi yayi shiru dan shi Bappa yafi ƙarfin makiyayinsa a wurinsa Bappa ɗan uwane". Cikin yin murmushi Bappa yace. "Eh ni ɗaya daga cikin makiyayansa ne". Yayi mgnar sabida fahimtar Abboi bazaice hakanba. Sai kuma suka sake wani sabon gaisuwa. Nan Babba ke cewa. "Tare muke da mai ɗauki shi da kuma ƙanwata sunzo ganin jikar tamu su sun isa can". Cikin tarin jin daɗi Galadima yace. "Masha Allah, Allah ya bada ladan ziyara". Amin Amin duk suka amsa. Dai-dai lokacin kuma Affan yasa hannunshi ya ture sarkin ƙofa dake tareshi yana cewa. "Lamiɗo yana ganawa da manyan baƙi". Cikin haki da ɗaga murya yace. "Kai da Allah bani wuri. Abbana nake nema Abba! Lamiɗo!". Yayi mgnar da ƙarfi tare da kutsa kai cikin falon. A tare suka juyo suka zuba mishi ido Abba kuwa da sauri ya miƙa tare da cewa. "Na'am Affan meya faru?". Cikin haki yace. "Abba Mamey Lamiɗo Mamey'nmu ta dawo wlh Mamey ta dawo gata can a Part ɗin Hamma Jabeer su Umaymah nata kuwa Mameynmu ta dawo a mutun ba tsuntsuwar Boleru ba". Kusan a tare gaba ɗayansu suka miƙe banda Lamiɗo dasu Abboi tare da cewa. "Kai Affan nitsu ka gaya mana". Cikin kaɗuwa ya kamo hannun Abban nasu tare da cewa. "Zo muje ka gani wlh Mamey na ta dawo a mutun ba tsuntsuwar Boleru ba". Ai kafin ma ya rufe baki Abba ya juya da sauri yabi bayan Abbanshi. Abboi kuwa da Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro kallon juna sukayi tare da yin murmushin zatonsu ya tabbata jinjinawa juna kai sukayi Sai kuma Bappa yace. "Ya ilahi meke faruwa?". Cikin yin Murmushi Lamiɗo yace. "An tashi taron fada sai gobe". Nan take duk sauran suka miƙe suka fita kowa ya nufi muhalli sa cike da alhini. Shi kuwa Lamiɗo Galadima ya kalla tare da cewa. "Muje gidan Jabeer ɗin Kuma taso muje ƙofar surkin naku". Yayi mgnar da yaƙini a ransa su Bappa ne ke tafe da abinda suka daɗe suna tsumayin wato dawowar Mamey (Ummey) kenen. Ai kuwa da sauri su Bappa suka bi bayansu. Fadawa na musu rakiya. Ɗan zagi na baza riga da cewa. "Gyara kimtsi, sarki ya gaisheku". A haka suka nufi Part ɗin Sheykhhhh. Kusan a tare suka isa dasu Abba dan rawan da jikinsa keyi ya hana masa yin sauri. Lokacin ɗaya kuma duk masararutar Joɗa ta cika da lbrin dawowar Mamey kamar yadda labarin juyewarta da bacewarta ya karaɗe ko ina na Masarautar Joɗa. Suna shiga Affan yaja hannun Abbansu har gaban Shatu da Sheykh wanda ke ruggume da Ummey har yanzu a sume. Sun kasa taɓuka komai, duk da shi dai Sheykh ya gane a sumen take. Cikin haki Affan yace. "Gata Abba ka gani ga Mameynmu". Wani irin farin ciki ne mai masifar yawa dake shirin ɗauke masa numfashin sa ne ya sauƙo mishi, jin hakane yasa yayi sauri ya sunkuya a tsakiyar falon ya fuskanci al'ƙibla ya faɗi yayi sujjada gaban Ubangijin talikai sarki buwayi gagara misali. Dai-dai lokacin su Lamiɗo suka shigo. Ganin Bappa ne yasa kukan Shatu tsananta murya na rawa tace. "Bappa Ummey na Bappa Ummey na". Da sauri irin na sarakuna su Lamiɗo suka ƙara so wurin. "La ha ila ha illalalhu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallam". Suka faɗa a baki a haɗe tare da zama bisa kujera. Cikin sanyi Bappa ya kalli Shatu kana a hankali ya juyo yankallesu gaba ɗaya hawayene cikin a fuskarsu. Ga Jamil a sume. Galadima kuwa da Lamiɗo murmushi sukeyi tare da maimaita ƙalmar hamdala". Da sauri Junainah tazo ta faɗa jikin Bappa tare da sakin kuka tace. "Bappa Ummey na ta rasu ne?". Da sauri ya jujjuya kanshi tare da juyowa ya kalli Khadijah ƙanwar Shatu cikin sanyi yace. "Khadijah in akwai zam-zam a gidan kawo min in kuma babu bani ruwan sanyi". Da sauri Ummi ta miƙe kitchen ta nufa tana mai cewa. "Akwai zam-zam bari in kawo". To kawai yace mata. Abba kuwa a hankali ya ɗago kanshi kana ya jingina bayanshi da sawun Lamiɗo ya kife kanshi bisa guiwar Lamiɗo sai ga wani kuka mai rauni ya subce mishi. Da sauri Bappa ya amshi goran zam-zam mai sanyin. Matsowa yayi kusa da Shatu. Da sauri ya buɗe goran zam-zam ɗin ya tsiyayi sassanyan ruwan a tafin hannunsa, kana ya saita fuskarta tare da cewa. "BISMILLAHI". Ya watsa mata shi a fuska da ƙarfi tare da sunan Allah. Shiru babu motsi da sauri ya sake tsiyayo wani ya watsa mata tare da bismillah. Stiil ba motsi da ƙarfi ya kuma watsa mata a karo na uku. Da ƙarfi taja wani irin nannauyan numfashin mai tsawo tare da cewa. "La'ilahaillaha Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam. Astagafirullaha wa'atubu illaik". Kusan a tare gaba ɗayansu falon suke furta Alhamdulillah. Cikin wani irin yanayi Jabeer, Jafar, Jalal, da Jamil wanda Bappa ya watsa mishi ruwan ya farfaɗo a firgice suka matso gabanta sukayi mata zobe. Kana Umaymah da Mamma da Aunty Rahma suna kusa dasu. Cikin wata iriyar murya mai raunin amo Sheykh ya kamo hannunta murya na rawa yace. "M...mah..Mam.. Mameyyy". Da sauri ta ɗago jajayen idanunta da tsananin ciwon kai ya rinasu ta watsa masa su cikin nashi ba tare da ta amsaba. Cikin rauni ya kuma cewa. "Mamey Mamey na Jabeer ɗinki ne! Mamey kin manceni ne, gani Ga Yah Jafar ɗina ga sakalallun tagwayenki ga Affan ɗinki ɗan lelenki ga Abba na Ga ƴan uwanki Umaymahna ga Mamma na ga autar Sitti Aunty Rahma Mamey Jabeer ɗinkin ne ga Ummi amintacciyar jakadiyarki mai riƙon amana". Shiru sukayi baki ɗayansu suka zuba mata idanu. Ita kuwa ido ta lumshe wasu hawaye masu ɗumi suka zubo mata cikin raunin murya tace. "Alhamdulillah Jabeer na tunoku gaba ɗayanku". Wani irin farin cikin ne mai tarin yawa ya cika musu zuƙatansu baki ɗayansu. Da sauri suka juyo suka kalli Bappa da yake cewa. "Alhamdulillah baiwar Allah ta tuno baya ta gane ƴaƴanta da ƴan uwanta". Da sauri Sheykh ya juyo tare da kamo hannun Shatu wacce cikin kuka da rarrafe ta matso gaban Ummey da kyau murya na rawa hawaye na zuba tace. "Innalillahi shike nan Ummey ta tuna baya kenan Bappa zata mantani kenan?". Wani numfashin Ummey taja tare da zubda hawaye. Ita kuwa Shatu kamo hannun Junainah tayi cikin rawan murya hawaye na kwarya tace. "Ummey ki kalleni Ummey nice Shatunki fa Ummey koda zaki tuna baya kada ki manceni Ummey kalleni fa nice Shatunki kalli Junainah'nki ƴar autarmu Ummey koda zaki manceni dan Allah kada ki mance Junainah ke kika haifeta a cikinku muka reneta bata san kowa ba sai nudake". Wani irin kuka ta saki mai ƙarfi tare da jawo Junainah da itama kukan takeyi juyowa tayi ta kalli Yah Sheykh cikin rawan murya tace. "Ummey nane fa da tun inada shekaru takwas a duniya na bar gaban Dedde na da Abboi na na dawo gabanta ita ta raineni kamar Uwa itace ta haifi Junainah itace ta bamu tarbiya sanadinta muka baro ƙasar Cameroon muka dawo Nigeria muka zauna Rugar Bani wayyoooooooo Allah na Ummeyna kada ki manceni". Shirun da Ummey tayi yasa gaba ɗaya tausayin Shatu da Junainah yasa kowa zubda hawaye sabida fargabar kada fa ya zamo ta tuno baya can ta mance yanzu. Kuka sukeyi baki ɗayansu hatta Afreeen dake hannun Aunty Amina kuka takeyi. Cikin rawan murya Shatu ta kamo hannun Ummey ɗaya Junainah kuwa ta kwantar da kanta bisa cinyar Ummeynta a tare suka haɗa baki wurin cewa. "Ummey kin mance mune?". Da sauri Shatu ta saki wani irin kuka tare da faɗawa jikin Ummey jin tace. "Ban mance kuba Boɗɗo na Autata". Murmushi sukayi baki ɗayansu falon ita kuwa Shatu da Junainah kukan farin ciki sukeyi. A hankali Bappa yasa tafin hannunshi ya share hawayensa dake gangarowa hakama Abboi sai suke tuno kamar yau suka samu ɓoleru'n nan. A cikin masarautar Joɗa kuwa gaba ɗaya labarin dawowar Mamey ya riski kunnuwan mutanen cikinta da kewaye. Cikin wani irin mamaki Gimbiya Saudatu ta miƙe tsaye tare da kallon Babba Basiru daya kawo mata lbrin cike da kaɗuwa tace. "Kai Basiru muje mu gani". Ai kuwa da sauri suka juyo suka nufi Part ɗin Sheykhhhh. Yayinda Babban ɗan ta Yah Hashim da Laminu mai binshi suka mara mata baya. Gimbiya Samira ma amaryar Abban da Mom mai bin Mamey da sauri suka nufi Part ɗin Sheykhhhh ɗin. Gimbiya Aminatu da Matar Galadima ma jiki na rawa suka nufi can. Hajia Mama kuwa wani irin ihu tayi tare da rugawa a guje ta nufi Part ɗin Sheykhhhh a gigice. Baba Kamal da ɗansa Sulaiman da sauri suka nufi can. Dr Aliyu ma da matarsa da ƴarsa Rahima da sauri suka nufi can. A cikin falon kuwa da sauri Shatu ta amshi gorar zam-zam ɗin da Bappa ke miƙa mata, ta sawa Ummey ita a baki. Sosai tasha kana ta janye goran. Da sauri ta miƙowa Aunty Amina hannu alamun ta bata Afreen miƙo mata ita tayi. Ita kuwa amsa tayi kana ta miƙa wa Ummey ita tare da cewa. "Ummey sa mata al'barka tunda kece kaka mahaifiyar uba da mai renon Uwa sai ki bawa Dedde na ita tasa mata al'barka itama". Murmushi Ummey tayi tare da amsarta sai kuma ta kalli Sheykh tare da cewa. "Jabeer na ya girma". Murmushi dake baiyana tsantsar jin daɗi sukayi. Nan suka ɗanyi shiru jin Lamiɗo yayi gyaran murya tare da cewa. "To Alhamdulillah wannan shi ake cewa ƙudurar Ubangiji babu bawan daya isa kaudashi. Sai kuma ya kalli Bappa da tare da cewa. "Dan Allah malam Liman bani lbrin yadda akayi Aisha ta kasance tare daku da kuma sanadin haɗuwarku da samun lfyarta?". Cikin sanyi Bappa yace. "Bazamu bari ta hutaba tukun?". Da sauri Ummey ta jujjuya kai tare da cewa. "A a Bappa gaya musu kawai domin nasan gaba ɗayansu wannan tambayarce a ransu. Duk da zanso inji ya lbrin Jaddana da Sittina naga kowa sune ban ganiba". Cikin sauri Umaymah tace. "Aunty Mamey Jaddanmu da Sittinmu suna lfy suna gab da tasowa zuwa nan suma". Cikin tarin farin ciki tace. "Alhamdulillah to Bappa gaya musu ko ince gaya mana meya faru?." Shiru Bappa yayi sai kuma ya kalli Umaymah dake cewa. "Dan Allah gaya mana a wacce suppar ka samu yar uwata a wani yankin". Cikin nitsuwa Bappa ya gyara zamanshi kana ya ɗan yi gyaran murya a hankali yace. "Ranar wata jumma'a data gabata tsawon shekaru goma sha uku a can ƙasar Cameroon a yanki dake gefen babban birnin Yahunde cikin Rugar Arɗo Babayo...! Da sauri suka juyo suna kallon bakin ƙofar shigowa sabida jiyo muryar Hajia Mama daga nesa tana cewa. "Zancen banza zancen wofi kenan ta yayama za'ayi ta dawo mutun har ta dawo nan cikin masarautar Joɗa". Ta ƙarashe mgnar da ƙarfi tare da banko ƙofar ta shigo a fijajan. Yayinda duk sauran tawagar masarautar Joɗa ke biye da ita a baya. Tana shigowa tayi wani irin zabura tare da zaro idanunta gaba ɗaya sai kuma tayi kan Ummey da gudu. Da sauri Shatu ta miƙe ta tsaya gaban Ummey tare da cewa. "Da dakuka cutar da ita kuka fitar da ita haiyacinta da halittar ta a zatonku a haka zata tabbatane?". Da sauri Sheykh yasa hannunshi ya kamo na Shatu yajata ya zaunar da ita. Ita kuwa Ummey idanu ta zubawa Hajia Mama tamkar zata manna matasu a jikinta sai jujjuya kai takeyi. Ita kuwa Hajia Mama ganin idon Ummey cikin natane yasa duk wani sihirinta ya dawowa jikinta kamar yadda Ba'ana yace musu zai bawa Ummey mgnin ƙaiƙayi koma kan masheƙiya duk randa tayi Ido biyu da wacce tai mata sihirin zai dawo jikinta. Bayan kwanaki biyar zata koma tsuntsuwar Boleru kamar yadda sukayi mata. A lokacin Bappa yaƙi shi dai yace ta samu lfy ta fara mgn amman da gaiya Ba'ana ya bata wannan mgnin sabida zalumcin da akayi mata ya tsananta. Cikin wani irin gigita Hajia Mama ta kai hannunta ta taɓa fuskar Ummey tare da cewa. "Kika dawo mutum kenan bokana yamin ƙarya yace min har abadan yadda matacce bazai dawo duniyaba haka bazaki dawo mutunba bazaki taɓa dawowa Masarautar Joɗa ba." Sai kuma ta kai hannu ta bugi gefen bayanta ta sosa tare da karkata baki kana tasa hannun ta ɗaya ta cire ɗan kwalin kanta ta cillashi gefe tare da cewa. "Shigayar balarabiya mai nacin tsiya ki aure min miji ki haife mishi zaratan maza harda tagwaye kana ace cikin ƴaƴan ki za'a samu mai gadar mulkin Masarautar Joɗa ai wlh bazata saɓuba". Sai kuma ta fara yatsuma gashin kanta tare da kurma ihu. Cikin wani irin yanayi mai cike da rauni kunya tashin hankali kiɗima gigita. Affan ya kife kansa da jikin sawun Sheykh ya saki wani irin kunyataccen kuka mai cin rai tare da cewa. "Innalillahi wa innailaihi rajiun Hamma Jabeer wanne yanayi ne wannan Hajia Mama take ciki wannan wanne ranane mai cike da kunya Allah ya zai nuna min". Da sauri suka juyo suna kallon Baba Kamal da yake fifita da hularshi tare da kecewa da dariya yace. "Hahaha ta haukace ta haukace na haukace, zasu haukace duk zamu haukace. Shegiya muguwar babarbariya ba ke kikayi mata sihiri ta zama tsuntsuwar Boleru ba kika haukata Jafar ba kika sawa Jamil bin mata Jalal bin mutanen banza bw". Da sauri ta juyo cikin wani irin rawa-rawan haka na sakayyar mugun aikinta tace. "Tafi daga nan mugun bafulatanin kai kuma ai kai ne kayi mishi ashirin kashe mishi lfyarsa dan kada yayi aure bare ya haihu kana zaton bansan duk abinda kakeyi bane". Sai kuma duk suka kece da dariyar hauka tare da faɗi ƙasa sunayi harda tafa hannunsu. Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil waɗannan sune kalaman da gaba ɗaya mutanen falon sukeyi sabida fahimtar sakayyace ta riskesu tun a duniya. Baba Basiru ne ya matso kusa da Baba Kamal tare da cewa. "Mugu bashi da kama Kamal kaida Hajia Mama tabbas kun cika mugaye masu cikekkiyar manufa wanda har kuka iya ɓoye muguntarku." Su dai su Sheykh Umaymah Shatu Lamiɗo Abba Bappa gaba ɗaya zuba sarautar Allah ido sukayi. Affan kuwa kukane mai cin rai yakeyi cike da kunyar abinda mahaifiyarshi ta aikata. Shi kuwa Baba Basiru a hankali ya matso gaban Gimbiya Saudatu daketa zazzare idanunta cike da mamakin jin tsantsar muguntar mutanen da kullum take faɗa dasu a zatonta masoyan Sheykh ne. A hankali ya kalleta kana yace. "Jabeer yau dai ka yarda ka gamsu da abinda nake ce maka ko". Cikin yanayi gamsuwa Jabeer ya kalli Baba Basiru wanda mutane ke zato maƙiyinshine har Gimbiya Saudatu ta haɗe dashi bata san cewa ƙididdigarta yakeyi ba. Shi kuwa Baba Basiru a nitse yace. "Dama na gaya maka Gimbiya Saudatu sha giri girbauce wautace kawai ke damunta da ƴar hasada, sannan kuma da zugan wannan maƙiyin nata". Yayi mgnar yana nuna Baba Nasiru wanda ita a zatonta masoyi ta ne. Cikin gyara tsayuwarshi ya kalleta kana ya kalli shi Baba Nasiru daketa karkarwa cikin zubda hawaye yace. "Ke Gimbiya Saudatu kullum Nasiru na ingizaki da zugaki da cewa Gimbiya Aisha da ɗan ta Jafar ne suka kashe miki mijinki babban yayanmu Yah Aumalu mahaifinsu Hashim da Laminu wan dan Jafar ya gaji sarautar Galadima ko?". Da sauri ta gyaɗa kanta. Yayinda suma duk saura suka zuba mishi ido. Cikin zubda hawaye yace. "Toh kinga Yah Nasiru ɗan uwanmu uwa ɗaya uba ɗaya shine ya kashe miki mijinki uban ƴaƴanki sannan yanke ingizaki kan su Sheykh da mahaifiyarsu yasa miki tsanarsu kiketa haushi a kansu kamar karya. Ita wannan muguwar kuwa Hajia Mama da Kamal da Hashim ɗanki da kuke gani kamar yana son Jabeer alhalin ya tsaneshi shi kuwa wai dan Lamiɗo yafi janshi a jikinshi. Duk sai suka fake a bayanki sunayiwa Sheykh da ahlinsa mugunta yayinda kowani sai yayi zargin kece kinga kin zama bushiya kamar yadda Shatu ta faɗa a zahiri in anganki jiki duk ƙaya amman cikin bushiya namansa ma maganine su kuma suka kasance belbela siffarsa fara cikinta baƙiƙƙirin". Cikin rauni Gimbiya Saudatu tace. "Innalillahi wallahi ni dai Allah ya sani ko garin marke ban taɓa nemowa da niyar cutar dasuba.. Yanzu ashe Hashim kaima muguwar zuciya gareka ban saniba har zaka iya cutar da ɗan uwanka." Ina Affan kam tuni yake kuka tamkar zai shiɗe dan baƙin ciki da takaicin abinda uwarsa ta aikata. Yah Jafar ne ya gyara zamanshi tare da cewa. "Tabbas kuwa Hajia Mama da Baba Kamal da Baba Nasiru da Hashim sune manyan Magautan mu". Da sauri Sheykh ya miƙa tare da kamo hannun Hajia Mama da taketa son kwaɓe kayanta. Da sauri ya nufi Side ɗinsa. A wannan ɗaya ɗakin yasata ya rufeta bayan yayi mata allurar bacci. Kana ya fito. Nan ya samu Lamiɗo yasa Fadawan shi sun fita da Baba Kamal dake ta ihun hauka. Sannan Jalal kuma ya miƙa ya damƙi Baba Nasiru dake son guduwa. Ya miƙashi hannun abokanshi sojojin daya kira bisa laifin kisan kai. Shi kuwa Yah Sheykh a hankali ya kalli Yah Hashim a hankali yace. "Ashe harda kai a cikin magautana Yah Hashim. Kai lallai ɗan Adam darene babu mai saninsa sai Allah". Lamiɗo ne ya kamo hannunshi ya zaunar dashi kana yace. "Kai Hashim fice mana daga nan bama buƙatar mai muguwar zuciya ko ɗaya a nan". Ai kuwa da gudu ya fice cike da kunya. Shi kuwa Lamiɗo gyara zamanshi yayi tare da cewa. "Jafar bamu lbrin meya faru da kai da mahaifiyarku a dare ɗaya ta sauya halitta daga mutun zuwa tsuntsuwar Boleru kai kuma ka dena mgn". Gyara zamansu sukayi baki ɗayansu dan wannan itace tambayar da take cinsu a rai tsawon shekaru goma sha uku kenan gaba ɗayansu. Cikin gyara zamanshi ya ya fuskancesu kana a hankali yace. "A ranar...! Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 babbancinsu a posting ne 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Ta wannan ac no zaku tura kuɗin sai kiyi screenshort na Debit Alert ɗin ki turo min shaidar biyan ki ta whatsApp 09097853276 ku yan 300 in baku da damar biya ta Account zaki iya sayan katin mtn na ɗari uku kacal sai ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* [4/2, 7:41 AM] +234 806 559 0880: "Aranar wata jumma da da wanna Zazzafar ƙaddara ta rufta damu shekaru goma sha uku baya." Sai kuma ya ɗan tsakaita tare da jan sassayan numfashi ya gyara zamansa tare dasa tafin hannunshi ya share hawayensa. Yayin da gaba ɗayansu kacokam suka mai da hankalin su kansa, Duk sun ƙagu suji yadda a kayi a wannan ranar da basu manceba. Shi kuwa Yah Jafar wani numfashin yakuma. Saukewa kana yaci gaba da cewa. "Ranar da dare bayan anyi sallan isha'i duk muna falon Mamey dani dasu Jalal Jamil Affan da Ummi da Imran yana ɗan sheksru takwas lokacin. Anan mukaci abinci kana muka zauna muna hira. Kasan cewar akwai shaƙuwa mai tarin yawa tsakanin Mamey da Affan da yake tana da son yara. Amman son Affan da banne a wurinta har su Jamil kance wa Affan na hannun daman Mamey. Takanyi Dariya tace. "Eh ɗin ai ya fiku nitsuwa". Muna zaune sai hamma Mamey keyi tare da miƙa da lumshe idonta hakane yasa tace mana. Duk ta sallamemu saida safe tanajin bacci. Ummi tace. To. Still Kuma sai mukaci gaba da hira. Da ido muka bita ganin ta miƙa cikin sanyi tace. "Kai zanje inyi bacci wlh wani irin bacci mai nauyi nakeji yana fuzgata tamkar zan faɗi. Ni na shiga saida safenku". Allah ya bamu al'khairi mukace dukanmu kana ta shiga. Tana shiga kwanta ko second uku batayi da kwanciya ba tayi bacci. Mu kuwa muna gama hira muka watse. To su Jalal ne ƙarshen fita ashe basu tasheta ta rufe ƙofarta ba a famintata kenan fa?". Ya ƙare mgnar yana kallon su Jamil. Da sauri Jamil yace. Eh. Cikin sanyi ya kalli su Lamiɗo kana yaci gaba da cewa. "Ina komawa ɗaki na kira Juwairiyya muka fara hira a waya kamar kullum. To bayan mun gama waya da Juwairiyya har na kwanta sai na mike na nufi ɗakin Mamey dan inaso nayi mata magana a kan Juwairiyya fa tasanar wa mahaifin su maganar auren mu da ita, tun da lokacin takammala karatun ta dan haka itama ta gayawa Abba na ayi batun aurenmu dan nima tuni lokacin na gama karatuna har na fara aiki. Kuma a kwanakin ne aka bani sarautar Galadima wanda da mijin Gimbiya Saudatu ce mai matsayin to daya rasune Lamiɗo ya maida mulkin kaina. A zatonshi ta hakane zaisa yaranshi bazasuyi faɗa da junaba tunda bazasuce ya baiwa wane ya hana waneba. Ni a lokacin dagani har Mamey da Jabeer da baya ƙasar ma ba son wannan mulkin mukayiba bisa dole aka bani ita. Sai kuma ya jingina bayanshi da kujera kana yaci gaba da cewa. Ina isa bakin kofar Mamey natura kofar da sallama nashiga ɗakinta. Da sauri naja natsaya nan bakin kofar. Can na hangi Mamey na kwance. Bisa gado tana bacci da alamun baccin mai nauyi ne. Hajiya mama kuwa na tsaye a kanta da wata iriyar shiga da tafi kama data bokaye ko ince matsafa. Da mamaki nake kallon Hajia Mama dake tsaye bakin gadon sanye da wasu irin jajayen kaya tun daga samanta har ƙasa, kanta babu ko ɗan kwali hannunta rike da wani ƙwarya. Tana yayyafawa Mamey wani ruwa dake cikin ƙwaryar tare da yin wasu surutai da sukafi kama da surkullen matsafa. "Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un, nafurta da karfi. Da sauri nanufo in da Hajia Mama'n ke tsaye cikin ruɗani da kiɗima ina faɗin. Meye hakan Hajia Mama? me kike mata? me kike zuba mata a jiki haka?. Dasauri tajuyo kaina tasaka hannunta cikin ƙwaryar taɗibo ruwan tashiga watsamin tana ƙara matsoni, kaucewa nashiga yi ina matsowa in da Mamey take kwance kamar gawa ko matsi batayi, itako Hajia Mama masoni tarikayi tana watsamin ruwan, Baki na buɗe da karfi sabida wani irin masifeffen suka da naji duk inda ruwan ya taɓa a jikina yanayi. Ƙara watsomin tayi wanda yasa na ƙara kaucewa da sauri tare da buɗe baki da nufin yin ihun zafin da nakeji da kuma fargabar halin da Mamey na ke ciki. Sai kawai naji harshena yafurta Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un,wannan kalmar narika nanawata da karfi madadin inyi ihu." Ita kuwa Hajia Mama da sauri tajuya cikin alamun tsoron tonuwar asirinta. dan lokacin dare baiyi nisa sosai ba misalin ƙarfe goma ne, da gudu tafita a ɗaki dan jin yadda na kara sautin salatin da nake. Ita kuwa Hajia Mama tana fita part ɗinta ta nufa direct bathroom ɗinta ta shiga gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi number'n bokan ta takira yana ɗagawa cikin haki da fargabar a bin da zaije ya da wo tace. "Boka yanzu nafito daga ɗakin matarnan na samu tayi bacci kamar yadda kace, kuma na watsa mata ruwan bata farka a sai daifa wani yaganni lokacin danake yayyafa mata ruwan maganin nan babban ɗanta Galadiman Masarautar Joɗa kenan ya ganni". Wani irin dariya irin nasu na hatsabibai bokan yayi kana yace. "Toh daya ganki me yakeyi? me kuma yake cewa?". cikin rawar baki da soron da ya ziyarce ta gudun kada ai kin ya ɓaci tace. "Sunan Allah yaketa ambata salati yaketayi babu ko kakkautawa da wasu addu'o'i". Cikin ɗan tsagaita dariyar mugayen bokan yace "To aiki kam zaici amma dai akwai nakasu aciki, amma kada kidamu yanzu shi yaron zamu rufemasa baki zai dauwama kurma ba mgna a bakinsa bazai iya yin maganaba bazai iya furta komai ba haka zai dauwama ba mgn saidai yayi ta mai-mai-ta abinda yake cewa. Sannan daga nan tagwayen kuma zamu haɗa ɗaya da bin mata ɗaya shaye-shaye shi kuma babban kinga zai zama kamar Mahaukaci, shi kuma wancan Jabeer ɗin na gaya miki tun yana ƙaramin akwai sihirin da wani yayi mishi kada ki damu dashi bazai taɓa yin aureba har gaban abadan ko an mishi bazai zauna da matarba, kinga kenan duk sun zama suna da matsalar da dole baza'a basu mulkiba sai dai a bawa ɗanki Affan tunda kinga shi Imran ɗan ɗaya kishiyar taki shine ƙarami kan Affan." Cikin sauƙe numfashi tace. "Yauwa boka na gode ni dama fatana ɗana yayi mulki dan bana son mulkin ya bar ɗakina tunda dai kace min tabbas cikin yaran Habibullah ne mijin wani zai gaji kakansa sarauta. Dariya yayi tare da cewa. "Kada ki damu mulki na gareki da ɗanki". Wa iyazubillah kaɗan kenan daga sharrin tsinannun shaiɗanu maƙiya Allah da Manzonsa bokaye taɓaɓɓu masu sa mai binsu ya taɓe ya gaza sauri a ranar da muminai ke sauri a bisa siraɗi. Acan cikin ɗakin Mamey kuwa. Sosai sautin addu'a da karatun da Jafar keyi yatsanan ta yana kankame da Mamey, wacce ke ƙwance ida nunta a rufe, har lokacin bata farka daga. Baccin sihirin da akasa takeyi ba saboda nauyin. Baccin da suka je fata ciki. Sheko bakinsa baya iya furta komai sai addu'o'in sai kuma hawaye da keta tsatstsafowa daga cikin ida nunsa sabida fargarba da kuma zafin da yakeji, Abba kuwa dake can part ɗinsa da yake Part ɗin shi na natsakanin na matan nashi ne. Yana cikin ɗakinsa dake sama. Haka yasa yarinƙa jiyo muryar Jafar da irin addu'o'in dayake cikin kiɗima, da kajin addu'ar kasan acikin tsananin firgici da tashin hankali yake yinsa, Wuf yamike yanufo part in Mamey kasan cewar babu wata tazara sakaninsu. Gudu-gudu sauri-sauri ya isa. Cikin hanzari yatura kofar bedroom ɗin Mamey cikin sananin tashin hankali da kaɗuwa ganin yadda Yah Jafar ke rungume da Mamey sai innalillahi yake da karfi hawaye yagama wanke fuskarsa idanunsa sun yi jazir saboda kuka da zafin da yakeji da fargabar ganin tamkar Mamey a mace take a kiɗime yanufo in da suke yana faɗin. "Subahanallahi kai Jafar meya farune me ya sameta?". Yayi tambayar hankali a tashe, tare da miƙa hannu ya ɗago kan Mamey dake kan kafar Ya Jafar yashiga girgizata yana kiran sunan ta. "Aisha! Aisha!! Ummu Jabeer!. Gani shiru bata ko matsi sai dai tana numfashi ya tsananta firgicinsa. Hankali a tashe yakuma kallon ya Jafar wanda keta addu'o'in babu ko kakkautawa. Mai da kan Mamey'n yayi ya kwantar kan cinyar kafar Jafar. Kana ya juya a kiɗime ya fita a ɗakin da sauri ya nufi sashin mahaifinsa Lamiɗo. Shi ko ya Jafar cigaba da maimata innalillahi yakeyi yana zubda hawayen. A can ɓangaren Hajia Mama kuwa. fitowar ta daga ɗakinta kenan cike da jin daɗin yadda bokan ya karfafa mata guiwa tanajin daɗi a ranta yanzu komai zai tafi mata yadda take bukata zata rabu da zugar yayan Mamey da ita duk kowa ya huta, tana fita ta hangi Abba ta window yafita daga cikin part ɗinsa hankali a tashe. Fuska ta ɗan yamusa tazauna saman ɗaya daga cikin kujerun parlour'n, can kuma tamike kamar an tsikareta tabi bayansa da sauri. Acan shashin Lamiɗo kuwa. Da sauri Lamiɗo da Galadima suka mike, bayan Abba yagama sanar musu abin da ke faruwa. A tare suka fito suka nufi part ɗin Mamey'n. Lamiɗo na gaba Galadima da Abba na biye dashi suka shiga ɗakin, in da Abba yabar Yah Jafar a haka suka iske shi yana ganinsu ya miƙe da sauri Mamey yashiga nuna wasu Lamiɗo da hannu yana kuka yana nuna musu ita da kwatanta musu yadda Hajia Mama tayi mata. Da sauri Hajia Mama ta turo kofar dan taga shigowar su Lamiɗo'n. Jafar kuwa yana ganinta yashiga nunata da hannu sai kuma ya nuna Mamey'n yana cigaba da ƙwatanta yadda tayi matan shidai baki kam babu shi sai dai addu'o'in da kuma kukan dayake tayi. Gaba ɗaya su suka maida kallonsu kan Hajia Mama nan take Lamiɗo da Galadima da Abba suka ɗiga ayar tambaya a kanta. itako ganin bawai magana Jafar ɗin keyiba sai bata damuba bata kuma fahimci cewa sun zargi meyafaru ba kuma basu gane me. Jafar ɗin yake cewa ba da hakan ba. Hajia mama kuwa cikeda da karfin hali irin nata na makiran mugaye mata tafara tafa hannu tana masar kwalla tana faɗin "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un Jafar me nake gani haka me yasami Mamey'n ku? kayi magana mana". Sai kuma tasaki kuka mai haɗe da salati. Lamiɗo ne yaɗanyi gyaran murya ganin Mamey'n tafara motsawa alamar tafarka daga nannauyan Baccin da take mikewa tayi zaune tare da zuba musu ido. Da sauri suka ɗan matso gareta kana duk suka mai da hankalin su kanta. Suna ce mata sannu Aisha, Amman shiru ba amsa. Cikin tsananin sauri da tsoro Abba ya matso kusa da ita tare da zubawa yatsun kafarta ido mamaki cike da kiɗima yake kallon yatsun kafarta da suka fara sauya kamannin halitta suka koma kamar na tsuntsu. Cike da alhini suma su Lamiɗo suke kallon yatsun kafar nata, hankali a tashe. Cikin gigita Abba ya kamo hannunta tare da nunawa Lamiɗo murya a daburce yace. "Innalillahi wa innailaihi rajiun Lamiɗo kalli yatsunta". wani matsanancin tashin hankalin ne yakuma dabaibayesu lokacin da suka ga yatsun hannunta yafara komawa irinna fiffiken tsuntsu. Gaba ki ɗaya su haɗa baki sukayi wajan furta "innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un hasbullahu wani'imalwakin". Sabida tsananin firgici da tashin hankali gaba ɗaya jikinsu rawa yakeyi. Cikin matsanan cin tashin hankali Lamiɗo da cushewar tunani Lamiɗo ya juyo ya kalli Galadima murya a hargitse yace. "Subahanallahi maza a kira Malam Musa yanzu nan". Cikin hanzari Galadima ya amsa da. "To". Kana yajuya da sauri yafita. Kan kace me labari yabaza masarautar Joɗo, Batare da bata lokaci ba sakon kiran da Lamiɗo yayiwa Malam Musa ya isa gareshi. Cikin ƴan daƙiƙu malam Musa ya iso cikin masarautar Joɗa Lamiɗo yabada umurnin a shigo dashi har cikin ɗakin Mamey. Yana shiga kallonta malam Musa yayi cikin tashin hankali ya girgizata kai kana yakallesu Lamiɗo yace. "Sihirine a kamata mai haɗe da tsafi kuma daga yanzu zuwa ko yaushe ko wanne lokacin zata iya juyewa daga mutun ta dawo tsunsuwa". Salati suka ɗauka baki ɗayansu nan kuma ɗakin yakacame da koke-koke su Jamil da Jalal Affan Ummi Jafar yayin da duk muryar Hajia Mama yafi amo wajen kuka da shiga tashin hankali ziraran miraran. (uhum makircin mugu kenan.) (Sai daifa akwai kishiyoyi na gari da matsalar kishiya kan sasu kukan gaske wlh.) Ranar kuwa wannan masarautar taga tashin hankali mara misaltuwa, Jiƙe-jiƙe da hayaƙi da shafe-shafen magungun gargajiya babu wanda malam Musa baiba, kiɗima yasa sun mance da suyi amfanin da ayatul shifa. Ganin anyi duk abinda za'ayi na gargaji abin yaci tura ne yasa hankalin. Dr Aliyu yakasa ƙwanciya gani yake ko wata cutarce ta da ban haka yasa ya fitadaga ɗakin yatafi part ɗin sa, kiran wasu manyan likitoci a bokansa. Yasanar musu koda wani shawarin da zasu basu bayan sun gama wayar kuwa. Kayan ai kinsa ya ɗauko yakomo ɗakin Mamey'n yayi iya gwaje-gwajen sa babu abinda ya gane na wani cuta ko wani abu. Cikin takaici Malam Musa yace. "Kama bar gwada ta babu wani cuta face sihiri". Daga karshe dai dole ya hakura. Ranar babu wanda ya rumtsa kusan a tsaye suka kwana nan cikin ɗakin Mamey'n ganin yadda gaba ɗaya kamannin halittarta ke juyewa, Gimbiya Aminatu tayi kuka iya kuka. Lamiɗo ya kira Jadda ya sanar mishi halin da ake ciki tashin hankali iya tashin hankali Jadda da Sitti sun shigeshi nan suka fara shirin tahowa. Can gabanin kiran sallar asuba lamari ya ƙara munana dan a lokacin suffar Mamey ta gama juyewa izuwa na tsunsuwar Boleru a gabana a gabansu Lamiɗo a gaban mafiya yawan al'ummar Masarautar Joɗa. nan take kuwa Abba ya yanke jiki yafaɗi yasuma. Cikin kiɗima Dr Aliyu yayi kansa yafara bashi taimakon gaggawa. Mamey kuwa da yanzu takoma tsuntsuwa fara kaɗa fiffikenta tayi alamun son tashi take. Ai kuwa tamkar al'mara sai gashi ta tashi firr ta fire tabi ta window dake a buɗe tayi tacikin Garden tashige cikin tawagarsa tsuntsayen dake wurin. Innalillahi Jamil Jalal kuwa suma sumewa sukayi. Cikin hanzari da kiɗima Lamiɗo da Galadima suka zo jikin window nan suka hango ta ta sauka cikin tsuntsayen kawai sai suka fashe da kukan tsoron al'amarin duniya. Wani irin kuka Hajia Mama tasaka tana faɗin "wayyo Allah na waishin meke faruwa damune kam". sai kawai ta yanke jiki tafaɗi ta kakkafe idanunta kamar wacce ta suma. Ranar Hajia Mama haka tawuni tana kuka ta rungume Jamil da Jalal dasuke keta kuka kamar ransu zai fita. Jadda da Sitti da Umaymah da Aunty Juwairiyya da babanta duk a ranar sukazo. An kamo tsuntsuwar Boleru suna killaceta, yayinda aketa tururuwan zuwa ganin tsuntsuwar. Ido da ido da Gimbiya Saudatu tazo da yake sokuwace. Sai cewa tayi. "Allah sarki wato al'haƙi kuikuyo ko sharrinta ya dawo kanta, ohoho larabawa an zama tsuntsuwar Boleru". Toh fa daga nanne Magautan su Sheykh duk suka samu suka fake suka laɓe a bayanta. Su kuwa haka sukaci gaba da kukan Hajia Mama ko uwartace ta mutu sai haka, duk wanda yaganta sai ta bashi tausayi akasin Lamiɗo da Galadima da suka sa zargi a kanta duk abin da take shirine da zallar iya tuggu munafurci da makirci. Tun daga lokacin tsuntsuwar nan ko ince Mamey ko yaushe sai ana kamata ita kuwa tana firewa tana komawa cikin tsuntsaye ƴan uwanta. Al'amarin ya magaga ya tada hankalin kowa. Ana kamata zata zille ta fire ta koma cikin Garden ta zauna cikin tsuntsayen cikin masarautar Joɗa. Duk wannan tashin hankali da ake ciki Sheykh Jabeer bashida labari dan lokacin yana karatu a jami'ar Madina sai dai kwata-kwata a lokacin hankalinsa yakasa ƙwanciya idan yakira wayar Mamey'n sai asa Aunty Rahma ta ɗauka tayi mishi mgn wanda ita kuma dama lokacin sun zo suna nan da Mamma. Yadda Hajia Mama ke nuna tashin hankali tane yasa suka yarda da ita. Wannan juyewar Mamey shine. Sanadin da Jadda ya samu hawan jini kenan. A ranar da dare Umaymah Mamma Aunty Rahma Aunty Juwairiyya Sitti duk sun gaza bacci, sun sa tsuntsuwar Boleru a gaba Magauta na musu dariya. Sai da asubane sun kabbarta yin salla asuba, tsuntsuwar ta tashi ta fire, Bata tsaya cikin masararutar Joɗa bama ta fuskanci ƙasar Cameroon ta nausa tayi can yankin Yahunde. Ɓacewar tsuntsuwar nan shi yafi tada musu hankali. Anyi neman duniya har an gaji. Ba ita ba dalilinta har dai aka ruggumi ƙaddara. Sai dai Lamiɗo da Galadima da Jadda da Umaymah sunci gaba da bincikawa da neman mafita. Lokacin da Sheykh ya kammala digirin sa na farko yazo. Nigeria nan ne ake faɗa masa abin da ya faru a lokacin tashin hankalin da kiɗimar rayuwar daya faɗa ciki baya misaltuwa wani babban tashin hankalin kuwa shine daya iske ya Jafar baya magana sai addu'o'in da yin karatun al'ƙur'ani mai girma da kuka, dakuma ya buƙaci yaje yaga Mamey'n shi a yadda take ɗin a tsuntsuwar ta ɗin, nan ake faɗa masa ai tun lokacin da abun yafaru da kwana ɗaya rak ta fire tabar cikin masarautar Joɗa. Ranar Sheykh kuka kamar karamin yaro ya rungume Jamil Jalal Yah Jafar da tun isowarsa Jafar ɗin ke ƙanƙame da hannun sa yana karatun yana kuka haka sukayi ta kuka Hajia Mama na tayasu. Ranar tazamo musu tamkar sabuwa. Tun daga wannan lokacin kuma sai yazamo kamar an cire hankalin Abba'n su a kansu madadin a lokacin ya janyosu jikinshi yazame musu Garkuwa dan suɗan sami sassaucin kunar dake cikin zuciyarsu sai yariƙa nisanta kanshi dasu. Shi kansa bai san dalilin hakan ba, duk wannan kuma acikin shirin Hajia Mama ce, kwana ɗayan da tsuntsuwar tayi tafire ma ita takoma gun bokanta tace tanaso tsuntsuwar tabar cikin masarautar gaba ɗaya dan taga sun dage da magungunan. Dariya bokan nata yayi tare da cewa. "Ke shar-shar banza da kika samu ma ba Addu'o'inku na musulmai sukeyiba ai da tuni sun karya sihirin". Cikin jin daɗi tace. "Aini gaba ta kaini da hankalin su baije ga canba". Lamiɗo kuwa lokacin ya ƙara jan Sheykh a jiki sosai. Sabida bayanin da Malam Musa yayi musu na cewar a sanadin aurensa da ba fulatanar daji mahaifiyarsu zata dawo. Haka yasa part in da a ka bashi kusa da Garden inda tsuntsayen suke. aka buɗe mishi wata kofa taciki in da daga cikin part ɗin direct zai sadashi da cikin Garden ɗin. Bai wani jima sosai a Nigeria ba yakoma Madina sabida jin yakeyi ya tsani ƙasar Nigeria Especially Masarautar Joɗa. Koda ya koma sosai ƴan uwan Sitti suka ga canji a rayuwarsa saida aka dage da addu'a kafin ya dawo hayyacinsa. Daga nan suka ƙara kula ta musamman a kanshi suka zame mishi uwa uba ƙanne yayu sukeyi mishi komai. Yakanyi shekara uku huɗu bai zoba. Sai dai yana yawan sawa Jadda yazo mishi da Jamil Jalal Yah Jafar da Affan yawanci duk shekara zasu zo sau biyu hajji da umra wani shekaranma sau uku. Ya maida hankali sa kan karatunsa da addu'a Allah ya baiya mishi Mameynshi a duk inda take ko a tsuntsuwar Boleru shi zaici gaba da rainonta da kula da ita iya rai da mutuwa. Daga nan yayi master's madadin ya dawo ya haɗe. PHD ɗinsa. daga nan yadawo Nigeria'n bisa tirsasawar Lamiɗo da Jadda da Galadima da Umaymah dake matsayin Uwa. Dole ya yarda ya dawo ya sanyawa ƙannensa ido wajen kula da su dakuma tarbiyyan su dakuma neman hamaifiyar su da kula da yayansa yakuma zame musu Garkuwa Da kuma bincikar Magautansu wanda dalilin haka ya samu matakin SS wanda dama shine burinsa to kuma Alhamdulillah ya gane komai Especially da ya samu damar aikin SS wanda dama burinshi kenan a dole Lamiɗo ya sashi karantan likitancin. A kwai sabo ƙauna tausayi da shaƙuwa da tsama tsakaninshi da kakanun nashi sosai. Hajia Mama kuwa da gayya ya barta da wayonta ita tanayi mishi kallon biri shi yana mata kallon ayaba. Dama kuma malam Musa. Ya faɗa musu cewa sanadin Sheykh ɗin ne Mamey'n zata dawo yabasu lbrin iya abinda Allah ya sanar mishi cewa bata rasuba tana raye kuma tajuye daga tsuntsuwar dasuke tunani tadawo mutum tuntuni tun bayan tafiyarta da watanni. (Rayuwa kenan takan iya sauyawa a duk san da Allah yaso domin shi yake juya daƙuƙu i zuwa sa'a wuni zuwa dare kwana zuwa shekara ya fidda matacce a cikin rayayye ko ya fidda rayayye a cikin matacciya) Ajiyan zuciya mai nauyi suka sauƙe baki ɗayansu da suke cikin falon. Bayan ya Jafar yagama basu labarin yadda akayi da abinda ya sani har Mamey'n su ta juye ta zama tsuntsuwa da kuma yadda akayi shima yakoma baya magana sai kuka da karatu. Gabaki ɗaya parlour'n ya kaure da ambaton sunan Allah da yiwa uban giji tasbihi. Ita kam Mamey sai murmushi takeyi tare da maimata. "Alhamdulillah! Alhamdulillah alakulli halin". Affan kuwa kuka yakeyi tamkar ransa zai bar gangar jikinsa. Cike da rauni Sheykh ya jawoshi jikinshi ya ruggumeshi suna masu zubda hawaye baki ɗayansu. Cikin rauni da tausayin irin kukan ƙuncin da Affan keyi Lamiɗo ya gyara zama tare da yin gyaran murya kana ya juyo ya kalli Bappa tare da cewa. "Ka bamu labarin yadda akayi. Aishatu tashigo hannun ku". Ai kuwa kaf hankalin jamar parlour'n yadawo kan Bappa dan kowa nason jin yadda akayi Mamey'n tashigo hannunsa gaba ɗaya shi suka zuba ido. A hankali yayi Bappa gyaran murya tare da gyara zamanshi kana ya ɗago hannunshi ya nuna Shatu da yatsarsa manuniya kana yace. "Shatu itace sanadin. Dan a lokacin da tashigo hannun mu mu muna mata kallon tsuntsuwar Boleru ne tsawon kusan wata bakwai muna tare da ita muna ganinta Giɗi yarona shike kula da ita saida ya zama tare suke cin abinci. To Shatu itace ta fara ce mana ba tsuntsuwar Boleru bace mutunce ita a ranar wata jumma'a da tazo tare da mahaifin ta Alhaji Abboi wanda ni makiyayinsa ne. Nan taga tsuntsuwar yara na son kamata su yaran damu manyan duk muna cewa tsuntsuwa ce. Ita kuma tana cewa mutum ce. Wanda haka yasa dole basu koma cikin birnin Yahunde a ranarba ita da mahaifinta suka kwana a gidana a Rugar Arɗo Babayo wanda nanne asalin mahaifata. haka ta kwana tana gaɗin tsuntsuwar har dai Allah yanuna mana ikon sa da asuba tajuya ta dawo mutum a gaban idonmu, Sai dai tana cikin larurar naƙuda. Cikin ikon Allah ta haifu ta sauƙa lfy ta haifi ɗiyarta mace. To lokacine mukaga sarƙar dake wuyanta. Mai ɗauke da tambarin masarautar Joɗa kasan cewar masarautar fulɓe ce kuma mahaifin Alhaji Abboi abo kine ga Lamiɗo akan ɗan ziyarci juna kaɗan kaɗan to sanadin hakane Alhaji Abboi ya gane tambarin dake jin sarƙar na masarautar Joɗa ce. Tofa anan muka gane cewa duk yadda akayi ita ahalin masarautar Joɗa ce. Kuma Sarkin bakanmu ya tabbatar mana ita mutunce aikin sihirine to sai dai babu yadda za'ayi mu fuskanceku da mgnar kai tsaye tunda bamu san komai nakuba." Ɗan tsakaita maganar yayi yaɗan ja numfashi kana yaci gaba da faɗin. "Ni banine mahaifin Shatu ba Alh Abboi shine mahaifinta ga kuma mahaifiyarta. Ni makiyayin mahaifinta ne. inayi masa kiwone yana biyan. Mafi akasari duk karshen wata suna zuwa tare da ita nan Rugar Arɗo Babayo. To ita Shatu tanason yanayin daji rugarmu shiyasa duk sanda zaizo da ita zai zo, in zai koma kuma wasu lokutan yakan koma yabarta anan Rugarmu da yake ranar Jumma'a yake zuwa, to sai ranar lahadi da yamma Al'ameen ko wani daga cikin yayunta yazo ya ɗauke ta su koma. Yawan zuwasu shi yasa tasaba da da yarana sosai da mai ɗakina. To amman zuwansu da Allah ya ƙaddara lamarin Ummey ta juye a gabanta fir babu yadda ba'ayi da ita ta komaba taƙi bin mahaifinta fir taƙi tace ita zata zauna da Ummey ita ta zaɓa Junainah suna. Wannan yasa dole mahaifinta ya koma ya barta. To lokacin da Ummey'n Shatu'n ta faɗo hannunmu muka kuma ga wannan sarkar dake wuyanta na masarautar Joɗa shine Alh Abboi yace mu ƙaura mu dawo nan. Nigeria kusa da masarautar Joɗa cikin Rugar Bani dan tasami kusan ci da masarautar. to nan fa muka dawo Nigeria har da ita Shatu'n dan taƙi yar da a raba su da Ummey'n ta ashe rabo ke jawota nan. dole iyayenta suka haƙura suka barta tare dani. Muna dawowa nan muka sata a makarantar cikin Shikan". Nan yaci gaba da basu labarin duk wani bayanin gwa-gwar mayar da Shatu tayi a ka Ummey duk sai da ya basu labari. Ya ƙara da cewa. "Lokacin da muka zo Nigeria da Ummey wato (Mamey) Ba'ana naɗan shekaru sha takwas a duniya, lokacin (Parvina) wato Shatu kenan ita kuma du-du shekarun ta takwas ne, to kafin mu dawo ma Mamey bata dawo daga haiyacin taba bata fara magana ba, lokacin da mukazo. Nigeria Rugar Bani sai Ba'ana yace zai bata mgnin zata fara mgn kuma zata zama dai-dai sai dai zaiyi wuya ta tuna baya, Amman zata dawo tayi mgn amman da sharadi. kasan cewar fatanmu ta tuna baya mu maidata ga ahlinta yasa mukace mun amince da sharaɗinsa wanda bamu san menene sharaɗin ba. Shi saida ya fara bata mgnin kuma yace sai da sharaɗin in Ummey ta worke ta fara mgn muyi al'ƙawarin aura mishi Shatu. To lokacin mu baƙine bamu san halinsa na ɓoyeba kuma burinmu da fatanmu ta worke mu maidata hannun ƴan uwanta sai muka amince mukayi mishi wannan al'ƙawarin bisa rashin sanin halin daga ranar Mata yake kiran Shatu. Kullum Shatu ita ke zuwa gidansu Ba'ana da safe tana karɓawa Ummey magani a gunsa, dan shi tun tashin sa yake wannan cacube-cacuben nasa, so kullum. Shike bawa Shatu magani ta kawo wa Ummey tana sha har Ummey tadawo tafara magana sai dai bata iya tuna baya ba nan. Ba'ana'n ke ce mana duk randa taga wasu nata ko ƴan uwan ta ko wani abu nata zai yiwu tunanin ta yadawo ta iya tuna baya." Sai kuma ya ɗan tsagaita tare da sauƙe numfashi kana a hankali yaci gaba da cewa. "Toh tun daga ranar ne muka fara neman hanya da dalilin da zai haɗamu daku mutanen masarautar Joɗa. Sabida munsan aikin sihirine dole akwai Magauta sannan a gefen Ba'ana kuwa ya addabemu ya hana Shatu salama duk mai sonta sai yaga bayanshi. To sai marigayi Cuɓaɗo ya bamu tabbacin bulalin Shaɗin masarautar Joɗa ne kawai zai karya duk wani sihirin jikin Ba'ana to kasan cewar yana sonta so na gsky bai cutar da ita in hankalinmu ya tashi kan muna tsoron ya aureta takan ce mana. "Abinda in na gama karatuna zamu koma Yahunde sabida ita bamu sanar mata mun gano asalin Ummey ƴar ina bane gudun ita yarinyace kada tai ta gayawa wasu. To munata son yadda alaƙa zata haɗamu sai kuma ga ƙabilar ɓachama su tasomu gaba. Ran da muka zo nan na forko da muka ga Jamil sosai muka ƙara ƙarfafa guiwar ita ahlin masarautar Joɗa ce dan akwai kamar jini tare dashi da ita. To da akayi faɗa kukaje mana jaje da gayya Arɗo Bani ya gaggayawa mai martaba Lamiɗo mgn dan ya tunzurashi ayi Shaɗi mu jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya kenan. Mun dawo da ita, mu kuma samu mgnin Ba'ana to kuma Alhamdulillah duk abin neman ya samu. Sai kuma yayi ƙasa da kanshi murya na rawa yace. "Sai dai sanadin faɗan ni na rasa kowa nawa". Bappa ya ƙarashe mgnar cikin rauni da zubda hawayen tuno matarsa da zaratan yaranshi. Cikin raunin tuno ahlinshi kuka mai rauni ya rufeshi yayinda Shatuma kuka mai ƙarfi ya kubce mata hakama Ummey sabida ita dai gata ta dawo ahlinta shi kuma garin dawo da ita cikin ƴaƴanta ya rasa nashi yaran. Cikin tsananin jin daɗi Sheykh ya ɗan muskuta cikin tsananin farin ciki da jin daɗin da godewa Allah daya bashi damar kuɓutar dasu ƴaƴan Bappa su Gaini shima zaisa Bappa farin ciki kwatankwacin yadda ya sashi. Cikin sauri da bada umarni ya kalli Jamil tare da cewa. "Jamil tashi maza kaje kazo dasu". "To". Jamil yace kana ya miƙe da sauri yafita batare da ɓata lokaciba sabida ya gano su waye Gaini. Yana zuwa yace. "Yah Gaini taso taso kuzo ga Bappanku da Shatu da Junainah". Ai kafinma ya rufe baki duk sun muƙe cikin tsananin zaƙuwa suka biyo bayanshi. Shi kuwa Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro da Alhaji Umaru rauninsu ya rigada ya dawo tuno irin kisan gillar da ƙabilar ɓachama sukayi musu. Shi kuwa Sheykh dasu Lamiɗo shiru sukayi sabida son yi musu ba zata. Da sauri Jamil yasa hannunshi ya tura ƙofar suka shigo tare da cewa. "Assalamu alaikum Bappa share hawayenka gasu Yah Gaini Seyo da Giɗi". Duk sauran mutanen falon duk suka ɗago kansu. Ido cikin ido Shatu tayi da Yah Giɗi'nta abokin tsamarta. Wani irin yunƙura tayi ta miƙe tsaye tare da cewa. "La'ilahaillaha Muhammadu rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam Alhamdulillah Bappa gasu Yah Gaini". Jin kalaman Shatu ne yasa Bappa dayake sunkuye ya ɗago kanshi yana kalli bakin ƙofar shigowa ya sauƙe kwayar idanunshi kan.....! Kuyi haƙuri da typing errors ina cikin ciwon kai nayi typing ɗin a daddafe. Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300. A yawan posting ne babban cinsu 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa in kin tura sai kiyi screenshort na Debit Alert ki turo min ta whatsApp 09097853276 ƴan 3oo in naki da halin biya ta Account zaki iya sayan katin mtn na ɗari uku ki copy numbers ɗin ku turo min ta whatsApp ɗin 09097853276. By *GARKUWAR FULANI* [4/3, 8:39 PM] +234 806 559 0880: Ya sauƙe idanunshi kan Giɗi Seyo Gaini. Cikin wani irin yanayin tarin farin ciki mai sanya rauni. Wasu zafafan hawaye suka kwaranyo mishi. Da sauri ya yunƙura ya juyo ya fuskanci al'ƙibila. Sujjadar godiyar Allah yayi kana ya ɗago yana mai zubda hawaye. Ita kuwa Shatu da sauri ta ƙarasa garesu, kawai sai ta faɗa jikinsu baki ɗayansu, tare da sakin raunataccen kuka. Cikin rauni da yanayin kula Seyo wa mai tausayi kamar uwa yace. "Shatu dena kuka, mu godewa Allah". Sai kuma ta kalli Yah Giɗi cikin sanyi ta ruggume shi tare da cewa. "Tunda na rasaka kusa dani na rasa abokin faɗa da tsama, shiyasa lokuta da dama ina jin daɗin inyi taƙaddama da Gimbiya Saudatu dan sai yana tunamin ta ƙaddamar mu, da Yah Giɗi na abokin faɗana". Cikin zubda hawaye shima Giɗi yayi murmushi tare da janyeta jikinshi kana yace. "Nayi kuka a lokuta ma banbantan da bazan iya ƙididdiga ba sabida tunoki da rayuwarmu". Hannun tasa ta share hawayenta kana ta kalli Yah Gaini wa mai matsayin Uba cikin kulawa da yanayin rayuwarta yace. "Shatu ina Ba'ana ko mun samu nasarar rabuwarki dashi". Da sauri tace. "Yah Gaini Allah ya rabamu da Yah Ba'ana". Cikin tarin jin daɗi yace. "Alhamdulillah". Dai-dai lokacin suka isa gaban Bappa daketa zubda hawaye. Zama sukayi a gabanshi gaba dayansu huɗu. A hankali Giɗi ya sunkuyo ya kwantar da kanshi bisa cinyar Bappa tare da sakin sassayan kuka a hankali yace. "Bappa mun ganka kaida Shatu ina Innarmu ina Ummey ina Junainah ina Yah Lado?". Da sauri Ummey tasa hannunta ta rufe bakinta jin kuka zai kubce mata. Sai dai tuni sautin kukan ya fito. Da sauri Giɗi ya rarrafo gabanta murmushi yayi still Ido na zubda hawaye a hankali yace. "Alhamdulillah Ummey Junainah ina Innarmu da Yah Lado". Cikin kuka Junainah ta faɗa jikinshi tare da cewa. "Arnan Ɓacama sun kashe Innarmu sun kashe Yah Lado sun kashe mutane da yawa na rugarmu". Da sauri Giɗi ya juyo ya kalli Ummey cikin tashin hankali da kubcewar kuka. Gaini da Seyo suma kuka mai rauni suka sake ganin Bappansu yana jinjina musu kai alamun zancen Junainah hakane". Shiru falon sukayi baki ɗayansu sai sutin kukan Giɗi, Shatu, Junainah, Ummey, Seyo, Gaini. Raunin da kukansu ya sauƙar a zuciyar Bappa ne yasa shima sakin kuka dan yau sai sukaji gaba ɗaya rasuwar Yah Lado da Inna ta dawo musu sabuwa. Sosai Shatu keyin kuka tana durƙushe ta tanƙwashe sawunta, hakama Ummey. Gaba ɗaya kab falon saida idon kawa ya ciko da ƙwalla. Cikin Rauni Sheykh ya matso inda Shatu ke durƙushe gaban yayun nata, cikin sanyi ya kalli Bappa Ummey murya a raunace yace. "Tabbas bansan irin ƙunar da kakaji a cikin ranka ba Bappa amman nasan kwatankwacin kamannin ƙunan rashin ɗa, a suman da Afreen tayi naji ciwo da ƙuna a zuciyata tamkar ban taɓa farin cikiba, nasan zafin rashin uwa, amman ban san zafin rashin mataba dan kamin gatan bani Mar'atussaliha ta zame min GARKUWA tana sani farin ciki a duk lokacin da nake cikin baƙin ciki." Shiru yayi sai kuma ga hawaye shar-shar a idanunsa cikin rauni yace. "Na samu komai da nake nema a rayuwata daga gareka ka bani mata ta gari, Allah ya azurtamu da samun ƙaruwar arzin haihuwa sanadinka Ummey na ta dawo. Inama! inama! ace Inna da Lado ɓata sukayi ba rasuwa ba, da tabbas zanyi iyakar iyawata in dawo maka dasu da izinin ubangiji. To amman wannan hurumin ubangijin sammai da ƙassaine. Kayi haƙuri Bappa Allah ne ya baka Inna matsayin mata ya ɗauketa ya sauyama da ƴar uwarta kuma Allah shi ya baka Lado ya ɗauke shi kuma ya killace maka Seyo Gaini Giɗi, wanda wata ƙil da suna Rugar ba'a sacesu ba da an kashesu. Gashi yanzu Allah ya dawo maka dasu. Bappa kace Alhamdulillah ka godewa Allah da ni'imar da yayi maka sai ya ƙara maka wata a kai. Kayi haƙuri ka bar kuka kaga kukanka na ƙara ingiza nasu". Ya ƙare mgnar yana sa hannunshi cikin tafin hannun Shatu yana murza a hankali. Cikin gamsuwa da jin sanyi a ransa Bappa yace. "Alhamdulillah". Da sauri Su Giɗi suma sukace. "Alhamdulillah". Hakama su Lamiɗo kab falon sai suka fara mai-mai-ta hamdala. Ai kuwa cikin ikon Allah duk ƙuna da ƙuncin da zuƙatansu keyi a take Allah ya sauƙaƙa musu shi. Cikin gyaran murya Lamiɗo yace. "Alhamdulillah komai yayi forko zaiyi ƙarshe duk abinda yayi tsananin tabbas zaiyi sauƙi Allah mun gode maka daka ara mana rai da lfy". Ya ƙarashe mgnar yana kallon Sheykh dake kallon agogon hannunshi sabida jin anyi kiran sallan azahar. Cikin tarin jin daɗi Abbansu Sheykh ya matso kusa da Bappa da Abboi murya cike da tarin jin daɗi yace. "Bappa Abboi dama duk al'ummar Rugar Bani da Rugar Arɗo Babayo ngd matuƙa Ubangiji yayi muka sakayya da gidan al'ljanna mafi ƙololuwa girma. Shatu Allah ya dafa miki ya tsareki dake da ahlinka". Amin Amin sukace baki ɗayansu. Shi kuwa Bappa Sheykh ya kalla tare da cewa. "Muhammad Ngd matuƙa Allah ya saka da al'khairi da kulawarka Alhamdulillah ga mahaifiyarku da ƙanwarku Allah ya bamu aron rai da lfy da ikon dawo muku dasu lfy". Cikin jin daɗi Ummey tace. "Bappa dani dasu ya kamata muyi godiya ba kuba kun gama min komai a duniya musamman Alhaji Abboi da matarsa Dedde sun min karar bani yar su duk da tarin son da sukeyi mata, suka amince muka dawo da ita nan, kana suka bawa Jabeer na aurenta." Sai kuma ta juyo ta kalli Shatu tare da cewa. "Kin min komai kin juya min Jabeer daga bauɗeɗɗen mutun zuwa dai-daice gashi yanzu har fara'a yakeyi ga Jalal na shima ya zama mai fara'a Jamil kuma ya nitsu. Sai dai yanayin Affan nane ke min ciwo a rai, Affan ka dena kuka kajiko Shalelen Mamey". Cikin rauni Affan ya matsota ɗaura kanshi bisa cinyarta yayi tare da sakin kuka. Gaba ɗaya kowa yasan takaicin abinda mahaifiyarsa tayine yake sashi kukan. A hankali Lamiɗo yace. "Kayi shiru Affan ita rayuwa kowa abinda ya shuka zai girba". Daga nan dai kuma akayi gaishe-gaishe. Kana mazan duk suka tafi masallaci. Matan masarautar Joɗa kuwa irinsu Gimbiya Saudatu da Gimbiya Aminatu dasu Mom da Samira duk ko wacce ta koma part ɗin ta cike da al'hinin sharrin ɗan Adam. Matan kuma duk kowa tai al'wala sukayi salla, kana suka sake fitowa falo suka zauna suna cin abinci. Affan kuwa Part ɗin shi ya koma ganin tashin hankali da yake cikine yasa Mami meda hankalinta gareshi. Shi kuwa Rumaisa yayarshi ya kira tana ɗagawa yace. "Uhummm tunda kullum kece kike zuga Hajia Mama kuna cutar waɗanda basu damu da kuba sai ki shirya kizo kiga halin da Mama ke ciki na girbar aiyukanta data shuka". Cikin tashin hankali Rumaisa tace. "Affan m.." Bai bari ta ida zancenta ba ya katse kiran. Su Sheykh kuwa dasu Haroon falon Sheykh Suka wuce. Bayan anyi sallan la'asar ne, Dedde ta kalli Ummey cikin kula tace. "Toh Ummeyn Shatu mu zamu koma Rugar Bani, sai jibi zamu koma Cameroon da izinin ubangiji Allah ya kiyaye gaba ya tsaremu". Cikin sauri Umaymah tace. "Yanzu-yanzu zaku tafine?". Cikin nitsuwa Dedde tace. "Eh ai su tuni ma sun shiga mota nida su Khadijah suke jira". Da sauri Umaymah tace. "Ayyah ni kuwa ina son ku gaisa da Sittinmu da Jadda kafin ku tafi". Da sauri Mamma tace. "Ai sun iso suna Part ɗin Lamiɗo. Amman yanzu zasu iso". Da sauri Shatu tace. "Toh Dedde am ki ɗan jira ku gaisa mana". Suna cikin mgnar Sitti da Jadda suka shigo. Allah sarki iyaye sai gashi Ummey a tsakiyarsu suna kuka gaba ɗayansu an rasa mai rarrashin wani. A hankali Sheykh da Haroon suka shigo falon cikin tsiya Sheykh yace. "Toh Alhamdulillah Jadda ni dai burina ya cika ko yau in kana son tafi ka gaida na gaba tunda kaga Mamey na ta dawo ta sameku cikar farin cikinta kusa mata al'barka". Dariya sukayi baki ɗayansu kana su Dedde suka matso aka gaggaisa. Sannan Jadda ya fita ya koma wurin su Lamiɗo. Cikin sanyi Shatu ta kalli Deddenta Aunty Amina Hafsi Khadijah waɗanda duk suke cikin shirin tafiya. A hankali tace. "Allah sarki da mu ƙara kwana mana, yanzu kuma in kun tafi shikenan sai yaushe ni na zama a nan ina gefe duk ƴan uwa suna Cameroon". Da sauri Ummi tace. "Kema kina tare da yan uwanki ga Ummeynki ta dawo kusa dake ga kuma Junainah gani ga Hibba". Da sauri suka kalli Jamil da ke cewa. "Kuma zan auro mana Khadijah ma ta dawo nan zaku bani ita ai ko Dedde". Ya ƙare mgnar cikin yanayinsa na wasa da dariya da kowa. Murmushi Dedde tayi tare da cewa. "Ai an baka ma Jamilu". Dariya mai sauti yayi tare da cewa. "Alhamdulillah". Junainah kuwa a hankali ta matso kusa da Ya Giɗi tare da cewa. "Ummey ni dai zan tafi tare dasu Yah Giɗi ban gaji da ganinsu ba". Cikin jin kewar juna Ummey tace. "Kije Junainah nima in Sitti na da Jadda sun tafi zamuzo tasu Mamma". Da sauri tace to. Kana ta kalli Shatu da tai shiru tana kallonta tare da cewa. "Kada ki damu Addana nima zanke zuwa masarautar Joɗa". Da sauri Jalal yace. "Zaki dawo dai Junnu gamu ga Abbanmu ga Adda Shatunki ga Ummey". Da sauri ta kalli Sheykh tare da cewa. "Toh Yan Junaidun fa". Dariya mai sauti Sheykh ya ɗan yi tare da cewa. "Shima zai dawo nan". Nan dai suka fito gaba dayansu dan yiwa su Dedde rakiya. Jadda kuwa harda kuka yayi yana yiwa su Abboi da Bappa godiya. A hankali Salmanu wanda yazo wurin ɗan Hafsi ne ya ɗan matso kusa da Ummey ƙasa yayi da murya tare da cewa. "Ummey ki roƙa min su Abboi a bar mana Hafsi mana". Dariya Ummey tayi tare da cewa. "Alhamdulillah kuce duk ma zamu kwasosu mu dawo nan dasu". Da sauri Salmanu ya shiga mota. Shi kuwa Yah Al'ameen gefen Shatu ya ɗan kalla tare da yafitota. Bayan Sheykh suna ɗan ratsa a hankali yace. "Wannan ƙawar taki Rafi'a fa, da batunta yasa su Abboi zuwa gobe zasuje su zanta da manyanta sai jibi zamu koma". Cike da mamaki tace. "Lahh Yah Al'ameen ashe mgnar taku har ta kankama". Da sauri yace. "Ke da Allah ni kada kimin shele". Baki ta ɗan tura tare da cewa. "Toh sai na gaya ma kowa yaji". Da sauri ya biyota ita kuwa cikin dariya tace. "Ummey ashe Yah Al'ameen da Rafi'a munahikai ne soyayyar sirri sukeyi". Dariya Sheykh yayi tare da juya mata ido alamun ai kema soyayyar sirri kikayi. Haka dai suka shiga motocin suka tafi cikin farin ciki da kewar juna. Cike da farin ciki suka koma cikin falon. Da sauri Umaymah ta amshi wayarta da Ishma ke miƙa mata. Amsa kiran tai da sauri ganin Abbansu Sheykh ne. "Assalamu alaikum Abban Jazlaan". Da sauri Abba dake part ɗin shi ya ɗan gyara zamanshi tare da cewa. "Toh wai Umaymah ni sai yaushe zan samu in gaisa da Yayar takune kun taru kun riƙe min ita da hira". Dariya mai sauti Umaymah tayi tare da cewa. "A a sai mun koma mana". Da sauri yace. "A a dan Allah kada muyi haka dake, kinga yara na cike nan ki kirata gefe kice mata ina kiranta". Murmushi tai tare da cewa. "Nawa zaka biya". Dariyar jin daɗi yayi tare da cewa. "Kujerar hajji tayi miki". Da sauri tace. "Sosai ma kuwa yanzu kuwa zan cika aiki". Tana gama wayar ta yafito Mamey suka tafi ɗakin Ummi ta gaya mata. Cikin jin kunya Mamey tace. "A'a kinga dama ke tsiyarki yawane da ita Khadijah ya da girmana kuma ana cike yarana da jikoki ku wani kawo min batun inje gareshi". Dariya Umaymah tayi tare da cewa. "Toh shike nan ni dai yar aikece. Cikin yanayin tarin shaƙuwarsu ta ya da ƙanwa Mamey tace. "To ai dai ya bari sai dare ko". Da sauri Umaymah tace. "Ohoh anaso ana kaiwa kasuwa". Hararan wasa tayi mata kana ta fito. Nanfa sukaci gaba da hira. Ana gab da kiran sallan magriba. Suka juyo ehu da kururuwar Hajia Mama da faɗe-faɗen da takeyi. Da sauri Sheykh ya nufi ɗakin daya rufeta, yana buɗeta. Ta fito tanata yayyarfa hannunta tare da cewa. "Wayyoooooooo zan zama tsuntsuwar Boleru". Da sauri yabi bayanta tuni ta iso falo. Tana kaɗan yatsun hannunta da sun fara komawa na tsuntsuwar Boleru. Cikin tsoro da mamaki da tausayi Mamey tace. "Innalillahi Jabeer kamanninta fa na sauyawa". Da sauri ya iso, yana mai kara wayarshi a kunne sabida kiran da yayiwa Affan. Yana ɗagawa yace. "Affan kazo kayi maza kazo". Cikin tashin hankali da tsoro Affan yace. "Toh". Yana fitowa yayi kiciɓis da Rumaisa a tare suka nufi. Part ɗin Sheykhhhh. Umaymah kuwa Abba da Lamiɗo ta kira ta gayawa. Kusan duk a tare suka iso. A tsakiyar falon suka sameta. Tana yayyarfa hannunta tare da cewa. "Na ji daɗi zan zama tsuntsuwar Boleru zanyi ta firewa kamar jirgi". Sai kuma ta kalli Sheykh da yake ta karanto Ayatul shifa yana tofa mata. Dariya tayi tare da cewa. "Kai bar ɓata lokacin ka a kaina ai al'haƙine kuikuyo ya dawo kaina wayyo ni Halima naga ta kaina". Da sauri Rumaisa ta iso gareta ihu tasa tare da kururuwar ganin yadda kafafunta duk suka zama cingil-cingil kamar na tsuntsuwar ladin kogii. Da sauri Rumaisa tace. "Dan Allah Affan mu kaita gidan bokan ya karya sihirin". Cikin tarin takaici da zubda hawaye Affan yace. "Banza mahaukaciya gafalelliya ni nan Affan babu gidan wani mushirkin mugun kafurin bokan da zanje. Anayi mata addu'o'in kina batun aje gidan boka". Cikin ihu tace. "Abba dan Allah mu kaita". Da sauri Abba yace. "In kika sake kirana kika haɗani da Allah dan inje inda zan tsaɓa mishi zan tsine miki shasha mara hankali". Sheykh ne ya ɗan kalleta cikin sanyi yace. "Aunty Rumaisa ki bari ki nitsu muyi mata addu'a in sha Allah zata samu lfy". Da sauri tace. "An ƙi ɗin sabida ba uwarka bace ai shiyasa zakace haka". Sai kuma ta zaro wayarta ta kira bokan bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga cikin kurma ihu da kururuwa yace. "Nima ƙonewa nakeyi, ita kuma a haka zataci gaba da rayuwa ita ba mutumba ita ba tsuntsuwar Boleru ba, zata zama aya ta yadda duk wanda ya ganta sai ya tambayi mai tayi. Domin dama shi mugunta ɗan aikene yakan iya dawowa wurin wanda ya aikeshi. Sai kuma ya kurma ihu da ƙarfi. A nan ya faɗi yana burburwa. Ya shiga gudu yana kwaɓe kayansa yana cewa wuta na ƙonashi ya zama mahaukaci tubran. Ita kuwa Rumaisa kamo Hannun Hajia Mama tayi suka tafi Part ɗin ta. Lamiɗo kuwa kai ya jinnina tare da cewa. "Ƙarshen mugu kena". Sheykh kuwa da Mamey da sauri suka zauna gefen Affan dayake kuka kamar ya haɗiyi zuciya cikin sanyi Sheykh yace. "Affan kayi haƙuri ka bar kuka in Sha Allah zamu dage da addu'a zata samu lfy". Cikin shassheƙan kuka. Ya tashi yabi bayansu. Sabida ita dai uwa duk yadda take uwace. Abba kam juyawa yayi ya fita ko a jikinsa. Domin shi tausayin Affan ne kawai ke cinsa a rai. Lamiɗo da Gimbiya Aminatu da Galadima ma kwaffa kawai sukayi suka fita. Umaymah kuwa cikin zafin zuciya tace. "Wlh Ni dai ko duk zaku yafe mata ni ba yafewa zanyi ba". Da sauri Sheykh ya kalleta idonshi cike da hawaye. Sai kuma ya kalli Mamma da Aunty Rahma dasu Yah Jafar da suma suke cewa basu yafe mata ba. Jin an kira sallan magriba ne yasa duk suka miƙe suka tafi masallaci. Ana idar da sallan Isha'i Sheykh ya nufi Part ɗin Hajia Mama kuka sosai ya sameta tanayi Affan na gefenta shima kukan yakeyi Addu'o'in ya rinƙa tofa mata. Har saida yaga tayi bacci kana ya fita. har yaje bakin ƙofar fita sai kuma ya juyo jin Affan ya ruggumeshi ta baya yana kuka tare da cewa. "Ngd matuƙa Hamma Jabeer Allah ya bar zumunci da ƙauna". Cikin rauni yace. "Amin Amin Affan". Daga nan suka fita kowa yayi Part ɗinsa. Hira sosai sukayi ranar hirar yaushe gamo kusan sai gab da kiran sallan forko kana duk suka tashi sukayo al'wala sukayi ta nafila suna godewa Allah. Washe gari da safe gaba ɗayansu suna falon Abba ya shigo. Suna gaisawa yana kallon Umaymah dake mishi dariya ƙasa-ƙasa. Hajia Mama kuwa da taimakon addu'o'in da Sheykh yake mata hankalinta ya ɗan dai-dai-ta yadda zata fi jin ciwo da zafin sauyawar halittarta, da gaba ɗaya yanzu kafafunta sun zama na tsuntsuwar ladin kogi, yatsun hannunta kuma sun zama fiffizgewa tsuntsuwar Boleru, idanunta kuwa kamar na tsuntsuwar Duji sunyi ƙuru-ƙuru tamkar an taka kwaɗo. Wannan al'amarin yasa Lugga da saƙo mutanen masarartar Joɗa shigowa sunayi mata kallon sabuwar halitta masu dariya nayi. Tsananin tsoron Allah ya wadaci zuƙatan mata da mazan Masarautar. Bayan Aunty Juwairiyya ta dawone take suffantawa su Mamma yadda Allah ya maida Hajia Mama. Sosai jikinsu yayi tsanyi. Umaymah ce ta ɗan kalli Shatu da yanzu ta fito wonka cikin shirin baccinta. "Naji kamar Jazlaan ke kiranki". Umaymah ta faɗa cikin kulawa. Da sauri tace to kana ta miƙe ta funi Side ɗinsa. A falo ta sameshi gaban steps ɗin hawa wurin Dinning area. Hannunshi na cikin zirin zirin igiyoyi dake sarƙafe da duwatsu masu daraja sheƙin Daimond. Wanda a ciki yake liƙe da CCTV camera ta sama wanda da wuya mutun ya iya ganeshi. Ruggume shi tayi ta baya tare da cewa. "I miss you so much Sheykh Malam akarmakallu Dr Hamma Jabeer". Murmushi mai cike da jin daɗi yayi kana ya juyo ya ruggumeta. A hankali tasa tafin sawunta saman rumfar sawunshi kana tasa hannun ta saƙalo wuyanshi. Ya zama tana lafe a jikinsa. A hankali ya fara taku a haka ya nufi Bedroom. Suna shiga ya maida ƙofar ya rufe. Da cikin tsokana tace. "Yah Sheykh Haroon". Baki ya ɗan taɓe tare da cewa. "Wannan jarabebben tun yaushe yaja Ƴar mutane suka shiga ɗakin nan suka rufe ko kunya babu". Murmushi tayi tare da cewa. "Mutun da matarsa". A hankali ya sunkuyo kan gadon ya kwantar da ita tare da yi mata rumfa da ƙirjinshi kana yace. "Okay to ai nima gani da matata". Da sauri tace. "Yah Sheykh jego nakeyi, kwana Afreen goma kacal fa". Hancinsa ya manna da wuyarta tare da cewa. "Eh mu samo mata ƙanwa ko ƙani mu samu irin tagwayen Nana Faɗima". Da sauri tace. "Uhum wuya". Kissing lips ɗin ta yayi tare da cewa. "Ke ai yar baiwa ce nine zanke mana laulayi da naƙuda". Murmushi tayi tare dasa tafin hannunta ta tallabe kanshi a hankali tace. "Harda naƙudar ma Yah Sheykh". Da sauri yace. "Sosai ma kuwa ai na Afreen ɗinma ni nayi naƙudar ke ba kallonki kikeyi hankali konceba..". Dariya mai sauti tayi sabida lbarta mata yadda yaji a lokacin da karayar da yayi ya ƙara da cewa. "Mata kuna jin azabar duniya akan hayhuwa bamu da abinda zamuyi muku kuji sanyi sai kyautata muku da nuna muku soyayya in kuna matsayin matanmu iyaye kuwa ayi musu biyayya da tausayawa da kulawa shine kaɗai tukuicin wahalarsu dan bazamu taɓa iya biyansu ba inaji kamar ko wuta Mamey tace in shiga zan shiga dan biyayya sabida azabar da naji wanda nasa irinshi koma fiye da haka taji. In matsayin yarane kuma mu jiƙansu mu sosu mu kula da amanarsu da Allah ya bamu". Cikin sauƙe numfashi tace. "Yauwa niko Yah Sheykh inada tambaya". Rigarta ya fara turawa sama yana shafa cikinta tare da cewa. "Allah yasa na sani Boɗɗona". Juyowa tayi ta ɗan kalleshi tare da yin murmushi kana tace. "In sha Allah ma ka sani". Murmushi yayi tare dasa yatsarshi cikin hudar jibiyarta tare da cewa. "Uhum ina jinki". Kai ta gyaɗa kana tace. "Yauwa Dr dama ina son kayi min ƙarin bayani ne kan batun laulayi cikin Afreen da kai tayi." Murmushi yayi tare da cewa. "To ina jinki tambayi in baki amsa in na sani". Muskutawa tayi ta fuskanceshi da kyau tare da cewa. "Bayanin sanadin faruwar haka. Nake son sani. Don yana da kyeu mugane dalilin hakan. Shin yawan shaƙuwace da soyayya tsakanin ma'aurata kawai ke sa hakan ya faru. Ko kuma wani biology ne na Ubangiji?. Yake sa miji yayiwa matarsa laulayin ciki a wasu lokuta?". Murmushi mai cike da shauƙi yayi tare da cewa. "Eh wato kina son kiji ba'asin miki laulayi ko irin kin huta ɗin nan". Kai ta gyaɗa mishi tare da cewa. "Eh mana kaga in zakayi ta mana laulayi da naƙuda to ko duk shekara zan haihu ba matsala." Lakace hancinta yayi tare da cewa. "Uhum". Kiss ta manna mishi a goshinsa tare da cewa. "Dan Allah gaya min". Zamanshi ya gyara kana yace. "Toh Aish ba yawan shuƙuwa ko soyayya ba ne ke sa miji yayiwa matarsa laulayi. Asali ma ai dangantakar ba tsakanin matar da mijin ba ne. Dangantakar tsakanin ɗan ne da ubansa." Sai kuma ya ɗan ƙara jawota jikinshi tare da cewa. "Samuwar ɗan, ana nufin kamar yadda ya shafi uwar kai tsaye, to haka kuma ya shafi uban. Don haka, irin yanayin da ta ji saboda zuwan yaron, shi ma yakan iya jin hakan. Sai dai kawai nasa bazai kai yawan na uwar ba, saboda ta fi shi kusance da ɗan, kasancewar yana jikinta kin gane ko?." Cikin gamsuwa ta gyaɗa kai tare da cewa. "Na gane na gamsu. To kuma batun naƙuda fa da kace kayi min. Shin dama na miji kan ji ciwon naƙudan matarsa kamar yadda wasu mazan ke jin ciwon laulayi ciki ne? Ko dai kwatakwata babu wannan!?". Kanshi ya ɗan cusa tsakanin wuyanta da kafaɗarta tare da shaƙar ƙamshin jikinta cikin fahimtarwa yace. "A dai iyakar abinda muka sani zuwa yanzu, wanda kuma bincike da gwaje-gwace likitocin duniya suka tabbatar shi ne, namiji ba ya iya jin ciwon naƙuda. Sai dai yakan jin tsananin damuwa da ciwon rai ne, maimakon ciwon jiki da raɗaɗi da mai naƙudar take ji. Sai dai bincike ya tabbbatar da cewa yana da tasiri sosai wurin sauƙaƙa wa matar ciwon naƙudar, idan zai kasance tare da ita har ta haihu". Da sauri tace. "Kamar yaya to dan yana kusa da ita zataji ciwon ya sauƙaƙa?". Kai ya ɗan ɗago ya kalleta tare da cewa. "Domin idan ya zauna a gunta, musamman in zai riƙe mata hannunta ko ya riƙa ɗan shafa goshinta yana yi mata sannu kamar dai yadda nai miki ta miki lokacin kina naƙudar gab da haihuwar. To tabbas zataji sauƙi da sassaucin naƙudar da samun haihuwa a sauƙaƙe da izinin ubangiji. Saboda yayin da suka kasance a haka, jikin matar yana samar da wani sinadari da ake cewa oxytocin , wanda yake sanadin tsattsafowar wannan ruwa mai tsantsi to zai sauƙaƙa fitar yaron daga jikinta. Da iznin Allah". Cikin gamsuwa ta sauƙe numfashi tare da cewa. "To kai kuma kace harda ciwon baya kaji ranar da zan haihu a lokacin ma meya kawo hakan?". Cikin sanyi ya jujjuya kanshi tare da cewa. "Allahu ahlamu, kawai abinda nasa a raina wannan wani ikone da ƙudurar ubangiji daya gwada a kanmu wanda tabbas na taɓa riskar makamancin lbrin miji yayiwa matarsa naƙuda, to amman dai a likitance bamu ganoba tukun, dan haka wannan fagene na ubangijin sammai bakwai da ƙassai bakwai, shiyasa nasan zafi da ciwon da mata kanji yayin haihuwa". Cikin gamsuwa tace. "Ayyah sannu Yah Sheykh". Murmushi yayi tare da cewa. "Ke kam ba cewa kikayi in dan zanci gaba dayi miki laulayin ciki da naƙuda ba, ko duk shekarama ki haihu ba matsala ko". Murmushi tayi tare da cewa. "Eh mana". Murmushi yayi tare da jawota jikinshi yana mai sa hannunshi ɗaya zai zare boxes ɗinsa. Fahimtar inda ya dosane yasa ta miƙe da sauri tare da cewa. "Bari inje wurin Ummey na naji alamun Afreen ta farka". Fuskarshi ya kwaɓe tare da cewa. "Kai Aish ni dai banjiba". Cikin son zille mishi tace. "Kaji can muryarta tana kuka". Komawa yayi ya kwanta Cikin jinjina ƙudurar ubangiji yace. "Toh ɗaukota kuzo". Murmushi tayi tare da cewa. "Toh". Kana ta fita. Tana fita ya maida kanshi bisa pillow'nshi yana tasbihi da girman zatin Allah daya samar da cikekkiyar dangantaka tsakanin uwa da ɗanta ta yadda ko bata tare dashi in zaiyi kuka ko ya tashi bacci. Mamanta zai sanar mata. Ita kuwa Shatu tana zuwa ta wuce bedroom ɗin Ummi. Umaymah da Ummin kawai ta samu sunata hira da dariyar Abba daya shigo da kansa ya kira Mamey wai tazo su gaisa da abokanshi, daga nan yayi Part ɗin shi da ita wanda yake kusa da nata. Umaymah na kwance Afreen na gabanta Ummi kuwa zaune. A hankali ta zauna gefensu tare da cewa. "Umaymah Ina su Ummey". Kai Umaymah ta juya tana danne dariyarta tace. "Sun tafi Side ɗin ta". Da sauri tace. "Harda Mamma". Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa. "Bakiga tun da yamma Mamma da Rahma sukaje suka gyara komai na Part ɗinta ɗinba. Sabida Abban yasa an kawo mata sabbin kayan ɗaki sannan anyi duk abinda ya kamata". Jinjina kai tayi tare da cewa. "Ayyah". Sai kuma tace. "Bari inje in kwanta". Sai da safe tayi musu. Ta fita ta tafi. Ishma da Hibba ta samu kwance bisa gadonta tuni sunyi bacci da alamun Hibba wayama takeyi tayi baccin. Gefenta ta kwanta. Su kuwa su Umaymah sukaci gaba da hira. Sai kusan ƙarfe biyu ne da Afreen ta tashi Umaymah ta kaita ta bata mama tasha kana ta dawo da ita wai karta hana uwarta bacci. Alhamdulillah fa komai na tafiya yadda ya kamata rayuwa ta miƙa. Gsky tayi halinta. Jadda da Sitti da Babansu Aunty Juwairiyya sun koma. Haroon ma da Jannart sun da Hibba sun koma. Saura Umaymah da Mamma Aunty Rahma. Tuni Mamey ta koma Part ɗin ta. Hajia Mama kuwa ta tabbata mai suffa hudu kafar ladin kogi, hannun fiffigen tsuntsuwar Boleru idanu na Duji, sauran jiki na mutun. Ta zama abar kallo Abba kuwa ya danƙara mata saki. Affan kuwa yana nan lfy da ƴan uwanshi. Yanzu Shatu ta kusa wata ɗaya. Wanda ya kama satin su Umaymah uku da zuwa kenan. Abboi kuwa dasu Bappa sunje ga iyayen Rafi'a sun nemi aureta ga Al'ameen an basu kuma. Kana su Bappa kuwa sun nemawa Salmanu auren Hasfi an kuma basu. Zaune suke Umaymah Mamey Lamiɗo Galadima Abba A hankali Lamiɗo ya gyara zamanshi tare da cewa. "Toh Alhamdulillah komai ya wuce ya zama tarihi. Manufar taruwarmu anan a kan Masarautar Joɗa ne. Na gama zama da duk manyan fada mun gama tsaida zance duk kowa ya gamsu da batun Jabeer ya mulkin Masarautar Joɗa. Toh amman inda gizo ke saƙan kun san ɗan naku, na kira sarki Jalaluddin akan batun to shi mgn ɗaya yayi cewa yasan Jabeer mai biyayya ne ga Khadijah da take ƙanwar mahaifiyarshi ma bare ke Aisha da Habibullah da kuke iyayensa yace ya sani tabbas in kuka cewa Sheykh ya mulki masarautar Joɗa ku bashi umarnine ba shawaraba tabbas zai yarda". Cikin gamsuwa Galadima yace. "Haƙƙun wannan haka yake tabbas zai yarda bisa dole bisa umarnin iyayenshi". Cikin sanyi Mamey tace. "In kuna son in bashi umarni zan bashi kuma nasan zai min biyayya to amman meyasa baza'a bawa wani cikin ƙannen mahaifinshi ba sai shi". Shiru sukayi baki ɗayansu jin Lamiɗo na cewa. "Sabida ina son masararutar Joɗa ta tsarkaka ta rabu da duk wata al'ada daba addiniba. Na sani babu mai iya sarrafa Masarautar Joɗa ya juyata daga bahahuwa zuwa ba damiya ya kauda al'adar bidi'a ya wanzar da sunna sai shi. Zai gyara masararutar ta yadda za'a dena zalama da son cutar da juna bisa kujerar zai sauyata ta yadda sai mai cikekken ilimin addini ne zai iya mulkarta." Cikin gamsuwa Mamey tace. "In sha Allah zaku sameni mai biyayya bisa umarnin ku na in bashi umarni kuma na sani zai min biyayya". Cikin jin daɗi sukace to. "Allah ya shige mana gaba". Amin Amin sukace. Sai kuma suka nitsu jin Lamiɗo na cewa. "Alhamdulillah yanzu Ita matarshi ta kusa gama wonka tana gamawa zukjne Rugar Bani suyi kwana ɗaya daga nan su dawo su shirya suje Ƙasar Cameroon wurin iyayen Shatu kuma zasuje da Aliyu (Dr Aliyu) kenan da Basiru da Galadima domin su nemawa Jamilu auren Khadijah ƙanwar Shatu". Cikin jin daɗi Mamey tace. "Alhamdulillah to Allah ya kaimu". Amin Amin sukace. Sai kuma Abba yace. "Jalal kuwa mun gama mgna da Abban Haroon kan batun Jalal da Hibba". Cikin tsananin jin daɗi sukace. "Alhamdulillah daga nan suka watse taron. Washe gari su Umaymah suka koma. Alhamdulillah yau Shatu ta gama arba'in. Sosai Afreen tayi kuɓul-kuɓul da ita gwanin burgewa ta cika tayi kyau in ka ganta kamar yar wata biyu. Sosai kuwa Shatu tasha gyara na musamman daga wurin Ummi da Mameynta. A can ƙasar Cameroon kuwa. Ba'ana ya gama shirin dawowarsa kab. Wanda da azatonsa zai kaishi watanni uku sai gashi cikin wata biyu ya gama shirinsa. Kana ya kamo hanya. Yau Alhamis da misalin ƙarfe tara na dare yayiwa Rugar Bani diran miki...! Ban samu nayi editing ba By *GARKUWAR FULANI*[4/3, 8:36 PM] +234 806 559 0880: Dirar mikiya tare da tawagar shi wanda Baroon na ciki. A bakin titi motar ta sauƙesu kana suka ƙaraso cikin Rugar tasu da ƙafa. Dai-dai bakin mashigar Rugar Bani ɗin suka tsaya, sabida ganin uban gayan tafiyar ya tsaya. A hankali ya lumshe idonshi, tare da shaƙan sassayan iskan garin dake kaɗawa yana ratsa jiki. Hannunshi ya buɗe ya waresu, ya tanƙwashe kansa bisa wuyanshi cikin muryar dake nuni da gskyar abin dake binne can ƙasan zuciyarsa yace. "Uhummmmmmm ko wani ɗan adam yanada yanki na musamman da yake cikin bugun zuciyarsa. Ni kuwa Rugar Bani ce bugun zuciya ta. RUGAR BANI itace mahaɗin soyayya da Mata. Allah ka sani kaine ma sannin sirrin zuciyata ina son Shatu son da ni kaina ban san adadinshi ba. Son da bana yiwa kaina shi. Mata itace cikon farin cikina ban taɓa son wani abu a duniya sama da Shatu ba ya Allah ka yafe min kura-kuraina na baya, ka bani ikon samun Shatu, ka tsare min imanina duk da nasan. Ban fiye aikata aiyukan gsky ba a rayuwata. Amman son Shatu gsky ne a cikin zuciyata kuma tuban da nayi gsky ne. Ya Allah ka jiƙaina ka tausaya min ka cika min burina ka ƙaddara Mata ta tabbata matar aure na, in rayu da ita inuwa ɗaya. Domin itace sanyin idaniyata in ka samar min ita rayuwata zata inƙanta." Ya ƙarashe mgnar cikin rauni da rawan muryar kana wasu irin tafasassun hawaye suna masu kwarya mishi. Sheykh kuwa dake jin duk abinda Ba'ana yake faɗa bisa kiran da Baroon yayi mishi. Da ƙarfi ya rumtse idanunshi, yana mai jin wani irin azabebben kishi mai masifar zafi da ƙuna yana caccakar zuciyarsa. So yake ya tashi yaje suyi hira da Mamey'nshi Amman gaba ɗaya yanayi shi ya hautsine kishi ajalin maza. Domin in mu mata kumallonmu ne tofa su maza yakan iya karsu. A can Rugar Bani kuwa, cikin rauni Ba'ana yaci gaba da magana cikin sanyin jiki da raunin da bai taɓa riskar shi ba yace. "Na sani na yarda akan komai ni bazan amsa sunan mai gsky ba ko mai tausayi amman akan tubana da Shatu ni mai gsky ne! Ya Allah ka mallaka min Shatu na yarda na gane babu wani sihiri ko tsafi ko boka ko dodon tsafin da zai mallaka min ita sai kai sarkin da bashi da tamka sarki buwayi gagara misali sarkin kowa na Annabi baban zara". Kawai sai ga hawaye shar-shar suna kwaranya daga idanunsa rusunawa yayi ya durƙusa bisa guiwowinsa ya kafa kanshi cikin sassayan yashin garin. Ya saki wani irin raunataccen kuka. Gaba ɗaya yaran nashi shiru sukayi cikin tarin mamaki da tsantsar gaskata soyayya ba ƙarya bace shirya kuma ta Allah ce dan tuni sun san yabar komai na tsafi saidai wasu abubuwan dake jikinsa basu karyeba kamar ɓacewa har yanzu yana iya ɓacewa. Saida yayi kuka mai tarin yawa kana suka miƙe suka nufi cikin gari. A tsakiyar wurin garken al'ummar Rugar Bani ɗin ya tsaya ya juya gabas da yamma kudu da arewa. Kana a hankali yace. "Duk da son hanaku ci gaba da nakeyi, ya rigada Allah ya lamunce muku kuna ci gaba da izininsa." Kai tsaye garken Bappa ya nufa bayan duk ya sallamesu sai Baroon kawai. A hankali yasa ƙafarshi ya ratsa tsakiyar garken cikin ɗan ɗaga murya yace. "Bappa". Cikin wani irin masifeffen tashin hankali da firgici Bappa ya miƙa tsaye. Tare da cewa. "Na'am Ba'ana". Giɗi da Seyo ne dake gefenshi suma suka miƙe da sauri cike da tsoron me zai faru. A hankali ya zame ya zauna gaban Bappa kana a hankali yace. "A nan a tsakiyar garken nan na rayu da ita tsawon shekaru goma sha biyu, na rayu da sonta kan gsky. Koda komai ƙaryane Bappa ka yarda ina son Shatu son da bana yiwa kaina". Cikin sauƙe ajiyan zuciya Bappa ya zauna jiki a mace hakama su Gidi da Baroon. Cikin nitsuwa yace. "Ba'ana yaushe ka dawo?". Murya na rawa yace. "Bappa yanzu na shigo Rugar Bani ko gidanmu ban jeba, ina so ka yarda cewa da gaske ina son Shatu". Yadda yayi mgnar yasa Bappa jin wani irin rauni da tausayinsa a hankali yace. "Na yarda Ba'ana na sani kana son Shatu". Da sauri yace. "Bappa ka tuna kun min al'ƙawarin aura min ita". Da sauri Bappa yace. "Na tuna Ba'ana ban manceba to amman al'ƙawarin Allah ya ture namu ya rigada Allah ya tsara Shatu ba matarka bace." Cikin sauri ya miƙe yana cewa. "A'a a'a bana son jin haka". Yana faɗin haka yana yarfa hannun a haka ya nufi cikin gari Baroon na biye dashi a baya. Shiru Bappa da su Giɗi sukayi cikin tarin rauni. Shi kuwa Ba'ana a tsakiyar gidansu ya zauna gaban Bukar da Bugulu mahaifiyarshi. Cike da mamaki suke kallonsa jin yadda yake kuka babu sassauci. Cikin tsananin tausayi da so irin na iyaye da yaransu. Sukayi kanshi cikin kula Bugulu tace. "Ba'ana yau ranar farin cikine a garemu ba ranar kuka ba. Kada kayi kuka muna cikin farin cikin ganin juna". Ba mgn sai kuka. Da sauri Bukar ya jawoshi jikinshi tare da cewa. "Gaya min me ya saka kuka haka?". Cike da rauni yace. "Karo na forko dai a rayuwata Baba zan roƙeku in kuna da hali ku aura min Shatu ku dawo da ita gareni". Ganin tsananin tashin hankali da yake cikine yasa sukace. "To kwantar da hankalinka ina shine kawai burinka zamu dawo maka da farin cikin ka". Da sauri yace. "Allah Baba?". Kai ya gyaɗa mishi cikin tausayinsa. Shi kuwa jin hakane ya zame ya kwanta ya ɗaura kansa bisa cinyar babanshi yana sauƙe numfashin kuka shima Baroon gefe ya zauna. Sheykh kuwa cikin tsananin tashin hankali na kishi ya rumtse idanunshi da ƙarfi. Kana ya taune lip ɗinsa na ƙasa. Shatu ce zaune ita da Mamey har cikin ɗakinta Afreen na hannun Ummi. A hankali Mamey tace. "Shatu". Da sauri ta ɗago kanta ta kalli Mamey tare da cewa. "Na'am Mamey na". Gyara zama tayi tare da cewa. "Shatu batun mijinki ne, nake son kisa baki a lamuransa". A hankali tace. "Mamey waɗannen lamuran ne?". "Shin kina son Mijinki ya mulki masarautar Joɗa?". Ta jefa mata tambayar kai tsaye. Da sauri Shatu ta zubawa Ummey nata ido ta karanci yanayinta na ƴan wasu daƙiƙu kana a hankali tace. "Mamey in dai kuna so ya mulka to nima zanso, hakan sai dai ina tsoro kada a sabautamu". Da sauri Abba dake shigowa yace. "A'a Shatu in sha Allah babu komai babu abinda zai faru sai al'khairi. Burinmu ya mulki masarautar Joɗa ne dan ya gyara ta zama Tsarkakkiyar masarauta mai wadatar sunna da ƙarancin al'adun bidi'a". A hankali ta gyaɗa kanta tare da cewa. "Shi kenan Abba Allah ya sanya al'khairi yasa hakan ya zama ci gaba ga Musulunci da musulmai". Amin Amin sukace. Kana ta ɗan yunƙura zata tashi. Ganin Abba ya shigo yana amsar Afreen tare da cewa. "Ƴar lukuta". Murmushi tayi kana ta kalli Mamey dake cewa. "Ki fara nuna mishi amfanin ya mulki masarautar bisa hikima ta yadda zaki sa mishi abin a ransa ba tare da yaji dole akayi mishi ba". Da sauri tace. "Toh Ummeyna". Har ta isa bakin ƙofar kuma sai ta tsaya jin Mameyn na cewa. "Umurnine fa Shatu ki fara daga yau". Ajiyan zuciya mai sauƙi ta sauƙe tare da cewa. "In sha Allah kuwa Mamey". Tana fita Ummi na biye da ita a baya. A bakin ƙofar shigowa suka haɗu da Sheykh shida Affan. Wuce sukayi kana su kuma suka fita. Kai tsaye har bedroom ɗin suka wuce. Suna hira ta tsakanin iyaye da yaransu. Da sauri Sheykh ya ɗan ɗago ya kalli Mameynshi tare da sakin murmushi jin tana cewa. "Jabeer wannan gemun haka ka ɗan rageshi mana ga saje ga gemu". A hankali yace. "Mamey bai min kyau bane?". Da sauri tace. "A'a wlh yayi maka kyau sosai ma fiye da zaton mai zato sai dai yasa kayi kwarjini da yawa ni kaina sai inji kana min kwarjini". Dariya mai sauti yayi tare da cewa. "Uwa mai daɗi Allah ya bar mana ke Mameynmu". Dariya Abba da Affan sukayi tare zubawa Sheykh ɗin ido jin yana cewa. "Toh gemu da saje ku kiyayi kanku da sa Mameyn Jabeer ganin kwarjini mai yawa". Jamil da Jalal da Yah Jafar Imran dake shigowa ne suka haɗa baki wurin cewa. "A to a haɗa harda mu dan muma kansu mana kwarjini yana mana yawa Hamma Jabeer". Murmushi yayi kana suka shigo suka zauna suna hira cikin jin daɗi. So a nanne yaji kaso 30 cikin 100 na azabebben kishin daya cakeshi ɗazu ya ragu. Ita kuwa Shatu suna shiga kai tsaye bedroom nashi ta wuce. Ta gyara komai ta killace komai ta ɗan ƙara gudun AC kana tasa turaren ɗaki Tuch me mai sassayan ƙamshi. Kana ta dawo ɗakinta, kamar kullum bayan tayi wonka ta fitone. Ummi ta shigo riƙe da kasko da rushi kaɗan a ciki. Gaban gadon ta ajiye kaskon tare da jawo kujerar ƴar tsuguno mai rami ta turaren gyara ta ɗaura kujerar kana ta jawo wani kolba dake kan mirror ta buɗe tasa hayaƙi mai ƙamshi ya fara tashi. "Zauna". Tace tana fita. Da sauri Shatu ta zauna bisa kujerar tana mai jin yadda ƙamshin yake game jikinta, Tabbas wannan turaren tana jin daɗin shi ita da kanta da kanta. Dan ko fitsari tayi sai taji yana ƙamashi sai dai tana ji yana tsuketa. Bayan kamar 30 minute Ummi ta kuma shigowa riƙe da cup da madarar gongoni a ciki mai sanyi da haɗin *Garin maɗi.* Motsashi tayi da cokali tare da cewa. "Yauwa amshi ki shanye". Ba musu ta amsa sabida tana masifar jin daɗin haɗin. Bayan ta shane ta ajiye cup ɗin kana ta matso gaban dreesing mirror'n humra mai sanyin ƙamshi ta murza a jikinta tare da zura wata tattausar rigar bacci royal blue mai ɗigo-ɗigon fari. Rigar iya karya guiwa. Turaren laylaytul sahrah ta fesa. Kana ta zura jibajinta har ƙasa. Su Sheykh kuwa bayan sun gama hirane. Yasa hannunshi ya amshi Afreen da Mamey ke miƙa mishi tare da cewa. "Kaita tasha mama". To yace. Tare da amsarta ruggume ta yayi a jikinshi tare da cewa. "Sai da safe". "Allah ya bamu al'khairi". Amin yace yana mai fita, sai kuma ya tsaya jin Abbanshi na cewa. "Kaje wurin Lamiɗo akwai takardun aiken masarautu da yakeso ya baka". Cikin bin umarni yace. "Toh". Yana fita Part ɗin Lamiɗo ya nufa. Gefenshi ya zauna ruggume da ƴarsa cikin kula Gimbiya Aminatu tace. "Kai ɗa da daɗi ko Sheykh". Murmushi yayi tare da kallon Afreen dake jujjuya ido tana lumshesu alamun bacci zatayi yace. "Uhumm sosai ma kuwa ɗa kam da daɗi Gimbiya Aminatu". Dariya sukayi baki ɗayansu. Shi kuwa kissing goshinta yayi tare da sa mata al'barka. Kana ya kalli Lamiɗo a fakaice yace. "Abba yace akwai takardun da zaka bani". Eh yace tare da miƙo mishi wasu takardu liƙe cikin wani, kekkyawan mazauni tare da tambarin hatimin masarautar Joɗa a jiki. Hannu yasa ya amsa tare da cewa. "Toh na menene?". Cikin tsareshi da ido Lamiɗo yace. "Aiken Masarautar Joɗa ce zuwa ga sauran masarautun gargajiya na Arewacin Nigeria, zaka kai musu ɗaya baya ɗaya". Da sauri yace. "Yaushe kuma aiken menene?". A daƙile Lamiɗo yace. "Gobe sai kaje ka dawo zan gaya maka na menene. Waziri, Wambai, Galadima, Chiroma, Durbi, duk sun sa hannun". Taɓe baki yayi tare da cewa. "Sai dai kuma ai kai ba ubana bane da zaka wani tirsasani ka sani abu dole. Harda wani wai gobe". Ya ƙarashe zancen yana miƙewa tsaye riƙe da takardun. Shi kam Lamiɗo murmushi kawai yayi ya bishi da ido. Kai tsaye Part ɗin su ya nufa. Ba kowa a falon haka yasa ya rufe ko ina ya kashe duk kayan wuta. Kana ya wuce Side ɗinsa ruggume da Afreen. A hankali yaja sassayan numfashi tare da shaƙar ƙamshin ɗakin. Wutan ya kunna, ido ya lumshe ganin komai fes-fes. A can tsakiyar gado ya kwantar da Afreen tare da gyara mata kwanciyarta dan tuni tayi baccinta. Addu'o'in yayi ya tofa a tafin hannunsa ya shafa mata. Bathroom ya wuce. Wonka yayi mai rai da lfy kana ya kimtsa cikin wasu tattausan riga da wondo pink guava color da ratsin Royal blue masu ɗan karen taushi. OudKareem ɗinsa ya fesa kana ya fito. A hankali ya ɗan zauna bakin gadon ba tare daya kashe wutanba. Miƙe sawunshi yayi bisa gadon tare da ɗan zamewa ya kwanta rigingine. Ido ya rumtse a hankali tuno kalaman Ba'ana a kan Shatu. Ita kuwa Shatu a hankali taja ƙofar ɗakinta ta rufe Sannan ta nufi Side ɗinsa. A hankali ta tura ƙofar tare da cewa. "Assalamu alaikum". buɗe idonshi yayi tare da zuba mata su. Murya can ƙasa yadda bata jiba yace. "Wa alaikassalam". A zahiri kuma sai ya haɗe fuska tare da tsuke bakinshi. Motsowa ta inda yake tayi tare da cewa. "Yah Sheykh kayi bacci ne?". Bai kulata ba kuma bai ɗauke idonshi a kanta ba. Ƙara matsoshi tayi tare da zare hijabin ta ninkeshi tana cewa. "Hamma Jabeer yau ba mgna ne". Bakinshi ya taɓe mata. Wanda hakan ya tabbatar mata yana fushi da itane wanda tasan fushin bai rasa nasaba da yadda yake buƙace da ita take kauce mishi. Ajiye hijabin tayi a gefe. Sannan ta ɗan matso gaban shi. Yatsun ƙafarshi ta ɗan ja tare da cewa. "Nooryat". Idonshi ya cire a kanta, yana mai ji kamar ya ruggumeta. Fahimtar dafa gaskene fushin yasa ta ɗan hauro saman gadon. A hankali ta sunkuyo kanshi tabi tsawon shi. Hannunta ta cusa cikin rigar tashi, ta fara mishi tafiyar tsutsa ta gefe da gefen cikinsa. Kana ta haɗa fuskarshi da nata. A hankali ta kamo lip ɗinshi na ƙasa ta tsotsa tare da fidda sautin. "Shyyyyuuyyh Yan Sheykh na tuba". Miƙa mai tsawo yayi jin yadda takeyin ƙasa da hannunta. Kana ta haɗe bakinsu wuri guda. Wani irin lasa tayiwa harshensa wanda yasa yaji. Sheykh ɗin shi ya amsa amo ya miƙe cike da zalama. Da sauri yace. "Barni". Cikin raɗa tace. "Naƙi". Kanshi ya ɗan ɗago tare da tsareta da ido. "Sai kuma ya tashi zaune yana riƙo hannunta jin tana kwance mishi zariyar wondo. Da sauri yace. "Wai menene hakan?". Cikin tura baki tace. "Abuna zan nema". Bai san lokacin da dariya ta kubce mishi ba ganin yadda tayi mgnar cikin dariyar yace. "Abun naki kuma babu inda zaki nemo shi sai cikin wondona?". Ya ƙare mgnar tare da jawota jikinshi ya ruggumeta gam-gam yana kissing wuyanta. Cikin jin daɗin ya huce da kuma son fara shigar mishi da ra'ayin sarauta tace. "Mai martaba Lamiɗo Jabeer. Allah ya nuna min randa zaka mulki masarautar Joɗa ka rabamu da duk wasu al'adu marasa kan gado". Cikin yi mata kallon shauƙi yace. "Yoh al'adun gida nama ai kin nuna ban isa in hanasuba bare na masarautar Joɗa". Cikin cusa hannunta cikin ƙugunshi tace. "Al'adar gidanka kuma wacce ta isa tafi ƙarfin ka hanata". Hannunshi yasa yana kunce igiyoyin dake sarkafe gaban rigarta murya can ƙasa yace. "Al'adar wai in mace ta haihu sai ta kwana arba'in kafin ta bari mijinta ya kusanceta. Kullum a wahale nake kwana ke ko a jikinki kina sane dai al'adace ba addiniba amman kikayi tauye min haƙƙina". Da sauri tace. "Toh ai hakanma Al'adar masarautar Joɗa ne ni yamin ka sani ma". Ta ƙare mgnar cikin gimtse dariyarta na ƙaryar da tayi na wai Al'adar masarautar Joɗa sai bayan arba'in za'a koma turaka, tayi ƙaryar ne kuma sabida ta samu ta ƙara cusa mishi tsanar al'adun da son kaudasu. Ai kuwa cikin kwaffa yace. "Zancen banza, ai wannan aikin jahilci ne ya za'ayi nida matata kuma ace sai wata Al'adar masarautar Joɗa ta bani izini da damar kusantarta". Murmushi mai cike da ƙauna tayi tare da cewa. "Toh ai shine muke fatan ka mulkemu ka kauda ire-iren waɗannan abubuwan". Tayi mgn tana kai bakinta gareshi. Wani irin dogon numfashi yaja tare dasa hannun duka biyu ya tallabe kanta. Tare da fidda sautin. "Shiyyyyyy Ahhhh Aishh". Sosai ta gigitashi da salon da tasan yana masifar so. Saida taga ya gama narkewa ta ɗan janye kanta kana ta ruggume shi a hankali ta kai bakinta kusa da kunnenshi murya can ƙasa tace. "Yah Sheykh ka mulki masarautar Joɗa dan Allah da manzonsa dan son samar da gyara". Cikin yanayin da bai san hali da duniyar da yake cikiba yace. "Tohhhhh Aish". Da sauri tace. "Kayi al'khairi". Jikinshi da muryarsa kab na rawa yace. "Nayi al'ƙawarin". Ai kuwa sai ta mirgina ta jikinshi da kyau. Bayan ta cire rigarta. Wani ɗan raunataccen ƙara ta saki sabida. Zafin da taji yayin ziyartarsa wanda dole ta janye ta kwanta tare da cewa. "Bazan iyaba". Jikinshi na rawa yayi mata rumfa. Da ƙarfi ta ɗan saki ƙara sabida ji tayi kamar yau ta taɓa sanin namiji dan gyaran da Ummi da Mamey da Umaymah sukayi mata ya haɗawa. Hannunta ta ɗan yarfa cikin raki tace. "Wash Honey". Cikin yanayin shiga duniyar maji daɗi Yah Sheykh ya rinƙa sanya mata al'barka". Cikin nitsuwa cikin sararin samaniya murya a narke tace. "Yah Sheykh zaka mulki masarautar Joɗa ko". Da sauri yace. "Eh eh ehhhhhhhhhhhhhh Aishhhhh". Sabida yana gab da jin numfashin sa na shirin ɗaukewa in bai buɗe bakinshi ba... Bayan komai ya lafane sunyi wonka sun dawo suna konce. Ajiyan zuciya mai nauyi ya sauƙe tare da shafa maransa kana a hankali yace. "Alhamdulillah naji sakayau". Sai kuma ya kai hannunshi bisa cikinta tare da cewa. "Allah yasa ƙanwa ko ƙanin Afreen ya kasantu". Cikin sauƙe numfashi tace. "Ai ni dai tunda ka yarda zaka mulki masarautar Joɗa ko duk shekara zan haihu ba matsala". Da sauri yace. "Toh yaushe kuma mukayi haka dake?". Cikin kwaɓe fuska tace. "Yanzu mana". Juya mata baya yayi yana gyarawa Afreen kwanciya yace. "Uhumm to ke waya ce miki al'ƙawarin a irin wannan lokaci yana aiki, ai ko al'ƙalai basa amsar shaida da al'ƙawarin mai fataucin kayan daɗi". Da sauri tace. "Yah Sheykh al'ƙawarin fa kayi". Jawota jikinshi yayi tare da cewa. "Kai sake wannan al'ƙawarin Aish, yoh ai sai ince miki na baki Makka da madina ma a cikin wannan yanayin ke baki san Y.M.D.G. bane". Dariyar da take dannewa ne ta kubce mata. Haka yasa ya lakace hancinta tare da cewa. "Ja'ira wato dariya ma zakiyi min". A haka dai sukayi bacci liƙe da juna. Washe gari da asuba suna dawowa masallacin. Abbanshi yake ce mishi. Wai yayi maza fa ya fito su tafi shi ɗaya ake jira. Sosai yayi mamakin ashe dama da gaske Lamiɗo yake yau zaiyi tafiyar. Bisa dole bisa umarnin iyayenshi ya fito suka tafi. Shatu nata bashi baki. Ta kaicinsa ɗaya da aka hanashi tafiya da ita. Alhamdulillah yayi tafiyar kai takardun murabus ɗin da Lamiɗo zaiyi ya bashi mulki ga masarautun gargajiya na Arewacin Nigeria. Gaba ɗaya sunyi na'am da haka sun sa hannun. Duk da shi baima san takardun me bane dan bai buɗeba. Randa ya isa masarautar su Umaymah kuwa daɗi kamar zai kasheta. Kwanashi goma ya gama zagaye kab masarautun ya dawo dasa hannun da buga hatimin dukkan masarautun. Koda ya dawo da Lamiɗo ya gani saida yayi ƙwalla sabida zallan farin cikin ganin yadda ya samu haɗin kan kab masarautu har aka ƙara da yabawa sarki maijiran gadon. Shida Shatun kuwa a ranar suka tabbatarwa juna. Sunyi bege da kewar juna. Kasan cewar ranar Al'hamis ya dawo. Tun a daren Shatu ke ta masa batun. Zuwa Rugar Bani. Toh yace dai ba matsala ran asabar zai kaita. Mamey ma da Ummi dasu Jalal duk sunce zasu je. Ba'ana kuwa zuwa yanzu gaba ɗaya. Ya zama wani irin al'ummar Rugar Bani kuwa sun cika da mamakin ganin yadda ya sauya jami'in salla baya wuceshi yayi sanyi ya sauya kamar ba shiba abu kaɗan sai hawaye. Yauma kamar kullum yaje ya samu Bappa a garkensa bayan ya gama magiyar a bashi Shatunsa Bappa ya babbashi haƙuri. Sai kawai ya jingina kanshi da jikin itacen nim dake gefenshi. Murya na rawa yace. "Zan sake barin Nigeria'n kuma tabbas da Shatu da duk dabbobinmu Rugar Bani zanyi awon gaba dasu muddin baku dawo min da ita cikin lumana ba." Ya ƙarashe mgnar cikin alamun wai baraza zai mishi. Ganin yadda Bappa ya zuba mishi idone yasa yaci gaba da cewa. "Wlh Bappa mutuwa ce kaɗai zata rabani da Mata in haƙura, bayan mutuwa babu abinda zai rabani da ita na barshi. Tabbas zan saceta. Sabida itace cikon farin cikina Mata ce burin duniyata". Ya ƙare mgnar hawaye na zuba. Kai Sheykh ya jinjina tare da cewa. "Uhumm da kuma ita zanyi maka tarko ka shiga hannun hukuma ba taƙadiri". Shi kuwa Bappa da Baroon shiru sukayi suna jin yadda sautin kukansa ke tashi. Washe gari ranar asabar. Misalin ƙarfe goma na safe. Tsaye suke gaba ɗayansu cikin shiga ta al'farma. Jalal da abokanshi sojoji mutun huɗu su motarsu da ban. Yah Sheykh kuwa shi yake jan motar da kanshi Shatu na gefenshi Ummi da Mamey na baya. Saratu kuwa tana motar Aunty Juwairiyya da Yan Jafar da yaransu. Jamil da Affan kuwa motarsu ɗaya a haka suka nufi Rugar Bani. Ƙarfe sha ɗaya dai-dai na safe tayi musu cikin Rugar Bani. Cikin wani irin masifeffen zabura Ba'ana ya tashi zaune. By *GARKUWAR FULANI* 👆🏻 👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 GARKUWA Page 11 Tare da kallon zoben azurfan dake yatsarsa wacce irinta ya sawa Shatu a yatsarta wanda in suna kusa da juna zasuyi ta yin haske. Wani irin dariya mai cike da jin daɗi yayi tare da cewa. "Mata". Ya faɗi yana mai miƙewa tsaye ya nufi ƙofar gida. Su Sheykh kuwa a hankali sukayi parking cikin nitsuwa suka fara fitowa. Ummi na Ruggume da Afreen yar wata biyu tayi kuɓul-kuɓul da ita gwanin burgewa da sha'awa gashin kanta yana kwance lib-lib kamar ɗiyar larabawa. Wasu irin tattausan kayane masu masifar kyau da taushi da tsada aka kimtsata a ciki rigar mai ɗan karen kyau. Yellow and Pink color masu taushi sai ɗan banɗanan nashi mai kyau da akasa mata a kanta yayi cib dashi. Sai Safar kafarta yellow sai takalmanta pink. Kana towel din da aka ninketa ciki shima pink color. Sai wani irin fitinenne ƙamshi mai daɗin shaƙa da takeyi. A hankali suka fito baki ɗayansu. Ajiyan zuciya Mamey da Shatu suka sauƙe tare da shaƙan daddaɗan iskan Rugar tasu. Kowa ya bar gida tabbas gida ya barshi. Da sauri Ummi da Aunty Juwairiyya da Sara suka matsosu. Mamey ce a gaba duk suna biye da ita a baya. Sheykh kuwa shine a gaba Yah Jafar da Affan dasu Jamil na biye dasu. A cikin gidan kuwa, Junainah ce riƙe da hannun Yah Giɗi tana ɗan tsalle-tsalle tare da cewa. "Yauwa Ya Giɗi muje lambu ka ciro min inabi mana". Gyara riƙon da yayiwa hannunta yayi tare da cewa. "Ba Junaidu ya kawo miki wani ba ɗazu". Da sauri tace. "A a ai na ajiyewa su Adda Shatu da Ummey na shi. In sun iso zan basu". Juyowa yayi ya ɗan kalleta tare da cewa. "Toh ai kije kawai kici abunki, su tun jiya da yamma bappa yasa na ciro musu komai". Dai-dai lokacin kuma suka iso ƙofar gida. Da sauri Junainah ta saki yatsarsa tare da cewa. "Oyoyo Ummey na Adda Shatu na". Tayi mgnar tana nufar inda suke a guje. Da sauri Shatu ta buɗe mata hannu ta faɗa jikinta. Ruggume juna sukayi suna dariya. Giɗi kuwa da sauri yace. "Kai maraba lale sannunku da zuwa". Ya ƙare mgnar yana isa gabansu Sheykh. Da sauri Bappa ya fito jin muryar Junainah na cewa. "Oyoyo Ummey na". Ai kuwa a cikin zauren yayi kiciɓis dasu Ummey cikin jin daɗi yace su isa. Kana ya wuce wurinsu Sheykh yayi musu jagora har barandar ƙofar ɗakin shi. Shatu kuwa kai tsaye ɗakin Ummey ta buɗe musu suka shiga. Inna Amarya kuwa daɗi kamar ta haɗiye haƙorinta Allah ya sani sun shaƙu da Ummey tayi kewarta ainun. Bayan sun zauna ne ta kalli Shatu tare da cewa. "Shatu taso kizo ki kaiwa su Sheykh ruwa". Da sauri tace. "Toh Inna Amarya". Kana tabi bayanta. Tiren saƙar kabar dake cike da fruits danginsu Ayaba, inabi, tupa, yazawa, goiba, mangoro, danino, masu masifar sanyi kasan cewar cikin tulu suka kwana. Sai kuma ƙwaryar damemmen fura da nono da zuma. Da fefeyin kayan ya'yan itatuwa ta rufe ƙwaryar kana ta ɗauki kananan ƙore da ludayayeyin suma masu kyau, ta riƙe, kana ta miƙe ta nufi ƙofar Bappa. Ita kuwa Inna Amarya ta ɗauki sauran ta nufi cikin ɗakin Ummey dashi. A hankali ta ratsa gefen Sheykh ta ajiye kwaryar a tsakiyar su. Kana a hankali tace. "Bismillah ga ruwa". Murmushi mai yelwa Sheykh yayi tare da cewa. "Mun gode". Jalal kuwa hannunshi yasa ya ɗan tsinko gefen nonon inabi kana ya fara kaiwa bakinshi yana tsinka. Ido ya lumshe tare da cewa. "Wai ni kam Adda Shatu kuna da Fridge ne a garin nan". Dariya sukayi baki ɗayansu. Bappa kuwa miƙewa yayi ya fita yana cewa. "Toh bari inje nan kusa kafin kusha ruwa". To sukace sanin bazai zauna ba. Ita kuwa Shatu ruwa ta koma ta kawo musu cikin kwanon sha na asalin gargajiya. Ajiyewa tayi tana kallon Affan da yake lumshe ido yana shan kindirmon. Jamil kuwa Ayaba yakeci. Yah Jafar ma nonon yake Sha. Shi kuwa Sheykh dabinon yake ci. A hankali ya kalleta tare da cewa. "Ni zan sha nonon amman zumar bata ji minba a ƙaro min". Da sauri tace to tare da miƙewa a nitse ta shiga cikin ɗakin Bappa. Ido ya ɗan zuba mata lokacin data fito riƙe da akoshi ta ajiye a gabanshi tana buɗe wa. Da sauri ya ɗan jawo akoshin ganin asalin farar zuma da sakarta, yatsarsa yasa ya laso yasa a baki. Girarshi ɗaya ya ɗan ɗaga mata tare da cewa. "Kefa baƙuwa ce, zaki shige musu har ɗaki". Da sauri tace. "Tab baƙuwa kuma ni da gidanmu". Yana mai lasan zumar yace. "Gidanku na can masarautar Joɗa". Murmushi tayi kana ta miƙa ta koma wurin su Ummey. Sosai suka sake anata hira da dariya ga sanyin safiya. Ga yanayin garin ga farin ciki. Junainah kuwa tana ruggume da Afreen tanata kiciniya da ita. Ganin Inna Amarya ta koma Kitchen yasa Shatu Binta a baya. "Inna Amarya me kike dafa mana ne?". Juyowa tayi tana kallonta bayan ta sauƙe tukunyar kana tace. "Tuwone miyar kase da man shanu. Sai Danderun Zabbi". Da sauri ta matso tare da cewa. "Kai Inna Amarya kin biyani dama na dade banci miyar Kase ba". Gefenta ta zauna tare da jawo akoshin dake gefenta babba da karami. Danderun ne a ciki sai tururi da ƙamshin yake zubawa. Da sauri ta rufe. Kana ta buɗe manyan da sukafi wannan tuwon ɗanyar shinkafane anyi mata asalin kwasan gargajiya an lailaye samanshi da man shanu. Rufewa tayi. Tana kallon Inna Amarya data buɗe tukunyar miyar data sauke. Murmushi tayi tare da cewa. "Wannan miyar harda ta gobena". Murmushi tayi tare da cewa. "Toh Shatu yanzu dauki tuwon da Danderun ki kai musu sai kizo ki kai musu miyar. Da sauri tace to. Ta ɗauka ta kai musu. Ta dawo ta kai nasu Ummey kana tazo. Ta zauna tana kallon yadda take zuba miyar. Ƙwaryar dake gefenta ta buɗe. Nanma tuwon ne da alamun na su Yah Giɗi ne. Gefe kuma kwanukan Bappa ne. Motsowa tayi tana cewa. "Inna Amarya su Ummey duk basu wani damu da nama, Amman waɗan can kuraye ne. Irin Jalal da Yayanshi sunfi son duk loma su tsakura da nama". Dariya Inna Amarya tayi tare da cewa. "Yoh kice irin Giɗi ne su". Dariya tayi da sauri ta juyo jin Yah Giɗin nata dake Ruggume da Afreen yana cewa. "Toh in banda irin Shatu wa zaiƙi nama, ko sunanshi mafa yana da daɗin ji". Murmushi tayi tuno lokacin da ya dirka mata dundu a tsakiyar bayanta sabida ta hana a yanka tsuntsuwar Boleru wacce da Ummey aka yanka". Ita kam inna Amarya naman ta kara musu. Ita ta dauki nasu Ummey ta kai musu. Ita kuwa Shatu ta kaiwa su Sheykh. Murmushi tayi ganin tuni Jalal ya buɗe akoshin Danderun. Yana ganinta yace. "Yauwa Adda Shatu a kawo mana tray'n mana ko plate". To tace. Kana taje ta kawo musu tirurruka guda biyu. Ajiyan zuciya Sheykh ya sauke tare da cewa. "Wai anya kuwa kunci abincin safe?". Da sauri Affan yace. "Bamu ciba". Murmushi Yah Jafar yayi tare da cewa. "Koma dai munci ai yanzu hantsi ya duba ludeyi. Dan haka Affan sa mana". Allah sarki rayuwa mai daɗi ba girman kai. Shatu ta raya a ranta. Shi kuwa Sheykh dariya yayi. Shi kuwa Affan ludeyin duma yasa ya zuba musu tuƙeƙƙen tuwon nan. Kana ya zuba musu miyar kasen da yaji nama da kifi banda a saman tuwon. Jalal kuwa ƙara min tray'n ya jawo. Danderun ya juye a ciki fiye da rabi. Ita kam Shatu juyawa tayi ta tafi. Shi kuwa Sheykh ido ya zubawa Affan, Jamil, Yah Jafar. Sun haɗa hannu cikin kono ɗaya suna cin abinci cike da gamsuwa da shaƙuwa da ƙaunar juna. Haka nan yaji wani irin daɗi. Jalal ne ya ɗan matso gabanshi da tray'n tare da cewa. "Ni dai Allah ya sani ba cin tuwo zanyiba, Hamma Jabeer muci Danderun". Jamil ne ya ɗan kalleshi tare da cewa. "Manyan kuraye ba". Eh ɗin Jalal yace kana sukaci gaba da ci suna hira. Ita kuwa Shatu bakin kitchin ɗin ta koma. Gefen Yah Giɗi ta zauna. Tare da sa hannunta cikin akoshin abincin da yake cin. Kana ta kalli Junainah dake gefenshi riƙe da Afreen tace. "Junnu kaita wurin Ummi kizo muci mana". Kai ta jujjuya tare da cewa. "Ni na koshi naci da Ummey na a ɗaki". A hankali ta ɗan juyo ta kalli ƙofar ɗakin Bappa jin Sheykh yayi gyaran murya. Ido ya juya mata, alamun me takeyi. Cikin jin daɗin yanayin tace. "Ina cin abinci da Yah Giɗi na". Murmushi yayi tare da juya kai. Shi kuwa Yah Giɗi dama ya kaiwa abokan Jalal dake can ƙofar gida zaune kan taburma a gindin bishiya. Suma sunci. Haka dai sukaci suka sha sukayi haniƙan. Kana Shatu ta tattare komai ita da Junainah. Bayan sun gama ne Bappa ya dawo nan suka sake sabuwar gaisuwa kana suka ci gaba da hira. Sannan sukaje sukayi sallan azahar a masallacin ƙofar gidan Arɗo Bani. Kana suka dawo sukaci gaba da hira. Shi kuwa Ba'ana yana fita. Ya kalli Babanshi cikin zaƙuwa yace. "Baba Mata tana Rugar Bani tabbas tazo". Da sauri Bukar yace. "A a Ba'ana banji lbrin ba". Da sauri yace. "Ga nan zobe na yana gaya min kana cemin a a". Sai kuma kawai ya juya ya nufi. Bakin garin inda yasan zai samu Baroon yana zuwa yace. "Baroon taso muje gidan malam liman indan mun isa ni zan zagaya ta baya kai kuma ka shiga ta ƙofar gida. Ina da tabbacin yau Mata na nan kuma yau zan tafi da ita. Yanzu bari in kira su Droo baki ɗayansu." Da sauri Baroon yace to. Kana sukayi maza suka nufi cikin garin. Shi kuwa Ba'ana ya kira duk sauran yaranshi suka biyo bayanshi. Ta bayan gidan suka zagaya. Shi kuwa Baroon ya shiga cikin gidan kai tsaye sabida sanin Sheykh na ciki kuma zaije ya bashi bayani ne. Yana shiga kuwa Sheykh ya yafi toshi da hannu da sauri ya iso. Bappa kam ido ya zuba musu jin Baroon nayiwa Sheykh duk bayanin abinda Ba'ana yake shiryawa. Murmushi Sheykh yayi tare da cewa. "Yanzu yana bayan gidan nan kenan?". Da sauri yace. "Eh dashi da sauran yaran". Da sauri Sheykh ya kalli Jalal tare da cewa. "Ka gayawa su Khalid su kula da duk wani dake jikin gidan". To yace kana ya kira su ya sanar musu. Nan take kuwa suka miƙe suka fara ɗan zirya Ajiyan zuciya mai nauyi Bappa ya sauke lokacin da Sheykh yayi mishi duk bayanin abinda ke faruwa. Ya ƙara da cewa. "Idan ban kamashi ba bazai daina bibiyar rayuwar Shatu ba, kuma zai iya ci gaba da yiwa mutane illa in ya rasata". Cikin sanyin jiki Bappa yace. "Hakane". Dai-dai lokacin ita kuma Shatu ta fito cikin ɗakin. Randunansu ta nufa. Dai-dai lokacin kuma Ba'ana yana ta wurin ta bayan danga. Tasa hannu zata ɗebo ruwa kenan taga zoben yatsarta ya kawo wani haske. Da sauri ta miƙe tsaye. Jin muryar Ba'ana cikin raɗa da leƙota ta tsakankanin karan da akayiwa danga a madadin katanka. Da sauri ta dafe ƙahon zuciyarta jin muryarshi ras cikin kunneta murya cike da rauni yace. "Mata! Mata!! Mata!!!". Ta sani duk duniya mutum ɗaya rak ke kiranta da wannan sunan. Murya na rawa tace. "Yah Ba'ana". Cikin rauni yace. "Mata ina kika shiga kika mance dani. Mata kika barni cikin ƙunci da ciwon rai da zuciya na rashin ki Mata wlh zan iya jure komai amman bazan iya jure rashin kiba". Kar-kar haka jikinta ya fara rawa. Da sauri ta juya, da nufin zata koma ɗakin Ummey sai kuma ta tsaya tare da rumtse idanunta da ƙarfi. Ganinshi ya ɓace ɓat ya dawo gabanta. Cikin rauni yace. "Ina zakije? Tafiya zakiyi ki barni!". Ya ƙare mgnar da rauni yana kuma ƙoƙarin kai hannunshi zai kamo nata. Cikin tsananin ruɗani tace. "A a, Yah Ba'ana kada ka taɓani ni matar aurece". Sai kuma ta kauce. Da sauri shima ya kauce ya bita. Cikin tsoro tace. "Dan Allah Yah Ba'ana ka bar fito min". Da sauri Sheykh ya miƙe tsaye cikin tsananin tashin hankali jin furucin da Shatu keyi tare kuma da kakkaucewan da takeyi alamun ana binta. Su Jalal ma kab miƙewa tsaye sukayi. Shi kuwa Sheykh da sauri ya nufi inda take. Dai-dai lokacin su Ummey ma kab Suka fito sabida karan da Shatu tasa. Sabida riƙo hannunta da Ba'ana yayi ya fara ja. A zahiri ita kaɗai ake gani amman a badini shike janta. Cikin rawan jiki ta tashin hankali tace. "Bappa Yah Ba'ana ne yake jana wai zai tafi dani. Yah Sheykh zai tafi dani". Ta ƙare mgnar da ƙarfi da kuma sakin kuka. Shi kuwa Ba'ana shima kukan yakeyi cikin rauni da tsananin so yake cewa. "Mata yanzu wani kike cewa yazo ya ceceki ya rabaki dani. Shin bakya so nane?". Dai-dai lokacin kuma Jalal ya iso gab da ita. Da sauri duk suka buɗe baki tare kallon yadda Jalal yayi sama ya faɗi ƙasa tib sabida wani irin azabebben naushi da Ba'ana ya kima mishi. Wanda su ba ganinshi sukeyi ba. Cikin wani irin tafasan zuciya irin na sojojin Jalal ya miƙe tsaye tare da nufosu. Jin Shatu na cewa. "No Jalal kada ka iso zai illa taka". Ina bai kulaba sabida ranshi ya gama tafasa. Ai kuwa kamar da fari, suka sake ganin Jalal yayi sama-sama yayi ƙasa har saida Ummey tayi kansa da gudu hannu tasa ta dagoshi. Tare da juyowa tana kallon gaban Shatu cikin sanyi tace. "Ayyah Ba'ana kayi haƙuri kada ka cutar min da ahlina nasan kai mai al'khairi ne a gareni. Bappa ne ya matso shima a hankali hakama su Affan da Yah Jafar. Shi kuwa Sheykh jingina kanshi yayi da jikin bishiyar Ceɗiya dake gefenshi. Hannunshi na dama yasa ya tallabe haɓarshi yana mai bin inda Shatu take da wani irin kallo. Sabida da fari zatonshi ko makaranta ne suka dawo. So yanzu ya fahimci ba makaranta bane. Hatsabibancin Ba'ana ne, Nazari yakeyi yadda zai fito mishi ta sigar da dole ya karya lagonshi da takwabin addu'a. Da sauri su Ummi duk sukace. "Innalillahi". Sabida ganin Ba'ana ya baiyana kansa garesu. A take kuma ya ɓace. Sai ya kuma sake baiyana ya kuma bace, saida yayi haka sau uku kana ya ɓace sai muryarsa ke tashin cikin rauni yace. "Baroon kaci amanata ina sane na Barka. Nayi hakane dan ka jawo shi wannan mai jajayen kunnuwa ya kawo min ita har nan. Ku a zatonku tarkonku na faɗa baku san cewa nawa tarkon kuka faɗa ba sa'ansu ɗaya nayi tuba na gaske bazan sake kashe raiba." Sai ya kuma bayyana still hannunshi riƙe da hannun Shatu cikin rauni murya na rawa tace. "Ayyah Yah Ba'ana dan Allah ka sakeni kada ka rabani da ƴan uwana da ƴata". Wani irin jujjuya kai yayi tare da cewa. "Bappa kun kasa cika min al'ƙawarin da kukayi min ko. Kai kuma Baroon kaci amanata ka muna furceni. Shatu ke kuwa kin yiwa soyayya ta ta gsky riƙon sakainar kashi. Wani abu kuke tunanin zaifi min ciwo da zafi sama da rabuwa da Shatu". Sai kuma ya kalli Sheykh daya zuba mishi ido yana takaronto addu'o'i babu ƙaƙƙautawa ido cikin ido ya tsare Ba'ana da ido. Shi kuwa Ba'ana murya a mace yace. "Ko na bar barun a raye kaima watan wata rana zai ci amanarka tabbas zaici amanarka maci amana kuwa gubane". Cikin sauri suka juyo kan Baroon daya saki wata iriyar gigitaciyar ƙara tare da komawa bayan Sheykh. Shi kuwa Sheykh ido ya zubawa inda Shatu take tana nufoshi alamun Ba'ana na matsowa inda yake. Da sauri sojojin dake wojen suka shigo da gudu Lokaci ɗaya mutane suka fara tururuwan shigowa gidan sabida ihun da Baroon yakeyi yana kiran sunan Ba'ana yana bashi haƙuri. Jalal kuwa da sauri ya kuma nufo inda Shatu take wanda da ita suke gane inda Ba'ana yake. Cikin tsoron kada ya cutar da Sheykh ya nufosu. Gib ya kuma ture Jalal tare da cewa. "Ummey ki gayawa wannan yaron zan illatashi fa ya dena matsowa inda nake". Gaba ɗaya tsoro ya rufesu jin furucinsa. Jalal kuwa hatsala iya hatsala ya hatsalo allurar ta motso to amman kuma faɗa da Ba'ana tamkar faɗa da iska mai kaɗawa ne ko kuma duhu. Da sauri Ba'ana ya juyo kawai sai ya fara dukan sojojin nan baki ɗayansu. Ya bugi wannan ta nan ya bugu wan can ta can. Kana ya haɗa da shaƙo wuyan Baroon. Kurma ihu da kakarin mutuwa Baroon yakeyi da ƙarfi. Wanda yasa gaba ɗaya gidan ya cika da mutane. Harda su Arɗo Bani. Bukar da Bugulu kuwa gefen Bappa suka tsaya suna kekrketa dariyar mugunta. Junaidu kuwa gefen Junainah dake ta kuma ta tsaya yana bata baki. Gaba ɗaya hankalin mutane ya tashi. Su Bappa da Arɗo bani da sauran dattawan Rugar Bani duk sai haƙuri suke bawa Ba'ana sabida ganin yadda yaketa dukansu Jalal ba sauƙi. Ita kuwa Shatu da gudu ta faɗa jikin Sheykh sabida saketa da Ba'ana yayi. Ganin ta nufi wurin Sheykh ne ya sashi sakin wuyan Baroon tare da barin dukan su Jalal. Ya nufo kansu Sheykh da Shatu. Cikin tsananin ruɗani Shatun ke cewa. "Yah Sheykh mu gudu zai maka illa". Jamil kuwa tuni ya fara aikinshi. Affan kuwa da Yah Jafar Kara matsowa kusa da Sheykh suke gudun kada a cutar dashi. Aunty Juwairiyya da Ummi da Sara da inna Amarya kuwa gaba ɗaya jikinsu rawa yakeyi. Shi kuwa Sheykh murmushi yayi jin Shatu tace. "Wayyoooooooo Allah Yah Ba'ana ka sakeni". Hakane yasa ya fahimci Ba'ana na kusa dashi. Ido ya lumshe tare da ɗago hannunshi kana a hankali yace. "Bismillahi". Yana faɗin haka yaji hannunshi ya sauƙa kan hannun Ba'ana kuma ya baiyyana kowa na ganinshi. Cikin nitsuwa Sheykh ya fara karanto Ayatulkursi'u yana mai kallon Ba'ana ido cikin ido wanda a take ya karya duk wani sihirin da Ba'ana ke tutiya da tinkaho dashi da ayar Allah. (Haske ya kori duhu) Da sauri Shatu ta koma bayan Sheykh ɗin. Shi kuwa Sheykh juyowa yayi ya kalli su Jalal daketa haki cikin haki da tsananin tafasar zuciya suka nufosu. Shi kuwa Sheykh ido ya zubawa Ba'ana ganin yadda yaketa fiffizgewa da buga ƙafarshi ta dama da ƙasa amman ina ya kasa ɓacewa. Cikin sanyi yace. "Jalal ku kamashi da sunan Allah bazai sake ɓacewa ba har abadan da izinin ubangiji". Ai kuwa da sauri Jalal yasa hannunshi ya damƙo wuyan Ba'ana tare da cewa. "Bismillahi". Ai kuwa bai ɓace ɗinba. Cikin wani irin tafasan zuciya da zafin yadda Ba'ana yayi ta libgarsu kamar shine sojan sune masu laifi cikin takaicin. Yayi mishi wani irin azabebben shaƙa tare da kima mishi naushi a cikinsa tare da kalmar "Bismillahi". Wani irin azabebben ihu mai rakaɗi da baiyyana azabar da yaji yace. "Wayyoooooooo Allah na rana,". Cikin haki Jalal ya kuma haɗa mishi wani naushin tare da cewa. "Kasan Allah ne kafurin banza matsafi". Dai-dai lokacin kuma sauran abokanshi sojojin suka rufe Ba'ana da azabebben duka da ammaton sunan Allah wanda hakan ke ƙara kwance duk wani ɗaurin sihirin dake jikin Ba'ana. "Ya ilahi ya mujibadda'awati." Mamey da Ummi ke faɗi sabida wani irin dukan zaban da su Jalal keyiwa Ba'ana. Ita kuwa Shatu cikin tsananin tsoro da kerma ta ɗan leƙo. Dai-dai lokacin Khalid ya murɗe hannun Ba'ana ɓas ya bada sautin karyewa. Da sauri ta rumtse idanunta tare da sakin wani irin kuka mai ciwo a rai. Da sauri Sheykh ya juyo yana kallonta. Bappa kuwa dasu Arɗo Bani dasu Yah Jafar kab Bukar da Bugulu suke kallo wa ɗan da suke wani irin kuka mai cike da tashin hankali. Jamil da Affan kuwa sarawa su Jalal sukayi. Mutanen Rugar Bani kuwa kab suna tsaye wasu tuni hawaye na zubo musu. Da ƙarfi Ba'ana yayi wani irin azabebben ihu da kururuwa sabida taka hannunshi da Khalid ya karya. Wanda Umar yayi ɗaya sojan ya murza tare da buga mishi naushin da saida yayi birgiman kule ya iso har gaban Sheykh. Cikin rauni da azabar raɗaɗi murya na rawa yace. "Mata! Mata zasu kasheni!". Cikin wani irin rauni da tsananin tausayi wani irin masifeffen kuka mai ƙarfi yan kwacewa Shatu. Da sauri ta zame har ƙasa ta durƙusa. Sabida wani irin azabebben tokara da guiwa da Jalal yayi mishi bisa tsakiyar bayanshi. A take sai ga jini ta hancinsa da bakinsa. Murya na rawa cike da rauni Shatu ta ɗago kanta. Ta kalli Jalal dasu Khalid kana ta kalli jinin bakinshi daya ɗan tsallo ya taɓa farin gyalen jikinta. Wani irin kukane mai cike da tsananin tausayi rauni ta fashe dashi tare da cewa. "Ayyah Jalal dan Allah ku barshi kada ku kasheshi ku barshi dan Allah". A hankali Jalal ya ɗan tsaya yana maida wani irin azabebben numfashin haƙi. Sheykh kuwa wani irin kallo mai cike da azabebben kishi ya watsawa Shatu. Tare da sa tafin hannunshi ya tallabe haɓarshi. Kana ya jingina kanshi da jikin bishiyar yana mai kallonsu. Mamey kuwa itama zamewa tayi tanamai sakin kuka. Ummi, Inna Amarya, Aunty Juwairiyya, Sara, dama duk sauran matan dake wurin wasu irin hawaye ne masu zafi suka tsastsafo musu. Junainah kuwa zuwa tayi ta durƙushe gaban Ba'ana gefen Shatu cikin wani irin azabebben kuka mai cike da rauni tace. "Wayyo Yah Ba'ana Dan Allah Adda Shatu ki hanasu dukanshi." Da ƙarfi Junainah ta faɗa jikin Shatu lokacin da Jalal yayi wani irin juyi ya kifawa Ba'ana wani irin masifeffen mari da tafin ƙafarsa. Tare da cewa. "Wato kai gaka shege har zaka sa hannu ka daki jamin soja". Wani irin azabebben karkarwa jikin Ba'ana ya farayi tamkar mazari. Wani irin kuka mai azabar ciwo da cin rai Bukar da Bugulu suka saki sabida ganin yadda hukuma ke azabtar da Ba'ana tamkar zasu ɗauke ransa. Cikin rauni murya na rawa ido na zubda hawaye Mamey tace. "Jalaluddin ku bar dukanshi". A hankali Jalal ya koma baya ya zauna bisa dakalin ƙofar ɗakinsu Giɗi. Sabida yasan muddin Mamey ta kirashi da sunanshi kai tsaye to abu ya ta'azzara gareta. Domin Babana take kiranshi, sai gashi yau full name ɗinshi ta kira bama Jalal kawai ba. Sai kuma ta kalli su Khalid kana ta juyo ta kalli Sheykh murya na rawa tace. "Muhammad ka hanasu dukanshi". Cikin wani irin yanayi Sheykh ya ɗagawa su Khalid hannu. Haka yasa suma suka koma gefen Jalal suka zauna suna haki da maida numfashi. Shi kuwa Sheykh ido ya zubawa Shatu dake kuka tamkar ranta zai fita. Gaba ɗaya wurin babu wanda rauni bai darsu bisa zuciyarsa ba. Yah Jafar da Bappa kuwa tuni hawaye suke zubdawa. Bukar da Bugulu kuwa da rarrafe suka iso gareshi. Shi kuwa Ba'ana wani irin dogon numfashi mai cike da azaba rauni nadama ya fesar a wahalce kana a hankali ya fara yunƙurin tashi zaune. Amman Ina ya kasa ganin hakane yasa Bukar yin sauri yasa hannunshin ya tallaboshi ya ɗagoshi. Ya jingina bayan Ba'ana nan da kirjinsa. Ya zama suna fuskantar Shatu dake kuka tamkar ranta zai bar gangar jikinta gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi. Cikin wani irin rauni murya na rawa yace. "Mata!". Da sauri ta ɗago jajayen idanunta ta ɗaurasu kanshi. Wanda haka yasa ta saki wani sabon kuka, Junainah ma kukan ta saki da ƙarfi. Shi kuwa Ba'ana hawaye na kwarya yana ƙore jinin hancinsa da bakinsa murya can ƙasan maƙoshi yace. "Mata". Murya na rawa kuka na kumbe mata tace. "Na'am Yah Ba'ana". Wani irin murmushi mai rauni yayi kana a hankali yace. "Mata Ranar da nake tsoro tazo, ranar da na gaya miki zata iya ɓaci zata zo, gata yau tazo". Sai kuma ya ɗago ɗaya hannun nashi mai lafiyar ya sharce hawayensa, cikin sanyi ya jujjuya kanshi dake masifar mishi ciwo. Ido ya zuba mata ganin yadda take kuka har numfashin ta na fizga. A hankali yace. "Shatu kin san son da nake miki gsky ne?". Cikin kuka tace. "Na sani Yah Ba'ana na sani son da kake min gsky ne". Wani dogon ajiyan zuciya mai nauyi ya sauƙe tare da cewa. "Alhamdulillah". Sai kuma ga hawaye shar-shar bisa fuskarshi. Cikin rauni yace. "Ke kuma kin taɓa sona a ranki da gsky?". Kanta ta fara ɗan bugawa da ƙafar Sheykh dake gefenta. Tare da cewa. "Eh eh eh Yah Ba'ana na soka so na gsky na soka so irin wanda naso mu gudu tare mu tsira tare nasoka irin son da nake yiwa Yah Al'ameen sabida bana son irin wannan ranar tazo mana". Kanshi ya jujjuya kana cikin rauni yace. "Shatu haka ƙaddarar rayuwata take." Sai kuma ya kalli Junainah a hankali yace. "Junnu me yasa kike kuka, bakya son a kashenine". Cikin kuka tace. "Bana son a kasheka Yah Ba'ana. Ina sonka kamar yadda nake son sun Yah Giɗi". A hankali ya sunkuyar da kanshi tare da sakin wani irin raunataccen kuka wanda saida Affan ya zubda hawaye. Cikin sanyi yace. "Mata ina ƴarmu?". Cikin wani irin rawan jiki hawaye na kwarya. A hankali tasa hannunta ta amshi Afreen dake hannun Ummi. Kana ta juyo da rarrafe tamkar ƙaramar yarinya ta iso gabanshi cikin rawan murya tace. "Gata nan Yah Ba'ana". Wani irin murmushi mai yelwa yayi wanda saida fararen haƙoranshi suka fito ras. Da idonshi ya nuna mata cinyarshi. Cikin kuka ta sunkuyo ta kwantar mishi da Afreen bisa cinyarshi. Kana ta kife kanta cikin cinyoyinta ta saki kuka. Shima kukan ya saki mai rauni. Kana yasa tafin hannunshi ya shafi kan tattausan suman gashin Afreen hawayenshi na kwarya suna ɗiga kan goshinta. A hankali yace. "Masha Allah, Allah ya raya mana ita bisa imani al'farma Annabi da al'ƙur'ani Allah yasa mahaddaciyar al'ƙur'ani ce, ya azur tata da miji na gari". Karo na forko da Sheykh ya motsa lips ɗin shi a hankali yace. "Amin ya Allah". Sabida daɗin Addu'ar da akayiwa ƴarshi. Itama Shatu cikin kuka tace. "Amin thumma Amin". Sai kuma ta ɗago kanta a hankali jin yana cewa. "Naji lbrin Ummey ta tuno baya ta gane ahlinta ance min ma wai ɗan ta ne ya aureki ko?". Ina ta kasa mgn sai kuka, Ummeyn ce ta sharce hawayenta a hankali tace. "Eh Ba'ana na tuno baya, na gano ahlina Allah ya saka da al'khairi ya biyaka da mafi kyawun sakamako". Cikin rauni yace. "Amin Amin Ummey". Sai kuma ya kalli Bappa dake ta kuka a hankali yace. "Bappa kana kukan baka cika min al'ƙawarin da kayi bane?". Da sauri Bappa ya gyaɗa kai alamar eh. Kai ya jujjuya kana a hankali yace. "Ba laifinka bane, ƙudirin ubangijine ba gashi yanzu Ɗiyar Shatu ce a cinyata, wani bazai haifi ɗan wani ba ai. Ni na yafe muku yanzu na yarda na gane komai nufin Allah ne. Sai dai kuma ina neman yafiyarku al'ummar Rugar Bani baki ɗaya busa duk wata cutarwa da nayi muku." Sai ya kuma kalli ɗaya daga cikin yaransa da suka shigo tare a hankali yace. "Koda bana da halin muku bayani, ga Droo zai muku dukkan bayanin abinda ke tafe, gaba ɗaya na mishi bayanin komai kafin mu taho". Sai kuma yayi shiru jin duk anyi shiru ana jinshi sai shessheƙan kukan Shatu dake tashi. Kalato yawun bakinshi yayi ya haɗiye sabida wata irin azabebben ƙishin da yakeji tamkar zai kashesa. A hankali ya kalli Ummey cikin rauni yace. "Ummey ƙishi nakeji ki sanmin ruwa". Yayi mgnar yana kallon Shatu data zuba mishi ido da sauri. Ya sani ta tuno bayanin daya taɓa yi matane na cewa in an bashi ruwa yasha zai ɓace zai tsiri. Haƙƙun kuwa itama abinda ta tuno ɗin kenan sai dai bata saniba ya kakkarya duk waɗan nan abubuwan. Cikin rani yace. "Shatu Insha". Yace lokacin daya amshi kofin ruwan da Ummey ta miƙo mishi. Shiru batayi mgna ba sai kukanta daya ƙaru. Sheykh kuwa zuwa yanzu Allah ne kaɗai yasan abin da yakeji a zuciyarsa sabida azabar zafin kishi. A hankali murya na rawa ido na zubda hawaye yace. "Mata ina sha, ko kada insha zaki gaya musu, ki gaya musu mana". Da sauri Jalal yace. "Adda Shatu menene wani tsafin zaiyi ne?". Da sauri ta kalli Jalal kana ta juyo ta kalli Ba'ana ta kuma juyowa ta kalli Sheykh. Cikin sanyi murya na rawa tace. "Ka." Dai-dai lokacin kuma Baroon yasa hannunshi ya bugi ruwan tare da cewa. "Idan yasha zai ɓace ne fa". Yayi mgnar sabida baisan Ba'ana ya ƙauracewa tsafi da asirce-asircen ba. A hankali ya juyo ya kalli Shatu tare da cewa. "Ƙarasa mgnarki domin itace kamar zaɓin rayuwata da mutuwa ta." A hankali tasa hannunta ta ɗauki Afreen dake kallon fuskarshi tana wasa. Cikin rauni tace. "Kada ka sha Yah Ba'ana ka bari hukuma tayi maka hukuncin daya dace da kai". Yana zubda hawaye yace. "Uhummm to shike nan Mata. Amman nasa baki san me nake aikatawa ba shiyasa kike tunanin hukuncin hukuma zai rageni da rai". Da sauri ta nufi cikin ɗaki tana kuka. Kana su Jalal kuma suka kamashi sukasa a motarsu sukayi gaba dashi. Su kuwa Bukar da Bugulu da kuka suka tafi. Yayinda duk mutane ke zubda hawaye. Bayan anyi sallan la'asar ne. Sheykh yace su fito su tafi cikin disashewar murya Shatu tace. "Jamil aini zan kwana biyu". Kai Jamil ya ɗan juya yace. "A a Yah Sheykh yace ki fito mu tafi, wai ya fasa baza ki kwana ba". Jin haka yasa Inna Amarya dasu Giɗi da Gaini da Seyo da yanzu suka dawo sukace. Tabi umarnin mijinta. Dole haka ta fito suka tafi, harda Junainah. Gaba ɗaya Rugar Bani tayi shiru tayi sanyi tamkar waɗanda akayiwa mutuwa. A can masaraur Joɗa kuwa. Cikin wani irin ƙunan rai Sheykh ya kalli A....! Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 a yawan posting ne babbancinsu yake. Idan kinaso turo kuɗin ta Account 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai kiyi screenshort na Debit Alert ki turo ta WhatsApp 09097853276. Sai in saki a group, ku ƴan 300 in baki da damar biya ta Account to ki sayi katin Mtn na ɗari uku kacal ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp 09097853276. Banbancin special Group da Normal group a yawan posting ne kada kizo kice in miki ƙarin bayani ɗan Allah. By *GARKUWAR FULANI* [4/4, 10:00 PM] +234 806 559 0880: Agogon hannunsa, ƙarfe 11:30 pm na dare har yanzu Shatu bata shigo inda yakeba. Idanunsa ya rumtse da ɗan ƙarfi, tare da gyara kwanciyarsa, ya mai jin wani irin zazzafan kishi na taso mai. Allah Ya sani yana jin ciwo da zafi acikin zuciyarshi, har yanzu idan ya tuno yanayin tashin hankali da kuma tausayi da rauni’n da ya gani a fuskar Shatu, lokacin dasu Jalal ke dukan wannan taƙadirin tsohon saurayin nata. Mchewww yaja wani dogon tsaki a fili yace. "Sabida shine zata barni ni ɗaya a ɗaki kamar wani marar galihu?" Muskutawa yayi tare da fesar da zazzafar iska ta bakinsa, sosai yakejin kuna acikin zuciyarsa, wanda kuma duk akan Kishin Shatou’n da yakeji ne. A haka dai bacci b’arawo yayi awon gaba dashi bayan yayi ta juye-juye. Ita kuwa Shatu tunda suka dawo ta gaza tsaida hawayenta. Allah Ya sani bata taɓa jin son Yah Ba'ana aranta ba, bata kuma jinsa a matsayin saurayin da take buri da fatan aure, sai dai tasan tabbas tana mishi so irin na ɗan uwan taka. Tana jinshi tamkar su Yah Al'ameen dasu Yah Giɗi. Tana mishi so irin na ƴan uwa musulmai da son ya gyara rayuwarsa ko ya samu rabauta ranar gobe kiyama. Kuka sosai takeyi, rungume da Afreen damunta da yarinyar tayi ne kuma yasa ta fito da ita. A falo ta samu Ummi zaune ita da Jalal. Cikin disashewar murya tace. "Ayyah Ummi ga Afreen kaina ciwo ina so inyi bacci ta hanani". Da sauri Ummi ta miƙo hannu ta amsheta tare da cewa. "Tasha mamanta ai ko?". Kai ta gyaɗa mata alaman “Eh.” Jalal ne ya ɗan kalleta sosai fuskarta, ta kumbura tayi jazir idanunta kuwa sunyi tib tib. A hankali ya maida kanshi ga Ummi yana mai ci gaba da cewa. “Ai daga can Rugar tasu cibiyar bincike na jiha muka kaishi. Alhamdulillah kuma shida bakinshi ya amsa dukkan laifukansa tare da yin bayanin komai, ya tabbata cikekken mai laifi da ake nema ido rufe, yanzu kai tsaye ba ɓata lokaci za'a kaishi kotu ta yanke mishi hukunci ranar Monday da izinin ubangiji.” Cikin sanyi Ummi tace. "Allah sarki, Allah yasa ya samu da sauƙi". Miƙewa Jalal yayi tare da cewa. "Wani da sauƙi kuma Ummi ai yadda yayi ta kashe mutane, da sace dabbobin su shima kasheshi za'ayi a rage mugun iri a duniya". Jin hakanne kuma yasa cikin sauri Shatu ta koma ɗakinta. Bisa kan gadonta ta kwanta tare da kifa kanta kan pillow, wani irin sassanyan kuka ne ya kwace mata. Lokaci daya Komai ya fara dawo mata sabo, tun randa ta fara ganin Yah Ba'ana da kuma yau da tayi mishi kallon da take tsoron kada ya zama na ƙarshe ne. Saboda ita dai bata taɓa sanin cewa yana sata da kashe mutane ba. Haka ta dinga sak’e sak’e acikin zuciyarta, a ranar dai haka suka kwana kowa da abinda ke damunsa. Washe gari kuwa, ranar Lahadi, Sheykh yana gida wuni zur amman Allah bai sa yaga idon Shatu ta fito ba. Wannan abun ya ƙara ingiza mishi zafin kishinsa, ji yakeyi tamkar yayi ta ihu dan takaici. Bayan sallan azahar ne. Ya dawo a falon ya samu Ummi da Aunty Juwairiyya da Mamey. Wacce kuma ta shigo ne dan ta duba Shatu, da yawan kuka ya sakar mata zazzafan zazzaɓi da ciwon kai. To ta fito daga d’akin Shatou d’in kenan, suna zaune afalo ya dawo. A hankali ya ɗan sunkuyo ya shafa kan Afreen dake cinyar Mamey. Tare da cewa. "Mamey ɗazu naje kina bacci". Tana kallon yadda yake shafa kan Afreen yana cewa. "Allah ya miki al'barka". Murmushi tayi tare da cewa. "To masu ƴaƴa kaima Allah yayi maka al'barka". Cikin jin daɗi yace. "Amin Amin Mamey na". Murmushi tayi kana tace. "Muna son mgn da kai". Da sauri cike da biyayya yace. "Toh Mamey gani". Miƙewa tayi ta nufi waje, shikuwa gyara al'kyabbar dake jikinshi yayi tare da bin bayanta. Kai tsaye Part ɗin Abbanshi ta nufa yana biye da ita a baya. Da sallama suka shiga. Murmushi Abba yayi tare da miƙa hannunshi ya amshi Afreen daketa raba ido. Ita kuwa Mamey gefenshi ta zauna. Da sauri ya zauna gabansu a ƙasa bisa Austrian carpet, ya tanƙoshe sawunshi ya fuskancesu da kyau. Gyaran murya Abba yayi tare da zuba mishi ido, wanda haka yasa shi yin ƙasa da kansa. Shiru-shiru basuyi mgna ba, hakane yasa ya sake ɗago kanshi da sauri yayi ƙasa da idonshi sabida ganin daga Abban har Mameyn ido suka zuba mishi. A hankali ya fara motsa lips ɗin shi yana cewa. "Astaghfirullah!!". Ya fara tubawar ubangijin mu. Kafin ya tubarwa iyayen nasa dan hakan da sukayi ya rauna tashi sabida bai san laifinsa ba. Su kuwa sun mishi hakane dan su sa mishi rauni da kuma halarto da biyayyarsa. Karo na uku ya kuma ɗagowa ya kallesu. Kawai sai ya tankwashe kansa bisa kafad’arsa murya cike da rauni yace. “Dan Allah Abba Mamey kuyi haƙuri ku gafarceni idan wani laifi nayi muku, ku sanarmin dan in kiyaye gaba kada in maimaitashi". Sai kuma ga idanunshi sunyi rau-rau sun fara wani sheƙi alamun hawaye na tsastsafowa daga cikinsu. Cikin tsare murya da fuska da kauda wargi Abba yace. “Muhammad!” Da sauri murya na rawa yace. "Na'am Abbana". Sai kuma ya kalli Mamey da itama ta kirashi. Amsawa yayi tare da zuba musu ido. Kai titsiyewar iyaye akwai sa rawan jiki da fargaba a zuciyar ɗan adam. Cikin tsananin kausasa murya Abba yace. “Ina bukatar in baka umarni kayi wani abu, ban saniba ko zaka iya min biyayya ko bazaka iyaba". Cikin sauri ya kalli Mamey da tace. "Ni umarni nake so in baka". Da rarrafe ya ƙara matsosu cikin rawan murya yace. "Abba matuƙar dai abin da zaka sani bai saɓawa umarnin Ubangiji da tsarin Addinin Musulunci ba, in sha Allah zaka sameni mai biyayya a gareka da izinin Ubangiji." Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe cikin yanayin gamsuwa. Shi kuwa a hankali ya kamo hannun Mamey, cikin sanyi ya had’a su ya tallafe haɓarshi sai ga hawaye shar-shar suna kwaranya murya na rawa yace. “Tsawon shekaru goma sha uku ina kuka dare da rana kuka na cikin zuciya, ina so in ganki da idona ma Allah bai bani Dama ba. Nakanji wani irin daɗi na musamman in Umaymah ta bani umarnin inyi abu kai tsaye, sai inji kamar ban rasa uwar da zata tirsasani yin abinda ya dace ba. Mameyna bani umarni da izinin ubangiji zanbi zan miki biyayya". A hankali tasa hannunta tsakiyar kanshi tare da cewa. "Allah yayi maka al'barka". Da sauri yace "Amin". kana ya kallesu yace. "Menene umarninku?." Kusan a tare suka haɗa baki wurin cewa. "Umarninmu shine ka amshi mulkin Masarautar Joɗa, da Lamiɗo yake son yin murabus, ka yarda ka mulki masarautar Joɗa domin kawo gyara da tsari irin na addinin musulunci, Ni Umarnine kai tsaye nake baka". Mamey ta kare zancen. Abba kuwa cewa yayi. "Ni kuwa al'farma nake nema". Abun ya zo mishi amatuk’ar bazata amman kuma saidai umarnin iyaye ya wuce wasa. Wani irin kukane mai rauni ya kwace mishi, take hawaye ya soma kwarara akan fuskarsa, cikin raunanniyar murya yace. “Mamey zanyi na amince zan mulki masarautar Joɗa, Abba kaima kace umarnine kawai na amince zanyi muddin hakan zai saku farin ciki". Cikin tsananin jin daɗi suka ɗaura hannunsu a kanshi tare da sa mishi al'barka. Sai kawai ya kife kansa bisa cinyar Mamey murya na rawa yace. “Kuyi min addu'a da bakunanku masu al'barka, ku roƙa min Allah ya bani ikon zama adalin shugaba mai tausayin al'ummar sa, ku roƙa min Allah ya bani ƙarfin zuciyar yin mulkin, sannan ku roƙa min Allah yasa kada giyar mulki ta bugar dani, ta sani danasanin muku biyayya ranar gobe kiyama, ku roƙa min Allah yasa talakawa suyi farin ciki da alfahari dani a matsayin shugaban su". Ya ilahi ya mujibadda'awati. Su kansu su Abba tausayin shi ya rufesu, domin yanzu suka gano abinda yasa yake tsoron mulki da gudunsa. Cikin sanyi sukayi ta jero mishi addu'o'i. Yana amsawa da. "Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati". Daga nan Abba yayi ta bashi baki da bashi ƙarfin guiwa. Dole sai kiran sallan la'asar ne yasa suka fito suka nufi masallaci. Bayan kuma sun idar da Sallah’n sun fitone. Abba ya sanarwa Lamiɗo da Galadima yadda sukayi. Sujjadar godiyar Allah Lamiɗo yayi sabida baiyi zaton abun zaizo da sauƙi haka ba. Shi kuwa Sheykh Part ɗinsa ya koma. Junainah da Mimi yaran Aunty Juwairiyya ya wuce a falo, har yaje bakin ƙofar shiga falonshi ya juyo yace. "Junainah zo". Da sauri tace “To” ta biyo bayanshi. A falon ya tsaya a hankali yace. "Ina Adda Shatu ?". Cikin sanyi tace. "Tana ɗakinta". Da sauri yace. "Kuka takeyi ne?". Kai ta ɗan gyaɗa mishi alaman “Eh” Uhummm kawai yace kana yace. "Jeki". Ƙarfe tara dai-dai na dare ya fito daga Bathroom ɗinsa cikin shirin bacci. Shiru yayi jiyo muryar Afreen nata kuka a falo. Da sauri ya jawo al'kyabba ya ɗaura akan men sleeping dress d’in dake jikinsa. Direct parlor’n ya fito. "Ummi lfy kuwa meke damunta?". Yace yana zama kusa da Ummin. Cikin damuwa Ummi tace. “Wlh tun ɗazu kuka takeyi, to uwar kuma Maman ba ruwa, saboda tun shekaran jiya bata wani ci abincin kirki ba". Cikin ɓacin rai yasa hannunshi ya amshi Afreen, daketa wawure-wawuren hannunta tana kaiwa baki alamun yunwa. A kafaɗarsa ya saɓa ta tare da miƙewa ya nufi Bedroom ɗin Shatu. Ita kuwa Shatu tsananin ciwon kai da alamun zazzaɓin da take jine yasa. Take turawa Ummi Afreen ita, kuwa sai tsotsan take so. Sabida ba'a barta tasha yadda take buƙata ba. Cikin takaici ya tura ƙofar ɗakin tare da yin sallama, sounding a bit harsh yace. "Assalamu alaikum, ke ina kike?” Shiru yayi saboda hangota da yayi akan sallaya, ta fuskanci al'ƙibila da alamun salla takeyi ko tayi ta idar. Rai a haɗe ya zauna abakin gadon yana mai jijjiga Afreen daketa ƙananan kuka, tare da tsotsar yatsarta babba da ciccila ƙafa. Bisa kafaɗarshi ya sakata yana ɗan jijjigata da hura mata iska a kunnenta. A take ta fara sauƙe ajiyar zuciya don dama kukan harda rikicin yin bacci. Da sauri ya juyo kanshi yana kallon Shatu jin kamar shessheƙan kuka take sauƙewa. Ai kuwa kukan takeyi ta ɗaga hannunta sama kaɗan tana addu'o'in. A hankali ya juyo ya ƙara matsowa gareta, cikin tarin takaici ya dawo bakin gadon ya zauna, wani irin dogon numfashi mai nauyi ya sauƙe kana cikin takaici murya a daburce yace. "Kuka! Kuka!! Kuka!!! kikeyi har yau har yanzu, duk kukan da kikayi a can bai isheki ba? Duk kukan nuna mishi soyayyan da kikayi bai isheki ba, sai kin dawo min cikin gidana kina min kuka? kina tauye min haƙƙina dana ƴata akan wani can banzan ɓarawo!". Da sauri ta juyo ta kalleshi, hawaye na zubo mata ta zuba mishi ido. Wani irin maƙoƙon kishine da baƙin ciki ya tokare masa wuya, a fizge da ɗan ƙarfi yace. “In ma ni bakya sona! baki da lokaci na! Bakya buƙatar ganina! Bare ki sauƙe haƙƙina dake kanki, ai ita dai Afreen ƴar kice kuma tana da haƙƙin ta a kanki ko? In kuma kinajin duk kin tsanemu ne baza ki iya rayuwa damu da bamu haƙƙinmu ba, dan Allah ki gaya min ba sai kin zauna kina ta min kuka a cikin gida, kina cutar min da yarinya da yunwa ba, sannan kina tayar min da hankali ba, Ki faɗa min in bakya sona, In sama miki salama kije can ki auri shi wanda kike so ɗin!!!” Ya ƙare maganar da ƙarfi. Cike da fushi da zafin kishi. Wanda har Ummi dake falon ta jiyoshi. Karo na forko kenan a rayuwar aure su da Shatu da taji yana mata faɗa haka. Jin hakanne kuma yasa da sauri ta kamo hannun Junainah suka tafi ɗakinsu. Ita kuwa Shatu cikin rauni ta zuba mishi ido tana mamakin fusatarsa da kalaman da yakeyi. Shi kuwa Sheykh cikin takaici yace. "Na sani ai dama ni na sani bawai sona kikeyi ba, dole akayi miki ko? dama shi kikeso! Wannan abun shi nake gudu da tsoron auren matar da ba sonka takeyi ba. Amman ba matsala kiyi ta sonshi. Nima ina da masu sona, kuma zan aurosu, su kuma kular min da ƴata". Idanunta da ta zuba masa tad’an lumshe, cikin rawar murya tace. "Yah Sheyk...". Da sauri cikin fushi da zafin kishin ganin son Ba'ana ne yasata wannan kukan. A faɗa ce ya daga mata hannu cikin tsawa yace. "Da Allah rufe min baki". Yana faɗin hakan ya juya ya fita daga d’akin, still rungume da Afreen akan shoulder dinshi. Kai tsaye bedroom ɗinsa ya wuce. Cikin tafasan zuciya ya kwantar da ita can ƙarshen gadon nasa. Kana a hankali ya miƙe ya zauna sabida azaban tafasar da zuciyarsa keyi. Ita kuwa Shatu wasu hawayene, masu sanyi suka zubo mata. Musamman da ta fahimci cewar, zafin kishine ya birkita mata salihin mijinta. A hankali ta miƙe tsaye, tare da soma takawa ta shige Bathroom. Ruwan ɗumi kawai ta watsa tare da yin Brush kana ta fito daga cikin toilet ɗin. Turaren Oud mai daɗin ƙamshi ta shafa ajikinta. Tare da zura wata royal blue sleeping gown ajikinta mai adon net. Yayinda kuma har yanzu ta kasa tsaida hawayen dake kwance acikin idanunta. Wasu lallausan sleeping shoe ta zura a ƙafarta, tare kuma da tubke long hair ɗin kanta, da bluesy ribbon. Tana gama kimtsa kanta kuwa, ahankali ta fito daga ɗakin, tare da jawo ƙofar ta rufe. kaitsaye ta nufi Side ɗinsa. Cikin sanyi ta tura ƙofar Bedroom ɗin nasa tare da yin sallama can ƙasan maƙoshinta. Ganinsa atsaye da tayi ne kuma yasa, ahankali ta jingina da jikin ƙofar tana kallon yadda yake zirya a tsakiyar ɗakin, shi kadai sai ya kai mari ya kau gouro. Ga wani irin numfashi mai ɗumi da yake fitarwa. Idanunshi kuwa sun kaɗa sunyi jazir. A hankali ta nufo tsakiyar ɗakin. Cikin sanyi da kuma rauni ta nufi inda yake. Dai-dai lokacin shi kuma ya juyo. Yana juyowa kuwa ta faɗa jikinshi ta rungumeshi tsam a jikinta. Ashagwaɓe ta saki wani irin raunataccen kuka mai kashe jiki da zuciya. Murya na rawa cike da rauni tace. “Kayi haƙuri Yah Sheykh ka gafarceni, na tuba please, kukana bawai inayi dan na ɓata ranka bane, banason fushinka, Dan Allah kada ka kwana kana fushi dani, I’m very scared dan bazan iya jurewa ba...” Kasa ƙarasa maganan nata tayi, lokaci ɗaya kuma ta ci gaba da sakin Shessheƙan kuka, tare dasa hannayenta akan chest ɗinsa. Shi kuwa Sheykh har yanzu fushi yakeji, saboda haka ma gaba ɗaya jikinshi rawa yakeyi dan tsananin takaici kukan da takeyi. Hannunshi yasa ya soma ƙoƙarin ɓanbareta daga jikinsa, murya adaƙile yace. "Ni Sakeni! ki barni!! kuma ki fita harkana!!! Kije can ki gama kukan naki a can ɗakinki, badai kinfi sonshi ba? maza fice min a ɗaki ni ɗakina ba wurin zubda hawayen soyayyar wani ƙato bane." Jin hakanne yasa, cikin sauri tasa hannayenta ta saƙalo wuyanshi, tare da cusa kanta a ƙirji shi, murya a raunace tace. "Ni banason shi, da gaske Yah Sheykh ka yarda dani bana sonshi, aduniya waye zanso sama da kai? kaine fa Mijina, mahaifin ƴata, sannan kuma Garkuwa ta, tayaya zan so wani bayan kai?” Da sauri yace. "Eh mahaifin ƴarki ko? Bama mahaifin ƴaƴan kiba, wato irin daga ita shike nan ko?". Baby face d’inta ta shag’wabe, cikin kasala da kuma son sauk’ar masa da fushinsa tace. "I’m very sorry Zawj mahaifin yaƴana." Idanunsa yaɗan lumshe, cikin kuma yanayin fara jin sanyi arashin ya tureta ya koma bakin gado ya zauna tare da cewa. "In dai bazaki bar kukan nanba fice min a ɗaki sanida kukanki yana ƙona min rai". Da sauri tasa tafin hannunta ta share hawayenta. Kana ta matsoshi Ahankali ta kwanta a jikinshi tayi lib, laɓɓan bakinta taɗan tattauna kana a raunace tace. “Please Yah Sheykh nabar kukan, amma ka yafe min, bazan sakeba dan Allah kayi haƙuri". Ajiyar zuciya mai sanyi, ya sauƙe dan ta haɗashi da Allah ta gama zance. Juyowa yayi asanyaye ya fuskanceta, tare dasa hannunsa ya ɗan tallafo kanta, shiru yayi batare daya ce komae ba, sai tsurawa fuskarta ido da yayi. Ganin hakanne kuma yasa ahankali ta sake matsowa jikinsa, wani sassanyan hugging tayi masa, tare da fara sauƙe tagwayen ajiyan zuciya cikin sanyi da taushin murya a hankali tace. "Nifa Bana sonshi, so irin wanda nakeyi maka, nadai soshi matsayin wana jinina, sannan kuma nayi kukane saboda rauni na. Musamman ganin yadda ake dukanshi, da kuma yadda iyayenshi ke kuka. Yah Sheykh Yah Ba'ana shine wanda yayiwa Ummey magani tsawon shekaru biyu ba dare ba rana kafun ta fara magana ta dawo haiyacinta. Naje gidansu dare da rana cikin ruwa da iska na amsowa Ummey na magani, Bai taɓa cutar da niba, Ya soni tamkar ransa, Nikuma na soshi matsayin ɗan uwa musulmi, Shekaran jiya tausayin dukan da akayi mishine ya sani kuka. Jiya kuma tunda Jalal yace min za'a yanke masa hukuncin kisa raunina yasa na kasa tsaida hawayena. Amman bawai dan ina sonsa so na aureba, kawai dai akullum Ina tuna al'khairinsa garemu ne, domin koba komae shid’in yayi taimako agaremu”. Wani sassayan numfashi ya sauƙe tare da, sa hannunshi ya ruggumeta gam-gam a jikinshi. Haka nan yaji duk jikinsa yayi sanyi. Jin yanda yayi hugging d’inta ne kuma yasa ahankali tace. "Nida Allah ya azurtani da miji kamarka, miji na gari! Mumini! Salihi! Mai tausayina! Mai riƙo da ibada! Mai cikakkiyar nagarta! Ta yaya idona zai iya ganin wani ɗa namiji da wata suffar, har in soshi? Nida nake da kai, na shaida Allah yamin kyakkyawan zaɓi! Ina sonka sosai Yah Sheykh nah, Hamma Jabeer, kuma Malam d’ina, ina sonka, zan kuma ci gaba da sonka iya rai da mutuwa, sannan please ka yafe min zuwan da banyi gareka ba, ka d’aukeshi amatsayin ajizanci da kowani d’an Adam keyi, then maganan Afreen kuma kaina ke ciwo shiyasa na barta dasu Junainah, ka yafe min ni bani da sama daku kaida Afreeen kune farin cikina. Kune silar dawowata Nigeria'n rankune ke ajiye dani a masarautar Joɗa". Wani irin sasayyan kiss ya manna mata a goshinta. Cikin kuma yanayi jin sanyi da daɗin kalamanta yace. “I Love you Aysh, I always Love you, I love you so much, Tabbas nayi farin ciki da samun aurenki farin ciki marar misaltuwa, Kece cikon farin cikina My Wife, kece sanyin zuciya da idanuna! sannan kuma har lau kece GARKUWA ta! Duk wani farincikin da zan samu yana tare dake ne, hakika ke HASKE ce acikin rayuwar Jabeer, zan rayu dake har abada!!” Yakai ƙarshen maganan nasa cikin wani irin murya, mai sauƙar da kasala, tare kuma da zame jikinsa, ahankali ya kwanta kana ya jawota ya kwantar da ita ajikinsa. Idanunta ta zubawa kyakkyawar fuskarsa, Cikin kuma yanayin sanyi tace. "Please Yah Sheykh, idan da hali kayi wa ya Ba'ana wata al'farma mana". Kallonta shid’inma yayi kana hankali yace. "Wacce irin alfarma kikeso ayi masa?” Cikin zubda hawaye tace. "Dan Allah kasa a meda case ɗinsa kotun musulunci, a yanke masa hukuncin Musulunci dan Allah". Kansa yaɗan jinjina, cikin yanayin jin rauni da tsananin tausayi kuma yace. “I’m understand My Shatu, but amma kiyi haƙuri kinji, ki daina kuka domin dama tuntuni kotun musulunci aka kai ƙarar, kotun su Abban Yusuf (HUKUNCIN ALLAH) za'a yanke masa Insha Allah" Wani sassayan numfashi ta fesar tare dasa hannu ta share hawayen ta. Kana anutse tace. "Alhamdulillah!” Shiru ta ɗanyi sakamakon jin yanda ya soma yawo da hannnunsa akan waist dinta, akasalance ta ɗago kanta ta kalleshi, wanda shi ɗinma kuma kallonta yake da lumsassun idanuwansa. Ahankali ta matso da fuskarta gab da nasa, tare da zaro harshen ta ta ɗaura akan lips ɗinsa, domin ta fahimci a irin wannan yanayin sam ba buƙatar ace, sai ta jira shi ya fara kissing ɗinta. Idanunsa da suka ɗan sauya kala lokaci daya ya lumshe, musamman alokacin da yaji sauƙan harshenta akan laɓɓansa. Wani irin sha’awa da shauƙinta yakeji, hakanne ko yasa shi buɗe bakinsa, ahankali ta zura harshenta acikin bakin nasa. Wani irin dogon numfashi dukansu suka Sauƙe alokacin da tongues ɗinsu suka had’e waje ɗaya. Azafefe suka shiga kissing din juna, Yayinda kowannensu ke transferring yawun bakinsa wa ɗan uwansa. Kissing ɗin juna sukeyi sosai, Yayinda Aysha’n ke neman zautar masa da lissafi, hakan kuwa shiya sanya azafafe ya zare vail ɗin da ta rufe jikinta dashi. Ganinta da yayi acikin royal blue sleeping gown ɗin da yayi ne kuma, yasa shi jin wani hot feeling ɗin ta. Lokaci guda ya soma sakar mata kiss tako ta Ina. Yayinda daga gefe guda kuwa daddaɗan kamshin Oud dinta ke sake kunna sa. Aninayen dake jere agaban rigar nata ya ɓalle, tare da zare rigar daga jikinta gaba ɗaya, haɗadɗiyar surar jiki dana kirjinta ya zubawa ido, yana me sakejin sonta acikin zuciyarsa. Jikinsa na rawa tamkar wanda bai taɓayin sex da ita ba, haka ya mannata da jikinsa bayan ya zama naked. Atare suka soma fitar da wani irin numfarfashi, saboda yanda duk suka ruɗa juna da salonsu. Zama yayi akan gadon tare da ɗorata asaman jikinsa, lokaci daya kuma yaji numfashinsa na kokarin daukewa saboda yanda yaji Manhood ɗinsa ta samu kekkyawan masauƙi, dumi da kuma daddaɗan sweet da ya samu kansa acikine kuma yasa tunkafun aje ko ina yasoma yi mata wasu kalan sambatun dake nuna yana matuk’ar enjoying mood din. Domin kuwa harji yake kaman zai shiɗe. kaman kuma yanda yake azauce haka itama Shatu’n... After 58minute Bayan kuma komai ya lafa sunyi wanka sun fitone. Ya kalleta da kyau ganin yadda ta lafe ta kwanta lib, da’alama ta ɗan gaji ne. Murmushi yayi sannan ya fice daga cikin dakin, Dinning area yaje. Tea mai kwauri ya haɗa da zafi ya cika ɗan babban kofi kana ya dowa daƙin. Hannunshi ya miƙa mata, ganin haka yasa ta kama hannun, Ɗagota yayi ta zauna, kana shi kuma ya zauna agefenta. Cup ɗin tea din ya kai bakinta. Babu musu kuwa ta buɗe bakin sabida wani irin masifeffen yunwa da takeji, shikansa yasan dole ne ma, taji yunwa, sabida yanda yayi heaven sex da ita yau din, is so special. Tasha tea din sosai, saida ta kusan shanyewa ne kuma ta janye kanta ahankali, tare dayin gyatsa asanyaye tace. "Alhamdulillah". Hannunshi yasa bisa cikinta a hankali ya shafa cikin kula yace. "Shanye shi ko mangana". Ya ƙare maganar yana sa mata cup ɗin tea din abaki. Shanyewa tayi kana ya aje cup ɗin bisa bedside. Sannan yazo ya kwanta ya jawota jikinshi. Washe gari ranar Monday kotu ta yanke wa Ba'ana hukuncin kisa ta Hanyar rataya. Sabida hujja da shaidar daya bayar a kan kanshi. Kana yayi bayanin duk shanayen da yake sacewa daga wannan ƙasar zuwa waccar ƙasar. Ya bada tabbacin duk suna nan. Ya kuma sa yaranshi sun medawa kowa nashi. Domin suma sun musulunta. Bayan kwana biyu aka shirya rataye shi. Bayan anyi komai an fito da shine. Ya kalli taron fulanin Rugar Bani. Cikin zubda hawaye yace. "Dan Allah ku yafe min". Wani irin raunine ya rufesu mai sa zubda hawaye. Kusan a tare sukace sun yafe mishi. Cikin sanyi yace. "Ngd". kana ya juyo ya kalli Sheykh dake gefensa, murya na rawa yace. “Ga dai ƙarshena ni kam, Allah bai nufa zan rayu da Shatu ba. Allah ya ƙaddara matarka ce. Dan Allah ka kula da ita Shatu mace mai rauni da tausayi." Cikin zubda hawaye Sheykh yace. "In sha Allah". Sai kuma ya kalli Bugulu cikin rauni yace. "Mama kin tuna kin min al'ƙawarin zaki musulunta kuma zaki bar sata". Cikin kuka tace. "Nayi al'ƙawari". Da sauri ya kalli Sheykh a hankali yace. "Dan Allah bawa mahaifiyata ƙalmar shahada, a gaban idona in samu in mutu da farin ciki". Cikin zubda hawaye Sheykh yace. "Toh". A nan ya musuluntar da Bugulu. Nan aka rataye shi gaba ɗaya mutane na kuka. Sosai Sheykh da kanshi yayi ta kuka sabida. Amanar kula da Shatu da Ba'ana ya bashi amana. Bayan an rataye shi ne. Droo yayi musu bayanin cewa fa. Ya musulunta tun da dadewa. Hakane yasa Sheykh da kansa yayi masa wonka kana ya limanci sallan gawanshi kana aka kaishi gidansa na gsky. Rayuwa kenan. Shatu kuwa sai dai ta buya tayi kuka, Ummey da kanta tayi tashan kuka. Alhamdulillah bayan rasuwarsa da wata ɗaya. Lamiɗo da kanshi ya shiryawa Sheykh da Shatu da Ummey da Dr Aliyu da Baba Basiru da Galadima su tafi ƙasar Cameroon dan yiwa iyayen Shatu godiya da kuma nemawa Jamil auren Khadijah, dan yana son ranar auren a kuma naɗa Sheykh a matsayin Sarkin Masarautar Joɗa. Alhamdulillah sun gama shirinsu, Washe gari zasu tafine. Batool ta kira Sheykh. Suna zaune da Shatu kiran ya shigo bayan ya ɗagane ta mishi bayani ta ƙara da cewa. "Affan ne ya bani number ka. Alhamdulillah aurena next week Ina gayyatarku ɗaurin aure". Cikin ɗan sake fuska yace. "Masha Allah, Allah ya kaimu in Sha Allah zanzo nida Affan". Cikin jin daɗi tace. "Toh ngd matuƙa Hamma Jabeer". Daga nan sukayi sallama. Da sauri ya sauƙe numfashi ganin Shatu bata kallonshi ma. Ranar litin da yamma jirginsu ya sauƙa cikin ƙasar Cameroon birnin Yahunde. Wasu irin motoci masu tsadar gaskene sukazo suka ɗauke su zuwa gidan Abboi. Suna isa bayan sunyi parking sun firfito gaba dayansu Jamil ne ya ɗan juya....! By *GARKUWAR FULANI* [4/6, 7:36 AM] +234 806 559 0880: *Lamiɗon Adamawa, Dr Aliyu Mustapha jama'ar Adamawa duk suna a gaisheka.😭😭😭 Allah ya jiƙanka da Rahama Lamiɗon Adamawa Dr Aliyu Mustapha. Wannan shafi gaba ɗayan shi sadaukar wane gareka. Jinjina da godiya ga Sarki mai ci Muhammad Barkinɗon Aliyu Mustapha. Allah ya taya riƙe!.!.. Ya juyo ya kalli Shatu dake sauƙe numfashi tare da yin murmushi mai cike da jin daɗin ganin gida. Yah Al'ameen ne ya matso gabansu Sheykh da sauri tare da cewa. "Bismillah mu isa ciki". “Masha Allah” Galadima yace tare da bin bayanshi kai tsaye parlon Abboi na musamman suka nufa. Kana suma saura duk suka bi bayansu. Shatu da Mamey da Ummi da Sara kuwa cikin gida sukayi. Tarba mai cike da mutuntaka akayi musu tare da Kekkyawar mu'amala. Kwana su biyu rak. Suka juyo suka dawo Nigeria, bayan sun gama tsaida batun auren Khadijah da Jamil. Hafsi da Salmanu. Rafi'a da Yah Al'ameen Jalal da Hibba. Bisa mutuntakan da kimar Lamiɗo da tsarin su, na son a ranar za'a naɗa Sheykh a sarautar Sarki Joɗa, yasa duk aka tsara batun ɗaurin auren a Masarautar Joɗa za'ayi shi. Sosai angwayen keta rawar ƙafa abun. Bayan sun dawo da wata biyu. Sosai Afreen ta girma dan yanzu watanta biyar, in ka ganta kace ƴar wata bakwai ce. Rarrafenta ya nuna ko ina zataje, tayi kuɓul-ƙubul gwanin burgewa da ban sha'awa. Kuma yanzu aurensu Jalal saura watanni shida cus da izinin ubangiji. Yau asabar ne, tun safe Sheykh yana gida. Kiran sallan azahar ne yasa ya ɗan miƙe zaune bisa kujerar 3 str da yake kwance. Cikin lumshe ido ya kalli Afreen dake wasanta a tsakiyar falon. Shatu kuwa nata binta zata kamota, ta tubke mata gashin kanta. A hankali ta zauna tare da cewa. "Allah na gaji in biki, nan ki zille can in biki can ki zille nan, na lura sam bakya son a taɓa miki kanki". Murmushi yayi tare da cewa. "Waya sani ko ke ta gado". Da sauri tace. "Sai dai in Junainah ta gado". Miƙewa tsaye yayi yana murmushi. Sai kuwa yayi sauri ya koma ya zauna Kamar wanda aka ture ya faɗi. Da sauri ta miƙe tare da matsoshi cikin kula tace. "Subahanallahi Yah Sheykh lfy kuwa?". Hannun yasa ya dafe kanshi da kai, tare da rumtse idanunshi. Da sauri ta zauna ta jawoshi jikinta, kanshi tasa bisa ƙirjinta cikin sanyi murya tace. "Yah Sheykh baka da lfy ne". Manna kanshi yayi da ƙirjinta murya can kasa, kana ido a lumshe yace. “Ba komai fa Aish kontar da hankali ki". Cikin rau-rau da ido tace. "Ta yaya zan kwantar da hankalina kuma, in ka tsaya kai ɗaya kana shirin faɗuwa na lura da hakan da daɗewa". Ajiyan zuciya ya sauƙe kana a hankali yace. "Lfya ta lau Aish bakiga ma, yadda nake yawan cin abinci ba, bini-bini naci abinci, toh amman kuma wannan karon laulayin da jiri yazo min, musamman in na daɗe a zaune, toh in na tashi tsaye sai inga har duhu yana rufe min ido". Cike da mamaki tace. "Laulayi kuma?". Ta ƙare mgnar cikin zaro ido. Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. "Eh mana". Da sauri tace. "Waye mai cikin?” Tashi zaune yayi tare da cewa. "Kece mai cikin mana nine kuma mai laulayin". Da sauri tace. "Na shiga uku Yah Sheykh ciki kuma?nifa tun jinin biƙi ban sake yin jiniba". Kiss ya sakar mata a goshi kana a hankali yace. "Toh kafin wani jinin yazone kuma ciki ya shiga". Cike da al'hini tace. "Yah Sheykh ban ganeba". Cikin tsananin jin daɗi yace. "Allah kuwa Aish kinada ciki, na kimanin watanni uku har ya shiga na huɗu, yana ma gab da fara motsi". Da sauri ta ɗan ja da baya ɗage rigarta sama kaɗan tayi tare da zubawa cikinta ido, ya ilahi ya mujibadda'awati ta faɗa hawaye na kwaranyo mata murya na rawa tace. "Innalillahi Dr. Afreen na da watanta biyar kacal kuma ace ina da ciki, yarinyata zata sha wuya, na shiga uku". Da sauri ya jawota jikinshi ya ruggumeta tsam cikin kwantar mata da hankali yace. “Baki shiga uku ba Aish, al'janna zaki shiga da izinin Ubangiji, aihuwa rahamace Shatu, wasu suna nema ido a rufema Allah bai basuba mu kuma ya bamu. Kuma Alhamdulillah batun Afreen nima da fari hankalina ya tashi so da naga. Ba abinda nonon yayi mata sai ban damuba, ni yamin ma ko kin sani kawai kina ɓoye min ne, sabida kada in sani in nuna farin cikina har Magauta su gane shiyasa baƙi in gaya miki na gane". Cikin zubda hawaye tace. “Yah Sheykh daga haihuwa da kwana arba'in fa kenan na samu ciki". Dariya mai sauti yayi tare da cewa. "Ance miki ni ɗin wasane, bugu ɗaya nakeyi ƙollo ke shiga raga. Gashi kema ɗin ma zalamemmiyace da an baki saiki karɓa. Toh mu godewa Allah kinji ko Mar'atussaliha, muyi farin ciki da abinda Allah ya azurtamu dashi, kiyi Sujjadar godiyar Allah kiyi hamdala sai mu roƙi Allah yasa tagwaye ne, ina kina son ƴan biyu?” Cikin jin sanyi da daɗi tace. "Uhumm sosai ma kuwa Yah Sheykh". Kai ya ɗan ronƙofa ya sumbaci lips ɗin ta kana yace. "Toh Allah ya bamu". Amin Amin tace. Kana yaje yayi al'wala ya wuce masallaci. Ita kuma ta ɗauki Afreen ta wuce da ita. A falo ta samu Junainah ta miƙa mata ita kana ta wuce. Bayan kusan wata biyu kenan lokacin cikin ya cika wata biyar. Sosai ya ɗan fito cas sai kuma tayi yar ƙiba. Afreen kuwa yanzu tana dafa abu ta miƙe tsaye. Aurensu Jalal saura wata 4. Alhamdulillah tana fama da karatunta, kuma wanda yanzu suke shekarar ƙarshe ita da Rafi'a shiyasa ma aka kai bikin da nisa dan Rafi'a ta ida. Tana ruggume da Afreen ta shiga Part ɗin Mamey, dawowarta daga makaranta kenan. Da sauri Mamey tasa hannu. Ta amshe Afreen sai kuma ta kalli Sara dake biye da ita a baya tace. “A'a Sara ya haka, kin barta da jaka da wannan lukutar ƴar tasu". Cikin sauƙe numfashi tace. "Wlh Mamey Afreen na min son inna a soka asha jinin jikinka, wai sai taƙi Sara ta amsheta dole sai ni zan riƙeta". Ta ƙare mgnar tana dungure kanta. Dariya ta karketa kanar tasan abinda akace..ita kuwa Mamey da sauri tace. "Toh Sara ɗauko mata abinci." To tace kana taje ta ɗauko mata. Bayan ta ɗauko ta ɗauki nata ta tafi. Ita kuwa Mamey serilac ɗin Afreen ta dama kana ta fara bata. Tana bata tana kallon Shatu. Sai kuma ta ɗan yi gyaran murya tare da cewa. "Da sauƙi ma ai duk da wahalan karatun da rainon bai sa kin rameba". Kanta ta ɗan sunkuyar ta kalli cikinta cikin yin ƙasa da murya tace. "Toh ba cewa yayi wai inada cikiba". Da sauri Mamey ta danne dariyarta tare da cewa. "Wai ne ma Shatu? Har yanzu a wai yake?". Cikin ɗan jin kunya tace. "Uhum". Nan dai sukayi ta hira daga bisani ta miƙe ta koma Part ɗin ta. Alhamdulillah shirye-shiryen aure nata kan-kama. Tare da shirin naɗin sarauta. Tako ina tako wani lungun da saƙon masarautun gargajiya na Arewacin Nigeria da kudancin, dama maƙotan mu kamarsu Niger, Cameroon, Chadi. Da dai sauransu duk takardar gayyatar naɗin sarautar sabon sarkin masarautar Joɗa ya riskesu. Shiri iya shiri akewa bikin da yake haɗe da ɗaurin auren mutane shida. Cikin Shatu kuwa ya girma ya fito ras, sabida yayi watanni takwas. Afreen kuwa Alhamdulillah tana gudu ko ina yanzu ga gwarancinta ras. Watanninta goma sha ɗaya amman in ka ganta zakayi zaton Yar watanni goma sha biyar ne. Alhamdulillah su Shatu sun kammala karatun su lfy, komai yayi yadda ake buƙata. Hajia Mama kuwa duniya tayi mata atishawar tsaki. Sabida kuturta ya kuma shiga yatsunta na tsuntsayen. A hankali take tafiya Afreen na riƙe da yatsarta. Tana ta gwaranci. "Abba! Abba! Abba!". Murmushi yayi tare da buɗe mata hannunshi da sauri ta tsaki yatsar Shatu ta nufi inda Sheykh ke tsaye, cikin tarin farin ciki yace. "Oyoyo Mamina". Kana ya ɗagata sama. Murmushi Affan yayi tare da cewa. "Afreen sarkin wayo ita kowa natane". Jamil ne yace. "Hmmmm ai ni jiya ta bani mmki. Wai Ance Abbanmu na kiranta zai bata sweet wai sai tace. “Bata so Abbanta a kawo mata". Dariya Ummi tayi tare da cewa. "Kuma daga baya ta bishi da gudu tana Abba cha ciwiut". Murmushi Sheykh yayi kana ya sauƙeta, tare da kallon Shatu dake zaune ta tasa cikinta gaba. Cikin wasa ya kalli Jalal daya shigo yanzu yace. "Jalal ko dai zamu ɗaga bikin kun nanne sai Aish ta haihu zatafi sakewa". Da sauri ya katse wayar da yakeyi da Hibba tare da cewa. “A'a me yayi zafi, tasha zamanta a ɗakinta mun hutasshe ta zuwa bikin". Jamil kuwa kwaɓe fuska yayi tare da cewa. "Uhumm wai a ɗaga". Dariya Affan yayi tare da kallon Sheykh dake musu murmushin wasa nan dai sukaci gaba da tattaunawa kan bikin. Alhamdulillah yau bikinsu Jalal saura mako ɗaya rak. Komai ya kankama. Tuni baƙi sun fara cika masarautar Joɗa tako wani yanki. Hotels din Ɓadamaya Lamiɗo da Sheykh sun kama fiye da rabinsu sabida, sauƙar baƙin da suke tsastsafowa tako wani yanki. Yau jumma'a wanda ya kama sauran kwana bakwai cin a nawa Sheykh rawani jumma'a mai zuwa kenan. Wanda ya kama kuma ranar za'a ɗaura aurensu Jalal tuni su Umaymah da tawagarta sun iso. Tun da safe kuwa yau Shatu ta tashi da ciwon mara, kaɗan-kaɗan. A haka take ta sabgoginta, sabida tana tare da amare duka uku. Sha ɗaya dai-dai na safe Allah ya sauƙeta lfy ta haifi ɗanta na miji santalele. Farincikin a ahlin Sitti ba'a mgn. Bayan an gama kimtsa mai jego da jaririnta kato fari ƙal dashi. Suna kwance Sheykh ya shigo. Cikin tarin farin ciki dan yana gidan Malam Abubakar ne Yah Jafar ya kirashi ya masa al'bishir. Cikin jin daɗi ya zauna gefen Shatu. Tare da miƙawa Safiyyah hannu ta miƙa mishi jaririn murya cike da zallan farin ciki yace. "Alhamdulillah masha Allah. Allah na gode maka, da wannan kyauta da kaimin. Ya Allah kasa baɗi iwar haka mu samu tagwaye". Dariya sukayi baki ɗayansu ganin yadda Shatu ta zaro idonta cikin alamun tsoron tace. "Wayyoooooooo Allah na. Yah Sheykh sai kace wata inji". Aunty Rahma ce tace. "Ato ai da alamar hakan zakuyi tunda gashi a shekara ɗaya an samo irin tagwayen Nana Faɗima". Ummi ce dake gefe tana fifitawa Shatu tea tace. "Ko ƴan ukune Allah ya kawosu akwai masu tayaki rainon su. Inji gashi yanzu Afreen tunda aka yayate, sai dai tazo ta leƙaki tayi gaba abinta". Da sauri yace. "Uhumm yauwa Ummi na gaya mata dai". Ya ƙare mgnar yana sumbatar goshin yaron cikin tsananin farin cikin da son yaron. Sai kuma ya kalli Mamey dake shigowa yace. "Mamey da waye yake kamane?". Matsowa gabanshi tayi ta kalli fuskar jaririn kana tasa hannunta ta tallabo tashi fuskar. Cikin jin daɗi tace. "Da kai yake kama". Cike da jin daɗi yace. "Alhamdulillah". Nanfa akaci gaba da hidima. Yau kwana biyu da haihuwar Shatu. Zaune yake agaban Mamey da Abbanshi, kai ya ɗan ɗago ya kalli Abbanshi tare da cewa. "Ummm Abba nace wanne suna za'a sawa yaron?". Murmushi mai cike da jin daɗi Abba yayi tare da cewa. "Na baka zaɓi zaɓawa ɗanka sunan da kafi so". Murmushi mai cike da jin daɗi yayi tare da cewa. "Mamey kefa, ko Jadda kikeso inyi mai suna". Yayi mgnar cikin raha. Da sauri tace. "Mutun da ɗan shi mun baka damarka a matsayinka na uba". Kanshi ya sunkuyar tare da cewa. "Ngd matuƙa da wannan damar". Daga nan ya sallamesu ya miƙe ya fita. Bedroom ɗinsa ya wuce. Yana shiga ya kira Shatu a waya, ta kawo mishi ɗan. Yayi mishi huɗu ba. Ido ta ɗan zuba mishi tare da cewa. "Me sunanshi?." Murmushi yayi tare da kashe mata ido a hankali yace. "Sai ranar suna zakiji". "Abinma sirrine kenan". Ta faɗi tana murmushi. "Ina da wani sirrine bayan ke, Y.M.D.G na". Ido ta zuba mishi tana mai nazartar baƙaƙen da yake yawan faɗi wasu lokutan. Kiranshi da akayi a wayane yasa ta bar zancen. Ranar jumma'a, da safe bayan an fito sallan asabu, aka raɗa sunan yaron kana suka nufi cikin gida kowa na mamakin sunan da Sheykh ya sawa ɗansa. A tare suka shiga falon shida ƙannensa. Da sauri Mamma tace. "Affan me sunan ɗan naku?". Murmushi Affan yayi tare da nuna Sheykh dake wucewa Side ɗinsa Haroon da Ibrahim na biye dashi a baya. Da sauri Umaymah tace. "Affan me sunan ana tambayarka kayi shiru". Cikin dariya yace. "Uhumm Yah Sheykh da abun mmki sunanshi fa ya sawa ɗan, duk zuriyar mun nan ya rasa wanda zaiwa takwara sai yayiwa kanshi". Cike da mamaki su Ummi sukayi salati, shi kuwa Sheykh murmushi yayi tare da juyowa jin yadda suke salati yana dariya yace. "Yoh duk zuriyar mu, nuni wanda sunanshi ya kai nawa daɗi Muhammad Jabeer, kuma kafin in burge wani gwara in burge kaina da kaina. Kuna ina son yaron yaji daɗin da nakeji a duk sanda naji an kirani da sunan sabida iyayena sunmin kekkyawan zaɓi". Murmushi Mameyn tayi tare da cewa. "Allah ya raya Muhammad Jabeer ƙarami yasa ya gaji halayyar mahaifinshi". Amin Amin sukace baki ɗayansu. Ita kam Shatu murmushi takeyi tana shafa kan jaririn. Tare da kallon Afreen dake zaune gefenta. Oh Allah mai iko wai itace dai Shatu da yara har biyu. Nan dai sukaci abinci. Kana duk mazan suka fara shirin fita ɗan sha biyu dai-dai za'a naɗa Sheykh. Ƙarfe ɗaya saura. Duk illahirin manyan Masarautar Joɗa, da baƙin sarakuna. Da duk maza ahlin masarautar Joɗa, hatta Jabeer da yau aka fita sunansa. Jalal yazo dashi. Gaba ɗaya ɗakin rantsawar ya cika maƙil da bani Adam. Babu abunda ke tashi sai sarewa da tambura da al'gaita da kakafi. A hankali Lamiɗo ya tashi bisa kujerar, kana ya matsa. Sarkin naɗi, ya kamo hannun Sheykh dake cikin shiga ta al'farma shigar limancin. Ya matso dashi gaban kujerar, kana a hankali yasa hannunshin ya zare hiramin kansa. Sannan ya sunkuyo ya amshi. Rawanin da Lamiɗo ke miƙa mishi. Yana daga tsayen ya naɗa mishi. Kana ya juyo bayanshi da niyar zare al'kyabbar jikinshi. Da sauri Lamiɗo yace. “A'a barshi da shirgarsa ta limancin, shigar sarauta bazata kori ta limancin ba.". A hankali Sheykh ya lumshe idonshi yana mai jin wani irin masifeffen nauyi dake ratsa kanshi nauyin rawanin mulkin Masarautar Joɗa. Shi kuwa Sarkin naɗi kai ya gyaɗa kana ya zaunar da Sheykh bisa asalin kujerar masarautar Joɗa da sunan Allah a bakinsa. Kana aka miƙa mishi sandan ya amsa ya riƙe, sarkin fada ya matso kusa dashi. Hakama ɗan zagi. Sauran fadawa kuwa duk sai suka matsa suka janye labulen da sukayi musu da manyan garunan su. Lokacin ɗaya gaba ɗaya mutanen cikin hall ɗin duk suka zauna Tare da jinjina kai, dan ko kai sarkine in kazo Masarautar wani sarkin to shine a sama. Sabida kalmar nan ta bahaushe. (Kare ma a gidansa zaki ne) Bare kuma sarki. Nanfa makaɗa da mabusa duk suka ɗauki amo. Cikin wani irin rauni Sheykh ya lumshe idanunshi tare da ci gaba da tasbihin da yake abokin rayuwarsa. Sabida wani irin tashi da tsikar jikinshi keyi. Sarautar tana ratsashi. Bayan an gama naɗa shi ne, aka naɗa Baba Basiru a matsayin Galadima. Wanda dama anfi son Galadima yafi sarki shekaru. Nan kuma aka naɗa Affan Chiroma. Kana Jalal Wambai, Jamil Durbi. Yah Jafar kuwa Majidaɗin Masarautar Joɗa. Masha Allah komai dai ya tafi yadda ya kamata. Nan aka naɗa duk sauran hakimai. Kiran sallan Jumma'a ne ya tadasu a taron. Nan kuma aka raka'a. Inda Sarki Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa ya kasance limamin kamar kullum. Bayan ya tsaya ya dai-dai-ta tsayuwarsa bisa mimbari. Ya fuskanci taron al'ummar Annabi dake cike maƙil a masallacin da harabar. Gyaran murya yayi cike da rauni dan fara hudbar jumma'a kamar kullum. Cikin taushin murya da lafazi. Murya na rawa yace. "Mulki, da sarauta". Sai kuma muryarsa ya fara rawa, sabida nauyin abinda yake jin tsoro daya ratsa kanshi. Hawaye na zuba yace. “Da ace ɗan Adam yasan nauyin dake cikin kalmar mulki ko sarauta da bai ɗauke ta ƙaramar kalmaba. Da daga cikinmu mun dena sha'awarta sabida nauyi da haƙƙin wanda kake matsayin shugaban su, da zai rataya akanka". Sai kuma ya sunkuyar da kansa. Cikin rauni da zubda hawaye ya fara zazzafan hudba kan sarakuna da kuma shugabannin. Wanda gaba ɗaya aka nitsu akayi cib. Mafi akasarin mutane rauni da tsoro ya sasu zubda hawaye. Bayan ya idane, akayi salla aka idar. Sannan dubban al'ummar Annabi Sallallahu alaihi Wasallam suka shaida ɗaurin auren. Jalaluddin da Muhibbar, (Jalal and Hibba) Khadijah da Jamil. Rafi'a da Al'ameen. Al'amarin yayi armashi matuƙa gaya. Nan aka fito, mafi akasarin manyan sarakuna da shugabanni da baƙi a take Airport suka fara wucewa, sabida komawa. Jirage kuma a ranar tamkar a jidda Airport a lokacin aikin Hajji. Haka jirage ke tashi. A Ɓadamaya International Airport. Tuni mutanen Cameroon sun tafi da amryarsu. Da duk mutane su. Hakama su Aunty Rahma sun kai Hibba part ɗin ta. Mutanen Cameroon kafin su tafi sun kai. Khadijah Part ɗinta. Sosai mutanen gidan suka ɗan rarragu. Sheykh kuwa hada-dadar jama'a ta hanashi shiga gida. Sabida zaman fada. Sai bayan sallan isha'i ya samu shiga gida. Kai tsaye Part ɗin Mameynshi ya wuce. A can kuwa ya samu su Umaymah gaba dayansu. Sai Shatu da Junainah dake Part ɗinsu suna gyarawa sabida mutanen sun tafi. Cikin jin daɗi Mamey da yan uwanta sukayi ta sanya mishi albarka da mishi addu'o'in Allah ya bashi ikon mulki kan gsky. Ga mamakinsu yana kuka. "Amin Amin". Daga nan ya fito ya nufi Part ɗinsa. Ita kuwa Shatu tuni sun gama kimtsa komai. Har tayi wonka, ta kimtsa cikin wata tattausar doguwar riga mai ɗan karen kyau. Afreen da Jabeer kuwa dama Ummi tayi musu wonka kafin ta tafi. Tana ruggume da Jabeer Afreen na biye da ita a baya ta nufi Side ɗinsa. Jin Junainah na ce mata. Adda Shatu Hamma Jabeer na kira. A hankali ta tura ƙofar tare da sallama a bakinta. Cikin sauri ya juyo dan dama bai ƙarasa shiga tsakiyar ɗakin ba. Wata iriyar sassayar ajiyar zuciya mai sauƙi Shatu ta sauƙe. Sabida ganinsa cikin shigar sarakuna yayi masifar ratsata kwarjininsa ya ninku ɗari bisa ɗari. Afreen kuwa da gudu ta nufoshi. Ta isa ya sunkuyo ya ɗagata sama, ya ruggume ta tsam a jikinshi da hannu ɗaya. Kana ya buɗewa Shatu hannun ɗaya. Da sauri ta iso ta faɗa jikinshi. Ruggume ta yayi tsam a jikinshi. Cikin sanyi murya na rawa yace. "Aish bayan nauyinku. Ke Afreen Jabeer da kai tsaye in ance iyalaina ku ake nufi. Kana Abbana Mamey dasu Jalal da in ance ahlina su ake nufi. An sake ƙara min nauyin da duk Ɓadamaya nine shugaba a garesu kuma abin dubawarsu". Tasan mijinta tasan rauni sa. Tabbas tasan baison mulkin nan, tamkar dolene. A hankali ta kuma ruggume shi gam jin yana cewa. "Mulkin nan yana ɗaya daga cikin manyan abubuwan da Lamiɗo ke tirsasani inyi a rayuwata. Sai dai na yarda da batun mulkin ne bisa Kekkyawar niyar yin gyara da kauda al'adun da ba tsarin shariya ba, da kuma kauda wasu abun da suke kamanceceniya da asiri". Cikin jin daɗi tace. "Allah ya baka ikon gyara ya kuma kare mana kai da kariyarsa. Ya baka rai da lfy da damar gyara al'farmar Annabi da al'ƙur'ani". Amin Amin yace cikin rauni. Alhamdulillah komai ya dai-dai-ta. Kab baƙin sun koma. Lamiɗo kuwa tunda aka naɗa Jabeer dole ya bar masarautar Joɗa domin ba'a sarki biyu a gari ɗaya. Dole ya koma Mubi da zama, sai dai Sheykh na yawan kai musu ziyara. Yana ɗaya daga cikin abinda yasa yaji baison Lamiɗo yayi murabus ya bashi mulki sabida yasan za'a nesan tasu. Junainah taci gaba da karatunta, nan cikin Joɗa. Junaidu ma yayi nisa da karatunsa. Alhamdulillah anyi auren Yah Salmanu da Hafsi ma, kana Yah Gaini da Binto. Yah Seyi da Mari. Sai Yah Giɗi kuma da yar Jamila ƙanwar Junaidu mai binshi. Rayuwa na juyawa, lokacin na tafiya, wuni zuwa kwana. Kwana zuwa mako. Mako zuwa wata. Wata zuwa shekara. Alhamdulillah an yaye Jabeer lfy lau Afreen nada shekara biyu da rabi shi yanada shekara ɗaya da rabi. A cikin haka ne Sheykh ya Haɗe kan ahlinsa suka tafi aikin hajji. Sosai sukaji daɗin zuwan domin kab ahlin Sitti sunje. Bayan sun dawone Shatu ta fahimci tanada shigar wani cikin. To Alhamdulillah wannan laulayinsa son sex ne Sheykh ya zama ba sauƙin. Yana fada ma in ta ciyosa zai gudo yadawo. Alhamdulillah Kuma haka dai sauke tafiya, wasu lokutan Shatu kan gudu ta koma Part ɗin Mamey. Yanzu cikin ya fara girma. Yauma kamar mafi akasarin lokuta. Suna zaune a falonta. Ita da Khadijah da Hibba wanda suma sunyi haihuwar farinsu. Kuma yawanci yanzu Afreen tana Part ɗin Hibba da Jamil. Shi kuwa Sheykh da sauri ya wuce Side ɗinsa yana cewa. "Mitcwww a wani saka tafiya a hankali kamar Wahainiya wai kai sarki. A riƙeka a fada a hanaka ganin iyalinka a duk sanda kake so. Mulki ko jaraba". Ya ƙare mgnar yana kiran Shatu a waya. Cikin kwaɓe fuska tace. "Na'am Hamma". Koikoyan muryar ta yayi tare da cewa. "Na'am Hamma. Dan Allah kizo kinji ko Shatu na. Kizo miyi wata mgnar dan Allah kada kice a a". Cikin sanyi tace to. Kana ta miƙa ta fita. Tana shiga ya juyo yana zare al'kyabbar jikinshi tare da cilla rawaninshi gefe ruggume ta yau tare da cewa. "Itta wannan harka da kike gani, babu ruwanta da rawanin sarki ko matsayinshi dole yayi ƙasa da ita yayi mubaya'a". Ya ƙare mgnar yana longoɓar da kai bisa kafaɗa. Murmushi tayi tare da cewa. "To me kuma kakeso?". Kanta ya nuna mata da ƴar tsarshi tare da cewa. "Abun daɗi na, nakeso". Ya ƙare mgnar yana zuge zip ɗin rigarta yayi ƙasa dashi. Murmushi tayi tare da kamo hannunsa ta daura akan mararta, cikin yanayin sanyi da shagwab’a tace. “To naji amma saidai kamin alk’awarin cewa bazakayi sosai yanda zaka takurawa unborn dinmu ba.” “Eh na amince.” Yafada yana me hade goshinsu waje daya, tare da daura lips d’insa akan nata ya shiga tsotsa, wani irin dadi yakeji sosai aduk lokacin daya gansa atare da Shatun. Kasa yayi da rigar jikinta tareda zame kansa ya daura bakinsa akan tsayayyun breast dinta. Cikin wani irin salo na musamman yake sucking nipples dinta, hakanne kuwa yasa duk ta rude masa, azafafe ta shiga aika masa wasu salo na musamman daya sa ƙafafunsu kasa ɗaukarsu, cikin zakuwa da kuma tarin sha’awarta dake damunsa, ya ɗagota caɗak suka ƙarasa kan makeken royal bed ɗinsu, daya sha zanin gado na alfarma. Shumfudeta yayi asaman gadon tare da zare mata duk wani kaya dake jikinta, cikin yanayin dake nuna tsananin shaukinta da yakeji, ya soma kissing din kowani gaɓa dake jikinta, more especially saman mararta da kuma kan breast dinta, saboda ya fahimci cewa aduk lokacin da yake kissing dinta awajen tanajin dadi sosai. Wani irin numfashi mai haɗe da nishi taja alokacin da taji saukan harshensa acikin privet part ɗinta, Idanunta ta lumshe tare da sake turo masa jikinta, saboda yanayin yanda yake tura harshensa garets yasa duk ta kara zaucewa. Haka shidinma gaba daya jikinsa rawa yake, musamman ma ayanzu da yaji yanda Shatun nasa ke leaking abun ba’a cewa komai. Wani irin sautin nishi na musamman suka sake atare, a dai-dai lokacin da taji manhood ɗinsa ya ziyarceta. Rungumeta yayi sosai tare da soma yi mata sambatu kala kala, wanda kuma tasan duk pleasure din da enjoying ya sasane. Domin ta fahimaci yanda ayanzu Sheykh din ke masifar enjoying mood Dinsu idan suna sex. Tabbas ayau wata duniya suka fada ta musamman, duniyar da daɗinta ya kusan zautar da Sarki kuma Sheykh Jabeer, domin wasu kalan sambatu da godiya ya dinga yiwa Shatun nasa, saboda dadin da tajiyar dashi ayau din na musamman ne. Domin kuwa bayan sex harda blowjob ta haɗa mishi, wanda dadinsa ya kusan gusar masa da tunani. Bayan komai ya lafane kuma, sun fito wonka. A hankali ta kalli wayarshi dake gefenta wanda kira ya shigo cikinta yanzu. Leƙowa yayi ya kalli wayar da sauri kuma ya juyo ya kalleta ganin taga wacce ke kiran nashi, Da sauri yasa hannunshin zai dauki wayar. Cikin sauri ta...! By *GARKUWAR FULANI*Ta juya kanta, ganin kamar baya son taga wayake kiranshi. A hankali ta miƙe tsaye tare da juyawa ta fita. Shi kuwa Sheykh, a hankali ya sauƙe ajiyan zuciya mai nauyi. Murya a daƙile yace. "Assalamu alaikum". Cikin yanayin tarin so bege ƙauna mai tsanani Jazrah ta saki wani irin sassanyan kuka murya na rawa fuska na zubda hawaye tace. "I love you Jabeer I love you so much in sha Allah bazan taɓa yin aureba in dai bazaka aureni ba." Cikin sanyi da tausayin yadda take kuka muryarta na rawa. Ya sani ya shaida Jazrah na mishi wani irin masifeffen so. Tunda a kanshi taƙi tayi aure. Babu yadda ba,ayi da itaba taƙiya. Cikin daƙilewa yace. "Thanks". Murmushi tayi cike da jin daɗin yadda yanzu yana amsa kiranta har ya saurareta, yau kuma ga ƙarin godiya. Ta buɗe baki zatayi mgn kenan taji yana cewa. "Please ki dena kirana ba tare da izinina ba. Ki gaya min ta text in na gani na baki lokaci sai ki kirani." Da sauri tace. "La ba'as". Daga nan ya katse kiran Yana mai ta ajjudin kafiyar Jazrah. A hankali a haka dai rayuwa tai ta juyawa. Lokacin na tafiya kwanaki na shiɗewa makkonni na juyawa zuwa watanni na gangarawa zuwa shekaru. ***** Bayan shekaru shida. Tuni yanzu Junainah ta zama cikekkiyar budurwa ƴar shekaru ashirin da ɗan ɗori. Tuni Junaidu ya kammala karatunsa har ya kama aikinsa da taimakon Sheykh. Soyayyarsa da Junainah kuwa ta kankama ta haɓaka manya sun saka baki. An gama komai na al'adar aure kamar tambaya da kai kayan aure. Daga bisani ansa rana nanda wata ɗaya rak. Alhamdulillah Shatu kuwa yanzu yaranta shida. Afreen. Jabeer. Muhammad. Abdulkarim. Habib. Khausar. Afreen, Jabeer, Muhammad takwaran bappanta, suna kiranshi da Bappan. Abdulkarim takwaran baban Sitti wanda randa tsohon ya rasu ranar aka haifeshi. Sai Habibullah takwaran Daddy kausar. A cikin shekarun shidan nan abubuwa da yawa sun faru, a ciki harda rasuwar. Jadda da Galadima. Yanzu Shatu ta zama cikekkiyar matar sarki mai iko. Gimbiya Saudatu kuwa ta haɗe da Mamey gwanin burgewa. Hajia Mama kuwa tana nan ita ba mutunba ita ba dabba ba. Gaba ɗaya matansu Jalal sunada ƴaƴa uku uku. Sosai aketa hidimar bikin ƴar auta. Yau tun da safe Sheykh bai fita fada ba. A cewarsa yau ranar Shatu ce. Dan yau suka cika shekara goma biyu ɗaya da aure. Suna cikin yaransu. Afreen da yanzu takeda shekaru goma da ƴan watanni a duniya tayi caras da ita gwanin kyau. Jabeer kuwa tuni ya kerera tsawo da girman jiki sau tari in waɗanda basu sansuba suka gansh akanyi zaton shine babban. Gashi shi halittar mahaifinshi Allah ya bashi kwarjini da kamala. Shiyasa tsama sosai ke tsakaninsu. Yanzuma tsaye take a gabanshi yana zaune bisa kujera yana lumshe da ido yana bitar addu'arsa cikin suratul Anfal. Cikin tsiwa da mamyancen son girma tace. "Daddy ba Kai nakewa mgna ba". Da yake haka suke kiransa kasan cewar sunan babansu gareshi. Tsaki taja tare da cewa. "Ina maka mgn ka manna min hauka ina ka ajiye min System na". A hankali ya buɗe idonshi ya kalleta, kasan cewar yaje ƙarshen surar. Murya can ƙasa yace. "Kifa dena min ihu a kaina, nace miki ban ɗauka ba, bana da shine da zan ɗauki taki argar ma". Cikin hatsala tace. "Ni kake cewa ina ihu Daddy ni mahaukaciyace da zakace ina maka ihu a kai. Wlh ka fito min da abuna". Bakinshi ya taɓe tare da cewa. "Masifeffiya ba sai kiyi ta yiba". Yana faɗin haka ya meda kanshi ya jingine ya lumshe ido alamun zaici gaba da bitar sa. Aifa ina wuta ta faɗa ciki. Cikin son girma da tsiwa tasa hannu ta dungure mishi kai cikin ɗaga murya tace. "Nice ma masifeffiyar ko Daddy, sabida raini". Murmushi mai yalwa Sheykh yayi jiyo yadda taketa masifan. Shi kuwa Jabeer sai yayi mgn kona kusa dashi bai jiba. Cikin dariya yace. "Wai Afreen kam meyasa takeda neman rigimane?". Da sauri Shatu dake gabanshi tana rage mishi kayan jikinshi tayi kwaffa tare da cewa. "J baya fa jin mgn wlh shike tsokanarta ƙasa-ƙasa". Murmushi Sheykh yayi sabida yana matuƙar jin daɗin sunan da take kiran Jabeer ɗin. In ba ya ƙureta ba da wuya ta kirashi da cikekkin sunanshi sai dai tace (J) ko kuma Mahmoud. Cikin ɗan ɗaga murya yace. "Afreen wai me nene kam?". Ya ƙare mgnar yana juyowa ya fito falo. Da sauri itama Shatu ta biyo bayanshi. Ita kuwa Afreen dake ta sababi ita ɗaya da sauri ta nufi falon Side ɗinsa da yanzu an bunkasa masa shi akwai ƙofar shigama ta gefe. Murya na rawa ido na zubda hawaye tace. Assalamu alaikum. Cikin nitsuwa ya zauna bisa kujera tare da ɗaura ƙafarsa ɗaya bisa ɗaya. Tare da cewa. "Wa alaikassalam shigo". Ya ƙare mgnar da sanin in ba yace ta shigoba nan zata tsaya. A hankali ta shigo gefenshi kusa da Shatu ta durƙusa tare da fara mgnar murya na rawa tace. "Abeey ai Daddy ne ya ɓoye min System ɗina, na tambayeshi kuma yace wai ina mishi ihu a kai, wai ni mahaukaciyace fitsarerriya wai." Danne murmushin sa yayi tare da cewa. "Jabeeer!". Da sauri ya miƙe cikin tsananin biyayya ya shigo bayan yayi sallama an bashi izinin shiga. Gefen Afreen ya tsuguna tare da yin ƙasa da kansa a hankali yace. "Na'am Abeey". Cikin tarin son yaron yace. "Me yasa zakace mata fitsarerriya?". Cikin tanƙwashe wuya yace. "Abeey ihu take min a kai kuma bitar hadda nakeyi". Da sauri yace. "Na'am wato dai ka gaya mata hakan?". A hankali yace. "Eh". Cikin danne dariyarsa yace. "Bata haƙuri". Da sauri ya ɗan juyo ya kalli Afreen cikin sanyi da ladab yace. "Kiyi Aunty Afreen bazan ƙaraba". Cikin yanayin son ɗan uwantaka tace. "Na yafe". Wani irin murmushi yayi tare da cewa. "Ina system ɗin nata?". Cikin sanyi yace. " Bappa nefa ya ɗauka ya tafi Part ɗin. Mamey dashi. Shine Khausar kuma tace mata nine na ɗauka". Murmushi Sheykh yayi tare da cewa. "Toh kinji ko Mamina a rinƙa bincike kafin ayi masifa ko!." Daga nan ya sallamesu suka fita. Jawo Shatu yayi ya ruggumeta gam-gam a jikinshi cikin tarin farin ciki yace. "Nafi jin daɗi da al'faharin in ganni tsakiyar yaranmu suna rigima ina sasantasu. Da yanke hukunci nan nake jina a cikekken sarki mai iko da dama da matsayi. Fiye da in ganni a fada in mulkar masararutar Joɗa dattawa na zama a ƙasa na." Cikin jin daɗi tace. "Na lura ai kana jin daɗin hakan". Yatsarshi yasa ya ɗan lakace hancinta tare da cewa. "Eh mana, sabida su ƴaƴa farin cikinsu nada yawa a rayuwar iyaye. Duk yawansu bazaka banbance sonsu ba. Kamar dai tsakanin mata in kana dasu sama da ɗaya." Shiru tayi tana kallonshi sabida taji ya saki layin zancen kuma, ta dade da fahimtar akwai abinda yake jimamin sanar mata. Shi kuwa ganin yadda ta tsareshi da idone ya sashi. Sauƙe numfashin sa tare da gyara zamanta a jikinshi. Murya cike da nagarta, kamala, nitsuwa, da tausasawa, yace. "Kin san meyasa nace miki haka". Kai ta jujjuya mishi alamun a'a sabida wani irin tsinkewa da zuciyarta ya fara. Shi kuwa a hankali yace. "Bari in miki kekkyawan misali. Kinga dai Afreen ita muka fara gani muka fara haifa ko. Ita Allah ya fara nuna mana matsayin ƴarmu ta cikinmu ko?". A hankali tace. "Eh". Cikin nitsuwa yace. "Gud to kinga dole ita muka fara so da sabo da ita da jin farin ciki da ita da buri da fata, da komai a kanta kawai mukayishi tsawon watannin da mukayi kafin ki haifo mana Jabeer ko?". Stiil kai ta gyaɗa mishi zuciya na tsinkewa. Shi kuwa hannunshi yasa cikin rigarta tare da cewa. "To kuma Alhamdulillah da muka samu Jabeer. Sai shima muka fara sonshi da begenshi da al'faharin samunshi. Ba tare da kuma mun dena don ita Afreen ɗin ba ko?". A hankali tace. "Eh." Kiss ya ɗan manna mata a saman breast ɗinta kana yaci gaba da cewa. "Kuma son da mukewa Afreen na forko bamu rageshi ba, saima ƙaruwar da yakeyi sabida tana girma muna ƙara shaƙuwa da ita, son kuma da muke mata bai hana muso shi Jabeer da yazo daga baya ba, har kuma muke jinshi matsayinsu dai-dai da nata. Sai dai mun san ta fishi girma dole mu nuna mishi ya bata girmanta". Cikin sauƙe numfashi tace. "Eh". A hankali yace. "Kuma gashi bayan Afreen da Jabeer ɗin yara huɗu Allah ya sake bamu, kuma duk muna sonsu, son sabbin bai ƙori na tsoffinba ma'ana sonsu Khausar bai kori na Afreen ba. Ita kuma Afreen sonta bai hana sonsu Khausar ba. Duk muna sonsu muna ji dasu, sai dai dole babba babbene kuma dole mu sosu tunda Allah ya bamu su." A tare suka sauƙe ajiyan zuciya. Harshensa ya ɗan zaro yana lasar saman breast ɗinta. Saida yaga ta ɗan nitsu kana a hankali yace. "Toh wannan itace cikekkiyar misali tsakanin miji da matasan son uwar gidan bazai taɓa hana na amrya ba. Haka kuma son amrya da take sabuwa bazai taɓa hana son uwar gidan da take sun dade tareba. Asalima tanada. Tata kimar da darajar a matsayinta na babba, wannan shine misalin daya kamata duk matan duniya ku gamsu dashi. Ki dena zaton wai in an auro amarya za'a dena sonki. Wlh sam ba haka bane uwar gidana. Ke kuma amarya ki daina gigi da zaton wai ba'a son uwar gidane ko an gaji da ita ko yayinta ya wucene aka auroki. Wlh sam ba haka bane." (Wannan itace falsafa mai kyau, in dai ke ba jaka bace ya za'ayi kiyi zaton dan ya auroki zai daina son uwar gidansa. Ke kuma uwar gida in banda kishi me zaisa kiyi zaton ke kece sama dake aka fara to ai uwarsa ma na nan kuma bare ke daya sameki rana tsaka da haƙora talatin cas a baki nai. Dan zai auro wata sai kiyi zaton ai dai nice uwar yayanshi. To babu ruwan soyayya da uwar yaya. Ke dai dage ki iya allonki ki wonke. Da kekkyawan mu'alama amrayar kanta zatafi girmamaki da ganin darajarki.) Cikin wani irin masifeffen maƙoƙon kishi kumallon mata da kuma tsantsar karantar miji da fahimtarsa murya na rawa hawaye na zuba cike da rauni Shatu tace. "Allah ya bamu zaman lfy Yah Sheykh, ƙarin aure ba laifi bane. Allah fa da kanshi ya baku wannan damar". Cikin rawan jiki da tausayin rauninta wanda yasan dole taji kishi. Cikin sanyi yasa harshensa bisa haɓarta a hankali ya fara lasar hawayenta cikin tsananin son da ganin darajarta da yabawa da kulawarta da fahimtar abinda yake son sanar mata. Shiru tayi tana jin ɗumin harshensa shi kuwa cikin sake mata kiss tako ina yace. "In bakya so ki gaya min Aish sai in fasa auren." (Toh sokuwa kada kiji mijinki yace wai in bakya so zan fasa, kice zakice bakya so. Yaseen farfaganda ce kawai, da son kwantar miki da hankali da irin su nuna miki kin isa dasu ɗinanne, kada kiyi zaton zasu tozar taki. To da kinyi wautar cewa eh. Ni bana so ban aminceba kada kayi aure. To kallon sokuwa zai fara yi miki yoh to ke uwarsace da zaki hanashi yin auren da Allah ya bashi damar yayi. Ke kuwa amrya uwar kaɗi firi ki shigo rana tsaka ki nunawa uwar gida kin fita sanin mijinta. Wawuya to wayayyu basa haka, wai ke irin ke ake so ɗinnan irin anai miki zaƙin bakin nan, to wlh kada ki kuskura kiyi zaton uwar gidanshi bata gabanshi maza bakin gangane duk ta inda yafi zaƙi ta nan suke bugawa. Domin dolene ya miki wannan zaƙin bakin. Sabida ai duk ɗan siyasa dole yayi kamfen yayin neman a zabesh to, hakama neman aure, kisa a ranki yana son matarsa. Kema mada kisa a ranki amryafa ana sonta sannan uwar gida kiyi haƙuri domin amarya ko ta buzuzuce za'ayi mata marmari, in kinga yana rawa da ƙafa ɗaya tattara ki watsarsu, basu lokaci zai dawo har kataryarki ya nemeki. Cikin tsananin zafin kishi Shatu tayi ajiyan zuciya data samu ya danne mata malolon da takejin yana gab da kasheta tace. "A'a Yah Sheykh na amince Allah ya bamu zaman lfy". Cikin tarin jin daɗi da gamsuwa da wayewarta yace. "Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati, Shatu my happiness my everything my life Mar'atussaliha". Ya fara jero mata sunaye, wani sunanma ranar ta taɓa jinshi. Da sauri ta miƙe ta fita. Tana cewa. "Laa na manta na ɗaura tukunya". Ta faɗi hakan tana fita dan kada ya gane halin da take cikin ( Sabida in mijinki ya gane miki kinada mahaukacin kishi to kallon zarerriya zai rinƙa miki, hattara mata). Tana fitowa bedroom ɗinta ta wuce. Tana shiga ta meda ƙofar ta rufe, kana ta faɗa bisa gado ta saki wani irin masifeffen kuka mai cike da kishin mijinta abin sonta. Da sauri Junainah dake Bathroom ɗin ta tanayiwa Khausar wonka ta fito. Gefenta ta zauna jiki na rawa tace. "Innalillahi Adda Shatu meya sameki meya faru?". Kawai sai ta mirgina ta ɗaura kanta bisa cinyar Junainah ta saki kuka mai rauni tare da cewa. "Ba komai Junainah na tuno su Yah Lado da Inna ne". Cikin rashin gamsuwa Junainah tace. "Adda Shatu wai yaushe kika fara ɗaukana a matsayin ƙanwar Hamma Jabeer? Kin mance tare muka tashi muka rayu bani da wani ɗan uwa ko ƴar uwa sama dake, gaya min gsky meya sameki?". Cikin yin ƙasa da murya tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa. "Yah Sheykh zai ƙara aure Junainah na kasa hana kaina kuka!". Murmushi Junainah tayi tare da cewa. "Shine zaki ɓoye min, to sa a ranki ni nan Junainah ko Ishman Aunty Rahma ya auro ni mai tayaki kishine. Kuma wlh auren a dole yazo mishi kana kada kiyi kokonton soyayyarshu gareki. Allah dole Abba ya sashi amsar auren Mamey ma har kuka tayi ita da Ummi wai kuna zamanku lfy kada a birkita muku zama sai dai naji sunce itama Aunty Jazrah Bata faɗa". Cikin jin daɗi tace. "Toh dan Allah kada ki cewa su Mamey nayi kuka hankalinsu zai tashi." Cikin gamsuwa da hakan tace. "Toh". Gyara zamanta tayi tare da cewa. "Wai yaushe kika dawo?". Cikin lumshe ido tace. "Yah Junaidu ne ya ɗaukoni wai rana tayi kada in sha rana ya kodar masa sani". Dariya sukayi baki ɗayansu. Kana sukaci gaba da hira. Haka dai aka fara shirin auren Jabeer da Jazrah, Junainah da Junaidu aure haiƙan ƙadaran. Alhamdulillah anyi aure lfy an watse lfy, amare sun tare. Kowa ya kama gidansa. Bayan shekaru goma sha ɗaya. Abubuwan da yawa sun faru cikin shekarun. Yusuf ɗan Affan ya auri Afreen sai dai basa ƙasar suna India. Jabeer ƙarami kuwa yana karatu a jami'ar Madina Bappa yana nashi karatun a India. Habibullah kuwa yana karatu a nan cikin jami'ar Ɓadamaya. Jazrah ma ta haifi yara uku Aliyu takwaran Dr Aliyu, sai Ruƙaya da Aminatu takwarar Gimbiya Aminatu wacce itama ta rasu. Shatu kuwa ta ƙara biyu Khadijah takwarar Umaymah sai autanta Sultan. Rayuwa fa ta miƙa komai yana tafiya. Hajia Mama ta rasu babinta ya ƙare a masarautar Joɗa. Yau kimanin mako biyu kenan da tafiyar Shatu Cameroon. Sai yau da hantsi jirginsu ya dawo. Habib ne ya ɗaukota da Jabeer ƙarami wanda yazo hutu. Sai Bappa wanda tare suka zo da Afreen da ƴan tagwayenta. Mu'azzatu da mu'azzam dan da tagwaye tayi haihuwar farinta. Suna zaune a falon Jazrah Aminatu na goye da Mu'azzam wanda takwaran Yah Sheykh ne. Tanata juyi tana cewa. "Sorry Mu'azzam Adda Afreen kizo ki bashi nono mana". Tura baki tayi tare da naɗewa bisa kujera, taci gaba da bawa Jazrah labarin littafin *Ba Kason ɗauka bane* na Aysha Aliyu Garkuwa. Da sauri Jazrah da yanzu take jin hausa ras tace. "Afreen kamar muryar Mamanku nakeji fa". Da sauri suka miƙa baki ɗayansu suka nufi. Side ɗin Shatu. Da gudu Afreen ta iso ta bayanta ta ruggume ta tare da cewa. "Oyoyo Mommy". Cikin sarkuri ta juyo don bayan ta tafi Cameroon Suka zo. Cikin jin daɗi tace. "Oyoyo Adda Afreen". Jabeer ƙarami ne ya ɗan harareta tare da cewa. "Toh ki barta ta shiga ciki mana, kin tsare mana ita a woje." Ya ƙare mgnar yana amsar. Mu'azzatu dake hannun Jazrah tare da cewa. "Aunty yunwa nakeji fa". Murmushi tayi tare da cewa. "Toh Yah J Jabeer ɗan Jabeer". Murmushi sukayi duka kana kab suka wuce falon Shatu. Bayan sun gaggaisa ne, sunci sun sha, Shatu ta wuce ɗakinta. Tayi wonka tare da al'wala tana fitowa tayi salla kana ta kimtsa cikin wani tattausan yadi Royal blue mai ɗan karen kyau riga da zani. Ta cancaɗa daurinta ras. Ta fesa turare, da shafe humra mai sanyin ƙamshi, Da sauri ta jawo wayarta jin text ya shigo mata a waya. Murmushi tayi ganin Habibi Da'iman. Sheykh kenan. Buɗe saƙon tayi. "Alhamdulillah barka da isa lfy Gimbiya Aysha, hasken Masarautar Joɗa, kina shigowa ƙamshinki har fada yazo ya gaidani. Yanzu zamuyi salla, Please dan Allah ki gama da yaranki da jikokinki kafin in dawo in sameki a ɗakina, kinji ko Aish na". Cikin jin daɗi ta maida mishi amsa "Uhummmm toh Yah Sheykh me zaka bani?". Murmushi yayi tare da rubuta mata. "Kayan daɗin ki". Murmushi tayi tana mai lumshe ido. Ai kuwa ana idar da salla ya nufo gida. Kai tsaye ta ƙofar falon Shatu ya shiga. Su Jabeer, Bappa, Habib, Aliyu, Sultan autanshi na biye dashi a baya. A falon suka samu Afreen, da yaranta da Amina da Khausar Ruƙayya da Khadija suna cin abinci. Suna ganinshi suka gaisa. Kan Mu'azzatu dake hannun Jazrah da yanzu ta fito ɗakin Shatu dan mata sannu da hanya da kyau. Shafa kanta yayi tare da cewa. "Jika wahal da kaka ko?". Murmushi Jazrah tayi tare da cewa. "Gata ƴar lukuta". Cikin jin daɗi yace. "Haka Mamanta take tana ƙarama. Kamar yau ina tunowa haka Abbanmu ke kiranta ƴar luku". Murmushi Afreen tayi cike da jin daɗi. Jabeer kuwa baki ya taɓe tare da cewa. "Abeey nifa". Cikin son ɗan nashi Yarima Jabeer kenan motsusu yayi tare da cewa. "Kai ai na musamman ne". Duk suma sauran sai suka zuba mishi ido. Ɗaya bayan ɗaya ya yabasu. To Sheykh kuwa da tsuntsaye ma sai ya yabawa ko wacce taji bata kishin ƴar uwarta ko ganin tafi ƴar uwarta bare yaranshi. A haka dai ya wuce ya tafi Side ɗinsa. Ita kuwa Jazrah ta wuce Part ɗinta dan tasan. Shatu ce dashi yanzu. Ita kuwa Shatu a hankali ta fito tana mai baza ƙamshi. Ganin kab yaranta suna sabgogin gabansu ne yasa ta shafa kan Mu'azzam dake zaune kusa da ƙofar ta wuce Side ɗin Yah Sheykh da ɗan sauri jin yana ɗan kiran Jabeer tare da cewa. "Kira min Mommynku. Da sauri ta ƙarasa cikin falon nashi tare da cewa. "Assalamu alaikum Yah Sheykh gani da kusa". Da sauri yace. "Wa alaikassalam *(Y!.M!.D!.G!.)* na! Nooryat Noor ƙalbi My love my happiness". Cikin jin daɗi tace. "Yah Sheykh kenan kamar wasu yara". Da sauri yasa hannunshin ya kamo nata ya jawota jikinshi tare da ruggumeta ajiyan zuciya ya sauƙe tare da sa kanshi tsakanin wuyanta da kafaɗarta yana sunsunan wuyanta yace. "Aish waya ce miki soyayya tana tsufa? Ai sai dai masu ita su tsufa. Mu kuma bamu tsufan ba tukun". Ya ƙarashe mgnar tare da wucewa bedroom ɗinsa da ita. A hankali ya meda ƙofar ya rufe kirib. Tare da sauƙe nufamshi kana ya sunkuyo ya ɗagata ciɗak yayi kan gado da ita. Cikin lumshe ido ta ƙanƙameshi gam a cikinshi. Haka yasa suka kwanta a tare. Da sauri yasa hannunshin ya ture rawaanin kanshi tare da cewa. "Hegen nauyi da takura". Murmushi tayi tana mai kunce igiyoyin dake sarƙafe gaban al'kyabbar jikinshi. Tare da cewa. Ash Yah Sheykh nauyi". Mirgina wa yayi gefe ya kwanta kana ya jawota jikinshi ya zama sunan fuskantar juna. A hankali ya kai lips ɗinshi kan mata wani ɗan sasayyan kiss ya manna mata kana a hankali yace. "I missing You so much my love". Sai kuma taga ya ɗan juya da sauri ya kalli windows ɗinsa. Fahimtar yana dubawa ko a buɗene yasata cewa. "Yauwa Hamma Jabeer niko inda da wata tambaya data daɗe min a rai." Da sauri yace. "Wacce tambayace haka faɗeta miji". Ya ƙare mgnar yana tura hannunshi cikin rigarta. Hannunta tasa ta ɗan shafa sajenshi tare da cewa. "Akwai lokuta da dama ina wani dalili yasa munje HOTEL duk ɗakin da ka kama in mun shiga sai ka bibbincika ka dudduba lungu da saƙo, wani lokacin ma kace in fita mu sauya ɗaki. Koma sauya HOTEL ɗin baki ɗaya, meyasa? Me kake dubawa?." Ronƙofawa yayi kanta yana zare zip ɗin rigarta yace. "Ok ban taɓa yi miki bayani bako?." Da sauri ta gyaɗa kai. Cikin nitsuwa yace. "Wato shi HOTEL wani wurine mai cike da ƙalubale ga duk wani mutumin kirki, Especially in a cikin ƙasar ka ta haihuwa kake, domin da yawa har yanzu mutane basu fahimci cewa larura zata iya kaika hotel, ba lallai dole sai ɗan iskaba kamar yadda wasu ke zato. Sai dai abin lura a nan abinda ya kamata ga duk ko wani musulmi, muddin larura ta kaika HOTEL, to ka tabbatar ka binciki duk ɗakin daka kama ciki da woje kama Daga jikin ƙofa, wurin kunna fanka, wurin ajiye Rimot ɗin AC, Jikin AC, tsakiyar jikin fanka, saman silin, jikin ƙarfen labule, jikin TV Especially in suna fuskantar gado, da kuma jikin kan gado kofar Bathroom dama cikin Bathroom ɗin". Da sauri Shatu tace. "Me yasa? Sabida me mutun zai tsaya wannan dube-duben duka!?". Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Sabida mafi akasarin HOTEL'S wasu ƴan iskan kajeme kawai dan su dasa na'urar Camera a jikin duk waɗannan wuraren da na faɗa miki. Ya ɗauka musu duk mu'amalar mata da miji ko ɗan iska da ƴar isa, daga nan sai su sarrafashi ya zama blue Film, da yawa waɗanda suke ciki basa sanin ana ɗaukar su. Na'urar Camera da suke amfani da ita ƴar ƙanƙanuwace kamar botur ɗin rigar maza, in sun liƙata sai ta ɗauki komai. Su kansu masu hotel basa sani. Wasu lokutan kuma su ɗin ne da kansu ke dasata. In baki mantaba akwai ranar da na samu camara ɗin ma liƙe a cikin abin AC. Har muka canza ɗaki masu hotel ɗin sukayi ta bani haƙuri suda kansu suka binciki ɗakin da muka sake shiga kin tuna." Cikin jan dogon numfashi tace. "Eh tabbas na tuna Hamma, eh to lallai kuwa in hakane dole musulmai muyi taka tsantsan". Kai ya jinjina tare da cewa. "Shiyasa shi musulunci yana da daɗi kinga koda mutun baya bincika in yana amfanin da hadisin nan da manzon Allah ya hanemu da yin jima'i tsirara har sai an rufu. Kinga mutun zai tsira. To amman dai mafi sauƙi ka bincika kawai. Dan in kayi garaje wata ran za'a yaɗaka a bazaka a duniya kana jima'i da iyalinka ace BF ka fara yi. Kaga anci zarafin ka anci zarafin addinin ka". Ya ƙare mgnar da fara yin ƙasa da rigarta. Ita kuwa Shatu kai ta jinjina tare da cewa. "Masha Allah da kamilin miji mai cikekkiyar kamala da Nagarta. Sai kuma wata tambayar". Da sauri ya kwaɓe fuskarsa tare da cewa. "Bazaki bari sai na nitsuwa ba dan in baki amsa mai kyau". Cikin narke mishi a jiki tace. "Afwan kada in mance ne ai, kuma tambayar ba tsawo". Hannunshi yasa yana jan zariyar wondonsa tare da cewa. "Toh ina jinki". Cikin maida nitsuwarta gareshi tace. "Menene ma'anar *(Y.M.D.G?)*". Wani irin kekkyawan murmushi yayi mai cike da shauƙi yace. "Sirri nane kalmar". Cikin fara murzashi tace. "Dan Allah ka gaya min". Wani sassayan numfashi yaja jin salon da ta fara yi mishi. Murya a narke yace. "Sai in kinyi al'ƙawarin bazaki gayawa kowa ba". Da sauri tace. "Nayi". Murmushi yayi tare da zare rigarta ya ture gefa. Cikin raɗa yace. "Zan gaya miki harufa ukun na huɗun na ƙarshe ki ƙarasa da kanki". Cikin zaƙuwa tace. "Toh ina jinka menene ma'anar Y.M.D.G. Please bani amsa da sauri na zaƙu?". "Matso da bakinshi yayi kusa da kunnenta a hankali murya can ƙasan maƙoshi yace. "Y. Yana nufin *Yarinya* M yana nufin *Mai* D yana nufin *Daɗin* G ɗin kuma ki gane kinga ukun dai suna nufin (Ƴarinya mai Daɗin...".) Narkewa jikinshi tayi tare da cewa. "Please na tuba gaya min". Murmushi yayi tare da kai bakinshi bisa kunnenta a hankali cikin raɗa yace. "Ƴarinya mai daɗin G..." Da sauri ta rumtse idanunta sabida wani irin masifeffen kunyan kalmar da ya rufeta. Haka nan taji kanta na huruwa yana sama tana jinta a saman gajimare ashe waɗannan harufan abinda kenan suke nufi, iya wannan sunan da yake kiranta ya isheta gane matsayin yadda Yah Sheykh ɗinta ke gamsuwa da ita ɗari bisa ɗari. Shi kuwa ya Sheykh cikin tsananin so, bege, shauƙi, kauna, yace. "Allah sarki *ƳAR FULANI* mai kunya Alhamdulillah da Na samu sa'ar samunki dan da na rasaki to tabbas da *NAYI NADAMA (MI WASMITI)* kinga ko lallai na yarda shi *NAMIJI BAYA KAƊAN* dan da shawarar Affan na fara gano magautan mu. Gashi a hankali muka samu Kekkyawan shaƙuwa da *TAUSAYAWA JUNA* sai daga baya na gano ashema ke *BANDIRAWO* ce a gareni tunda uwa ɗaya ce ta bamu tarbiya. Gashi cikin ikon Allah *RUBUTACCEN AL'AMARI* ya ƙaddara saduwarmu da aurenmu cikin *HUKUNCIN ALLAH* harda yara. GASHI MUN ZAMO tamkar hanta da jini. Tsorona ɗaya a duniya kada *RIGAR KOWA* ta fara ɗaukanki ta barni." Wani sassayan numfashi ta fesar a hankali tana maijin tattausan kalamansa gareta. Shi kuwa Sheykh cikin gsky da gsky yaci gaba da cewa. "Gwara ta ɗaukeni ta barki. Domin duk da nasan cewa *NAKASA BA KASAWA BACE* tofa in ta ɗauke min ke ta barni zan rabu da rayuwar farin ciki domin Shatu kece *GARKUWA* a gareni sabida sam Rashin ki *BA KASON ƊAUKA BANE* Agareni. Ya karashe mgnar tare da yujowa yayi mata rumfa da ƙirjinsa tare da jawo tattausan blanket ya rufesu yana mai cewa. "Mu ɓuya Shatu na kada wannan ƴar darun Hammanta AYSHA ALIYU GARKUWA, ta hangomu ta samu abin rubutawa makarantanta. iyayen son ganin ƙoƙob sai kuma ya fara tasbihai tamkar yadda ya saba. Subahanallahi Alhamdulillah wa la'ilahaillahu, Allahu Akbar Astagafirullaha..............................! Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Allah na gode maka da ka bani aron rai da lfy da nitsuwa da kwanciyar hankali ka bani iko da dama na kare wannan littafina mai suna GARKUWA lfy kamar yadda na farashi lfy dani da makaranta shi baki ɗayansu. Yah ka jiƙaina ka gafarta min al'farma Annabi da al'ƙur'ani a duk abinda nai kuskure, ka tsare min al'ƙalamina a karo na gaba. Abinda nayi dai-dai ya Allah ka taramu bisa ladan nida masoyan Manzon Allah waɗanda in an haɗa su da Allah da manzo kan kada suyi abu bazasuyi shiba. Afwan! Afwan!! Afwan!!! Masoya na makarantana, na nesa dana kusa waɗanda na sani da waɗanda ban saniba waɗanda suka biya da masu karanta na sata, wanda na taɓa mgn dasu da waɗanda ban taɓa mgn da suba. Dan Allah ku gafarceni in akwai wani abu da nayi miki/ka bisa rashin sani da ajizanci na ɗan adam ko kuma gajiya da yawan jama'a da rashin hutu yasa kinyi mgn ban kulaba kuyi haƙuri ku yafe min abubuwan ne suna min yawa. Ina mai fatan Allah ya ƙaddara saduwarmu a wani littafina lfy al'farmar Annabi da al'ƙur'ani. Godiya ta musamman gareku wadanda suka biya kuɗin littafin suka karanta da kuɗinsu ba na sataba yan na sata ba sai na ƙarasa ba yaseen doguwa bullulutu baƙar mutuwa🤣🤣🤣. *Alhamdulillah na godewa Allah da ya bani ikon cika alƙawarin da nayi ko ince yarjejeniya da nayi daku ƴan special Group, na posting PAGE bibbiyun kullum Alhamdulillah ina al'fahari yadda ko rana ɗaya rak rana ɗaya kacal dai cikin rakun littafin ban taɓa tsallakewa ko ƙetarewa banyi muku posting ba Alhamdulillah nayi al'ƙawari kuma na, cika wannan ma yana ɗaya daga cikin manyan nasarorin da na samu a littafin GARKUWA. Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah zanyi bacci hankali konce in tashi sanda nakeso* Littafin GARKUWA na kuɗine idan kinaso ki karanta wa, bada haƙƙin na a kankiba, ki sai katin Mtn na ɗari uku kacal, ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp number na 09097853276. Sai in saki a group kota ac no 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWAR FULANI* An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels