An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 01 [ 12/1/2022 1:10 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                      *FREE PAGE 001* Ina the name of Allah the most beneficient, the most glorious and the most merciful. Dubun salati ga fiyayyen halitta Manzon tsira Annabin mu Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam. Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah maɗaukakin sarki mai kowa me komai da ya Wada ta ni da rai da lafiyar da na sake dawowa gare ku cikin wani salon rubutu na daban, Allah yadda ka bani ikon fara rubutun nan lafiya kasa in gama lafiya, Allah ka bani ikon rubuta abinda ze amfane ni ya amfani al'umma gaba ɗaya, ya Rabb ka hane ni rubuta abinda ze cutar dani ya cutar da ƴan uwa musulmai. At long last nake cewa hellooooooo to You my fans💃💃💃💃💃. Gani dai na sake dawowa, Ouummey ce dai taku tafe cikin wani sabuwar tafiyar da nake fatan ku so kuma ku ƙauna ce shi fiyeda littattafai na na baya, soyayyar da kuka nuna min a littafin *SARAKI da ABOTA CE KO SOYAYYA* is really amazing and unpredictable, am using this opportunity to say thank you once again, Ouummey loves you so dearly 💖. Sedai fa ba kamar baya ba this novel isn't FREE kamar na baya, it's a *PAID BOOK at ₦300 ONLY!!!.* Na sani you guys won't make me feel unloved or ashamed, nasan zaku nuna min ƙaunar da kuke min ta hanyar siyan littafina dan rubutu na ba abin yar wa bane, isn't so??!. Kar dai na cika ku da surutu, ga duk me buƙata zai/zata biya kuɗin ta ta wannan account ɗin, RABIATU ABDULLAHI 2391368231 ZENITH BANK tare da turo shaidar biya ta 09013101854 Ko a turo katin MTN ta wannan number 09013101854. Son so fisabilillah 💋💋. WANNAN LITTAFIN SADAUKAR WA NE GARE KU MY FAMILY, HEART U ALL AND ALLAH YA QARA MANA ZUMUNCI DA QAUNAR JUNA, AMEEN💞💝💖💗. ________________________📖 Gudu take cikin fitar hayyaci cikin dokar dajin dake da shegen duhu duk kuwa da cewa ba wai dare ne ba dan lokacin bai wuce ƙarfe huɗu da rabi zuwa biyar ba, takun mutanen da take jiyo wa a bayan ta yasa ta tabbatar basu daina bin ta ba haka suna daf da ita, wani irin kuka ne ya kubce mata ta shiga yin shi tana sakin numfarfashi, bata san me yasa azzalumai suka yi yawa ba a duniya, bata san me ita ko ƴaƴan ta suka tare wa maƙiyan ta ba da suke san se sun shafe labarin su ta kowace hanya, a rayuwar ta bata da abokin gaba tun daga yarinta har zuwa girman ta, kai har zuwa yanzu da take wannan gudun na ceton ranta da na ƴaƴan ta bata san dalilin neman kashe su ba. Kukan da yarinyar bayan ta fara ne yasa na gane jaririya ce sedai ba wai ɗanyar haihuwa ba dan zata kai watanni, bata rufe bakin ta ba wani kukan ya shiga tashi, se a lokacin na lura goyon gaba da baya ne matar tayi kuma da alama ƴan biyu ne dan itama ta gaban macece, wannan kukan shi ya kuma ruɗar da uwar ta saki nata kukan me sauti tana cigaba da gudun da take yi. "Yauwa gata can, ku ƙara gudu mu cin mata tun kafin ta kai ga ficewa dajin nan dan na gaban sa ya fishi duhu ba lallai mu iya ganin ta ba". Cikin azama ta ƙara gudun ta dan jin abinda wani da take zaton shine babban su yace, burin ta a lokacin be wuce ta fita daga nan ta faɗa dajin gaban ba dan tsira da numfashin su sedai bata kai ga hakan ba taji saukar katako ta bayan ƙeyar ta, su ne suka jefo mata ko kuwa daga ina yake ba ta sani ba. Faɗuwa tayi sedai da sauri tasa hannu ta dafe ƙasa dan gudun kar ƴar ta taji ciwo, jin takun su daf da ita yasa ta hanzar ta miƙewa duk kuwa da yadda taji jini na bin wuyan ta ban da kuma jirin da take gani, neman wajen fakewa take yi sedai kamar babu wani loko a dajin, a lokacin ba ta rayuwar ta take yi ba ta rayuwar ƴaƴan ta ne, ta sani ba lallai su tsira daga hannun wadan nan azzaluman ba sedai tana fata ƴaƴan ta su tsira ko da kuwa ita zata hallaka, yara ne da basu san komai ba basu kuma fara komai a rayuwar su ba dan yanzu ne suke watanni na uku da haihuwa, ba zata so rayuwar su ta tsaya iya nan ba haka kuma ba zata so maƙiya suyi galaba akan ta ba, ta sani saboda yaran ake neman kashe ta saboda kada uban su ya sami wani haske ko ƙanƙani a rayuwar sa. Bata san me yasa marasa imani suka cika faɗin duniya ba sedai tana tausayin mijin ta kuma uban ƴaƴan ta, yaran ne dukkan wani farin ciki, jin daɗi da walwalar sa shiyasa mahassada ke neman ganin sun raba shi dasu har itama ta samu nata rabon ƙaddarar, rayuwar su cike take da baƙin duhun da bata taɓa tunani ba se a yau da take wani siraɗi na mutuwa ko rayuwa, se a yanzu ne abubuwa da dama suka dinga dawowa kanta da yaci ace ta ankare da su tuntuni sedai tsabar pious heart ɗin ta yasa bata taɓa zargi ko kawo wani mummunan lissafi ba, se a yanzu ta tabbatar da tabbas tayi kuskure, kuskure kuma mafi girma na ɗaukar cewa kowane ɗan Adam kyakkyawar zuciya gare shi. Wani ɗan haske da take hangowa yasa ta nufi wajen cikin matsanancin gudu cikin fatan Allah ya kawo mata matserata ko da ta rayuwar ƴaƴan ta ne kaɗai, ta yarda ita ta mutu in har zasu rayu, tana fatan suyi kyakkyawar rayuwa ba dan saboda komai ba se dan kwaɗayin samun addu'ar su, Manzon Allah yace addu'ar ƴaƴa salihai ga iyayen su karɓaɓɓiya ce haka kuma sune kawai arziƙin da mutum ze mutu ya bari a duniya ya tadda shi a ƙiyama bayan sadaƙatul jariya wanda tasan bata da rabo a wannan ɓangaren dan ko tunanin hakan bata taɓa yi ba. ********** Kamar ko wane hutun makaranta in an yi, yau ma tafe take da ƙafa kamar yadda ya zame mata jiki ba kamar ragowar ƴaƴa masu gata ba da za'a je ɗaukar su a mota, mashin ko keken amalanke ko kuwa motar ƙurƙura, ita da ƙafa take takawa har zuwa ƙauyen su wanda tsakanin shi da makarantar tafiyar awa huɗu da mintuna ne a ƙafa, bata taɓa jin ba zata iya ba dan tana matuƙar son karatun kuma ta san in ma ba tayi ba kanta kaɗai ta cuta dan shine kaɗai gatan da take tunanin zata iya samu da ze zama sanadin canjuwar rayuwar ta da ma duniyar ta gaba ki ɗaya. A hankali ta shiga takawa lokacin dan ta gaji, tsakanin ta da ƙauyen su be wuce tafiyar mintuna Talatin ba dan ta kawo kusa sosai sedai a yadda ta gaji se take ganin in tayi yanke ta cikin daji zata fi saurin zuwa gida maimakon ta bi ta hanya sosai, ba ɓata lokaci ta danna kai cikin dajin cikin dajin ba tare da tsoro ba dan shiga daji a jinin su yake dan sun saba, in basu shiga yin itace ba sa shiga tsinkar magunguna ko kuma kayan marmari ko kuma yawon su. Ƙarar gudun da taji yasa ta ɗan dakata tana tunanin anya lafiya, jin kamar gudun ba na mutum ɗaya ba yasa ta ɗare wata doguwar bishiya da sauri ta yadda zata samu damar ganin abinda ke faruwa, mace take hangowa da goyo har biyu wato gaba da baya tana gudu yayinda wasu mutane masu riƙe da makamai suke binta, hankalin ta taji ya tashi duk da bata san me tayi musu suke bin ta ba sedai a ƙananan shekarun ta tasan ba abu me kyau yasa suke bin ta ba tun da har ga makamai banda haka kuma mutane da yawa na shiga wannan dajin dan aiwatar da munanan ayyukan su saboda duhuwar dajin na basu kariya daga idanun jama'a, bata san me yasa ba sedai kawai taji a ranta ya zama dole ta taimaki wannan matar, ba zata bar wannan azzaluman su yi galaba a kanta ba. Da sauri ta ɗirko daga bishiyar tareda nufar wajen matar da saurin ta dan gasu da suka saba da dajin bawa wani ganin duhuwar sa, da sauri ta fizgi hannun matar daidai lokacin da wani yayi nasarar sakar mata harbi a ƙafa ganin yadda take wahalar dasu, wani kogo ne na bishiya ta shigar da matar haka kuma da sauri tasa hannu ta since goyon bayan ta ganin wuyar yarinyar na reto alamun ta suma ko ta mutu, a galabaice matar ta kwanto ta gaban ma ita kuma tayi saurin tare ta. Numfarfashi kawai matar ke yi dan ta galabaita to the extent da bata iya ko da buɗe idanun ta sosai balle tayi magana, hannun yarinyar da bata san wacece ba ta ruƙo da sauri tana fizgar numfashi kamar me asthma, da ƙyar ta buɗe baki da idanun ta tayi magana mara tsayi "A...am..maa..naa, su..su..tsira..dan.. Allah". Wani irin duka ƙirjin yarinyar ya shiga yi jin abinda matar ke faɗa, da sauri ta shiga jijjiga ta, "Ki tashi Aunty mu gudu, kar ki rufe idanun ki ni ban san inda zan kai yaran nan ba wallahi". Bata iya tace mata komai ba se yatsun ta duka goma ta ɗaga mata kafin ta shiga nata nuni da zobunan dake jiki wanda guda biyar ne, uku a hannun dama biyu a hannun hagu, da sauri ta sa hannu ta cire mata dan a tunanin ta sun dame ta ne, wuyan ta ta sake nuna mata nan ma ta cire mata sarƙar jikin ta da ɗan kunne, ajiyar numfashi matar ta saki tana buɗe ido sosai cikin ƙure ƴaƴan ta da kallo kafin wannan karan cikin cikakkiyar magana tayi magana "Ki kula min dasu dan Allah, ban bar komai ba a wannan duniyar se su, sune fitilar zuciyar mahaifin su, kije dasu na baki halak malak amma dan Allah su tashi cikin kyakkyawar tarbiyya kamar kowane cikakken bahaushe musulmi, kije dasu ki kula dasu da wannan kayan sarƙar na hannun ki dan Allah kar su cimma na su kashe mu gaba ɗaya, kar ki tsaya wata magana dan ni tawa ta ƙare ko basu kashe ni ba mutuwa zan yi dan bana jin akwai ragowar jini a jikina, fatana ƴaƴana su tsira kuma alhamdulillah Allah ya turo min ke dan cetar su, ki tafi, ki tafi gasu nan, dan Allah ki tafi". Jin takun nasu da gaske kusa daf da bishiyar yasa yarinyar damƙe set ɗin sarƙar hannun ta ta zuba cikin jakar makarantar ta ta buhu dake hannun ta tare da saɓa yarinya ɗaya a ƙafaɗar ta ta goye ɗaukar tare da ɗaukar jakar buhun ta shige cikin dogayen ciyayin wajen cikin rarrafe dan kar su gan ta, seda ta ɗan yi nisa sannan ta tsaya jikin wata bishiya tana kallon yadda suka cimma matar a inda ta bar ta, haske haske sauka dinga yi da wayoyin hannun su cikin neman inda ta ɓoye yaran sedai basu ga komai ba, tsawon lokaci kafin suka koma wajen da suka bar uwar da mutum ɗaya na gadin ta, "Yanzu ya zamu yi, me zamu cewa matar nan game da ɓatan yaran?". Ɗaya daga cikin su ya faɗa kafin ɗaya ya kai ƙafar sa yana shurin matar da ke jingine har lokacin yana tambayar ta inda ta kai yaran sedai tuni ta faɗi rigija alamar rai yayi halin sa, tsabar jinin dake kwance a inda ta jingina zaka yi zaton wata ƙaramar dabba aka yanka, wani mugun tsaki mutumin ya saki kafin ya umarci ragowar su ɗau gawar tata sukai mota shi kuma ya cigaba da bincika wajen sedai dake ba sanin kan dajin yayi ba ko kaɗan be ko kai wajen da yarinyar take ba rungume da baby ɗaya a ƙirjin ta idanun ta na zubar da hawayen tausayin matar da kuma ƴaƴan dake hannun ta da yanzu suka zama marayu, bata san wane irin marasa imanin mutane ne yanzu ke rayuwa a wannan duniyar ba, ko ina cike da azzalumai, kowa ba ya tausayin kowa, kowa ba ya san kowa, kowa kan sa kawai ya sani, ya ilahi duniya ina zaki damu. Ganin kuka me sauti na neman kufce mata yasa ta miƙe wa ta shiga tafiya a hankali cikin takatsantsan dan ba zata so abinda ze jawo hankalin mutanen cen ba balle har su kashe Innocent babies ɗin hannun ta, tafiya me ɗan nisa tayi kafin ta fita daga dajin ta yanka ta cikin gonaki ta shiga ƙauyen su, garin yayi luf luf babu rana se iska me daɗi kasancewar magrib ta doso kai dan yanayin na nuna alamun be fi karfe biyar da rabi zuwa shida na yamma ba. Ba tare da  tunanin komai ba ta nufi gidan su da yake babban gida kuma ginin ƙasa ba, sallama ta shiga kwaɗa wa a ƙofar babban zauren su sedai ba wanda ya amsa mata kamar ko da yaushe, sa kai tayi ta nufi sashen da take rayuwa yayinda tsirarun mata da yaran dake babban tsakar gidan bin ta da kallo suna maganganu ƙasa ƙasa ganin ta goyon jaririya ga kuma wata a hannun ta. Wata sallamar ta kuma yi a ƙofar sashen su sedai nan ɗin ma ba'a amsa mata ba se dogon tsakin da aka ja, kai a ƙasa ta shiga ƙofar tana tafiya a hankali kamar wata ɓarauniya ko wadda ƙwai ya fashewa a ciki, inna mariya dake tsugunne bakin malalallabta tana rege shinkafa ta tsugunna har ƙasa tana gaisar wa sedai maimakon amsa se zagi da yarfe ne ya biyo baya kamar yadda ta saba "An dawo daga yawon ta zubar ɗin da sunan Makarantar boko, atoh mun dai sani ba wata wata boko se tambaɗewa da karuwa ci da ake yi ake fake wa da boko, wa ya sani ma ko an yi guzurin ɗan boko a ciki". Bata wani damu da abinda Inna mariyar ta faɗa ba dan ba yau ta saba ba, ba ita ba kusan duk ƴan gidan ma haka suke cewa, bata damuwa ne dan tasan ita karatu take yi ba yawon kafuwan ci ba kamar yadda suke faɗa, gaban ta ne yayi kwanci kwanci ya faɗi lokacin da yarinyar da ta Saɓa a kafaɗa ta calla wani irin kuka me sauti cikin Muryar ta ta jarirai, ashe ta daɗe da farkawa tun lokacin da sanyin la'asar ya buge ta amma bata dawo hayyacin ta ba se yanzu. Zabura Inna mariya tayi tana dafe ƙirji cikin zare ido "Me nake ji haka kamar kukan jarirai?". Ta faɗa tana juyowa ga yarinyar da tayi saƙare cikin tashin hankali, bata yi tunanin me ze je kazo ba lokacin da ta karɓi yaran, bata yi tunanin abinda ze iya faruwa ba dan a lokacin ba abinda ke ranta face ganin ta tseratar da rayuwar su, sam a lokacin ta manta da wane kalan mutane take rayuwa se yanzu da yarinyar ta shiga kuka kamar yadda aka san jarirai ƴan watannin ta da haihuwa. "Innalillahi, a'uzubillahi ni mariya jikar me shanu, me nake gani a hannun ki haka SALAME kamar jaririya?". Yarinyar da aka kira da salame bata iya tace komai ba yarinyar bayan ta itama ta shiga kuka alamun itama ta farfaɗo, gaba ɗaya se hankalin ta ya rabu kashi kashi, ga kukan yaran ga kuma kururuwar da Inna mariya ke yi mata, bata san me yasa taji zuciyar ta na zafi ba jin kukan yaran dan har tsakiyar ranta da kanta take jin kukan dan haka d sauri ta zauna tana ɗora ta hannun ta kan laps ɗin ta ta shiga kiciniyar kunto ta bayan ta, jijjga babyn ta shiga yi tana tapping ta kan cinyar ta dan tayi shiru shiyasa sam bata lura da mutanen da suka taru saman kan ta ba se da Muryar kawu Habibu ta ratsa kunnen ta lokacin da ya daka mata razananniyar tsawar da ta sa har ta kusa yar da ƴar hannun ta kafin tayi saurin tare ta....................✍🏻 Ya Rabb ka tsare mu daga sharrin zuciyoyin mu ka hana mu hassada, baƙin ciki da ƙyashi ga nasara da ɗaukakar wani, Ameen. ©️ Ouummey 📚✍️. ☑️Ote, Comment, share and patronize fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 02 [ 10/11/2022 12:16 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                       FREE PAGE 002 ________________________📖 "Dama na daɗe da sanin lalacewar ki kawai kika saka gaba shiyasa kika dage ke se kin yi wani karatun boko saboda ki samu mafaka dan kin san a nan bazan lamunci wannan iskancin ba shi kuma megari har da wani ɗaure miki katara, zaki faɗa min wanda yayi miki cikin da kika haifi waɗannan shegun ƴaƴan ko se naci uban ki, shegiya ƴar iska kawai". Kakkarwa jikin ta ya shiga yi haka ma bakin ta rawa yake tsabar tashin hankali, da ƙyar ta iya buɗe bakin ta tana sharar hawaye "Kwarankwatsa ni ba ƴar iska bace kawu, wallahi bani na haifi ƴaƴan nan ba ni ban taɓa iskanci ba ku yarda dani". Wani tokari kawu Adamu ya sake mata a bakin da take magana take kuwa bakin ya fashe ya shiga fitar da jini, dafe bakin tayi da sauri hawayen ta na ƙaruwa saboda azaba "In ba ke kika haife su ba to tsinto su kika yi?, Kaji min sheɗaniyar yarinya, wato har kin san ki buɗe wa wani gardi cinyoyi ko, Abu bani icen can me wuta, yau in baki faɗi gaskiya ba ba abinda ze hana ni kwaye fatar bayan ki da wuta". Kukan ta ne ya ƙaru ta shiga rantsuwa da magiyar su yadda ita ba ƴar iska bace sedai ina no one is willing to listen to her, ɗebe yaran Inna mariya tayi ta dangwarar da su a dandaryar jar ƙasar wajen shi kuwa kawu habibu ya shiga dukan ta da wannan icen,ihu ta shiga yin tun ƙarfin ta har Muryar ta ta dishe amma ba wanda yaji ko ɗigon imani ko tausayin ta balle ya bawa kawun haƙuri. Seda ya dake ta iya yadda yaso kafin ya jefar da icen dake fitar da hayaƙi alamun akwai wuta a jikin sa har lokacin ya dubi kawu Adamu "Kaje yanzun nan ka sanar da maigari kafin su iro su dawo mu tafi mu kai shegun yaran can, mukam Kamisu ya mutu ya bar mana annoba wallahi, haka kawai muna zaman zaman mu ya haifo shegiyar ɗiyar sa ya mutu ya bar ta gashi nan ta jawo mana abin kunya da Allah wadai zata lalata wa ƴaƴan mu suna". Da kallo kawu Adamu yabi bayan kawu habibu da ya fice yana ƙananun magana saboda masifar da ke cin sa a rai kafin ya maida hankali inda Salame ke tsugunne a takure kayan jikin ta duk sun yayyage saboda dukan da tasha, tsaki yaja ya sa ƙafa ya fice yana shura siɗaɗɗun takalman sa da suka ci duniya dan ƙullin leda a jikin su ya fi biyar. Feƙeƙƙen zanin ta Inna Abu ta tattare tana kaiwa zaune kan jar ƙasar da ta kwanta saboda ruwan da aka yayyafa mata "Ni yanzu damuwa ta saurayin A'ilo kar yace ya fasa auren ta saboda kayan kunyar da wannan annobar ta jawo mana". Ta ƙarashe tana jefa wa Salame dutsen da yayi nasarar sauka a kan ta take kuma kanta ya fashe sedai ba'a iya banbance yadda yake zubar da jini dan ciwukan jikin ta ma duk jinin suke fitar wa so se ya haɗe. "Sauƙin abin ma shima ƙanwar sa wasila ta taɓa yin cikin nan kin ga ba zasu ɗaga mana kai ba". Cikin rashin jin daɗin maganar ta Inna Abu ta haɗe rai dan duk abinda ze sa a Faɗi aibu ko a soki saurayin A'ilo bata so dan ba ƙaramin morar shi suke yi ba, wannan maganar da Inna mariya ta fara yasa ta miƙe tana ficewa da ƙafar ta da duk take cike da faso manya manyan saboda rashin sa takalmi. Hararar ƙofar da ta fita Inna mariya tayi dan ba ƙaramin haushin Inna Abun take ji ba saboda yadda take musu ɗaukar kai kan saurayin A'ilo dan gaskiya duk gidan ba wanda ya taɓa saurayi me maiƙo kamar ta dan ɗan gidan maigari ne, kukan da yaran suka kuma sanya wa a tare yasa taji takaicin ta ya ƙaru. Ji take kamar taje ta shaƙe su har se sun mutu sedai rashin imanin ta be kai haka ba so se ta dubi Salame da bata ko numfashin arziƙi saboda wahala ga kuma azabar da ciwukan jikin ta ke mata "Kin tashi kin kwashe wannan tsiyar dake neman hanani nutsuwa ko se na kwashe su na watsa a rijiya?". Duk yadda jikin ta ya kai ga nauyi saboda dukan da tasha ban da azabar da take ji amma haka ta miƙe ta shiga takawa cikin ƙarfin hali har ta kai inda suke kwance se ciccilla hannaye da ƙafafu suke yi, a kafaɗa ta ɗora ɗaya tana runtse ido saboda zafin da taji dan akwai ƙuna a wajen ɗayar kuma ta rungume ta wuce akurkin ɗakin ta da ke daf da zubewa saboda yadda ya takwarkwashe, duk da gidan dukan sa na ƙasa ne amma babu ɗaki mafi muni kamar nata dan madafar su ma tafi shi nesa ba kusa ba. Kan yagalgalallen buhun da take kwanciya ta shimfiɗar da yaran kafin ta kuma fice wa ɗauko jakar buhun ta, cikin ɗan hanzari ta ƙara sa ta ɗauke jakar ganin Inna mariya bata wajen da alamu ta shiga bayan gida ne. Cikin cije baki ta kai zaune gefen yaran ta shiga bin su da kallo tana yaba kyan su a ranta kafin kuma ta ji wani sabon so da tausayin su na ratsa ta tuno yadda aka kashe mahaifiyar su, 'duk abinda ze faru bazan yarda in rabu da ku ba, mutuwa kawai zata  raba tsakanin mu insha Allah". Ta faɗa a ranta tana jingina da bangon ɗakin sedai da sauri ta janye jin raɗaɗin da ya ratsa kwanyar ta hakan na shaida mata akwai ciwo a nan ɗin ma. Ƙofar ɗakin taje ta saya kafin ta tuɓe kayan makarantar jikin ta da suka yagalgale saboda ƙunan wuta da kuma dukan ice, wani koɗaɗɗen zani ta ɗauko wanda dama uku ne kawai da ita kuma da su take rayuwar yau da gobe ta ɗaura, wanka take son yi sedai ta san yau ko mutuwa zata yi ba zata samu ruwan zafi ba se kawai ta ƙudure yi da na sanyin ta fita zuwa ƙatuwar rijiyar su dake tsakiyar gidan. Babbar rijiya ce dan dukkan su na iya ɗiban ruwa a lokaci ɗaya dan tana ɗaukar guga sama da biyar, ƴan mata biyu ne suke ɗiban ruwa suna hirar su, tun da ta nufo wajen suke dariya suna nuna ta, duk da bata jin me suke cewa dan da ɗan tazara tsakanin su amma tasan ba abu me kyau suke faɗa ba, hakan ba sabon abu bane a wajen ta dan duk faɗin gidan ba zata iya ɗaga mutum ɗaya tace gashi me son ta da ƙaunar ta bane, daga masu ƙi da tsanar ta se kuma ƴan ba ruwa na sune wanda ba zasu dake ta ba ba zasu zage ta ba sedai ba zasu taimaka mata ba irin su kawu Adamu kenan. Ƙaramin guga ta ɗauka ta zura cikin rijiyar ignoring all the curses da suke rending mata ta shiga ɗiban ruwan ta dan tun da da basu samu dalili ba ma ƴar iska suke ce mata balle yanzu da ta zo da ƴaƴa har biyu gida, "Iyayen karuwa dai sun yi asarar haihuwa, ke in kika bibiya ma sule me shago ne yayi mata cikin da ta haifi yaran nan dan kin ga shine kaɗai yake kulata a garin nan". "Kai anya kuwa sule ne, kin ga fa Inna tace yaran sun yi kusan watanni biyu da haihuwa shi kuwa ai rabon shi da ita tun da tayi ƙaryar jarabawa ta zauna wata goma a makaranta". "Eh ba mamaki ma a can wani malamin ya ɗirka mata cikin, kin san dama buba ya faɗa mana kafirai ne". Haka suka cigaba da maganganun su na aibata ta amma bata kula ba ta ɗibi ruwan da take buƙata ta koma sashen su, da saɗab saɗab ta zagaya wani ɗan fili dake bayan ɗakunan su ta yaye zanin ta kwara wa jikin ta ruwan, sauƙin ta ruwan rijiya akwai ɗumi ban da haka kuma yau ɗin an yi rana sosai shiyasa ya sake yin ɗumi kamar an gauraya dana zafi. Zanin ta mayar tana barin cinyayyen bokitin a nan wajen ta koma ɗaki bayan ta leƙa ta tabbatar Inna mariya bata wajen, yarinyar da ta fi yin kuka ta ɗauka ta shiga jijjigawa har ta yi baccin wahala dan yunwa suke ji sedai bata san me zata basu ba, haka tayi wa ɗayar ma ta samu itama tayi bacci. Tuno da wata hamsin a jakar ta yasa ta maza ta jawo jakar ta shiga zazzage ta, kayan sarƙar babar ƴan biyu da suke zube a ƙasa ta ɗaga ta shiga kalla tana yaba kyan su kafin ta shiga hawaye sanin me su ta daɗe da zama gawa, hawayen ta share ta shiga tattara su tana mayar wa haka dan ta san a yadda suke da kyau muddun Inna mariya tayi ido biyu dasu shikenan sun zama nata. Hamsin ɗin ta shiga juya wa a hannun ta tana tunanin ta yadda zata fita daga gidan ba abin ta haura ta katanga ba jikin ta na mata ciwo. Dan son samun sauƙin fita ta siyo musu kunu ta basu ta ƙara sa inda take ajiye gishiri dan tasan hakan kawai zata yi taji sauƙin raɗaɗin ciwon har ta iya haura katanga zuwa anjima. Gishirin ta ɗauka tare da kwance ƙullin da tayi wa ledar ta ɗebo a hannun ta tana runtse ido saboda azabar da ta dan zata ji ta kai kan guraren da ƙunar take, duk yadda zugi da raɗaɗi ke ratsa ƙwaƙwalwar ta bata dena ba har se da ta gama kafin ta kwanta tana fidda numfashi ɗaiɗai kamar me cutar asthma. Wannan horon kawu habibu ne lokacin da tana hannun matar sa Inna Abu kafin ta dawo hannun kawu iro, tun tana yarinyar indai tayi laifin da aka dake ta haka kawu habibun ze ɗebo gishiri ya dinga danna mata a wajen ciwon, karon farko da ya fara yi mata da hankalin ta suma tayi amma ko da ta farfaɗo haka ya sake yi mata. A lokacin seda ta suma so uku amma ba hakan yasa ya fasa abinda yayi niyya ba, tun daga lokacin kuma yake mata wannan azabar, tun tana damuwa tana shiga tashin hankali har tazo ta daina ba kuma wai dan bata jin zafi ba se dan ta riga ta saba danne zafi da raɗaɗin a ranta. Tsawon lokaci kafin taji kamar an yi ruwa an ɗauke duk ta daina jin azaba shigar gishirin jikin ta haka kuma tuni waccan azabar ta disashe ta zafin ciwon shiyasa se ta ke jin yanzu kamar babu ciwo a jikin ta, koɗaɗɗen zanin ta ta maida tare da zura rigar sa ta salallaɓa ta fita jin an shiga sallar magrib, ta katanga ta haura kamar yadda ta ƙudira. Gudu ta sha sosai kafin ta kai ga isa wajen Sare me kunu, hamsin ɗin ta miƙa mata tana numfarfashi tare da faɗa mata ta bata na Naira goma ƙullin biyar biyar, a farar leda aka ƙulla mata ko wanne kafin a saka a baƙar leda ta miƙa mata,da hanzari ta karɓa sannan ta wuce wajen sule me shago, bata tsaya amsa tambayoyin da yake mata ba na ance ta dawo da ɗanyen goyon shegun yaran da ta haifa har biyu ba tace ya bata siga na goma se madara ta Ashirin. Madarar kusan Naira ɗari ya zuba mata haka sugan ma ya fi na hamsin ya bata yana faɗin tabar kuɗin kawai dan ba ƙaramin so yake wa Salame ba, godiya ta masa ta juya zuwa hanyar gidan su cikin gudu sosai har ta kai, ta katanga ta koma kamar yadda ta fita dan ba wata katangar arziƙi bace kun dai san fences ɗin ƙauye. Hango Inna mariya a Zaune kan tabarmar da take zama daga bakin ƙofar ɗakin ta yasa ta rasa yadda zata yi ta wuce, ta daɗe tsaye kafin taga shigowar kawu iro sashen nasu, kayan hannun sa Inna mariya ta karɓa ta shige ɗaki tana masa sannu da zuwa shima ya mara mata baya, da wannan damar ta samu ta saci kofi ɗaya cikin kofunan sashen ta shige ɗaki da sauri. Seda ta saya ƙofar duk da ba mai shigo nata dan ko neman ta Inna ke yi sedai tai ta ƙwala mata kira, kunun ɗaya ta juye cikin kofi ta sa sigar kaɗan ta juya da wani kara kana ta ɗau yarinya ɗaya ta fara tashin ta har se da ta buɗe ido, buɗe baki tayi da nufin komai Salame ta maza ta sa mata kofin a baki, cikin yunwar da ta galabaitar da ita ta shiga sha ba wani musu, sosai tasha kunun kafin ta saki tana sa harshen ta tana lashe saman cute small lips ɗin ta, murmushi Salame tayi ganin yarinya ma ta san zaƙi dan ta tabbatar da bata sa sugar ba baza ta sha da yawa haka ba. Ajiye ta tayi inda yarinyar ta shiga cilla ƙafafu tana wasa da hannayen ta, ƴar uwar ta ta ɗauka itama ta tashe ta tare da bata kunun, itama ta sha da ɗan yawa duk da be kai yawan na ɗayar ba, ajiye ta ta ƙara ɗaya na biyar ɗin kan wanda suka rage ta ƙara sugar ta shiga sha itama dan ta san yau kam ko itace tafi kowa maita ba zata samu abinci ba a gidan nan, da ɗan dama ta rage saboda kar yaran su ji yunwa su nema kuma babu, jakar ta ta ɗora ta rufe cup ɗin dashi sannan ta juya ga yaran ta ƙure su da kallo. Kyawawan yara ne Masha Allah kamar ƴaƴan turawa, ba ramammu bane dan da ƙibar su daidai sanye da kayan masu kyau suma kansu an kakkama da soso da ya daɗa ƙara musu kyau, addu'a ta shiga yi musu tana tofa masu na Mayu da baki dan akwai Mayu sosai a ƙauyen. Seda ta gama yi musu addu'a sannan tayi wa kanta ta nemi waje kan buhun ta ta kwanta dan zannuwan ta biyu ta haɗa ta shimfiɗa wa yaran da har yau bata san sunan su ba dan maman su bata faɗa mata ba ita kuma bata san da sunan da zata kira su ba. Washegari kuwa tun kiran sallar biyu da ta tashi bata koma ba, tana idar da sallah ta fita tsakar gidan su ta hau aikace aikace kamar yadda ya zame mata wajibi muddin tana garin, tana gama wa ta ɗau bokitan su ta fita rijiya ta shiga jido ruwa, se da ta cika ko ina kafin ta hau kunna ruwan komo, tana juye kokon ta kai duban ta kan ƙofar su Inna mariya dake kulle har lokacin, da sauri da sauri ta dafa ruwan zafi ta kai ɗakin ta ta ɓoye cikin wata madaidaiciyar roba sannan ta dawo wajen ta kashe wutar. Ɗakin ta ta koma ta surka ruwan a bokitin ta ta shiga yiwa yaran wanka, wankan jariri ba sabon abu bane dan tun tana shekara bakwai aka fara bata rainon yara haka kuma tana shekara sha biyu suka fara sa ta wankan jariran su, tana gamawa Hassana kamar yadda ta raɗa wa wadda taga tafi girma a idon ta ta ɗau Ussaina ta mata ita ma sannan ta ɗau ruwan nasu ta shiga banɗakin su ta kwarawa jikin ta ta maza ta fita tare da maida bokitin ta bayan ɗaki. Ko da ta koma tuni yaran sun koma bacci da alama sun ji daɗin wankan, murmushi tayi tana jan kumatun Ussaina daidai lokacin da taji Muryar kawu habibu cikin ihun kiran sunan ta.......................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment, share and patronize fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 03 [ 10/12/2022 12:08 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.                       FREE PAGE 003 _________________________📖 A gigice ta Fito daga ɗakin har tana yin karo da durƙusasshen bangon ɗakin wanda banda tsari da kariyar Ubangiji wata iska me ƙarfi nan in aka yi ze zube ne. A firgice ta ja baya tare da maƙewa jikin garun ganin dukkan su mazan gidan ne a wajen wanda tasan ba dan kowa suka haɗun ba se dan ita. Wani irin rawa jikin ta ya ɗauka haka ma zuciyar ta ta shiga addu'ar Allah ya taimake ta kar su ƙara mata wani ciwo da nauyin jikin da sabon dukan da ta san in ba Allahn ne ya tare ba se ta sha shi. "Shegiya munafuka me suffar muminai, tana sussunkwi da kai tana baɗala a haka kuma take cutar wasu suke mata kallon saliha ta gari se gashi ƴaƴan namu dai da ake zagin sune nagarin, kin matso kusa ko se na harbo ki da ƙafa ta, tambaɗaɗɗiya kawai". Da sauri ta matsa dan ta san kaɗan kenan daga aikin baba iro ya harba tan kamar yadda yace, ƙasa ta sa gwiwoyin ta tare da kai kanta ƙasa abinda su kuma suka fi tsana kenan dan sunce hakan wani salo ne na munafurci. "Me zata zauna tayi mana a nan iro, kawai taje ta kwaso ƴaƴan shegun nata mu wuce wajen megari dan wallahi ji nake kamar in watsa a turmi in dake shegu ita kuma uwar in shaƙe ta har se ta mutu". Baba habibu ya faɗa da iya gaskiyar sa yana demonstrating da hannayen sa, ita dai tana duƙe har lokacin dan ba'a ce ta tafin ba shawara ce suke yi a tsakanin su. Uban dundu Inna mariya ta ɗuma mata ta kuma bita da zagi "Ka ga min fitsararriyar da ba zata rama ragon sunan ta ba, wato ga sa'annin matacciyar uwar ki na magana shiyasa kika zauna kina kallon mu, to bari in kwaso shegun yaran in watsa a masai muga ta tsiya". Ai kafin inna ta gama rufe bakin ta tuni ta ɗiba tayi ɗakin a guje jin za'a watsa mata su a masai, Hassana ta riƙe a hannu yayinda ta goya Ussaina dan ta fahimci Hassanar tafi haƙuri dan bata fiya kuka ba se in Ussaina nayi ta kama. A saɗaɗe ta fito dasu wannan karon kanta a daidai tana bin su da kallo har ta kai gaban su ta sake tsugunnnawa, a yanzu kam Inna A'i da kallon da take bin su dashi ya ɓata wa rai itace ta kai mata duka a fuska, ba wai mari ba dan ba kuncin ta ta nufa ba kuma ta na sane ta kuma same ta a idon ta na dama, duk yadda idon ya ɗau raɗaɗi bata ko motsa hannun ta da niyyar taɓa wa ba. Ta daɗe da sanin idanun ta na ɗaya daga cikin abubuwan dake jawo mata tsana, kyara da tsangwama a cikin gidan, wato wani irin ido Allah ya halitta mata me kamar na maciji ko mage za'a ce, dan ƙwayar idon ta ba baƙa bace haka ma ba brown ba, wata color so similar to golden, sedai golden ɗin irin me ɗan duhu kaɗan. So da yawa su kawu, matan su ko ƴaƴan su sun sha goranta mata yanayin idanun nata duk tayi laifi, kai koma bata yi ba indai zasu haɗa ido se sun tanka mata, shiyasa tun lokacin da malamin Islamic studies ɗin su yayi musu addu'o'i ciki har da na baki shikenan ta ke yi, la haula kuwa kowane dare se tayi adadin da bata sani ba dan ba carbi ne da ita ba ta shafa a fuskar ta kafin ta kwanta haka kuma da asuba in ta tashi. Bata san a wajen wa ta gado irin wannan idon ba cikin iyayen ta dan bata yi wayo da ko ɗaya ba sedai da alama ba wajen babanta da yake ƙanin baba Habibu da baba Adamu wa ga baba iro ba ne, tafi kyautata zaton wajen mahaifiyar ta ta gado ko kuwa dai Allah ne yayi mata nata halittan daban, ko a makaranta seda hakan yaso ya zame mata barazana dan har se da shugaban makarantar ta tsawatar tukunna shiyasa har tayi ta gama bata da wasu cikakkun ƙawaye sedai na gaisuwar mutunci, kowa gudu da tsoran ta yake saboda kalar idon ta da ba'a saba gani ba cikin jama'a, tun bata saba da hakan ba har ya zo ya zame mata jiki ba ta ma damuwa. Zama suka yiyyi kan tabarmin da ke shimfiɗe a fadar me gari kafin suka shiga kai gaisuwa shikuma dattijon dake amsa sunan maigari na zaune kan kujerar ƙarfe kan sa ɗaure da rawani yana amsa musu. Kafin kace me jama'a sun fara ciki dan haka ake wa duk ƴaƴan da suka yi ciki a garin amma fa marasa galihu dan da Allah yasa ƴar maigarin tayi shiru kake ji wai maye yaci shirwa, karuɗuf ƴar magulmaciya tayi ciki, ba wanda yasan da zancen seda faɗan kishiyoyi ya haɗa shima kuma har rana wata yau ba'a yi irin wannan zaman a kanta ba gashi har ta haife tuni. Seda fadar ta gama cika sannan maigari ya fara sanar da abinda ya tara su wato dai batun cikin da Salame tayi ta haife batare da sanin su ba har gashi ƴaƴa sun kusa rufa watanni uku, hayaniya ce ta shiga tashi inda mutane da yawa ke Allah wadai da ita yayinda ƙalilan da abun ya faru kan ƴaƴan su suma suka shiga yi mata fatan Allah ya shirya a ganin su ai hakan ƙaddara ce (saboda ya faru ga nasu). Se da gurin ya lafa kafin maigari ya shiga jawabin sa kamar yadda ya saba "Bisa ga tsari na wannan gari bamu yadda da abun kunya ba ko yaya yake kuwa dan haka zamu aiwatar da abinda muka saba yi duk sanda aka samu irin wannan san zuciyar, a yanzu haka zamu karɓi ƴaƴan a kai su can nesa inda ba wanda ze san nata ne balle ayi mana gori kamar yadda muka saba tun da wannan shine karon ta na farko, da na biyu ne kuwa ko sama da haka to fa kun san hukuncin kora ne a kanta". Yana gama faɗar haka wasu fadawan sa suka nufo ta da zummar amsar yaran inda ita kuma cikin matsanancin firgici da tashin hankalin jin abinda ake kiran ze faru ta sake ƙanƙame ƴaƴan ta ta shiga kurma ihun ba ta yadda ba ba zata bayar dasu ba, kowa a gurin ya shiga mamakin abinda tayi, a ganin su ƴaƴan shegen take ihu dan za'a raba ta dasu, to meye abin so cikin ɗan shege?!. Muryar Salame da fiye da rabin ƙauyen zasu ce basu taɓa ji ba se gata ana jiyo ta tun daga farkon hayin maigari saboda yadda take ihun da iya ƙarfin Muryar da Allah ya bata, duk irin tsawa da zagin da babannin ta ke mata bata ma san suna yi ba balle ta saurare su ta daina ihun har se da maigari yasa fadawan su janye daga kusa da ita kafin tayi shiru ta sake matse ƴaƴan tana sauke numfashi sedai sam hankalin ta be kwanta ba dan tasan ba wai an ƙyale ta bane. Seda megari ya gama ƙare wa jama'ar wajen kallo kafin ya muskuta yana zarar ido "Tun da har wannan yarinya taƙi yadda da hukuncin mu to mun bata zaɓi biyu kuma a yanzu a nan gurin zata bayyana mana wanne ta ɗauka, na ɗaya ko dai ta bada yaran nan ayi kamar yadda aka saba dasu ko kuwa na biyu ta tattara ta bar mana garin ma'ana mun kore ta daga ita har ƴaƴan haka kuma duk sanda muka sami labarin shigowar ta to tabbas hukunci mai tsananin tsauri ya hau kanta, wannan sune zaɓin". Shiru kowa yayi kallo ya koma kan Salame da take jin komai da aka faɗa haka kuma ba tare da second thought na halin da ita ko yaran zasu shiga ba sanadin zaɓin ta ta buɗe baki ta zaɓi abinda take ganin ya fiye mata "Ba gari ba ko ƙasa ce zan iya haƙura in bar ta akan ƴaƴana dan haka na zaɓe su akan komai da nake dashi ciki kuwa har da asalina". Kusan a tare duk su baba Habibu, baba Adamu da baba iro suka miƙe jin abinda ta faɗa, wato ta zaɓi ta bar garin saboda ƴaƴan ta haka ta zaɓe su akan Asalin ta wato su dangin ta kenan. Shi kan sa maigari ba haka yaso ba dan a tunanin sa zata zaɓi bayar da yaran ne tun da in ta bar nan wa ta kama?, Bata da kowa banda dangin baban ta, mahaifiyar ta kuwa bama ƴar nahiyar bace, a yawon tuƙin babban mota baban ta ya auro ta dan haka ba wanda yasan komai a kanta kamar yadda basu faɗa wa kowa komai game da ita ba har kuwa ranar da ta bar duniya sanadin hauka da aka sa mata da ya kai sedai a ɗaure ta a ɗaki. Umarni me gari ya bayar kan dogarawa su bita gida ta ɗebi abinda zata ɗauka a rakata bakin gari ta tafi sedai fir baba iro yace ba abinda ta aje a sassan sa bare ta koma ɗauka dan haka su rakata bakin garin kawai, bata Musa ba ta shiga gaba dogaran na binta a baya dan tun da ta shafa taji jakar makarantar ta na jikin ta hankalin ta ya kwanta. Seda suka tabbatar tayi nisa da gari kafin suka juya zuwa gidan maigari suka sanar dashi an cika umarnin sa inda ya amsa da cuskunenniyar fuska dan ba haka yaso ba. Abinda mutanen garin basu sani ba shine maigari siyar da jarirai yake wa ƴan birni da suka rasa haihuwa da kuma masu aikin asiri though be san me suke dasu ba, shidai kawai a bashi kuɗi shikenan, da an samu yarinyar da tayi ciki se ya hana a zubar yace ta haife shi kuma ya sami ƙarin jari. Lokutan da kuma ba'a samun na banza hatta na sunna kaiwa yake dan akwai ungozomar da suka haɗa kai in ba na shege se a kai na sunna, yadda suke yi kuwa se an gama haihuwa lafiya lafiya se ta shafawa yaron wani magani da ta samo a wata asibiti dan ta taɓa zaman birni shikenan yaro se ya birkice da koke koke, ƙin kama nono da sauran su daga nan se a nufi wajen babban me maganin da suka yadda dashi da dukkan imanin su, dake shima nasu ne se yace ai ɗa ko ƴa na aljanu ne sun ɗauke naki sun musanya miki dan haka maza maza akai daji kaza daidai wuri kaza a ajiye musu kayan su, se an kai an ajiye ita kuma tabi dare ta ɗauka ta kaiwa maigari cikin gidan sa na sirri dake can bayan gari gefen dajika inda yake harƙallar sa. Guri ta samu ta zauna tana haɗiyar busasshen yawu dan gaba ɗaya bakin ta ya bushe da ƙishirwa, tafiyar ƙafa sabon tace dan haka ba zata ce ta gaji ba sedai rashin ruwan ke neman kassara ta ga kuma ƴaƴa har biyu gaba da baya ga jaka me nayi se abin yayi mata yawa. Mutsu mutsun Ussaina da taji yasa ta san ta farka dan haka ta sauke ta dan ta ɗan huta da goyon sedai ita ba hutun take nema ba abinci take nema da bata samu ba kuwa ta buɗe baki ta shiga canyara kuka da ƴar Muryar ta na jarirai, kukan Salame ta shiga yi itama dan abin ya haɗe mata goma da ashirin. Haka Ussaina tayi kukan ta har ta gaji baccin yunwa ya ɗauke ta kafin itama ta haƙura ta goge fuskar ta ta maida ta baya dan ba zata iya riƙon hannu ba ta cigaba da tafiya. Se da rana ta faɗi gaba ɗaya kafin ta shiga wani ƙaramin ƙauye dan gaba ɗaya gidajen dake ciki basu fi a ƙirga ba haka kuma daga ganin gidajen su kasan har yau su kam suna cikin duhun rayuwa wato ba wayewa ko ta misƙala zarratin dan duk bukkoki ne ba gidan ko ƴar jar ƙasa ɗaya. Kan wani kututturen dabino ta kai zaune tana ajiyar zuciya tare da numfashin ta dake fita ɗaiɗai saboda wahala da jigatuwa, nan take zaune har se da wani tsoho ya zo wucewa ya ankara da ita kafin ya ɗan matsa nesa da ita ya shiga ƙare mata kallo Sannan ya gyaɗa kai ya wuce. Be daɗe ba ya dawo dashi da wasu dattijan da kuma matasa suka dinga magana da Yaren su da bata san wanne bane kafin ɗaya daga cikin matasan ya nufi ta. Tambaye ce daga ina take, me ta shigo nema a shiyyar su, me take buƙata haka dai, amsa ta bashi da sunan garin su wato BA MUNI wanda sunan ya samo asali ne daga yadda duk wani ɗan garin yake kyakkyawa sedai wani yafi wani amma mummuna kam babu sedai ko baƙo shiyasa suke saurin gane baƙo a cikin su. Iyayen sa ya koma ya sanar da amsar da ta bashi, sunan garin su da kuma taimakon da tace ta zo nema, seda suka kuma sake zantawa cikin dai Yaren nasu kafin wani saurayi ya tafi be daɗe ba ya dawo da wata tsohuwa sedai ba tukuf ba, nuna mata ita suka yi inda ita kuma ta ƙarasa ta kamata ta miƙe kuma cikin fara'a tace mata "Kunto min jikokin nawa mana, da alamu sun daɗe a goye". Bata ƙi ba ta kunto Hassana ta bata ta bar Ussaina "Ita ma sauko ta ta huta hakana". "Tana da kuka ne Inna". Murmushi innar tayi alamun ta gane kafin suka shiga tafiya hannun ta dafe da zanin ta dan cikin sa ta ɓoye jakar ta da zasu je wajen Maigari ashe Allah ne yayi suna da rabo da yadda kawu iro yace ba zata koma masa gida ba shikenan sun salwanta. Bukka ce me ɗan girma suka shiga sedai abin mamaki har dasu gadon ƙarfe a cikin ta, fita Inna kamar yadda ta kira tsohuwar tayi bayan ta kwantar da Hussaina tsawon lokaci tukunna ta dawo da bahon katako a hannu, ruwa ne masu zafi a cikin sa haka kuma ba fari bane da alamun an zuba wasu abubuwan banda kuma ganyayyaki dake ciki, tuɓe Hassana tayi ta mata wanka da yasa yarinyar ta ringa sauke ajiyar zuciya a jejjere, Ussaina kam ta sha ihu da ana yi mata dan alamu sun nuna ba su taɓa shiga ruwa masu zafi haka ba. Se da ta tabbatar sun gasu kafin ta ɗau abin ta fice inda Salame ta yi saurin isa ta ɗau yarinyar ta shiga jijjiga da lallashi har tayi shiru, "Ga can ruwa ki je kiyi wanka kema ko kya watsar da gajiya". "Toh Inna". Tace tana kwantar da Ussainar a hankali gudun kada ta tashi daga ɗan baccin da ya fara sanɗar ta............................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment, share and patronize fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 05 [ 11/27/2022 9:24 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.                     FREE PAGE 005 _________________________📖 A sittin ta runtse ido tana taune leɓen ta sabida zafin da ya ziyarce ta ita kuwa Hassana da zaƙuwa take zuƙa tana sauke ajiyar zuciya har ta ƙoshi kafin ta saki. Se lokacin ta buɗe idon ta da ya ɗan canja kala ta kalli yadda yarinyar ke numfashi a hankali a hankali tana ciccilla ƴan ƙafafuwan ta tare da wasa da hannayen ta se ta ji wani sabon farin ciki ya kamata har ma taji zafin ya tafi. Zanin ta ta gyara a ƙirji ta miƙe ta saɓa ta a kafaɗa ta shiga jijjiga ta dan tayi gyatsa, a haka baba Husaila ta tadda ta se ta kwantar da Ussaina ta karɓi Hassana ta fita da ita a kafaɗa ita kuma ta koma ta zauna tare da ɗaukar Ussaina. Haka ta shayar da ita itama sedai ba kamar Hassana ba Ussaina akwai ci dan se da ta daɗe kafin ta ƙoshi hakan ma se da ta canja mata ɗayan shiyasa gaba ɗaya ƙirjin nata ya ɗume da zafi. Tun daga lokacin take shayar dasu amma duk da haka baba Husaila na haɗa musu da ƴan dabaru musamman Ussaina da ta fahimci yarinyar akwai tsotso in aka barta bata ƙi ta wuni da nono a baki ba. Iya ƙauna da mutuntaka baba Husaila da ƴan uwan ta sun gwada mata, Abinci da abin sha bata taɓa rashin su ba, ga kula da ita da ƴaƴan ta da suke yi tun bare baba dan ko rigimar Ussaina ce ta tashi da dare bata bari ta tashi cewa take ta koma tayi kwanciyar ta ita kuma tayi ta fama har se tayi bacci tukunna hankalin ta ze kwanta. Ruwan wankan su kuwa kullum se ta sa musu magani shiyasa alhamdulillah jikin su yayi ƙwari se fatar su da ta ɗan dafe saboda zafin ruwa da kuma kalar magani duk da yanzu sun fara sabawa da zafin ruwan. Sannu a hankali har ta cinye wata ɗaya tare dasu basu ankara ba saboda zama da yayi daɗi, jakar ta kuwa baba ta adana mata dan ce mata tayi da su ne za'a bar ta ta shiga makarantar in taje, yadda ƴan uwan baba ke son ta ita abin har mamaki yake bata, wai yau ita Salame da kowa ke gudu itace yau ake so ko da yake ai ba ita ake so ba ƙaunar ƴaƴan ta ce ta shafe ta dan haka be kamata tayi wani kauɗi ba. Mace ɗaya ce ta taɓa son ta a Karan kanta yadda take wato Hajiya Hadiza principal ɗin su, Allah ya sani tana son matar a ranta irin son da bata san yadda zata kwatanta shi ba. Ta so ta a lokacin da kowa ya ƙi ta, ta bata gatan da bata taɓa zaton samu ba, a bayyane yake badan ita ba da ba zata taɓa samun damar karatun da take so ba, ita ta ɗau ɗawainiyar komai na makarantar ta, kuɗin PTA, uniform, littattafai, takalmi, Safa, abinci da komai da zata buƙata a makaranta tun da ta fara kuwa bata gaza ba har wata ɗaya da kwanaki baya da ta gama, ita kuwa ai sedai tace da ita Allah ya saka da kuma ya zame mata wajibi ta so ta. Kallon baba Husaila dake zaune gaban ta tana mata lissafi kawai take yi yayin da idanun ta suka tara ƙwalla, kuɗi ne daga kan ƙwandala zuwa na takarda wai wanda aka haɗa mata dan tafiya makarantar su da zata yi duba mijin ta in yazo (kamar yadda tace musu). Hannu ta sa ta share hawayen "Dan Allah baba ki maida musu kuɗin nan kin ji, zan fa iya zuwa da ƙafa".ta faɗa murya na rawa "Amma dai salamatu baki da kirki, ya za'a yi mutum yayi alkhairi a maida masa, to kul kar in Kuma ji ko ke kin yi hakan kin ji ko?". Da kai ta amsa wa baba kafin ta shiga yi musu godiya da addu'a kamar Allah ne ya aiko ta har se da baban ta gaji ta fice ta bar mata ɗakin. Tuhumar kanta take kan me yasa tayi masu ƙarya gashi su kuma sun yarda da ita sun zauna da ita da zuciya ɗaya, jaddada wa kanta take Allah ma ya sani ba'a san ran ta tayi ƙaryar ba, bata so a raba ta da yaranta ne kawai. Da wannan ta tattara kuɗin da suka tasamma dubu ɗaya ta zuba cikin jakar makarantar ta, ta kuma haɗe kayan ƴan biyu ta ninke ta zuba cikin jakar su ta rakuɓa nata kala huɗu da take dashi. Kashegari tayi sallama dasu cikin rashin daɗin rai dan har da kukan ta haka ma baba Husaila da ta zauna wajen ta, ji take kamar yarinyar ta dawwama tare da ita dan bata da matsala sam, yarinya ce me kirki ga ladabi da biyayya, gata ba har dama, ga nutsuwa da rashin ƙyuya, duk sanda taga ta tashi aiki bata bari tayi komai se karɓe ta shiga yi shiyasa so da yawa ma bata tashi yi saboda tasan ba zata bari tayi ba. Su kuwa ragowar ƴan gari da matasan su ƴaƴan ne suke jin kamar su ƙwace ta tafi ita kaɗai dan sun shiga zuciyoyin su barin ma Hassana da bata da rigima, in aka fita da ita har se an tausaya an dawo da ita dan bata kuka se dai in ko Bata da lafiya ko kuwa ta kai maƙura wajen jin yunwa, toh haka dai aka rabu kowa na mararin kowa, rayuwar kenan! Ganin tana da isassun kuɗi a hannu se kawai ta tare mota bayan ta fita sarari, sunan Makarantar su ta faɗa masa suka yi ciniki ta hau ya kai ta har bakin gare kuwa. Wajen baba megadi ta bada ajiyar jakar kayan su ta wuce office ɗin Hajiya Hadiza wato principal, ba abinda ya dawo da ita makarantar illa son karɓar sakamakon ta tare da certificate ɗin kammala karatun ta dan tana so a duk inda taje ta ɗora karatun ta dan shine burin ta tun bata san ze iya cika ba ko kuwa ze rushe ne har zuwa lokacin da ta fara hasashen cikar sa wato da maigari ya sanya baki a kan karatun. Ba kaɗan ba Hajiya Hadiza taji daɗin ganin Salame wadda ke amsa sunan Salama kamisu a makarantar, cikin nutsuwa ta bata takardun ta da WAEC result ɗin ta dan dama alƙawari ne tayi mata ana sakin result zata bada a ciro mata nata. Cikin ikon Allah tana da credit bakwai da excellent biyu, Salame kam har dasu kukan godiya ga Allah dan ta san shi yayi mata komai ba wai ita ba haka kuma ta sanadin wannan matar me kyakkyawar zuciya ne wato Hajiya Hadiza, godiya kam haka ta dinga zuba ta tana yi tana hawaye lokacin da take faɗa mata ga Form nan na College of Education ƴan gora, wata local government a babban garin da ƙauyen su yake ta cike ta mata submission in tana so ita Kuma zata biya mata komai, da ƙyar ta iya tsayar da kukan ta sukai sallama ta tafi. Se da ta tsaya ta karɓi kayan ta wajen Maigadi ta ma sallama tukunna ta wuce, mota ta tara zuwa tasha inda batare da tunanin komai ba ta biya motar garin GAMJI dan a can ne makarantar da take son yi take. Motar na cika aka fara tafiya inda ita kuma ta fara nata tunanin kan irin rayuwar da zata yi a can ita da yaran ta dama yadda rayuwar karatun ta zata kasance, shafa Form ɗin da Maah Hadiza ta bata ta sake yi tare da lumshe ido tana ayyana batutuwa da yawa a ranta. Zata cike Form ɗin tayi submitting a can makarantar a karan kanta batare da jiran Maah Hadiza ba dan bata jin nan kusa zata kuma komawa koda hanyar ƙauyen BA MUNI ne, da kanta zata tsaya wa kanta tayi komai sedai ta yaya tunda ba kuɗin hakan ne da ita ba, gashi yanzun nan in bata manta lissafin da Maah take mata na kuɗin da za'a kashe kusan dubu sha biyar ne, registration goma da ɗari biyar ragowar kunji kunji kuma su cinye sauran. A ina zata samo wannan kuɗin ita da ba ta da kowa bata da kuma komai? Wannan shine tunanin Salame yayinda mota ke ta tsuga gudu a titi, ragowar passengers kowa da abinda yake yi, wasu hira, wasu kallo, wasu karatu wasu kuwa bacci. Itama dai cikin tunanin ta da yake kakare mata sanadin rashin abokan rayuwa wato kuɗi nata baccin ya saɗaɗa saɗaf saɗaf yayi wuf! Yayi gaba da ita. Hayaniyar da ta cika wa kowa kunne ce ta sanar da masu barci an iso in da zasu wanda Salame na cikin su, miƙa tayi a hankali ta kalli Hassana dake ɗaure a gabanta tana baccin ta hankali kwance, tun da aka fara tafiyar bata yi wani rigima ba se Ussaina da ta ɗan yi kuka ta kunto ta ta bata tasha ta kuma maida ta bayan ta ɗan bata ruwan leda da ta saya guda biyu tun a can tasha kafin su tashi. A hankali ta sauka daga motar hannun ta riƙe da jakar kayan su ɗayan kuma jakar makarantar ta da ta saka Form da ragowar takardun ta a ciki. Tun da ta sakko taji ana shelar kowa ya kula da jakar kuɗi ko kayan sa saboda ɓarayi ta kuma damƙe jakar makarantar a ƙirjin ta ɗayar kuwa ta mata riƙon da tasan ba me iya fincike ta a hannun ta ta sauƙi. Tunanin inda zata nufa ta shiga yi se kuma ta tuno yadda suka yi da Maah Hadiza da ta tambaye ta ko ina zata zauna in ta zo karatun tace mata ai duk me napep ɗin da tace ya kai ta gidan haya ze kaita dan ba ya wahala a garin GAMJI. Bakin tashar ta fita taƙi kula duk me napep ɗin dake cikin tashar dan bata yarda dasu ba, suma zasu iya zama ɓarayi ne, a nan titi ta sami wani tace ya kai ta gidan haya. Seda suka fara tafiya ya tambaye ta gidan mutane da yawa ko kaɗan "Kamar dai biyar ko bakwai". Amsar da ta bashi kenan shima be kuma magana ba ya shiga tuƙa abar sa cike da ƙwarewa, wata unguwa ya shiga mara wadatacciyar tsafta ga nan gidaje a wajen ba fasali se uban yara da suka cika layin jikin su ba kyan gani. Gaban wani gidan bulo yayi fakin tare da nuna mata gidan "Ko a layin in kika lura gidan na cikin gidaje masu kyau haka ma ɗakunan su suka da yawa megidan ma a nan take rayuwa a ɗaki ɗaya, yanzu dai bani kuɗi na in tafi". "Tsaya dan Allah, nawa ake biya na hayar?". "Wata shida dubu uku shekara kuma dubu shida". Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta sauka tare da fidda kayan ta ta bashi Naira hamsin ɗin shi ya tafi. Cikin ɗari ɗari gaban ta na faɗuwa ta shigar da kayan zauren gidan ta shiga doka sallama kamar sabuwar warkewar makanta "Kai haba wannan wane irin bala'i ne tun ɗazu ake ta waalaikumussalam amma dan baƙin rashin mutunci an ƙi shigowa, to dan Allah mutum ya ɗige a wajen ƙarƙari in na gaji in ɗau taɓarya in jirge mutum dan na gaji da iskancin ƴan unguwar nan, me ake da gidan haya ni saratu ban da dai ƙaddara". "A ƙaddarar dai ya rufa miki asiri in ba haka ba mutum ya fita titi mana ya kwanta, se shegen baƙin faɗin rai yawa ƴar ƙaruna, naga kuɗin hayar ma har yanzu ina bin ku ciko amma har kika samu bakin kankanba ". Salame dake zauren banda zarar ido ba abinda take yi jin sabuwar duniyar da ta shigo yau da rana tsaka, a gidan hayar ma wato dai ba hutawa mutum ze yi ba, ya baro masifar dangi ya shiga masifar wasu mutanen daban kuma. "Bismilla, ina me sallama ta shigo in ga kowace da kuma me ya kawo ta tunda Allah ya rufa asiri yasa nidai ba'a sanni da cin bashi ba". "A'a Hajiya wannan magana taki kuma me kike nufi, ina ce faɗan ku tsakanin ke da saratu ne to me kuma ya shigo da ni ciki?". Matar ɗaya ɗakin ta yi but ta fito tana faɗin haka acewar ta Hajiya ita take neman faɗawa magana da tace ba'a san ta da cin bashi ba. "Ai ba zan yi mamaki dan kin yi uwa kin yi makarɓiya a zance na ba Huwaila, in ma Baki yi magana ba ai se a canja miki suna, to ni dai na faɗa ba'a sanni da cin bashi ba sedai in ke aka biyo dan kece gandun bashi mara haƙuri da kaɗan a gidan nan". Turo ɗankwali gaba Huwaila tayi da alama zata karta rashin mutunci ne se kuma ga Salame ta shigo dan ta gaji da tsayuwa ta kuma fahimci da ɗaiɗaya da ɗaiɗaya wannan maganar se ta fiddo duk matan gidan ita kuma ba zata iya jumurin su gama ba, so take ta sami wajen sauke yaran nan ta huta. Kallan kallo aka shiga yi tsakanin ta da magidanta biyu wato Hajiya da kuma saratu se kuma matashiya ɗaya wato Huwaila, "Dama nace a kai ni gidan haya zan kama ɗaki shine aka kawo ni nan". "Aiho Allah sarki, ashe abin arziƙi ne ya same ni saratu da Huwaila ke neman yi min tawaiwai, shigo baiwar Allah ai nice me gidan ɗaki kuma Allah ya soki akwai ɗaya da masu shi suka tashi". Ajiyar zuciya Salame ta saki tana ɗaukar jakar ta ratse Huwaila da saratu ta shige ɗakin Hajiya da tace ta shiga. Ruwa me sanyi ta bata ta sha kafin tayi mata bayanin kuɗin ɗakin da ya ragu be kai sauran ba dan duk shine ƙarami dan haka zata bada dubu biyu wata shida dubu huɗu kuma shekara se ta zaɓa in sunje ta ga yayi mata. Buɗe ɗakin tayi suka shiga a tare sedai gani kaya a ɗakin yasa Salame juyowa ta kalle ta "Wanda suka saki ɗakin basu sami kwashe kayan su bane?". "To ni dai abin ne da mamaki, ganin gida suka tafi basu dawo ba dama sun ce min ba lallai su dawo ba dan haka suka kwashe kayan sawar su, wannan kuma suka ce in suka rufa wata uku basu dawo ba to sun bar min, yanzu kuma ana batun watan su na shida kenan basu dawo ba, ina ta son ɗaukar kayan ina kuma tsoro amma tun da gaki ga yara kuma naga baki taho da komai ba se ki yi amfani da kayan sedai zan ɗau ƴan abubuwan amfani da nake so acikin kwanikan". Saroro tayi tana bin Hajiya da kallo kamar wadda bata gane abinda tace ba, se da Hajiyar ta taɓa ta sannan ta sunkuyar da kai "Amma Hajiya daga gani na yau har se ki bar min duk wannan kayan arziƙin bayan ke aka bawa?". "Kin shiga ɗakina fa kin gani mene bani dashi da zan ce zan ɗauka?, wanda nace ɗin ma sha'awa ce kawai irin ta ɗan Adam amma gwargwado ai Allah yayi min suttura, kinga ki kwantar da hankalin ki ni ba haka nake ba dan haka ki shiga ɗaki in har yayi miki gobe zaki bani kuɗi na". Tana faɗa tayi gaba abinta Salame ta bi bayan ta da kallo tana murmushi, da alama matar zata yi daɗin zama ɗan alamu sun nuna bata da ƙyashi da hassada haka kuma bata da san kai. Jakar su ta shigar sannan ta shiga ta tsaya tana sake bin ɗakin da kallo, labulaye masu kyau kuma sababbi, fenti me kyau ga katifa ma me taushi da tudu, flower vase ƙarama a gefe, dustbin, tiles, carpet ƙarami tabarma nannaɗe a tsaye ga kuma wardrobe madaidaiciya itama a gefe. Hamadala ta shiga yi tana hawaye kafin ta kwance yaranta ta shimfiɗe kowacce kan zanin ta ta shiga gyara ɗakin..........................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment and share please. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 06 [ 11/27/2022 9:29 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.                       FREE PAGE 06 _______________________📖 Seda ta Gama gyara ko ina dan dama ƙura ce kawai a ɗakin sannan ta lura da ƙaramin toilet tsayuwar mutum ɗaya, wanke shi shima tayi da ruwan da Hajiya ta bata jarka biyu ta roƙe ta gawayi ta ɗora musu ruwan wanka. Ƴan biyu ta fara yi wa wanka sannan itama ta samu tayi, bata iya ta nemi abinci ba ta kwanta bacci saboda gajiya. ★★★★ "Haba bawan Allah, ya kamata a ce ka saurara wa kanka wannan ɗimbin damuwar, fisabilillah shikenan kai in aka ga fara'a a fuskar ka sedai fake, ka sake kayi rayuwar kamar kowa ka ƙi, in ance dalilin da yasa rayuwa take zamar maka baibai kuma kaƙi yarda". A hankali mutumin da aka kira da bawan Allah ya shiga ɗago kan sa daga sunkuye da yake har ya ɗago baki ɗaya. Tsurawa wanda ya gama magana ido yayi na wasu sakanni kafin ya miƙe tsaye yana duban agogon hannun sa, bece masa komai ba ya shiga tarkata takardun sa ya zuba cikin briefcase sannan ya fita. Baki buɗe ɗayan mutumin ya bishi da kallo kafin kuma ya gyaɗa kan sa ganin yau iskancin bawan Allah har a kan sa, halin sa ne dama Amma ze iya rantsewa ya manta rabon da ya karta masa in ba yau ba. Fita yayi yana sanar da masinjan sa ya kulle office ɗin shima ya fita, kamar yadda yayi tsammani be ga ko shatin tayar motar sa a parking space ba, tasa ya shiga ya bar building ɗin shima. ★★★★★ 'Ban san wane irin aiki na tafka ba, ban san wace irin ƙwaƙwalwa gare ni ba da kullum bata bani mafita miƙaƙƙiya, duk da Riyya ta faɗa min nayi gaggawa in jira tukunna amma ni gani nake in na zauna to zan ta jira ne har na gaban abada, in bana son haka ya faru me zanyi kenan, me zan yi?!' Wannan shine tunanin da matashiyar ke tayi tana kai kawo a madaidaicin falon da yaji kayan alatu da alama dai tana cikin state of confusion ne dan se cije yatsun hannunta take cikin son samun mafita. Shigowar wata dattijuwa ɗakin yasa ta nemi kujera ta faɗa kamar wadda bata da laka, kallon ta dattijuwar tayi tana kaiwa zaune itama kan wata kujerar kafin ta shiga mata kallon tambaya "Yanzu shikenan Anna mu haka zamu zuba ido muna kallon komai na faruwa a gidan nan, ki duba fa watan yaya nawa yanzu da rasuwa amma ba wanda ke bin takan mu ke kuma naga ma abin ko ɗaɗa ki da ƙasa be yi ba". "Ni kin sa ba wani gane magana cikin magana nake ba gwara ki fito fili ki sanar dani me ke faruwa a gidan bamu sani ba". "Amma Anna kin san in mukai sake mun kusa barin daular nan mu koma kwana ƙarƙashin gada ko?". "Tuf tuf, Allah ya tsare ni.....". Anna ta faɗa tana tofar da miyau a gefe ".....banda neman masifa da bala'i irin naki me yakawo batun komawa ƙarƙashin gada kuma da ko a mafarki na gani in na tashi se na yi sadaka". "Nima ba so nake yi ba sedai in dai bamu motsa ba abinda ke daf da faruwa kenan". "Dan Allah yi min dalla dalla dan kin san bana san jan rai a magana". "Kamata yayi ace nice Abdu ze aura amma muna nan mun zuba ido yanzu haka naji jita jitar ze aure ƴar uwar Hajiya Babba". "Kam babban bu**uba, ni za'a kawo wa iskanci har gida, lallai Hajiya Babba ta ɗebo ruwan dafa kanta, ki kwantar da hankalin ki Audu bashi da wata mataa gidan duniya suke, da alama zan gwada musu barikanci na da basu sani ba". Cikin jin daɗi matashiyar ta gyara zama tana kai fuska gefe "Atoh abinda ya kamata dai muyi kenan dan yana auro wata kin san dole zamu bar gidan nan tun da yaya da ta haɗa mu ta raba Ni kuma shine bana fata". "Ki sa a ranki hakan ma baze taɓa faruwa ba, mu da gidan nan kuma mutu ka raba, mun shigo shi kenan fita kuma ba rana". ★★★★★ "Amma dai kin san ni ke san auran yarinyar nan shine kike wani batun wancan lusarin, yanzu da nayi magana kuma kice komai dan mu kike yi, ko ina basira a wannan tunanin naki oho, na daɗe ina faɗa miki tsufa yasa duk wata basira taki gujewa amma kin ƙi yarda, to wannan karon kam sedai kiyi haƙuri dan wallahi ba zan iya bin tsarin ki ba". "Kai kam ai dama baka da fahimta, komai se an zauna an maka gwari gwari kafin kake ganewa, yanzu kamata yayi mu kama yaron nan a hannun mu kuma dole se ta hanyar matar sa dan ai shi ba sakarai bane da ze dawo ya yarda damu bayan duk abinda suka dinga faruwa, amma ina matar sa ta zama tamu ai ruwa tasha kaga ta nan zamu dinga samun duk bayanan da muke so a kan sa kuma mu dinga aiwatar da shirin mu a kan shi hankali kwance har mu kai shi ƙasa". "A soke shi, ban yarda da wannan tsarin ba in har se ita zaki aura masa to a fasa". "Zo tsaya mana jarumina, tsaya ka saurare ni kaji?". Ta faɗa tana bin bayan shi da sauri sedai ko juyowa be yi ba balle ya tsaya saurarar ta kamar yadda take so, seda ya kai bakin ƙofar falon ya juya gare ta "In har aka gabatar da tsarin nan tabbas za'a samu matsala dan haka kar kuce ban faɗa muku ba, a soke shi shine kawai kwanciyar hankali". Yana faɗa ya fice yayin da dattijuwar ta dafe kanta tana koma wa bedroom ɗin da sauri ta ɗauki phone ɗin ta ta shiga dialing wasu numbers, tsawon lokaci tana ringing amma ba'a ɗauka ba har ta katse, tsaki taja ta kuma dialing, wannan karon ma kamar ba za'a ɗauka ba dan se a kusan ringing ɗin ƙarshe aka ɗauka, bata jira wani gaisuwa ba ta shiga kora dalilin kiran da tayi "Plan cancelled, a daƙile komai a kuma tsayar da komai zuwa lokacin da zan sanar dake yanzu akwai matsala a ƙasa". Tana gama faɗa tayi hanging call ɗin tare da wurga wayar kan bed itama ta biya cikin tunaninnikan dake yawo a kwanyar ta.                          ★★★★★★                          5 years later                          ★★★★★★ Cikin sauri sauri take Rolling veil ɗin a zagayayyar fuskar ta, pin ta manna a jiki bayan ta daidaita zaman mayafin sannan ta matsa daga wajen mirrorn, rashin ganin su a ɗakin yasa ta ja ƙwafa ta kwashi bags da food flask ɗin su ta fita dashi tare da jawo ƙofar ɗakin ta sa mata key. Ɗakin dake kusa da nata ta idasa tana ɗaya labulen "Barka da asuba Hajiya". "Barka kadai uwar biyu, ina dai kun tashi Lafiya". "Lafiya lau na tashi, su kam na san tuni kin san ya suke tin da sun ƙaura nan". "Aikuwa dai muna tare da ƙawaye tun ɗazu muna gaisawa". "Ai yayi kyau, bari mu wuce mun kusa makara, Ibty, Ifty maza ku taho mu tafi". "To se kun dawo, Allah ya tsare ya bada Sa'a". "Ameen Hajiya, mungode". Daga bayan labulen Hajiya suka fito se zarar ido suke yi dan sun san sun yi ba daidai ba, ita kam bata tsaya wata wata ba ta kama hannun su a each hand ɗin ta suka fita daga gidan. Napep ta tare musu suka hau inda ta e ya kai ta Star light Academy wato makarantar yaran. Juyowa tayi ta kalli Ibty dake gefen daman ta, da sauri yarinyar ta sunkuyar da kanta haka ma da ta kalli Ifty kafin kuma su haɗa baki wajen faɗin "We are sorry Mamma". Girgiza kai tayi ta maida hankalin ta batare da tayi responding masu ba "Please kiyi haƙuri Mamma, Allah Ifty ce tace muje mu gaida Hajiya tun da baki gama da wuri ba". "So Ifty ce yayar ki ko kece yayarta?". "Ba zamu kuma ba, insha Allah Mamman musu". "Allah yayi muku Albarka". Ta faɗa tana rungume kawun su, suma sosai suka kwanta a jikin ta suna faɗin ameen. Ko da suka je school ɗin bata bar su ba seda ta raka su class ɗin su primary one Sannan ta tafi bayan ta sake jaddada musu zama good girls. Cikin rashin jin daɗi ta tare wani napep ɗin ta shiga zuwa wajen aikin ta, sam bata so ba yau tayi latti, tun da ta fara aiki dasu zata iya cewa yau ne kawai ta makara amma se ta ke jin kamar ta aikata wani crime babba duba da yadda aka dinga maimaita mata rashin son makara a gare ta kasancewar tana riƙe da post ɗin secretary ɗin C.E.O na wajen baki ɗaya. Bakin makeken building ɗin ta tsayar da me napep ta biya shi kuɗin sa ta nufi gare ɗin. Ƙarin building me da yaji glass ta kusan ko ina haka kana kallon shi zaka bashi hawa kusan biyar ko bakwai a ƙiyasce, daga can saman building ɗin aka rubuta da manyan harufan, A.A GAMJI Company. Kamar ko da yaushe yau ma se da aka caje ta duk kuwa da kasancewar ta ma'aikaciya a wajen wanda wannan doka ce hatta shi kan sa C.E.O ɗin in ze shiga ko so nawa ne se an caje motar sa da shi kan sa, wannan yasa kamfanin ke daga cikin manyan kamfanonin da ke da cikakken tsaro da doka. Tun a bakin gate ta zare baƙar after dress ɗin da ta ɗora kan white hijab ɗin ta iya kafaɗa da rigar jikin itama fara iya gwiwa se dogon dark blue ɗin wando daga ƙasa, ƙafar ta kuma sanye da blue ɗin socks da takalmin ta wedge baƙi. Da sauri da sauri ta dinga takawa batare da ta kula gaisuwar da ma'aikata ke mata ba ta wuce lifter tayi pressing kan fifth floor inda nan ne office ɗin C.E.O ɗin yake, seda tayi wani gasping air ganin yau ya rigata zuwa dan ga nan office ɗin a buɗe alamun yana ciki. Kan table ɗin ta ta ajiye jakar ta da komai ta ƙara sa cikin office ɗin sosai da sallama, kanta a ƙasa amma yaji sautin amsawar sa can ƙasa. Ta jima a tsaye shiru tana jiran yace wani abu da zata sami damar bashi haƙuri kan lateness ɗin da tayi sedai shiru bece komai ba kamar ba kowa a ciki se sautin Ac dake aiki a hankali. "Ehm..am..amm..sorry sir..for the...lateness...it wasn't intentional, am sorry please". Ta faɗa a rarrabe baki na ɗan rawa jin shiru be da niyyar cewa komai. "Any schedule for today?". Da sauri ta ɗago tana gyaɗa kai uwa ƙadangaruwa "Yes...sure sir". Ta fice da sauri zuwa table ɗin ta tare da fara ƙoƙarin ciro iPad ɗin ta, inda Allah ya taimake ta duk sanda ta zama less busy ba wai ɓata lokacin take a banza ba, a'a tana rage wasu ayyukan ne kamar wannan schedule ɗin tun jiya ta haɗa shi gashi kuwa se mata amfani. Komawa tayi office ɗin.ta matsa gaban table ta ajiye masa iPad ɗin ta shiga yi masa bayanin schedule ɗin ɗaya bayan ɗaya, seda ta gama gaba ɗaya sannan yasa hannun sa dake cike da gargasa ya ɗau ipad ɗin yana bi, sanar mata da wanda zeyi attending yayi yayinda yace ayi postponing ragowar. With due respect ta karɓa ta juya ta fita first office inda nan take, gyara kayan ta tayi kana ta zauna ta shiga aikin ta cike da ƙwarewa da sanin makamar aiki. Tana nan zaune ya taho shiga office ɗin, kamar kullum cikin mutunta juna suka gaisa dashi, tana matuƙar girmama shi domin yasan mutuncin ma'aikata haka kuma ya riƙe nashi mutuncin, manager kenan HAISAM ƘADEER, babban makusanci ga CEO ɗin su da alama dan shi kaɗai ne bashi da wani shamaki na shiga office ɗin sa a duk wadda yaso. Alarm ɗin da ya shaida mata lokacin meeting ɗin da zasu yi yayi yasa ta miƙe ta tafi duba tsaruwar wajen, komai yayi yadda ya kamata se gabatar wa kawai, komawa tayi ta sake daidaita nutsuwar ta sannan tayi knocking a ƙofar, sakanni kaɗan aka bata umarnin shiga, kanta a ƙasa ta shiga "Its time for the meeting with Al-azhar group of companies sir". Takardun kan tables ɗin sa ya tura mata ta ƙarasa ta shiga tattara su har ta gama shirya su tas sannan ta riƙe a hannun ta ta fice dasu. Duban sa ya maida kan Haisam dake zaune ba shida ko alamun tashi "Haven't you heard what she said or you're deaf?". "Won't mind repeating sir". Dukan table ɗin yayi da hannun sa cikin nuna ɓacin ran sa da ba wanda ke katarin yawan gani se Haisam ɗin "For God sake ba wasa nake ba Haisam ka kuma san ba lokacin wasan bane, when it comes to business kafi kowa sanin wane ni dan akan haka zamu samu matsala, babbar matsala wallahi cos I won't mind suspending you". "Ai fa an taɓo rayuwar ka dole bakin ka ya buɗe, dan rashin mutunci tun ɗazu nake maka magana kamin banza amma yanzu ka cika min kunne da ihu, an ƙi aje meeting ɗin in ka tashi ba suspending ba kayi firing ɗina oga sir, aikin banza kawai". Haisam ya faɗa yana ficewa daga office ɗin bayan ya doka ƙofar da ƙarfin da har yasa salma ɗan firgita. Fashionable wrist watch ɗin ta ta duba taga its five minutes past exactly lokacin meeting ɗin, me yake damun boss yau, shine abinda take tunani, he's always a man of his word and time, Yana mutunta lokaci ta yarda ba'a jiran sa sedai ya jira, wannan principle ɗin sa ne. Buɗewar ƙofar yasa ta gyara tsayuwa ta yi ƙasa da kai, seda ya wuce gaba sannan ta bi bayan sa har zuwa scheduled hall ɗin, kamar yadda tayi zato kuwa kowa ya hallara hatta da manager kuwa se ita dashi ne kawai. Wajen zaman su suka ƙarasa ya zauna ita kuma ta ajiye kayan hannun ta ta gaida mutanen wajen ta shiga gabatar da bayanan da ya kamata ta wajen ta har ta gama tsaf kafin ta zauna ana tafa mata manager ya miƙe yayi nashi ƙarin bayanin da su kaɗai suka gamsar da mutanen siyan share a Company ɗin so shi bece komai ba se negotiation kaeai da aka yi dashi. Ya daɗe yana respecting yarinyar dan ta san ta kan aikin ta uwa uba tana da kaifin tuanni ga basira ga kuma kamewa ba kamar sauran mata da ya dinga ɗauka kan post ɗin ta ba da ko daɗe wa ba sayi yake sallamar su saboda halayyar akuyancin da suke yi......................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment and share fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 07 [ 11/30/2022 3:18 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable. FREE PAGE 007 ________________________📖 Seda ta tabbatar an gyara an kuma rufe hall ɗin sannan ta koma bakin aikin ta. Haka ta wuni aiki kamar yadda ta saba se in ta samu ɗan lokaci ta huta se kuma ta ɗora, ƙarfe biyu lokacin sallah yayi dan haka ta ajiye ta wuce cike da tunanin dawowa ta gyara wajen da tayi mistake. Ana idar da sallah cikin babban masallacin Company ɗin da suke sallah ta miƙe bayan ta idar da azkhar ɗin ta ta nufi komawa ta steps Wanda haka kawai taji tana son bi ta nan dan ta motsa jiki. A step na kusan Ashirin da something suka yi bumping into each other batare da sun lura ba, baya tayi zata gangara ya yi maza yasa hannu ya tallafe ƙugun ta yayinda itama cikin firgicin tasa hannun ta ɗaya ta riƙe rigar sa ta wajen ƙirji ɗayan kuma ta zagaye wuyan sa dashi. Se da tayi regaining balance ya sake ta sannan ta lura da abinda tayi, da sauri ta zare hannun jikin ta na ɗaukar rawa, raɓawa yayi ta gefen ta ya wuce yana adjusting rigar sa da ta cukurkuɗa masa. Ranar har suka tashi aiki by 4 kamar yadda suka saba she wasn't herself tana dai daurewa ne kawai. Seda ta biya ta makarantar su Ibty ta ɗebe su dan four thirty ake tashin su kasancewar boko haɗe da Islamic school sannan suka wuce gida. Ta daɗe kwance kan katifar su kafin tayi ƙarfin halin miƙewa ta dafa musu ruwan wanka ta musu itama tayi sannan ta dafa musu spaghetti Dan tana da soyayyar miya. Ranar kasa gane kanta tayi dan gaba ɗaya jikin ta ya rikice kasancewar wannan karo na farko da ta taɓa samun close intimation da namiji babba kamar haka, a duk rayuwar ta tsakanin ta da maza baya baya ne ma'ana daga nesa nesa se gashi yau itace ɗare ɗare kan ƙirjin wani baligi hannun sa a cikin jikin ta. Duk da it was an accident amma se take jin ta wani guilty, kamar wata me laifi ko wadda ta aikata wani gagarumin laifi. Da ƙyar ta yaƙi tunanin ta shiga rayuwar ta kamar ko yaushe, ka shegari bata bari sun makara ba da wuri ta miƙa su school ita kuma ta wuce. Tun daga bakin gate ta lura da wani irin kallo da security ɗin ke bin ta dashi kamar wata mai laifi ko kuwa irin kallon kin shiga ukun nan, sosai ƙirjin ta ke bugu ta dai daure ta shiga ƙara sawa kaina building, ko a nan ɗin ma bata canja zabi ba haka mazan wajen ke mata kallon kamar munafuka ko me fuska biyu matan kuma na mata kallon an ji kunya. Jiki a sanyaye ta ƙarasa office ɗin sa ta gyara abinda ya kamata itace zata gyara ta gama ta koma nata, a irin kallon da mutanen Company ɗin ke mata yau se taji sam ba zata ko iya sarrafa jikin ta wajen yin wani aiki ba har se taji ba'a sin kallon hakan ya sa ta zauna jiran CEO ko manager taji gagarumin laifin da ta aikata. Har ƙarfe tara ta wuce ba CEO ba labarin sa haka ma manager abinda bata taɓa ganin ya faru ba haka kuma ya ƙara sata cikin zulumi, se after ten sannan CEO ɗim yazo, yanayin yadda fuskar sa take a haɗe yasa ta sha jinin jikin ta ta tabbatar tabbas laifin da ta aikata maigirma ne tun bare ma da ya tsaya ya ƙare mata kallo na kusan minti biyu kafin ya shige office ɗin sa. Be daɗe da shiga ba manager ya ƙaraso shima dai expression ɗin fuskar sa wasn't helping ko kaɗan, yau kam ko da ta gaishe shi hannu kawai ya ɗaga mata ya wuce. Jagwab ta koma ta zauna cikin seat ɗin ta tana addu'ar ko meye Allah ya kawo mata da sauƙi ya kuma taƙaita yasa kar su kore ta daga aiki dan in suka kore ta ba bata san ina zata kama ba. Ta daɗe tana shan wahalar neman aiki kafin ta samu wannan da ta ke ɗaukar ɗawainiyar kanta da ƴaƴan ta dashi, ta ya ba zata yi fatan kar a kore ta ba. Kusan hours ɗaya da shigar su office landline ɗin kan table ɗin ta ta hau ƙara, manager ne ke bata umarnin shigowa office ɗin CEO ta same su, a tsarge ta miƙe ta shiga takawa zuwa office ɗin, bata jin ɗaya daga cikin su ya amsa mata sallamar da tayi dan ita dai bata ji ko tarin ɗayan su ba "Have a seat miss Salma". Taji muryar manager Haisam haka kuma baya Musa ba ta samu kujera ta zauna kanta a ƙasa "Take a look at this newspaper please". Ya sake inquiring bayan ya ajiye mata takardar kan table a gaban ta. Hannun ta na rawa ta ɗaya ta kai kan takardar tare da juya front page ɗin ta shiga bin heading ɗin da kallo, cikin mugun sauri ta yar da takardar ta miƙe tsaye jikin ta na ɓari gaf gaf gaf kamar wadda aka watsawa ruwan ƙanƙara lokacin tsananin hunturun sanyi, girgiza kan ta ta shiga yi bakin ta na rawa tana son yin magana amma takasa, daga ƙarshe tasa hannun ta biyu ta dafe kanta tare da sulalewa ta faɗa kan sofar wajen tana ambatar kalmar innalillahi wa Inna ilaihi rajiun. "Relax, take it easy miss Salma, everything is gonna be fine". Abinda Haisam ya ringa maimaita mata kenan ganin yanayin da ta shiga sedai ita ba saurarar shi ma take ba "Bani bace, it wasn't me sir, wallahi bani bace". "Is okay, keep calm Please". Shiru tayi tana sauke numfashi tare da ajiyar zuciya kamar wadda tasha tseren gudun kilomita dubu ko sama da haka, sedai ta fara dawowa daidai kafin Haisam ya sake mata magana "Shin kin gane hoton nan miss Salma?". "Bani bace sir, taya zan gane hoton da bani bace a jiki". "Har na farkon ma bake bace?". "Sure, babu ni ko ɗaya a nan, editing kawai aka yi aka sa fuska ta, taya ma zan iya wannan abun and with someone I do respect the most, wannan wani tuggu ne kawai na maƙiya". "The first picture is real, kece a jiki and nima nine a jiki, it wasn't edition". Ya faɗa for the first time tun shigowar ta office ɗin "But taya ya zama real sir, yaushe har ma, har".ta kasa ƙara sawa "Yesterday's accident, we accidentally bumped into each other shine aka sami wanda yayi snapping iya inda suke buƙata wajen ƙulla makircin su". "Hasbunallah wani'imal wakeel". Ta faɗa tana dafe kanta dan ita se yanzu ma ta tuna da abinda ya faru jiyan dan tun da ta tursasa kanta mantawa bata kuma yarda ta tuna ba sam. Tsawon lokaci suna zaune shiru bame magana kafin Haisam yayi cutting silence ɗin "He'll marry you". A firgice ta ɗago jin wani sabon batun yashin hankalin "Who, how, why?". Ya jero tambayoyi ukun a tare, duk yadda suke cikin tashin hankali seda Haisam ya murmusa ganin yadda ta kiɗime da jin batun har ma fiye da lokyda ta ga hotunan "Firstly, lemme answer your question why, ko kun san a garin nan ba inda wannan jaridar bata shiga ba lungu da saƙo inda jama'a ke ta zagi da tsine muku ke da boss ɗin naki, a dalilin haka ba abinda zaki yi da ze dakushe batun se aure dan kullum maƙiya da mahassada zasu sami sabon abin faɗe ne akan hakan kuma duk ɓacin suna ne gare ku musamman shi da yake harkar kasuwanci ya kuma zama sananne, tun farko na ke kawai kin taka sawun ɓarawo ne amma ɓacin sunan wa shi ake nema nake ba. For your question how, to yadda ake kowane aure haka kuma za'a yi naku in less than a month insha Allah. For the last question, who, the answer is Alh ABDALLAH ABDULSALAM GAMJI. Hope I answered all your questions?". Gana ɗaya she's totally speechless, ita a bayanan sa ba kowanne ta gane ba, tukunna ma Who's Abdallah Abdulsalam Gamji? "But sir who's with the name da ka faɗa yanzu?". "Your boss here, the CEO A.A.Gamji company". Zuwa yanzu kam bata da abin cewa, to me kuma zata ce. "Kiyi haƙuri, auren ne kawai ze zama solution dan a yadda aka ɓata miki suna nan da shekara goma na bana jin akwai namijin da ze yarda ya aure ki, dan dai baki karanta abinda aka rubuta bane, yanzu ki sanar damu a ina zamu sami magabatan ki". "Bana tare dasu, ina rayuwa ni kaɗai da ƴaƴana a gidan haya". A hankali ya buɗe idon sa ya zuba kan Haisam irin me wannan take nufi, kau da kai Haisam yayi "Na fahimta, sedai su ɗin a ina suke dan kin san dole a wajen su za'a nemi auren ki". "Ƙauyen BA MUNI sedai bana tunanin zasu saurare ku dan ni ɗin korarriya ce". "Bangane ba, korarriya kamar yaya?". "Nayi aure ina secondary school batare da sanin su ba inda na haifi ƴaƴana biyu, bayan mun gama WAEC muna shirin zuwa gida mijin ya gudu se ni kaɗai na koma da ƴaƴan shine suka shegan ta su suka buƙaci in ba da su akai inda ban sani ba dan gujewa abin kunya acewar da naƙi shine suka bani zaɓin bada yaran ko kuwa barin su nikuma na zaɓi ƴaƴana". Kallon kallo aka shiga yi tsakanin Haisam da Abdallah inda kowa da abinda yake kitsawa a ransa, ture komai dake ransa Haisam yayi "Ina ce dai ƴan garin ku sun san wannan labarin in Kuma na faɗa za'a gane ke nake nufi?". "Sosai ma kuwa". "Shikenan za ki iya tafiya yadda ake ciki kuma zan sanar dake". Miƙewa tayi zata fita ya dakatar da ita "Ji nan, rabon ki da garin naku shekara nawa yanzu?". "Shekara biyar da watanni". Da kika shigo garin nan a ina kika fara zama, ko kuwa kuna da ƴan uwa ne?". "Sam ban san kowa ba a nan, na fara zama a gidan haya da nake zaune har yanzu". "Waye yayi sponsoring karatun ki". "Ni na ɗau nayin kaina da sana'ar haɗa turaren wuta da na dinga yiwa wata ƴar Maiduguri tana rarrabawa a faɗin Nigeria gaba ɗaya". "Sunan product ɗin fa?". "Ƙamshin amarya". "You can go". Fita tayi tana sauke ajiyar zuciya jin wasu tambayoyi daga boss ɗin ta kamar wani ɗan jarida, bata taɓa sanin yana magana haka me tsayi ba se yau, ita bata ga wani point ba a auren ta da suka ce ze yi, ita da sun ƙyale ta dan sam ita aure baya gaban ta balle mazan gaba ɗaya sedai dole saboda ƴaƴan ta da suka kasance mata tana buƙatar garkuwa irin ta ɗa namiji wanda ba ta inda zata sama musu ita se ta hanyar auren. "Amma meye point a tambayoyin da ka dinga yiwa yarinyar?, Beside Ina cewa kayi bayan komai ya lafa zaka sake ta?". "In shi kuma yaje ya jiyo abinda mu bamu sani ba a kanta ya riƙe matsayin makamin hana auren fa?". "You so stupid man, ya Ina tambayar ka kana maida min tambaya matsayin amsa?". "And what did I say wrong?". Dunƙule hannu Haisam yayi ya kai masa duka a kafaɗa shi kuma ya goce yana sakin silent smile na ganin yadda ya harzuƙa Haisam ɗin wanda ba wanda ke iya tolerating halin sa se shi kaɗai da Allah ya sallaɗawa so da ƙaunar sa. "Please bawan Allah let's be serious, kaga wannan auren ina so ya faru at all cost ko banda hatsaniyar jaridar nan har ma da jama'ar gidan ku, na rasa gane wace irin cukurkuɗaɗɗiyar rayuwa ce ke faruwa a gidan ku, da na zauna nayi tunani dole se da mace a tare da kai zamu fahimci kome ke tafiya dan na tabbatar wanda suka farmaki nafisa zasu sake yunƙurowa tun bare ma in ya zama kai ka samo matar da kanka". "Rayuwar gidan mu bahaguwar rayuwa ce da hatta ni da nake cikin ta ba komai nake fahimta ba, abu ɗaya na sani shine kowa mara gaskiya ne, kowa macuci ne haka kuma kowa mugu ne shiyasa na zaɓi na rayu on my own haka kuma bana don shigar da kowace ƴa cikin haɗarin dake tattare da rayuwa ta dan maharana suna da yawa Haisam, dalilin kenan da na haƙura da aure amma for now ya zama dole in miƙe in har zata shiga rayuwa ta ko da na kwanaki ne kuwa". "Me kake gani, mu bata hutu zuwa lokacin da komai ze tabbata ta fara amsa sunan matar ka ko yaya?". Relaxing yayi cikin kujerar da yake kai yana lumshe ido "Kasan meye damuwa ta?, Ƴaƴan ta, bana san a cutar da kowanne saboda ni, bana a ringa cutar da yaran da basu ji ba basu gani ba saboda wani ƙiyayya da ake min". Ya ƙarashe yana buɗe idanun sa da lokaci guda suka canja kala zuwa jajaja brownish "It hurts, it deeply hurt Haisam". Ya faɗa yana dafe ƙirjin sa ɓangaren hagun sa alamun yana masa ciwo "Calm down Abu Aulad, calm down insha Allah ba abinda ze same su". Rufe idon sa yayi tare da kife kan sa kan table ɗin gaban sa ya shiga ajiyar zuciya akai akai tare da haɗiye wani ƙullutu me matuƙar ɗaci da ke taso masa duk sanda ya tuno yara, yana matuƙar san yara a rayuwar sa hakan yasa ake masa Indiya da Abu Aulad tun yana saurayi, da ya zama magidanci kuwa yayi aure burin sa da fatan sa ya haihu ne kawai, lokacin da Allah ya bawa matar sa ciki irin murnar da yayi ba me misaltuwa bace sedai Allah be nufa rayayyu bane daga uwar har ƴaƴan. Miƙewa yayi ya zafi key ɗin sa ya fice da sauri kamar ze tashi sama haka ma Haisam ya bi bayan sa, yau dai kam ba abinda suka tsinana....................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️ Ote, Comment and share fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 09 [ 12/1/2022 1:04 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.                      FREE PAGE 009 ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable. _________________________📖 tafiya ce sosai daga Gamji kafin a kai ƙauyen Ba muni dan har se dasu Ibty suka gaji da kwaramniya suka yi bacci a jikin Haisam dake baya a tare dasu. Ita kam salma wani irin nervousness da faɗuwar gaba ne ya sarƙe ta, after good five years da barin ta gida yau gashi zata koma kan mau'idin da bata san wanne bane, abu ɗaya ta sani shine akan maganar auren ta ne aka tashi tafiyar. Motar shiru baka jin tashin komai se numfashin su a hankali a hankali da kuma gudun Ac dake tashi, Haisam kam wayar sa yake pressing hankalin sa kwance yana chat abinsa da budurwar sa yayinda a ta gaban motar kuwa tamkar wasu kurame ko saƙaguna haka suke zaune. Shi tuƙin sa kawai yake ita kuwa ba abinda take se bin hanya da kallo kamar me irga bishiyun da suke wucewa, tunanin yadda zata riski garin bayan shekara biyar da tayi bata cikin sa take, maganar tarba kuwa tasan ba wata tarba da zata samu a wajen ƴan uwan mahaifin nata. Abu ne ba ɓoyayye ba cewa murna da jin daɗi suka yi lokacin da ta zaɓi barin su saboda ƴaƴan ta, irin wulaƙancin da suka yi mata na ƙin barin ta ta ɗau ko tsinke a gidan be bar kanta ba kuma bata jin ze barin har nan da gaban abada. Wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya ta saki lokacin da suka shiga garin tana me lumshe ido cikin kiran sunan Allah a ranta, a kaikaice ya kalle ta dan sosai ajiyar numfashin nata ya fito fili. Gidan maigari ya nufa kamar jiya, seda duk suka fita daga motar suka barta dan ji tayi gaba ɗaya kamar bata da wani sauran laka a jikin ta, jikin yayi mata nauyi kamar baya tare da ita, Haisam da ya lura bata biyo su bane ya juya ya tabbatar sannan ya maida kallon sa kan Abu Aulad "Madam fa bata fito ba, ina ganin kaje kaji ko da damuwa ne ni Bari in ƙarasa ciki". Ya faɗa yana yin gaba da sauri dan yasan kaɗan daga aikin bawan Allah yace shi yaje ya duba. Ganin yadda ya tafi yabar shi a wajen yasa cikin takaicin abinda tayi kamar wata ƙaramar yarinya ya koma wajen motar, murfin ɓangaren da take zaune ya kama ya buɗe da ɗan ƙarfi dan ransa ya ɓaci da abinda tayi, ya zata wani nemi waje ta zauna a mota bayan tasan suna da abubuwan yi da yawa a gaban su. A ɗan firgice ta buɗe idon ta da ke lumshe hakan yasa suka yi wani walai kafin suka shige cikin nasa da ya tsare ta dasu, da sauri ya kau da kan sa dan jin wani dam da gaban sa yayi ganin ƙwayar idon ta, be taɓa sanin haka ƙwayar idon ta take ba se yau, "Kina jira a ɗauke ki ne kafin ki fito?". Tsam tayi jin abinda ya faɗa dan bata gane me yake nufi ba "Malama ki fito mu yi abinda ya kawo mu dan ba kwana zamu yi ba kin sani ko?". Ƙafarta dake ajiye gaban motar ta ɗaga a hankali ta fitar waje kafin ta fara ƙoƙarin fitar da gangar jikin ta hakan yasa aya matsa daga tsayuwar da yayi jikin motar, seda ta gyara mayafin kanta sannan ta yi gaba shi kuma ya kulle motar da mukulli bayan ya buɗe glass ɗin baya kaɗan saboda su Ibty dake kwance suna bacci. Gaba ɗaya ido mutanen wajen suka zuba mata suna kallo yayinda ƙananan maganganu ke tashi dan jiya da yawa da suka san abinda ya faru da ita da suka ji batun ɗaurin auren ta ba ƙaramin tu'ajjabi suka yi ba barin ma da suka ga zuƙeƙen mijin da Allah ya bata. Yanzu kuwa ba wai sun gane ta bane maganganun kan irin kyan ta da kuma na kayan jikin ta ne, ƴan gayu irin ta dasu Haisam ba kasafai suke shigowa garin ba shiyasa duk sanda suka shigo suke zama abin kallo da sha'awa ga jama'ar garin. A hankali ta saluɓe brown heel shoe ɗin dake ƙafarta ta kai zaune kan shimfiɗar fadar maigari kafin cikin sanyayyar Muryar ta ta shiga gaida shi kamar yadda suke yi a al'adance. Cikin rawar jiki maigari ya amsa duk da bai shaida cewa Salame bace, a tunanin sa wata ce daga dangin su ɗan birni suka zo da ita tare maybe dan taga mahaifar matar da ya aura ko wani abu. "Ala gafarta malam, ga Salman nan gaban ka mun zo da ita dan kayi mata bayanin yadda auren ya ƙullu jiya a kuma bata sadakin ta dan ta shaida". "Ikon Allah, yaro kana nufin nan Salame ce a gabana, lallai Allah mai iko, sannu Salame, sannu kinji". Maigari ya faɗa cikin ruɗewar jin wai wannan tsaleliyar budurwar ce Salame da suka kora da goyon ƴaƴa biyu shekara biyar da suka gabata, yarinyar da ko da ta bar garin ba komai gare ta se tarin tsumma dan hatta takalmi babu a ƙafarta ranar. "Nice baba maigari, fatan mun same ku lafiya". "Lafiya lau salamatu, ya yaran naki? Ko kin bar su a gida ne?". "A'a baba suna mota bacci suka yi shiyasa ba'a ɗauko su ba". "Allah Sarkin hikima, yanzu sun girma abin su ko, hekara biyar ai ba nan bace dole yanzu sun girma". "Aikuwa dai". Ta faɗa tare da jan bakin ta ta tsuke ganin surutun na maigari bame ƙare wa bane ita kuma ta zaƙu taji bayanin da aka ce yayi mata da in ba kunnuwan ta ne basu jiyo daidai ba kamar taji ana batun an ɗaura mata aure ne tun jiya "Wato salamatu jiya yaran nan suka zo nan suka same Ni da batun neman auren ki, duk da ko a Shari'a ni me bayar da auren ki ne amma se na bawa iyayen ki haƙƙin su ta hanyar sawa a ka kira su na shaida musu abinda ke shirin aukuwa sedai dake Habibu ba ɗan bana da arziƙi bane se yace shi sam babu shi a lamarin ki haka ma iro, se Adamu ne shi dake wani sa'in yana da tunani ya saurari yaran nan amma yace sedai in a ɗaura auren a jiyan dan baze juri a Kuma tado shi daga wajen sana'ar sa domin ki ba wannan yasa dole aka ɗaura auren bisa sadakin da shi mijin ki ya biya wato dubu hamsin gashi nan a zaune, yanzu bari in tashi in ɗauko su gare ki, kin ji yadda batun ya kasance". Wani irin suya zuciyar ta ta shiga yi cikin ƙirjin ta jin irin cin kashin da ƴan uwan mahaifin ta suka aikata yayin neman auren ta, shin me ta kashewa mutanen nan ne da suke neman se sun wulaƙanta ta ido rufe?, Shin akwai ɓoyayyen dabi ne tsakanin mahaifin ta dasu ko kuwa, su dai ba ƴan uba ba balle tace ƴan ubanci suke gwada mata, ko kuwa duk ƙiyayyar mahaifiyar ta ce ta shafe ta har haka. Hannu tasa ta goge hawayen da suka gangaro kan kuncin ta daidai lokacin da maigari ya miƙawa Abu Aulad sadakin ta shikuma ya ajiye mata kan cinyar ta, murya na rawa ta shiga magana "Nagode sosai baba, Allah ya saka da alkhairi ya ƙara girma sedai Ina son ganin su baba habibun game da gado na dake wajen su". "Babu komai salamatu, ke ɗin ai ɗiya ce gare ni, abinda ya faru a baya ma saɓanin fahimta da kuma zugar iyayen ki ne, yanzu bari in aika su zo se ayi batun gadon naki". Ɗaya daga cikin dogaran sa ya aika azo dasu baba Habibu dukan su, ba'a jima ba dogarin ya dawo tare dasu suna bin shi abaya se ƙunƙuni suke na yadda ake shiga rayuwar su kan wata banza can Salame da suka daɗe da tsamewa matsayin jinin su. Gaban maigari suka zube suka yi gaisuwa, salma ya nuna musu bayan ya amsa ya shiga kora musu bayani "Ga Salame nan mijin ta ya kawo ta na mata bayanin auren su da aka ɗaura jiya se kuma gashi tazo da batun gadon ta dake hannun ku tana neman a bata kason ta". Maigari ya ƙarashe yana gyara saɓa hannun babbar rigar jikin sa tare da furzar da tiƙar goran dake bakin sa, ido waje baba Habibu da ƴan uwan sa ke kallon tsaleliyar budurwar da aka nuna musu wai Salame, cikin rashin yarda baba Habibu ya furta sunan ta "Salame". "Na'am baba barka da rana". Ta faɗa tana buɗe idanun ta sosai a kan su dan su san fa yanzu ba da bane da take shakka da tsoran su, cikin sanyin jiki baba iro yai gyara zama dan ƙwayar idon ta kawai ya kalla ya shaida ita ce. "Dama nace gadon baba na dake hannun ku nake buƙata baba dan Ina son yin amfani dashi". "Eh to, gado ko, tabbas kam kamisu ya bar gado sedai yana wajen Adamu ai bani ba". Da sauri baba Adamu da yaji baba Habibu na neman zame wa ya bar shi a ciki ya buɗe baki "Ina ce gona ce kawai a wajena Habibu?". "Ai dama ita nake nufi, am ke Salame sedai fa kiyi haƙuri dan kiwon da ya bari tuni babu su, da su ne mukai ta amfani wajen ciyar dake har zuwa lokacin da kika bar wajen mu dan haka gona dai tana nan ban da ita kuma babu komai". Ya faɗa yana kai da kai gefe cikin rashin gaskiya. Girgiza kai akwai tayi dan tasan ba wani an ciyar da ita an cinye ne kawai babu su yanzu, gonar ma tasan ban da albarkacin yanayin da ya ganta na wadata da kuma waɗanda ke tare da ita da baze bayar ba itama cewa ze yi an siyar an kula da ita. "Allah ya amfana gonar, sedai ina da buƙatar ta ujila zan yi amfani da ita". "Amma ina ce kinji ance tana hannun Adamu, shima amfani yake da ita dan haka sedai kiyi haƙuri, gona na mazaunin taki amma ya riga yayi shuka dan haka se yayi girbi se ki karɓa". Cikin rashin tsoro ko shakka ta dubi baba Habibu dake maganar cikin hatsari da gadara "Zan bar tane sabida a hannun baba Adamu take banda haka bana jin da wani ne ba shuka ba kome yayi se dai ya kwashe ya kai inda yake dashi tun da dai gona mallaki nace". Daga baba Habibu har baba iro tsumu suka yi cikin kunya dan sun san da su take, wato da ba Adamu bane dole a bata a bar ta, lallai yarinyar nan ta goge. Abu Aulad da yaji an kawo matsaya ya miƙe dan tuni yake kallon agogon hannun sa, baya san suyi dare kamar jiya dan a tsarin sa a yau yake son ta tare a gidan su dan ya nuna wa duk wani dake tunanin ce iya juya shi ko iko dashi ƙarya yake, be isa ba kuma be kai ba, anyi a da amma banda yanzu!. "Mungode sosai, ga wannan a siya horo, Allah ya ƙara girma, ku tashi ku tafi ko?". Ya faɗa yana ajiye wa maigari bundle ɗin ɗari bibbiyu, miƙewa tayi tana adjusting pin ɗin mayafin ta da taji ya ɗan matse ta, har bakin mota maigari ya raka su inda su baba Habibu suka zama ƴan kallo, Haisam ne ma yayi tunanin basu ƴan canjika dan shi uban gayya ko kallo biyu basu samu daga gare shi ba. Tun jiya mutuncin su ya zube tsaf a idanun sa saboda abinda suka yi, me ɗan daman cikin su ne baba Adamu dan shine kawai ya samu gaisuwa daga gare shi. Haisam na buɗe bayan motar Ibty ta fito tana mutsittsika ido tare da tura baki gaba cikin son fashewa da kukan rashin ganin Mamman ta, da sauri Salma ta riƙo hannun ta tare da jawo ta gaban ta. Duƙawa tayi zuwa tsayin yarinyar ta cire mata hannun ta dake kan fuskar ta, ɗaga mata gira tayi tare da jan kumatunta tana sakin mata murmushi itama yarinyar ta maida mata sannan ta shige jikin ta tana sakin ajiyar zuciya, seda ta tabbatar ta dawo daidai sannan ta kama hannun ta ta buɗe gaban motar zata shiga baba maigari dake kallon su ya magantu "Masha Allah, tubarkallah, hala wannan ɗaya daga cikin yaran ne salamatu?". "Eh baba, Hassana ce Ussaina na bacci bata tashi ba". "Allah Sarkin hikima da buwaya, tubarkallah yarinya kyakkyawa kamar ƴar turawa, Allah ya raya yayi musu Albarka, Allahu Akbar da girma yake". Da Ameen ta amsa masa tare da shigewa motar dan shima tasan borin kunya ne ya ke yi na abinda yayi mata lokacin da tafi buƙatar taimakon su shiyasa duk wani rawar ƙafar sa be ɗaɗata da ƙasa ba. Numfashi ta sauke na samun relief lokacin da motar su ta fara tafiya kan burjin har ƙasar dake garin, tasbih tare da godiya kawai take yi cikin ranta wa Ubangiji da ya canja mata rayuwa daga wata mara ma'ana zuwa wadda take ciki yanzu. Nauyi taji ƙirjin ta yayi mata lokacin da ta tuna cewa yanzu fa ita ɗin matar aure ce, matar Abdallah Abdulsalam Gamji shugaban fitacaccen kuma shahararren kamfanin A.A Gamji. Bata san wace irin rayuwa ce kuma ke jiran ta nan gaba ba a gidan auren ta sedai tana fata koma wace irin ce ta zo mata da sauƙi, akasin haka kuma Allah ya bata wuyan ɗauka ya kuma yi riƙo da hannun ta wajen ganin ta samu mafita akan dukkan matsalar da zata tunkaro ta. Ta daɗe da sanin ita rayuwar gaba ɗaya jarrabawa ce, gwaji ce da bawa ba zai daina samun shi ba har se lokacin da rai yayi bankwana da gangar jiki wadda ranar ce ba wanda ya sani tunda ita mutuwa ba sallama take ba haka kuma ba wai notice take bayarwa ba bakuna allo ne da ake rubuta jadawalin sunayen mutanen da zasu tafi yau, gobe jibi da ma kullum ba. Cikin wannan tunanin suka shigo garin Gamji, tafiyar ba kamar ta ɗazu ba yanzu kam hira ce suke yi shida Haisam jefi jefi yayinda ita tayi nisa cikin duniyar tunanin da take yi tana daga zaune rungume da Ibty a jikin ta. Haisam ɗin suka fara saukewa inda suka yi sallama da abokin nasa kuma shugaban sa kan se sun yi waya yayinda cikin nutsuwa ya cigaba da driving motar har zuwa gaban gidan su da bata san yaushe ya sani ba kuma ya wa ya sanar dashi ba. Parking yayi a ƙofar gidan, ganin yadda ya kai kai gefe yasa ta shanye mamakin ta ta buɗe ƙofa Ibty ta fita zuwa cikin gidan ita kuma ta zaga baya ta ɗau Ifty dake bacci har lokacin ta kai ciki wajen Hajiya dan bata samu zarafin tsayawa buɗe ƙofar ɗakin su ba ta koma gare shi. Gefen ƙofar da ta fita ta tsaya tare da duƙar da kai ƙasa "Mungode sosai Allah ya huta gajiya, a gaida gida Allah ya tashe mu lafiya". "Shigo". Kallon shi tayi tana sake nanata kalmar shigo ɗin da yace, to ta shiga tayi me bayan yanzun nan suka dawo tare dashi?. Ganin kallon da ya ɗago ya jefa mata yasa bata san sanda ta kai zaune kan kujerar motar ba sedai ƙafafun ta na waje...............................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment, share and patronize fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 08 [ 11/30/2022 3:14 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable. FREE PAGE 008 _________________________📖 Gaban tanƙamemen gare ɗin gidan ya tsaya yayi horn, cikin sakanni gate ɗin ya fara zugewa da kan shi har ya gama ya tura hancin motar cikin babbar harabar gidan. Daga kallo ɗaya in kayi wa cikin gidan zaka san gidan family ne ma'ana gida ne da ya kasu kashi kashi (parts-parts). A lot ya kashe motar ya fita cikin cikakken takun sa da yake da ƙarfi ya nufi sashen mahaifin sa, a yanzu base anjima ba yake san isar da saƙon sa gare shi. Yana yin sallama ya ɗaya labulen ƙofar tare da shiga falon, zaune kan kyakkyawar shimfiɗar da ta kewaye falon gaba ɗaya yake zaune tare da dattijuwar matar sa, dattijo ne da kallo ɗaya zaka masa kasan shekaru sun tura amma ba alamar yanƙwanewa ko wani rashin ƙarfi tattare da shi. Zama yayi gaban sa bayan ya tanƙwashe ƙafafun sa ya gaisar dashi cike da ladabi sannan ya ɗora da batun da ya kawo shi batare da ya dubi tsohuwar dake zaune ko ya nuna ya san da ita ba. "Na samu matar da nake son aura har ma mun gama daidaitawa, nasan an kawo maka wata jarida game da ni to yarinyar jiki ce zan aura ɗin, sunan ta Salma, magabatan ta na garin BA MUNI bana san a ɗau lokaci sosai ne, ba budurwa bace ta taɓa aure da yaran ta biyu". Tun da ya fara magana wani irin firgicin ya wanzu kan fuskar matar har hannun ta ya fara ɓari wanda se da ta jimƙe shi tukunna ya tsaya, da sauri ta maida duban ta ga mijin ta dan jin me zece "Amma ai ka bari ayi bincike a kan ta ko, banda rashin hankali irin naka Abu Aulad ka rasa matar da zaka aura se wadda hotunan ta ya gama zaga gari da sunan ɓatanci, to sam ban lamun ta ba ma, hakan ba ze taɓa yiwuwa ba, ga nan babar ka ta daɗe da sama maka mata tsoron halin ka yasa ta kasa faɗa maka amma ni yanzu na sanar da kai kuma sati biyu masu zuwa za'a yi auren". Wannan karon gaba ɗaya ya ɗago yana kallon mahaifin sa cikin yanayin ba fa zan yarda ba "Sam hakan baze yiwu ba Baba, a wancan karon ka kawo min nafisa ban yi musu ba amma a wannan karon kam bana jin akwai wanda ze dakatar da ni, bincike akan yarinya ni duk na gama shi, hotuna kuma nawa da nata ne sukai yawo dan haka ba matsala mata da miji dan sun zaga gari an san su, batu na wata ƴa kuwa bani da uwa balle ta zaɓar min, infact babu wani mahaluƙi da ya isa ya min auren da bana so a wannan karon, ka samin albarka dan a gobe zan je in auro ta Dan addini ya bani damar nemawa kaina aure kasancewa ta namiji, se an jima". Yana gama bayanin sa ya miƙe tare da ficewa da sassarfa, yana fasa bari nan da sati ɗaya tun da ya fahimci abin iskanci ne, a gobe ze je ya auro ta ya ga wanda ya isa yace ya sau ta in akwai shi. Dan anga yana yin shiru se a dinga maida shi wani soko ko wanda be san kan sa ba, to an shigo da'irar da ba ragayya tsakanin sa da kowa yanzu, ze fubi ifon kowane mahaluƙi da yanemi shiga hanyar sa sannan ya kawar dashi. Waya ya ɗauka ya shiga kiran Haisam da tuni ya wuce gida tun lokacin da ya tabbatar gida ya nufa, ringing bitu ya ɗaga "Ka fito bakin titi gani nan zuwa, ina nufin a ƙafa". Ya faɗa batare da ya jira jin me Haisam ɗin zece ba haka be tsaya sauraren me ze faɗa ba bayan ya gama bayanin sa ya kashe wayar. Kamar yadda ya faɗa a titin ya same shi, gefen sa Haisam ya shiga yayi wa mota wuta batare da ya sanar dashi ina suka nufa ba, shima tun da yaga yanayin sa se be tambaya ba. Gudu ya dinga tsugawa a titin har suka fara fita gari, be tsaya ba seda aka kira sallar Azahar suna idarwa kuma suka sake ɗaukar hanya. Ƙarfe biyar sannan suka shiga ƙauye BA MUNI, kai tsaye gidan me gari ya tambaya aka nuna masa ya wuce, suna zuwa suka fita sannan ya kalli Haisam "Auren yarinyar can muka zo nema, gobe zamu dawo a ɗaura aure". Baki sake Haisam ya bishi da kallo jin wani sabon tsari kafin kuma ya bi bayan shi ganin har ya kusa shigewa fadar me garin. Kan shimfiɗun wajen suka zauna maigari kuwa se rawar jiki yake yaga ƴan gayu cikin kaya masu kai da walƙiya, cikin ƙanƙanin lokaci ya sanar dashi abinda ke tafe dashi aikuwa da sauri maigari ya tashi ɗan aike aje a taho da su kawu iro. Ba'a daɗe ba se gasu sun bayyana gaban maigari kowanne futu futu dan yawancin su dawowar su kenan daga gonaki da wajen aikin ƙira. Baɓata lokaci maigari ya sanar dasu dalilin kiran, baba Habibu yayi tsalle yace shi ba shi a cikin maganar yarinyar da ya zaɓi shegun ƴaƴan ta akan su haka ma baba iro. Baba Adamu ne yayi sassaucin cewa sun bayar a ɗaura yanzu in har da gaske yake kawai dan shima ba ze yadda a Kuma tado shi daga wajen sana'ar sa ba gobe kan batun auren wata can wai Salame. Ba ɓata lokaci kuwa aka ɗaura auren Salma Khamees da Abdallah Abdulsalam Gamji bisa sadaki dubu hamsin da ya bayar lakadan ba ajalan ba a fadar maigari. Basu kuma jiran komai ba suka juyo da ɗimbin goron da suka siya a garin na ɗaurin aure, basu kai gida ba se wajejen goman dare, Haisam ya fara saukewa kafin yayi masa godiya ya wuce gida shima. ********** "Ina sam ba zan bari haka ya yiwu ba wallahi, taya ya yaran nan ze shammace ni haka bayan ina nan ina shirin aura masa shuraiha, kai dole ma ita ce aura dan ba zan yi sanyar ya ɗauko wata a waje ba, nasan duk ma wannan fuffukar ta banza ce dan haka bari gobe tayi zan yi wa tufkar hanci, auren nan da sati za'a yi inga ta tsiya". Hajiya Babba ta faɗa wa kanta cikin tabbatar da abinda zata iya taba kaiwa zaune cikin sauke ajiyar numfashin samo mafita da tayi, ta daɗe tana zaune ƙafarta ɗaya kan ɗaya tana karkaɗawa ciki sake zurfafa tunani har dare yaja kafin ta haƙura ta kwanta bayan ta sake maimata shawarwarin da ƴaƴan ta suka babbata ta ɗau na ɗauka ta watsar da na watsarwa. ******** "Anna da zafi zafi fa akan daki ƙarfe ya kamata gobe kije ki sami baba ki Masa magana kan meze hana na maye ɗakin yaya ta, kinga wancan karon shi ya Abdu yace a bar zancen tukunna amma yanzu ai yaci ace a tada maganar, shekara takwas za'a shiga ta tara da muke, kar mu tsaya garin kallon ruwa kwaɗo yayi mana ƙafa". "Bari haka za'a yi, shi Abdallahn zan fara kira nan nayi masa kuka ta yarda baze Musa min ba kinga da kan sa ma se ya kai zancen naku can wajen baban nasa ta yadda ba wanda ze zargi ni nake son tusa ƙi ko". "Sosai ma kuwa Anna, wannan idea ɗin tayi, bari in je in kwanta Allah ya kaimu goben da rai da lafiya". Da Ameen Anna ta amsa mata yayinda ta shige ɗakin kwanan ta dake part ɗin marigayiya yayar ta nafisa da suka gaje tun bayan mutuwar ta. A can kuwa baiwar Allah salma ta tasa ƴaƴan ta a gaba tana kallon yadda suke bacci hankali kwance ba abinda ke damun sa yayinda ita take cikin damuwa, damuwar da bata san dalilin ta ba wadda haka kawai take samun faɗuwar gaba duk ta tuno boss ɗin ta da auren da yake batun zasu yi, aure kuma kwana kusa in less than two weeks abinda bata taɓa shiryawa ba balle ta zauna tsara yadda ze kasance. Alwala ta ɗaura ta shimfiɗa sallaya ta shiga nafiloli tana kaiwa Allah kukan ta kan ya shige mata gaba, seda ta gaji kafin ta zauna ta ɗau ƙur'ani ta shiga karatu har seda ta ji bacci yaci ƙarfin ta kafin ta rufe tayi addu'a ta kwanta. Safiyar Laraba yazo wa mutane da dama cikin wani irin yanayi, ga salma wani irin nauyi take ji a ƙirjin ta da kanta kamar wadda ta aza dutsen dala a kanta, yaran kansu da ƙyar ta iya shirya su dan har se da suka makara yau, jiki ba ƙwari ta rakasu ajin su ta koma ta tare wani napep ɗin zuwa wajen aikin ta. Ko da taje ta tabbatar boss ya rigata zuwa amma yau bata ji wannan fargabar ba illa wani nauyi da ta tuno sunan sa da abinda ke ƙoƙarin shiga tsakanin su. Seda ta ajiye jakar ta da files ɗin hannun ta ta gyara wanda zata kai masa Sannan ta ƙwanƙwasa ƙofar, amsa mata da akayi tareda bata izinin shiga ya sa ta buɗe ƙofar ta shiga ta ƙara sa gaban table ɗin sa ta ajiye masa files ɗin duk da bata gan shi a kan kujerar sa ba, juya tayi da zummar fita amma ya dakatar da ita daga cikin inner office ɗin sa kan ta zauna ta jira shi, zama tayi ta shiga bin office ɗin da kallo a hankali cikin admiration, office ɗin ya daɗe yana birge ta ba tun ba yau ba yadda ba'a cika masa shirgi da hauragiya ba amma komai a tsare fes wajen da ya kamata. Cikin haka ta sauke duban ta kan ƙofar inner office ɗin dake buɗe ko kafin ta kai ga ɗauke idon ta tuni ya bayyana cikin shadda riga da wando ɗinkin tazarce sedai maɓallayen wuyan a buɗe suke yana gyara su, haɗa idon da suka yi yasa ta maza ta sauke nata gaban ta na faɗuwa, iya zaman ta a Companyn zata iya rantsewa yau ne ƙwayar idon su ta shiga cikin na juna dan indai tana gaban sa kanta ya kan kasance a ƙasa ne har se sanda ta bar wajen sa shiyasa ba zata iya cewa ga cikakkiyar ainahin kamannin sa ba dan kwarjinin sa kaɗai kan hana mutum iya kallon sa fuska da fuska. Idon sa a kanta ya shiga takawa har ya ƙarasa ya ja kujerar opposite ɗin ta ya zauna tare da ɗaukar wayar sa ya shiga kiran Haisam "Kasan tafiyar da zamu yi da tsawo amma kabar mutane na jira?". Yana gama saurarar abinda yace ta can ɓangaren ya kashe wayar tare da ajiyewa ya shiga gyara agogon hannun sa, files ɗin ta jawo ta shiga yi masa bayani cikin mamakin yau kam be da niyyar zama kan kujerar sa sedai tuni ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu se kuwa taja bakin ta ta tsuke. Ƙwanƙwasa ƙofa masinjan sa yayi ya bashi izinin shigowa, leda ya ajiye masa cike da girmamawa sannan ya juya ya fita, ledar ya jawo ya buɗe tare da kallon kayan ciki sannan ya tura mata gaban ta "Ki shiga ciki ki canja wannan uniform ɗin dan ba zan iya tafiya dake dasu a jikin ki ba". Binsa tayi da kallo har ya fice kafin ta sauke ajiyar zuciya, ta canja kaya to akan me, ina ruwan sa da kayan jikin ta ko basu ne suka bata a matsayin kayan aikin ta ba da yau ze kawo mata wani sabon sanaben ta canja. Haka dole ba dan taso ba ta ɗau ledar tare da shiga toilet ɗin sa ta cire kayan jikin ta ta maida wannan, doguwar riga ce ta mata se mayafin ta, kayan coffee and milk se suka yi mata kyau sosai dan tana da hasken ta daidai gwargwado. Cikin ledar ta fito tana ninke uniform ɗin ta zuba su ta sake neman kujerar da ta tashi ta zauna "Mrs Gamji bismilla ko". Haisam ya faɗa daga ƙofa bayan ya buɗe, da rashin fahimta take kallon sa jin sunan da ya kiraye ta dashi yau "Muje salma, inda zamu ba nan kusa bane". Jiki ba laka ta miƙe ta bi bayan shi dan har ya fita, Allah ya sani bata san zuwa ko ina da su tunda ba muharraman ta bane haka ba wani cikakken sani tayi musu ba banda na wajen aiki yanzu kuwa mutum abin tsoro ne bare ma ita da bata da galihu ba wanda ze tdaya mata in wani abu ya same ta. Gaban mota Haisam ya buɗe mata, cikin ɗarɗar ta shiga tana me karanto addu'a a bakin ta, wani irin sanyi ne ya ratsa fatar jikin ta na Ac dake tashi yayinda hancin ta ya shaƙo mata daddaɗan ƙamshin turaren motar da na jikin sa da suka gaurayu suka bada wani launi na ƙamshi daban. Rufe murfin Haisam yayi ya koma ya buɗe bayan motar ya shiga, tada motar Abu Aulad yayi suka fita daga Companyn yayinda ma'aikata ke aikin kallon su sedai shi kam ko mutum ɗaya be nuna yasan da zaman shi ba balle ya kalle shi. "Garin ku fa zamu je Madam". Da sauri ta shiga ta kalli Haisam da yayi maganar kafin ta juyo ta kalli Abu Aulad da idanun sa ke bisa titi, bakin ta na ɗan rawa ta furta "Taraba, suna school, ba wanda ze je ɗaukan su". "Ba ze yiwu muje mu dawo kafin su tashi ba?". Da sauri ta girgiza kanta, " ƙarfe huɗu suke tashi". "Ze yiwu muje har mu dawo". Da sauri ta shiga girgiza kanta "A'a nidai mu tsaya a ɗauke su, ba zan iya tafiya in bar su ba, pleaaseeee". Ta faɗa wannan karon directing to Abu Aulad "Ya sunan Makarantar?". "Star light Academy". Be Kuma cewa komai ba ya saki hanyar da yake kai ya ɗauki wadda zata kai shi makarantar da ta faɗa. Har ciki ya shigar da motar sannan ta fita zuwa wajen principal, uzuri ta bayar kan dalilin da yasa za'a ɗauki yaran, be Musa ba ya yarje mata dan yaran ta are one of their daily and punctual students da basa fashi sake da ƙwaƙƙwaran dalili. Rungume su tayi a tare lokacin da suka fito daga aji kafin ta ja hannun su zuwa wajen motar suna ta yi mata surutu. Tun da suka tunkaro su ya kafe yaran da ido cike da sha'awa da muradi, sha'awar dama nasa ne, muradun samun kamar su ya cike ransa. Buɗe musu bayan motar tayi suka shiga a hankali sannan ta sa musu lunch box ɗin su, gaishe da Haisam suka yi inda suka kira shi da uncle batare da sun lura da Abu Aulad ba se da ta nuna musu shi "Babies, baku gaisar da other uncle ba". "Yes, baku gaishe da daddy ba". Haisam ya gyara mata da sauri "Mamman wai daddy ne da gaske?". Gyaɗa musu Kai tayi a sanyaye dan bata so yace daddy ba, in suka girma suka san ba daddyn su ne ba fa. Da sauri Ifty da tafi ƙiriniya dan itace Ussaina ta tsallake ta shiga gaba tare da faɗawa kan shi tana tsallen kiran Daddy "Daddy dama mamma tace Mana kayi tafiya ne, daddy yanzu ka dawo kenan?". Da murmushi a fuskar sa ya gyaɗa mata kai tare da shafa fuskar ta cike da shauƙi, juyawa yayi ga ibtisam da tayi tsaye ya ruƙo ta itama ya zaunar kan sa, wasa wasa seda suka ɓata kusan 30 minutes sannan suka tafi bayan yaran sun koma baya kusa da Haisam ita kuma ta koma mazaunin ta.....................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment and share fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 10 [ 12/1/2022 1:07 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                      FREE PAGE 010 LAST FREE PAGE!!! This is the last free page, make your payment and continue enjoying the movies else you'll be left behind 😜! ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card to 09013101854, note VTU is not acceptable. ________________________📖 Shiru na ƴan wasu sakanni kafin ya motsa bakin sa "Na so ki tare yau sedai baze yiwu ba tunda munyi dare but be ready gobe da safe insha Allah zan zo mu wuce". Tsrewa, yau, gobe da safe, wucewa, gaba ɗaya bata gane ma'anar wannan kalaman ba. It may sound funny ko kuma a ɗauka rainin hankali ne but dagaske a wannan lokacin manta ma'anar su tayi, sam bata gane me yake nufi ba haka yasa tayi saurin yin magana "Wucewa, gobe, zuwa ina?". Seda ya kalle ta sosai kafin ya kau da kai trying not to look at her face again, tun lokacin da ya ga ƙwayar idon ta a ƙauyen su yaji yana sha'awar sake gani, so yake ya tantance wane kala ne da eyeballs ɗin ta tunda ya tabbatar ba baƙa bace sedai baya san ta ɗau hakan da wata manufa shiyasa yake kauda Kai "Nace ki tattara abubuwan da kuke buƙata na iya suttura zaki koma gidan auren ki gobe insha Allah". Zuwa yanzu kam she's speechless dan ba zata ce bata gane me kuma yake nufi ba yanzu tunda gwari gwari yayi mata, ita kam ta rasa a wane layi zata ajiye wannan auren nata, da neman auren da ɗaurawa duk cikin kwana ɗaya zuwa biyu aka yi su, yanzu kuna ga tariya, a al'adar malam bahaushe dangin amarya kan haɗu su rakata gidan auren ta cikin soyayya da ƙauna amma ita gata ana batun tariyar daga ita se mijin ta da ƴaƴan ta, lallai auren ta wani iko ne na Ubangiji. A hankali ta saci kallon sa cikin son furta abinda take so sedai bata san ya akayi ta tsinci harshen ta da furta abinda ba shi ne a zuciyar ta ba "Allah yasa zamu ga goben da rai da lafiya". Ameen ya faɗa daga nan kuma suka cigaba da zaman shiru, ita bata ce komai ba shi ma haka, tsayin lokaci har ta gaji da zaman ta gyara amma bashi da niyyar cewa komai "Ki taso yaran mu tafi". "Mu tafi, ina kenan bayan dare kuma yayi, its almost ten fa". "And me kike nufi da zaman da kike yi a nan?". Wani irin tuƙuƙin takaici ne ya cika mata maƙogaro, daga ɗazu zuwa yanzu ta fahimci mutumin nan wani bahago ne na daban, ko saboda ba wani kusanci ne tsakanin su na daban ba a office maybe shiyasa bata San hakan ba tuntuni. Bata ce komai ba ta fita daga motar tare da maida murfin ta rufe masa ta wucewar ta cikin gida tana gunguni ita kaɗai. Seda ya ga shigar ta gidan sannan ya tashi motar ya fita daga layin cike da sanyin jikin da gajiya ta haifar masa, wannan dogon tuƙin da yayi jiya da yau sam be saba masa ba shiyasa gaba ɗaya jikin sa yayi masa nauyi. Kulle motar yayi ya fita batare da ya kula ganin ta da yayi tsaye ba, da sauri tabi bayan sa har tana haɗawa da gudu saboda takunsa irin na cikakkun maza ne masu isasshiyar lafiya "Yaya Abdu, ya Abdu". Yana jin ya tsaf amma yayi mata banza hakan yasa ta kuma kwasa da gudu tasha gaban sa lamarin da ya tilasta masa tsayuwar dole sedai tuni ya sake ɗin ke fuska tsaf kamar wanda be taɓa sanin wani abu wai shi annurin dariya ko murmushi ba a duniya. "Dama Anna ce ke neman ka, tuntuni nake kiran wayar ka in faɗa maka yaƙi shiga, gashi ita kuma se kuka take da kiran sunan yaya nafi wuni guda yau taƙi cin komai". "Kije ki faɗawa baba". "Zuwa yanzu ya kwanta yaya Abdu, Please ka taimaka kazo muje kayi mata magana ko zata ji, na bata baki amma taki saurara ta". Sam baya son kallon ta sabida irin shigar dake jikin ta, duk da kasancewar dare ne amma gidan nasu tarwai yake da haske da ko allura ce ta faɗi tsaf mutum ze tsugunna ya ɗau abar sa ya tashi. Tun ba yau ba yasan ita da yayar ta nafisa Allah ya ji ƙan rai kamar gabas da yamma ne, sam bata inda suka yi kamanceceniya se ko ta fuska da kuma jini shiyasa ko da sam be sake mata fuska balle ta samu damar kawo masa raini bare kuma yanzu da yake jin kowa ma daidai yake dashi. "Kije zan zo in nayi wanka, nayi gumi da yawa I can't go to her a haka". Ya faɗa yana wuce ta cikin tafiyar nan tasa me cike da karfi da isa, bin bayan sa tayi da kallo cike da maɗaukakin shauƙi, lumshe ido tayi tare da rungume hannuwan a ƙirji inda take ji kamar shine ta rungume, wannan maganar da ya mata ji take kamar an mata albishir da shiga aljanna. Tun yayar ta na da rai take so da ƙaunar yaya Abdu sedai tayi ta ƙoƙarin dannewa, yanzu kuwa da babu yayar ta bata tunanin akwai abinda ze tsayar da ita kuma. A saɗaɗe ta juya zuwa part ɗin su, bakin ƙofa ta tarar da anna tsaye, da sauri ta riƙo hannun ta suka ƙara sa ciki kafin ta dube ta "Yaya, cewa yai baze zo ba?". "Yace zezo amma se yayi wanka, dawowar sa kenan baze iya zuwa gare ki a haka ba". "Kai masha Allah bari maza in shafa rob ɗin nan a ido na ɗan suyi ja su dinga hawaye, insha Allah buƙatar mu zata biya bari ki gani". Tsohuwa Anna ta faɗa tana murza Rob a fuskar ta, duk yadda idanun ta ke hawaye be sa ta fasa ba se da ta saka sosai ta yadda in ka kalle ta zaka ce ta daɗe tana kuka dan yadda fuskar ta tayi jajir kasancewar ta fara haka ma idanun ta suka yi ja suka tasa. A can ɓangaren Hajiya Babba kuwa da sauri shuraiha dake tsaye jikin window riƙe da curtains tana kallon abinda ke faruwa tsakanin Abu Aulad da Nuriyya ta saki uban ashariya "Kan uba". Ta faɗa da sauri tana sakin curtains ɗin, bata tsaya wata wata ba ta zura bedroom slippers ɗin ta tayi waje without minding cewa kayan bacci ne a jikin ta ba, burin ta a lokacin shine ta kai gare su taji me suke tattaunawa a wannan tsohon daren. Baza tayi sanyar da wata can daban zata ƙwace mata Abdallah ba bayan an gama kwaɗaita mata shi tare da lasa mata zuma a baki yanzu kuma a ce za'a janye, ina ba zata yarda ba. Sedai kash ko kafin ta kai ga fita daga part ɗin su tuni ya shige nasa part ɗin ita kuma Nuriyya ta koma nasu hakan yasa ko da ta fito compound ɗin bata tadda kowa ba se ma'aikata dake ɗan kai kawo dan wasun su ma tuni sun nemi makwanci. Haka ta koma part ɗin nasu tana cizon yatsa, taso taji me waccan karuwar ke faɗa masa wanda har ya tsaya saurara haka sedai kash bata samu ji ba, ya zama dole ta tunzura Hajiya Babba ayi ayi ai bikin su ko hankalin ta ya kwanta, daga lokacin da ta sami wannan damar a lokacin ita kanta Hajiya babbar zata raina kanta dan kallon ta kawai take itama da tata tsarin da buƙatar akan Abdallah ɗin. A hankali yake rage kayan jikin sa cike da gajiya, wanka yake buƙata yake kusan sanyi dan yadda yake jin jikin sa na ƙaiƙayi shine kawai abinda se yi yaji sauƙi. Singlet ɗin jikin sa yake ƙoƙarin cirewa se kuma ya fasa sanadin hango inuwa da yayi jikin labulen sa alamun akwai wani laɓe a ta wajen. Cikin nutsuwa ya shiga takawa har ya kai wajen yasa hannu ya yaye curtains ɗin da suka rufe tagar, tsaye take cikin shaiɗanun kayan da dasu da babu a jikin ta basu da wani banbanci, suna haɗa ido ta sake masa wani arnen murmushi cike da barikanci kafin cikin kwarkwasa ta shiga lauya jikin ta tana magana da wata seducive voice "Sannu da zuwa Abu Aulad, ga dukkan alamu ka gaji, don't mind I can takeaway all your stresses, yanzu dai muje kayi wanka ko super man?". Kamarw anda garwashin wuta ya taɓa haka yayi watsi da hannun da takai jikin sa, ya rabbal alameen be san ya zai yi da rayuwar sa a cikin wannan gidan da a wajen sa gara kabari dashi ba. Wani irin birkitaccen mafi ya watsa mata da yasa ta yin katantanwa ta faɗi can gefe kanta ya bugu da jikin Centre table ɗin dake falon, cikin wata irin zuciya da ta ciwo shi ya bita yasa ƙafa ta taka sangalalin hannun ta har se da yayi ƙarar dake shaida alamar in har bata sami fracture ba to tabbas ƙashin nan ya fita daga bigiren sa. Wani wahalallen ihu ta saki da be wani fita da karfi ba saboda tsabar wahala yasa a take Muryar ta ya shaƙe, cikin wani dakusasshen Muryar da ɓacin rai ya haifar masa ya shiga yi mata concrete warning "This is the first and last time da zan kuma ganin ki a part ɗina, na rantse da Ubangijin da ya busa min rai da second time na kuma ganin ki zan iya ɗaukar ranki dan ko banza an rage mugun iri, annoba kuma jinin shaiɗan, before the count of three ki fice min ɗaga ɗaki in ba haka ba wallahi rataye kibzan yi jikin fanka, fitsararriyar fasiƙa kawai mara kunya da tsoron Allah". Ai ko kafin ya gama bayanin sa tuni ta tarkata hannun ta tayi waje da mugun sauri dan a yadda ta gan shi da kuma rashin imanin da ya gwada mata ta tabbatar ze iya rataye tan kamar yadda ya faɗa. Da numfarfashi da komai takai kanta part ɗin ta zube kan kujera tana maida numfashi, wani irin zufa ne ke keto mata na wahala da azabar da take sha a jikin ta, bata taɓa sanin haka zafin karaya yake ba se yau. Ƙwalla take zubar wa tana bin hannun da kallo yayinda cikin ranta take shan mugayen alwashi kala kala a kan shi, tun da ta riga ta ɗora ido a kan shi takuma kwaɗaitu da shi ta rantse ita kuma se ta same shi, in kuwa ba haka ba to tabbas sedai ayi biyu babu uku ba ko ɗaya ma'ana indai ba zata same shi b ato sedai kowace mace ta rasa. Da sauri ta runtse idon ta lokacin da ta auno shi a idanun ta tare da wata mace, inaaa, ba'a haifi macen da zata amfane shi ba, ada dai tayi wannan imanin amma a yanzu zata iya yin komai in tace komai tana nufin komai wajen ganin ta saka kyakkyawar barrier tsakanin sa da duk wata ƴa mace kowace ita kuwa. Ranar haka ta kwanan cikin azaba da raɗaɗin zuci da na jiki, ga dai jinya ya kwantar da ita kuma wai batare da ya bari ta amfanu da komai daga gare shi ba, ita da ta samu abinda taje nema to da sauki ba karya ta ba ko kashe ta yayi ba zata damu ba tunda ta cika burin ta. A ɓangaren Abu Aulad ma haka ya kwana a zaune cikin wani irin yanayin da baze fassaru ba, be san da wane suna ze Kira gidan da yake ciki ba haka be san da wane suna ze kirayi mutanen cikin sa ba, be taɓa sanin bawa kan zaɓi mutuwa kan rayuwar sa ba se a kan shi, da ace kisan kai ba haram bane a musulunci da tuni ya daɗe da sheƙe kan sa ya huta. Tun tasowar sa be san wani abu wai shi farin ciki ba, kullum cikin baƙin ciki da damuwa yake tun fara wayo sa har kawo yanzu da yake shekarun sa na cikakken namiji mai ji da sabon jini da ƙuruciya. Rayuwar sa a hagunce ta faro kuma har kawo yanzu a haka take, be san se yaushe ne ze samu daidaito na rai, ruhi da rayuwa ba balle har ya samu salama, a duk sanda yaga mutane na rayuwa suna dariya da nishaɗi ya kan tsinci kansa da ayyana dama shine, so da yawa yasha kusan yin saɓo in ya zauna tunani dan ya kan dinga aiyana me yayi wa Allah da yasa ƙaddarar jarabawar tazo a haka, me yasa ba wata daban ba. Kiran sallar asuba da ake yi ne yasa shi miƙewa yana dafe kan sa dake sara masa ya shiga toilet, daga tsayen da yake ya sakarwa kansa ruwa masu sanyi sanye da wandon shaddar da singlet ɗin batare da ya cire ba, tsayin lokaci Sannan ya gabatar da wanka ya ɗaura alwala ya fito. Jallabiya ya zura a jikin sa tare da ɗaukar tasbah ɗin sa ya wuce masallaci, seda aka idar da sallah har gari yayi haske kafin ya taho gida. Jiri yake gani dan rabon shi da abinci tun na safen jiya kafin su tafi ƙauye ga kuma rashin bacci sedai kasancewar tsayayyen namiji ba wanda ze fahimci hakan se wanda yayi masa sani na sosai. Wata jallabiyar ya canja kawai ya ɗau key ɗin motar sa zuwa gidan su, ɗauko ta ze yi dan se yayi hakan hankalin sa ne kwnata, mutanen gidan su are so cunning, gwara tun kafin su farga yayi outsmarting ɗin su ya shayar dasu mamaki ya kuma basu tsoro ba kuma ta kowace hanya ba se ta kawo macen da ya nema wa kan sa auren ta cikin gidan. Ya sani in da mace a tare dashi abubuwa da yawa zasu masa sauƙi sedai matsalar shine shin itama irin su ce, wane assurance yake dashi na ba zata zama kamar su ba, shin in aka mata tayi da zunzurutun kudi ko matsayi zata karɓa ko kuwa?!. Wannan sune tarin abubuwan da tuntuni suke hana shi aure sedai a yanzu da yayi ba wai ze saki jiki da ita bane, hasalima auren su na da wa'adin da ya ɗibar masa wanda yana cika ze sauta, zaman sa shi kaɗai ya fiye masa dan be yarda da kowa ba baya kuma jin ze yarda ɗin. Yaro ya samu ya aika gidan, tana cikin sawa Ifty rigar school ta jiyo Muryar yaron na faɗin aiken da aka turo shi "Wai salma ta fito inji Abdallah". Sedai rigar ta kubce ta faɗi daga hannun ta saboda yadda zuciyar ta ta doka da jin sunan sa, hannun ta na rawa ta sake ɗaukar rigar ta shiga kici kicin sa mata sedai ta kasa saboda ruɗewar da tayi, Hajiya ce ta amsawa yaron da gata nan fitowa saboda jiya ta zauna tayi mata bayanin komai dan kamar mahaifiyar haka ta ɗauki Hajiya saboda ba ƙaramin taimako tayi mata ba a rayuwar ta. Ɗakin Hajiya ta shigo ta karɓi shirya Ifty dan tuni ta gana da Ibty "Je ki bashi uzuri daga nan ki nemo yara su fara fitar miki da jakunkunan, in an kwana biyu insha Allah zan zo in ga mazaunin ki, tashi kije". Jiki ba laka ta fita, zaune cikin motar ta same shi ƙafar sa duka biyu a waje ya lumshe idanun sa tare da jingina kan sa da makarin kujerar, seda ta tattaro duk dauriyar dake gare ta kafin ta iya gaida shi "Barkada safiya". Saukar Muryar ta yasa ya buɗe idon sa, kallo ɗaya yayi mata ya kau da kai tare da maida ƙafafun sa cikin motar ya fara ƙoƙarin kunna ta "Kayi haƙuri Ban ƙara sa shirya Ifty ba amma yanzun nan zamu ƙarasa, Bari in Sami yaro ya fitar min da jakunkunan". Fasa kunna motar yayi ya koma ya kwanta kamar ɗazu ita kuma ta matsa ta sami wani almajiri suka koma ciki tare, ko da ta shiga tuni Hajiya ta gama shirya Ifty tare da haɗa musu launch box ɗin su, manyan jakunkunan kayan su dake shaƙe ta fara jawowa tana fitarwa tsakar gida almajirin na fita dasu har suka gama, kallon ɗakin take cike da matsanancin kewar sa da zata yi kafin kuma ta maida kallon ta kan Hajiya, matar da tayi mata halaccin da har abada ba zata manta ba, a rayuwa da ita da bana Husaila sun mata abinda in har ta manta to ita ɗin butulu ce cikakiya. Nasiha sosai Hajiya ta yi mata da har tasa ta kuka ba dan komai ba se dan kewar mahaifiyar ta da kakarta da ta taso mata, ta sani da suna nan su zasu yi mata wannan nasihar. Haka Hajiya ta rakata har mota, ko da suka je tuni ya zuba jakunkunan a booth ɗin motar sa ita kawai yake jira. Duk yadda yake moody be san lokacin da ya saki fuska ba da Ifty ta ƙarasa tana ɗane shi Ibty kuma na gaida shi, haka ya ɗauke su duk biyu ya riƙe yana kallon su cike da shauƙi yana sauraren shirmensu har Hajiya ta gama mata nasihar da zata yi suka idasa bakin motar, har ƙasa ya tsugunna ya gaida Hajiya abinda yayi salma matuƙar daɗi a rai. Hala suka ɗau hanya zuwa gidan da bata sani ba tana cike da kewar rabuwa da Hajiya da ragowar ƴan uwan zaman hayar ta da basu san da maganar auren ba ma se yau da safe amma duk da haka suka bita da fatan alkhairi. Har bakin ƙofar party ɗin mahaifin sa ya kai motar sannan ya fita ya zagaya ya buɗe mata itama ta fito a ɗarare sannan ya buɗe wa su Ibty baya suka fito, hannu yasa ya ɗau Ifty yayinda ya riƙewa Ibty hannu ya nufi falon mahaifin nasa ta rufa masa baya itama. Gana ɗaya mutanen ɗakin suka zuba musu ido zuciyoyin marasa gaskiya na dukan uku uku, masu gaskiya kuma na musu kallon rashin fahimta. "Barka da safiya baba, ga salma matata da ƴaƴan ta kuma nawa". A zabure mutane shida dake falon suka miƙe tsaye kowanne da kalar tambayar da yake jefowa "What?, Me?, Kutumar uba?, Mata?, How comes?, Haba da Allah!. Wannan sune ruwan tambayoyin da suka dinga yawo a falon cikin ihun muryoyi daban daban yayinda Abu Aulad ya saki hannun Ibty ya saka hannun ya jawo salma cikin jikin sa ya rungume.........................✍🏻. Tooooooooh jama'a, gamu a ƙarshen free page da izinin Ubangiji, ko yaya paid pages zasu kasance?!. Shin wacece Abu Aulad ya karyawa hannu jiya da dare?! Wacece shuraiha?, Wai ma tsaya ita kanta Hajiya babbar wacece, meye alaƙarta da Abu Aulad?! Jarumi, jarumi!, Shin kun Tuna shi?! Wanne shi?. Nuriyya ƙanwar nafisa ƴa a wajen Anna, ko meye ƙudurin ta kan Abu Aulad?!. Yace be yarda da kowa ba se kan shi kaɗai, what about Haisam?!. Haisam, Haisam, anya shima babu wani ƙulli kuwa a under sunan nan?!. "Wai ma ku tsaya, wace irin rayuwa ce Abu Aulad ya taso a cikin ta, meye tarihin wannan gidan, wane irin bahagon rayuwa ake yi a cikin sa. Duk ma ba wannan ba, yaya rayuwar auren Abu Aulad da salma zata kasance, me kuke hangowa, gashi dai auren ya ƙayyade masa wa'adi, shin kuna ganin ze sake ta?!. Ni abinda bangane ba shine shi kan sa Abu Aulad ɗin waye shi, ina mahaifiyar sa, anya baba mahaifin sa ne kuwa, to in ba mahaifin sa bane waye mahaifin nasa?!. Shin ina labarin dangin mahaifiyar Salma, zata haɗu da dangin mamanta ko kuwa?, Baba Husaila da mama Hadiza principal, shin shikenan an rabu ko kuwa akwai wata rawa da zasu taka a rayuwar salma nan gaba?! Duk amsoshin wannan tambayoyin na cikin paid pages, sister kar ki yadda ayi tafiyar nan bake domin na tausaya miki rashin da zaki yi dan littafin ze tabbatar da sunan sa akan ki wato ANJANE (RASHIN SANI) dan da kin san irin nisa da ƙarkon da tafiyar zata yi da ba zaki yadda a yi ta bake ba,!. Ga duk me buƙatar yin payment ɗin sa ne bi ta wannan procedure ɗin, ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels