An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels MIJIN BUZUWA complete BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM MUNA GODIYA GA ALLAH DA YA BAMU DAMAN RUBUTAWA DA KARANTA WANAN LABARI UBAGIJI YADDA MUKA FARA LAFIYA MUKAI KARSHEN SHI LAFIYA . KISHI DA BUZUWA SAI KA KWANTAR DA HANKALI KA KAI AIKI DA HIKIMAR KA WAYEWA DA ILIMI BAI FITAR DAKAI A GARESU, , , , GODIYA GARE KUMA KARANTA NOVEL DINA DA KUKE KOKARIN DAUREWA DA HAKKURI WURIN KARANTA LABARAINA WANDA ABUBUWAN DAKE YAWAN FARUWA A NAHIYAR MUCE MUKE TABOWA DON HASKA KAN YAN UWA DAMA MU DUKA. NOVEL DINA NA KAUYAWA NE BABU YAWAN KARAYAN ARZIKI A CIKIN SHI SAI DAI ABINDA LABARIN YAZO DASHI BABU FAYYACE FITSA A FILI YADDA WASU KE SON IN SAUYA ZUWA HADI DA FITSARA NA KASANCEWAN MACE DA NA MIJI A GADO A HAKKAN KUMA NAKE DA DINBIN MASOYA MASU KARANTA SHI A HAKAN, GODIYA GARE KU HAR KULUN MASOYA DA MASU KAUNA NA. GAMA SU SON NOVEL DIN ZAKU IYA KIRA NA DA WANAN LAYIN DON NEMAN KARIN BAYANI DARI UKU NE GA MAI SON BIYA TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 09026931792 KO 08036959257 Hadari ne ya hade garin sosai baka ganin komai sai walkiya da kara kainan motoci a lokacin wanda suke haskawa don ganin gaban su. A daidai wanan lokacin ne motoci guda uku da suka karyo titin a jera wanda ke nuna wani mai akwaine tafe a lokacin yadda mutane suke ta kaucewa a titin suna basu wuri. Wasu daga bakin titi ke fadin yanzun haka ma ba maigidan bane tafe wanan fitsarariyar matan tashine haka da bata ganin kowa da mutunci a idon ta. Wani gida motocin suka shiga a lokacin gini ne na zamani motan ne suka dan tsaya da alama magana akeyi da wani a cikin gidan. Ba a dade ba suka wuce zuwa cikin gidan kai tsaye security ne suka fito don bude motar nan naga wata farar mata buzuwa ta fito tasha ado na fada da gani daga saman ta har kasanta kwaliya ne. Doguwa ce sosai ga fari sai dai idan ka kura mata ido zaka iya gano farin ne kawai ke aki yake rudin mutane don kyau akwai kyau inda bamu matan mu na Nigeria masu kyan asali da dire bayan farin da gashi da kuma tsayi babu abin da suka dara matan Nigeria dashi na fannin kyauwo. Tana wani tako ta shige ciki zuwa part din ta ta dan jima ciki ta fito tana kwala ma wata mata mai suna Labara kira da karfi . Da saurin matar ta iso gareta tana dukawa tare da fadin hajiya barka da zuwa an dawo lafiya yaya han, , , , Dakata tace wa matar yaya naga witan part din can a kunne ko mara zuciyar nan ta dawo ne kuma ? Matar ta dago kai a hankali tace wa hajiya babba kike nufi waye hajiya baba ina nufin fatima matar wancan shiyan ta fada a fusace jin an kira uwar gidan nata da hajiya babba taji haushi. Eh ta dawo laraba tace ai tun ranan da kuka wuce washe gari ta dawo kutawa tayi tare da juyawa da karfi ta shige part din ta a hasale. Anan tabar laraba da kallon mamaki ta nisa tana fadin ikon Allah mata da mijin ta kinzo kin hana zaman lafiya a tsakanin su haka ? Ita kuma a daki sai faman huce takeyi ita daya nan ta dauki waya ta kira mijin nasu da suka rabu yau ya tafi waje yin wani aiki. Duk da tasan dare ne a duk inda yake amma bai hanata kiran shi ba a wanan lokacin saboda tsananin kishin dake damun ta a lokacin. Kiran farko ya tsunke bata hakkura ba ta sake kira a karo na biyu bai daga ba sai wayan na gap da katsewa ya dauka da alaman barci yake a lokacin . Murya irin ta masu barci ya daga wayan tare da fadin Nafisa lafiya kira da dare haka yanzu fa kin san dare ne nan sosai a wanan lokacin. Bata jira ya gama magana ba tace watau munafuntana zakayi ashe kasan matar ka ta dawo shine baka fada min ba tun muna tare sai kawai in dawo in samu ta dawo gidan. Ajiyan zuciya ya sauke tare da fadin tadawo fa ni ban san ta dawo ba don basu fada min da cewa zata dawo ba ma kit ta kashe wayan. Ta wurga a gefen gadon ta tana fadi a fili duk sai nayi maganin shegun tsofin don sai auren nan ya mutu inga ta bakin naci irin nasu. A daidai lokacin ne kuma aka turo kofan side din nata wata matace cikin dogon riga ta dora hijjab a saman rigan nata. Fuska da murmshi tace mutanen Abuja ashe kuna tafe yanzu ne an sauka lafiya yaya hanya fuska a daure ta juyo tana fadin eh muna tafe ko idan zan dawo sai na sanar da wani akace ko ma ? Ke yanzu don baki da zuciya dawowa kikayi duk da maigidan ya nuna baiyi dake saboda rashin zuciya irin naki sai da kika dawo kamar ana zama dole ne. Matar tadan sake murmushin dabai kai ciki ba tace nake ganin ke nan haka amma ni nasan yana yi dani har gobe ke ce dai ganin ki ke rudin ki ga hakan don ko na bar gidan shi bamu rabuba don ga diya ga zumunci a tsakanin mu. Fati ke nan zakiko ga abinda ba daidai ba wallahi in dan kin nace sai kin zauna min da miji don sai na rami ya fiki shan iska a gidan nan tunda haka kika zaba wa kanki sannu sugar mai iyali ko tasbi sarkin zumunci shida bakajan da daya bai biyo ka ba . Murmshi tayi Allah na tare da mai gaskiya dama jin kin dawo ne yasa nazo taron ki da dawowa ba wani abu ya kawo ni ba a huta lafiya bata tsanmanin ta amsa mata ta fice daga dakin . Zuciyar ta yana ciki da mamakin fitsara irin na Nafisa wanda sam babu kunya a cikin shi ko kadan sai zallah cin fuska da fitsara filli. Daki ta nufa a daidai lokacin da ruwa ya gauce sosai a garin na kaduna kamar da bakin kwarya da sauri ta isa ta rufe mirrow da sauran abinda baison walkiya a dakin saboda tsaro wanda ba kowa ke wanan ba a wanan lokacin sai masu sani da hakan a baya suka saura rufe irin wa yan nan abubuwan a daki yayin da ruwan sama ke zubuwa daga samaniya don kariya daga fitinan walkiya. Falo ta dawo ta zauna tare da yaranta dake cin abinci a wanan lokacin ido ta tsurawa yaran biyu sai da ba wai don tana kallon su hankalin ta yana gare ta ba ne tunane takeyi a zuciyar ta na irin rayuwan da ta tsunci kanta a ciki yanzu. Tun shigowan Nafisa cikin su komai na rayuwan ta da mijin nata ya sauya sallo a lokaci daya ba yadda suka saba gudanar da rayuwan su ba suda yaran su da sauran yan uwa. Hatta yaran yanzu a matse suke da zama gidan mahaifin nasu sun fison zama a gidan kakanin su da zaman gidan nasu saboda matsin da suke ciki a yanzu. Ita dai tasan aure ne a tsakanin ta da mijin ta na soyayya tun tana karama soyayyan su ta samu asali don gidajen su basu da nisa da juna shi din abokin yayan ta ne. Kuma akwai zumunci na makwabtaka da ya koma kaman na jini daya a tsakanin gidajen su tun kakan su zumunci ya kulu a tsakanin gidajen biyu. Wanda yakai bako ba zai iya banbanta tsakanin su ba sai wanda yasan tushen abin koda ta girma bai daina kulata ba cikin yan uwa haka ya kai har aure ya kullu a tsakanin su. Tayi haihuwan farko lafiya ga cikin na biyune ya samu aiki kano suka koma can sun koma bada dadewa ba ya hadu da Nafisa yar mutan Niger da suka shigo Nigeria neman kudi da iyayyenta ta lake mai tun bai kula ta har ya soma kulata don suna sayar masu da abinci a bakin ma,iakatar su ne. Yaron ta ne dayazo inda take zaune tana tunane ya katse da da fadin mama daddyn mu bai dawo bane naga anty ta dawo. Shafa kan yaron tayi taja sauke ajiyan zuciya tace bai dawo ba Affan da kaga ya shigo nan ai anty ce ta dawo ita kadai. Yaushe daddy zai dawo mama yaron ya kara jefa mata tambaya kuma tace Affan ban sani ba idan ya dawo ai zaku ganshi. Bai barta ta huta ba ya sake jefo mata tambaya again yace mama ai anty ce bata bari mu ganshi ko munje wurin shi sai tace mu fito muna damun shi yana hutawa. Murmushi tayi tace kai Affan ba yana zuwa nan ida muke kuna ganin shi ba to may kuma kake so shiru yaron yayi kamar yana tunane a zuciyar shi. Sai kuma yace ni mama ban ma son ya dawo saboda may Affan uwar ta tambaye shi yace saboda idan ya dawo sai ki ta kuka mama su kuma suna dariya da anty kuma su fita tare. Affan ban son yawan surutu fa ka faye surutu ina jin tsoron wanan bakin naka kullu naji ka kara fadawa wani matsalan mu sai na yanke ma kunne daya. Shiru yaron yayi yana tunanen kada uwar ta yanke mai kune kamar yadda tace din kayan da sukaci abinci ta kawar ta gyara wurin suka shige dakin kwanan su. Da safe bata fito ba sai da ta gyara part din nata ta nufi kitchen don dafa ma yara abincin zuwa school sai ta samu kitchen din a rufe. Dakin kwanan laraba mai aiki ta nufa a nan ta samay ta tace yau laraba lafiya naga kitchen a rufe Labara tace aikin hajiya karama ne hakan. Nima na fito zan gyara tace na barshi taja kofa ta rufe nayi tunanen zaki fito don saboda abincin yara gashi kuma ta kulle kitchen din. Dan jimm tayi tana tunane a ranta wai may Nafisa take nufi da ita ne haka abinci dai na kowa ne a gidan amma haka take mata idan ta bushi iska sai tace wai ana barnan abinci da yawa gidan. Bayan abinci ma da take ita daya sai ta ba wasu balle yanzu da ya samu karin girma sosai a wurin aikin shi basu da talaucin komai a rayuwan su. Muryan Laraba ne ke fadin sai hakkuri hajiya idan mutum ya ci gaban ka sai dai bi wallahi gama tana ganin ta samu miji a hannu sai abinda tace a gidan. Ba komai Laraba na gode badin tura su can cikin gida wurin hajiya su karba haka ta juya ta wuce zuwa part din ta tabar Laranba a wurin tana jin tausayin ta. Daki ta koma ta shirya yaran ta fito dasu da kanta ta mika wa kanin mijin su dake zaune dasu a gidan ya kaisu cikin gida wurin hajiya a basu abinci. Yace yau kun makara ne tace eh salis koda na tashi har gari ya haska sosai wallahi kaga idan nace zan tsaya dafa masu yanzu sai su makara. Ta koma ciki ya kwashe yaran zuwa gidan su dasu don duk a unguwa daya suke zaune da iyayyen nasu gida uku ne a haka kuma Nafisa ke tsula tsiyar ta a gidan. Don tafi son zaman kaduna saboda anan kawayen ta suka fi yawa da yan yaren su na buza da suke kara zugata tana iya shegen. Salis na shiga gidan kafin ya isa part din mahaifiyar mijin nasu da yaran matan gidan suka fara magana a, a su Affan ne haka yau da safe nan. Salis yace eh maman su ta makara ne yau bata tashi da wuri tayi masu abin karyawa ba shine zasu zo nan su dauka. Murmushi hajiya kubura tayi tace Fatice zata makara da safe kawai dai yar bakin halin gidan su ta dawo jiya akwai da wata a kasa. Ba an mayar da Fati bata san tadawo ba shine ta dawo ta samay su bakin halin nata na banza ya tashi yanzu ta soma ke nan har sai ta kure ta ta tanka mata. Allah dai ya sauwa dayar matar gidan ta fada daga daki tace shi kuma da yazo sai ya biyewa iya shegen nata ba daga daki suke magana. Sun shiga gun kakan su tana ganin su tace ai na sani ba yar iskan yarinyar nan ance ta dawo jiya ba nan yanzu tsiya zai tashi a gidan wanan karo ko ba zan saurara mata ba wallahi. Salis yace cewa tayi makara tayi fa bata samu dafa masu abinci ba yau yaya maganan ku yazo daya da na mommy ne ? Hajiya bata iyayin magana ba sai jan yaran datayi zuwa cikin part din ta ta zuba masu abincin da tayiwa yan marayun jikokin ta da suke hannun ta. Bayan ta gama sallaman yaran ne ta dauki waya ta kira Fati din tace wai may ke faruwa ne yau a gidan naku cikin fara a ta fara gaida surukar nata da bata ko tsaya gaisawa da ita ba. Amsawa tayi sama sama dakyat tare da maimaita tambayan ta a gare ta tace hajiya makara nayi tace jinan fati na san komai walahi nasan abinda yar banzan yarinyarin nan zata iya. A sanyaye fati tace hajiya ba haka bane makara nayi yau din ban samu dafawa ba kashe wayan hajiya tayi badon ta yarda ba. Kashe wayan nata yayi daidai da shigowan hajiya kubura wurin ta tace sai gasu Affan na ga sun zo karban abinci kuma ? Bari hajiya Kubura duk da uwarsu ta boye min na san akwai wata a kasa wallahi bai yuyuwa haka kawai taki tanadarwa yara abin zuwa makaranta. Nan suka zauna suna maganan hajiya kubura tace idan ita fatin bata iya magana mu ba kyalewa zamuyi ba ai ana horo da yuwa ne kuma ? Kai hajiya ta dafe tace Allah ya kawo muna karshen wanan yarinyar a gidan nan hajiya kubura tace amin tana mikewa tare da fadin bari mu gani zuwa rana idan har sun dawo nan kin ga hasashen mu ya tabbata ke nan ta rufe kitchen din nasu ke nan. Ta fice ta bar hajiya a cikin bacin rai tana tausaya ma wanan rayuwa da yayan nasu suka tsunci kan su a ciki na bamin auren buzuwa da ya dorawa rayuwan shi yana zaune kalau da matar shi ya jajibo masu wahala haka. A gidan Fati kuma bata karya ba tun safe ba tunanen kanta takeyi ba a yanzu sai tunanen idan yaran sun dawo may zata basu idomie ne ya fado mata arai ta sayo ta dafa masu suci. Damay zaki dafa wani zuciya yace mata tsaki taja tana tausaya masu a ransu take tunanen da can baya lokacin tana ita kaida ya fado mata a rai. Abinci sai wanda ransu ke so zata dafa da ita da yaranta da maigidan ta har sai taba makwatab wani lokaci yau kuma gashi a sanadiyar kishi da buzuwa har horo yakai ga a rufe store da madafar abincin gidan baki daya. Babu wanda zata kara kai kara gareshi tunda baji mijin nasu keyi ba ko ta fada karshe ma ya dawo ya hauta da masifa gashi ita ba son masifa take ba a rayuwan ta. Haka ta taso da tsoro sam bata fada ko kadan saboda ruwan ciki irin na matan hausawa da ta taso a cikin shi wanda a cikin tarbiyan diyan hausa yake. Kamun kaina a diyan hausawa rasgin hayani da fada da mutane barkatai wanda akasarin matan hausawa hake ne ke cutar su a gidan mazaje su da gun kishiyoyin su yan bana bakwai. Tana tuna yadda Nafisa tazo gidan daga ita sai ghana most go din yan kayan ta a ciki amma yau ta koma kamar wata hamshikiya a gida. Auren ta da aka dauro ba tare da sanin iyayyen su ba can bariki suka dauro auren su da ita inda ta tare a gidan da yake a lokacin a kano. Sannu a hankali har ya samu iyayyen shi suka hakkura ta fara shiga cikin su inda take baiyana harin ta na zahiri a hankali. Da farko ta yaudari mutane inda taja yan uwan miji a jikinta duk suka yarda da ita ta gama jin sirin su kaf kafin daga baya data bunkasa ta fara fitar da kalan ta ga mutane. Inda yanzu kowa ya gama gane ta wasu masu zuciyar imani sun gujeta masu kwadai kuma har wanan lokacin suna tare da ita duk da abin hannun ta bai ban baruwa wasan dadi sai kayi mata bauta kafin kaci abu daga gare ta. Don haka take kallon kowa a wullakance sai uan uwanta dakan zo jefi jefi cin arziki wurin ta wanda ba a wuce wata daya basu zo gidan ba. Tazo da wata yarinya da take cewa wai kaunar tane sai da tafiya yai tafi aka gane cewa yar tace ta cikin ta yarinyar. Nafisa zata girmay ma Fati ga shekaru haka yasa tafi fati wayo sosai har take jin tsoron ga fin karfi ga sihiri don bata shigo haka kai tsaye ba sai da ta shirya ta shigo gidan . Shi kan shi maigidan ba a banza ta barshi ko yanzu kuma bawai ta fasa abinda takeyi din bane sai ma abinda yaci gaba a cikin halayen nata. ZAINAB IDRIS MAKAWA Ina isa na fara bude kofana na lokacin yarinyar ta iso da kayan da Yusuf ya bata tana mika min kallon kayan nayi sai na karba ta karasa min da sauran a cikin daki na. Godiya nayi mata tace babu komai ai ana tare bayan na aje kayan na fada saman katifa na wasu hawaye masu zafi ne suke silalo min a fuska na. Idan na tunana da maganganun da ya fada min masu zafi duk da nima din nayi karfin halin ramawa a lokacin sai nake ganin ya kwaraini da yawa. Na dade a wurin ina neman hanyan da zan rama abinda yayi mun din don yaji zafin da naji ban kai ga samun mafita ba wayana yayi kara a lokacin. Yusuf ne ya kirani sai da ta kusa tsukewa na dauka na kara a kunne na ina sauraron shi yace har yanzu kina fushi ne yar mama. Daurewa nayi nace ai ban fushi dakai don bakai min komai ba yaya na yace dakyau ina son ki saurare ni dakyau magana nake so muyi dake yanzu. Ina jinka nace mai. Khadija don Allah ina son ki bani hankalin ki ki fahinci abinda zan fada maki yanzu naji na kara furtawa. Don Allah ina son in rokeki wata alfarma wani aiki zaki nake son ki min a kan aboki na amma aikin yana da wahala sosai sai dai indan kin daure ba wani wahala a cikin sa. To ina jinka Allah yasa zan iya kuma Allah yasa dai aikin bai fi karfina ba, murmushi yayi yana fadin bai fi karfin ki ba ma insha Allahu don zaki iya. Nace fada min inji aikin idan ba zai shafe karatuna ba da rayuwa na zan iya insha Allahu yace good girl dama na dade ina neman mace irin ki mai gaskiya da zan saka. Ba wani abu zan saki ba sai taimako rayuwan abakina Samad nake son in danka a hannun ki don kice a yanzu kadai nake da ita da zatayi min wanan kokari. Nace ni kuma yayana yace kwarai kuwa ke khadija don ko zaki iya idan munyi laakari da irin halin ki na san zaki iya shiyasa na zabo ki. Tun ranan da muka shiga dakin hajiya mama na fara ganin ki da kuma abinda yafaru dake da Nafisa matar shi kika tsaya min a rai. Ban kuma gaskanta hakan ba sai da naga kin iya biyu su a motar su zuwa nan Abuja kuma komai bai faru ba yasa na kara yarda da abinda nake shirin yi din . Sai gashi kuma yanzu abubuwa suna wakana a yadda nake son su tafi a tsakanin ku cikin hukuncin Allah komai yana tafiya daidai. Khadija ko kin san ba macen da ta isa ta tsaya kusa da Samad tun lokacin da ya auri Nafisa buzuwar matar shi kuwa. Nasan kin san matar shi Fati da akai masu auren gida har suka haifi yaya biyu shigowan buzuwa gidan ya sa suka rabu da ita badon basu son junan su ba. Khadija kin san abinda ya daure min kai nace a a yace yadda Yusuf ya aminta dake a lokaci daya duk da nasan ba abu bane mai wuya a wurin Allah idan ya tashi yin ikon sa akan abu. Don haka nake son ki taimaka muna ki sake jiki da shi tayadda zai aminta dake idan haka ya samu gare mu na tabbatar da sheri buzuwa yana gap da karyewa. Da sauri nace ba zan iya ba gaskiya ku nemi wata wanan miskilin mara mutunci ai buzuwar ne daidai dashi yace khadija zaki iya zaki iya komai. Kyau dai Allah ya baki shi ilimin addini da na boko duk kina dasu a wadace to may zai saki ce bazaki iya ba ai ko ba don niba ko don hajiya mama da fati da yaran ta zaki iya. Nace yanzu may kaka son in yi wai yace shina ke son in fada maki da farko dai idan ki bi labari na zaki gane Samad bai iya ssoyayya ba shine matsalaan farko da aka samu gare shi. Murmushi nayi nace bai iya soyayya ba ta yaya ya auri matan shi har suka zauna Fati har ta haihu dashi biyu shima din murmushi naji ya dan yi yace. Bamu tare ke nan kin manta na fada maki ita fadi hadin iyayyene auren su ita kuma buzuwa abu biyu muke zaton shine silar auren su na farko dai ta rude shi da kyaun ta na biyu kuma ta hanyar sihiri da sauri nace sihiri kuma bada ni ba gaskiya. Yace da zata iya maki komai da tayi tuntuni ai shine ya bani daman sakaki wanan aiki a yanzu. Nace a takaice dai kana son in bata lokaci na a kan shi abinda ya kawo ni in barshi inje taimakon wani wanin ma wanda bai san darajan mutane ba. Aikin da zaki muna ke nan dama ki koya mashi zama da mutane da sauran abubuwan da ya watsar a baya ki dawo muna dashi Abdulsamad din shi na baya. Babban magana ke nan yayana yace ba wani babba bane a matsayin ki na mace zaki amfani da daman ki taimaka muna ki tai maki hajiya dake cikin halin bakin ciki a kashi. Shiru nayi ina tunane ko badon Yusuf ba ko don hajiya da yaran Fati zan iya kasadan yin wanan gwajin da suke sona dashi yanzu. Nace to shike nan naji zan yi matukar hakan ba zai shafi mutunci na ba dai yayi saurin cewa idan nasan zai zubar maki da kiman ki ba zan saka ki ba ai. Nace amma fa in ya nemi keta min mutunci ba zan kyale shi ba zan dauki mataki da kaina yace wanan ba halin shi bane don nasan halin shi tare muka taso tun muna yara dashi. Nace Allah bamu sa,a yace amin na godd da kika fahince ni yanzu zan samu lokaci in shigo inji mai kike bukata don kin san dole sai kin koma ke ma babban yarinya sosai. Kada ka damu zanyi amfani da wanda nake dashi yace kin wuce wanan yanzu khadija zaki zama budurwan mayan garin abuja ne fa. Yace ina son ki fara daga yau nace yau din nan ina zanganshi yace zai bugo maki waya ba yana da layin ki ba nace eh zaki kaga ya kiraki kan abinda yayi maki. Amma sai dai please ki bishi a hankali yana da izza da saurin fushi da zuciya bai son yawan magana idan ba yaso ba amma banda wanan baida komai da zaki damu. Ni kuwa nasan haka nida ya fada ma magana yau sun ranshi sai dai zan jure kamar yadda kuke so inyi din. Ajiyan zuciya naji ya sauke yace ban san irun godiyan da zanma maki ba ga wanan haracin da kikai muna wanda nasan insha Allahu zai zamo maki alheri ke ma nan gaba. To Allah yasa hakan alheri ne a gare ni dai fatana in ga ya koma da iyalin shi normal sai naji ya sauke ajiyan zuciya yace final shine dama bukatan mu . Mukai sallama ya barni ina tunanen yadda abin namu zai kaya tsakanina da miskilin mijin buzuwa ta ina zamu fara nace anya ban daukar wa kaina abinda ba zan iya ba kuwa. Gashi kuma Yusuf yace sirine ne tsakani na dashi sai Allah sai ko nan gaba da zai fada ma hajiya mama shirin shi. A raina nace zan iya insha Allahu indai iyalin shi zasu dawo gare shi sai dai ban taba zaton abin zai zo a kaina haka ba amma ba komai wahala bata kissa ai. Nan dai nayi ta tunanen ta yadda zan fara deal din akan shi amma dai Yusuf yace shi zai fara aiwatar da komai kamar yadda yake yi da farko. Safiyan lahadi wanki nayi sai wanan bakuwar yarinyar da ta shigo min da kaya don dai han san ta a gidan ba tazo min hira dakina ina gugan kayan da suka bushe min. Nan take fada min ai ita yar jos ne amma tana zaune ne da yayanta a nan cikin gari ta dawo hostel ne don ta samu yin karatu da kyau naji dasin haduwa na da ita ko banza zan rage zaman kadaici ni kadai da nakeyi ni kadai. Waya na yai kara na daga Yusuf ne bayan mun gaisa yace fito gamu kofan hostel din ku dam naji gaba ya bada na kalli maryam dake gefe na nace ina zuwa ta mike ita tace zata je ta gyara daki don gobe akwai classes. Ba wani dogon kwalliya nayi na dan yafa gyale na na fito tun fitowa idon su yana kaina har na iso inda suke a cikin motar su. Na gaida Yusuf din yace ga abokina ogana baki gaida shi ba na dan juya wurin shi a yatsune nace oh ashe tare kuke ina wuni. Haushi da takaici ya kama shi ya rasa ma zai yi sai da Yusuf yace khadija na gaishe ka fa cikin yanayi da alama na ko in kula yace lafiya kawai ya kawar da kanshi gefe. A ranshi yace i hate dis girl wallahi Yusuf ya katse shi da cewa oga gata nan ta fito fa ya fada cikin tsigar tsokana ya juyo da sauri yace wa wurin na tazo dama. Yace bakai kace muzo kabata hakkuri ba abinda kai mata jiya kasa ta kuka ya damay ka da sauri na tare Yusuf da cewa ai nice zan bashi hakuri nida na bata mashi rai jiya. Don fadin gaskiya ni kuma nasan gaskiya na fada duk cikkaken namiji da yasan ciwon kanshi ba zai tsaya mace na juya shi macen ma kuma buzuwa wai. Yusuf dama ka kawo ni nan ne don ta kara ci min mutunci ko may haushi ya ishe shi yarasa may zai ce min wallahi na tsani wanan yarinyar ya fada a hasale . Cikin ko in kula nace i hate you too dama abinda yasa kuka zo ke nan daga ganin ka nasan ba yin kanka bane buzuwa ta hasala ka ka koma ma matar ka kawai ta asali ko mutuncin ka zai dawo ga idon jamma, a. Yusuf yace kai oga fitina khadija ko rigima nace bai son gaskiya ne gadai mutum har mutum amma bai kai ga cikan kamala ba har yanzu ga idon jamma a. Oh stop it gara ku fito fili kununa ma duniya soyayyan ku da wanan sallon soyayyan naku da kuke yi kullun u don't need to pretend garama ku fara tun yau. Wai Yusuf may kake nufi dani akan wanan yarinyar ne da kullun kake kawo ni wurin ta taci min mutunci hakane. Ni dramar kuce take burgeni wallahi don naga idan na kawo ka wurin khadija tana saka magana kana rage damuwa ko yaushe kuma tana ma tuni da abinda ka manta. Gyara zama yayi a motar ya kwantar da kai tare da harde hanaye shi wuri daya yana kallon bakin hostel din mu yadda mutane ke ta shiga da fita ciki. Nima kallon Yusuf nayi nace yayana wani wuri zaku ne yace muna dan yawata wane muka zo duba ki kin san ke amanan hajiyan mu ce gare mu yajuya wurin shi yana fadin ko ba haka ba aboki na ? Tsaki yaja ya kara kawar da kanshi gefe nace sai dai tsiyan abin indan yayi fushi fushin bai mashi kyau sai ma ya kara mai muni sosai. Murmushin dole ya sake yace kai Yusuf muje don Allah wanan na gane zata iya haukatani in banyi da gaske ba. Kaiko daukanta zamuyi mutafi da ita adan sawo mata wani abin mana kaga sai ta kara hucewa ko tunda gashi har ta baka hakkuri yanzu ai komai ya wuce kenan. Kinga ba sai kin fada ma hajiya mama dukan bakin ki da yayi ba jiya ai yanzu kun zama friends kuma ko fada ya kare ke khadija ba yayaki hakkuri don Allah. Da sauri ya juyo inda nake sai na dan durkusa nace ya Samad kayi hakkuri don Allah idan na maka laifi. Oh baki san ma kin min laifi ba ke nan Yusuf yace shigo mota sai mu karasa magana a hanya yamma nayi kwarai. Banki ba tunda nasan plain ne na shiga motar a hankali ya harba titi ina harara dan iska a inda nake zaune Yusuf ne ya shiga aiwatar da nashi shirin a lokacin cikin motar yana dan muna nasiha. Yace kar kuji komai indan nine take a deep breath and confess your love to each other wani irin dogon nunfashi yaja tare da lumshe idanuwan shi. Da sauri nace yayana love kuma a ina kataba jin anyiwa mutum dole haka akan abinda yaki jini yace don't say dat again just say yes to each other don kuna bukatan hakan. Khadija ina son ki rike min oga na tsakani da Allah ko babu soyayya ku zama aminan juna muna son ki gyara tsakanin shi da hajiyan mu ta fahince shi ta bar hushi dashi. Sai lokacin ya kallo Yusuf ya sauke wani ajiyan zuciya don ya zaci Yusuf yana son hakane don gyara tsakanin shi da mahaifiyar shi. Nace yaya zanyi in gyara mashi laifin dashi yayi da kan shi har kake tunanen nice zan gyara hakan yace yes idan hajiya taji kuna tare nasan zata ji dadin yin hakan da kuka kin ga zata fitar ma abokina da zargin da suke mashi na buzuwa bata bari ya rabi wata mace sai ita. Sai yanzu na gane nufin ka abokina ya danyi gyaran murya sai kuma yayi shiru can yace da farko dai na gane manufan ka yanzu Yusuf . Yace zamu shirya dake idan har zakiyi min wanan taimakon iyayyena su fahince ni a hankali nace idan ka shirya yin hakan a shirye nake in taimaka ma in har zaka koma masu da zuciya daya. Maganan ta dan soshi ranshi amma haka ya dake yace na gode a hankali ai lokacin gode min baiyi ba nace mashi. Tsayar da motar yayi a bakin wani babban sai da kayan sawa irin na mata da maza ga motoci birjit a wurin an paka su a haraban wurin. Bissimilah yace muna kallon shi yayi yace wa wai ni kake nufi kowa yace daku duka nake magana ai yace may zanyi a wanan gurin yace kaunar mu zamu ma sayayya mana. No kuje kawai yace yana gyara zaman shi a yadda yake nace da ka barshi ma ban bukatan komai a yanzu yace tunda nayi niyar yin haka barin in fita induba zaku iya jira a mota yana bude motar zai fita yake wannan magana. Da sauri nace dashi barin fito mu shiga tare yace No ki zauna abinki yanzu zan fito ba dadewa zanyi a ciki ba. Yana wuce na koma na zauna bayan na bishi da kallo wayana na dauko ina dubawa shiru motar babu mai maga a cikin mu sai can naji yaja guntun tsuki wai da bai harka da kananan mata sai manya masu aji ko su sai a waje idan yafita duk da ba wai yana yawan hurda dasu bane yanzun ga Yusuf yana son ya dauko mashi wani aiki ga wanan yar karamar yarinyar dako sa,an kannen shi batakai ba sosai. Nima tsakin naja ina gyara zama cikin tunanen da nakeyi nashi. Ga dai mutum har mutum kudi kwaliya kwarjini duk Allah ya bashi sai dai yawan miskilanci da girman kai da jan aji din yayi yawa kamar ba mace ce ke juta shi ba a gida. Ke ni kike wa tsuki ko kowa ya juyo tare da zuba min kyawawan idanuwan shi a kaina na ma mance kana cikin motar nan murmushi mai kama da takaici yayi yaci gaba da zuba min kyawawan idanuwan shi can ya koma ya lumshe su tare da komawa saman kujera ya zauna. Ya sake cewa kina aji nawa ne yanzu ba tare da ya juyo ya kalle ni ba shiru nayi ina game da wayana batare da na nuna mai dani yake magana ba. Dake nake magana ko bakiji bane nace wa ni ai na dauka da kurma nake a motar a hankali ya kada kanshi ta dan sake murmushi yace ke dai ba zaki bar wanan halin naki ba ke nan. Nace ba halina bane hakan a ra nayi don in kare kai na daga masu raina ma tallaka hankali ya fido ido waje yace haka kika dauke ni ke nan . Hakan na gani kamar kana tsoron talaka a kusa da kai sai dai ba abun mamaki bane don ko a gida haka naga kanayi masu wanan daure fuskan. Kin san nayi ma aboki na alkawarin ban kara fada dake yanzu don haka ki kama min bakin ki tunkan in hasala da wa yan nan maganganun naki. Kai ashe kasan girman alkawari haka ne nakoji dadin jin hakan saidai kamar yadda kai mashi alkawari ka cika nima ada hakana naiwa kaina alkawarin ba zan tsaya da wani namiji ba sai gashi a sanidin taimako ina son karya alkawarin da na dauka ma kaina. Yaja numfashi tare da cewa wanan deal ne a tsakanin na dan wani lokaci banga abinda zai sa ki dauke shi kamar serious ba. Nayi dariya tare da cewa wasa mai kamar wahala ba indan buzuwa ta sanda hakan akwai matsala babba ashe sai na kwashe da wanni irin dariya mai ban haushi dake wa yayi bai ce komai ba cikin kuluwa. Yusuf ya fito da manyan jakkuna a hannun shi yana kokarin bude motar ta kofar baya ya saka jin dariya yasa shi cewa abin ya fara tafiya ke nan dai. Ya dai kusa na bashi amsa a takaice kai a fasa wanan deal din nace a fasa gaskiya zai fi don wanan ba zai kai ko ina ba. Zai kai mana yace yana rufe kofan motan ya zagaya ya shiga kallon Samad dake dafe da kan shi yayi muka kama hanya a lokacin hadari ya hadu sosai a garin ruwa na iya zuba a ko wani lokaci. Mun iso Yusuf ya tsayar da motar yace khadija mun gode sai mun kara haduwa yanzun ba time hadari ya hade gari ta ko ina nace nagode kwarai. Ka kula min da mijin buzuwa don Allah na bude motar zan fita yace ga kayan ki nan ki kwasa duka naki ne godiya na sake mai karo na biyu na fice daga motar. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUYanayin damana yanayi mai cike da albarka yayin da ban gare guda yake burge alumma ko babu komai yanayin da daminar kan haddasa jamma,a sha,awan ta saboda ire iren abunda damanan kanzo wa jamma,a dashi musanman musan nan abuja da ba noma suke ba amma yanayi yana kawatar da jamman cikin ta yayin da damanan ta fara mikewa zaka ga tsirrai iri daban daban dake kara kawata garin. Wanan yanayin yakan saukar min da nishadi sosai musanman idan naga garin ya gaure da hadari kasan ba wuya ruwa ya sauko masu. Yau ma na fito daga aji ke nan naga yanayin garin ya sauya nasan bamu nisa da samun ruwan sama ke nan kusan kwana shida ke nan ana zuga muna ruwa a irin wanan lokacin. Tafe nake a hankali nake takawa daga cikin haraban makarantan zuwa hanyar da zai fitar dani daga cikin makarantan sai dai zuciyana cike yake da tunanen rashin kudin da ban samu fita zuwa turawa daddy ba har yau ko da zan fito hadari ko ruwa zai tare ni gashi ban son inyi missing din lecture da safe. Abu biyu ne yake damu na yanzu yunwa da tunanen daddyn mu saboda banci komai ba tunda safe da na fito don yau na makara ban tsaya na karya ba. Saboda nacin karatu da nake dashi a raina don koda dare haka nakan raba dare ina karatu ni kadai a daki sai na gaji zan dan taba barci asuban farko kuma in tashi in fara nafila ina kusanta kai na ga Allah idan na gama kuma karatu zan dan dasa a wurin sai zuwa haskawan gari zan tashi in wanka in karya in kama hanyan shiga cikin makaranta. Yau sai aka samu akasi na makata ban tashi da wuri ba har rana ya fito hakan ne ya hanani tsaya in karya wanan tsarin dana dauka yana matukar wahal dani . Amma ni ina aganin shine daidai don iyakacin abinda ya kawo ni kenan a garin indan ban yi ba may zanyi. Domin karatu na bar gidan mu na bar dangina da kowa nawa a gida nazo nan idan ban mai da hankali ba mai zanyi sai shiririta ke nan kamar yadda naga sauran dalibai suna yi. Don a ganina karatun shi yazama min dole dashi na dogara dashi nake saka ran samun ci gaban rayuwa na dana iyayyena nan gaba . Buri na ne burin iyayye na da yan uwa na ya ta,allaka ne akan karatun don haka babu dalilin da zai sa in zauna ina wasa dashi. Nikan zauna in dinga tunanen yadda nake ganin wasu dalibai suna wasa da daman su ta hanyar zibar da abin da ya kawo sai in rika mamakin su ina tausaya masu don nayi imani da cewa suna cutar da kansu ne sun kuma ha,inci iyayyen da suka turo su karatu . Ire iren su gasu nan da yawa sai yadda suke so sukeyi a cikin makaranta kwata kwata basu damu da karatun ba sai idan jerabawa yazo ne ido ya rena fata duk dadai wasun su ne suke damuwa da hakan. Wasu ko iyayyen su ko samarin su suna masu hanya su haye ire iren tunanen da nake yi ke nan ina tafiya saman dogon titin da zai sada ni da gidajen da muke ciki. Ido na zubawa wata dankareriyar motar jeep dake nufo inda nake a hankali ba ka gane wanda ke cikin motar dan glassen motar da ya kasance masu duhu baka gane na cikin motar balle ma wana sani ni anan. Ta gefen ido nake kallon motar har zuwa lokacin da motar tayi gaba kadan dani ta tsaya a gaba na ban dauki komai a raina ba don a gani na wani abin maishi ya tsaya yi. Nazo zan wuce motar ne naji muryan kamar wanda na sani yana cewa yar garin mu yanzu nake tunanen ki da hanya ya biyo dani ta wurin ku. Don sheda muryan maishi da nayi yasa ni sakin dan murmushi kadan nace kaine kuma yau a wurin namu yace wallahi aiki ya biyo dani tanan din kuma ashe da rabon ganin ki. Murmushi nayi na fara gaida shi ya amsa yana fadin ummm Khadija ko nace eh ashe baka manta da sunan yar garin naku ba dai. Murmushi yayi yace ina zan manta da yar mama baki tambaye ni mijin bazuwa ba yau murmushi na kara yi nace kace dai miskilin mijin buzuwa. Yace kin kara masa inkiya ke nan nace shine daidai dashi ai suna lafiya ko ya labarin gida koda yake muna waya dasu Binta ma nasan suna lafiya koda yake tace an ma mama rasuwa zariya ta tafi can tun jiya zata kwana uku a can. Yace kai haba bata ko fada muna ba wallahi wa ya rasu a can zariya din sai kuma yace kada in tsare ki a hanya don naga kamar bakin son hakan ke. Murmushi nayi nace idan hakan ya dauro yaya zanyi sai yace shigo mana in karasa dake idan ba damuwa nace lah ai ba wani nisa don na kusa karasawa ai. Sai dai don Allah ina zaka bi don ina son sauka a bakin, banki in tura kudi yace to shigo mana in sauke ki ai ke din kanwar mu ce na zagaya gefen ina fadin na gode. Mun dan fara tafiya wayar shi tayi tsuwa ya daga yaya akayi ne mijin buzuwa banji may yace ba don karan kira,an dake tashi a motar murya malam Ahmed sulaiman kano ne. Yace wallahi gani nan dawowa sai dai kuma uzuri ya tare ni din na hadu da yar garin mu a hanya na rage mata hanya zamu banki da ita. Wake nan ya tambaya a cikin wayan yace khadija wama surname din ki Adamu nace mai a takaice yace khadija a dabu kawar tafiyan ka na ranan. What Yusuf sai da ka kara nemo yarinyar nan don Allah yarinyar nan bata da kunya fa ganin Yusuf nata dariya yasa ni wafce wayan ina karawa a kunne na naji yana fadin wanan yarinyar matsalace wallahi sam bata ganin girman babba. Nace nakai matar kane rashin ganin girman dan adam kai har kana da bakin fadar haka yace baki da kunya ko nace aikai kana dashi kada ka kara kirana da mara kunya wallahi. Yusuf ne ya karbi wayan a hamnu na yana dariya yace kadai ji abinda tace kada ka kara kiran ta da mara kunya ehheh. Yusuf abin naka ya girmay sani na yanzu tunda har ka iya mika mata waya ta zage ni yace bata fa zage ka ba man ina jin yadda kukayi da ita sarai. Mun iso ya tsaya na fita ina mai godiya yace shiga ki fito ina nan ina jiran ki har ki gama kin ga akwai hadari a garin sosai komawa zai maki wuya kuma. Nagode nace dashi ina fita yace ara min wayan ki kafin ki dawo dan jimm nayi kamar ba zan bashi sai kuna mika mashi wayan na fice daga motar sai da na gama abinda nakeyi na tabbatar da kudin sun shiga na fito lokacin har an fara yayafi kadan kadan a gari yana zaune yana duban wayan shi na dawo na samay shi ina shiga yace har kin gama eh nace mai ina rufo kofar motar waya na ya miko min na karba ina fadin ka gama dubawa ne yace dama waazi neke dubawa a ciki murmushi na danyi kasan baki na. Lokacin aka fara ruwa mai yawa duk da ban ganin hanyan da kyau amma na gane ba hanyar da muka fito bane muka bi yanzu. Dan kallon shi nayi yace kada ki damu zan dauki mutumi ko ne ya gama mintin driver kuma wai yakai Nafisa Nasarawa bai dawo ba. Banji dadin jin hakan ba sai dai ba yadda ja iya kuma a wani ma, aikata muka shiga ya tsayar da motar da sauri ya fito ya shiga motar ni kuma na koma baya. Kamar ban cikin motar don banyi magana ba sai fada yakewa Yusuf wai ya dade baizo ya dauke shi ba yace kan wani aikin da kasa kanka can . Ya haba taimako ne fa nayi kasan ace a taimaki mata ai a duk sanda suke ga bukatan taimako cikin tsawa yace ya ishe ka hakana Yusuf enough ta fada da karfi yana dafe kan shi da hannun shi daya. Nan zan sauka nace a daidai lokacin da yake dafa kkan nashi da alama bai san dani a cikin motan ba ma sai a lokacin dan juyowa yayi yana kallo na da mamaki a fuskan shi ya sai kuma ya juya yana kallon Yusuf din. Na sake fadin a nan zan sauka nace fa nace ma Yusuf ya juyo yace acikin ruwan nan zaki sauka haka a ina zaki samu abin hawa nace kada ka damu ai zan samu idan na fita. Yace to bari in dan karasa dake inda zakiyi saurin samun abin hawa ya fadi shima fuska a dake da alama yaji haushin abinda yayi mashi a lokacin. Karasa da ita ka ajeta yace ba tare da ya kalli kowan mu ba yai magana dama ba sauke ta zanyi ba ai sai na kaita inda na dauko ta. Ba wanda ya sake magana a motan har bakin gidan ya tsaya da mota lokacin an dan rage ruwa sosai amma anadan yi kadan kadan yace ashe hajiya an mata rasuwa ne. Ina fita naji yana fada mai hakana na gode yaya Yusuf agai da gida da mutanen gidan Allah ya kara rufa asiri na fice daga cikin motan abina. Ban tsaya ba don ruwan sama bai bani lafiya idan ya buge ni sai dai ban tsira ina fita ruwan ya sake saukowa da karfi da gudu na karasa cikin . Sun kama hanya ya dubu Yusuf din yana fadin wata hajiya akaima rasuwa nace yace hajiya mama mana hajiya mama nawa kake nufi ita yanzu wanan yarinyar ke fada min . Shiru yayi bai sake magana ba sai zuwa can yace wata ce ma yarasu a zariya din kana son sani kake daure fuska haka tsuki yayi sai can yace barin kira hajiya din in ji. Har ya dauko wayan ya fara duba lanban mama din sai kuma ya dago kai yace kana da nomban wanan yarinyar kaba in kira ta. May zakayi da layin ta kuma yarinyar da bata da tarbiya yace malam idan zaka bani ka bani kawai ba dogon zance nake so ba kyale shi yayi kamar bada shi yake magana ba. Sai zuwa can yace ana son ai maka gata kana wani jiji dakai wanan jida kai din ba zai kaika ko ina ba a harzuke yace nomba nace kabani kada ka fada min wani magana da zai kara bata min rai bayan wanan. Har saida yakai shi hara ban gidan shi ya ajeshi zai fita ya miko mai wayan shi yana fadin ga nomban nan kamar ba zai karba ba sai kuma ya daure ya karbi wayan ya kwashe nomban. Ya mika mai wayan ya shige ko sai anjima baice dashi ba shiko murmushi yayi yadan bugi sitiyaein mota shi ya juya ya fice gidan. Nafisa buzuwa ce suke tafe da kawar ta nan cikin garin Abuja sun fito nasawa state ganin wani malamin su a can da tai ma mijin karya zasu duba wata aminiyar ta ne . Bai hanata zuwa duk inda take so shiyasa tale samun yin yadda take so a gidan don shi kwata kwata bai dauke ta da irin wanan halin ba na matan dake shige shige. A hankali suke magana yadda sani driver ba zai fance su ba shiko a idan yake tuki ya mayar da hankalin shi ga hannya ne amma kunnuwan shi yana gare su. Nafisa ke fadin kin san Allah wanan sakawa zanyi yai min aikin da ko uwar shi ba zai iya daga ido ya kalla ba balle wata mace don naga alaman wanan arnen yada aiki sosai. Don su malam kasan mu ko ka basu aiki irin wanan sai sun kawo maka Allah kusa kafin su duba maka kukan ka. Suwaiba kawar ta ya mutsa baki tace ke ma kikan so damun kanki nafisa mijin da ko a yanzu a hannun ki yake wanda kika sa ya kore uwar yayan shi kuma ka zauna lafiya may kuma yanzu zai wani daga maki hankali. Bai fa kallon mace sau biyu a yanzu hakan ba anan matsalan yake ba suwaiba wanan abokin nasa da suke kamar tagwayen sheri dan iska mara zuciya nayi kora da hali nayi na fili amma ya na lake kamar kaska dashi. Kina ganin ko baiyi niyar yi ba shi bai iya dauko ko mace ya kawo mai ke komai tsiyan su fa baki taba gane sirin su dashi dashi. To ai yanzu ba tashi zakiyi ba tunda shi kin riga da kin samay shi a hannu ko sai yadda keki so dashi yanzu akan wanan abokin nasa zaki koma ki san yadda kika raba su. Gaban Sani driver ne ya fadi har yana batun kauce hanya dama yana zargin gidan da yakai su din ga zargin shi ya zama gaskiya har ana batun raba ogan nasu da aminin shi. Wanda yasa in tayi nasaran yin hakan ta gama da ogon nasu ke nan gaba daya tunda shi kadai ne dama ya saura yana sashi a hanya yanzu. Muryan ta yaji ta daka mai tsawa ya kula da tukin da yake yi ya dubi hanya mana yace hajiya rami na kaucewa shi ya kawo hakan. Suwaiba tayi mata rada su bar maganan harsu sauka kada yaji abinda suke kullawa sai suka dauko wani sabon hira. Sai kuma tace malam sani ke nan dama ina son magana ta siri dakai sai dai maganace ta taimakon juna dani dakai. Yace hajiya wani taimako kike sona dashi tace siri ne kuma amana a tsakanin mu dakai amatsayi na matar ogan ka kuma wanda yasan wasu abubu nawa. Idan kuma kaga bazaka iya taimaka min ta wanan hanyan ba to zamu hada deal dakai in dinga biyan ka akan aikin ka. Dan juyowa yayi yadan kalle su zuciyar shi ya tabbatar mashi da cewa wani abu mai muhinmanci zata saka shi yai mata da ya shafe ogan nasa. A fili yace hajiya fadi bukatan ki a shirye nake da in aiwatar maki matukar bai fi karfin iyawa na ba murmushi tayi tace ai ba wani abu mai wuya bane zan saka ka yi. Ogan ka nake son ka sama ido don Allah duk wata mace da kaga yana hurda da ita a bayana har sun shaku a tsakanin su banda gaisu ka sanar dani ni kuma nayi maka alkawarin duk wata zan baka dubu biyar bayan wanda mai gida ke baka. Yai dan dariya yana shafar kanshi yace hajiya idon wanan ne kar kiji komai aran ki nayi maki alkawarin ko gaisawa da wata naga yayi wace bata gamshe ni ba zan fada maki. Suwaiba tace dakyau dan gari dama ai na fada maki babu abinda kudi bai bayar wa ke bude bakin jakkan ki ga aiki da cikawa kawai. Da sunan zuciyar Sani driver da basu furta komai a gaban shi ba don nasiha hajiya mama kullun suka je kaduna ya shiga gaida ita shine don Allah ga amanan yaro na baka Sani ko ba komai yanzu mun zama daya dakai tunda ana wuri daya. Duk da kasalan dake damu na a lokacin bai hanani tashi in girkawa kaina abinda zanci ba lokacin bayan na gama ne na fitar da kayan da nayi aiki na wanka na shiga bayi na watsa ruwa masu zafi don ruwan sama bai bani amana ajikina. Ina fitowa daga bayi ne mukai kicibis da zarah da ta shigo dakin nawa a lokacin wanda alama ya nuna yanzu ta dawo daga cikin gari sabada ledan da take dauke dashi a hannun ta. Nasan key din dakin ta tazo dauka tana saye da wasu kaya da ya matse mata jiki sosai kin dawo nace mata eh kin gani sai yanzu na dawo wallahi. Inda key din yake na nufa in dauko mata na mika mata leda daya ta aje min daga cikin ledejoji dake rike a hanun ta nace lah dakin dauka wallahi na fada maki ai ban son komai daga irin abinda kike dawowa dashi. Lumshe idon ta tayi cike da jin takaici na tace na sani amma wanan ba inda kike zato na samo shi ba sako ne da samu an kawo min daga gida naga idan na barshi ma a hannu na baci zai yi shiyasa nace bari kawai in mika maki. Ledan nabi da kallo a raina nace watau sakon da iyayyen ta suka aiko mata dashi bai da wani amfani a gare ta sai na mazan da take bi ke nan. Karban key din ta tayi ta fita dakin na bita da kallo tana saye da kayan da ya matse mata jiki sosai ga kitson kanta da ta sako su har kafadan ta. Tsuki nayi na shimfida anbin sallah na tayar da sallah na na idar na koma na jingina da katifa na ina jan casbi a hankali waya na dake gefe yayi kara a lokacin. Number ne ba suna na daga ina mamaki waye mai wanan special number yake kirana kuma kusan kiran zai katse na dauka. Da sallama a baki na sai naji shiru kara maimaita sallaman nayi wanan karon sai aka amsa min a gadarance kamar naso in sheda mai kiran amma na kasa canka. Shiru har lokacin na sake cewa hello naji ance ina jinki nace wai waye please ko wrong number aka kira ne yace ke kina magana da Abdulsamad Abdulrahim ne . Nace waye haka kuma bazaki sani ba don ba lallai ne ki sani din ba nace kai ta shafa wanan kuma banda lokacin irin ku haka kuke kiran mutane don bata masu lokaci kawai. Ke ban son rashin kuyan da kika iya ke har a wayan ma sai kin nunawa mutane halin ki ba wani abu yasa na kiraki yanzu sai don inji wayarasu hajiya ta tafi zariya. Au kace min miskilin mijin buzuwa ne nikan ina zan sani kaji ka da wani magana ni zaka tambaya wa hajiya ta rasa kuma ? A har zuke yace eh don a bakin ki mukaji ta tafi zariya shiyasa nake son jin wanda muka rasa din bawai na kiraki bane kimin rashin kunya. To ban sani ba kuma kada ka kara kiran layi na kaji na fada maka zan kashe nace wai ma a ina ka samu layina dan fitina ? Wanda kika ba ya bani layin ki mara kunyar yarinyar kawai zaki gane baki da wayau idan na kama ki don naga rashi kunya yana nema yakawo kaina. Kit na kashe wayan ban bari ya gama fadin abinda yake fadi ba don ba zan iya tsaya in saurare shi ba nace wanan wani iri fitina ne kuma? Ina ruwan shi dani da zai wani bugo min waya wai yana tambayana wa mahaifiyar shi ta rasa da ta tafi zariya gaisu dan rainin wayau shi ba danta bane baifini kusa da ita ba waini may hadina da wa yan nan mutanen ne haka da suke son su shiga min rayuwana ina zaune kallau. Shiko a ban garen shi ji yayi kamar ya samay ni ya fafala min mari ya sauke haushi yaya akayi ne na raina shi haka ne. Yaja tsuki ya fara laluben nomban mahaifiyar tashi dole ba don yaso ba yaji may yasa har abu na faruwa irin haka take nisan ta shi da ita duk da yasan fushin da hajiyan keyi dashi a kan Fati ne ba komai ba. Kamar bata dauka ta dauka tare da fadin sallamu alaikum ya karba mata a cikin ladabi sai ya fara gaida ita bayan gaisuwa ne yace cikin kwantar da murya hajiya naji ance anyi maki rasuwa a gida kin tafi ? Eh haka ne nayi rashi amma ni ya shafa ai rashin da nayi don jin ka baida wani amfani a gareni inda dai dangin ka na kauyen maradi ne da ka tafi ko tuntuni. Shiru yayi yana sauraren zafafan maganan da mahaifiyar shi take fada mai tace wai tunkuna ma wani dan karabanin ya fada ma nayi rashi a dangina har kaji duk da nasan ba kiran mutane yanzun kake yi ba buzuwan matar ka da dangin ta sun ishe ka. Hajiya kiyi hakkuri nima a wurin yariyar nan Yusuf ya jiyo muna shine nace ba a fada min ba tunda har zaki je zaria ki kwana biyu haka ba karamin rashi kika yi ba. Tace wace yarinya ke nan kake magana a kanta yace yarinyar da kika hadamu da ita kwanaki muka taho abuja sai dai yarinyar bata da kunya ban gane inda maganan ta ya dosa ba. Au khadija kake nufi ko wa yace ina ganin sunanta ke nan Yusuf ya hadu da ita take fada mai yaban layin ta na kirata tana karanta min shirmay . Tace Ladi ce matar kawun ka Allah ya karbi abinshi shine nazo ita khadijan kuma ta damu da nine shiyasa tasan damuwa na har taji. Yanzun kai bakaji kunya ba ace wai har khadija zata ji zance na kai bakaji ba haduwan ka da yarinyar gaba daya ya canza muna kai kana ko tuna makomar ka ga Allah. Bani ba ba mahaifinka ba duk kayi watsi da alamarin kowa kana ganin buzuwa da yan uwan ta sun isheka rayuwan duniya. Mu din dai da kake gudu din mune dai iyayyen naka har gobe zance guda ne abin nan da ka guje mu akan shi yana nan yana jiran ka . Sannan da kake kiran khadija mara kunya ita ma ka sa mata tsanar ne na babu gaira babu dalili saboda da tafi karfin matar son naka ko may . Zai yi magana ta kashe wayan ta ta kyale shi ranshi yaji ya baci sosai da maganan hajiya yasan akan Fati take wanan fushin haka dashi to shi may ye laifin shi a ciki. Hajiya suna gama waya binta ta kira tana tambayan ta ko sunyi waya da khadija tace mama ta kura tana tambaya na ke nace kin tafi zariya an maki rasuwa acan zaki kwana biyu. Tace oho yanzu yayan ku ya kira waya wai sin hadu da yusuf take fada mai a wurin ta suke jin an min rasuwa don baida kunya har khadija taji abu ya samay ni tana jajantawa amma shi bai ji ba. Sai kokarin son ya zagi yar mutane yake wai bata da kunya shi waya fishi rashin kunya yanzu shida ya nuna muna ba komai muke a gare shi ba. Sun gama da binta gulma ya ci binta sai ga kiranta ina shirin kwaciya ya shigo min. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: 🧠MIJIN BUZUWA🧠 2ï¸âƒ£ ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU NOVEL DIN NAN NA KUDI BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAN IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA Hayaniyar yaran da suka dawo daga makaranta ya dawo da ita ga tunen tace shike nan nawa ta samay ga Affan da dan banzan wayo kawai na shiryasu zuwa cikin gida wurin kakanin su tasan idan sunje can sa samu abinda sukaci a cikin su. Yaran suna shigowa suka fada mata a jiki suna fadin mama mun dawo yunwa nakeji sosai wallahi karamin ya fada take taji gabanta ya fadi don hakan halin su ne . Sai subar abinci a cooler makarantarsu su dawo dashi kuma suce yunwa suke ji halin yaro ke nan oya a cire uniform kuje cikin gida wurin su hajiya kwaci abinci a can banson yawan hayaniya yau. Acan cikin gida kuma dawowan yaran gidan makaranta yasa hajiya ta kasa kunne taji shigowan jikokin nata da take zaman jiran tsamanin su tunda safe. Ba afi min ashrin ba ta fara tsinkayo hayaniyar su daga kofan shigowa gidan tace a ranta nasan a rina dama tabbas hashe na ya tabbata ke nan wanan yarinyar har takai can. Yaran suka shigo dakin da murnan su don anan kawai suke samu su sake suyi yadda suke so batare da wani tsangwama ba. Suna shiga Affan ya cire rigan jikin shi ya rage daga shi sai singlet yana fadin hajiya maman mu tace muzo nan muci abinci a wurin ki wai yau bata son damuwa. Yar ta Aisha ta kwala wa kira tazo ta basu abinci sai gata ta fito daga daki tana saye da dogon riga a jikin ta tana ganin yaran tace a a su Affan ne yau da rana tsaka anan zakuci abincin rana ke nan ? Hajiya tace zuba masu Abinci don Allah ki kawo masu nan ta wuce kitchen cika umurnin mahaifiyar nata da sauri sai gata dauke da plate din abinci ta kawo masu. Hajiya na zaune gefe ta kurawa yaran ido tana kallon yadda suke cin abincin gwanin ban tausayi dasu tunane tayi aranta da yau babu ita fa kamar yadda babu ran kakarsu ta wajen uwa yaya Fatima zatayi da wanan ukuban haka ? Hajiya kubura da take matse ita tunda rana sai gata ta shigo wurin hajiyan da mamaki a fuskanta tana fadin yaya kin ga hasashen yana son ya tabbata a kan yarinyar nan ko sai ga hajiya karima uwargidan su tashigo a bayan su tace tabbas maganan mu ya zama gaskiya. Ya tabbata ke nan ta ki bari yarinyar nan ta girka abinda zasuci a gidan abin har ya tashi ga ta hana mai aiki yi masu girki suci ya koma ta hana masu abinci. Sallama ake daga kofan shigowa dayar yarinyar gidan ta leko daga kofan hajiya karima tana fadin sannu da zuwa yaya Suraj. Bai amsa mata gaisuwa ba sai tambaya yayi ba kowa a gidan ne ina sallama gidan shiru tace suna dakin hajiya mama ina gani can yanufa dakin don yasan idan sunyi irin wanan taron akwai abinda ke faruwa da ya shafi dayan su ne don don iyayyen nasu nada hadin kao sosai a gidan. In ka debe ko wanan ya kasance amaryan su Asiya bata gida ne a lokacin da su hudu zasu hade a dakin kofan ya nufa yana saye cikin uniform din shi na sojoji. Sallama yayi a bakin kofan daga ciki suka amsa mashi mahaifiyar shi hajiya karima tace kamar muryan suraj nake ji a kofa yace nine ummi. Dakin ya shiga kallo daya yayiwa iyayyen nashi alokaci guda ya gane akwai wani matsalan da suke fuskanta wanda ya shafi hajiya mama a gidan. Gaida su ya fara yi a cikin ladabi kamar ba soja ya samu wuri ya zauna bayan sun karba mai gaisuwa. Duban hajiya kubura yayi yace mommy akwai matsalane su Affan dake cin abincin su hankali kwance ta nuna mai tana fadin wanan fitinaniyar matar uban tasu ce kila ta rufe dakin girkin gidan ne yau ko da safe a nan suka dauki abincin zuwa makaranta. Yanzun kuma kaga uwarsu ta turo su nan su da sauri yace ita Fatin fa may zataci to ya tamnaya yana kallon fuskokin su gason jin amsan su. Mommy tace ai shi muke tunane a nan dafe kai yayi yace wanan mata ban san abinda take nufi ba a gidan nan tana son mayar muna da dan uwa binan. Kada kaga laifin ta ai shine mai babban laifi mama ta fadi a hasale sai mummy tace ba yin kanshi bane yaya bar irin shuuman matan nan wallahi. Suraj ya mike a hasale yana fadin yau sai naci mata mutunci idan haka gaskiya ne wallahi ko a gidan maza ana ma mutum horo da yunwa ne balle gidan brother za a ce anyiwa mutum haka. Ko maigadin gida ai yana iya kyauta da abinci tunda bai rasa ba balle diyan shi ummi ta kalle shi lokacin da yake shirin fita daga dakin tana fadin ina zaka ? Kai tsaye yace gidan zanje wallahi idan na samu gaskiya ne yau sai tabar gidan nan wallahi ummi tayi saurin cewa dashi kaifa mahaukaci ne na sani a dai karbe key din ka bude wurin shike nan. Kasan yadda dan uwanka ke son ta hakan zai iya kawo matsala a tsakanin ku yace wallahi sai dai ya kawo ummi wanan wani irin bakin haline haka ? Ai haka suke mommy tace mashi abinda ake mai gudu ke jan tun farko bai gane ba basu son kowa sai kan su da yan uwan su kawai wanan halin su ba wai ba. Mama dai ta rike goshin tada hannun ta sai wanda duk yai magana cikin su ta bishi da ido kawai shine nata yayin da zuciyar ta ke mata soya a ciki tana jin wani irin ba dadi a ranta. Yana tsaye daga kofa mommy tace bari muje tare dakai zaifi da sauri ummi tace haka zaifi kan don wanan kin san mahaukaci ne ya shawo Alluran shi ja sojoji kar yaje ya sauke wa yar mutane a kai. Ai da zai sauke din haka zai fi gani take duk ta gama da kowa a gidan babu wanda bata iya takawa shiyasa take abinda taga dama inji mama. Yanzun dai bari mu tafi idan munje ni zan fara shiga wuri ta inji ba asin yin hakan da tayi sai asan abinyi sukace yayi kyau hakan mikewa tayi zuwa dakin ta ta dauko hijjib din ta ta saka suka fice da suraj din a motar shi suka karasa gidan. Daidai lokacin Abba ya dawo shi da anty amarya daga asibiti da dan ta da bai da lafiya ganin motar suraj ya gilma ya nufi gidan dan uwan nashi yasa suke mamaki. Anty amarya ke fadin yau suraj ziyara zaikai gidan Abdul ne haka mahaifin nasu yace kila yazo ya samu Fati ta koma dakin ta ne zai dubuta. Sai da suka shiga gidan ne suke jin abinda ke faruwa karban key anty Amraya tayi bata shiga dakin taba ta bar yaron wirin uwar gidan nata ta mara masu baya. Sun samu kofar gidan a rufe wai taba maigadi sallahu cewa kada ya bari kowa ya shigo gidan ya damay ta don yanzu ta dawo da yarta daga makaranta zasu huta. Da kyat ya bude masu kofa sai da suraj yayi mashi jan ido wanan abin shiya kara harzuka suraj din rashi ya baci sosai kusan a tare suka shiga gidan da anty amarya don samun delay din shiga da sukayi. Bin gidan Suraj yayi da kallo daga sama har kasa kafin ya karasa fitowa daga motar shi cikin hasala mommy tace ashe kun dawo ke nan take cewa anty amarya tace mun dawo ina shiga ake fada min abinda ke faruwa nace barin biyo ku don ba mutunci ne da ita ba. Anty tasan ida take rashin mutunci ta ai nika yau idan tayi min wallahi balbalata zanyi in daki banza sai dai mu rufe da mijin ta ai mun saba. A tare suka shiga gida jin karan bude get din gida ta fito a fusace tana fadin maigadi wani dan bura, uba kabudewa, , , , , ganin su mommy yasa tayi shiru ta juya da saurin tana zaton basu ganta ba suko sun ganta. Kafin su iso ta wuce part din ta ko da sauri don tasan ba bakin ta bane na Fati ne don ita suke zuwa gidan su . Tunda ta sallamay sallah la,asar take zaune saman sallaya ta tun tana addua ta koma tunane ga tunanen ya bowayeta don yunwan da ke cin ta. Sun shiga da sallaman su aka gaisu tace mommy kune tafe ashe mune fati har kasa takai tana kara gaida su cikin mutunci suka amsa mata ta dago tana fadin yaya Suraj marmari daga nesa. Ke kin ci abinci yau ko baki ci tambayan da ya jefo mata ke nan a lokaci daya tayi murmushi tace kajika da wani magana kuma ba a gida ka samay ni ba zakai min wanan tambaya haka ? Mommy tace Fati ba tambaya muka zo yi ba don mun san abinda ke wakana a gidan ko yau dai bakici komai ba tunda garin Allah ya waye haka ne ko ba haka ba. Kai ta sadda kasa tace hakane mommy tace to akan may Fati zaki zauna ana maki horo da yunwa dake da diyan ko haka abincin nan akwaishi ba babuba kuma. Mommy yau fitina take ji tun jiya data dawo ta samu na dawo gidan ta fada min bakaken magana har tana ikirarin sai na rami ya fini shan iska a gidan nan. Shine yau da safe zan shiga kitchen na samu ta kulle komai tunda asuba wai kada a dora girki a gidan ta fadawa Laraba ni kuma ban koma ta kanta ba tunda nasan don ni tayi hakana. Haba Fati sai ki zauna da yunwa ai zaki kashe kanki ne idan kina haka yanzu bari muje mu samay ta muji may take nufi wai. Suraj bai bisu ba ya dan tsaya ganin Fati din yana kuma tambayan ta may zataci yaje ya sayo mata tace duk abinda ta samu yace kayan tea fa tace suna store acen muke ajewa fita ya yi ya mara masu baya. Sun shiga da sallama cikin isa ta karba masu sai suka tsaya gaisawa da ita tunda iyayye ne su bayan gama gaisuwan mommy tace munzo ne dama muji dalilin rufe kitchen da tsore din gidan da akayi wa mutanen gidan. Hajiya nan fa gida na ne ina da daman da zan rufe ko ina nake son don Abdul bai bar abinci da Fati a gidan nan ba tunda bai cata dawo ba ta dowo don haka sai ta jira idan ya dawo ya bata abinci ita da diyan ta suci. Karya kike yi munafukar Allah kuma baki isa ba wallahi muryan Suraj ne da batayi tsamani ba ya fado dakin yana zazzare mata ido a cikin hasala yake magana yana huci. Tare da daka mata tsayawa yana fadin ban makulin nan tun ban balbalaki yanzu a wurin nan in kuma sa sojoji suzo su kwashe ki sukaiki barikin mu su daure har ranan da miji ku ya dawo inji shiku idan shiya ai horo da yunwa haka. Kallo da tayi wa Suraj raga fuskan nan nashi ba imani a cikin sa zai iya aikata abinda yace a kanta tsoran ta Allah tsoran ta soja da sauri ta mike ta shige dakin ta yabi ta da harara. Yadawo da fuskan shi kan yar ta dake cin abincin da tayo masu take away a hanyan dawowanta gida ya watsa ma yarinyar harara da sauri ta noke kanta kasa ta kasa cin abincin da tun shigowan su dacin abincin ta take yi bata ko gaida su ba. Da sauri tafito daga dakin dauke da key din a hannun ta tana mika mashi cikin ladabi ya fisge a hannun ta har ya fara tafiya su mommy zasu bishi sai kuma ya juyo yana fadin. Ina ne kitchen din da tsore suke ki taso muje yau za a yi ta ta kare and idan bayan tafiya ko harara naji kin ma yar uwa wallahi yau ba ubanda zai hanani daureki a garin nan jiki na rawa ta bi bayan shi zuwa tsore din yace ta bude da kanta ta bude. Laraba da mai masu aikin gida namiji da ta dauko dan kabilar su can garin su wanda ya zama kamar CID din ta ga komi a gidan ko tana nan ko bata nan ya kira. Komai na tsore din aka fito dashi waje aka kasa uku yace Fati ta kwashi kashi biyu ita da diyan ta kashi daya ta dauka nata ne. Ga abin magana ba halin yi don tsoron soja da ke zuciyan ta tun da zasu shigo Nigeria sojoji suka latsu a hanya take tsoran soja inda duk ta ganshi. Yana tsaye a rike kunkurun shi da hannayen shi biyu yake tambayan fati akwai wani tsore da kitchen a gidan tace eh akwaishi a part din ta wanan nata ne ita fatin suke amfani dashi in generar. Kwashi naki kikai part din ki da sauri taja wani kwali da kyat tana fadin kasiye dauko mun sauran ta matsu tabar wiein wanan dan banzan soja mara hankali dake gabanta. Dama tun zuwan ta gida da ta fara ganin shi aka nuna mashi ita a matsayin sabuwar matar wan shi bai yi murna da ganin ta ba a fili ya nuna hakan kowa ya gani. Don shi kyamar irin su yake yi bai dauke su wasu cikakkun mutane ba a idon shi, yafi daukan mayaudara aduk inda ya gasu haka yake kallon su a yatsune. Shine dan uwan shi ja jini ya auro ya kawo ta cikin zurian su take juya mutane yadda ta ga dama a gidan da takaicin ta ya juya tafi bai shiga gidan nasu ba a lokacin mommy tare da anty Amarya suka koma gida bayan sun yiwa Fati nasiha kadan. Nan suka tafi suka bar Fati da tsoro a zuciyar ta fam sai dai abinda bata sani ba a halin yanzu Nafisa tafita shiga tashin hankali don tsoranta Allah tsoron ta Suraj soja. Wanda ta hango mugunta zalla cikin kwanyan idon shi abinda ya fadi tasan karamin aikin soja ne yayi shi ya aiwatar da abinda ya fada din dole ga magana nacin ta da zata fadawa Fati a yau sai dai babu halin yin hakan gare ta dole ta kawo ido ta saka mata a gidan tana jiran dawowan mijin nasu wanda zata sa ya ci fuskan Fati din a gidan. Ai idan sun san wata basu san wata da makirici zataci galaban su gaba daya don ta gane yan uwan mijin da iyayyen shi duk munafukai ne a kanta. Can gidan su hajiya sun koma kumshe da dariya a cikin su sai da suka shiga mota suka fara dariyan abinda suraj din yayi wa Nafisa . Yanzu sun gano takon ta Suraj ne zai dinga mata hukunci irin nasu na sojoji na rashin imani sun shiga gida nan suke bada labarin abinda ya wakana a gidan. Mama taji dadin har cikin ranta ko banza Suraj ya kwantarwa Fati incin ta yau wanda inba shi din ba, ba wanda ya isa yayi haka a zauna lafiya da ita tunda tayi niya. Maganan mommy ne ya dakatar da ita da taji abinda Nafisan ke fadi a lokacin shigan su gida da take fadin wai babu rabon su Fati da yayan ta ga abinda maigidan ya bari a gidan. Lalaima wanan matar tantiriya danta ya dauko mata ba kwai ba donge amma har take ikirarin cewa wai ba abincin su a gidan. Wani zafi na bakin ciki irin wanda iyayye ke ji a gamay da diyan su idan sun yi abu ba daidai a cikin alumma wanda sai uwa ko mahaifi suka san da irin zafin da mama taji a lokacin. Haka dai ta shige daki a dadafe bakin ciki da takaicin da matan dan nata ke kumsa mata a zuciyar ta yayi yawa kuma dan nata ya sani amma bai iya daukan wani mataki akan hakan. Wunin ranan haka suka kare shi da maganan Nafisa wanda hakan ba bakon abu bane agurin anyi sau tari da yawa sai dai na yau din ya banbanta da sauri don ta fito ta nuna masu karfin iko da izan da take dashi a cikin kan dan nasu . Wanda suka haifa suka tarbiyartar da hannun su kuma ya tashi da tarbiya suke saka ran samun farin ciki a wurin shi kamar yadda duk wasu iyayyen ke fata ga diyan su idan su samu Amma lokaci guda Nasifa ta shiga rayuwan dan nasu wanda ya watsar da duk wani rayuwan farin ciki da suke hasashen samu daga gare shi. Gashi a yanzu yana a cikin ganiyan samun duniyan shi wanda bai zauna ba tsaye yake wurin neman na kanshi a rayuwan wanda ba komai yakawo hakan ba sai addun mahaifa da yawaita ta sadaka akan diya yake bibiyan shi a yanzu. Don a baya in zata iya tunawa bata da aiki sai yawai ta sadaka fiye da kowa a gidan in anyi magana sai tace ba neman duniya nake wa kaina nemawa na baya nake madogara. Ga yawan taimakon na kasa da ita tundai idan ance yaro maraya ne sai mama tasan yadda takai alherin ta ga yaron ko ta saka yayan ta suyi mai alheri daga abinda suke dashi na jikin su mai kyau wanda zai farauta ran yaron da za a ba abin. Don Allah iyayye mata mu kula kada muyi sakaci da wanan dama akan marayu da muke gani zaki iya dafa kan yaro maraye zai ji dadin hakan da kikai mai har a cikin ranshi. Bawai duka maraye bane zai bukaci taimako wasa ma da dariya a gare su sadaka ce dan abinda zai farauta masu rai sadaka ne Allah ya bamu ikon yi ga maratun dake a kusa damu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: 🧠MIJIN BUZUWA🧠 3ï¸âƒ£ ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU NOVEL DIN NAN NA KUDI NE BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA YAN UWA. Tsaye take gaban mirrow tana gyara rigar da ta sa a jikin ta na tampha wanda akai mata dogon riga dashi mai wani launi kamar jikin damisa brown colour. Dinkin mai dan kwala sai da wuyan rigan V neck akayishi wanda yasa gaban ta ya fito dakyau daga cikin rigar kasan rigan ma an bude shi free yadda zata iya walla kafafuwan ta ba cikin matsuwa ba. Turare ta dauka ta feshe jikin ta dashi ta juya ta dauko gyalen ta dake saman godo gefe ta fesa mashi turare ta mayar a hand bag din ta dan kwali ta dauko ta dan daki lokaci tana daurawa take fuskanta ya fito tsonen a jikin mudubin. Duk wanan shirin da take yi ranta ba dadi don bata son zancen zuwa kaduna a zuciyar ta tafi son tayi rayuwan ta a gidan ubanta dake a cikin garin Minna. Inda gidan su yake a kwangila road asalin su su hausawa ne zamane na kakan ni ya kawo su garin minna har suka zama yan ainihin gari baza kace su bakin gari bane yanzu don kowa nasu anan aka haifeshi. Daga wajen gidan wanda irin ginan da can bayane na siminti wani murya ya kirata da fadin Khadija kina makara fa a cikin irin hausan mutane Niger shiba kananci kuma ba hausa pure ba do ya dan hade da surkin harshe. Muryan Khadija ne ke fadin mama shiri nakeyi gani fitowa yanzu da sauri ta karasa shirin ta jawo dan trolley din da ta sa tufafin ta a ciki tare da rataya handbag din ta a kafada ta fito waje. Kallon ta mama tayi wace zance a wurin ta khadija ta debo kyau da na saba kafin in ga mahaifin ta farar mace ce doguwa yar kabilan gwarin may kunkele dake a cikin minna din. Kallon yar nata tayi tace kin fi son ko yaushe kiyi tafiyan marance mama nina fison in shiga da yamma yafi ba wanda yasan zuwan ka sai dai a ganka. Maimakon tayi haraman tafiya sai ta ja kujera roban dake gefenta ta zauna kallon ta uwar tayi tare da fadin yaya haka kuma ? Banbara nake jira na aika a sayo dashi zan tafi bana son in mising din shine idan naje ke dai yanzu na gane baki son zuwa wurin yar uwan naki tunda kika girma kika fara karatun jamia . Ta dan ya motsa fuska mai kama da sallo ko yanga wanda ba haka bane kusan yanayin yan garin ne haka suke maganan su da kamar sallo da yanga tace ni nafison in yi hutu na a gida. Amma ita ya Amina kullun sai tace sai mutum tafi wurin ta hutu yanzu kuma ba da bane ban son ina missing din gida sosai murmushi kawai uwar tayi don tasan halin yar nata. Ba ajima ba mahaifinta ya shigo gidan yana ganin ta yace a Khadija an fito ke nan eh baba zan tafi hannu yasa ya fara laluban aljihun shi sai ya fito da dubu biyu ya cire guda ya miko mata. Kai ta girgiza mai tace baba ka barshi kawai kudin da anty ta turo min zai ishe ni na gadone a daidai lokacin yaron da ta aika ya sawo mata banbara ya iso da leda a hannun shi yana mika mata da canjin karike canjin tana bude ledan ta debo banbaran ta mika mai ta mike tana gyara jakkan ta yaron ya taima ya fita mata da kaya ida ta tare Napep zuwa Abdulsalam garej . Tana isa saura mutum daya ta biya suka shiga suka kama hanyan garin kaduna yamma lis suka shiga gari lokacin kuma akai hadarin marancen nan da Nafisa ta dawo ta samu Napep din da zai kaita unguwar da yar uwar nata ke aure wanda kusan rabin zaman ta a baya a nan tayi shi sai data girma ta koma gida karutun da take yi Abuja yanzu shine silar mayar da rayuwan Khadija gida Niger state. Tun ranan da khadija tazo kaduna bata fita ba tana daga daki sai falo indan ta fito ko kuma ta shiga kitchen tayi masu girki a gidan. Yau da yamma ya Amina ne ke kwala mata kira tana zaune tana cin banbara da tayi worming din shi kamar yanzu akayi shi bai kwana ba. Ya Amina gani ta fito tana fadi cikin ranshin kallon fuskanta don Allah zo ki shiga gidan su mommy ki karbo min sako tace yanzu in tura a karbo min. Fuska khadija ta ya motsa tace ni ban shiga ba tunda nazo banje na gaidasu ba Amina tace wai khadija may ke damun ki ne haka ? Ke a rayuwan ki sam baki son shiga jamma a ban san inda kike dauko wanan rayuwa naki ba haka cikin bacin rai ta juya dauko gyalen ta kayan da tazo dasu garin ta kara sakawa a jikin ta. Yaran anty nata biyu ta, ta kira su rakata gidan da aka aike ta din fitowan su bakin get din gidan yayi dai da zuwan wata mota a guje ta watso masu ruwan dake kwance a wani dan rami saman hanya. Cikin bacin rai Khadija ta dago kai tana fadin you are very stupeid bakya gani ne kika watso ma mutane ruwa haka. Horn kawai Nafisa tayi masu ba tare da ta tsaya khadija tabi motar da hararan takaici tana dan kakabe riganta da ruwan ya dan taba a lokacin. Raina yayi matukar baci haka muka doshi gidan mutane ina mita wani saurayi dake tafe a bayan mu naji yace yar iskan buzuwan nan ne haka take tuki kamar mahaukaciya wallahi. Dan juyawa nayi na kalli mai maganan nace sannu yace yawa bata dai zuba maku ruwan sosai ba ko nace kadan ya taba mu inayi har lokacin ina kakaban ruwa a jikina. Gidan muka shiga wanda har lokacin raina a bace yake da buzuwar da naji saurayin nan yace min da sallama muka shiga gidan. Wanda sai kawuce kofan falon gidan kabi wani dan siririn hanya da zai sadaka da cikin gidan da muka shiga wanda babban gida na ba yau bane farkon shigana gidan don duk zuwa nayi sai anty ta aike da gidan ina shiga akai akai yanzu tunda na girma bani shiga idan nazo sai da wani dalili. Sallama mukayi inda kofan uwargidan ne fara isa sai na mama daga can ciki sai kuma wasu biyu dake kallon nasu din na mommy dana anty Amarya ke facing din su. Hajiya ummi da yaranta nake jiyo hayaniyar su daga kofan part din ta na dan matsa daga kofan dakin ina gaida su dakyat aka amsa min ban tsaya ba na wuce. Lekowa akayi daga dakin ummi don ganin mai gaidasu din da bai shigo ba bata gane ni ba alokacin har nakai kofan mama shiyasa ban son shiga wanan gidan don yawan dake garesu kuma sai kabi kowa kagaida shi dole don hadin kai irin na matan gidan. Koda baka gaida mutum ba wanda kaje wurin shi zaice dakai ka ko gaida mutanen gidan sanin haka danayi yasa na fara binsu daga daga ina gaida su. Dakin mama ma a kofa naja na tsaya ina fadin ina kwana mama ta amsa min daga ciki tana fadin waye shigo mana ciki. Dole na shiga daga cikin dakin tare da kara gaida ita inda nakai gwiwana duka biyu a kasa irin gaisuwan mu na mutanen Niger. Daga kuryan dakin ta aka fadin muryan wa nake ji kamar khadija Adamu da sauri mai maganan ta fito falon ida nake wani irin ihu ta sake a lokaci daya tare da kwalawa binta kira tana fadin ga khadija Adamu ashe tana garin nan mukayi maganan ta jiya. Murmushi nayi ina dagowa daga gaida mama da nake nan suka shiritar dani nace anty ta aiko ni wurin mommy. Bayan nagaida amaryan su ne na wuce zuwa dakin mommy ta tareni da fara anta mun dade tana jana da hira wanda ni ban iya sake jiki dasu muyi hiran sosai saboda mutunci da girma da nake gani a idona. Sakon ta dauko min na fita mukai sallama dasu nan suka rakoni suna dan taka min in baki mantaba mai karatu na fada maki a nan kaduna nayi rabin rayuwa na. Kamar abin tsokana wanan motar dai ne na dazun ta dawo a guje ta kara yin facali da ruwa a take nace wanan wani irin iskanci ne wai haka ? Har motar ta wuce sai ta dawo baya a hankali zuwa gare mu a lokacin zainab ke fadin Nafisa ce fa ta dawo zai tai muna cin mutunci kila taji zagin da khadija tayi ne. Gab damu ta tsaya tare da sauke glass din motar wata farar mata nagani ciki tare da wata zaune a gefen mai zaman banza. Tace wace yar iska ce cikin ku take zagina shiru naji sunyi suna soke kai kasa nan san lokacin da nace mata kece dai yar iskan da baki san darajan mutane ba kika gudu da mota haka a wulkance cikin gari kamar yar koyo. Ke tafadi a zafafe tana kokarin bude kofan motan da sauri naji su Binta da zainab na fadin yi hakkuri anty bata san ke bace . Cikin zafin rai nace ke wacece da zaki watsa ma mutane ruwa kice kada ayi maki magana wallahi ko diyar shugaban kasa kike sai nayi maki magana . Karasa fitowa tayi daga motan tana fadin ke yar gidan uban waye a garin nan take raina ya kara baci nace kedin yar gidan uban waye da baki da tarbiya fada min naki in fada maki nawa. Fisgan hannu na Zainab keyi ni kuma ina turjewa don ban ga wani kimar ta da suke gani ba idons a lokacin don sam ban da tsoro akan gaskiya na. Ke yar waye da zaki tsaya kina fada min magana son ranki nace ni yar gidan ubane ke kuma cewa akai titin na gidan ubanki ne da zaki dinga gudu kina watsa ma mutane kura da ruwan titi. Yadda taga ina yi sai ta tsaya tana kallo na kafin ta mayar da fadan akan su Binta da zainab din tana fadin zamu hadu da kune wallahi don nasan da sanin ku take min hakan. Nace wai kun san wanan banzan ce da kuka tsaya tana fada maku maganan banza saman hanya haka ? A harzuke tace nice banza nace an fada maki idan ba banza kike ba may kike zaki tsaya kina ma mutane son raki ke gaki mai kudi ki takamu ki wuce lafiya kin taki banza ko ? Zaki gane kurenki wallahi wani kallon banza na watsa mata nace sai dai mu gane kuren mu amfada maki don kina da kudi zanji tsoron ki ne ko may kudin ki bai damay ni ba tunda ban taba zuwa wurin ki neman wani abu ba. Matar da take cikin mota ne taji abin yayi yawa kuma dukkan mu munki bari ta bude mota ta fito tana jan ta tana fadin haba Nafisa zaki tsaya kan wanan karamar mara kunya kuna raba hali a saman hanya ai sai ta ja maki raini ga jama, a. Kuta tayi ta watsa min harara na mayar mats ta shiga mota tana fadin zaki san kin shiga hurumi na nace inga alheri . Fisgan mota tayi sai da yayi wani irin kugi suka nufi hanyan cikin gari zainab tace wai Khadija kin san kowacece ita din ? Wacece kuwa banda kila matar wani ko wata kusan gwaunati shike nan don muna kasa sai ta rena mu Binta ce ta katse ni da fadin matar yayan mi ne kishiyar anty Fati. Inda motar yabi nabi da kallo nace yanzu wanan matar matar dan uwan ku ne wallahi na dauka irin matan bariki din nan ne masu zaman kasu nima ban san yaya akayi idona ya rufe haka ba naci mata mutunci. Nan nake fada masu abinda tayi muna da zamu shiga gidan su yanzu kuma ta sake maimaita muna shiyasa raina ya baci don naga kamar da gaiyya tayi hakan amma kuyi hakkuri don Allah. Binta tace ai mu yau kin muna daidai wallahi don ba karamin dadi naji ba da kikaci mata mutunci nan a gaban mu. Mun da jima a tsaye dasu karshe mukai sallama muka shige gidajen mu har lokacin ina da zafin matar nan a raina. Nafisa ko sai fada take kawar ta na bata hakkuri tana fadin ban son ki biye mata ba tunda kinga kannen mijin ki a wurin may yuyuwa tasan ki ke baki santa ba. Zanyi maganin ta wallahi sai ta rena kanta zata san ba a taba ni a zauna lafiya ko wacci tuwo dani miya ya sha na san dai ba yar gidan uban kowa bane ita. Su zainab na shiga gidan su suka fara bada labarin arangaman mu da matar yayan nasu nan mutanen gidan suka fito suna sauraren su. Mommy tace kai amma wanan yarinyar wallahi ta burge ni sosai yau da haka Fati ke daurewa ta mayar mata da martani da abin nata ya rage. Anty amarya tace ai ba zata iya ba ne don ta riga tasa mata tsoron ta a zuciya kuna ganin a banza ta bar mutane ne haka da kowa ke shayin ta. Ummi tace kwarai ai irin su ba a banza suke barin gida ba sai sun kama bakin kowa sun daure yadda ba mai iya motsawa a kan su. Sai lokacin mama tayi magana tace aini wanan yarinyar ta gama shereni wallahi tayi min daidai yanzu zata san in ta daure bakin wasu bata iya daure na wasu. Nikan da muka shiga gida ya Amina tana daki mika mata sakon nayi a cikin wani dan leda wanda ban san abinda ke ciki ba dakina nakoma na fara rage kayan jikina. Na mayar da dan riga mai karamin hannu da bujen body hook dana cire sai hula dana dora a kaina kitchen na nufa don dora abincin dare saboda yamma yayi. Kafin wani lokaci har na kammala na gyara wurin na mayar da kauan da nayi aiki a inda suke daki na kofa nayi wanka kafin a kira sallah na fito na canza kayan jikina. Kananan kaya na kara sawa a jikina don idan ina gida sune kayan sawa na wayata na jawo ina duba sakon dana samu daga abokaina da muke karatu dasu. Lokacin sallah yayi na mike na gabatar da sallah ban daga ba sai da na yi har isha,i na nike abin sallah na fito din in ba yaran anty na abinci. Anty ce ta fito daga dakin kwanan ta muryan ta naji daga baya na tana fadin har kin fito eh kawai nace mata ba tare da na juya ba ina zuba abincin a plate na mika ma yaran dake zaune suna jirana. Juyowa nayi inda nake tsanmanin take zaune nace in zuba mata abincin yanzu ne kallo na naga tanayi cikin mamaki tambayan da ta jefo min a lokacin ban zaci ji ba. Khadija may ya hada ki da buzuwa yau kin ko san waye buzu kin san ko matar waye don Allah ki rufa min asiri tunda nake unguwan nan ban taba fada da wani ko wata ba ina jin tsoron rashin tsoran nan naki wallahi. Kara daure fuska nayi nace ina ruwa da wata buzuwa ko baturiya take ba zan yarda ta wullakantani ba ga banza don tana takama tana da kudi tunda ba kudin ta nace ta bani ba. Don Allah dai ki bari ban son irin haka ni na dauka kin bar halin nan naki yanzu da kika girma ashe halin na nan baije ko ina ba. Mijin ta fa na iya sakawa a kore mu a unguwan nan wallahi don suke fada aji yanzu a garin don Allah dai ki bari. Kamar zan yi magana sai nayi shiru ranan banci abinci ba saboda haushin buzuwan nan dake ci min rai haka na kwana da tunane kala kala a raina. Hajiya mama haka ranan itama ta kwana tana tunane a ranta kan yadda zatayi da danta akan buzuwan da ta zama masu fitina da masifa a cikin zuri,an su. Dan ta ya zubar mata da mutunci da kimar da mutane ge gani nata duk a kan auren wanan matar da bata darajja mutane da halin ta. Da safe nafito na hada breakfast har na gama ya Amina bata fito ba tana daki na gyara ko ina na gidan sai na koma na shiga wanka na fito na shirya tare da hayewa gado in dan huta. Sai lokacin na fara jin hayaniyar su a falon gida alaman sun tashi ke nan daga barci hakan baisa na fito ba sai kara lafewa danayi saman gadon barci ne ke son dauka na a lokacin. Muryan ya Amina naji na bude idona a hankali ina kallan ta daga inda nake kwance nake mata ina kwana murshi tayi ta karaso gare ni tana fadin. Har kin gama kin kwanta yau barci ne ya dauke ni tana fadi tana kaiwa zaune a saman gadon da nake kwance jin banyi magana sai naji tayi murmushi . Tace khadija fushi kike yi akan maganan da nayi maki jiya akan buzuwan nan bata da mutunci ne khadija shiyasa kowa ke tsoron shiga tsabganta don mijin ta zai iya keta ma kowa a kanta yadda yake son ta. Dagowa nayi nace OK shike nan don mijin ta na da kudi ko mulki ba zanyi fada akan dama na na dan adam ba murmushi naji tasake yi tace khadija ina raba ki da shiga tsabgan irin mutanen nan. Kai na kawar gefe ina hade miyau takaici da yazo min a lokacin haka abin yai ta cina har na gaji na sake na manta da wata can a zuciya. Jin shiru da su Binta sukayi yasa su ranan biyo ni gida a falo suka samay mu dukkan mu nan muka zauna har anty muna hira suna min korafi wai kullun ina gida kumshe ban fita. Zainab tace kodai kina tsoron haduwan ki da Nafisa ce nace waye Nafisa kuma tace matar yayan mu mana da kuka kwasa ranan . Oh kuce mi buzuwa mana ai sai in gane ba Nafisa ashe sunan ta ke nan ni na fi gane ma buzuwa ai Binta tace ai bata son a kira da buzuwa shiya sunan ya mutu a bakin mu. Ranan da ra kai kara wajen yayan a gidan bakiga irin fadan da yai muna ba ni tun lokacin gidan ya fita raina wallahi. Ashe ya zama mijin buzuwa ke nan yar sani in fika wai agola da rabon gida ina kika san yar sani in fika ne ai sai kin ga yadda ta mayar da anty Fati a gidan. Ita da mijin ta yanzu ta koma yar kallo a gidan ko dan aikin gidan yafi ta daraja a gidan kwanan fa sai da ta fito aka maida ita kin san may ? Da ta koma bata gidan tana dawowa sai cewa tayi wai uban wa yace ta dawo gidan sai ta kama kitchen da komai tarufe na gidan ta hana ma anty Fati da yaranta. Sai lokacin anty dake gefe ta saka baki a hiran da mukeyi a falon tace amma samun wurin nata yayi yawa wallahi nace wai wace anty fati kuke magana haka ? Wanan da ta taba haihuwa har mukai fati daku a baya dan tunane nayi nace nagane ta itace mijin ta ya auri wanan matar wallahi itace inji Binta zainab dai sai dakilan wayanta takeyi tana charting. Anty ce tace yanzun yaya akayi akan abincin nan dai take fada muna yadda suka kwashe da suraj anty ce ke dariya ni banga abin dariya ba tunda ba dukan ta naji yayi ba. Sun kai wani lokaci suka ce zasu tafi na mike na dan taka masu har bakin get din gidan anty na na dawo ciki. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Bayan mun gama waya da ita naji raina ya baci sai a lokacin na gode ma Allah da ban goge number shi ba a wayana kira nayi har sau biyu bai daga ba sai na tura mashi sako masu zafi na kashe wayan. Don nasan zai gani da safe in ma kwanciya yayi a lokacin haka yasa na danji zafin da nake ji ya rage min da kyat barci ya dauke ni a ranan. Har na rufe ido sai nayi wayana yana kara na dauka a zatona shine yaga sakona ya kira wayan sai dai ba number daya kirani daya kira dashi bane. Nace ummhumm ina jin ka naji ance haka ake karba kiran wanda baka sani ba na sheda muryan Yusuf din nace yayana kaine a na dauka wani ne. Yace nice injin ruwa bai saki jin zazzabi ba dariya nayi nace ai na watsa ruwan zafi a jikina yace good dama na kiraki ne don mutumin ki ya karbi number ki a hannu na nasan zai iya kiranki kada ki biye ma halinshi don Allah don bansan abinda zai kiraki ya fada maki ba koda yake yace akan maganan hajiya mama zai kiraki yaji don Allah , , , Na katse shi da fadin ai ya kirani ko har munyi tsiyan shi ya dauka kowa nema yake a gare shi ko yaushe ni kuma na wanke shi tass. Da karfi naji yace haba don Allah nace wallahi na kwashe komai na fada mai har text din da na tura mai mai zafi yace amma baki kyauta ba wallahi. Nace saboda may zai mun hadi yace khadija kin san kuwa kece mukee son kizama weapon din mu wurin yakan buzuwa nan gaba. Don Allah ki dinga sausautar harshen ki gare shi nace wa ni ni ina ruwa da shi da zan zama muku makami a gare shi da buzuwan shi. Dariya yayi yace ke ko ke dashi khadija ke da komai da zaki yakar muna buzuwa don kin cancanci yin hakan. Ni din yayana yace kwarai kuwa kauna na sai dai idan mun hadu zan maki bayani yadda zaki gane nace to shike nan tunda haka ka fada yace bani na fada ba umurni nima aka bani kan hakan . Yace sai dai idan mun hadu din zan maki bayanin komai nace Allah ya kaimu ina saurarenka da haka muka yi sallama dashi ya barni da tulin tunane a zuciyana. Da safe zarah ce take buga min kofa jin bugun kofan na tashi na bude daki tana tsaye kofan dakin nawa ganin tana son shigowa na bata hanya ta shiga daga ciki. Tambaya na tayi ko da safe zan fita nace ai kemakin sani yanzu haka shiri nakeyi kada in makara take cewa dani zata fita amma wai za a kawo mata sako shine take son in karba. Nace zarah fitan kuma zakiyi yanzu tayi dan guntun tsaki tana fadin eh wani friend dina zaiyi tafiya nake son inje muyi sallama dashi. Zarah ba zaki wankan ki fada ki zauna ki abinda iyayyenn mu suka kawo mu yi ba wanan dabiar da kika dauko bai da amfani gare ki nan gaba. Ta dan yi murmushi ta nufi wurin da taga na aje plate din abin ci da tukunya tana bude bayan ta bude ta dago tana dariya tace an fada maki yadda bakin san wayen kai ba haka kowa yake yanzu da anganki kamar may wayayen kai . Nace in dai irin wanan wayen wane kada Allah ya nufe ni da yin shi ina neman tsarin Allah ga irin wanan dabian naku Allah kuma ya shirye ku ku gane gaskiya. Ta juya ta debi arish a plate ta zauna ta fara ci ni kuma ina ta shirina nace kiyi ki gama gada ki makarar dani anan don banson in makara. Tayi murmushi tana kai abinci a bakin ta sai da ta hade tace wanan halin naki na ina kika fito karatu ina zaki karatu sai ke khadija. Khady look at you me kika rasa ke kanki jarin kanki ne amma kin tsaya kina wahal da kanki haka har kina wani girki tunda safe kamar wata matar aure amma waike nacin karatu sai wahala kike haka. Wallahi da zaki yarda akwai wanda zan hada ki dashi cikin kwana biyu kiyi clean ke baki daukan misali a kwaina khady da haka nake ? Amma yanzu gani tunda hanya ya bude min mai na rasa na rayuwa atare da ni amma ke gaki da abin kawo kudi kina ta faman kumshe shi a jikin ki ta fada tana dariyan shakiyanci. Ni dai ina tsaye ina mata kallon mamaki da huduban shedan da take min har kuryan dakina ta dauka nasihan ta ya na shigana ne ganin yadda na tsaya ina kallon ta. Tace ina son ki fahimci wani abu tsarin rayuwa yanzu ya canza ki shigo kawai a dama dake yarinya. Nace cikin murmushi zarah baki fance ni batsarin rayuwa ta daban yake da naki ban sanya ma zuciyana kwadayi ko son jin dadi a ko wani irin yanayi ba don haka kada kiyi tsammanin guntun huduban ki zaiyi tasiri a raina . Ni da kika ganin nan ina da mutunci na kuma nasan ciwon kaina dana iyayyena kada kiyi tsammanin kananan kwarin da kike bi zasu iya rudana da wani abu. Shi jin dadi lokaci indan lokaci yayi sai inji amma ba ta hanyar wullakata kai yadda kukeyi din nan ba kema idan da zakiji sharata da kin watsar da wanan rayuwan ki rungumi abinda ya kawo ki Abuja. Su kansu mazan da kuke bi aida karatun suke amfana yanzu bance maki ban saurayi ko rayuwa ba sai dai in gajarce maki ni indan zanyi mai tsabta da sanin ciwon kai zanyi amma bana kwanan gida irin naku ba. Baki zarah ta tabe min tana dariya ta saba da nasihana kullun wanda ita a ganin ta ni har yanzu ban waye ba ban san ciwon kaina ba bansan ta kan duniya ba kuma. Nace keyi dariya amma ni idan zan faso gari ba irin wa yan nan kanana kwari masu gurbata rayuwa zan tsaya dububa ba sai wanda ya san kanshi da mutuncin kanshi. Ta mike bayan ta gama ci dama ina magana ina kallon agogona ne kada in makara tace ina son ki fahince ni a yanzu ba a samun irin wa yan nan mazan da kike hasashe kinga ko zaki shawa wuya wurin neman su. A naki ganin ke nan zarah amma muna nan dake zakice na fada maki watarana ta miko min key din ta nace kenan yauma till down zakiyi tace yo may za a fasa kuma. Ta fita na rufo kofana muka fito tare da ita a titi muka raba hanya tana neman lift ni kuma na nufi cikin makaranta ina mamakin wanan rayuwa da zarah ta daukan ma kanta. Itama yar minna ce kama na dalilin haduwan mu ke nan da ita don ko a minnan ba unguwa daya muke ba su suna zama a cancaga ne ni kuma muna tsakiyan gari. Kasancewar mu yan gari daya yasa muka zama kamar yan uwa da ita da farko halin ta mai kyaune kafin idon ta ya bude da bin mazan abuja. Sai lokacin muka raba hannu da ita amma hakan baisa mun daina kula junan mu ba kamar baya sai dai ban taba yarda naci abinda take samuwa ba daga wurin yawon banzanta ba. Tun abin na damun ta har yazo ya daina damun ta ta daina ba sai wanan da iyayyen ta suka kulla suka aiko mata yanzun tana ganin tafi karfin shi ita shine ta kawo min inyi amfani dashi. Tun asuba yake tayar da ita ta tashi tayi sallah amma tana kwance tana barcin ta har yagaji yatayar da ita da karfin tsiya ta zauna tana mustsukan ido alaman barcin bai isheta ba har lokacin yana ganin ta tashine yasa shi fita daga dakin azaton shi zata tashi tayi sallah. Ya fita zuwa dakin motsa jikin shi da yakeyi duk safe inda kuma yake aje wasu kayan amfanin shi jiya anan yabar wayan shi yana canji ya je ya kwanta yana tunanen rashin son ibadan da batayi. Ya gama komai na motsa jiki da yakanyi da safe ya wuce zuwa inda wayan shi yake jone ya dauko din ka idan shine sai takwas yake bude waya da safe. Budan wayan yasa sakon da suka taru mai shigowa ya gane su wanda farko budewa nawa ne ya shigo da farkon. Mamaki yayi don ba suna sai lamba ga dogon sako kuma da maishi ya turo mashi kamar kada ya karanta tunda baisan mai sakon ba sai kuma wata zuciya tace dashi karanta kaji mana abinda sakon ya kumsa kila mai amfani ne gare ka. Fara karanta sakon ne yaji ranshi ya baci don ya fahinci inda sakon ya fito don ganin farkon rubutun nawa kamar haka Mijin buzuwa a zaton ka zaka iya rabani da hajiya mamane ko ka zubar min da mutucina da take gani kayi kuskure wallahi kuma kayi karya don bakina da naka ban fada ma hajiya mama tana gida an mata rasuwa ba. Ga wanda yasan mutuncinta yasan darajan ta na fadawa shida ya tambaye ni ko ina da labarin su bakai da buzuwa wace bata da daraja da galihu tasa ka zubar da matan ka da yayan ka da kowa naka kana ganin tsohuwar buzuwa tana maka rudi da huduban shedan kullun. Kai bari ma kaji wallahi wanan buzuwar ta zubar ma da kima da komai naka a idon duniya tunda kiri kiri ta mai dakai mijin hajiya. Ga mutum har mutum amma baida ta cewa saboda mace macen kuma buzuwa wace bata san Allah how dear you kaida mace bata bari ka zauna dako matar sunnan ka har kake da bakin yi mun hadi a wurin mama, , , , Jikin shi har rawa yakeyi da yake karata text din kasa kai kashen rubutun daki ya nufa da sauri da zuman ya shiga yai wanka ya fita ya samu Yusuf shida yaja mashi rene da wullakanci wurin yar karamar yarinya harta iya turo mashi text din banza haka. Sai yayi magani na a garin sai yasa na raina kaina may nike dashi may nake takama dashi da zan iya yimai cin fuska haka ina aibanta shi shi da matar shi. Waya ya fada min maganan da sukayi da hajiyan su hajiyan ne zata fada min kowa komai dai may nene sai ya rena min wayo sai na gane banda wayo yau a garin nan duk inda na shige sai ya tononi a cikin garin nan yayi min wulkanci Sai dai yana shiga dakin su kuma sai bacin ran nashi ya karu ganin Nafisa kwance tana barcin ta hankali kwace rashi ne ya kara baci ya tuna abinda nace a text dina. Bai san lokacin da ya isa wurin ta yakai mata mugun maka a tsakar bayan ta ba ta mike firgigit tana fadin Samad may nayi maka ? Tsawa ya daka mata yace wanan abin zai hada ni dake ke sai yaushe ne zaki rike ibada a zuciyar ki ne yaja tsuki ya shige wanka. Da sauri ya watsa ya fito ranan ya fito bai wani dauki dogon lokaci ba ya shirya ya fita daga gidan koda ta fito ta samu baya gidan. Tun a mota ya kira Yusuf yana fadin kana inane yanzu? Gani gidana ya bashi amsa OK kajirani ganin zuwa yanzu gidan yace eh mamaki Yusuf yaji yana tunanen mai zai kawo Samad gidan shi wanan lokacin haka. Don ka idar shine sai takwas yake fitowa ko takwas da rabi ware hannu yayi alaman shi ya sani ya mike ya shiga wanka kada yai mashi girshi. Yana shiri ya sake bugo mai waya gashi kofa gidan shi ya fito ya karasa ya fito ya samay shi don ko driver bai fito dashi ba Yusuf din na gani haka ya rufo gidan nashi ya fito ya samay shi. Anan ya bude mai mota ya shiga yarufe sai ya dauki hanya batare da yasan inda zasu nufa ba sai yaga ya miki mashi wayan shi duban wayan yake da mamaki yake fadin na maye wanan kuma ? Ka duba mana cewa fuska a daure ya karbi wayan ya fara karantawa a hankali yana sake murmushi ya gaba yana mika mai wayan yace kai amma wanan yarinyar takai jaruma wallahi haduwan zai zama abin shaawa ga mai kallo. May ne kace yanzun kai baka ga abin jin haushi ba a nan yace ban gani ba sai ma wani abin da na hango na daban tsakanin ka da beauty din. Yau sai nanu namata ita ba kowa bane a garin nan sai na wullakanta ta a garin nan dariya yayi sosai yace da kaima kan ka wallahi da ka tozarta kan kuwa. Wai kaiko kaga yadda kukai balain dacewa da yarinyar nan kuwa wallahi ni abin naku burgeni yake yi idan kuna yi har wani dadi nake ji. May kake nufi ne wai yace abinda idona ya hango min mana a kai saidai fatan alheri amma zancen ka ci mata mutunci bai taso ba ko kaje ka tozartata duk ba wanan a tsakanin ku ko kamanta da hikimar hajiya na hada ka da wanan yarinyar ne ko kana nufin kai baka gane hakan ba. To bari kaji Khadija itace zata iya fitar dakai daga zargin da ake maka na cewa Nafisa ta gama dakai da cewan da ake saboda ita ka kasa zama da Fati. Akan wani dalili zata fitar dani ta yaya din zata fitar dani yace muje zuwa nan gaba zaka sani idan lokacin hakan yayi yanzo ina zamu ne kadauko ni tunda safe haka. Wurin ta zamu in gwada mata ita din ba kowa bace ya kwashe mai da dariya yace ta zama kowan ke nan tunda har zaka iya biye ma shirmay ta na mata. Bai kara magana ba sai juya kan motar yayi zuwa office din su ya shige bai tsaya jiran Yusuf din ba. Anan malam musa driver ya tsayar dashi yana fadin yana da magana dashi na siri da yake son suyi a tsakanin su yace da malam sani din wani abu ya faru ne yace eh to sai dai maganan nason siri gaskiya yace dashi babu damuwa kasa may ni a gida da yamma idan mun tashi. Ga haka suka bar zancen da malam sani din sai dai ya barshi da tunane a zuciyar shi ko akan may yake bukatan kebewa dashi bai sani ba ya san dai abune mai muhinmanci sosai. Shiko gogan acikin office maganan da sukayi da Yusuf ne yake ta mashi yawo arai wai zata zama mai garkuwa a kan matsalan shi da Fati da Nafisa ta yaya ma haka zai faru . Nan dai ya watsar da maganan ya ci gaba da aikin dake gaban shi sai dai yanayi yana tuna zancen a zuciyar shi. Kai tsaye da na fito kamar yadda na saba gidan da muke na nufa yau yawan ci basu da lectures sai karan gida ke tashi ko ina a cikin gida. Yunwa nake ji don ban tsaya nayi karin kwarai ba da safe sallah nayi sana fara hada tea na nasha sai da na dan huta a wurin na mike ina sauya kayan jikina. Na saka dan guntun rigan da nake zama a daki dashi gyaran dakin nayi na gyaro ko ina na dakin sai na dora girkin dare don shinkafa da miya nake son yi irin na yan makaranta. Bayan na gama miya na dora shinkafan na koma na zauna a bakin katifa ina tunane zarah ne ta fado min a rai yau in zan lissafa kwananta biyar bata dawo ba. Zarah tana daya daga cikin "ya"ya dake cin amanan iyayyen su don babu inda suka rageta don koba a fada ba zarah tafi gata don sati biyu bai shigewa iyayyen ta basu turo mata da sako ba. Amma duk ta watsar da wanan gatan nata tabi ra,ayin kwadan abin hannun samari wanda ya rufe mata ido a yanzu har yakai ga ta watsar da karatun ta. Ido na lumshe tare da girgiza kaina ina cewa ubangiji katsare mu ka karemu ya Allah kasa mufi karfin zuciyar mu don yanzu rayuwa abin tsorone . Sai gata washe gari ta dawo dakina ta nufa don karban key din ta koda ta shige ban sake mata fuska ba daga inda nake kwance ta tambayi key din ta na nuna mata da hannu kawai ta nufi wurin ta dauka. Harara na bita dashi tana ficewa daga dakin andan jima kadan sai gata ta dawo dakin daga ita sai wani dan guntun tawul da ta daura iya cinyan ta tana tambayana wai ban rage abinci ba in bata. Wani kallo nayi mata nace inda kika fito gantalin ki kwana da kwanaki baki kici abinci bane acan ? Tace kin san yanzu wata yayi nisa ba wani abin kirki ake samu ba sai maneji nace sai ki je gaba ki nema ni banyi abinci ba yau. Ta ce khady yaushe kika fara rowa haka ba halinki bane rowa nace ban dafa ba nace maki ashe karyan iskanci kike yi da zaki dawo kwana da kwanaki hannu empty. Ta dan tsaya jin ganin ban kulataba ina karatuna sai ta fice min daga dakin dagowa nayi nabita da kallon mai kama da harara har tafice daga dakin. Bayan ya gama saurare abinda malam sani ya gaya mashi jikin shi ne yayi sanyi karshe yayi mai godiya tare da jaddada mashi kan kada ya fada ma Nafisa komai ya dai saka ido ga alamarin ta kawai. Bayan fitan shi gidan nine na fado mashi a rai wayana ya kira mun gaisa dayake shi mai son wasa ne nan yajani da wasa wanda bai wuce hiran mijin buzuwa. Yace gobe dai weekend ne ba shiga aji ke nan nace eh sai dai ina son zan fita zuwa wurin wankin kai don ina son gyaran jiki gobe dai. Yace ashe shi gyaran ma sai anje wani guri yin shi dariya yaban don irin zolayar shi nace ana mace ba gyara ne yace kwarai kuwa har in ta san kanta. Karfe nawa zaki ya tambaya nace wuraren goma zan tafi nasan zuwa karfe sha biyu ko da rabi na gama yace da safe banda time da nazo na kaiki sai dai ki fada min sallin din da kike zuwa in duba ki idan na rarage abinda nake yi. Nace No kabarshi kawai ba wani nisa yake dashi da inda muke ba nagode yace aini nace ki fada min ko nace beauty hair drasses na fada mai layin da yake a saman babban titi. Munyi sallama ina mamikin halin shi da saurin sabo irin nashi na zauna na tsefe kaina a cikin daren nan don kada in makara in samu mutane a wurin. Washegari da safe na shirya na isa sallon din ba wasu mutane dayawa don haka nabi layi sai da akawanke min akai min drying din shi kafin su fara min kitso. Ranan nasha gyara sosai na jiki daidai zan fito sai ga wayan Yusuf shigo yana tambayana ina wurin ko wuce nace an kusa gamawa nan da minti talatin zanbar wurin . Nakashe wayan akaci gaba da min gyara sai yaba yawan gashina da tsayi suke yi nidai murmushi kawai nake masu ban wani dogon magana da kowa a wurin. Sun fito daga kubuwa duban fili da sukaje gani a hanyansu na komawa gida yaga Yusuf ya dauki hanya bai iya magana ba yana aiki a system din shi kan shi a duke yake. Sai dai yasan ba hanyan gida Yusuf ya nufa dasu ba aikin da yakeyi ya dauke mashi hankali a lokacin ganin ya tsaya a bakin wani gyaran jiki na mata yasa shi dago kai yana tambayan shi ina ne nan kuma ? Kafin ya bashi amsa yaji yana fadi a wayan shi fito gamu a kofa idan an gama maki nace gani tafe na fito tun fitowa na ya hango nice tafe kallon mamaki yake wa Yusuf din. Har na karaso bakin motar nasu sai a lokacin nasan tare suke dashi fadi yusuf ke yi da na karaso wai wanan haduwa haka fa kanwata . Kaike kara zuzuta yayi maganar kamar bashi ya fada ba yace ba dole ba in zuzuta kanwata yar gidan mama wanan ai kyasa ayi karo a hanya nidai murmushi kawai nayi mashi. Na fara gaida su yace shigo mu sauke ki mana ba hostel zaki koma ba nace a a nagode yayana ku tafi abinku kawai dakai dayane zan shiga amma dai ku tafi kawai. Yace au don wanan miin buzuwan da kika gani ai bashi ke jan motar ba ko shiga muje don ki kawai muka biyo nan fa. Jin haka yasa na bude motar na shiga batare da na sake wani magana ba shiko sai aikin shi yake yi kawai ana tafiya mun kai wurin wani babban shago yace don Allah ku bani minti biyu in dawo. Ya faka motar yafita sai mu biyu a cikin motar kowa da abinda yake yi a lokacin sai can naji yaja tsuki yana kallon shagon na dauka dani yake yi nace dakata malam bafa kai ka dauko ni ba da zaka ja min tsuki haka. Da mamaki ya dago kai yana kallo yace ke dani kike nace da wani nake haka kawai zaka kama jamin tsuki a mota da mamaki yake kallo na yace ke wata irin yarinya ce da bata da tarbiya. Kadai gyara maganan ka malam tarbiya ai ko makaho yasan akwaishi nan sai dai a lalaba a gani ai ba bace marasa tarbiya suke ba. Bai kai karshen magana ba cikin zafin nama da kunar zuciya ya juyo inda nake yace wa kike nufi baida tarbiya cikin muryan nan nashi mai dadin saurare da yake rowan ta. Tsoro naji ganin irin kallon da yake bina dashi mai kama da harara ko tsana sai nayi kasa da kaina na kasa furta komai don kwarjin da yai min a idona Ya nuno yatsan shi daidai saitin fuska na tare da tsure ni da idanuwan shi lumsarsu yana fadin ke in badan Yusuf da bai san ciwon kan shi ba har kucaka irin ki ta isa ta shiga min mota na a tare dani. Yace kallani nan ko a hanya nagan ki baki isheni kallo ba a cikin mata don banga abin gani a wurin irin ki ba cikin dakiya da dauriya nake kallan shi ina jin kalamin shi har cikin raina sai dai ina tara abinda zan mayar mashi ne a zuciya ta duk da naji tsoran yanayin shi. Yaci gaba da fadin idan baki hankali da ni ba watarana sai na balbala ki wallahi don ni mace bata kawo min raini nace dashi. Don Allah malam matsamin bakumayi mamaki jin haka don ba abin mamaki bane don ka fadi hakan tunda dama kai irin maza nan ne dake raina jinsin su sai kai ido ga mata ketere saboda zalama irin na rashin sanin ciwon kai. Don wanan matar taka abin kyama ga jamma a da kai ka mayar mutum har kake ganin tafi ko wace macen kasan nan dadin abin dai kaima macen kasan nan ta haife , , , , Fat naji yakai min bugu a baki don zafi sai da na dafe baki na ina dubawa ko jini yake min ban san lokacin da idona ya fara fitar da hawaye ba na yun kura zan fita daga motar yasa hannu ya danna lock mutar ta rufe kit yace kuma ki saurare ni. Duk kika sake ganina a mota kikayi gigin shigan shi sai ya jefar dake a waje mota ya take ki kin mutum in kashe ki in kashe bazan . Nace ni wallahi ba banzan bace sai dai in kaine yace bakin naki bai mutu bako yana kokarin kai hannun shi ya kamo baki na na noke kaina a kafana sai bai samu kama bakin nawa ba. A daidai lokacin Yusuf ya iso wurin da manyan ledoji a hannun shi yana bude motan zai sa ganin mu haka yasa shi ya sake murmushi. Ina jin shi nayi saurin dago kai nace mugu kawai azzalumi yace kai yaya haka may kai mata don Allah take kuka kuma ya waigo zai kara jamin baki na noke ina son fita a motan Yusuf ya tare ni yana fadin haba dai yaya zakaci zalun ta kuma haka ? May tayi maka haka wai kasa ta kuka ya juya yana cewa bakin nan mai rashin kunya na daka ido ya zaro yana cewa ka dake ta Abdul ? Kadan ma ke nan nayi mata ai fita nake son yi ba hanya don Yusuf dake wurin yayi rufe kofan ya zagaya ya shigo motar sai da muka fara tafiya yace ka bata hakkuri Abdul. Ina baya ina kuka naji ya fada mai hakan yace nace ka bata hakkuri yace wani zanba wanan yariyar hakuri ko wa yace bakai ka zalunce ta don may bazaka bata hakkuri ba ko kafin ka tafi da hakkin ta ne a kanka ? Baiyi magana ba sai aikin shi dayaci gaba dayi yace wai may ya hada kune haka da sauri nace zagina yayi na rama. Motar ya tsaya a kofa gidajen mu na fita da sauri ya biyo ni yana kirana ban tsaya ba wata yar gidan yaba kayan ta shigo min dasu suka tafi ban san yadda suka karata ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Bayan mun gama waya da ita naji raina ya baci sai a lokacin na gode ma Allah da ban goge number shi ba a wayana kira nayi har sau biyu bai daga ba sai na tura mashi sako masu zafi na kashe wayan. Don nasan zai gani da safe in ma kwanciya yayi a lokacin haka yasa na danji zafin da nake ji ya rage min da kyat barci ya dauke ni a ranan. Har na rufe ido sai nayi wayana yana kara na dauka a zatona shine yaga sakona ya kira wayan sai dai ba number daya kirani daya kira dashi bane. Nace ummhumm ina jin ka naji ance haka ake karba kiran wanda baka sani ba na sheda muryan Yusuf din nace yayana kaine a na dauka wani ne. Yace nice injin ruwa bai saki jin zazzabi ba dariya nayi nace ai na watsa ruwan zafi a jikina yace good dama na kiraki ne don mutumin ki ya karbi number ki a hannu na nasan zai iya kiranki kada ki biye ma halinshi don Allah don bansan abinda zai kiraki ya fada maki ba koda yake yace akan maganan hajiya mama zai kiraki yaji don Allah , , , Na katse shi da fadin ai ya kirani ko har munyi tsiyan shi ya dauka kowa nema yake a gare shi ko yaushe ni kuma na wanke shi tass. Da karfi naji yace haba don Allah nace wallahi na kwashe komai na fada mai har text din da na tura mai mai zafi yace amma baki kyauta ba wallahi. Nace saboda may zai mun hadi yace khadija kin san kuwa kece mukee son kizama weapon din mu wurin yakan buzuwa nan gaba. Don Allah ki dinga sausautar harshen ki gare shi nace wa ni ni ina ruwa da shi da zan zama muku makami a gare shi da buzuwan shi. Dariya yayi yace ke ko ke dashi khadija ke da komai da zaki yakar muna buzuwa don kin cancanci yin hakan. Ni din yayana yace kwarai kuwa kauna na sai dai idan mun hadu zan maki bayani yadda zaki gane nace to shike nan tunda haka ka fada yace bani na fada ba umurni nima aka bani kan hakan . Yace sai dai idan mun hadu din zan maki bayanin komai nace Allah ya kaimu ina saurarenka da haka muka yi sallama dashi ya barni da tulin tunane a zuciyana. Da safe zarah ce take buga min kofa jin bugun kofan na tashi na bude daki tana tsaye kofan dakin nawa ganin tana son shigowa na bata hanya ta shiga daga ciki. Tambaya na tayi ko da safe zan fita nace ai kemakin sani yanzu haka shiri nakeyi kada in makara take cewa dani zata fita amma wai za a kawo mata sako shine take son in karba. Nace zarah fitan kuma zakiyi yanzu tayi dan guntun tsaki tana fadin eh wani friend dina zaiyi tafiya nake son inje muyi sallama dashi. Zarah ba zaki wankan ki fada ki zauna ki abinda iyayyenn mu suka kawo mu yi ba wanan dabiar da kika dauko bai da amfani gare ki nan gaba. Ta dan yi murmushi ta nufi wurin da taga na aje plate din abin ci da tukunya tana bude bayan ta bude ta dago tana dariya tace an fada maki yadda bakin san wayen kai ba haka kowa yake yanzu da anganki kamar may wayayen kai . Nace in dai irin wanan wayen wane kada Allah ya nufe ni da yin shi ina neman tsarin Allah ga irin wanan dabian naku Allah kuma ya shirye ku ku gane gaskiya. Ta juya ta debi arish a plate ta zauna ta fara ci ni kuma ina ta shirina nace kiyi ki gama gada ki makarar dani anan don banson in makara. Tayi murmushi tana kai abinci a bakin ta sai da ta hade tace wanan halin naki na ina kika fito karatu ina zaki karatu sai ke khadija. Khady look at you me kika rasa ke kanki jarin kanki ne amma kin tsaya kina wahal da kanki haka har kina wani girki tunda safe kamar wata matar aure amma waike nacin karatu sai wahala kike haka. Wallahi da zaki yarda akwai wanda zan hada ki dashi cikin kwana biyu kiyi clean ke baki daukan misali a kwaina khady da haka nake ? Amma yanzu gani tunda hanya ya bude min mai na rasa na rayuwa atare da ni amma ke gaki da abin kawo kudi kina ta faman kumshe shi a jikin ki ta fada tana dariyan shakiyanci. Ni dai ina tsaye ina mata kallon mamaki da huduban shedan da take min har kuryan dakina ta dauka nasihan ta ya na shigana ne ganin yadda na tsaya ina kallon ta. Tace ina son ki fahimci wani abu tsarin rayuwa yanzu ya canza ki shigo kawai a dama dake yarinya. Nace cikin murmushi zarah baki fance ni batsarin rayuwa ta daban yake da naki ban sanya ma zuciyana kwadayi ko son jin dadi a ko wani irin yanayi ba don haka kada kiyi tsammanin guntun huduban ki zaiyi tasiri a raina . Ni da kika ganin nan ina da mutunci na kuma nasan ciwon kaina dana iyayyena kada kiyi tsammanin kananan kwarin da kike bi zasu iya rudana da wani abu. Shi jin dadi lokaci indan lokaci yayi sai inji amma ba ta hanyar wullakata kai yadda kukeyi din nan ba kema idan da zakiji sharata da kin watsar da wanan rayuwan ki rungumi abinda ya kawo ki Abuja. Su kansu mazan da kuke bi aida karatun suke amfana yanzu bance maki ban saurayi ko rayuwa ba sai dai in gajarce maki ni indan zanyi mai tsabta da sanin ciwon kai zanyi amma bana kwanan gida irin naku ba. Baki zarah ta tabe min tana dariya ta saba da nasihana kullun wanda ita a ganin ta ni har yanzu ban waye ba ban san ciwon kaina ba bansan ta kan duniya ba kuma. Nace keyi dariya amma ni idan zan faso gari ba irin wa yan nan kanana kwari masu gurbata rayuwa zan tsaya dububa ba sai wanda ya san kanshi da mutuncin kanshi. Ta mike bayan ta gama ci dama ina magana ina kallon agogona ne kada in makara tace ina son ki fahince ni a yanzu ba a samun irin wa yan nan mazan da kike hasashe kinga ko zaki shawa wuya wurin neman su. A naki ganin ke nan zarah amma muna nan dake zakice na fada maki watarana ta miko min key din ta nace kenan yauma till down zakiyi tace yo may za a fasa kuma. Ta fita na rufo kofana muka fito tare da ita a titi muka raba hanya tana neman lift ni kuma na nufi cikin makaranta ina mamakin wanan rayuwa da zarah ta daukan ma kanta. Itama yar minna ce kama na dalilin haduwan mu ke nan da ita don ko a minnan ba unguwa daya muke ba su suna zama a cancaga ne ni kuma muna tsakiyan gari. Kasancewar mu yan gari daya yasa muka zama kamar yan uwa da ita da farko halin ta mai kyaune kafin idon ta ya bude da bin mazan abuja. Sai lokacin muka raba hannu da ita amma hakan baisa mun daina kula junan mu ba kamar baya sai dai ban taba yarda naci abinda take samuwa ba daga wurin yawon banzanta ba. Tun abin na damun ta har yazo ya daina damun ta ta daina ba sai wanan da iyayyen ta suka kulla suka aiko mata yanzun tana ganin tafi karfin shi ita shine ta kawo min inyi amfani dashi. Tun asuba yake tayar da ita ta tashi tayi sallah amma tana kwance tana barcin ta har yagaji yatayar da ita da karfin tsiya ta zauna tana mustsukan ido alaman barcin bai isheta ba har lokacin yana ganin ta tashine yasa shi fita daga dakin azaton shi zata tashi tayi sallah. Ya fita zuwa dakin motsa jikin shi da yakeyi duk safe inda kuma yake aje wasu kayan amfanin shi jiya anan yabar wayan shi yana canji ya je ya kwanta yana tunanen rashin son ibadan da batayi. Ya gama komai na motsa jiki da yakanyi da safe ya wuce zuwa inda wayan shi yake jone ya dauko din ka idan shine sai takwas yake bude waya da safe. Budan wayan yasa sakon da suka taru mai shigowa ya gane su wanda farko budewa nawa ne ya shigo da farkon. Mamaki yayi don ba suna sai lamba ga dogon sako kuma da maishi ya turo mashi kamar kada ya karanta tunda baisan mai sakon ba sai kuma wata zuciya tace dashi karanta kaji mana abinda sakon ya kumsa kila mai amfani ne gare ka. Fara karanta sakon ne yaji ranshi ya baci don ya fahinci inda sakon ya fito don ganin farkon rubutun nawa kamar haka Mijin buzuwa a zaton ka zaka iya rabani da hajiya mamane ko ka zubar min da mutucina da take gani kayi kuskure wallahi kuma kayi karya don bakina da naka ban fada ma hajiya mama tana gida an mata rasuwa ba. Ga wanda yasan mutuncinta yasan darajan ta na fadawa shida ya tambaye ni ko ina da labarin su bakai da buzuwa wace bata da daraja da galihu tasa ka zubar da matan ka da yayan ka da kowa naka kana ganin tsohuwar buzuwa tana maka rudi da huduban shedan kullun. Kai bari ma kaji wallahi wanan buzuwar ta zubar ma da kima da komai naka a idon duniya tunda kiri kiri ta mai dakai mijin hajiya. Ga mutum har mutum amma baida ta cewa saboda mace macen kuma buzuwa wace bata san Allah how dear you kaida mace bata bari ka zauna dako matar sunnan ka har kake da bakin yi mun hadi a wurin mama, , , , Jikin shi har rawa yakeyi da yake karata text din kasa kai kashen rubutun daki ya nufa da sauri da zuman ya shiga yai wanka ya fita ya samu Yusuf shida yaja mashi rene da wullakanci wurin yar karamar yarinya harta iya turo mashi text din banza haka. Sai yayi magani na a garin sai yasa na raina kaina may nike dashi may nake takama dashi da zan iya yimai cin fuska haka ina aibanta shi shi da matar shi. Waya ya fada min maganan da sukayi da hajiyan su hajiyan ne zata fada min kowa komai dai may nene sai ya rena min wayo sai na gane banda wayo yau a garin nan duk inda na shige sai ya tononi a cikin garin nan yayi min wulkanci Sai dai yana shiga dakin su kuma sai bacin ran nashi ya karu ganin Nafisa kwance tana barcin ta hankali kwace rashi ne ya kara baci ya tuna abinda nace a text dina. Bai san lokacin da ya isa wurin ta yakai mata mugun maka a tsakar bayan ta ba ta mike firgigit tana fadin Samad may nayi maka ? Tsawa ya daka mata yace wanan abin zai hada ni dake ke sai yaushe ne zaki rike ibada a zuciyar ki ne yaja tsuki ya shige wanka. Da sauri ya watsa ya fito ranan ya fito bai wani dauki dogon lokaci ba ya shirya ya fita daga gidan koda ta fito ta samu baya gidan. Tun a mota ya kira Yusuf yana fadin kana inane yanzu? Gani gidana ya bashi amsa OK kajirani ganin zuwa yanzu gidan yace eh mamaki Yusuf yaji yana tunanen mai zai kawo Samad gidan shi wanan lokacin haka. Don ka idar shine sai takwas yake fitowa ko takwas da rabi ware hannu yayi alaman shi ya sani ya mike ya shiga wanka kada yai mashi girshi. Yana shiri ya sake bugo mai waya gashi kofa gidan shi ya fito ya karasa ya fito ya samay shi don ko driver bai fito dashi ba Yusuf din na gani haka ya rufo gidan nashi ya fito ya samay shi. Anan ya bude mai mota ya shiga yarufe sai ya dauki hanya batare da yasan inda zasu nufa ba sai yaga ya miki mashi wayan shi duban wayan yake da mamaki yake fadin na maye wanan kuma ? Ka duba mana cewa fuska a daure ya karbi wayan ya fara karantawa a hankali yana sake murmushi ya gaba yana mika mai wayan yace kai amma wanan yarinyar takai jaruma wallahi haduwan zai zama abin shaawa ga mai kallo. May ne kace yanzun kai baka ga abin jin haushi ba a nan yace ban gani ba sai ma wani abin da na hango na daban tsakanin ka da beauty din. Yau sai nanu namata ita ba kowa bane a garin nan sai na wullakanta ta a garin nan dariya yayi sosai yace da kaima kan ka wallahi da ka tozarta kan kuwa. Wai kaiko kaga yadda kukai balain dacewa da yarinyar nan kuwa wallahi ni abin naku burgeni yake yi idan kuna yi har wani dadi nake ji. May kake nufi ne wai yace abinda idona ya hango min mana a kai saidai fatan alheri amma zancen ka ci mata mutunci bai taso ba ko kaje ka tozartata duk ba wanan a tsakanin ku ko kamanta da hikimar hajiya na hada ka da wanan yarinyar ne ko kana nufin kai baka gane hakan ba. To bari kaji Khadija itace zata iya fitar dakai daga zargin da ake maka na cewa Nafisa ta gama dakai da cewan da ake saboda ita ka kasa zama da Fati. Akan wani dalili zata fitar dani ta yaya din zata fitar dani yace muje zuwa nan gaba zaka sani idan lokacin hakan yayi yanzo ina zamu ne kadauko ni tunda safe haka. Wurin ta zamu in gwada mata ita din ba kowa bace ya kwashe mai da dariya yace ta zama kowan ke nan tunda har zaka iya biye ma shirmay ta na mata. Bai kara magana ba sai juya kan motar yayi zuwa office din su ya shige bai tsaya jiran Yusuf din ba. Anan malam musa driver ya tsayar dashi yana fadin yana da magana dashi na siri da yake son suyi a tsakanin su yace da malam sani din wani abu ya faru ne yace eh to sai dai maganan nason siri gaskiya yace dashi babu damuwa kasa may ni a gida da yamma idan mun tashi. Ga haka suka bar zancen da malam sani din sai dai ya barshi da tunane a zuciyar shi ko akan may yake bukatan kebewa dashi bai sani ba ya san dai abune mai muhinmanci sosai. Shiko gogan acikin office maganan da sukayi da Yusuf ne yake ta mashi yawo arai wai zata zama mai garkuwa a kan matsalan shi da Fati da Nafisa ta yaya ma haka zai faru . Nan dai ya watsar da maganan ya ci gaba da aikin dake gaban shi sai dai yanayi yana tuna zancen a zuciyar shi. Kai tsaye da na fito kamar yadda na saba gidan da muke na nufa yau yawan ci basu da lectures sai karan gida ke tashi ko ina a cikin gida. Yunwa nake ji don ban tsaya nayi karin kwarai ba da safe sallah nayi sana fara hada tea na nasha sai da na dan huta a wurin na mike ina sauya kayan jikina. Na saka dan guntun rigan da nake zama a daki dashi gyaran dakin nayi na gyaro ko ina na dakin sai na dora girkin dare don shinkafa da miya nake son yi irin na yan makaranta. Bayan na gama miya na dora shinkafan na koma na zauna a bakin katifa ina tunane zarah ne ta fado min a rai yau in zan lissafa kwananta biyar bata dawo ba. Zarah tana daya daga cikin "ya"ya dake cin amanan iyayyen su don babu inda suka rageta don koba a fada ba zarah tafi gata don sati biyu bai shigewa iyayyen ta basu turo mata da sako ba. Amma duk ta watsar da wanan gatan nata tabi ra,ayin kwadan abin hannun samari wanda ya rufe mata ido a yanzu har yakai ga ta watsar da karatun ta. Ido na lumshe tare da girgiza kaina ina cewa ubangiji katsare mu ka karemu ya Allah kasa mufi karfin zuciyar mu don yanzu rayuwa abin tsorone . Sai gata washe gari ta dawo dakina ta nufa don karban key din ta koda ta shige ban sake mata fuska ba daga inda nake kwance ta tambayi key din ta na nuna mata da hannu kawai ta nufi wurin ta dauka. Harara na bita dashi tana ficewa daga dakin andan jima kadan sai gata ta dawo dakin daga ita sai wani dan guntun tawul da ta daura iya cinyan ta tana tambayana wai ban rage abinci ba in bata. Wani kallo nayi mata nace inda kika fito gantalin ki kwana da kwanaki baki kici abinci bane acan ? Tace kin san yanzu wata yayi nisa ba wani abin kirki ake samu ba sai maneji nace sai ki je gaba ki nema ni banyi abinci ba yau. Ta ce khady yaushe kika fara rowa haka ba halinki bane rowa nace ban dafa ba nace maki ashe karyan iskanci kike yi da zaki dawo kwana da kwanaki hannu empty. Ta dan tsaya jin ganin ban kulataba ina karatuna sai ta fice min daga dakin dagowa nayi nabita da kallon mai kama da harara har tafice daga dakin. Bayan ya gama saurare abinda malam sani ya gaya mashi jikin shi ne yayi sanyi karshe yayi mai godiya tare da jaddada mashi kan kada ya fada ma Nafisa komai ya dai saka ido ga alamarin ta kawai. Bayan fitan shi gidan nine na fado mashi a rai wayana ya kira mun gaisa dayake shi mai son wasa ne nan yajani da wasa wanda bai wuce hiran mijin buzuwa. Yace gobe dai weekend ne ba shiga aji ke nan nace eh sai dai ina son zan fita zuwa wurin wankin kai don ina son gyaran jiki gobe dai. Yace ashe shi gyaran ma sai anje wani guri yin shi dariya yaban don irin zolayar shi nace ana mace ba gyara ne yace kwarai kuwa har in ta san kanta. Karfe nawa zaki ya tambaya nace wuraren goma zan tafi nasan zuwa karfe sha biyu ko da rabi na gama yace da safe banda time da nazo na kaiki sai dai ki fada min sallin din da kike zuwa in duba ki idan na rarage abinda nake yi. Nace No kabarshi kawai ba wani nisa yake dashi da inda muke ba nagode yace aini nace ki fada min ko nace beauty hair drasses na fada mai layin da yake a saman babban titi. Munyi sallama ina mamikin halin shi da saurin sabo irin nashi na zauna na tsefe kaina a cikin daren nan don kada in makara in samu mutane a wurin. Washegari da safe na shirya na isa sallon din ba wasu mutane dayawa don haka nabi layi sai da akawanke min akai min drying din shi kafin su fara min kitso. Ranan nasha gyara sosai na jiki daidai zan fito sai ga wayan Yusuf shigo yana tambayana ina wurin ko wuce nace an kusa gamawa nan da minti talatin zanbar wurin . Nakashe wayan akaci gaba da min gyara sai yaba yawan gashina da tsayi suke yi nidai murmushi kawai nake masu ban wani dogon magana da kowa a wurin. Sun fito daga kubuwa duban fili da sukaje gani a hanyansu na komawa gida yaga Yusuf ya dauki hanya bai iya magana ba yana aiki a system din shi kan shi a duke yake. Sai dai yasan ba hanyan gida Yusuf ya nufa dasu ba aikin da yakeyi ya dauke mashi hankali a lokacin ganin ya tsaya a bakin wani gyaran jiki na mata yasa shi dago kai yana tambayan shi ina ne nan kuma ? Kafin ya bashi amsa yaji yana fadi a wayan shi fito gamu a kofa idan an gama maki nace gani tafe na fito tun fitowa na ya hango nice tafe kallon mamaki yake wa Yusuf din. Har na karaso bakin motar nasu sai a lokacin nasan tare suke dashi fadi yusuf ke yi da na karaso wai wanan haduwa haka fa kanwata . Kaike kara zuzuta yayi maganar kamar bashi ya fada ba yace ba dole ba in zuzuta kanwata yar gidan mama wanan ai kyasa ayi karo a hanya nidai murmushi kawai nayi mashi. Na fara gaida su yace shigo mu sauke ki mana ba hostel zaki koma ba nace a a nagode yayana ku tafi abinku kawai dakai dayane zan shiga amma dai ku tafi kawai. Yace au don wanan miin buzuwan da kika gani ai bashi ke jan motar ba ko shiga muje don ki kawai muka biyo nan fa. Jin haka yasa na bude motar na shiga batare da na sake wani magana ba shiko sai aikin shi yake yi kawai ana tafiya mun kai wurin wani babban shago yace don Allah ku bani minti biyu in dawo. Ya faka motar yafita sai mu biyu a cikin motar kowa da abinda yake yi a lokacin sai can naji yaja tsuki yana kallon shagon na dauka dani yake yi nace dakata malam bafa kai ka dauko ni ba da zaka ja min tsuki haka. Da mamaki ya dago kai yana kallo yace ke dani kike nace da wani nake haka kawai zaka kama jamin tsuki a mota da mamaki yake kallo na yace ke wata irin yarinya ce da bata da tarbiya. Kadai gyara maganan ka malam tarbiya ai ko makaho yasan akwaishi nan sai dai a lalaba a gani ai ba bace marasa tarbiya suke ba. Bai kai karshen magana ba cikin zafin nama da kunar zuciya ya juyo inda nake yace wa kike nufi baida tarbiya cikin muryan nan nashi mai dadin saurare da yake rowan ta. Tsoro naji ganin irin kallon da yake bina dashi mai kama da harara ko tsana sai nayi kasa da kaina na kasa furta komai don kwarjin da yai min a idona Ya nuno yatsan shi daidai saitin fuska na tare da tsure ni da idanuwan shi lumsarsu yana fadin ke in badan Yusuf da bai san ciwon kan shi ba har kucaka irin ki ta isa ta shiga min mota na a tare dani. Yace kallani nan ko a hanya nagan ki baki isheni kallo ba a cikin mata don banga abin gani a wurin irin ki ba cikin dakiya da dauriya nake kallan shi ina jin kalamin shi har cikin raina sai dai ina tara abinda zan mayar mashi ne a zuciya ta duk da naji tsoran yanayin shi. Yaci gaba da fadin idan baki hankali da ni ba watarana sai na balbala ki wallahi don ni mace bata kawo min raini nace dashi. Don Allah malam matsamin bakumayi mamaki jin haka don ba abin mamaki bane don ka fadi hakan tunda dama kai irin maza nan ne dake raina jinsin su sai kai ido ga mata ketere saboda zalama irin na rashin sanin ciwon kai. Don wanan matar taka abin kyama ga jamma a da kai ka mayar mutum har kake ganin tafi ko wace macen kasan nan dadin abin dai kaima macen kasan nan ta haife , , , , Fat naji yakai min bugu a baki don zafi sai da na dafe baki na ina dubawa ko jini yake min ban san lokacin da idona ya fara fitar da hawaye ba na yun kura zan fita daga motar yasa hannu ya danna lock mutar ta rufe kit yace kuma ki saurare ni. Duk kika sake ganina a mota kikayi gigin shigan shi sai ya jefar dake a waje mota ya take ki kin mutum in kashe ki in kashe bazan . Nace ni wallahi ba banzan bace sai dai in kaine yace bakin naki bai mutu bako yana kokarin kai hannun shi ya kamo baki na na noke kaina a kafana sai bai samu kama bakin nawa ba. A daidai lokacin Yusuf ya iso wurin da manyan ledoji a hannun shi yana bude motan zai sa ganin mu haka yasa shi ya sake murmushi. Ina jin shi nayi saurin dago kai nace mugu kawai azzalumi yace kai yaya haka may kai mata don Allah take kuka kuma ya waigo zai kara jamin baki na noke ina son fita a motan Yusuf ya tare ni yana fadin haba dai yaya zakaci zalun ta kuma haka ? May tayi maka haka wai kasa ta kuka ya juya yana cewa bakin nan mai rashin kunya na daka ido ya zaro yana cewa ka dake ta Abdul ? Kadan ma ke nan nayi mata ai fita nake son yi ba hanya don Yusuf dake wurin yayi rufe kofan ya zagaya ya shigo motar sai da muka fara tafiya yace ka bata hakkuri Abdul. Ina baya ina kuka naji ya fada mai hakan yace nace ka bata hakkuri yace wani zanba wanan yariyar hakuri ko wa yace bakai ka zalunce ta don may bazaka bata hakkuri ba ko kafin ka tafi da hakkin ta ne a kanka ? Baiyi magana ba sai aikin shi dayaci gaba dayi yace wai may ya hada kune haka da sauri nace zagina yayi na rama. Motar ya tsaya a kofa gidajen mu na fita da sauri ya biyo ni yana kirana ban tsaya ba wata yar gidan yaba kayan ta shigo min dasu suka tafi ban san yadda suka karata ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: A raina sai mamaki nake wai wanan matashin da nagani wanda bai wuce ace yanzu zaiyi auren farko ba ke da mata har biyu haka. Buzuwan nan dai da za a zauna a fadi gaskiya tana iya girmay mashi daga shi har matar shi sai idan ance yanayin jikin su kawai da ba a gane hakan. Ita kuma Fatin baka ce sai dai da zata zauna ta gyara jikin ta banga abinda buzuwan nan zata gwada mata ba sai dai kasshh yanayi irin namu na matan hausawa yana cin rayuwan ta da haka nake hango buzuwa ta kwace mata miji . Yau da gobe sai Allah dama sati uku zanyi don hutun ba yawa shiyasa ban so zuwa kaduna ba a wanan lokacin amma anty na ta dage sai nazo ita kadai ne a gida mijin ta yayi tafiya. Ashe kuma da rabon mu kwasa da matar mulki ne a garin ya kawoni don haka shiri nake inda ba komai nake shiryawa sai kayana don ban daukan provition da ga gida sai na tafi can nake saya. School zan wuce direct sai nakwana biyu zan shigo mina in masu weekend in kwashi abinda na samu in koma bayan kwana biyu don haka nake ta shirin komawa makaranta a lokacin. Kwatsan da safe muna karyawa saura kwana biyu tafiyana sai ga wayan mommy ta bugo ma anty wai Fati ta dawo gida yanzu haka tana nan gidan su naji anty na fadin o o Allah yanzu matan nan da karfi da yaji sai ta raba wanan auren take nufi. Banji may mommy ta fada mata ba nadaiji tana fadin gaskiya haka nane idan abu yaki sai ayi hakkuri kada zumunci ya baci idan abin ya sake shi inda rabon komawan ta gidan sai ta koma. Bayan ta kashe waya tace mummy tace ki shiga kafin ki wuce kada ki tafi baki sallamay su ba nace haba anty may yasa kika fada mata zan wuce ai sai yazama kamar roko idan naje sallaman su. Kai ta girgiza min tace ba haka halin su yake ba dauka na sukeyi kamar wata ta gida a gurin du duk zuwa kikayi kika wuce sai sunyi min korafin hakan. Shiru nayi sai tace o Allah sarki wanan buzuwan dai ta hana Fati zama gidan mijin wai yanzu kuma ta kara fitowa tace bazata koma ba. Dudufa baifi wata da ta koma gidan na yanzun kuma ta kara fitowa jiya wai sai dai na shiga inji may kuma ya hadasu fada yanzu. Takaici bai barni nayi magana ba sai dai a zuciyana nake bankawa mijin zagi da rana su binta suka shigo gidan mu anan muke jin labari wai tunda ya dawo buzuwa taki bari ya ke be da fati hakan bai isheta taja Fatin da fada har tana fadin sai ta kashe ta. Shiya ba Fati tsoro tace barin gidan yafi mata nace shike nan ta samu galabanta ai ta kashe ta din idan ta isa mana. Gaskiya matan nan ta samu wuri da yawa wallahi nace shiko sokon yayan naku fa may yayi a kai tace jiya baban mu ya kirashi sai cewa yayi shi yagaji da halin fati tana bata mashi suna. Ai wallahi idan da nice tace sai ta kashe ni da na nuna mata hauka ke matsorata ne fa iskancin abaki yake masu kawai Fatin dai ne wallahi she is to slow . Anty tace khadija baki san aure ba fa shi wanda ake abin a kansa bai nuna wani feeling din shi akan ta gara dai da ta hakkura ta basu wuri. Zata tafi nace barin bisu daganan in masu mommy sallama tun ranan da mukai fada da buzuwa ban sake shiga sai yau da zan tafi sallaman su da anty ta matsa min. Tsab na shirya na fito cikin wani dogon riga mai hannu shara shara shara da gyalen shi na yafa akaina sai turaren da na fesa a jikina. Mun shiga gida inda na fara zuwa dakin mama na gaida ita sai na fito naga anty amarya a waje anan na gaida ita har zan wuce tace khadija ashe haka kike ina ganin ki shuru shiru dake ashe ke ma jaruma ce ban sani ba. Dan guntun murmushi nayi nayi kasa da kaina kawai dakin mama na nufa ina jin suna maganan a waje da mai masu aiki na shige wurin mama in gaida ita. Tana zaune a falon ta tana waya haka yasa na samu wuri a kasa gefeta na zauna ta gama wayan ta dago kai cikin fara a tana fadin yau khadija ne gidan nace mama ina kwana. Ta amsa min fuska a sake nace mama nazo in sallamay ku gobe zan koma school tace a a har hutun ya kare wanan karon nace eh mama. Ta sake cewa gida zaki ko Abujan zaki wuce aa zan wuce school ne daga nan tace barin baki tsaraban yan makaranta ko nace mama da ki barshi ai ba zan dauki kaya daga nan ba sai naje can saya. Tace a a wanan kan zaki so dambu ne da akai ma yayan zai tafi dashi kin san yana son dambun nama sosai shine na aikai mashi shima gobe zasu tafi. Ta mike ta shiga daga ciki sai gata da roba dan madaidaici ta fito da kudi a hannun ta ta miko min nayi godiya namike zan fita ko ba a fada ba yanzu na sheda wanan kamshi ba kowa bane sai dan ta Abdulsamad mijin buzuwa. Zai shigo ni kuma zan fita ban yi tunanen in kauce mashi ba a lokacin dole suka jaye a hanyan na fita ashe da buzuwa suke tana bayan shi. Mama ce naji ta kwala min kira sai na dawo wanan karon sai da na bari sun gama shiga na shiga dakin nima na karasa wurin ta gwiwa na biyu a kasa na zube ina fadin mama gani. Buzuwa ke gaida ita ta tsaya amsawa ta dago tana cewa dan ta gobe ne zaku tafi din ko yace insha Allahu mama yanzu ma mun zo mu sallama ku ne don goben sakko muke son yi dan zan shiga office. Ta juya gare ni tana fadin gobe sai ki shirya su tafi dake indan zasu wuce gaba na ya ba da damm da sauri nace a a mama ba tafiyan safe zanyi ba ni. Khadija yayan ku ne fa ki shirya ki bishi yafi shiga motar kasuwa su wuce da ke shidai baiyi magana ba ya rike goshin shin da hannu guda . Sai buzuwa ne tace motar tamu ai a cike take dayan ni dashi ne sai driver dayan kuma na masu aiki mun ne su larba sai na security din mu . Naku zata shiga don ita din ba bare bace yar gida ne kaji na fada maka tau mama yace ta shirya da safe din kada ta makara sukuku na mike tare da fadin mama na gode. Fitana dakin mommy na tafi ina nuna mata abinda hajiya mama ta bani tace ai yaya tafi danan ban fada mata zancen bin mijin buzuwa da tace in yi ba a lokacin itama daki ta shiga sai gata ta fito min da wani bakin dogon riga da takalma cikin na sayarwanta tace ga wanan a samu na sakawa. Binta ce ta shigo dakin tana dariya mommy tace maynene kuma tace khady nakewa dariya mommy mama tace da yaya gobe su tafi da ita. Ga buzuwa can tana fada bayan fitar mama daki wai bata yarda ba bata san mama ta jita ba shine mama ta fito tana fadin har ta isa tace ga abinda take so tace ita bata yarda ba yaya ce shi baice ba zata bisu ba ai. Juyowa mommy tayi ta kalle ni nace nifa ban iya bin su gaskiya don idan tayi min wallahi nima yi mata zanyi gara ko kada in bisu din. Dariya take min mommy tace akan may kin samu sauki bazaki bisu ba ai shi Abdulsamad baida hakana tunda har yaya tayi mai magana da bai daukan ki tun a nan zaiyi magana balle yanzu da yasan yaya tana hake dashi ai ba zai so ya bata mata rai ba kuma. Daga cikin dakin mommy anty Fatine ta fito tana saye da wani hijjab har kasa fuskan ta duk ya kode alaman tasha kuka har ta gaji. Gaida ita nayi ta amsa kasa kasa ta zauna a daya daga cikin kujerun falon mommy tace kin tashi tace eh mommy tace ga mutanen ki can sun shigo sallaman mu zasu koma gobe wai. Shiru tayi batayi magana ba sai mommy ta kara cewa kin san yaya da son jan magana wai cewa tayi gobe su wuce da khadija da zata koma makaranta goben. Wai ai ba zata bari ba wallahi bata son kowa ya rabe shi balle wanan da take gani mace haka maikyau kuma gasu da wata a kasa daman. Aiko banyi niyan binsu ba da amma yanzu sai na bisu tunda abin haka inga yadda zatayi a motan dani idan na shiga. Murmshi mommy tayi tace ki shirya da wuri don shi da wuri yake tafiyan shi idan zai tafi tashi nayi nayiwa mommy sallama muka fita da binta ta rakani. Naje gida na nuna ma ya Amina tsaraban da suka bani don da zanfito anty amarya taji zan wuce ta dauko min wani set din turare mai kamshi ummi ce bata ban komai ba a cikin su. Sai can muna hira nace ya Amina kinsan wai mama cewa tayi in shirya gobe in bi mijin buzuwa da buzuwa idan zasu koma. Da sauri tace may ne ? Nace wallahi da banyi niyan binsu ba amma tunda ta nuna bata son haka zan bisu din inga yadda zatayi dani a hanya . Nidai wanan zuwan wai damay yazo muna haka ne da tarihin buzuwa ko damay yanzu ke binsu din zakiyi, ba zaki hakkura kibi motar kasuwa ba. Don mama ne kawai zan bisu kada in bata kunya tunda tana sin gwada masu ikon ta ne a kan su da kuma ita buzuwan zantafi. Da yamma sosai na fito zan shiga gari in karbo dinkina da nakai ina fitowa bakin get sai ga motan shi tundaga nisa na kawar da kaina don ban san wanda ke cikin motar ba sun kawo kusa dani na gane su ne na watsa mai harara na kawar dakai. Yusuf wacece wanan yarinyar wai da nake gani a gurin mama yarinyar bata da kunya ko yanzu baka ga wanj harara da ta watsa muna ba kullun shi take min fa har a falon mama da muke haduwa. Dariya Yusuf din yayi yace amma kuma tana da kyau gaskiya koda yake kai yanzu baka ganin kyaun mace gaka da buzuwa a gidan ka. Wai Yusuf may ya kawo wanan magana haka daga tambayan ka yarinya idan baka santaba kace kawai baka santa ba period. Dariya Yusuf din yayi yace kai ke nan da anga mace mai kyau kace kada ayi magana wallahi yarinyar ta hadu sosai shiya take da jan aji da yawa. Nafisa fa tayiwa rashin kunya a gida na ka sani kuma kake wanan magana yace a a suka dai yiwa juna ta zage ta ta rama don uba baifi uba ba. Matsalan Nafisa tace kowa zata juya don tana takama mijin ta na da kudi kaji dai abinda yarinyar tace mata ai batazo roko wurin ku ba zumunci ya kawo ta. So tayi ka kama mata kuyi wa yar mutane cin mutunci a banza. Yace ai don na ganta a wurin mama ne yasa na kyale ta amma da ba zan yarda ta shigo min gida tayi min tujara ba for what ? Matar ka ce yar cin mutunci ai ya furzo iska daga bakin shi yace matsalan ta ke nan wallahi cikin ina tsawata mata ta bari ke nan ma. Yanzu dai kun kori Fati kun huta tabar maku gidan yace ta dai kori kanta amma ni ban kore ta ba ai ban san irin Fati ba wallahi . Bandai san irin ka ba malam buzuwa ta hanaka ka ba Fati da yara hakkin su kai kuma ka biye mata ranan fa a gaban kowa ta banbare hannun Fati a jikin ka kuma ka yarda. Wallahi idan zakai ma kan ka fada kayi tun baka makara ba kana ganin su Affan idan suka girma sukaga kanawa uwar su haka zakaji dadin su ne. Kai wa kan ka fada wallahi akan buzuwan nan kada ka tashi ranan lahira da bari shayaye . Bugu yakai ma abokin nashi yace Allah man abinda akace yana samun masu karkata gin mace daya ke nan na fada ma tun farko ban yarda da ita ba yanzu kaji abinda hajiya ta fada muna ranan. Nisawa yayi yace ai Fati ta riga da ta hadani dasu har baba fushi yake dani a gidan da sauran yan uwa. Yusuf yace buzuwan ka kuma tana jin dadi ba ta kori yar masu gida an bar mata gida tana yadda take so ita kadai tayi hankali wallahi da iyayyen nan namu. Shiru yayi yana nazarin maganan abokin nashi baice komai ba san cen yace kasan hajiya don jan magana cewa tayi gobe da wanan yarinyar zamuyi tafiya. Ina Yusuf ya tambaya da sauri yace wai Abuja zamu tafi a can take tace nowarder idon ta yake a bude haka bata da tsoro da ganin ta ai. Na karbo dinki na dawo na shirya kaya na bayan na gama komai na zauna ina tunanen yadda tafiyan mu zai kaya a goben. Ya Amina ta ban abinda zata bani taja min kunne don Allah kada in kula buzuwa har mu isa nace ni ina ruwana da ita su dai kaini su sauke kawai. Da safe ya Amina ta tana dani da wuri na shirya jiran kawai nake ace in fito mu tafi ya Amina tace in dauki jakkana da sauran kayana inje dasu gidan su mommy nace ai wanan ya zama tonon asiri haka . Ni madai su wuce idan haka ne dole ta kyaleni don ba yadda zatayi dani na gama komai har da karyawa ya Amina ta sani yi da safe don tafiyan da zamuyi din. Can sai ga su Binta sun shigo wai in fito da kayana ga su buzuwa nan sun fito suna ciki suna sallaman su mama zasu biyo nan su dauke ni inji mama. Tashi nayi na fara fito da kaya na waje suna tayani fitarwa kofan gida sai ko ga motan su ya tsaya suna baya dashi da buzuwa gaba zan zauna dani da driver su. Ina jin ya Amina tana gaida su binta ta bude min na shiga duk da kamshin turen su amma nawa ya karade motar har na shiga na zauna ban yi masu magana ba ina daga wa su ya Amina hannu muka tafi. Tsayawa sukayi suna bin motar da kallo Binta tace yau akwai tafiya a wurin nan jifa yadda anty Nafisa ke cika tana batsewa kamar ta fashe. Zainab tace suna daidai da khady ai ta fita iskanci daidai zasuyi a motar niko saida aka fara tafiya na dan juyo nace dasu ina kwanan ku murya can ciki bai fita. Ina kokarin cire airpies dina na sa a kunnuwa na tare da sake kira, a a wayan na lumshe idanuwa a hankali ban kara bi ta kansu ba kuma. Tun ina bi sai dan barci ya dauke ni ina yi ina falkawa na gyara zama tare da dan satan kallon su ta karkashin idanuna na naga yadda suka zauna manne da junan su sai dai aiki yake a laptop din shi. Ita kuma tana gyangyadi daga zaune da yake lafiyayun motoci ne kafin wani lokacin har mun kusa isa Abuja driver yaiwa magana yatambaye ni ina za a sauke ni . Ya juyo idanuwa suna lumshe ya dan taba sit din na bude ido tare da cire airpies din dake a kunne na yace yallabai yace a ina za a sauke ki ne ? A hostel nake zaune na bashi amsa ya juya gun ogan nashi yana fadamai abinda nace mai bai kara magana ba har muka shiga gari. Ban ankara ba sai naga suna shiga jerin gidajen dake asorock a wani gida motar ta danna kai suka shiga katon gida ne mai wani babban get ginin gidan sai mutum yace a turai yake sai lokacin na cire airpies din kunne na naji buzuwa na fadin ita a ina za a sauke ta banji may mijin ya fada mata ba nidai ban fita motar ba su kuma sun shige ko godiya ban masu ba. Driver ya shiga masu da kaya ciki ni dai sai bin gidan nake da kallo a raina nace shiyasa yake abinda ya ga dama ashe yasan abinda ya taka, Ga wasu manyan motoci gudu uku a fake wata katuwar jeep ta dauke min hankali har ina satan kallon ta a wurin motar sai sheki take tana daukan ido da gabin ta sabuwace. Sai dai ga daular duniya matashi dashi amma ya kasa auren yar kasamu suci arziki a tare sai wata bare ce buzaye ne gidan naga suna fitowa daganin su kasan yan uwan buzuwa ce ba sai an fadi ba nace mijin hausa ke nan inwar giginya na nisa ka more ka. Driver ne ya fito tare da wani dan saurayi buzu a baya shi yana dauke da tire da drinks yace gashi mai gida yace a kawo maki No na gode na fada tare da juyawa da kaina gefe a can cikin gida kuwa fitina na tsakanin buzuwa da mijin ta. Wai sai dai in shiga motar haya akaini hostel bata yarda ya wuce su sauke ni ba dole yasa driver yakai ni sai ya dawo ya kai shi office daga baya. Mun kama hanya driver ke cewa kai matar oga akwai kishi yanzun haka ta rike shine ciki wai bata yarda ya fito atafi kai ki dashi ba. Murmushi nayi nace mahaukaciyar banza kawai itake nata haukan ni ko a jikina yace nayi mamakin yadda ta yarda aka dauki ai nasan shi take ma fushi har muka zo ba shiri a tsakanin su. Surutun nashi ya isheni don haka nakawar da kaina gefe kamar ina kallon titi don abokin gulma yake nema da alama ganin na kyale shi shima yaja bakin kishi yai shiru har muka isa gidan da nake ba a cikin hostel sai dai gidane na haya da yan makaranta ke kamawa. Driver shi ya taimaka min da kayana har zuwa bakin gidan namu ya shiga min dasu sai dai bai shiga ciki ba kudi ya miko min yace gashi oga yace idan na sauke ki in baki. Dan jimm nayi kamar bazan karba ba sai dai nasa hannu na karba tare da fadin kace nagode sai dai ban faye karban irin kyautar nan ba kallo na yayi ganin na fara jan trolley dina yasa shi wuce yana mamaki na a ran shi. Dakina na bude wanda mijin ya Amina ne ya kama min hanyan shi dakine ciki da falo da bandaki a cikin sa sai inda mutum zai danyi girki daga waje haka dakunan suka a jere har dari da wani abu. Dakin yayi kura dan sati biyar din da nayi ban ciki daga kofa na aje kayan da na dawo dashi na fara gyara dakin tukun sai da na sharo ko ina na dakin. Na mayar da komai yadda nake son shi na fito ba zan iya fita ba haka yasa na kwanta don in sauke gajiyan dake jiki na a lokacin. Ba wanda yasan na dawo do haka na rufe kofa na kwanta abina sai barci mai nauyi ya dauke ni a cikin barci sai gashi wai muyi mumunan fada da buzuwa mijin kuma na tsaye yana kallon mu baiyi magana ba. Falkawa nayi don kiran wayana da akeyi na lalubu wayan da kyat saboda barci da yaci idona ya Amina takirani. Ina dauka naji muryanta tana cewa ina kika shiga ne haka waya nata kara baki dauka ba cikin muryan mai barci nace wallahi barci nakeyi anty. Tace yaya kuka sauka shine koki kirani hankalina ya kwanta nace wallahi lafiya kalau muka sauka tace badai wani matsala ko ke da buzuwan ki ? Naja guntun tsaki nace suna can gidan su muka sauke su driver su ya kawo ni hostel ni komai bai hada mu ba a motan bayan gaisuwa. Tace to barin barki ki huta an jima zan kira son naga yanzu barci yaci karfin ki nace ai na tashi yunwa ma nake ji yanzu tace to ki samu abinda kikaci kin san kina da ulcer nace yanzu zan tashi. Baki sayo komai ba ma ke nan nace yau na gaji ne anty ba zan iya zuwa ko ina ba sai dai gobe idan na fito lecture. Allah yakai mu tace muka kashe waya ina jin dadin yar uwa ta sosai saboda kulawan da take bani na musanman shiyasa nima nake mata komai kamar ita ta haife ni. Mafalkin da nayi ne ya fado min a raina lokaci guda yake dawo min dan dariya nayi nace ikon Allah wanan buzuwar kamar manya ta tsaya min a rai haka ? Sai a lokacin kudin da driver nan ya bani ya fado min a rai na jawo jakka na daga kwance na kirga kudin ido na zaro ganin har dubu hamsi ya bani nace wanan yasan zafin kudi kuwa ? ZAINAB IDRIS MAKWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Ina shiga ruwa na saukowa daga sama da karfi dama hadarin da ya gama haduwa a lokacin kiris yake jira ya fara zuban ruwa. Ruwa ake sosai a lokacin na kuma san basu kai gidajen su ba duk da ba zan iya cewa ga nisan gidajen su ba a lokacin. Na fara cire kayan jikina aka turo kofan dakin nawa da na saya da sauri na juya don ganin wanda ya shigo min a wanan lokacin haka. Maryam yace sabuwar kawar da nayi a cikin hostel din namu tana rike da wani warmer dain abinci na silver mai marika tashigo tana dauke da murmushi a fuskanta nima murmushin na mayar mata a lokacin nace cikin ruwan nan kika fito. Tana aje kulan tace tun dazun nake dakon dawowar ki ai sai yanzu na ga wuta a dakin ki na san kin dawo gami da yi min sannu da dawowa na amsa ta. Na karasa cire kayan na daura zani a jikina tace abinci na kawo muci don yanzu na samu yar uwa na huta zaman kadaici hakana murmushi nayi ina zama a saman katifan nace fitan nan nawa har kikai girki haka ? Tace dama akwai miyan a fridge sai shinkafa ne kawai na girka muna yanzu nayi mamakin jin har da fridge a dakin ta don ban taba shiga ba sai ita ce mai zuwa dakin nawa. Ido na ta kai ga ledan da na shigo dasu dakin yanzu na dauko na fara budewa kayan mata ne a ciki irin doganyen rigunan nan har kala biyar sai takalma da jakka biyu. Sai dayan ledan mai dauke da kayan drinks da su packed din sweet irin mai tsadan nan tace woow duk wanda yayi sayayan nan yasa kansa wanan rigunan duk letes ne fa don anty na business din da take yi ke nan wanan dawowan da tayi daga dubai naga ta dawo dasu har nace taban guda daga ciki tace sai dai in saya. Nace uhmm kyautar maya ne haka maryam wasu yan yan gari mu ne da suka zo yanzu muka fita tare suka saya min su. Maryam tayi dariya tace manya ko ba nawa sa ba nerbough don wanan wawan kyautar sai da wata a kasa kin san ko ba karamin kudi aka kashe wurin nan ba. Nace kuma kin ga ba wani abu a tsakanin mu sun dai ce ne mudan fita in rakasu wani wuri ni ban ma shiga shagon ba Yusuf kadai ya shiga sai gashi da wa yan nan kayan haka ya fito. Tace haka abin yake ai don masu kudi basu jin zafin fitar da kudin su, ga abinda suke so don wanan kyauta ai ta maya ne daganin su duniya na damawa dasu Allah. Nace sam ban san yayi min wanan mahaukacin sayayya ba da na dakatar dashi wallahi ni na dauka ko irin dan drink's din nane da sweet fa. Maryam tace may ye na damuwan kan ki tunda bake kikace su saya maki ba sai dai gaskiya kyauta yana nuna alama ga abinda ake so ne. Nace so kuma ai sun san ban da lokacin wani so a yanzu kawai dai raayin su ne yin hakan sai dai zan dakatar dashi ga yi min haka nan gaba. Abinci ta fara zuba muna muna hira na kwashe kayan na kawar gefe guda ina ce mata kinga yanzu sai dai mu canza tsari ba wai kullun kita dafawa kina kawo min muna ci ba haka. Dariya tayi tace kin manta da rana naki mukaci shiyasa nima na dafa muna yanzu muci ai ko hakan kuma laifi ne nerbough ? Muna ci muna hiran makaranta da ita har mun kusa gamawa wayana dake gefe yayi kara da sauri na mika hannu na dauko don kada ya tsunke. Daddyn mune akan layin na dauka da sauri ina hadiye abincin da ke a bakina yace may kike ci haka khadja ko dadi kuke ci a makarantar mu muna nan gida muna hadiyan shikafa da mai ya fada cikin zolaya . Nace daddy Allah ya nuna muna mun samu kuma kuji dadin da iyayye ke ji ga diyan su watarana indai zakuyi farin ciki da hakan. Yace ko yanzun ma mun gode maku don muna cin moriyan ku a haka yaushe yaushe kika turo muna da kudin hannun ki wai mu kara nayi fada ai da yar uwarki nace ke da kike makaranta kin fimu bukata a yanzu ai. Burin mu daya shine muga kin tsayar da miji da wuri kiyi koyi da yar uwar ki kema kiyi aure basai kin yi dogon karatun nan dakike so ba. Dariya nayi nace kai daddy aure yanzu kuma nida nake son in zama babban lauya kafin in aure amma tunda naga raayin ka ke nan ba damuwa . Daddy da izzinin Allah zan cika maku burin ku daddy na karasa fadi cikin sanyin murya daddy yace da sauri . Dear kada ki sa wanan a rai yanzu buri na fada maki kawai shi aure ai dan lokaci ne indan lokacin yayi ko da shiri ko ba shiri zakiyi ne ai nafison in ganku cikin farin ciki a koda yaushe bana son bacin ranku kada magana na ya kara maki zuciyar ki akan karatun ki. Ya kara da fadin Allah dai yayi maku albarka dake da yan uwanki don baku taba bata muna rai ba da halin ku. A hankali na goge hawayen da ya zubo min a idona nace mukai sallama dashi bayan ya gama kwatar min da hankali na. Maryam ido ta tsura min ina aje wayan tace dani ina son nima inga ina haka da iyayyena wallahi sai dai hakan bai samu ba a gare ni don na taso ne ba tare da iyayyena a wuri daya ba. Mahaifiyar mu sun rabu da babban tun muna kanana sai dai idan naje inkai masu ziyara dukkan su tunda riko na yadawo hannun yayata. Nace Allah sarki lalai dole kiji sha, awan hakan gaskiya don iri haka babu daddy ni kinga iyayyena sun fi son suga nayi aure ko yaushe maganan su ke nan a kaina. Sai dai ko yaushe auren nawa zai zo ban sani ba tunda ko sauriyi tsayayye ban kai ga tsayarwa ba a yanzu haka. Tace to ina ga dai yazo din ne tunda ga wanan yanzu da ya fito ya fara nuna maki son shi dariya nayi nace maryam ke nan baki ganewa ne ke. Bandai fada mata komai ba mukaci gaba da hiran mu sai goma ta koma dakin ta nima na gama abinda nakeyi na kwata. Har na kawanta naji wayana na verviration a gefena nasa hannu na dauko wayar nace salamu alaikum. Yar mama kina lafiya yaya ruwa , ? Na sauke lafiyayyen murmushi nace lafiya kalau yaya Yusuf yace kina kara fasa min kai fa da yayan nan da kike kirana dashi nace kai ka saya a kira ka da sunan. Nace yaya kuka isa gida kuma yace lafiya kalau sai yanzu na kai mutumin ki gida yanzu haka ina hanyan gidana ne na kiraki mu gaisa. Yace bayan mun rabu dazu mun dade muna maganan ki da mutumi na nasan zai kiraki yau din na shiya na kira ki in fada maki don naga ya yarda sosai da shawarana. Nace anya kuwa zan iya cika maka alkawarin da na dauka don mutumin naka akwai zuciya sosai wallahi ni kuma ban iya daukan haka don nice zan taimake shi ba shi zai taimake ni ba. Dariya yayi yace a yadds kuke yi din nan shakuwa zaizo ya shiga tsakanin ku sosai zakice na fada maki watarana bagashi yanzu ya fara saukowa ba. Idan ba ta haka na fito mashi ba da wuya yayarda mu aiwatar da komai yadda muke so amma ki daure don Allah mubi abin sannu ni dai buri na shine ki san yadda kikayi kika kara ma wanan buzuwar kadarin ta a gurin jamma,a. Abin ne da kamar wuya yaya na sai dai zan yi kokari inga nayi yadda kuke so din yace good girl Allah ya taimaka ya bada sa,a nace amin. Shine kuma ka yi min dawainiya haka mai yawa don Allah nan gaba kada ka kara min irin haka don hakan zai yi maida ni cikin wani yanayi daba shi nazo yi a gatin ba. Dariya yayi yace Khadija kin san dai sutura shine mutum yanzu don haka farawa akayi don ina son ki goge sosai ki fito a cikin classes ladies ta yadda zamuji dadin aiwatar da komai a cikin sauki nace to na gode sai dai a rage don Allah. Kada kiji komai mana lokacin kine yayi kawai ki kwantar da hankaki kici arzikin ki a saukake wanan ba komai ba kada ki damu da hakan don har motan shiga ba dadewan nan ba zaki samu in komai ya tafi daidai. Zanyi magana ya katse ni da cewa na iso gida zan shi sai dai indan mun kara waya don yanzu zamu rage haduwa sosai kada a zargi wani abu a gare ni. Mun gama wayan ina mamakin su kudi kamar na sata haka nikan ban cika amincewa da irin haka ba azo ba a daidaita ba shirin mu ya watse abarni cikin wahala daga baya. A hankali ya shigo gidan babban falon su ya samu su hidaya da sauran yan su zaune suna shan bakin shayin su na buzaye. Gaisuwa sukayi bai tsaya ta kansu ba ya shige ciki bai jin dadin yadda suke cika mashi gida a ko wani lokaci haka. Duk da wani lokaci abin yana taba mashi zuciya ganin yanzu babu wani nashi da yake zuwa wurin shi kamar lokacin da suke zaune kano da fati . Yan uwan shi na yawan ziyarar su maza da mata amma tunda abin ya juye haka sai dai kulun idan ya dawo gidan ace mai akwai bakin da suka zo daga kauyen maradi. Dakin ya nufa ya tura kofa a hankali dakin na nan a yarda ya barshi da safe ba a gyara shi ba in zai iya tunawa yau kwana uku ke nan bai samu lokacin da zai tsaya ya gyara dakin ba. Don cikin yan kwana kin nan suna zirga zirgan filin da suke son saya a kubuwa ga kuma wanan shirin da Yusuf yake son yi a kan shi. Rigar shi ta sama ya jefar a saman gado ya kara bin dakin da kallo ya ja tsuki ya nufi yanyar bathroom din shi wani zarni ne ya daki hancin shi da sauri ya fito ya nufi hanya wajen dakin. Dakin Nafisa ya shiga don yana kyautata zoton tana ciki tunda bai ganta falo ba kuma bai ganta a nan dakin shi ba. Yana shiga nan ma wani tsami ya tare shi mai kama da karni karni yabi dakin da kallo ga kaya a ko ina watse a dakin tana kwance saman godon dake tule da kayan da bai san ko na maynene ba. Nafisa na ganin shi tace ka dawo ashe yanzu nake tunanen ka fa a raina nace ko ina ka shiga tunda ka fita da safe baku dawo ba. Haushine ya kamashi yadda take kwance ta mike kafa sai kadasu take yi tana magana kamar wata basaraka da ita. Kallon da yake mata ne yasa ta tsargu yace Nafisa wai ke dadin may kike ji ga kazantar nan naki ne haka don Allah dubi dakin da mutun ke rayuwa wai a cikin sa. Kina mace kice ba zaki iya gyaran muhalin ki ba sai wasu sunyi maki wai ma ina masu aikin da kikace kin dauka ban ga wani abinda suke a yi a gidan nan ba. Tace Samad yan uwana ne fa ko kuma yanzu kana bakin ciki da zaman su ne a gidan ko suyi aiki ko kada suyi zasu dai zauna anan tare dani ne ko ? Nasan wanan munufakin kila yaka su hadiye a falo ya zuga kwanan nan sai nayi maganin shi wallahi ni banga dalili da zai sa yayi ta shigo min gida ba haka ba gaira ba dalili yana sa muna ido. Ke na fada maki duk abinda zakiyi idon ki ya fita ga Yusuf don idan kikace zakiyi kokarin raba ni dashi kan ki zakiyi wa kin dai san halina and kuma ki tashi kije ki pulloshing din rubish din da kikayi min a bandaki tunda ba dakin ki bane. May nayi kuma kewayawa fa kawai nayi a ciki na fito yace zaki tashi ko sai na bata maki rai yanzu ya fadi yana dan zare mata idon shi. Mikewa tayi da kyar tazo ta wuce shi zuwa dakin ya bita da harara ya mara mata baya yana sa kai warin bayin ya ji har cikin dakin da sauri yafita zuwa dakin hutun shi tare da rufo kofan da key don bai son damuwa. Anan ya cire kayan shi ya yi wanka ya fito sallah ya gabatar ya dade zaune a wurin yana tunanen halin Nafisa ga gida da ta cika mai da yan uwanta babu halin ya zauna a tsararen falon shi ya sha iska a ciki. Tsuki yaja ya mike don ya kwanta nan yaga wayan shi da ya jefar saman gadon daya shigo dakin kafin ya kewaya dauko wayan yayi yana duba lokacin maganan Yusuf ya fado mashi a rai. Da yake ce mashi kabi yarinyar nan a sanun har mu cin ma manufar mu a kan hajiya ba wai nace kaso ta bane dole a a wanan wani dama ne da muka samu zamuyi amfani dashi. Nomba na ya bida a wayan da ya rubuta ma tsoturburn girl ya danna kira sai ko kiran ya shiga tunanen ya fara yi idan na dauka may zai ce min sai yaji na dauki wayan da sallama a bakina. Queen yar matsala yaya kika shiga gida yaya kuma ruwa i hope bai taba ki ba dai ? Murmushi nayi sai da yaji shi cikin zuciyar shi nace au mijin buzuwa ne a layi lallai kana son aikin nan da zan maka ke nan ? Yace to yaya na iya tunda Yusuf yace ke ce maganin matsalata yanzu indai har zaki min hakan ai ya zama dole in koyi zama dake da halin ki . Nace ashe shiyasa na samu queen din yan matsala yace idan akwai abinda yafi queen din su kinci a baki wanan muka min. Murmushi na sake yi nace nace nako gode da wanan sunan da aka rada min sai dai ina ganin bada ni sunan ya dace ba yanzu ai. Da sauri yace dawa ya dace nace kaida buzuwar matarka mana fara yar dagwas mai gashi har baya sai dai kassh kuma gashin sai naga kamar bai samun gyaran da ya dace dashi balle har kaji dadin shakan shi dakyau. Ke kada fa kiga na kiraki ki nemi tozarta min matata don kin san tafi komai da kike takama don wanan banzan dalilin na Yusuf da yakawo bashi ne zai sa ki samu daman fada min maganan banza ba. Wanan kuma fadi kayi mijin buzuwa don yanzun haka ma nasan tunanen yar asaline ya hana ka shakat sai da ka kirani kaji yaya nake sai dai kana tsoron buzuwar ka nasan ma yanzu haka wani wuri ka samu ka labe kake wanan waya dani. Idiout stupied girl kawai ya fada ya ja tsuki ya kashe wayan yana huci wai may yarinyar nan take takama dashi ne wai zuciyar shi tace kyau ilimi tsabta da fadin gaskiya. Idon shi ya lumshe yana tunane sai kuma ya sake guntun murmshi a yadda yake rigingine a kwace taba kofan da Nafisa keyi yasa shi bude idon yana jin ta har ta soma bugun kofan bai tashi ya bude mata ba sai gyara kwanciyar shi yayi dakyau ya fara adduan barci haka har barcin ya dauke shi yana tunane. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: A zoto na shika dai ne a cikin motar sai da na isa kusa ne naga sabanin haka ashe tare suke da dan baiwa yana zaune kamar kullun ya aza Laptop a cinyar shi yana dubawa. A sanyaye nake nace dasu sannu ku da zuwa yaya hanya yaya mutanen gida kun barsu lafiya ? Yusuf yace ke ce African ta gidi khadija tambaya haka a jere lokaci guda wani zamu fara amsa maki daga cikin wanda kika jero muna a lokaci daya ? Nace amsa daya ya wadata gareni wanda nake fatan alheri a cikin shi yace to duka amsan ki alheri ne don duk Alhamdullahi gaba daya kowa na lafiya kuma hanya lafiya. Murmushi nayi sai yace baki gaisa da oga na ba kuma aboki na dan satan kallon shi nayi nace ai bugu daya nayi maku gaba daya nashi gaisuwan daban ne kuma ? Yace oga ne fa khadija kema kin sani ai dole gaisuwan manya ya zama daban da na saura nace a wurin ka yake daban don kace shi din ogan ka ne amma ni a wuri na duk daya kuke gare ni. Eh to kya iya fadin haka yanzu amma dai nasan nan gaba bazaki fadi hakan ba dariya nayi nace saboda may kana ganin zanyi aiki a karkashin shi ne ko may , ? In wanan kake tunane may zai kai lawya aiki a FCDI kuma sai in dai bukatan haka yataso mu a bukace mu a wurin muyi aikin mu mu bar wurin. A a a ashe da babban lauya muke bamu sani ba haka nace cikin murmushi lawyer to be insha Allah ba ya juya gare shi yace kai kaji ashe da Barister muke bamu sani ba shike nan yanzu muyi abin mu ba kwabo muna da mai kare mu. Nace wa ni ai nice ma zan tsaya sai na kama masu cinye ma gwaunati kudin filayen ta in daure mutum inga tsiyan kwashe kudi ana tura ma yan Niger suna cinyewa dama yan Nigeria kuke ba sai in maku sausaci a kai. Sai lokacin ya dan sake murmushi yace ashe har kin fara hada evendece a kaina ban sani ba nace tun yaushe na fara hadawa zan tura babban kotun mu. Dariya sukayi sosai gaba dayan su yace dama karatun da kike yi ke nan ashe nace kwarai don kama manyan bariyin gwaunati ba. Yace ashe aiki ya ganki magana yake ba tare da ya dago kai ya kalle ni ba sai dakilan laptop da yake yi hankali kwance da gani abin ya zama mai jiki hakan. Yusuf yace wai kin san ban taba sanin abinda kike karantawa bs ke nan sai yanzu na dan natsu nace shi nake karantawa ai Allah ya bada saa yace nace amin nagode. Still bai dago kai ba yace wace zata kama ka kakewa addua haka kuma yace ai addua ya zama dole muyi mata shi fadi take yi kawai mutum ya taba kama kanshi da laifi ne. To wai ni fa kun barni a cikin duhu yakamata ace yanzu ina gida kun tsayar dani a nan aikin oga ne haka khadija bai son ki bar garin nan yanzu ne yasa ya tsayar dake. Kallon shi nayi sai faman aikin shi yake yi hankali a kwance bai dago ya kalle mu ba nace ni ai ba yar Niger bane da yake tarawa a gidan shi kamar almajirai. Dama titi yake bi yana ba mabukata alheri da zai fi samun lada ga Allah da wanan ciyar da mayaudaran dayake yi zai fi mai Alheri sosai. Rufe Laptop yayi tare da fadin wai ke maye matsalan ki da yan Niger ne cikin rashin sani nayi subul da baka nace kishi mana lokaci daya suka ce kishi nace wallahi. Murmushi naga yayi yana lumshe ido Yusuf ko sai kallo na yake yana dariya shi ya bude idon shi yace kishi yana jijiga kai nace na kasata ba . Sun zo suna kwashe muna dukiya suna raya kasan su da sunan aure nan ko barayi ne na zaune Yusuf yace a a kada ki gyara zancen kuma mana khadija yar mama. Nace a in ba kishin kasata ba kishin may zanyi kuma Yusuf yace gashi a gaban ki kishin dai kike yi amma kada ki gyara kice kuma wai kasan ki. Ikon Allah akan may zanyi kishin shi shi mijina ne ko wani nawa ba hadin kifi da kaska ai Yusuf yace waye kifin waye kasa yanzu. Yace itace kaskan mana nine kifin ba ita ta lake min ba kana gani kuwa ido na waro waje nace ni din yace Yes kamar zanyi magana sai kuma na kalle su tare da fadin sai anjiman ku. Ina juyawa da sauri Yusuf yake kirana ban tsaya ba ya fito daga motan ya sha gabana shiko yana ciki sai murmushi yake ba abinda ke mai yawo a rai sai kallaman kishin da nace. Ya samu na tsaya yace ke ko daga wasa zaki mai da abin wani magana nace ina nuna shi bakiji may ya fada min bane yanzu wai ina like mai. Yace ai wasa ne ko shima yasan baki like mai shiyasa ya juye maganan yace ke ce mai like mai yanzun bamu muka zo wuri ki ba wake nan kaskan a cikin mu ? Bude motar yayi ya fito yana mika tare da nufo inda muke tsaye yana fadin wai may kaskan nan take fadi ne haka ka tsaya wani bata magana can. Yusuf yace kin gani ba har ya kai ga fitowa a mota don ki yace ai ita ma ta fito don ni ko, kallon shi nayi na kauda kai na gefe daya. Ya karasa takowa zuwa inda nake yace wai yaushe ne zaki tafi in samu in huta da wanan matsalar taki. Nace nice yar matsalar yace gashi ko kina muns ko yanzu kai na girgiza kawai nace ba komai baka da laifi fito war maryam ya tsayar damu daga maganan . Ta fito tana gaishe tare da masu yaya hanya da mutanen gida yusuf yace suna gaida ku tace kuna nan da miss barister ne yace wallahi kuwa kauna a kwai rigima ai. Tace da kyat na shawo kan ta ta tsaya da yanzu tana gida baku samay ta ba Yusuf yace kin kyauta shi dai tunda ta fito bai mata magana ba ko gaisuwan da tayi bai karba ta ba sai ma daure fuska da ya kara yi yanzu. Yaushe ne zata wuce Yusuf ya tambayi maryam tace bataki ko yanzu wanan ta bar gari ba ta isa da dare da sauri shi yayi magana da fadin No bako a cikin daren nan ba kan gaskiya. Nace may ye a hanya da zaka ce ba da daren nan ba zan isa ko lafiya yace No sai gobe za a zo a kai ki har gida. Nace a a kada ku wahal da kan ku motar kasuwa nake shiga yanzun ma shi zan bi in Allah ya yarda bani kadai ba kowa dake wurin yayi mamakin maganan shi da yace. Ba zan yardan ba ki bi motar haya ke kadai idan wani abu yaje ya samay ki fa a hanya ki sani a wani hali don haka ki shirya gobe zan turo malam sani ya kaiki gida da safe. Ido gaba dayan mu muka tsura mashi da yake maganan kamar wani uba da yar shi ko miji da matar shi yadda ya hakikance yana fada a hasale dani. Zan yi magana Yusuf yace ya gama yanke hukunci akai Allah ya kai mu gobe din ai yau da gobe duk na Allah ne ko amma ki bi motar haya wani abu yaje ya samar mashi ke a hanya kuma ? Maryam ne tayi dariya nikan hararan shi nayi mai dani gida yace a dake Yusuf yace to bissimillah muje in sauke ka ko ya juya ya fara tafiya ba tare da yayi magana ba kuma. Sai Yusuf ne ya tsaya yana ce muna yar mama ni zan tafi ban sani ba ko zamu sake haduwa ga wanan ayi ma kanne tsara ba dashi ya mika ma maryam sai kuma ya sake ciro wasu yana miko min wai na karba. Kai na girgiza mai nace daka barshi don ni ina da kudin mota a hannu na tsaraba kuma ai kowa yasan makaran ta naje basu expecting din tsaraba a wuri na. Yace daga wanan time din sai ki fara masu tsaraba baki san tsaraba ko ga babba yana da muhinmanci ba ne mutuka kauna na. Dole ya mika min na karba tare da mashi godiya har dan Baiwa ya fara mashi horn a mota yace Allah sada mu da alherin sa nace amin yaya Yusuf ya juya ya tafi sai da suka shige muka koma ciki. Maryam bata shigo daki ba don haka ni kadai na shiga na adana kudin tare da cire rigar da nasaka a jikina. Can ta shigo ta hada muna abinda zamu ci ina kwance a wurin tunane ya addabe ni a raina har ta gama tace inzo muci don na idar da sallah a lokaci. Sai da muka zauna cin abincin ne muka fara hira da ita take tuna min maganan shi da yayi dazun tare da fadin guy din ya hadu wallahi Daure fuska nayi nace a naki ganin kike ganin haka amma ni mai zaisa in sawa raina abinda nasan ba mai yuyuwa bane gare ni ai ko a mafalki wallahi. Ko dai baki san ko shi waye bane yasa kike wanan magana haka shima dai Yusuf ai yanayi ne don wasa kawai amma ba gaskiya bane so kima daina wanan zancen don Allah. Wayana dake gefe ne yayi kara ban gani don wayan a silent take lokacin sai maryam ne ta gani take ce kamar kiran ki ake a waya fa sai nayi saurin juya don in duba. Tashi nayi na dauko wayan mai kiranane yaban mamaki tunda basu dade da barin wuri na ba, daukan wayan nayi na kara a kunne na da sallama yace fito gani waje. Da mamaki nabi wayan da kallo muryan shi naji yana fadin kin ji abinda nace nace eh maryam na kalla da ta tsareni da idanuwan ta nace a sanyaya wai shine a waje . Ta kwashe da wanin irin dariya bance da ita kala ba komai ba na zura rigana na fita zuwa jin may ya kawo shi kuma. Ina fita na hango motan shi dan nisa kadan damu na karasa wurin na samu ya fito da kafa daya a waje yana duba abu a cikin motar na iso wurin. Ina wuni ya dan juyo ya kalle ni yace zagaya ki shiga dan jin nayi bai zagaya ba kamar yadda ya umurce ni dayi ya sake dagowa bayan ya rufe cabinet din motar yana fadin baki ba ne dole na zagaya kamar yadda ya umurce ni din dayi. Bayan na shiga naga ya tayar da motar ya bar gurin down hostel din ya halba motan muka hau expresse ba wanda yayi magana a motan sai dai gaba na yana dan fadi don ban san ina muka nufa dashi ba. Mun dan yi nisa da gurin ya juyo ya kalle ni yana fadin maman ki ita kadai ne a gurin mahaifin ki ? Mamakin tambayan nashi nayi sai ban iya bashi amsa ba na kawar da kaina gefe yace ina magana kin kyale ni nace akan may zakai mun wanan tambayan haka. Yace don na isa na tambaya yasa na tambaye ki OK idan kana son sani sai kaje ka gani da idon ka ai. Kan nen ki nawane dariya tambayan ya bani sosai nace yau ni naga ikon Allah to kannen na biyar ne na bashi amsa tare da kawar da kaina. Ok kawai yace mukaci gaba da tafiya sai wani katon Plaza muka tsaya ya juyo yana fadin bissimillah fito mu shiga yace. Ban ki ba na fito muka shiga shagon sai faman gaida shi masu shagon keyi layin kayan sawa muka nufa yana gaba ina bayan shi. Abin ya ban mamaki yadda naga yana jidan kaya a wurin ya ban mamaki ya koma layin kayan yara sai lokacin ya juyo ya tambaye ni shekarun su nawa ne kallon shi nayi nace a kwai sha uku da sha daya sai takwas da shidda mutum biyu. Maza da mata ne ya kara tambaya nace maza uku mata biyu sai yaran yaya na biyu yan she kara takwas da shidda maza. Bayan mun gama wurin takalma muka nufa muka zaba sai layin zanuwa nan ya zaba da dama ya zaba sai ya duba kudi ya gani yake daukan mafi tsada a wurin. Ya sa yaron shagon ya tura yakai yace a samu trolley masu kyau a saka mai kayan a ciki muka bar shagon hanyar down hostel muka nufa sai lokacin hankalina ya kwanta. Bayan ya tsaya da motar nayi kokarin budewa naji ta a rufe gam na juyo na dan kalle shi naga shima ni yake kallo a lokacin sai na kawar da kaina gefe daga kallon shi. Ina son in maki godiya amma kin kasa tsaya ki bani daman yin hakan gare ki nace godiya akan may fa ? Au baki ma san abinda kikayi ba ke nan nace ban sani ba sai ka fada min iska ya dan furzu daga bakin shi yace OK you can go zamuyi waya idan kin isa ki gaida gida na gode kawai nace na fita. Banji yace dauki kayan ko wani abu ba nikan na shige abina ina fadin dan rainin wayo kawai dama sayayya zan rakashi shine yake min tambayan bazan a hanya. Har yasa gaba na faduwa ina zan kai wanan uban kayan danaga ya jida a shagon sai yanzu hankalina ya kwanta. Koda takwas na safe yayi mun gama shirya komai muna zaman jiran su sai na tafi maryam tace zata wuce itama takwas da wani abu ya bugo min yana fafin in fito da kayana ga mota a waje ana jirana. Fitowa nayi da kayan maryam ce mai karasa min su a wurin motar har aka gama na rufo kofana na saka key din a jakka ta mukai sallama tace za a zo yanzu a dauke ta ta buga waya gida itama. Driver ya bude min baya na shiga muka dauki hanyan minna shigan wuri zan ma minna wanan karon ba yadda na saba ba da dare nake shiga garin. Tunda muka kama hanya barci ya dauke don sanyin motar da lafiyar ta sai faman gudu driver ke shararawa dani ina barci na hankali kwance. Barci nayi sosai driver naji ya tsaya a wani gari na bude ido fita naga yayi zuwa gun masu sai da manja da doya a hanya ya saya aka loda mashi a motar muka kama hanya kuma. Tun ina duban waya sai na koma barci abina muryan driver ne ya tayar dani yana fadin hajiya wani unguwa zamu je na bude ido ina kallo har mun isa deport din mai zamu shiga cancaga . Nace a cikin gari kwagila road, zaka kaini yace ban san wurin ba don ni bakon garin ne nace OK mushiga sai in nuna maka. Miko min envelop yayi yace oga yace idan mun iso in baki wanan sako wai sai kin shiga gida ki bude nace OK Mun wuto ina mashi kwatance har kofan gidan mu motar ya tsaya duk da rana ne kowa na zirga zirgan gaban shi nai hana masu zama layin namu zama suna ganin motar ya tsaya kofan mu suka sako ido caa suga waye a motar yazo gidan mu. Driver ya fito ya bude min motar na fito can naji wani classmates dina na primary yana fadin yau Khadija ce a garin namu. Murmushi nayi mai nace Faisal mun samay ku lafiya ya karaso muna gaisawa dashi na shiga yace bari ya taimaka min da saka kaya a gida. Da sallama na shiga inda kanne na dake daki suka fito da gudu taro na suna ihu na rungumay su tsayawa nayi ina kallon kayan da su Fesal ke shigowa dashi gidan namu. Na kasa furta komai mama ma kallon kayan take da mamaki yaran suka fita sai gasu suna shigowa da ba adadi nace wai duk mu muka zo da wanan kayan haka wai ? Mama tace waya zo dashi in ba ke ba bagashi kin ga ana shigo dasu ba tare da kayan ki ko kina nufin baki san da su bane wai ? Wallahi mama ban sani ba sai yanzu nima nake ganin su anan kamar kowa yadda ya gansu mama ta katse nu da cewa motar wa kika shigo ne naji yara na fadin kin zo a mota mai kyau. Shiru nayi na dukar da kaina ba tare da magana ba har suka gama shigo da kayan mama tace ku dauki ruwa kusa a plate kukai ma mai motar kafin ya tafi. Yaran suka ruga da gudu suka dauki ruwan leda suka sa a plate suka fita dashi waje kamar yadda mama tace dasu ta wuce tabar ni tsaye a gurin. Dakina na nufa tare da dan hand bag dina dake rike a hannu na rai na babu dadi ko kadan a tare dani ina fadin yaya wanan mutumin zai min haka ya hadani fada da iyayyena su fara zargina. Anty khadija wai yace a fada maki zai wuce nace ya kice Allah ya kaishi lafiya nace a hasale yaron ya fita da gudu daga dakin zuwa fada mashi. Daddy ya shigo gida yana fadin ance baby na ta dawo sai kuma yaja ya tsaya yana kallon kayan da mamaki dake zube a tsakar gida. Mama tace kai nake jira dama kazo ka gani ko zata fada ma inda kaya ya fito haka don wai ita ma bata sani ba tace kuma su sukazo da kayan. A sanyayye na dago labule dakin na fito ina fadin daddy sannu da dawo wa mun samay ku lafiya ? Lafiya baby na sai dai wanan kayan kuma fa ina suka fito haka nace wallahi daddy ban san da su ba sai da muka iso na gansu. Kamar yaya bakin san dasu ba bake kika zo dasu ba sai nayi kasa da kaina ban yi magana ba kuma kayan yake bi da kallo tiryan tiryan yace ikon Allah. Shiga ciki ki huta zamuyi magana anji yanzu zan tafi inyi sallah ne ya wuce gurin da buta yake yana dauka ni kuma na sake labule na koma ciki jiki a sanyayye. Na fada saman gadon dakin duk da kuran da yake ciki don ba gyara ake ba a kai akai tunda ba kowa a cikin sa ina zaune kamal kanina ya dawo shiya fara shigo min da kaya yana min sannu da zuwa. A dadafe na amsa mai ina kallon akwatinan daya shigo min dasu akwatunan da muka sayo a daren jiya ne dashi inba idona ke min gizo ba. Watau kayan de na yan gidan mu ne kenan ba wasu ya saya wa ba mikewa nayi don in yo alwala ina shiga banda ki sai na samu ai period dina yazo min ba daman inyi sallah ke nan haka na fito jiki a sabule na aje butan. Sai mama ta aiko da abinci a kawo min ban kali abincin ba nace kaunata ta aje min a nan kawai ina jiran dawowan daddy daga wurin sallah. Envelop din da driver yaban na tuna dashi na dauko a cikin jakata na bude a hankali kudine a ciki sabbi ful din su anyi rubutu kamar haka a wrafer farko daddy sai na biyun mama. Na ukun ne bai rubuta komai ba na shiga uku nace tare da yin nadama da haduwa da shi karo na farko a rayuwana don ban san yadda daddy da mama zasu fahince ni ba. Nayi dana sanin tsaya jiran shi da yace inyi har na tsaya din sam ban kawo komai a raina ba irin haka don ban taba zaton hakan ba dayayi min. Muryan daddy daya shigo naji ana gaida shi yasa ni kaduwa bai min magana ba har yaci abincin shi ya fita haka na tashi na gyara dakin tsab na fita da na wankewa na wanke a ranan. Na dawo na sa kamshi a dakin tare da gyara komai a yadda nake bukatan shi a dakin na koma na zauna wayan maryam ne ya shigo tana tambayana yaya muka isa ? Nace wai kin san abinda mutumin nan yayi mun kuwa maryam nan dai na koro mata labarin abinda ya faru bayan isowar mu gida da driver. Tace ikon Allah sakayyan da yai maki ke nan ashe kai lallai mutumin nan yaci sunan sa dan Baiwa ne shi din. Nace ke maryam har kin samu bakin yabashi ko may may kike son in fada ma iyayyena yanzu don Allah wa zance yake gare ni da yai min wanan kyauta haka. Tace ki fada masu gaskiya taimakon shi kikayi ya saka maki da alheri haka nace ban sin su san ko shi waye tundai Ya Amina . Dariya tayi tace komai dadewa ai zata sani ne nace amma fa ba yanzu ba koda zata sani din don ban son ta fasara ni da wata manufa. Har dai dare banji daddy yayi min magana ba haka yasa na dan sake jiki naji shigowan daddy gidan sai na sha jini jikina a daki ban fito yadda na saba muyi hira ba dashi. Ina nan kwance wayana yayi kara na dauka kamar yadda na rubuta a sunan shi dan Baiwa shi ya baiyana a wayan. Kamar ba zan dauka ba dai na daga maimakon inyi magana sai na kama kuka nace may yasa zakai min haka don Allah ? May kake son in fada ma iyayyena yanzu a kan kayan nan yace daddy na gida nace yana nan yace dama shina ke son magana dashi na kira ki yanzu. Da sauri nace may zaka fada ma daddy din yace gaisawa nake son muyi dasu in masu bayanin kayan ba shike nan ba. Yasir na kira nace ya kaiwa daddy waya ana magana dashi ban san yadda sukayi ba a wayan har mama naji suna gaisawa da ita. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Bayan gama wayan mu dashi jikina ne yayi sanyi sosai a kan maganganun da yayi sai naji wani iri ba dadi a raina yadda mutum kamar Abdulsamad yake magana da ni haka acikin mutuunci da girmamawa. Karatun da ban sake komawa gare shi ba ke nan cikin sanyin jiki da tunane barkatai barci ya dauke ni a wurin maryam dai batace dani kala ba a ranan. Washegari bayan munyi sallah asuba zaune nake saman sallaya na nakasa motsawa abubuwa da yawa ne suke min yawo azuciya na. Na dauko kura,ani na fara karatu don ka,idane duk safe sai nayi kafin in fita dakina sai dai idan ina cikin lalura a ranan. Wayana yayi kara ban kula in duba mai kirana ba har sai da nakai karshe sanan na mayar da hankali da wayan da ke neman agaji kuma mai kiran bai fasa kira ba. Yusuf ne ke kirana akai akai haka mamaki naji don bai taba kirana da safe irin haka ba ga kuma kiran dana gani yayi yawa. Yasa nace lafiya wanan kiran haka da safe haka na tambayi kaina kiran ne ya kara shigowa again da sauri na dauka don kada ya kara katsewa a lokacin tare da fadin yaya Yusuf lafiya dai. Naji yace ina kika shiga haka waya nata ringing baki daga ba nace ina zaune karatun kur,ani nake a lokacin yace da kyau yar mama da alama dai ke din babban malama ce hakan na dakyau wallahi. Tambaya shi nayi lafiya kira yau da safe haka yace ina fa lafiya yar mama ta ruda min ogana kuma abokina nima umurni aka bani akan lallai in kiraki in fada maki don Allah kada ki tafi yau ko gobe ki bari mu shigo abuja gobe. Katse shi nayi da fadin yaya Yusuf may zan mashi duk abinda nayi kona fada mai da ya faru wanan haka Allah ya kaddara a kan shi. Sai mu godema Allah da yasa yayi saurin ganewa yasa kuma halin ya dore a gare shi haka kada yayi nadaman mazuru don jiya yakirana wai yana min godiya. Ni abinda na fahinta shine rashin mai fada mashi gaskiya a tare dashi yadda ya dace yasa buzuwar matar shi ta samu galaba a kan shi haka sosai. Yanzun kuma na tunar dashi Alhamdullahi tunda ya fahinci gaskiya har yayi niyar gyarawa da kanshi so ni yar barni don Allah ban son matsala ko wani abinda zai jawo ma karatuna matsala. Dariya naji yayi yace duk mun san da hakan amma ki dan daga muna kafa kijira har mu dawo din please maryam ne ta wafce wayan a hannu na tana fadin insha Allahu zata jira ku dawo yace maryam mun gode da hakan. Bayan ta kashe wayan na kalle ta nace akan may zan tsaya jiran su maryam ki tuna fa na gama abinda ya shigo dani abuja satin nan iyayyena kuma sun san da haka mai zaisa na kara kwana. Wanan ba komai bane mai yuyuwa shima so yake ya saka maki da makan mancin abinda kikai mashi idan ya dawo. Maryam bayi don ya saka min saboda Allah nayi haka tace dole ne tunda yana ganin kin cece shi daga halaka abinda wanan shi bai taba lurar dashi ba. Don Allah kiyi hakkuri har su dawo din gobe ne fa kawai ba wasu kwana masu tsawo zaki kara ba hakan shiru nayi ban nata amasa ba sai dai zuciyana cike yake da tunanen dalilin da yasa yake son in tsaya sai sun dawo garin zan tafi. Khadija godiya ya kamata kiyi ga abinda kikayi ya zama alheri gare shi wurin Allah nace nayi maryam kuma na gode ma Allah da haka ya kasance ta sanadina. Amma maye dalilin shi na son ya tsayar dani wai sai ya dawo zan tafi tunda yasan bashi ke da ikona ba, tace dole akwai dalilin dayasa yace ki dan dakance su din yau da gobe ne fa kawai insha Allahu. San nan kuma nasan dai dalili daya ne kawai don kin cancanci hakan a gare shi yanzu amma mu bari din har yazo muji. Kila kuma dai sai kuma ta kama dariya a hasale nace don Allah dai ki bari karki bata min in ce na fasa tsayawan. Shiru tayi do ganin yanayina daya sauya tasan zan iya abinda na fada din ita kuma bazata so ace na wuce ban jirashi ba. Haka kawai naji kaina yana sarawa raina yamin mugin baci haka yasa na mike daga wurin na koma saman katifa na, na kwanta ina ci gaba da tunane a raina. Wayan aminiyar ta takira cikin tashin hankali take mata bayani tana kuka wai samad din ta yana son juya mata baya a lokaci daya . Don ma idon ta naga ala,amarin shi ne yasa tayi saurin ganewa da wuri ta kare da cewa na shiga uku madam tawa ta samay ne wallahi idan Samad ya fara neman mata ni yaya zanyi. Tace haba ki kwantar da hankalin ki tunda akwai mafita zamu iya kaishi wurin mai rafanne yasan yadda ya lankwasa muna shi ko uwar shi indai mace ce ya dinga jin ko ganin ta kamar jaba. Ke dai kada ki nuna mai kin fahince shi lankwasa shi zamu a cikin ruwan sanyi batare da wani hayaniya ba. Wa ni tun yaushe nagama buda mai wuta wai fa satin nan har kaduna ya shiga ba tare da sani ba kinga ke nan abubuwan sun lalace don samad bai taba shawaran zuwa gida batare dani nabashi shawaran ya tafi ba ko shi sai idan ina da abinyi acan. Don haka nayi mai kaca kaca kafin yatafi wai ma kin san may wanan zuwan don ki san komai ya fara lalacewa har sayayya yayi masu da zai tafi abinda ban taba gani ba tun zuwa na gidan nan. Madam tace matsalan ki ke nan Nafisa baki da kwanciyan hankali idan abu yazo maki abishi a sannu sai kinyi hargowan nan naki da kika saba ko yaushe. Don haka yanzu ki kwanta kamar komai bai faru ba yadda muka saba ta haka zamu fito mashi mu kara kaifin aikin mu a kansa don ba zamuyi sanyi muna kallo Samad ya kubuce muna ba don muna samu a wurin shi sosai. Don haka ki kwantar da hankalin ki zan shigo gidan naki sai mu tsara yadda zamu shawo kan ala,amarin tace da ita Madam hankalina baya kwanci don natsani in bude ido inga samad yana mu,amula koda na aiki ko na yan uwantaka da wata mace a duniyan nan musan man matan hausawa yan uwanshi. Kada ki damu madam tace da ita zanzo gobe sai muyi magana a tsanake amma fa sai kin kwantar da hankalin ki . Ajiyan zuciya ta sauke tana fadin zanyi kokari hakan suna gama waya ta sake kiran wata wai hajiya Auta da ke mata shige shige a kaduna. Itama bayani tayi mata na halinda take ciki tace kada ta damu gobe zata je mata zaria wurin malamin da take zuwa tayi mashi bayanin halinda take ciki. Daga nan kuma gida Niger ta kira tayi ma yar ta wace ke mata shige shige acan bayanin halin da take fuskanta daga Abdulsamad din yanzu tace kada ta damu za,a yi komai yadda ya dace. Sai lokacin hankalinta ya kwanta don tana ganin kamar har anyi aikin mako don ta yi believe da aikin bokaya da malamanta sosai. Shawaran da madam ta bata take so ta fara aiwatarwa indan ya dawo daga kadunan inda take sa ran dawowan shi yau din don tasan ba zai wuce kwana daya ba can tunda ba tare suka tafi ba. Nikan nace Abdulsamad da sauran mazan dake cikin irin halin nan sun shiga uku ga matan su ruwan sha surukule abinci ma haka wurin kwanciya ma hakane Allah ya tsare ya kare ya shirya zukantan mu. Baidawo ba ranan kamar yadda tayi tsamani abinda ya kara tayar mata da hankali ke nan ta kwana a cikin tashin hankali da damuwa. Yana gurfane a gaban hajiya mama yana mata sallama zasu tafi inda take zaune akan kujera falon ta . Akwai wani nauyi da kawaici dake tsakanin shi da mahaifiyar tashi tun farko kansancewar shi dan fari a gurin ta ba wani sakewa ko shakuwa mai yawa a tsakanin su tun farko don kawaici. Ya dubeta sanan ya sunkuyar da kanshi tare da fadin hajiya mu zamu koma ke nan ta dan dubeshi ta kawar da kai gefe tace. Allah ya kai lafiya mun gode da hindiman da akaimu Allah ya karams dukiya albarka cikin sauri suke hada baki da Yusuf wurin cewa amin hajiya mungode. Sai dai kuma rufe bakin su yayi daidai da cewan ta yaya zancen iyali ka kuma har yanzu bamuji shawaran da ka yanke a kai ba kai suka dukar kasa gaba dayan su don basu zaci hajiya zata kawo wanan zancen ba a yanzu. Taci gaba da fadin babangida kayiwa yarinyar nan adalci da diyan ka don ko sune ne jigon ka watarana kana ganin wanan abinda ka dauko na tallaban wata wace ko haihuwa bakuyi da ita ba zai haifa maka da mai ido gobe. Yaran nan fa girma suke yi yanzu idan har suka san abinda kake yi ma uwar su kana ganin abin ba zai shafe ruwan ka ba wataran. Yusuf ne ya kawar da shirun dakin bayan hajiya ta gama magana yace hajiya a dan bamu lokaci kadan don Allah akwai shirin da muke yi komai zai zama daidai bada dadewa ba da yardan Allah. Sai dai a taya mu da addua da rokon Allah wanda shi muke bukata gare ku yanzu amma nan gaba kowa zai dara in Allah ya yarda. Allah ya yarda tace dashi bata kara magana ba suka mike suna fadin zasu tafi ta bisu da addua wanda yasa zuciyar shi jin kamar an gafarta mashi a lokacin. Abinda ya dade bai samu ba daga gare ta idan yazo da fada sukan rabu a gidan rayuka sukan baci sosai. Tunda suka kama hanya ba wanda ya iya magana a cikin su kowa da abinda yake tunane aranshi saida sukai nisa Yusuf yace wanan abin yayi min dadi matuka. Yau hajiya ta rakamu da addua tare da fatan alheri a gare mu abinda ta dade batai muna fatan alheri da sakin fuskan da muka samu gareta ba irin yau. Murmushi yayi tare da kwantar da kan shi saman widow motar yana lumshe idon shi cikin jin wani irin yanayi a jikin shi. Har suka iso Abuja kamar bai cikin motar gida ya wuce dashi direct inda ya samu gidan kamar yadda ya barshi Nafisa ce da yan uwanta suke yadda suke so su kadai a gidan babu kowa nashi a ciki. Bayan sun gaisa ne ya haura zuwa sama dakin shi ya fara rage kayan jikin shi don ya dan watsa ruwa ya kwanta ya dauki lokaci a bayin kafin ya fito ya fara saka wasu kaya masu sauki a jikin shi don ya sha iska. Yana saka kayan Nafisa ta shigo dakin bako sallama tana cewa kun dawo ashe yadan juyo ya kalleta ya mayar da hankali ga abinda yake yi din. Ba laifi yau ta sa kaya masu dan kyau a jikin ta da alama kila tafita ne ko zata fita din don idan ba fita zatayi ba ita kwalliya bai damay ta ba haka take zama a gida ga kaya nan kamar ya kashe ta kuma bata kyauta wasan dadi. Cike da sallo ta karaso gare shi ta amshi dan tawul din da yake tsane jiki dashi tana goge mai kai tare da fadin kaje gida hankalin ka ya kwanta ke nan ? Bai mata magana ba haka kuma bai saki fuskan shi ba har lokacin tace nayi mamakin zuwan ka gida a wanan lokacin bayan ba haka muka saba zuwa ba. Yace banda daman zuwa ganin mahaifana sai mun tsara dake ko may ba haka nake nufi ba gani nayi ya kamata ace nasan da zuwan ka tun wuri ai. Sai da ya soma tafiya yace yanzu na canza sallon tafiya ne ba dole bane sai naje dake indan zan tafi don kema idan zaki gida ba binki nakeyi ba ai. Cikin yanayi mamaki tasha gaban shi tace may kake nufi da fadin ka canza tsarin ka yanzu yace komai ma don na fahinci baki kaunar yan uwana yanzu da ci gabana. Na fahinci sakin fuskan da nake maki ne ya jawo min abubuwa da dama daga gare ki na koma nine mata kece miji a yanzu gidan nan. Don zan tafi wurin iyayyena har kike tayar da jijiyoyin wuya wai jayi masu sayayya ke nawa nake baki idan tafiya gida ya kama ki. Kuka ta sa mashi wai yayi mata gori kan abinda yake mata ita da iyayyen ta kallon ta kawai yayi ya fara kakabe gadon shi inda yake son ya kwanta cikin kuna rai. Ta dawo bakin gadon bayan ya gama kakabewa ya kwanta ta zauna a bakin gadon tashi gaba tana kukan munafunci. Sai da kukan ya ishe ne ya juyo gare ta yana fadin kukan ya isheni hakana in zaki gyara ki gyara dan gaba tace haba Samad may kake nufi da maganan da ka fada min. Kana nufin ina hanaka yiwa yan uwanka alheri ke nan yace baki hanawa kikayi bakin ciki ga abinda zan dan kai masu a gaban kowa. Tace kowa su wa baidai Yusuf bane gurin da sauran drivobin ka yace su ba mutane bane komai tace to kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa ba insha Allahu. Nasan ban kyauta raina ne ya baci a lokacin bayin kaina bane ka sani son kane ya rufe min zuciya na. Yadan dubeta yace don kina sona sai ki hanani yima iyayyena da iyalina alheri ko may kai min afuwa ba zan sake ba tana fitar da hawaye gwanin ban tausayi. Nace naji ya wuce kuma kada ki sake yi min haka don ranki zai baci dani idan kin sake ina son in kwanta in huta ne haka yasa ta mike ta fita jiki a sabule da ita. Mamaki take a zuciyar ta yau ita Samad ke da bakin fada mata haka da bakin shi babu shayi ko tsoron da yake gwada mata. Tace zaka san koni waye idan na kulleka a wuri daya a karkshin ikona ba yan uwanka ba har iyayyenka da iyalin ka sai abinda nace maka a kan su. Kwantawa yayi don ya huta amma ya kasa samun sukuni a lokacin saboda damuwa dayayi mashi yawa ga tunanen zuwa ya duba khadija ya damay shi ga kuma Nafisa da ta fita tana kuka yanzu a dakin. Mun gama exam na dawo hostel tun jiya da na shigo ba fita ko kofan gida ba ina jin ya gidan nata parkin suna fita daya bayan daya a gidan. Kwaciya na gyara ina jan tsoki haka kawai an tsayar dani don wani bukatan da ban sani ba an bata min lokaci na ga banza. Da yanzu ina gida don tun da yamman jiya naso wucewa tunda ba wanj mugun nisa ke ga Abuja zuwa minna ba ko goma na dare zan iya tafiya gida idan na so. Wayana yayi tsuwa ban yi saurin dagawa ba sai da na lalabo na dauka naga ya Aminace take kirana a lokacin . Dauka nayi ina mata sallama bayan mun gaisa da ita ne take tambaya na kama hanya karya nayi mata nace ban gama ba sai gobe zan gama sai in tafi tace Allah ya kaimu. Na tambaye ta ina su boy yaron ta tace sun shiga wurin mommy ta aike su can. Nace ke dai da mommy sai Allah anty tace suna da kirkine mutanen akwaisu da so jamma,a sosai wallahi. Dan murmushi nayi kawai tace ah ai na manta in fada maki mutumin ki fa yazo gida ya kawo wa iyayyen shi da matar shi alheri da yan uwa kowa yana ta mamakin sauyi da aka gani a gare shi. Nace ah haba dai don Allah tace wallahi baki ga irin alherin da ya kawo masu bane khadija nima da na shiga gidan mommy take nuna min . Nace shidai ya sani ai kila buzuwan matar shi ta barshi ya kawo masu ne tace bai ma zo da ita ba ai shika dai yazo wanan karon. Nace kila shiyasa ya samu kawo masu alheri tace waya sani khadija Allah dai ya kyau ni ba kishiya nake gudu ba irin wa yan nan matan dake juye kan miji a lokaci daya ka rasa gane kan mijinka ne abin tsoro ai. Nace da sauri No no ya Amina don Allah kada ki hada yaya da wanan mutumin don ba halin su daya ba ma tace saboda may shima ba namiji bane irin sa nace na fada maki ba daya suke ba ya Amina. Tace Allah ya sauwaka nace amin tare da kawar da zancen nace idan naje gida may zance ma daddy tace nima ai zanzo kafin ku koma school idan anty hauwa ta haifu. Don ina ganin tun last month ake sa ran haihuwan ta gata ta wuce lokacin ta nace ashe cikin ya tsufa haka ne muna gida zata haihu ke nan tace insha Allahu. Mun gama waya mun kashe na ci gaba da tunanen hiran mu da ya Amina din murmushi nayi nace baki san komai ba yar uwa. Zaki sha mamaki idan kin san nice mai shirya wanan plain din haka murmushi na dan sake nace ashe nima shu,umar kaina ne ban sani ba. Kiran Yusuf ne ya shigo min yana tambayan ina ina nace hostel a takaice yace akwai mutane ne nace akwai su amma kadan yace gashi nan zuwa yanzu sai kazo nace dashi ya kashe wayan. Maryam ta dawo daga wurin gyaran kai ta samay ni akwace take fadin ai na dauka barci kike yi nace na fara ya Amina ta tayar dani ga waya. Nan nake bata labari hiran ya Amina dani tayi dariya tana bude tukuyan abincin mu tace bata san ke ce mai director ba yanzu na zuciyar shi. Da sauri nace zuciyar shi fa kikace tace uhumm wai ke baki sani ba idan baso a tsakanin ku kina nufin zai ko kalle ki ne ma. Shiru nayi ban bata amsa ba sai da ta zauna nace wai ke da tunanen ki ke nan akai mu tace bani ba kowa ma saboda kun dace dashi. Nace baki ji ba ke nan don babu ta ida muka dace dashi wallahi ni ina ni ina wanan miskilin mara dariya da fara,a. Zaiyi dariya wata rana sai kinyi mamaki zakice nace maki watarana amma fa idan kinyi nasaran canza shi din don kan ki ne zaki taimaka ba wani ba. Nace a a gyara maganan ki dai maryam don ba gaskiya zuciyar ki take fada maki ba tayi murmushi ta soma cin abincin ta. Yusuf ya kirani yace fito gani a waje ban bata lokaci ba na mike saboda na matsu inji abinda yasa suka tsayar dani garin har wanan lokaci. Dan simple makeup nayi na fito a can nesa da mu na hango motar su a fake na karasa inda yake da sallama na gareshi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Agidan su kuma Nafisa ne ke waya da kawar ta da ta baro kaduna wace suke kira da madam a cikin su tantiriyace ta kwarai na fada. Da mijin ta sai dai kamar itace mijin ba mata ba don sai yadda tayi da mijin a gidan idan tace kada ya zauna bai isa ya zauna ba. Atakaice dai ya zama mijin tace ga madam ko kawayen nata zasu iya aiken shi ya tafi komai nisan wuri koda da kafane sai yatafi yadawo. Itace Nafisa ta kira tana son fada mata abinda ya faru da ita bayan barin su kaduna ta dauko wayan ta madam ta soma nema a wayan sai dai wayan nata ringing ba a daga wayan ba takaici ne ya kama Nafisa. Ta ja tsaki ta na fadin yar iskan ko gidan uban wa ta shiga waya nata ringing haka bata dauka ba har ya katse bata dauka ba kin sake kiran layin tayi a lokacin sai taci gaba da tunanen ta tanayi tana kada kafan ta daya dake har de. Babu abin da take tunawa sai irin shirmay da ta tafka jiya din akan bakin kishin dake damun zuciyar ta akan mijin ta wanda take mashi son daba taba yi ma wani abu ba sai dai kuma a kasan zuciyar ta ba so bane can na har abandan don da zai iya shiga wani halin jarabtan rayuwa a yanzu tsaba zata iya gudun shi ta koma wa mai maski. Wayan nata aka kira ya hanata karasa muna jin birnin zuciyar sai ta dan sake guntun murmushi tana daukan wayan nata tare da fadin Aloh ina kika shiga nake ta kiranki baki daga waya ba. Cikin muryan barci madam din tace tana hamma baki hangale bata fasa magana duk da tana hamman tace wallahi barci nakeyi tunda rana. Tsuki Nafisa taja tare da fadin barci sai kace wata mai ciki ko kasa ni don Allah watseke fuskan ki kiji ni magana nake son muyi dake ki ban shawara. Madam tace ina jin ki matar manya dadi Nafisa take ji idan su madam na fada mata wanan sunan madam din ne tace ke nake sauraro fa. Wallahi ke dai madam kin san ko sai da munafukar tsohonwan nan ta hadamu da yarinyar da nake fada maku tace mu rage mata hanya ? Don Allah ki bari madam ta fada itako tace sosai kuwa ai saida muka dauke ta a mota daya mukai tafiyan. Tace yaya kika bari haka ya faru don Allah kin ko san iein mijin ki neman su mata keyi ido a rufe nasha fada maki ki nisanta shi daga ko wace mace in ba muraharamin sa bace har kika yarda hakan yafaru dake. Ke dai bari madam nanu mashi rashin yarda na ga hakan amma ya rufe ido yace shi yace umurnin mahaifiyar shi ce dole ya bi. Madam tace yaya kukayi a motar injin baki basu daman sakewa da juna ba a motan ? Tace ai in fada maki ban yarda ko daga kai yayi ya kalle ta ba kuma nima ban sake ayi hakan ba sai dai mun kwashi rikici dashi sosai da muka iso gida wai zai tafi office a sauke shi sai a wuce da ita. Bude mashi wuta nayi sosai in fada maki sai da mukayi kaca kaca dashi na kuma hana shi fita sai da aka kaita a ka dawo san nan ya tafi. Da haushi da bakin ciki ya kamani duk na farfasa kayan falon nan gaba daya don in nuna mashi bacin raina don gobe kada ya kara min haka. Madam tace kash aike kinji matsalan ki ke da zaki bishi da lalama ki nuna mai ba wata mace sai ke a duniya daga baya sai mu sake shirya wa tace. Madam idona ya rufe a lokacin da kishin ganin wanan yarinyar a kusa dashi amma da ya fahintar dani shi irin su ba su gaban shi shi yanzu wace mace zai kalla ta bashi sha,awa sai naji hankalina ya dan kwanta a lokacin. Madam tace amma kin so ki bada mu wallahi kai kin ma dai kwafasa wallahi yanzu ke ko irin matan abujan nan ya lalubu maki har ki ta da hankalin ki haka mudake da wuka a hannun mu nama kawai muke jira. Kawai yanzu idan ya dawo kije ki bashi hakkuri akan abinda kikai mai din don kada ya zarge wani abu a gare ki. Kin ga zaki ji a bakin shi ko ita wanan yarinyar wacece a garesu kin dai san yadda zaki bugi cikin shi ai muji komai a saukake. Tace zanyi kamar yadda kika ce din amma ba yanzu ba zan dai saka ido in gani idan suna tare ko basu tare sai musan abinda zamuyi daga baya. Sun dauki lokaci suna maganan akaina ana ta kulla sheri da tugu akan mazajen su kafin suyi sallama madam tace zata kira zuwa gobe taji indan da wani matsala kuma. Na gama shiga da komai daki na da taimakon wata yar gidan namu da ta dawo tagan ni da kaya ta tsaya taimaka min. Kayan jikina na fara cirewa san nan na fara gyara kayan ina aje komai a inda nake bukatan shi na gama na zauna ina tunane a raina. Bakomai nake tunane ba sai mijin buzuwa da Allah ya jefo a rayuwana a dan lokaci ya taimaka min yau gani da kudi a hannu na wanda yakai dubu dari ta dalilin mijin buxuwa da iyayyen shi duk na samay su. Waya na dako a cikin handbag dina ina neman layin ya Amina don in fada mata abinda ya faru don komai ya faru dama nakan kirata in fada mata. Kira uku ta daga wayan ina ji bata kusa da wayan ne a lokacin mun gaisa nake tambayan yaranta tace suna lafiya sun tafi islamiya. Nace anty kin san wani abu da ya faru yau tace ina zan sani Khady nidake kaduna zaune kina abuja ke. Nace anty yau na hadu da mijin buzuwa danaje sayayya tace kun sake haduwa kuma again nace wallahi anty wai duk wanan uban kayan da na sawo nazo biya sai ake ce min ai ya biya bayan da suka sauke ni ranan ya ba driver dubu hamsim ya bani. Kai da gaske khadija nace wallahi anty kuma su suka kaini gida sai dai shi bai so su dauke ni ba sai abukin shi ne yace saboda mama ne suke min haka. Dariya tayi tace to Allah ya saka da alheri ki dai bi a hankali inda duk kuka hadu don buzuwan nan ba imani ke gare ta tana iya komai akan mijin ta. Ya Amina ni inama zan kara ganin shi kuma Allah dai ya tsaga rabona daga Aljihun shi wanan karon mutumin da ko yaushe take a cikin hade fuska banda gaisuwa may zai hada ni dashi kuma. Daga haka muka kawar da zancen shi muka dauko na iyayyen take fada min cewa sunyi waya da baba yana fada mata kudin su na ritaya ya kusa fitowa kwanan nan. Ihun jin dadi nayi don murnan iyayyen mu zasu fita acikin hali talaucin da suka shiga na ritayan da mahaifin namu yayi muke cikin halin kaka nakayi. Tace ai zan riga ki ji idan kudin sun sauka don haka sai abinda kika samu daga baya nace ai ni indai daddy zai samu bukata na ya biya ke nan. Yanzun ma shawara nakeyi inje banki gobe in tura mai kudin da mijin buzuwa ya bani don akwai kudaden da zasu isheni a hannu na tunda ina da abinci waddatace . Tace haka akeso mutum idan ya samu ya tuna da iyayyen shi dama dako kin kyauta wallahi dama sallaman ki ya hanani tura mashi kudi wanan watan. Haka dai mukai ta hira da ita daga karshe mukayi sallama na kashe wayan tare da mikewa na jona electric dina don in dafa dan abinda zanci da dare. Kira, a na saka a wayana ina aiki ina bin kira a don ni gwanace a wurin iya hadda tun ina yar shekara sha hudu na sauke alkurani mai girma na sake maimaitawa yakai kashi uku yanzu don duk wanda yasan yaran minna ya sansu da ibada da kamun kai ga girmama na gaba dasu a duk inda suke. Da wanan halin namu nake shiga ran mutane farat daya kowa tsakani na dashi gaisuwa ne na mutunci da sani girman wanda ya girmay mun. Na gama na zuba a plate na dauko ledan ruwa guda cikin wanda na sayo na aje a dakin na zauna don in fara cin abincin sai ga kiran waya ya shigo min. Binta ce ta kirani a lokacin na dauka kafin wayan ya tsunke hiran mukayi sosai ranan da ita har nake mamakin ko nawa ta sa awayan ta haka don da mun sake wanan hiran take dauko min wani. Har take fada min yadda akayi ranan da zamu wuto da buzuwar yayan su tace bazata shiga mota dani ba mama ta dage daya zo mata da maganan kan lalai sai sun tafi dani. Nace kin ko ga tunda muka kama hanya batai min magana ba nima ban masu ba daga ita har mijin ta. Tace wanan ai dama shi miskili ne magana kamar aiki yake ganin sa a gare shi zai iya zama da kai kuyi awa daya baice uffan ba haka kuma matar shi anty fati itama take shiru shiru bata magana. Nace aiyanzu sun samu mai magana a tsakanin su haka yasa ta samu daman musguna mata yadda take so ai. Tace ke kin ko san halin wanan matar shu,uma ce wallahi ta karshi da farko da tazo boye halin ta tayi kamar wata mutumiyar kwarai da ita. Sai daga bayane ta fitar da kalar ta kowa ya sani bata kaunan ko dan uwan yaya ta ganshi a gidan nan wallahi. Nace wuri ta samu wallahi ni kar nake kallon ta don banga abin tsoro ba anan ku dai na fahince ku kuna bata girma ne don mijin ta yana da hali a cikin ku. Tace ga tsiya nace eh mana haka din ne amma in bashi ba ta yaya zaku zauna wanan matar ta dinga raina maku hakali har tace wai idan tana wuri kada ayi dariya . Tace ina ma kika sani khadija ai sai wani lokaci da mukaje hutu wurin su a abuja ba girma muka dawo gida kwanan mu biyar ko sati bamu kai ba matsi yai muna yawa a gidan. Muka matsa ma yaya zamu dawo ga yan uwanta nan muna ganin yadda take ji dasu amma mu ko falo ta hana mu fito muka koma kamar wasu bare ba yan uwan maigidan ba. Dariya nake mata sosai tace Allah ko magana mai karfi wai ba ai mata a gida tace ba kallo ba komai sai zagi da hattara ga anty Fati damu da ita duk muka koma daya. Bayan mun dawo sai ga anty Fati ma ta dawo wai a kaduna zata zauna bata iya zama da buzuwa a abuja bata bari ko miji ta gani idan yana gida. Nace ke ki bari don Allah ashe ba karamar shuuma bace tace baki santa bane Khady wanan fa ko kashe mutu tana iyawa fa. Nace wanda Allah yabata ikon kashewa ba wani kan ai yafi karfin ta wallahi ba abinda zata iya wanda Allah bai tashi yi da bawan shi ba. Ni don Allah har kin ban haushi da wanan maganan naki don ba a gidan ku nake ba wallahi da taga tsiya a guri na nifa irin matan barikin nan haushi irin su nake ji. Zako kiji nata don bata da hali mai kyau ko kadan akan mijin ta zata iya yiwa mutum komai musan man ma ce ko waya tayi da wata ranan sai sunyi jidali sosai da ita ke ta zama mai kaya ko shi yanzu bai da yadda zaiyi da ita ne kawai wallahi. Nace ya dai ga dama ne Binta idan ka ganshi ga mutum har mutum amma baida kuzari gun mace tir yayan ku ya zama mijin hajiya wallahi. Haushin abinda na fadi taji da fada muka karasa wayan a rana na kashe ina mata dariyan shakiyanci na gama na wanke kayan na samu wuri na kwanta. Washe gari da wuri na fita don ban yarda in makara in ba wani dalili ya tsayar dani ba mai karfi shi kadai zai sani makara kawai. Ban da yawan kawaye sai mutum biyu yan department din mu kosu shirin mu dasu don sun ga nafisu kawo wuta sosai a class din shine likewan su dani. Banda wasa ga abinda ya kaini abujan daga school sai gidan mu sai ko idan wani dalili zai sa na fita a ranan zan fita. Yau ya dawo a gajiye don daga wurin aiki ya wuce wuri wasan polo da suke yi don dan wasan ni ne sosai wanda yana daya daga cikin abinda ke kawo mashi kudi a lokacin bai dogara ga aikin shi ba yana buga buga irin na maza gida da waje shike sa yana samun mahaukacin kudin da yake riko. Wanka yayi yana saka kaya a jikin shi ta shigo dakin dan juyawa yayi ya kalle ta ya kawar da kan shi yaci gaba da abinda yake yi. Karaso wa tayi gare shi tana wani rangaji na daukan hankalin shi ta sake abinda yake so ya sauko mata har mazaunan ta. Cike da sallo ta iso gare shi sai dai tsiyan shi da ita duk gayun ta bata damu da saka kamshi ba kuma har yanzu ba gwanewa tayi ba da iya kwalliya shine ma yake kokarin wurin gyara mata idan tayi wani kwaliyan zasu fita. Gata da son karya sai dai ko bokon kasar su bata samu ba kuma babu na Allah a tare da ita abin ya taru yai mata yawa amma hakan bai hana shi son abin shi ba. Rungumoshi tayi ta bayan shi ya sauke wani ajiyan zuciya yana dan murmushin jin dadin ganin ta tace yau ina ka shige haka ne ta dawo ta gaban shi suna fuskantar juna. Bai ce komai ba yadan jajeyeta ya dauko turare yana fesa ma jikin shi tace har da daren ma sai an feshe jiki da turare ko fita zakayi ne haka ? Sai lokacin yayi magana yace sai zan fita ne zan saka kamshi a jiki na ke baki son kamshine ashe yasa baki sakawa . Taji zafin maganan amma ta daure don in da sabo ta saba da gorin saka kamshin da yake mata din ko yaushe kuma hakan bai sa ta saba da sakawa ba. Tace muje kaci abinci yace na koshi ta dubeshi da sauri tace tare da fadin ban gane ba yace mun ci abinci da Yusuf kafin in dawo. Juyawa yayi ya nufi saman gadon su yana jawo laptop din shi tasan idan ya fara dakilan laptop sai ranta ya baci kafin ya gama. Idan tayi magana kuma yace business yake a ciki shi ko wani abin dariya tayi ya dago yana duban ta na lafiyan ki kalau kuwa ? Sai yaji tace maganan turaren da kayi ne dai yaban dariya har na tuna da yarinyar da mama ta saka mu dauko ranan. Bakaji wani irin kamshi tiraren da takeyi ba kamar tayi wanka dashi yace tasan kan ta ne yasa ta saka turaren haka don kada a raina ta. Tace shi saka turare kuma har wani sanin kai ne dashi wai ma may ye alakan ta da mama ne data nace sai mu dauko ta wai ? Yana bude laptop din yace sai yanzu kike son jin halakan su da mama da kishi ya rufe maki ido baki tsaya tambayan ta ba da farko. Tace kayi hakkuri cikin yanayin tausasa harshe tace nasan ban kyauta ba kishin ganin ka kusa da wata mace nakeyi tundai irin wanan yarinyar dake cikin ganuwan kurciyan ta ga kyau kuma da gani tana kuri da ilimin ta. Ina tsoron ka hango kyawon tane wallahi kazo kace zaka dauko min ita a gidan nan wata rana son ka nake har karshen zuciya ta ka sani. Ya tsaya yana mata wani irin kallo yace don kina kishina sai ki min hauka mata nawa nake gani a rana da ina raayin mata ne zaki san lokacin da zan nemay su ne. Har kina fada min cewa mahaifiya ta da biyu ta hadamu tafiya da yarinyar don in so ta kika haukace har kina fashe fashe a gida. Kwantowa tayi a jikin shi ta dan shafi kan shi tace kai min afuwa don Allah haka ba zai sake faruwa ba a tsakanin mu. Yaji hakkurin da ta bashi har cikin ranshi yace ki rage kishin nan nake don ni din mijin mace hudu ne watarana. Da sauri ta rufe mai baki tana fadin don Allah ka daina fadin haka don kana sa zuciya ta tana bugawa da wanan zancen kishiyar da kake min. Yace idan lokaci yayi ai yi zanyi sai dai ki tausasa zuciyar nan naki bakiga mahaifina matan shi hudu ba kin sani ko in gado shi nima ? Kuka ta soma mashi tana fitar da hawayen munafunci a idon ta dariya yayi mata yace akan kishiya kike wanan kukan haka fati fa ba kishiyar ki bace kin ga ai ko yanzu kina da ita ke nan. A bar maganan Fati tace don ni kaina ma kunya nakeji ace wai ita din kishiya ta ce balle kai ace matar ka ce Fati ta sunna. Ohh kin fison indan zai ne ma yanzu in nemo wace idon ta ya bude sosai don itace ta dace dani tace ba haka nake nufi ba don Allah mu bar zancen kishiyan nan haka na. Tambayan ka nayi cewa wacece wanan yarinyar ne sai ka dauko min wani dogon zance kuma akan kishiya ? Yace nima ban san ta ba a gurin mama wanan zuwan da nayi na fara gani ta koma waye dai ita nasan alakar ta da mama mai muhinmaci ne sosai. Shiru tayi tana nazarin maganan shi daga karshe dai data ga ya fara aikin shi ta kwanta tana ci gaba da tunane kala kala a zuciyar ta. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Maryam kamar jirana take in gama debe kayan a jikina ina zama tace amma friend zurinfin cikin ki yayi maki yawa wallahi. Ashe wanan guy din da ake nema ruwa a jallo dan uwan ki ne ban sani ba saurin kallon Maryam nayi nace ruwa a jallo ake nemas may yayi. Tace tsadan ganin gare shi mana gashi dai matashi ne amma Allah ya kai shi ga babban matsayi nace wani matsayi ne gare shi wanda kike zuzutawa haka wai ? Kai haba friend zakice baki san koshi waye ba kina tare dashi haka mutumin nan fa na hango tsatsan son ki a kwayar idon shi. Nace baki hango gaskiya ba idon ki bai hango maki gaskiyan alamarin ba kuma koda kin hango ma bai taba zama gaskiyan magana. Mutumin da gidan shi yafi karfin shi a karskashin mulkin ki mace yake wanda baida mutucin duban yan uwan shi tunda na fara magana ta kafe ni da idanuwan ta. Shiru nayi don na farga na fara sakin layi dariya tayi tace min kin dakata kuma mana nace barni da abin haushi don Allah kwantawa nayi rigingine ina tune a raina sai kuma na bushe da dariya ni kadai. Kallo na tayi tana mamakin abinda nakewa dariya haka ni kadai nace yau akwai bura uba a gida Samad tace akan may kuma nace ke dai bari. Buzuwar matarshi ta bugo waya tana tambayan shi na dauki wayan nace mata gashi nan wuri na baida lafiya. Ido ta zaro waje tace kika amsa kiran matar tashi khadija nace kwarai kuwa ina dariya nace zata gane shayi ruwa ne maryam. Ba gani take ta mallake shi ba ba macen da ta isa tazo kusa da shi hatta uwar shi ta raba shi dasu duk yan uwa ganin su take muggaine bata yarda dasu ba. Kirikiri ta hana matar shi zama a dakin ta dole yanzu saida ta koma gida take zaune ba ruwan shi da yaran da ya haifa da cikin shi. Tace khadija kina nufin wanan guy din yana da iyali haka dama idan ka ganshi sai ka dauka ko auren farko baiyi ba a rayuwan shi. Nace wa mai iyali ne da kike ganin shi wurin nan auren gata ya samu ga iyayyen su shine kuma bai iya riko ba saboda buzuwar matar shi. Nace Wasa farin girki yanzu muka fara wasan da ita sai na manna mata karamin hauka a zuciyar ta tunda tace bata son hurdan shi da ko wace mace. Haduwa goma zamuyi dashi sako goma zan tura mata muje zuwa indai nice ko wace mace da dabaranta ake haihuwan ta sai dai na wata yafi na wata kissan. Khadija kin ko san kisan macen buzuwa macen buzuwa fa duk inda take shu,uma ce bata bari miji ya zauna da matar shi lafiya sai ita. Nace maryam kin san ko matan minna ko waye su ba buzuwa ba ko tsakiyan matan maradi za a kaini na shirya mata indai akwai ayar Allah. Zan bi dare in bi rana sai na nuna mata muma matan Nigeria akwai shu,umai cikin mu ai banda matsala tunda na san lagonta ta . Allah ya bamu saa tace nace amin sai na girgiza kai nace bawai da manufar yaso ni har cikin ranshi nake wanan abin ba yi dai nake in nuna mata boka da malam karya ne. Tace yanzu yaya kuka kare dashi nace korata yayi daga motar shi kai tsaye dariya ta kwashe dashi tace ai ba zaki kara ganin shi ba ko. Nace gobe ma yayi nesa ki gan shi nan ai ni abin har mamaki nake ji wallahi tace don dai kince buzuwa ce matar shi amma da sai in ce wani namiji zai samay ki ya bari ki kufce mashi khadija. Kyau Allah ya baki tsayi da gashi ga ilimi addini dana boko kin tara ranan da naji kina karatu wallahi har rudewa nayi na raya a raina da naje gida komawa zanyi makaranta ni ma na samu in sauke. Tun ina karama fa na sauke maryam yanzun haka ban bar karatu ba don ina nan ne bana zuwa amma a gida ban wasa da karatu ko kadan kinga yayata malama ce sosai wallahi. Tace ai naga alama tun haduwa na dake idan kuna waya da ita zata tana makaranta ko gata tana shiri fita makaranta may yafi wanan dadi ga mace. Nace kinga mu zama yakawo kakannin mu zama garin minna amma aslin mu yan wani gari ne da ake kira ka,oje tun ana hade da sokoto da Niger yanzun haka mu bamu san gida ba mu filani ne na asali wallahi. Mahaifiyar mu ce kwarin minna amma saboda zama muka juye muka zama mutanen minna baki sanin mu baki ne idan ba mun fada ma ba. Haba nature din ki yayi kama sosai da na fulani ashe ma ke ruwan su ne nace ada ke nan ina so zuwa garin mu sosai inga yan uwana wallahi. Don ance har yanzu yan uwan mu suna garin don daddy din mu shi yasan gari har yakan je lokacin da bai tara iyali haka ba. Tace ya kamata ku nemi gida su san ku fa nace muna da burin haka nida ya Amina ai sai dai kin san abin sai an shirya ne . Dakin shi ya nufa ya fara cire kayan shi zuciyar shi yana mai soya yana jin kamar ya ganin a gaban shi ya shake ni don haushi da takaicina da yake ji. Nafisa ce tazo dakin har lokacin a hasale take daidai ya fito daga wanka ta yi mai wani mugun kallo tace yau sai ka fada min gurin wace kaje har ta dauki wayan ka ta kirani dashi. Baiyi magana ba sai kokarin saka jallabiyan da yake yi a jikin shi ta karaso tana ce mai wata yar iska yar kasada ke son shiga rayuwan ka Samad ? Ido kawai ya tsura mata yana kallon ta batare da yayi mata magana ba ta sake maimaita tambayan shi samad ka fada min wa cece kaje wurin ta har ta dauki wayan ka ? Ta karaso tana rike mai kwalar dogon rigan da ya a jikin shi yanzu kama hannuwan nata yayi ya murde ya wurgata saman goda ya nufi inda turaren shi suke ya dauko yana fesawa jikin shi. Ta kara juyowa ta nufo shi a hasale tana cewa kunji kun gama iskancin ku shine ka dawo gidana kana min wankan tsarki anan. Da mamaki yake kallon ta ya bude baki da kyar yace Nafisa yau ni kike wa zargin aikata zina da wata kace tace dole in maka samad may ye hadin ka da wata mace , ? Yace dani mazanaci da akan ki zan fara tunda dashi kika gabatar min da soyayyan ki farkon haduwan mu dake. Haushin maganan shi taji sai ko ta haushi da duka da yakusa tana ture shi tsayawa yayi yana kallon ta da mamaki. Jayeta ya kara yi ya hakadata gefe ya fice daga dakin ta biyo shi tana zagi ta uwa ta uba ya shige dayan dakin ya kyale ta. Yana shiga wayan shi na kara ya dauka Yusuf ne yake son fada mashi ya gama tsara masu tafiyan da zasuyi kaduna. Yace sai dai abinda zamu saya wa yaran nake son mu dauko khadija ta zaba muna abinda ya dace dasu tunda mu ba zaben kayan yara muka iya ba. Yusuf ya ambaci sunan shi a kasalance Yusuf din ya amsa mai yace don Allah ka rabani da wanan yarinyar dake batun tarwatsa min gida da rayuwa na. Cikin mamaki Yusuf din yace tayi ma wani abune kuma ban sani ba yace may ne ma batai min ba yanzun haka in ka saurara zaka iya jiyo hargowan Nafisa akan khadija. Da sauri Yusuf din yace dashi kai haba sun hadu ne komai ko ta samu labarin khadija din ne yace basu hadu ba sai dai yau kaddara ya hadasu a wayana. Nan ya koro mai abinda ya faru yau din dariya sosai Yusuf ya kwashe dashi lokaci guda yace kai khadija akwai jan magana da rashin tsoro. Yace ni yau taja min masifa da fushin Nafisa a gidan nan ban son wanan bakin kishin na Nafisa wallahi idan ya tashi bataji bata gani imagine wai har ni Nafisa ke ma zargin zina yau. Intrested ashe yau tasan zaka iya kara aure ko wani lokaci ke nan wow i am impress da jin wanan labarin Allah yasa haka yasa ta fara gyara halin ta. Rikici kake son jawo min Yusuf da ka hada ni wanan aljanan yarinyar mai shegen rigima wai dole sai itace zatai min wanan aikin ne ? Kana son mu canza wata ce ya tambaya shi a cikin gatse yace No da sauri yace ta faye matsala ne wallahi. Yace da matsalan nata za a gyara komai kai dai ka kara hakuri don Allah yace wallahi yarinyar ta fara shiga raina amma kuma ta faye matsala ne ai. Yanzu yaya zan iya shawo kan Nafisa a gidan nan gaba daya ta birkice min yau kan kishin wace ma bata sani ba har da duka na fa takeyi. Duka kuma subbahanallahi kai kuma sai kai tsaye tana dukan ka ko mai yace to may zan mata Yusuf kit Yusuf din ya kashe waya alaman yaji haushin maganan abokin nashi. Dariya ya soma yi bayan ya kashe ma Samad waya yace komai na zuwa yadda nake so da alama samad ya fara son khadija. Wayana ya kira bayan mun gaisa yake tambayana ashe yau mutumin yazo gurin ki shi kadai nace eh dan matsalan yazo min wai bashi da lafiya. Sai bayan na taimaka mai da magani yaji sauki ya soma karanta min haukan shi wai na fita mai a motar shi tunbai balbalani ba. Dariya yayi yace may ya hada ku har haka nace bakin rigima na yasani daukar mai wayan matarshi da take neman shi ganin kamar barci yake wayan nata ruri nikuma sai na dauka. Dariya yayi sosai a lokacin yace aiko nasan yau suna can suna tafka fitina a tsakanin su kin ja mashi aiki yau Nace shi ta sha matsoracin namiji kawai wanan ma ko ga maza yan uwan shi nasan matsoracine wallahi dariya Yusuf yayi sosai. Yace to yanzu na kiraki ne don Allah gobe indan kina free zaki taimaka muna da sayen kayan yaran samad don Friday zamu shiga kaduna insha Allahu. Nace idan dashi ne gaskiya ba zan tafi ba yace saboda may khadija kefa kika kawo wanan idea din zaki ce kuma bazaki tafi ba. Ki daure ki karasa ladan ki don Allah ai ba don shi zakiyi ba yaran fa kika dauki alkawarin taimakawa saboda Allah shiru nayi yace may kikace nace a hankali naji sai dai idan ya wuce gobe ba zan samu fita ba don ina da exam talata kuma zan wuce gida. Yace nagode khadija Allah ya biyaki da alherin sa yadda kike muna Allah ne kadai zai saka miki sai mun hadu goben zamuyi magana Allah ya kai mu nace dashi. Na kwanta cike da tunane a raina wai dama da gaske akwai mazan da suke irin wanan rayuwan a gidajen su don dai ni nasan mahaifin mu zaki ne a gidan shi akan iyalin shi. Wai duk gidajen masu kudi haka yake ne rayuwan su sai mata ke juya su yadda suka ga dama idan ka gansu awaje sai kai masu kallon isa da izza amma a gidajen su sai ka raina su. Yaya matashi kamar Samad zai zauna mace tana juya shi haka yadda take so wai kuma yana sunan miji a gidan shi gashi da ilimi daya dace yayi amfani dashi ako ina ya kama amma mace ta na juya shi son ranta. Kwafa nayi nace wallahi gobe zasu ga tsiya don sayayya zanyi masu kamar na hauka inta gani ta haukace da tushe. Washe gari nace ma maryam ta shirya zamu fita da su yaya Samad zasu zo mu muyi wa iyalin shi sayayya tace tau da murnan ta. Mun shirya tsab don Yusuf ya bugo min waya suna kan hanya zuwa wani dan abu ne ya tsayar dasu yanzu. Sun iso wayan Yusuf ya shigo min gasu a kofan mu nace gamu tafe yace keda wa khadija nace da kawata maryam zata tayani zaben kayan ne sai kun fito yace min. Mun fito daga gidan kwanan namu na dalibai muka hango su can nesa kadan inda suka aje motar su muka karaso wurin . Motar Yusuf ya fito ya bude muna muka shiga ya rufe sai da muka zauna muka fara gaida su wanda nidai kusan Yusuf kawai na gayar maryam ne tace da Samad yaya jikin shi yace cikin daga hannu da sauki. Sai looacin ciwon kan da yazo dashi jiya ya fado mashi a rai don fitinan da suka kwana sunayi da Nafisa yasa ya manta da komai nashi. Kawar ki bata magana ne Yusuf ya kawar dashirun da motar yayi a lokacin maryam ne ta bashi amsa da fadin ai itace dai magana ya zama aiki a gare ta nikan ko aku ya ganeni ya kauce min wurin zuba. Ashe kuna da aiki shi yasa abin yazo maku daidai naji mamakin da kika iya zama da wanan mai zubin yan ruwan dariya ta danyi tana cewa ashe kaima kyaunta na ruda ka haka. Haka take ruda maza a cikin makarantar dama wajen makarantar amma kunsan may wai duk wanan bata ga may mata ba har yanzu ga kyau yana tafiya a banza a gurin maza. Tsuki yaja tare da juyowa ya dan watsa mata harara lokacin da take fadin ni wallahi ina son ganin lucky man din zai iya sace zuciyar wanan yar kwalisan yarinyar. Zaki ko sha zaman jira don maza basu son zuben mace irin wanan da ko ina tabi surar ta na rawa sun fi son mace mai natsuwa da kamala. Yusuf yace har kin sa yau na fahinci wani abu da kika kawo wanan maganan haka nayi real sign ba karamin kyau ki ga khadija ba da har na kasa fahintar abinda yasa abokina yake yawan rudewa idan ya hadu da khadija ashe kyawon tane yake yawan tsorata shi yana mata kallo mai kama da tsoro but still yanzu da yai maganan nan sai na gane kyauta ne yake yawan ruda shi. Da na dan shiga rudanin wanan abin amma yanzu maganan nan da kikayi yasani a hanya watau a takaice aboki na yana rudewa idan yaga khadija sai take mashi zubin yan ruwa idan ya kalle ta. Tayi saurin fadin ya gano sirin da Allah ya boye ne anan ai khadija matar manya ce wallahi duk namijin da yai saa ta kalleshi da manyan idanun nan nata yakan shiga rudu ne ya rasa inda yake ina ga shiya take tsoron fita wallahi. Don Allah malam idan kun gama kaja mota kakai mu inda zamu ko ka mayar damu inda ka dauko mu zaifi ya fada batare da ya juyo gare shi ba Yi hakkuri malam abinda na gani na fada yasin khadija ta hadu ba karya a gurin nan kai mai dani inda ka dauko ni ya fada a dake. Nidai nayi kamar badani suke yi ba kaina yana duke ina danna wayana dake hannu na muna charting da zarah. Yusuf yace karkai fushi dani abokina gaskiya muka fada anan take a deep breath and confess khadija ta fi matan da kake gani haduwa. Bude baki yayi ya zaro ido yana kallon yusuf da mamaki kalaman shi dayaji na bazata yasan Yusuf ne kadai duk duniya yake iya fahintar shi lokaci daya. Yusuf ya sake kallo shi ya dan lagabe kai tare da girgiza mashi kai yace dont give me that look just say yes to your mind she is realy beautiful as you see. Take ya daure fuskan shi tamau tankar bai taba dariya ba yace Yusuf kayi kuskuren furtan hakan a gare ni don kafi kowa sanin banda lokacin yin hakan . Nace kunyi babban kuskure Yusuf da kuke son kamanta da wanan mutum matsoraci ko kuna zaton sakewan da nayi daku kun dauke shi da wani manufane ? Ba so ko wani abu makamancin haka cikin zuciyana don ban taba daukan haka ba a tsakanina dakai sai mutunci da niyar taimakon ka a zuciyata don rayuwan ka na bukatan taimako da agaji ga wanda yasan shi. Tsakanina daku kuma sai dangantarkar irin na zumunci na an fito wuri daya da biye min da kukeyi da kyautatawa . Da ka sani da baka dauki haka ba da zafi don zuciyar ka ta baka ba daidai ba me yasa zakayi zaton soyayye zai yuyu a tsakanin mu don kana kyakyawa mai kudi maiji da ilimi da wayewa ko may ? To ni duk wanan nasaban naka baya burge ni don ni ina fatan samun miji ne wanda yasan kanshi yake iya mulkata ba in mulkeshi ba ko wata tana mulkanshi. Barin fada maka ban taba jin son ka wallahi a raina don halinka bai mun ba bai kuma taba burgeni ba tausayi ne da fatan alheri ka shirya da iyayyen ka takowani hali . Don halinka da dabiar ka yanayin rayuwan da ka shiga da komai naka yana bukatan gyara a yanzu. Ya isa yace da karfi ya fada cikin kuna rai, yayin da maryam tunda na fara magana take rufe min baki waina bar maganan . Idon shi yayi mai jawur hankalin shi yana neman barin jikin shi zuciyar shi yana son tarwatse mai yace ba laifin ki ba ne. Yaja wani irin huci ya furzar a bakin shi yace Yusuf ka juya mu sauke su inda ka dauko su don Allah. Bana son inkara ganin fuskan yarinyar nan na tsane ta wallahi bana son kara haduwa da ita a rayuwa na . Shiko Yusuf a ranshi ya gigice da fadan mu sosai yana rayawa yaushe ne zai samu cin ma manufar shi a kan mu yaushe zasu bar wanan halin may yasa Samad ke biye mata suna haka kamar wasu yara kanana. Ya zama mai dole ya shiri mu tun yanzu tun kan mu rabu a hakan ba wani ci gaba gashi ya fara ganin hasken alamarin tun ba a je ko ina ba. Ya zama dole ya gyara wanan abin tun anan don ba zai yarda abokin nashi yaci gaba da zama haka ba yanzu in ya bari muka watse a hakan abin bayi ba wallahi. Naji Yusuf din yace Khadija ba nufin abokina ke nan ba baki fahince shi bane tun farko kin san tun jiya fa yana da haushin ki a ranshi don haka don Allah bashi hakkuri ya huce dake haka please. Yadan juyo yana kashe min ido sai na gane manufarshi da sauri sai da na hade wani bakin ciki na iya furta to kayi hakkuri don Allah ban fahince ka bane na fada a sanyaye. Da kyau Khadija matar na tuba ko bata laifi komai rintsi ya juya gurin shi yace kayi tsamanin jin hakan daga bakin ta yanzu a yadda tahau din nan. Wani iri yaji yace a ranshi may yasa na kasa fahintar wanan yarinyar ne wai me yasa na fadi wanan maganganun masu zafi gareta yanzu bayan nasan gaskiya Yusuf suka fada. Halinta daban ne da na sauran matan dake bina suna ribibin in so su kai tsaye zata iya fada ma gaskiya batare da tsoron komai ba kuma ya amfane ka. A sanyaye yace Yusuf ban san may yasa take son bata min rai ko da yaushe muka hadu ba zan bata dama taci gaba da min yadda take so ko yaushe. Motar ta tsaya a bakin wani plaza babba ba wanda yayi magana Yusuf ne yace bissimila mun iso mu shiga mu fito tukun. Fita mukayi a motan har lokacin jikina a sanyaye nake jin shi don abinda ya faru a motan Yusuf ne yazo daidai inda nake yace khadija na gode da kika fahince ni ba komai nace dashi cikin yake. Muna shiga shi yana bayan mu yana tako a cikin izza da kamala maryam tazo daidai kunne na tace dan dakata mai ku jera mana. Hara na aika mata nace sai dai ya mutu idan sai na jera dashi din ya dai ci albarkacin Yusuf da kuma na iyayye wallahi. Ban garen kayan yara muka nufa inda maryam ta fara duba kayan ina tayata har lokacin ban sake ba nan muka shiga jidan ma yaran kayan sawa da sauran abubwan yara. Mu koma bangaren takalma da dasu sauran abin bukatan yara harda su tawul da sabule da su kulan zuwa school muka hado dashi a hankali na taka wurin kayan mata na zaba ma anty fati kusan kala goma masu kyau da tsada. Su dai ido kawai suka saka min har lokacin da muka gama Yusuf yace mu zabi abinda muke so ni wani jakka da takalma kawai na dauka maryam kuma ta dauki wani dogon riga da jakka. Munje gun biya muka da ja baya naga ya ciro katin shi na bakin ya basu suka debe kudin su suka miko mai mun shiga motar mun zauna. Yace kina ganin mun sai komai da zasu buta nace insha Allahu har maman su ma da sauri ya juyo yadan kalle ni kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa yusuf yaja motan muka tafi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Hutun sati uku kacal muka samu wanan karshen zangon don haka naji dadi sosai da bai kasance dogon hutu bane don zan samu zama a minna tare da iyayyena in yi hutu. Wanda rabo da in samu kasancewa dasu haka a wadace har na manta yanzun haka na fito daga zana jerabawan karshe na wanan zangon da mukayi da yazo min da rikicin haduwa da Abdulsamad da abokin shi Yusuf. Ba ranan zan tafi ba sai washe gari don haka maryam ta tsaya jirana don taso muje gidan yayar ta na nuna mata ban son zuwa can din. Komai na gama shiryawa a dakin sai kayan da zan saka ne da katifa ban samu daga wa sama ba don kwantawa da zanyi na yau kawai da safe in dage shi sama in tafi gida. Bayan mun rabu dasu yusuf ya kirani yana tanbaya na ya muka isa hostel din mu tare da kara yi min godiya . Bayan mun kashe wayan gidan Abdulsamad suka nufa sun kusa shiga gidan ne Abdulsamad din yace dashi idan sun tafi kada a sauke kaya da aka sayo a gidan shi abar kayan acikin mota kawai idan sun isa Yusuf yagane manufan shi na fadin haka. Sai dai bai ma abokin nashi magana ba gamay da abinda ya fahinta na son kada a sauke kayan dayace kada ayi har lokacin gidan ba dadi tsakanin su da Nafisa. Wanka ya fito yana goge ruwa akanshi ta shigo dakin har lokacin tana nan cikin fushinta da shi zuwa tayi tambayan shi kudin da tayi requesting wana zata yi tafiya zuwa gida. Tace Samad kwanaki na ta matsowa har yanzu bakai magana kan abinda na bukaci ka bani ba wanda zan je gida dashi indan zan tafi sai in wuce dashi. Yadda take magana bai sa ya daga kai ya kalle ta ba Samad dakai fa nake magana ya dan wuce ta zuwa bakin gado ya zauna . Ta juyo gareshi tace magana fa nakeyi maka kana ji kuma ta fadi a hasale sai lokacin ya dago yace kada ki kara yi min maganan nan. Don bashi ke gaba na ba gobe kaduna zan tafi in daba iyayye da iyali na wani irin gumzi tayi tayo kan shi tana fadin wallahi baka isa ba. Ba kuma inda zaka kaje na fada ma don baka fada min zancen tafiya ka ba don haka ban shirya ma tafiyan ka yanzu. Murmushi yayi yace kice ma mai shirya min tafiyan don kece zaki sallamay ke nan ko ? May kake nufi da wanan maganan haka ban ci na sani bane idan za kai tafiya yanzu koma ko da da kake fada min ni nake sa ka fada min . Yace shine kuskuren da na aikata a baya yanzun kuma a shirye nake da na gyara komai da ya faru ido ta zuba mai cikin firgici take. Ganin zata damay shi yasa ya fice ya bar mata dakin don da dakin yaso ya gyara kafin ya kwanta don ya kwana biyu ba samu tsayawa ya gyara ba. Don yanzu gyaran dakin kwanan nashi ya dawo kan shi saboda indan yan uwan nata sun mashi gyara sai abubuwan da dama suyi ta bacewa a dakin. Wanan yasa ya daina bari su shiga mai daki suyi mashi gyara sai shi ya ke gyaran dakin nashi da kanshi ya don yafi mai sauki idan bai gyara ba ita bata da lokacin gyaran . Haka kuma zata shigo ta kwanta a cikin dakin ba kunya ba tsoron Allah haka dai ake rayuwan a dunkule ba wani jin dadin irin na aure tsakanin mata da miji. Laptop din shi ya dauko ya na dubawa sai dai tunane ya hana shi yin wani aiki a ciki bakomai yake tunane ba sai irin maganan da nake fada mai, mai kama da shagube yana jin haushi na ashe gaskiya nake fada mashi. Yaushe rabon shi da yaran shi suzo kusa dashi su zauna a matsayin shi na mahaifin su suji dadi babu. Ya tanbatar da ya tafka babban kuskure da Allah zai iya kama shi da laifin da ba zai iya amsawa ba gobe kiyama. Khadija khadija ya furta a hankali kin taimake kin ceci rayuwana ta yadda ban taba zato ba wanan wace irin yarinya ce mai hikimà da basira. Ya dade a wurin zaune har ya kai kwance sai da wayan shi yayi ringing ya daga wani yaron shi na wurin aiki ke gaya mai an samu wasu filaye ns gwaunati a gwagwalada da wasu mutane ke son ci. Yace da yaron nashi ya bari sai next week za a duba case din idan Allah ya kaimu sun gama waya kiran Yusuf ya sake shigo mai inda yake fada mai gashi a kofan gidan shi sin dawo da motaci an gama duba su . Yace gaya nan fito mikewa yayi ya zura santala santalan kafan shi cikin wasu budaddun takalma ya sauko zuwa kasa inda ya samu falon cike da yan uwan Nafisa kamar suna shawara. Ganin yadda ya fito yasa ta dago kai tana kallon shi ya fito ya samu Yusuf din zaune a saman dan wani dakali yana jiran fitowan shi. Ya fito ya fara mai baiyanin komai basuyi aune ba sai ganin Nafisa sukayi a gaban su tana huci ba bata lokaci ta shiga dura ma Yusuf din zagi tana ai banta shi. Bai tanka ta ba sai faman kururuwa take masu a kai tana kiran da munafuki dan bakin ciki ko bai so sai ya gansu da Samad agidan shi. Dama tasan duk wani munafuncin da ga wurin shi yake fitowa daga shi har samad din sai ta dauki mataki a kansu. Amma dai karki manta bakece Allah ba ko don haka babu wani abin da zaki iya muna sai Allah don in da sabo ya saba da wanan halin na Nafisa. Sau da yawa idan sun kwaso rikici da mijin ta a kanshi take saukewa don tana ganin shine mai zuga shi sai taga ta kamo shi da kyau dan lokaci kadan kuma sai abin ya juye mata. Wanda take ganin Yusuf din ne ke mata zagon kasa a hakan sai dai bai nasaran rabata da Yusuf din da yake son yi ko yaushe. Da kyat yan uwanta suka samu takoma ciki bayan sun kare masu kallon banza suka shige da ita cikin gida tana ta haure hauren rashin mutunci. Washe gari tun da safe ya shirya Yusuf yazo zasu tafi kamar yadda ya saba motoci uku zasuyi tafiyan da shi sai dai wanan karon tafiyan ya canza masu sallo. Na farko su kadai ne ba tare da buzuwa ba na biyu kuma tare da a abin arzikin da bai saba tafiya dashi ba zasu dunfari gidan. Ana kara gyara kaya kamar daga sama sai ganin ta sukayi a wurin motacin tana ganin kayan ta shiga tonawa har ta gano abinda ke cikin buhuhunan da akayi siling din su din. Ranan sun ga masifa haka sukaja mota suka tafi ransu bace da halin da Nafisa ta nuna masu din sun isa a cikin lokaci gari bai je gidan ba sai da ya karasa gidan shi ya huta don sun iso kan shi yana mashi ciwo sosai saboda hayaniyar da baiso. Tunda Yusuf ya sauke shi yanufo gidan nasu da abinda suka zo inda sai gani motane keyi anata shiga da kaya a cikin gidan ana jibgeasu a kofan hajiya mama kamar yadda ya umurce shi da yi. Sun kasa boye mamakin su anty amarya ce ta fara tambaya anya wanan abin da Nafisa ko aka zo wanan karon dariya Yusuf yayi yace bada ita bace anty muka dai muka zo. Mommu tace abin kan da mamaki gaskiya Allah yasa babangida ya canza daga wanan karon dariya Yusuf yayi yace insha Allahu mommy kudai taya mu da addua. Ya shiga dakin hajiya mama don ya gai da ita ya samay ta da yan matan ta suna mamakin wanan sayyayan da suka gani haka wai daga gun Abdulsamad ya fito haka ? Ya shiga dakin sai da ya zube kasa ya fara gaida ita sai faman murmushi take yi har lokacin ta kasa boye mamakin ta bayan sun gama gaisawa dakin take tambayan shi wanan sauyin yanan Abdul din data gani. Yace hajiya adai taya mu da addua kusan kece sillar canzawan nan nashi lokacin fada maki komai baiyi ba amma nan gaba insha Allahu zan sanar dake komai so nake komai ya tafi haka yadda muke so dashi . Don yanzu insha Allahu akwai canji sosai wallahi nan dai suka dan taba hira yace Abdulsamad na tafe zamuyi bayananin komai idan ya shigo. Duk da zaman lafiyan da akeyi gidan bai hana a kebe gefe ba ana gulman wanan sabon yanayin da aka hango a gare shi. Sai dai kowa ya matsu yaga abinda ke cikin buhuhunan wanda ba wanda ya iya gane komau ye a cikin su su indan gaiyan aikin nasu ya shigo. Saida suka sauko sallah jumma a ya shiga gidan iyayyen nashi a falon Alhajin su ya fara shiga ya gaida shi da mashi yaya jiki ranan yaga sauyi sosai na sakin fuska a wurin mahaifin nashi wanda ya dade bai gani ba. Bayan sun gama da mahaifin nashi ne ya shiga ciki ya fara gaida ummi sai mommy sai anty amarya ya wuce dakin hajiya mama wanda dama kullun itace karshen shiga da yafito kuma sai ya bar gidan. Sun gaisa da ita acikin sakin fuska ya dubi Affan dake zaune gefenta yana cin abinci ya kira yaron saboda rashin sabon da basuyi ba dashi ya dago ya kalle shi kawai ya gaida shi. Sai baiji dadin yadda yaron yayi mashi ba shiru ya dan biyo dakin take tambayan shi iyali ya amsa da duk sina lafiya hajiya tace dole ita da yan uwanta zamu tambaye ka don sune yanzu iyalin naka. Babangida yanzu kana ganin abinda kakeyi kana aikata daidai a rayuwanka mutum ya watsar da iyalin shi ya rugumi wasu bare can. Shiru yayi ya dukar da kanshi tace kaima kanka fada kada ka mutu a cikin wanan halin kasan Allah na zai barka ba Yusuf ne yace ayi hakkuri hajiya komai zai zo daidai in Allah ya yarda adai tayamu da addua. Nan ya fara mata bayanin kayan da suka zo dashi inda ta fahinci komai yace saura kayan abinci muyi magana ko za a kawo zuwa yamma sai a raba yadda ya kamata. Yayi mamakin yadda yaji mahaifiyar tashi tana kwararo mashi addua yau da saka mashi albarka wanda ya dade baiji ba daga gare ta duk zuwan da yake yi da fada sukan kare ya fita rai a bace. Yau sai gashi sanadin yarinyar da yake gani mai matsala a gare shi yaja mai samun addua irin haka a gurin mahaifan shi bai fita gidan ba sai da yayi masu alheri yakuma mata alkawari zai je zaria yayi masu taaziyan rashin da akayi can. Taji dadin jin hakan sosai na ya fito ya barsu a cikin farin ciki ya koma gidan shi don yana bukatan hutu a lokacin bayan fitar shine hajiya ta kira su mommy tana masu bayani aka shiga bude kayan da ta nuna masu din. Kowa yayi mamakin ganin hakan don basu zaci haka ba yanzu a gare shi sai addua suke mashi da fatan gamawa lafiya kowa aka cire mai nasa cikin farin ciki da jin dadi. Tunda ya koma wake kwance a dakin shi na gidan ba abinda yake tunane sai irin yadda na fada mai magana mai amfani acikin gatse kuma yayi mai tasiri. Yani yace a ranshi lalai ya zama dole in san yadda zan gyara alamarina da yarinyar nan don ita din ba abin yar wa bace . Cikin dan lokacin kadan tayi min sanadin dawo min da farin ciki tsakani na da iyayyen har da yan uwa wanda wanan tunanen bai taba zuwa min ba ko wani ya tsayar dani ya fada min gaskiya yadda take fada min kai tsaye. Tayi namijin kokari wurin ganin ta tsaya ta fada min maganna irin haka kai tsaye bataji shakka ko nauyin fada min yadda kowa ke shayi na ba. Wayan shi aka kira ya daga Faiza ce take mai godiyan abinda aka kawo masu yace babu komai ta kashe kuma Lawisa yar wurin ummi ma ta kirashi tana mashi godiya haka suka dinga kiran shi sai da yagaji ya kashe wayan shi ranan. Wani irin farin ciki yake jin kanshi ciki mara misaltuwa da wanan kiran da yan uwan shi suke mai a lokacin don ba zai ce ga ranan da suka kirashi karshe ba. Ya zama dole gare shi ya san yadda ya gyara mu,amulan shi da duk wani dan uwa nashi da ya watsar da farko. Sai yaji yana sha, awan ya kira layin khadija a lokacin yayi mata godiya haka yasa ya jawo wayan shi ya kira layin ta. Ina fitowa cikin makaranta na samu guri na zauna ina jiran maryam tafito mu wuce cikin gidajen mu don an kara muna kwana daya yanzu. Kiran shine ya shigo min wanda tun bayan rabuwar mu ranan ban kara ji daga gare ba sai yanzun da ya kirani din na tuna dashi. A hasale na dauki wayan ba tare da nayi magana ba don na gane shine jin shiru ya danyi yawa banyan na dauki wayan sai nace A hasale nake fadin lafiya ka kirani ko ka kirane ka fada min ka tsane ni din da kake fada min ko yaushe ?. Murmushi naji yayi kasa kasa sai ya sake kiran suna full yace khadija a zuciye nace ina jinka ai yace ba wanan kiran nayi maki ba yanzu. Nace may ye ka kira malam ni kada ka bata min lokaci haushi ne ya ishe shi a lokacin yana rayawa a ranshi yaya zai yi dani ne wai ? Cikin sanyi murya yace min thanks khadija na gode kwarai da taimakon ki gare ni sai dai don Allah, , , , Dama abinda yasa ka kirani ke nan don ka samu wani sabon yaudara ka zageni kuma dashi na fahince ka don haka banda lokacin ka ni yanzu. Na fadi a cikin tsigar tsokana tare da saurin kashe wayan sai dai a zahiri jikina yayi sanyi da yadda naju yana maganan cikin wani yanayi. Shiko ina kashe wayan yabi wayan da kallo kamar nice wayar ya sauke wani irin ajiyan zuciya yana fadi a fili shi kadai a daki. Wanan yarinyar ni yaya zanyi da ita ne wai ta fahince ni yanzu ya girgiza kai yace kina da matsala khadija yarinya haka bata da kwaciyar hankalin fahinta. Why why khadija baki so na da kwanciyan hankali a tare dani yanzu ne mikewa yayi daga kwancen da yake ya nufi fridge ya dauko goran ruwa mai sanyi a ciki ya kwankwada tare da wurgi da goran ya fito falon shi. Mutane ya samu sunzo gaida shi inda ya bisu da alheri sai yamma lis ya samu suka rage nan ya nufi bathroom din shi don ya dan watsa ma jikin shi ruwa ko zai ji sanyi. Dan ruwan dumi ya hada saboda yanayin garin na kaduna ya shige jacuzzi ya dan dauki lokaci yana tunane kafin ya fito ya sa kaya a jikin shi ranan a maslcin uguwan su yayi sallah magariba tare da jamma, an unguwa da mahaifin shi aciki. Ba abinda yake tunane sai yadda zai samu mu shirya a tsakanin mu gashi dan lokaci kadan yarinyar ta shiga zuciyana ta samu wuri a ciki. Tunanin yadda zai shawo kaina amma ya kasa samun mafita har wanan lokacin shigowan suraj soja wurin shi yasa ya matan halin da yake ciki don sun dauki lokaci dashi suna fira kafin Yusuf ya shigo mai da abincin da mommy ta girka masu. A tare da Suraj da Yusuf din sukaci abincin suna hira a tsakanin su bayan fitan Suraj ne suka samu kebewa da Yusuf wanda tun bayan zuwan su basu samu zama a tare ba. Nan yake kara mai godiyan kokarin da yake mashi inda yake sanar dashi ya kira ni don yai min godiya amma naki fahintar shi Yusuf din yace ya sake kirana zan fahince a hankali. Ba laifi yace dashi sun dan dauki lokaci sukayi sallama akan da safe zai shigo su tafi zaria idan sun dawo yana son kuma ya dan je wurare masu muhinmanci a kaduna daya dade bai tafi ba. Yusuf na fita ya kira waya maryam ta dauka ta miko min bayan ta dana recieve na dauka da sallama na kara a kunne na. Bayan mun gaisa ne yake rokona da in karba wayan abokin shi inji may zai fada min dariya nayi tare da fadin abokin nan naka ne ai sai a solo baida mutunci. Yace kada kice haka Khadija baki fahince shi bane amma abokina mutumin kirki ne wallahi ki bashi dama ku fahinci juna yanzu zai bugo waya godiya yake son yi maki akan taimakon da kikai mashi na bashi shara kuma yabi yaji dadin shawaran ki shine zai maki godiya akai. Munyi sallama dashi ranan maryam tazo dakina wai a nan zata kwana saboda exam din da zatayi washegari yana da zafi ita kuma tana son tayi karatu a daren ranan. Muna tsaka ga karatu wayana yayi kara na daga tare da karawa a kunne na muryan shi naji yana tambayana har yanzu baki barci bane. Karatu mukeyi na bashi amsa yace OK dazun na kiraki in maki godiya kika kashe waya nace ina busy ne a lokacin. Khadija ya kira sunana amsawa nayi ciki ciki yace please ki bani dama in maki godiya akan abinda kikai min shiru nayi na kasa magana. Khadija kina jina nace ina jin ka mana sai naji tayi wani kasalalen murmushi yace in tambaye ke zaki ban amsa tsakani da Allah ? Nace sosai makuwa idan har na sani may zai sa in boye maka tunda ba rike min baki zakayi ba. Ajiyan zuciya naji ya sauke sai can yace may yasa kike son yawan bata min kina son ganin hasalana ni koda ban tashi hasala ba ? Kin tsane ni kin ki jini baki kaunar ki ganin a cikin farin ciki why khadija why kika zabi wanan rayuwan a tsakanin mu. Shiru nayi na kasa magana nauyin shi da kunyanshine suka kamani a lokaci daya na rasa may zance dashi don yadda yake magana bazakace shi din bane mai izza da jiji da kai. Nasan kin san bawai son soyayya ne a tsakanin mu ba amma kuma kika zabi yin haka a gare ni ki fada min may ke sakina tsana na haka da yawa. Dan murmushi nayi tare da fadin yaya Abdulsamad ke nan ni nasan babu dingo soyayya ma a tsakani mu tun farko sanan kuma ni ko in so ka ko da so ka ba abinda zai ragaka dashi duk dayane a wurin ka. Ni dama ba kai na tsana halin ka na tsana da matar ka da bata san mutucin yan uwanka ba har hali ku ya juye iri daya da ita. A yau in rayuka zai sauya kasan mutucin kan ka dana yan uwanka ka farga ka dawo yadda mahaifan ka suke son ganin ka da yan uwanka ka san darajan su da mutuncin su fiye da kowa. Amma ni may zai sa na tsane ka kana a matsayin yayana aiko don mama zan so ka zanyi muamula dakai kamar kowa. Don dama ba kinka nayi bani halin ka dai na tsana bani ba kowa ma zai so ya kulla halaka dakai ta yadda baka zata ba. Murmushin da naji yayi yasani shiru yace khadija idan nace maki ashiri nake da in caza yanzun zaki yarda koma in ce dake din na canza a sanadiya ki. Jin shi kawai nakeyi ta yaya ni zan iya canza mutum kamar Abdulsamad a lokaci daya haka. Muryan shi naji yana fadin kina mamaki abinda na fada ne yanzu yace yes ke khadija kin tunatar dani abinda na manta acikin abinda nake dauka shirmay kukeyi ke da Yusuf a lokacin. Nace ba abinda mukayi da har zai kawo sauyi gare ka haka da wuri sai dai idan dama Allah ya kaddara tamu din abin zai fito ma. Kuma ina mai farin ciki da jin haka idan ya kasance gaskiya ne maganar ka da sai nafi kowa farin cikin haka a duniya. Yace to ki fara farin ciki daga yau don ko kin sa iyayyena sun min abinda suka dade basu min ba a yau don haka khadija ban san ta yaya zan gode maki ba da tunatar dani da ki kayi ga abinda na manta hakki na ne yinsa a baya. Koda da wasa ko gatse kika fada min wanan magana to ki sani your words inspired me har nakai ga samun kalmar albarka a bakin iyayyena yau abinda na dade baji ba a gun su. Yau kin dawo min da farin cikin dana rasa da dadewa a tare dani kalman ki na ranan gare ni sun sa na dawo da natsuwana. Ya kuma fara dawo min da respect da power na ga idon mutane dana rasa a baya wa yanda ya kamata ace komai wuya komai dadi ina tare dasu. Ba zan iya kwantata maki dadin da naji ba yadda na kasance da yan uwana da abokai kai har ma da makwabta na ayau suna murna da zuwa gare su. Don haka yazama dole in gode maki please khadija kada kiki fada min gaskiya a duk lokacin da kika ga na kauce ma hanya. Murmushi nayi nace naji dadi kuma na tayaka murnan dawowa farin cikin ka gare ka don ko yau ranan kace ranan farin cikin ka. Ka kuma gode ma Allah da bai sa ranan ya kasance ranan nadamar ka bace ya fargar dakai da wuri haka. Allah ya kars shirya zukatan mu ni zan kashe karatu nakeyi ka tsayar dani don gobe zamu gama exam jibi gida zamu. Da sauri yace jibi wata rana nace talata inda Allah ya kaimu da safe zan tafi gida don yin hutu a can. Yace No kada ki tafi don Allah ranan ki jira in dawo akwai abinda nake son in shirya akan tafiyan ki nace Allah sarki dama ka hutar da kan ka don ni a shirye nake yanzun haka. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Zaman da maryam yana min dadi sosai don itama bata da wasa da karatun ta gashi musan mutuncin junar mu kamar mun dade da haduwa da ita. Ita ta tilasta min fara amfani da kayan da Yusuf ya saya min tace may ye amfanin ajesu da nakeyi gara dai a fara gani a jikina zai fi. Ban sake bi takan su Yusuf din ba na mayar da hankalina ga abinda ya kawo ni garin sosai sai dai muna waya da kowanin su har yanzu wanda wayana da Samad duk ya kira fada ne da zolayan junan mu har ai fada a kai ga kashe wayan. Munyi jerabawan karshen zango na farko inda muna gap da gamawa Yusuf ya kirani nake ce mai sati mai zuwa zan tafi minna don ba zan leka kaduna ba wanan hutun saboda hutun ba mai yawa bane . Nan yake ce min suna tafe gurina kafin in wuce gida don suma zasu shiga kaduna don Samad ya dade bai je gida yana kokari yaga ya shawo kan shi su tafi. Nace ka barni dashi in gwada in gani idan zamuyi sa, a da nawa dabaran yace ya gode muka kashe wayan suna zaune tare aiki suke a wani file. Yusuf yayi mamakin jin ya tambaye shi khadija yace tana nan lafiya kasan jerabawa suke yi kwanan nan wayan shi ne yai kara baiyi saurin dubawa sai da ya gama abinda yake ya dago wayan. Kallon Yusuf yayi da mamaki tare da fadin Yusuf yarinyar nan ko mutum ce jifa itace ke kirana yanzu muna maganan ta. Yusuf ya kalle shi yace mutum ce mana kamar kowa kaima kana ranta kamar yadda take a ranka ke nan . Ya dauka ciki daure fuska kafin in magana ya fara fadin lafiyan kirana ina aikina nace lafiyan ya kawo haka ai . Ya sake kiran suna na a zuce da karfi yace matsala na amsa mai da cewa may ye ne haka zaka fasa min kunne da kira haka kamar makaho. Kai na tsani wanan yarinya ya fada a hasale na amsa mai da nima haka wallahi cikin yanayin na bashi amsa. Nace dama abinda yasa na kiraka don in fada ma ya kamata kaje gida ka duba tsofin ka don gudun su da kakeyi ba shine mafita ba gare ka. Yace what da karfi don bai yi tsammanin jin wanan magana haka ba a baki na Duk wani da mai neman albarkan iyayyen shi yana tare da su a kullun suna saka mai albarka da fatan gamawa da duniya lafiya don samun haske a gare shi. Kai kana ganin kudi da girman kai da suke rudin ka zasu iya sama ma farin ciki haka ne a gare su, sunyi ciwo sun yi rashi amma bakai tunanen zuwa ka duba su ba har yau. Who dear you are da zaki fada min abinda zanyi akan iyayyena, nace ni bakowa bace sai mai neman albarka iyayyena don haka kai ma na tunar da kai akan hakan. Kuma kada ka manta da su Affan don sun fi kowa bukatan ka a wanan lokacin don nasan zaka iya zuwa masu hannu sake kai ba abin kunya bane a wurin ka. Don haka oga aje a duba su kada a shagala da yawa wataran sune masu duba mu you are stupid kece zaki tunatar dani komai kike nufi wai ke wacece wai waya baki wanan right din da zaki min wanan magana haka. Nace gani kamar kowa na tsoron fada maka gaskiya don suna ganin kana da kudi niko kudin ka ba damuna sukayi ba wallahi gaskiya komai dacin ta dole ne in fada ma mutum shi. Amma gani nayi buzuwan ka kamar kanta kawai ta sani sai yan uwanta ai don haka nima dan uwa na na sani a yanzu. Kit na kashe wayan ina dariyan keta shima Yusuf dake zaune yana jin yadda mukayi dashi sai murmushi yake yi yana huci yabi wayan da kallo. You see abinda nake fada maka kenan gashi yarinyar nan har ta hango tunda kaji ta fadi haka akwai abinda taji ya faru a gida may be. May yarinyar nan ta dauki kanta ne wai zanyi fa maganin ta a garin nan Yusuf da sauri Yusuf din yace kunfi kusa ai ni dan kallo ne a tsakanin ku sai dai ya kamata ka bincika idan ba wani taji bai da lafiya a gidan ba. Tsaki yaja yana rufe file din da suke aiki akai alaman rashi ya baci sosai ya dafe kai da hannun shi daya tunane ya shiga yi yaya akayi yayi sake rainin da bai taba shiga tsakanin shi da kowa ba har shiga tsakanin mu haka wai abinda nake mai zakace ko mu din cousin ne. Kan shi yana dafe da hannu shi daya Yusuf yace muci gaba mana yace kana iya tafiya yanzu makarasa next yanzu matsala ya shiga . Dariya yayi yana mikewa yace matsalan khadija ke nan ko hararan shi yayi da idanuwan shi da sukai mashi ja shidai ya fice bai yi magana ba. Ya dade zaune a gurin a karshe ya jawo wayan shi yana neman layin mommy don ita kadai ce zai tsaya yayi magana na fahinta da ita ya gane komay ke guda. Kira biyu ta dauki wayan da sallama a bakin ta ya amsa mata tare da fadin mommy kowa na lafiya ko kwana biyu ban kira waya ba. Tace lafiya kalau muke sai dai Alhaji ne jikin nasa ba dadi wallahi wanan matsalar tashi dai ta kwanaki ke damu shi kuma sai kuma Affan da suka kwanta asibiti amma dai yaji sauki sosai yanzu. Wanan yarinyar takai shu,uma wallahi mommu tace wace yarinyar ke nan kuma yace da sauri No magana mukeyi a nan bayan ya gama waya da mommy sai ya kira hajiya mama. Sun gaisa ta fara mai korafin rashin kula da kyautatawan da bai yi take mai fadan ga mahaifin shi nan ba lafiya yan uwan shi na kai da komo akan sa amma ace shi yayi biris dasu badon suraj da yazo ya kai shi asibiti ba may yake son mutane su fada a kan shi. Hakkuri ya fara bata yana fadin in Allah ya yarda jumma,an nan mai zuwa zai shigo ya tabayi jikin Affan sai bata bashi amsa ba. Bayan sun gama waya ya dade zaune a wurin kafin ya mike ya nufi hanyar fita office din ya rasa abinda ke yawan shagaltar dashi yanzu gamay da iyayyen shi haka. Zuciyar shi ne tayi mashi zafi don haka ya nufi gidan shi dan ya dan sarara batare da ya sanar da kowa ba ya fice a ma,aikatar nasu sai gida. Tun a kofa yake jin suruntun yana shiga Nafisa tana zaune a tsakiyan falon tana shan bakin shayi a dan karamin cup tana lumshe idanuwanta. Ganin shi a wanan lokacin tayi mamakin dawowan shi gida yanzu rigar da ya barta dashi na barci ne saye a jikin ta har wanan lokacin ga su hadiye na busa shisha duk falon ya gauraye ta ko ina kamar ba falon da ya narka ma makudan kudi ba haka. Batare da yabi ta kansu ba ya haye sama zuwa part din shi har ya kama hanyan da zai kaishi dakin shi sai kuma ya juys ya shige dakin hutun shi ya rufo kofan. Sai da ta gama shan attayen ta ta mike zuwa wurin mijin nata ba tare da damuwa da irin shigar dake jikin ta ba bata samay shi a dakin ba don haka tasan yana dayan dakin da yakan kebe kan shi wani lokaci. Can ta nufa duk da tasan ba lalle bane ta samu kofan a bude sai dai tayi mamakin da ta tura taji kofan a bude ta sa kai ta shiga yana kwance yayi rub da ciki a saman gado ta iso gare shi tana fadin. Samad yau lafiya ka dawo irin wanan lokacin tana kokarin hawa saman gadon ta zauna a kusa dashi juyowa yayi yana fuskantar ta wani irin karni da bashi kanta da jikin ta ke sakewa da kyat ya daure yace banjin dadi jikina ne tace oho ba sannu ba Allah sauwaka. Samad dama ina son in fada maka satin nan akwai bukin da zamu maradi sai kuma wayan nan kannen nawa maza da suka zo zasu koma gida. Gashi kuma ina son ka canza min mato don wanan naje dashi har sau biyu an sani dashi sai kuma su hadiye da nake son inyi wa sayayya kafin mu tafi dakuma, , , , Ke enough ya ishe ni don Allah duk wanan abin a cikin sati daya kike son inyishi ko kay wai may yasa ke baki da tunane ne wai ? Tsayawa tayi tana kallon shi galala tana mamaki yadda a dan lokaci yake son juya mata baya haka a lokaci guda tace Samad ni kake dakawa tsawa haka. Kallon ta yayi yace an daka maki ke baki da aiki sai na abaki dai a naki ai ma yan uwanki kaza ai masu kaza sam baki damu da na wa yan uwan ba da damuwar su. Tace amma kasan ina da yan uwa da ka aure ni ko yace wa kika fi yan uwa da bukatu ni nawa yan uwan basu son ai masu ne komay. Tace wanan kai ya shafa matsalar kace kuma ni dai nawa yan uwan na sani kuma dole kai masu don dani sula dagora. Mamaki da karfin halinta yaji yadda take fadin magana son ranta kai tsaye ta nuna mashi nata kawai ta sani shi yaji da nashi. Queen matsala kinyi gaskiya yace a ranshi ya ta tunar dani wani abu mai nauyi da na manta a rayuwana shiru yayi taci gaba da masifan ta akan shi bai iya furta komai ba a lokacin. Tashi yayi ya fada bathroom ya rufo kofan da karfi ruwa ya watsa a jikin shi yai wanka tare da yin alwala don yayi sallah la,asar don har lokaci ya dan gwauta da mintoci. Har ya fito tana zaune a wirin inda ya barta ya dauki room fresh ya fesa a dakin don bashin da dakin ya dauka ganin zai ta da sallah ya sa ta fita daga dakin ta barshi. Gyaran kai da jiki mukayi na zuwa gida don haka agajiye muka shigo hostel din mu maryam ta zauna dafa muna abinci ni wanka nashiga don zafi nake ji jikina ina ganin yayi min dauda. Tsab na fito nayi sallah a wirin na jawo ledan ice cream din da maryam ta sayo muna na fara sha a hankali maryam tace wallahi ji jake kamar kada ai hutun nan da za ayi. Da sauri na juyo ina ce mata saboda may maryam kika fadi haka tace ban son rabuwar mu wallahi yanzu ko ja koma gida banda wata abokiyar hira a kusa dani don anty na ba zama takeyi ba tana da yawan tafiye tafiye kullon don ita business woman ce . Nace ko dai ai koya nene kyayi kewan gida mana ni banki ba yanzun haka in bude ido in gani a cikin garin minna ma. Tace kin ji dadin ki wallahi khadija na yarda ba jin dadi bane farin ciki don ko dashi ne da bazan fadi haka ba farin ciki yana ga inda kake da sukunin aiwatar da komai. Kafin in magana wayana yayi kara na dauka kina ina nace maynene yace ki ban amsa kada ki min halin ku na yan African don Allah . Katambayi mutum ya mayar ma da tambaya shi kuma nace ina hostel mana yace ok kawai ya kashe wayan shi dip bin wayan nayi da kallo nace miskilin banza kawai. Maryam ta gama abinci wanda indomei da kwai ta dafa muna wanda yaji danyen attarudu mai yaji a ciki zubawa tayi a plate guda ta dauko muna lemon kwali a cikin fridge din ta wanda muke ajewa yanzu a ciki ida mun samu. Na fara cin abincin ke nan cibi biyu kawai nayi wayana yayi ringing na duba yaya Samad nagani a layin kamar kada in dauka dai na dauka kuma gani a kofan ku ya fada kawai. Kofan mu na maimaita da mamaki nace may kazo yi a nan kuma ban sani ba yace idan zaki fito ki fito sai ya kashe wayan kawai. Tsaki nayi na wurgar da wayan tare da fadin dan wahala kawai maryam dake zaune ta tsura min ido tana kallo na murmushi tayi tace. Uhm wani lucky guy din ne yazo haka ake ja mashi aji kuma abinda wasu ke nema ido rufe a zo gurin su anzo kike wanan masifa haka ? Nace sister kin faye bin kwakwafi wanan fa ba masoyi na bane zuwa kawai yayi ya bata min lokaci na ina zaune kalau. Don Allah ko may ya kawo shi kije ki saurare shi ba dadi mutum yazo wurin don ka ka wullakanta shi haka muje in zaba maki kayan da zaki saka in maki rakiya. Dole na mike muka tafi dakina ita da kanta ta zaba mi wani dogon riga mai ruwan ganye da dan karamin gyale shi sai da na shirya tsab a cikin rigan tabi jikina ta feshe da turararuka masu kamshi muka rufo kofan muka fito tare. Yana zaune a cikin motar shi riga da wandon shadace mai guntun hannu rigar ma iya ciya dinkin yake light green kayan su matukar karban jikin shi da dinkin . Wurin dirkekiyar motar shi da ke fake a kofan can dan nesa kadan damu muka nufa ko ganin maryam ya hana shi fada ban sani ba sai cewan da yayi. Ita ko maryam tunane take a ranta ina tasan fuskan nan nashi ne ya katse mu da cewa kin san ina waje zaki shanyani a wanan wurin naku mai kazantar tsiya haka ? Nayi dan dariya tare da cewa cikin wayance abinda yafa da nace ga kawata maryam tazo gaida kai don ma ita ta matsa min in fito yanzun haka. Anyway maryam ga yayan mu Abdulsamad Abdulrahim nan ku gaisa tace dama nace kamar nasan fuskan nan ai tace ina wuni yayan mu anzo lafiya yaya iyali. Yace lafiya kalau yaya karatu koda yake exam kukeyi yanzu ko yana wani kauda kai yana basarwa . Tace karatu Alhamdullahi mun kusa cin ma karshen shi da yardan Allah ai a huta gajiya dama nace barin zo mu gaisa ne kawai yace to na gode kwarai da alama kin fi kawar taki kirki sosai. Dariya tayi tace a a wallahi ai kirkin khadija na daban ne wallahi tana da kiki matuka shiyasa ma nake jin dadin zama da ita wallahi. Baki ya tabe ta juya ta tafi tana mashi a huta gajiya ta nufi hanyan shiga hostel din namu sai lokacin na sauke ajiyan zuciya bayan tafiyan ta. Katse ni yayi da fadin tsaye zaki min sai kace wanda tazo tadi da buduruwar shi haka bude kofan motar shi yayi na zagaya na shiga sai naji ya rufe motar. Shiru daga ni harshi ba wanda ya iya magana a lokacin sai ma gyara kwanciya yayi a motar bansan lokacin da nace dashi baka da lafiya ne Yaya Samad. Shiru yayi kamar baiji ni ba sai can yace may kika gani a tare da ni nace yau na ganka so weak ne ba miskilancin nan naka yasa na gane bakajin dadi ko baka cikin good mode. Wai ke aljana ce ko may dazun kin fada min magana akan ahalina ya zama gaskiya yanzu kuma waya fada maki banjin dadin jikina ? Nace yanayin ka ya nuna min haka sai ya dago da sauri ya na kallo na nima kallon shi nake yi sai dai ba zan iya jimirin kallon nashi ba a lokacin saboda kwarjin shi da ya cika min fuska a lokaci daya dukar da kaina nayi kasa ina wasa da yan tsun hannu na. Yau ina bakin naki ya shiga nace ko don Yusuf ne dama kike da bakin a gaban shi nace da sauri ko daya wallahi gani nayi yau kana bukatan kulawa don baka cikin hayacin ka sosai. Don jikina ya bani baka da lafiya sai naga ya koma ya kwanta kamar yadda yake da farko ya fadi a kasalance cewa kaina kamar zai rabe biyu nake jin shi khadija. Kasha magani na tambaye shi da sauri yace ban sha ba wani magani kake sha yace panadol extra nakan sha wani lokaci. Wayana na fara dannawa ina neman layin maryam ta dauka nace fito min da panadol extra din nan da goran ruwa don Allah yaya Samad bai jin dadin jikin shi tace to da sauri na kashe wayan. Motar shiru ba a dauki lokaci ba sai ga maryam ta iso da maganin ta kwankwasa glass din motar ya bude mata karba nayi ina mata godiya tace babu komai mana Allah ya bashi lafiya. Maida marfin motar nayi na rufe na fara kokarin bare mashi maganin tare da bude goran ruwan nace mai gashi ka sha. Ya dago kanshi da kyat ya kalleni ya kalli maganin da ruwan da nake mika mai sai naga ya bude min bakin shi alaman in bashi da kaina . Dan rankwafawa nayi ina saka mashi maganin a baki na kawo goran ruwan na bashi ya hadiye da kyat yana wani lumshe idonun shi yana bata fuska. Komawa yayi ya kwanta tare da fadin thanks nace Allah ya baka lafiya amin yace da kyat ni dai komawa nayi na zauna na zuba mai ido. Wasu irin jijiyoyi naga sun fito rada rada saman goshin nashi wanda ban taba kula ko yana dasu bane dama tsoro ne ya kamani kada wani abu yazo ya samay shi fa a nan wurina nawa ya samay ni kuma. Shiru daga ni har shi ba wanda yayi magana a cikin mu har mintina na shudewa a hakan suna batun zama awa daya muna nan a hakan dashi kamar mai barci. Abu daya ne yasa hankalina dan kwantawa ganin yana numfashin shi normal a lokacin yasa nayi shiru tare da zuba mashi ido kawai ina kallon ikon Allah. Wayan shi dake aje a motan ne ke ringing ganin anata kira bai dauka ba yasa na daga kiran don ba suna batare da na saurari mai magana ba nace mai wayan bai da lafiya please. Naji muryan mace tana fadin ke wacece da sauri ya dago ya kwace wayan a hannu na ya katse kiran yace akan may zaki daga min waya waya baki wanan damar da ikon daga min kira a wayana. Zanyi magana yace get out tunda ka samu lafiya yanzu zaka iya ci min mutunci sai dai ka sani ba zan ce ma komai a yanzu ba don yanayin da kake ciki na bukatan natsuwa. Get out i said na bude motar na fita ba tare da na juya na kalle shi ba naji ya tayar da motar ya jata da karfi yabar gurin nashige ciki abina. Dakina na shiga na wurgar da sauran maganin saman katifana na fara kokarin cire kaya a jikina sai ga maryam ta shigo tace ashe kin dawo. Eh ya tafi ya samu lafiya ai nace mata ina daura zanin a jikina na nike kayan na za saman jakkunan kayana dake gefe daya a dakin. Shiko tunda ya kama hanya yake jin wani bacin rai da bakin ciki a ranshi yana fadin wanan aljanan yarinyar sai ta kasheni wata rana. Yarinya yanzu ta sauke min bacin raina yanzu kuma ta kara sakani a wani anya ma mutnce kuwa dai , ? Yana shiga gidan a hargitse ya samay su duk kan su Nafisa ta haukace masu daga ita sai dan buje a jikin ta tana fadin yaushe samad ya fara cin amana na haka ? Yaushe samad ya canza ban sani ba nayi sakaci da yawa har na bari haka ya faru a yau da ban dauki mataki ba. Haka ya shigo ya samay ta tana wanan sambatun a cikin yan uwanta da suke ririke da ita kamar sabuwar mahaukaciya. Nan ya shigo baice da kowa kalaba cikin fushi ya shigo gidan don haka basu ga fuskan wani magana a gareshi ba. Tayo cikin shi da zagi tana fadin macuci mayaudari sai Allah ya isar min a gare ka har zaka dauki waya kabawa wata mace ta fada min wai baka da lafiya a wurin ta. Da karfi ya banbare hannun ta da ta rike mai wuyan rigar jikin shi ya fisge ya shige dakin shi a hasale. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Bai iya bata amsa ba sai kokatin wuceta da yake yi ya karasa cikin dakin rigar shi ta riko ta baya da mamaki ya juyo yana kallon ta. Shi da magana take mai wuya ina shi ina tsayawa fada irin haka da mace sau da yawa nafisa takan tunkare shi da irin wanan fita tana kokarin kama mai kaya ko ta sha mai kwala sai dai bai biye mata sai dai ya shige ya kyale ta tayi ta masifanta har ta gaji. Inda ita kuma a nata ban garen take ganin tafi karfin shi ne, dan bai da yadda zaiyi da ita dole ya zauna da ita take gani yau da ta cakuma rigar shi ta baya tana kokarin kaimai duka ya juyo da sauri yana fadin Nafisa ki na da hankali kuwa ? Cikin shi tayi tana banda hankali sai ka fada min wacce aka ganka da ita a asibiti dazun hannu yasa ya banbare hannun ta da karfi ya jefar da ita gefen kujera. Zafin kishi sosai ya rufe mata ido nan ta fara ja mai Allah ya isa ya ci amanan ta ya cuce ta sai taga bayan ko wacece ke son mata katsalandan a rayuwan ta. Yan uwanta suna tsaye cirko cirko suna kallon ikon Allah sai yare ne ke tashi suna magana rai a bace suna nuna goyon bayan yar uwan su. Harara ya watsa masu sai suka fara sulalewa daga falon kowa yana barin gurin don yanayin kallon da yayi masu din . Sama ya hau a hankali inda yake tafiya yana jin sautin kukan Nafisa yana isa inda yake. Tsaye yake yana balle bottom din rigar shi a hankali sai dai zuciyar shi cike yake da mamakin waya gan shi ya fada ma Nafisa cewa ya ganshi tare da wata mace a asibitin doctor Bisi.Doctor Bisi ne ya fada a ranshi sai kuma yace No it can't be doctor bisi is a man he can do such full to me. Beside, ma nine na hadasu da doctor bisi din anan don bata san kowa ba a Abuja sai zuwan da yayi da ita ne tasan kan garin. Bayan wucewan mijin nata ciki ne ta watsa ma yan matan uku da suga rage a falon harara tace a cikin yaren su na buzaye. Simi simi suka mike suka bar gurin itama mikewa tayi ta bishi ciki su karasa a can sai dai ta samay shi har ya shiga wanka ko. Zama tayi a bakin gadon cike da masifa tana jiran fitowan shi daga wanka su aza a inda suka tsaya. Zancen malaman ta ne ya fado mata a rai da kyat ta yaki zuciyar ta ta dan sasauta zafin da take ji nashi koda ya fito anan ya samay ta zaune cikin masifa bai kula ta ba ya fara gyaran jikin shi kamar yadda ya saba yi idan ya fito daga wanka. Kallo daya yayi mata fuska a daure ya kawar da kan shi gare ta ta mike ta tako gare shi tace samad ka daina ganin laifina. Ni kadai ce macen da ta dace kai a duniya da ina da iko ko macen kudi ba zan bari ta sauka a akan ka ba balle macen mutum. Ta hade wani miyaun fitina da yazo mata a makoshi tare da fadin nasha alwashin duk macen da tayi gigin shiga gonar ka sai naga bayan ta a duniyan nan. Kallonta yake da mamakin abinda ta fada yaga kuma gaskiyar maganan nata har cikin kwayan idon ta da gaskiya take maganan. Kuma ko wacece wanan macen sai na tono ta a garin nan na nuna mata ruwa ba sa, an kwando bane. Juyawa tayi ta fita daga dakin a fusace bayan taja wani uban tsuki tare da rufo kofan da karfi, binta yayi da kallo bayan ta fita ya girgiza kan shi ya tabe bakin shi gami da daga kafadan shi yace mahaukaciyar banza kawai. Karasa shirin shi yayi ya fara gyara gadon shi don yana bukatan ya huta don ya gaji yau sosai ga maganan Nafisa da ke ci mashi rai kishi kamar wace bata da hankali. Gadon ya hau ya kwanta bayan ya gama gyara yana sauke ajiyan zuciya a hankali may Nafisa take nufi da kalamin ta na sai taga bayan khadija. Yasan zata iya abinda ta fada mashi a yanzu karfa ya ja ma yarinyar mutane matsala a rayuwan ta don bai san abinda Nafisa zata aikata mata ba. Tunane yayi kada ya sare Nafisa ta samu daman da zats yi mai abinda taga dama a rayuwan shi don haka zuciyar shi ta bashi shawaran gwada Sa,an shi akan khadija ko zai yi nasara akai. Bai koma ta kanta ba yadda ya saba binta yana bata hakkuri har sai yaga ta hakkura yake samun saida a ranshi wanan karon sai yaji ba zai iya tunkaranta ya bata hakuri ba akan kuskuren da take tuhumar shi da aikawa ba. Kamar yadda Nafisa itama a dakin ta take zaune abin duniya duk ya damay ta ji take tankar tayi hauka don bacin rai wai yau samad din tane yakai wata mace asibiti ba ita ba. Wai wacece wanan da samad har ya iya tunkara da sunan so may take dashi may take tunkaho dashi a duniya wanda ake cewa tafi ta komai. Zubur ta mike ta fara zagaya dakin duk da dan cikin ta dake mata motsi a lokacin bai sa ta damu ta tuna da yadda take kaunar cikin nan ba. Kishi ne zalla a rayuwan ta kawai so take tasan wacece wanan yarinyar don tasan ta inda zata iya fito mata da shirin ta. Tana yi nata kallon lokaci don tasan dole yazo gare ta idan ta yi mai irin wanan boren nata sai dai a yan watanin nan tana ganin abubuwa suna son sauya mata sallo ga aikin ta. Shiko Abdul a dakin shi yana kwance barci yaki zuwa mai a lokacin tunane kala kala yayi shi a wurin Yusuf ya kirashi yana tambayan shi ko yaji yaya jikin nawa don ya kira wayana yana a kashe. Yace ban kirata ba don likita yace zatayi barci sosai a idan maganin ya fara mata aiki a jiki wata kila ta samu barci ne ta kashe wayan. Nan yake labarta mashi yadda suka kwashe da Nafisa da ya dawo gida hankalin Yusuf ya tashi yace sai nake zaton doctor ne ya fada mata tunda kace baku hadu da kowa ba a gurin. Yace idan shine ya fada mata kuwa yayi kuskure don cikin shi tayi don zan can za wani likita ke nan yanzu. Yusuf yace baka tunanen kada Nafisa ta gano a inda khadija take tayi mata wani abin yace haka ma ba zai faru ba zanyi tunane mafita akan hakan. Sukai sallama bayan sun gama tataunawa ga maganan ya kashe wayan yana gyara kwanciyar shi a hankali. Bai dade da gama wayan ba yaji an turo kofan an shigo dakin yasan ita ce don ita kadai ce mai shigo mashi daki. Ta karo gaban gadon ciki da mamakin ganin shi a kwance da tayi cikin rashin damuwa da ita har ta iso a gadon ta zauna tana fadin nasan ba barci kakeyi ba. Ya dago ido ya dan kalle ta yace banyi barci ba kuma hutu nake so a yanzu ta gyara zama tana kallon shi tace samad cikin sanyayar murya. Wai may na rage ka dashi a duniya may ye wanda ban maka har kake kokarin hadani da wata mace a duniya bayan kasan irin son da nake maka ba na wasa bane. Ta kamo hannun shi tana fadin gaba daya ka canza min a yan watannin nan ko dan ka gani da ciki ne ka dauko yimin hakan. Ka hana mu kwanciyar hankali gaba daya a gidan nan sai faman takura min kake yi ko yaushe. Sai ga hawayen da yaki zubu mata a daki yazubo mata a lokacin tace ko wacece sai na kashe ta a garin nan idan na gane ta. Cike da jin haushinta yace ashe ko ke ma za a kashe ki ke nan kinga matsalar ki ko meyasa ne har kullun ke baki tunane a rayuwan ki sai bakin kishi . Ni ina kokarin ganin ko yaushe inga lafiyan ki ke ko sai wani banzan kishi ke a gaban ki ban tsamaci haka daga gare ki ba na dauka kece mutum ta farko da zata shedi rayuwana a idon jamma,a. Yarinyace na kadai ta zan dawo gida in dubaki dole na dauke ta na kai asibiti doctor Bisi ya dubata ashe yariyar bata da lafiya shine ya taimaka mata. A rashin wayo na Nafisa sai cewa tayi ashe wanan likitan munafuki ne shine ta kirani yana fada min wai yaga ka kawo amaryan ka asibitin shi yanzu. Kawai may yake nufi don ya hada mu fada yayi min wanan maganan ko may yace da yake ke baki da tunane sai ki biyewa zancen shi ko ? Ace kulun mutum ba zai saka ma zuciyar shi salama ba koda yaushe sai bakin kishi ke baki hangen nesa akan ki fa duk yan uwana suke fushi dani. Hakan bai maki dadi ba sai kin tayar min da hankali kuuma har na tunzura na aikata abinda ban tashi yi ba. Tace da sauri don Allah samad kayi hakuri sherin shedan ne wallahi dana doctor Bisi sai da ta san yadda ta bashi hakkuri har ya hakura suka koma dai dai suka sulhunta kan su. Bai fita ba sai washegari bayan ya gama abinda yakeyi ya fice a gidan kiran Auta tayi ta fada mata ta koma kusfa ta fada ma malamin ta ya duba mata idan akwai matsala. Sai da ya duba wasu file ya dan huta tare da kiran layina maryam ce ta dauki wayan tana fada mashi ina bandaki amma naji sauki. Bai kai ga magana ba tace gani nan ma na fito tana mika min wayan tayi tana fadin yaya Abdulsamad ne a layin. Karba nayi tare da kara wayan a kunne nace hello cikin murya kasa kasa yace yaya jikin naki nace da sauki baki je class ba ke nan nace sai anjima zan shiga. Kin karya ko nace yanzu zan karya dai to idan kin karya kisha maganin ki zan shigo idan na rage aiki zuwa yamma in dubaki. Nagode na tsunci kaina da fadi Allah ya sauwaka ya fadi yana kashe wayan maryam tana gefe tana sauraren mu bayan ya kashe wayan na zauna saman katifa tare da kaiwa kwance. Tashi kisha tea din kada yayi sanyi gashinan na hada maki yamutsa fuska nayi nace miko min in sha bakinane bana jin dadin shi har yanzu. Daure dai kisha ko kadan ne sai kisha maganin ki gashi ta mike tana dauko min ledan maganin dake aje a gafen kayana. Tea din nasha tare da hade magani na koma na dan kwanta wayan daddy ne ya sake shigo min yana tambaya na ko lafiya jiya tanemi wayana yaji ta a kashe. Daddy iam sick yace may ke damun ki khadija murmushi nayi nace naji sauki ai period time dinane yake damu na amma kin je asibiti yace ? Naje daddy wanan mutumin ya kaini asibiti jiya yace good zan buga inyi mashi godiya don kwana biyu bai kirani ba yace nace bai kasan ne daddy ya kara da Allah ya sawaka ki kula da kanki ki abinda kika je yi khadija insha Allahu daddy na gode ka gaida mama. Madam ranan a gidan Nafisa ta wuni sun kule a dakinta suna jiran kiran Auta daga zaria suji abinda malam zai fada masu. Madam ta kawar da shirun da cewa wai shi wanan mijin naki wani irin mutum ne da baijin magani haka sai anyi kamar an samu kanshi sai abu ya zo daga baya ya can baki daya. Tace shike damu na madam dubi irin kudin da nake zubawa akan bawan Allah nan sai naga nasara daga baya sai komai ya lalace. Komai zan iya yi akan Samad din in dsi zan samu ya kawar da ido akan ko wace mace a dunuyan nan. Madam tace idan shiya kawar da idon shi a kan mata su matan kina tsamani zasu kawar da ido su ne akan shi dole suma dole da tasu shirin da suke don suga sun kamo shi. Don shegen kyau da daukan hankalina da wanan mijin naki ga abinda mata keso a tare dashi kudi da kyawo da hali. Hankalin Nafisa ne ya tashi sosai da maganan madam tace wallahi da ina da hali da boye shi zan dinga yi a gida. Dariya madam tayi tace idan kika boye shi kuce may ke da yan uwan ki Nafisa karki matanta shine hannu da kafar ku kaf zurian ku. Yanzun dai zan tafi Ondo ance akwai wani boka acan may aiki kamar yanka yuka wata kawatace ta gano hakan. Nikan ina can na dan samu karfin jikina shiryawa nayi zan leka cikin makaranta don kada a wuce ni da karatu da nazo yi. Daddy ya kira Abdul yana mashi godiyan kaini asibitin dayayi yace ba komai insha Allahu zai kula dani kamar yadda zai kula da kaunar shi. Bayan ya gama abinda yake ya kira Yusuf don su leka wurina kafin yaje gida Yusuf din yabar abinda yakeyi yazo suka tafi. Sun samu na dawo ke nan ya kirani a waya na fito na samay su a waje lokacin da na karaso wurin su na samu suna magana suna kallon laptop din dake a saman kafan Abdul din nasan wani abu suke duba a ciki. Karasowana suka bar abinda sukeyi din tare da maida hankalin su a gareni Yusuf ke fadin lalai jiki yayi sauki kauna na sai dai har kin dan fada kadan wallahi. Murmushi nayi na dan jingina jikina ga motar su nace naji sauki sosai yusuf yace barin in dan je can inga shagon yan makaranta indawo ina son duba wani abu a gurin. Nasan yayi haka ne don ya bamu wuri mu gana dashi wuce wanshi yace dan gyara zama yana fadin abin ya daina zuba ke nan ko ? Harara na aika mai tare da fadin ban sani ba sai ka fito ka duba ai tunda kana son sani ne sai yau naga dariyan shi yace kin dai ji abinda likita ya fada saukin abin ai. Banji ba kuma bana son naji tunda ba kai ke da lalurar ba au yanzu tunda kinji sauki kina da bakin magana ashe jiya fa nan kike ta murdemurde ina tausaya maki. Kawar da kainayi gefe guda ban bashi amsa ba na share shi yace na tambaye ki jiya ciwo ya hana ki ban amsa na. Nace may ka tambaye ni jiya din yace kwana nawa kike dauka kina off shiru nayi tare da bashi ba a raina ina fadin wai shi baisan ina matukar jin kunyanshi bane da yasan abin dake damu na. Gashi kuma ya tsare ni da tambaya irin haka da zai sani jin kunya da nauyin shi ai wanan kamar kamar yar iska ya dauke ni. Niko gidan mu in badon ciwon mara ba har zanyi in gama basu sani ba ji nayi yace may nene abin jin kuya kibani amsa na kawai don ya kama ne in sani. Nace don Allah yaya Abdul ka daina wanan zancen naji yace na daina tunda baki son zancen yanzu. Badai kina shan maganin ki ba akai akai nace ina sha na gode daddy ma ya bugo waya nake fada mai ka kaini asibiti yace zai kiraka yayi ma godiya. Yace ya kirani ai dazun sai danace mai kaina nayiwa aiki ba sai ya godd min ba nace ka fada ma daddy hakan ? Yes ya dace ne in fada mai don lokaci yayi da zai fahinci hakan daga inda Yusuf yake tsaye yake kallon mu yana jin farin ciki a ranshi. Hikimar yin haka da yayi ke nan a gusa daga wurin don mu samu daman sakewa da junan mu don idan yana wurin komai bazai wakana ba a tsakani karshe ma muna iya yin abinda muka saba fada ke nan. Ka samu zuwa duban su Affan kuwa na kawar da zancen da wanan tambayan murmushi yayi yace ban samu komawa ba sai dai na fara shirin komawa. Sai dai wanan karon ban san wani shiri kikai ma tafiyan nawa ba idan zan koma nace dama idan zaka nike shirya maka tafiyan. Yanzu shirin ya dawo kan ki don haka kece mai shirya komai ta wanan bangaren ya kamata ace na fara maki albashi a wanan bangaren don kin ci hakan a gare ni . So ki fara shirya min nan da two weeks zan tafi ina jira inji shirin da kai ma tafiyan nawa da abubuwan da zan yi a can. Yusuf ne ya iso gurin yana fadin mu tafi ko kada lokaci ya kure maka anan tunda munga lafiyan kaunar tawa sauki ya samu. Har kagama duba shagon nace mai yace ko dai in koma ne kada in takura maku kuna hiran ku na jin dadi zan katse ku kai haba yayana wani hira kuma a haka ? Ni dai daukar shi ku tafi kada yar buzaye tace ina shigewa mijin ta yanzu Abdul yace kina tsoron ta ke nan ? Nayi saurin fadin tsoro fa tsoron mace yar uwana kuma macen ma kuma buzuwa da kyau kauna ta haka nake son naji mace jaruma wallahi. Kai kaji ya juya wurin Abdul din yana fuskantar shi tare da fadin na fada ma kauna ta jaruma ce ba irin ka ba mai tsoron buzaye yan haure. Idan bata tsoro ai sai mu gani a kasa ba cika baki a nan ba nace ko agaban ta wallahi zan cika baki idan ya kama in cika akan may zanji tsoronta ne wai ? Mace ce fa yar uwata kowa sai ya gwada sa an shi yayi mai fishe shi duk abinda take takama dashi wallahi ni khadija ina dashi fari kyau da tsayi kagako ba zanji wani shakkata ba. Irin kallon da yake jifana dashi daga cikin motar yasa nayi shiru dole don kallone da ke dauke da fassara irin mai nuna feeling ga mutum din nan. Mun gama shan matan juna suka ja motar su suka tafi ni kuma na koma ciki tare da tunanen da yawa a raina na canjin yanayin da na hango a kwayar idon shi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Alhamdullahi mun sauka lafiya inda na samu maryam ta dawo ko saboda kwanakin da na kara ta rigani shigowa na samu har ta gyara min daki ko. Anan driver ya zube mu ya wuce abinshi ko ba a fada min ba nasan anty ta biyoni ne don taga yanayin zaman da nake a Abuja inda tazo da sunan kwana daya sai gashi ta share biyu kuma muna tare da ita ban je ko ina ba. Washe gari da safe na rakasu tasha suka shiga motar kaduna suka tafi bayan yan nasihohin da taimin na in kula da kaina in maida hankali ga abinda ya kawo ni. Muka rakata garage ta shiga motan kaduna wanda ta dauka ita kadai sai yaranta har kaduna mun dawo hotel a gajiye don haka na kwanta barci don nadan ji dama jikina. Tun da na kwanta ban tashi ba sai bayan sallah la,asar na tashi nayi wanka na tare da gabatar da sallolina ban dade ba maryam ta shigo tana fadin kin tashi ? Nace wallahi tace ga abinci nan ki cikin kula idan kin tashi ci ni na koshi sauran kayan bukin da ya rage na zauna ina ci nace abinci sai da dare. Ina zaune kamar daga sama zara ta shigo dakin nace mutumiyar ashe ke ma kin dawo ke nan tace dazu fa na gama tunanen ki. Zarah tayi dariya tace ai ni na riga ku dawowa tun wancan satin daya wuce na dawo school da sauri nace ai lokacin ba ai resuming ba. Ta wallahi gajiya nayi da zaman gidan shine nace hutumu ya kare aka shiryani na dawo school kaina jinjina nace Allah ya kyauta da halinki zarah tunda har kin san ki aikata haka. Dariya ta sake min tana fadin gidan ne babu dadi yanzu da na saba da ruyuwan independent din kaina . Sai da taci abinci a dakin ta koshi tana bani labarin tafiya sukayi da saurayin ta ta raka shi kano shiyasa ban ganta ba maryam baya ta bamu tana diban takardun da take hadawa har zarah tabar dakin. Sai lokacin ta juyo take ce min irin wa yan nan bai kamata mutum yana hurda dasu ba ai kada su bata ma mutum suna a banza. Nace yaya zanyi mun fito gari guda da ita bazan iya kyale ta ba ai kin ji dai ina bata shawara ko zata daina halin nan da tasawa kanta. Allah ya kyauta tace muka canza hiran kada muci namanta bamu sake fita ba har gari ya waye muka shiga school. Wanan karon Nafisa bata yar da ba dakanta ta shirya tafiya zuwa kaduna bayan ta dawo Niger don an bata labarin wani sabon malami a Kusfa. Abdulsamad bai hanata zuwa ba don tace kaduna zata leka don ta kwana biyu da zuwa shiri sosai yayi mata don zuwa kadunan a ganin shi ai gida zata. Ranan da ta isa kaduna bata samu zuwa ko ina ba sai washegari suka tafi ita da Auta yar take ga su Abdul din sai dai halin kwadai irin nata zata iyayin komai akan kudi. Haka yasa suka kule sosai da Nafisa har aminci ya shiga tsakanin su tana mata shige shige dama Auta irin yan duniyan matan nan ne tunda ta fito gidan mijin ta bata sake aure ba tana zaman rayuwa kawai a gida. Su biyu sukai tafiyan sai driver daya kaisu bayan sun gama yi ma malamin bayanin komai ne malamin yayi dariya yace kamar yadda take zargi gaskiyan maganan ke nan ya fada tarkon son wata yarinya a yanzu sai dai abin bai wani yi nisa sosai ba. Idan kuma bata bi alamarin a hankali ba zafin kishin da take nunawa ne zai sa komai ya iya faruwa da ita. Hakalin ta ya tashi sosai wanan ne mutum na biyu daya fada mata haka malamin yace alamarin yarinyar yana da karfi sosai. Don asiri baya kamata kai tsaye da zaran zamcen yakai ga iyayyen shi komai zai iya faruwa a tsakanin su a yadda bata zata ba. Don haka sai kin natsu aiki zamuyi maki wanda zaki kama mijin ki a hannun ki indan shi ya kamu yadda muke so komai zai iya zo maki da sauki. Amma koda zakici nasara akan hakan sai kin bi a sannu don yarinyar tafiki komai da kike tunanen kina dashi abune wanda sai an aiwatar dashi a sannu saboda mijin ki yana mata mugun son da bai san yana mata ba. Nashiga uku tace malam tafini komai fa kace yace kwarai da gaske don gata nan a gaban mu kina gani ta shige maki gaba ko a wurin shi. Kuka ta fara tana fadin don Allah malam kai min rai ka taimake ni ko nawane zan iya baka indai zaka min aikin da za a raba su hayatan hayatan ya ji bai kaunar ta ko kadan. Gaba daya yanzu na daina gane kan shi ada komai yana min kai tsaye yanzu sai yaja min rai yake min abu da na dauka ko cikin dake gare ni ne yasa yake min hakan. Yace magana dai guda ce ga yarinyar nan kina gani taurarin ta na da matukar haske sosai duk abinda ta sama gaba takan cin ma nasara a kan shi lokaci daya. Yana nuna masu zanen da yayi a kasa wanda su basu fahintar abinda ya zana sai dai bayanin da yake masu wanda ke matukar tayar wa Nafisa da hankali. Yace saukin abin daya ne yarinyar mijin ki baya gabanta don wani dalili nata amma shi yana kokarin cusa kanshi ko yaushe a wurin ta ne. Tace da karfi shi samad din malam yace kwarai kuwa muddin muka ce zamuyi aiki na gagawa komai zai iya faruwa na fada maki. Idan baki yarda ba zaki iya zuwa gurin wani kiji nasan duk wanda zai fada maki tsakani da Allah ba zai fada maki sabanin abinda na fada maki ba. Tana share hawayen dake zubo mata take fadin malam yanzu may ye abin yi don ko yanzu da dabara na samu nazo nan din. Wanan ba wani matsala bane aiki zamuyi mashi wanda hankalin shi zai fita a kan wata mace baki daya sai mu cus mashi kaunar ki ke kadai. Ta gyara zama tana fadin in hakan zai samu malam shi nafi bukatan ai min a kan shi a raba shi da ko wace yar iska ce kison tayi min kutse a gidana. Ya zayyana masu aikin da zai masu din ta yarda ta amince zata biya makam din abinda ya bukata a wurin ta suka biya shi ba tare da taji komai ba sukai mashi sallama. Tun a mota take zazaga balai tana zaginshi da iyayyen shi Auta tana kara zugata da fadin wanan wata irin yarinyar ce da za a ce ta fiki komai har kyau ke nan malam yake nufi ko may. Don banda kyau babu wani abu da Nafisa ke kadagi dashi don ba arabi ba boko haka take dip dinta bakauya kuma. Koda ta dawo kaduna bata biya gidan su Abdul din ba bata mayi tunanen shiga gurin su ba don daukan su take a makiyan ta dama balle yanzu da sunan su ya fito ga zancen. Kwanata uku a kaduna bayan Auta ta koma ta koma ta karbo abinda zasuyi amfani dashi idan ta koma sauran sai ya hada yace zai kira Auta ta karban mata don sai ya nemi abin hadi. Haka ta shirya sai da zata wuce ne ta dan shiga tsatsaye ta gaida su hajiyan shi da sauran mutanen gidan ta juya suka tafi. Almarina kuwa tunda na dawo sau daya muka hadu dashi koshi a tsatsaye don ina sauri zan tafi class karatu don muna da test din da zamuyi washe gari. Yazo min da provition mai yawa kamar ba gobe har sai danace kayan suyi min yawa yace naci da kawayena. Sun tafi abisa alkawrin zamuyi waya amma har wani lokaci bai kirani ba Yusuf ma haka bai kira ba nikan haka yafi min nono fari. Don dama neman mafita nake dashi kuma na samu yanzu sun sarara min ranan muna hira da maryam take tambaya na su. Nace banji komai daga gare su ba na nuna mata ni basu gabana yanzu abinda ya kawo ni nakeyi. Tace kai amna abin mamaki ne khadija ace sun share ki haka ba labarin komai daga wurin su ko yusuf ai ya kamata ace ya kira musan halin da suke ciki. Ke kuma baki neme su ba halarci baice haka ba fa khadija shiru nayi mata don mu kawar da zancen su da ta dauko min ina zaune kalau. Sai bayan da na kwanta sai kuma maganan ya damay ni a rai gaskiya maryam ta fada min ya kamata ka kula mai kula ka koba komai zai san ka damu dashi ai. Ranan da kyat na samu nayi barci da tunanen su a raina sai dai ni ba zan iya kiran shi ba sai dai dan dama dama Yusuf din. Washe gari haka na tashi da jin bakin rai a zuciyata sai dai kawai na danne abin a raina don na kudurta a raina ba zan taba kiranshi ba indai nice zakira inji ko lafiya suke. Tunda dama ba wani soyayya ko wani abu ke tsakanin mu haka ba mai karfi kawai dai ya gaji danine shima ya hutar da kan shi. Na share kawai kada maryam ta fahince ni na shirya muka nufi cikin school don daukan lectures na watsar da maganan su a raina kada in sa wa kaina damuwa a banza. Alamarin gidan shi kuwa yanzu tun dawowan Nafisa daga kaduna sallon zaman su ya sauya don yana dan samun kulan daya kamata daga gareta duk da ba wani dadin yake ji ga hakan ba don baya samun sakewa har yanzu a gidan shi yadda yake so. Shima Abdulsamad din ina a ranshi yakan so ya kirani yaji lafiyata sai dai yanzu duk lokacin shi na aiki ne dana Nafisa a haka har yayi tafiya tare suka ketara da nafisa zuwa wanan tafiyan. Satin su biyu suka dawo Nigeria koda suka dawo abuja bai samu kafan kiran na ba don Nafisa ta mamaye komai a lokacin. Yau suna tare da Yusuf a office din shi Yusuf ma wanda yayi tafiya yake tambayan shi labarina ya yamutsa fuska yana fadin wallahi banda labarin ta itama bata neme ni ba. Yusuf yace haba kai ma kasan bazata nemay ka ai, amma hakan bai mun dadi ba wallahi dakace baka kirata ba waya ya dauko daga Aljihun shi ya fara neman layina a lokacin. Ban shiga school ba ranan don na tashi da ciwon mara ina kwance a dakin mu ko karyawa ban yi ba har lokacin don haka ina cikin barci mai nauyi daya dauke ni naji kira a wayana. Da kyat na lalubo wayan dake gefe na ina jan tsakin wanda ya tayar dani a wanan lokacin dana dan samu sa,ida na samu barci ya dauke ni. Koda na dauko har kiran ya katse sunan Yusuf na gani akan wayan ban kai ga tunane ba wani kiran ya sake shigowa again. Tunane nake a raina may kuma zai fada min yanzu mutanen da suka shareni kusan wata daya ke nan yanzu kuma zai kirani yace min may ? Kamar in share shi kiran ya katse sai dai na danna recieve inji abinda zai fada min a lokacin na amsa da sallama cikin muryan barci da yanayin ciwo a tare dani. Naji yace subbahanallahi khadija baki da lafiya ne may ya samay ki naji muryan ki a haka ? Da sauri ya dago kai yana kallon Yusuf dake magana a waya yaji yace ayya sorry sannu ko kin je asibiti ne nace nasha magani ai ba sai naje asibiti ba. Idon shi har lokacin yana akan Yusuf din yace may ke damun ta ne naji Yusuf din na fada mai wai banda lafiya ne a kwance nake ma. Taje asibiti Yusuf yace tace ba sai taje asibiti ba wai karban wayan yayi daga hannun Yusuf din naji muryan shi yana fadin ki shirya yanzu gani nan zuwa nakai ki asibiti ya fada kai tsaye. Nace naji sauki ba sai kazo ba na kashe wayan wayan ya kalla tare da mikewa tsaye yana rufe file din dake gaban shi ya fara tafiya. Yisuf dake zaune ya mike juyowa yayi yana fadin ka zauna ka karasa aikin barin je na ganta in dawo Yusuf yace amma kana ganin zata saurare ka idan kaje kai kadai. Wani kallo yayiwa Yusuf din kamar zaiyi magana sai kuma ya juya ya fita Yusuf ta girgiza kai yana murmushi halin abikin nashi na bashi mamaki ace mutum haka da girman kai. Nikan ina kashe wayan naja tsuki nace mayaudari kawai naja filo na gyara kwanciya na barcin da ban koma ba kenan idona a rufe nake tunane nace yanzu na tabbatar da karkashin mace yake. Wata kila matan shi tasamu labari ne ta hana shi kula kowa yanzu ya dawo zai yaudare ni kuma ya bata min lokacina a banza. Dama ban sa zancen ko kadan a raina ba balle ya damay ni in ma junin shi iya yaudaran mata ne ya bata masu lokaci Allah ba zai bashi saa ba anan naja tsuki na gyara kwanciyana. Na samu barci ya fara dauka na naji wayan shi ya shigo min na duba na bar wayan nata ruri har ya katse kira uku yai min ban daga ba . Ranshi ne ya baci sosai yana shirin juyawa sai ga maryam kamar daga sama ta dawo don hankalin ta bai kwanta a yadda ta barni ta dawo ta dubani. Sai ganin shi tayi yana shirin juyawa da sauri ta karsa wurin shi tana gaidashi tare da fadin wallahi tana ciki bata da lafiya ne tun jiya nima yanzu na dawo in dubatane. Yace shi yakawo ni yazu asibiti nake son zuwa da ita a ranta tace boye min khadija ke nan rayi ashe suna waya dashi shine take boye min. Taji yace nakira wayan ta taki ta ga bayan yanzu Yusuf ya gama waya da ita ta fada mai bata da lafiya tace barin shiga in fito maka da ita nasan fushi take daku. Fushi ya tambaya da mamaki dariya tayi tace ina zuwa don Allah ta wuce ya bita da kallo har tabace yana mamakin kalamin ta wai fushi take da ku fushi akan may ? Tana shiga dakina ta nufa ta samay ni a kwance zama tayi a gefe na tana min sannu tare da fadin ga mutumin ki nan a bakin get yana jiran ki wai kuje asibiti yanzu. Wani kallo mai kama da harara na watsa mata nace rabu da mayaudari nine zai kai asibiti akan may zai zo min a yanzu da bana son ganin shi. Haba khadija kin san uzurin da ya tsayar dasu basu nemay ki ba tunda har yanzu ya iya zuwa da jin baki da lafiya ai ya kamata ki saurare shi. Haba maryam abinda kika sani ne nafi jin dadin zaman da nake yanzu babu takuran kowa a kaina akan may kuma kike son in kara fadawa tarkon mayaudari irin wanan mutumin da matar shi tafi karfin shi kuma. Kada kice haka khadija ko ba komai ya nuna kulawan shi a kan ki yanzu ina laifin wanda ya nuna maka haka a lokacin da kake cikin halin ciwo. Don Allah ki tashi ki daure badon ni ba sai don Allah ki tafi ki ganshi ko ba komai zakiji abinda ya tsayar dasu kwanaki mai tsawo haka baki ji su ba. Allah da kika hadani dashi ne zai sa in tafi badon wani abu ba can nasa, don ina son inyi nisa da shuumancin su yanzu tace daure kiwa Allah da kika ce zato kike yanzu kila ma ba matar shi bace ta hana ya kulaki. Kalaman ta yayi tasiri sosai a raina koba komai ina son jin abinda ya hana injisu kwana biyu don ban sin jawa kaina wulakanci ko kadan. Ita ta taimaka min na shirya atamfa na daura don yanayin da nake ciki tare muka fito zuwa ida yake zaune a motar shi. Yana yi yana kallon agogon hannunshi can ya ga fitowan mu tare da maryam ina tafiya da kyat yanayin ina jin jikin nawa sosai. Har muka karaso bai dauke idon shi a kan mu ba yi hakkuri mun barka kana jira wallahi barci na samu tanayi yanzu na tayar da ita. Bai yi magana ba sai kallona yayi yana fadin shiga mota mu tafi nace basai naje asibiti ba na sha magani naji sauki ina magana da kyat cikin daure fuska. Shiga muje nace maki da sauri maryam ta riko min hannu ta nufi gefen mai zaman banza tana bude min motar tare da fadin sai kun dawo Allah ya sauwaka. Sai da na zauna da kyau ya tayar da motan muka hau dogon titin da zai kaimu cikin gari sai da mukai nisa kaina da duke na dafe goshina da hannu na daya naji yace. May damun ki ne haka ban bashi amsa ba sai gyara zama da nayi ina cije baki don dan motsawan da nayi maran yana min ciwo yanzu. May damun ki ya sake maimaitawa shiru nayi can nadan sauke nufashi nace da kyar banda lafiya ne kawai tare da dan dafe mara na. Au ko abin ne yazo maki na manta yanzu kike cikin time din period din ki ko hararan shi nayi tare da kawar da kai ina cewa a raina kaji min mutum da bin didigi haka ? Kwana nawa yakeyi halan sake dago kai nayi na kalle shi kamar bashi yake maganan ba nayi saurin kawar da kaina daga kallon shi. Yace bakiji bane kwana nawa kike dauka kina period din nace ya fada tare da dan kallo na nace ban sani ba kada ka wuce hurumin da ba naka ba mana na fada ina kwantar da kaina. Murmushi yayi yace haka kike ce ko nace na fada din ni banga dalilin tambayana haka ba kai ba likita ba wani sai nayi shiru. Yace go ahead you say your words out, shiru nayi tare da kawar da kaina gareshi gaba daya ya sake fadin you free to say komai zaki iya fada don ance fushi kike damu. Da sauri na jiyo ina kallon shi nace fushi fa akan may zanyi fushi daku in ba ina son sama kaina nauyin da bai hauni ba ? Murmushi yayi da sai ka saurara zakaji shi yace kwana biyu bamu kasan ne daga ni har Yusuf na fita da madam dina ne mun tafi check up ciki ke bata matsala. Don Allah malam ni ban tambaye ka ba in zaku iya ma ku tare a can ba damuwa na bane wanan ciki kuma Allah ya bata lafiya ya sauketa lafiya amma mi ya hadani da tafiyan ku kuma. Kwana yasha muka shiga wani clinic inda yasa na fito muka shiga guri ya sama min na zauna ya nufi gurin tankan kati ba mu dade ba duk da mun samu mutane a gurin yace in taso mushiga gurin likita. Mun shi likitan yare ne don turanci suke dashi sun gaisa naji likita na cewa kayi sabin aure ne ashe yace mashi eh yace madam ta kwana biyu bata shigo ciki ya zaunu ko yace eh a gadarance yake ma mashi magana yace ina son ka duba min ita tana fama da mesturalpain ne. Yace ayya sorry madam yakamata ace ya rage maki ciwo yanzu da kiyi aure ya kamata ace kin rage jinshi haka indan zakiyi period don agana kawai matsalan hakan. Nauyi kunya ya rufe ni a wurin na kasa daga kaina shima wayan shi yake dakila baibi ta kan likitan ba sai da likitan ya fara tambayana ina mashi bayanin ya dago yana kallo na. Tashi nayi zuwa inda likitan yace in kwanta ya dan dadana cikin nawa na dan sake kara daidai kasan mara na daya tausa da dan karfi yace in tashi ya dawo ya zauna yana rubutu a wani farin takarda ya mika mai lokacin na dawo na zauna dakyat dafe da marana dake min tsananin ciwo sosai. Bayan ya mika mai yayi mai bayanin anemi wanan maganin in sha zasuyi min allura kuma zan samu sauki da yardan Allah ya mika mai hannu tare da fada mai inda zamu kai takardan a duba ni. Sai da muka gama komai muka fito yana min sannu muka dauki hanya wani shago ya tsaya yace min yana zuwa ya shiga ciki yadan jima sai gashi ya fito yaron shagon na binshi a baya dauke da wasu manyan ledoji biyu a hannun shi. Ya saka bayan motar ya shiga muka tafi bayan ya mikawa yaron kudi yana mashi godiya kaina na duke yace sannu likita yace zaki samu sauki dan anjima kadan amma zaki barci sosai ki ci wani abu don kince baki karya ba. Bana jin shi do murdan da mara na keyi ina dan cije baki ina jijiga kafa na da matse hannaye na duk yadda na so in daure na kasa sai da na yi ya gani a bakin down hostel din mu ya tsaya da motar shi. Zaki kara kawar ki ta taimaka maki ne ko in taimaka maki ki fita duk da ciwon da nake ji sai dana harare shi na bude motan na fita ko godiya ban mashi ba. Ina fita yace turo min kawar ki ta daukan maki magani kai na iya dagawa na shige ciki na samu maryam na girki a dakina din bata da kiuyar girki ita tana gani na tace har kun dawo kaina gyada mata na fada saman katifa nace yana kiranki a waje. A saka hijab da sauri ta fita daga dakin zuwa wurin shi bata jima ba ta dawo dauke da ledojin nan da ya sayo tace yana maki sannu wai sai kunyi waya yace kici wani abu kafin ki kwanta. Itace ta zauna ta bude ledan kayan ciyeciye ne a cikin dana sha tarkace dai gasu nan sai dayan ledan dake dauke da pad din mata always kamar mai bude shago dashi ban san ranan da zai kare ba. Abinci ta debo min na dan ci kadan na kwanta sai barci mai nauyi ya dauke ni a gurin ban kara sanin inda nake ba kuma. Yana fita ya daga wayan shi six miscall ya gani na Nafisa da sauri ya danna wayan ya kirata yana fadin sorry ina wani abune yasa banga kiran ki ba. Tace Samad ina kaje wacece akace mi an ganku tare a asibitin doctor Bisi yanzu waka kai asibiti wata macs ce aka gan ku tare tare ta fada cikin tashin hankali. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Washe gari muka shirya zuwa beji duba wani kakan mu dake zaune acan kanin mahaifin maman mu ni da ya Amina da yaran su. Bayan Nkwa bamu iya wani gaisuwan kirki ba sai habalu da sauran kananin kalma irin na gwarawa da muka rike a bakin mu. Tsohon yaji dadin ganin mu yana ta murna da zuwan mu gidan duba su anan muka wuni tare da su sai yamma muke son mu dawo mu biya maikunkele gidan iyayyen mama din. Tsohon bagwaren yana waje zaune da bakon shi muka fito zamu wuce muna masu sallama bakon nashi ne yayi yare sai naga tsoho yayi dariya tare da fadin yaki nan amarya na. Nazo na duka a gaban shi yace bako na ne ke son ganin ki sai na gaida dattijo ya mika min hannu alaman in bashi nawa hannun. Ban ki ba nayi kamar yadda yace min sai da ya kalli tafin hannu na da kyau yayi murmushi yace Allahu akabar akwai tarin alheri ga wanan hannun naki sosai zan ba kaka ku wani abu ya baki gobe ba mai wuya bane abin inda zaku tsaya na awa daya zan iya hada maki ko anan ma. Don tsari juyawa nayi na kalli ya Amina tace ai zamu iya tsayawa mu karba nan saman tabarman muka zauna ya bude jakkar shi ya ciro wani dan farin abu a wani kwanko yayi ta abinda zaiyi a abin sai ya miko min hannu na mika mashi nawa. Ya fara murza min abin a tsakiyar tafin hannu na har saida abin ya bace bat a hannu na ya dan dade rike da hannu na yana min tofi har kaina sai daya dafa yayi min yadda yayi a hannun ya sake ni dama tsamin jikin shi duk ya isheni sosai. Ya Amina ma tace aiwa yaranta da ita ba irin wanda yayi min yayi mata ba zamu tafi na bude jakka na fido dubu daya na bashi ya girgiza kai. Yace idan ina da dari biyu in bashi kawai yaci goro dashi na duba naga wani sabon dari biyo na dauko na bashi nayi mai godiya muka tafi. Muna cikin mota ya Amina tace na rasa may sa tun kina karama idan mun fita ke kawai mutane ke taimakawa wanan karo na biyu ke nan da haka ya faru dake. Nace su suka san abinda idon su ke gani a kaina wanda mu bamu gani hakan dariya tayi tace kila ya hango maki buzuwan ku ne . Kai ya Amina may yasa kuke fadar haka ne karfa maganan nan yakai kunnen su mommy da yan gidan su fa. Tace indan ya kama suji ai ji zasuyi khadija lokacin jin su ne baiyi ba kawai amma duk wanda yaji mamaki zai yi wallahi. Sai dare muka isa gida don mun bata lokaci a maikunkele wurin yan uwa da abokan aarziki ko da muka dawo wanka kawai nayi na samu wuri na kwanta abina. Da safe muka tashi da labarin haihuwan antyn mu Anty Hauwa dake aure a pilamigo easther wanka mukayi muka nufi gidan ta acan muka wuni sai four muka baro gidan ta. Koda muka dawo gida mama tana dora girkin dare sakwara zatai muna da miyan egushi tubewa nayi na fara taya mama aikin dakan sakwara don doyan ya dahu ko. Ya Amina data fito dakin ta tsaya tana kallon yadda nake dakan sakwaran ta kwashe da dariya tace ashe kin iya idan nace muyi sai kice bakya son ci. Sallaman da muka jiyo a kofan shigowa gidan mu ya hana ni bata amsa naci gaba da dakan sakwarana. Anty Amina ce ta dan leka raga mai sallaman sukai kicibis da Yusuf a tsaye yana gyara rigar shi da ya dan takure ga zaman mota. Kamar daga sama ta san shi a gidan su mommy shine dai bai santa ba tace cikin mamaki Yusuf kune tafe haka da yamman nan ? Yayi mamakin sanin shi da tayi haka shi bai santa ba sai dai ya gane muna da kama da ita sosai sai dai tsayin da nafita da kuma hasken fata don ni daddy na fadin gidan mu na debo sosai ina da zubin fulanin su na ka,aje ne. Ta juya tana fadin barin sanar da Khadija gata can yau sakwara take daka muna a gidan yayi dariya ta wuce ciki ina ganin ta shigo tana dariya ina rike da tabarya mama na duke tana saka wanda na daka a leda tace khadija ga ki da baki fa a kofan gida. Da sauri nace da ita su waye ya Amina tace wa kike tsamani zai zo maki yanzu banda su Yusuf da abokin shi nace kai haba dai ya Amina may zai kawo su nan in ba gulma ba. Tace to gulman ko ya kawo su gasu can a waje dai nace wai da gaske tace ina wasan haka dake ne dama tabarya na aje ina fadin yau na shiga uku. May suka zo yi yanzu kuma don Allah tace kyaji idan kin fita ai ni wallahi sai naci masu mutunci don may kuma zasu biyo ni har gida haka ? Harara mama ta watsa min tace idan zaki natsu ki natsu kije ki gan su falo ya Amina ta shiga ta fara gyara wurin inda zasu zauna ko kafin in fita na samay su da daddy suna gaisawa a waje na juyo na dawo ciki abina. Har ciki daddy ya shigo dasu ina labe a dakin mu ina kallon su sai da suka shiga sun dade ciki da daddy da ya Amina kafin ta fito ta kwala min kira ban fito ba ta samay ni a dakin tana dariya. Ya Amina may wanan mutumin ke nufi da nine wai for god sake may ya kawo su har gidan mu ne don bata min suna. Kallona tayi da mamaki tace zuwa gidan ku shine barnan suna khadija ai gara da suka zo zai fi hankali mama ya kwanta. Ni kan na shige su wallahi tace don Allah ki natsu kije ku gaisa sunce hanya ne ya biyo dasu nan suka ratso su gan mu. Ina shiga na samu har da abinci aka aje masuz sai hira Yusuf keyi da daddyn mu shiko sarkin miskilanci ido kawai ya zuba ma kofan shigowa falo. Da sallama nashiga tare da samun wuri gefe na zube gwaiwa na a kasa ina gaida su Yusuf ne ya amsa min shiko ido kawai ya zuba min kamar yadda na samay shi zaune. Daddy ya fita falon yana cewa dasu yana zuwa ya fita daga falon bayan fitan daddy ban daga a yadda nake na dago ina kallon su nace may ya kawo ku may kuka zo yi gidan mu ? Baiyi magana ba sai bude kula abincin yayi yana kallon sakwaran tare da fadin ke kika yi wanan abincin wai ? Yaya akayi suka san haka nake tambaya kaina a zuciyana Yusuf ma budan abincin yake yana faadin yar mama ashe kin iya girki ne haka ? Yayana may kuka zo yi nan yace gashi kinga munayi kawai dai mun yi marmarin cin girkin gidan ku ne mukazo muci dan harara na aika masu. Abdulsamad din ne yace kina ganin zaki iya kashe min waya don kada na kiraki da sauri nace ni ba kashe ma waya nayi ba. May yasa baki kuna wayan naki ya tambaya cikin kura min idanuwan shi dake ban tsoro yanzu nace wayar ce bata da lafiya. Baiyi magana ba ya fara cin abincin ba ko kunya hankali a kwace nace baku da kunya ne zaku ci a binci a gidan mu ku wai wasu irin mutane wai ? Ruwan abincin gidan ku zaki muna ya fada nace ni naci na gidan ku ne to yace wayasan iyaka wallahi ban taba shan ko ruwan gidan ku ba ni. Yusuf yace saboda may yar mama yana kai lomar sakwara a bakin shi kunya su nake ji ban iya shan ko ruwa a gidan don nauyi. Ashe ko kin cuci kan ki don ni dai a sani na gidan mu bako bai shiga ba a tare shi da abin sha ko na ci ba daddy ya kwala min kira daga cikin gida na mike na fita da sauri ya daga kai ya bini baya na da kallo. Saurin kawar da kanshi yayi yana cin abincin da yaji dasin dan danon shi har cikin ranshi ina fita naga baba da leda ya sawo drinks. Yace in kai wa baki a falo a tire na saka nakai na dire masu a gaban su nace gashi kun sa baba kashin kudi bai shirya ba. Murmushi magana na yadan yi sun ci abincin sosai suka wanke hannu na fita da kayan bayan sun gama ne suka ce inyi masu iso su gaida mama zasu tafi. Fita nayi na kira ya Amina ina fada masu abinda suka ce man ita ta fada ma mama zasu shigo su gaida da ta nan mama ta gyagyara suka a kofan daki aka shimfida masu tabarma suka zauna. Bayan fitar sune na samay su a waje har sun shiga mota ina isowa Yusuf ya miko min waya kallon wayan nayi ina tambayan shi ta may yace ogana yace a baki tunda naki ta lalace kiyi maneji da wanan kafin ki dawo Abuja a sai maki wani. Amma don Allah kada ki kara kashe muna waya mu kira bamu samay ki ba ran mu baya dadi rashin jin ki da bama yi a koda yaushe. Kai na girgiza tare da fadin kubar wayan ku ni wayata lafiya take kashewa nayi kawai don, , , Ban karasa ba naji yace don kada kiji muryan mu ko may khadija nace kawai abubuwa ne sukai min yawa a nan bata waya nakeyi ba. Yaushe zaki dawo school don hutu ya kara nake gani nace sai anyi sunar yayan mu data haihu zan dawo uffer week may zaki zauna yi har uffer week Abdulsamad ya tambaya. Ba a gida nake ba tare da iyayyena na bashi amsa da hakan yace ranan tuesday zan turo a dauke ki yana fadin haka ya rufo kofan motar Yusuf yayi min sallama tare da kara mika min wayan suka tafi. Azato sun tafi ne sai ga yara suna shigo da drinks da wasu abubuwa a kwali wai i ji su ina daki ina kallon wayan daya ba babban wayace mai tsada fara kwal da ita. Ya Amina ne ta shigo dakin tana kallo na tare da fadin wai shi baya gajiya da wanan daiwaniyar da yake haka ne kuma kin ce ba soyayya kuke dashi ba. Wayan da ya bani ne na miko mata ta karba tana fadin ta maye wanan kuma nace shiya bani do kawai nace tawa ta samu matsala ne yasa basu samu na . Abin nayi ne ashe yanzu a ka fara wasan da ba ansan maci tuwo ba sai miya ta kare nace ba wani wasan da aka fara indai nice da na koma zan kakabe shi in huta da zancen su gaba daya. Tace ai wanan da alama kin samu kaska baya kakabuwa wasan dadi don ko ya fiki dabara yanzu gashi ya gama daure ki a gurin daddy da mama ko. No way to exscape daga tarkon shi a kwai game da na sani kan nan gaba din ba karamin aiki kika banbaro muna ba yarinya. Kai ke ya Amina ke kekara ma abin wuta wallahi ni may zanyi da mijin da wata ke juyawa a gidan shi kina so in shiga nima in koma yar bi ce kamar fati ? Ke zaki tsayane ki zauna kamar ita a wirin shi ta kai zaune tana fadin da farko ina tsoron abinda ke shirin faruwa tsakanin ku da shi. Amma yanzu zuwa na gida da daddy ya wayar min dakai sai hankali na ya kwanta da zance nake ganin kece haske da zai yaye duhun da Abdulsamad din ya shiga. Ya Amina ki bar wanan magana kimun fatan alheri a rayuwana ba irin wanan fatan ba na shiga wurin da fitina ta nuna kan ta a fili. Khadija kin taba ji ko ganin Abdulsamad ya taba bata lokacin shi ga wata mace irin haka amma sai gashi a kanki abubuwa na ta shirin faruwa a tsakanin ku. Na tabbatar da su hajiya mama zasuyi fari ciki da jin wanan labarin don wata kila adduan su ne ya fada kan ki. Shiru nayi ina sauraren ta tace abu daya zuwa biyu ne na farko gaba dayan mu sai mu dage da addua gaba dayan mu na biyu kuma kiyi kokari ki cusa mashi so da kaunar ki ta yadda buzuwa ba zata iya mashi gibi ba. Har muka gama magana ta fita ban iya cewa komai ba ta barni ina cike da tunane a raina na yadda abubuwa ke zo min a haka. Sai dare sosai suka shiga Abuja inda Yusuf ya aje shi gida ya nufi nashi gidan da motar shi da ya bari gidan don tafiya da ba shiri sukayi. Ko da yashigo gidan shiru yaji kamar yau mutanen gidan nashi basu ciki bai tsaya falon ba ya haura sama inda dakunan kwanan su yake. Ga kaya nan ko ina a warwatse ko ina agidan anyi amfani dasu an kasa kawar dasu don tsabagen kiuya da lalaci har ya kai kofan dakin ya tura a hankali ya shiga. Baiyi mamakin ganin ta a yanayin da ya samay ta ba don duk kwanankin nan a yamutse take a gidan ba wani gyara ko kwaliya da take samun yi . Tana zaune saman gado gashin kanta a wawatse ba gyara ta dago ido ta kalle shi tare da kallon agogon bangon dake dakin tace Samad ina kafito a wanan lokacin. Aikena kikayi da kike tambayana ya bata amsa tare da wuce wa wurin wardrobe din shi yana rage kayan jikin shi. Samad neman mata kafara ko mai yace idan na nemay su ba namiji nake ba wallahi baka isa ba ta fadi da karfi ya juyo gare ta yace ban isa ba fa ki ka ce Nafisa. Tace baka isa ba wallahi may na rage ka dashi a wanda ban baka da har zaka lakanci neman mata a yanzu daga sama. Ya ciro wani dogon jallabiya baka yana fadin waya san iyaka Nafisa baki san komai ba banda son kan ki da kashin kudi abaki kuma baki godiya. Kudi dole ne ka bani don kasan sune buri na kuma akwaisu bathroom ya shiga ya barta ta ta fadin bakaken maganganu gare shi har ya fito bata fasa magana ba. Gadon ya duba yace duba don Allah wai a inda mutum zai kwanta ke nan ya fara kakabe shimfidar da wani dan karamin towel daya fito dashi daga ban dakin. Yace mace sai tarin kazanta na fada maki bani son wanan kazantar taki amma ke abin sai gaba yake yi gare ki. Ai kasan a haka nake kuma ka aure ni na dauka idan kin shigo cikin daula zaki canza ne ashe ni ban san abin a jinin ki yake ba. Kazantar ne a jina na yake Samad yace in ba ajiin ki yake ba za a ce duk yawan ku baku iya gyaran wuri tace samad wa kake so in sa aiki a cikin gidan nan. Kafa san daga kanne na sai yayyena anan sai kuma kawu naina da gwago na yace may yasa kika boye min hakan da farko kin fada min yan aiki ne kika samo min kuma biyan su nake duk wata. Sai yanzu zaki ce min wai yan uwan ki ne na jini baki iya saka su aiki a gidan nan kin zo gidan nan kin samu masu aiki kika ce baki yarda dasu ba. Na baki go ahead da zaki kawo wanda kika yarda su suyi mana aiki ashe ke yaudarana kikayi ki kwaso yan uwanki kika cika min gida dasu. Samad ta fada da karfi kawo yan uwana danayi a gidan shi ne kake kira da yaudara yace yaudara ne mana mutum da gidan shi ba dama ya shigo ya huta a ciki yaji dadin ranshi. Samad yau ni kake fada ma haka don ka gani da ciki kake kokarin ka wulakantani yanzu ko may babu zancen wullakanci sai maganar gaskiya. Haukace mai tayi ranan tana fadin bai isa ya rabata da yan uwanta ba don tare ya gansu ya kuma yarda ya aureta a hakan. Haka ya kwana da tarin bakin ciki babu kunya washe gari kuma sai gata ta neman sulhu dashi don dai kawai ya biya mata bukatan ta don bata iya hakkuri dashi duk yadda ranta ya baci dashi ga wasu kudi da take son karba a wurin shi masu yawa don ai mata aiki a kan shi. Bata samu ko daya ba ranan don asubanci yayi ya fita wirin aiki da wuri koda yaje gurin aikin bai iya aiwatar da komai ba. Yusuf ya shigo ya samay shi a haka yake tambayan shi wai may ke faruwa dashi ne bai tsaya boye mashi ba ya sanar dashi halin da yake ciki da nafisa a gidan shi. Da yan uwanta da suka cika maigida da sunan yan aiki ta kwaso yana biyan su a wata ashe ba haka abin yake ba. Kai inji Yusuf lamarin Nafisa akwai daure kai wallahi Abdul yace nima bashi ba kazantar nan ke damuna Yusuf. Ka san dai halina da kyakyami wallahi komai na gidan nan yanzu kazantar shi nake ji in ba ruwan gora ba ban iya cin komai a gida na . Yusuf yaya zanyi da wanan masifa dana dauko ma kaina nasan ina son nafisa sosai why da ba zata gyara halin ta ba may ye ban ma Nafisa a rayuwan ta. Kamar karta samu cikin nan yanzu abin ya karkare jagule mata mace ba wanka ba saka sutura a jiki idan anyi magana sai tace wai lalurar cikine haka take cikin ta. Au dama ta taba ciki ke nan naga auren budurwa mukai mata wani kallo ya jefe shi dashi yace Nenan yar waye idan bata taba haihuwa ba nima daga bayan nan na fahinci yar tace ashe. Yanzun haka zan kare ga yawon restaurant ina cin abinci a garin nan kamar wani mara galihu dani. Kai innalillahi abin nakune akwai daure kai wallahi saukin abin khadija zata dawo next week zaka dan samu sauki a awurin ta. Saukin may zan samu a gurin ta ya tambayi Yusuf a yanayin rashin fahintar maganan shi Yusuf yace koba komai tunda ta iya girki naga ai zata dan dinga maka idan tana da time. No ban san in jefa rayuwan yarinyar ga halaka ko kadan nafi son ayi komai a kaidance yace kana nufin auren ta zakayi. Shiru yayi ya dafe kanshi bai sake magana ba ya fahinci bai son maganan don haka ya kyale shi tare da canza topic. Yusuf na fita ya jawo wayan shi ya kira layina muna gida ya Hauwa mai jego ya kira wayana ina wanke kayan miya a kitchen aka kawo min wayan. Sai da ya kusa katsewa na dauka tare da sallama yace ina kika shiga kika bar waya na ruri haka nace ina kitchen ina girki wa ya hauwa da ta haihu. Kuna gidan ta ke nan ya tambaya nace eh may kike girka mata nace miyar shuwaka zanyi mata da tuwon shikafa. Ke wa ya koya maki girki haka ne wai nace girkin ma har sai an koya ma mutum yin shi idai kana mace ai zaka iya girki ko wani iri dole. Aranshi yace ga macen da ta san kanta ba sai kuma yace ke wace irin yarinyace da baki iya kiran mutane kiji ko sun sauka lafiya ? Na aiku tafiyan dare ne ko ni na saka ku yin tafiyan da kuyi din yace OK haka zaki ce ma nace haka din ne ma ai. Sai naji ya kashe wayan dariya nayi nace zaka kaji ai ka daina in yar da magoro in huta da kuda har dare muna gidan sai tara muka dawo gida a gajiye . Ban kara bi ta kanshi ba har akai bukin suna aka watse lafiya drinks din da suka kawo muna yayi muna rana do shi mukai amfani dashi wurin taron sunan. Mun fara shiri don tare da yaAmina zamuyi tafiyan kamar yadda na fada mata yace zai turo mota hakan ne ya faru sai ga mota zuwa sha biyun rana ya tsaya a kofan gidan mu. Nan muka fito mukayi haraman tafiya nasha nashi ha a wurin mama da daddy kafin mu wuce muka dauki hanyar Abuja tare da ita don zata kwana a wurin mu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU INA BUKATAN ADDUAN KU YAN UWA ALLAH YASA MU DACE 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Kamar yadda yace nice mai tsara mashi tafiyan haka yasani a gaba dole sai dana tsara mashi zuwa gidan da zai yi da abinda zai kai gida. Da farko na dauka zolayane sai da naga abin nasa da gaske ne na tsaya na tsara da taimakon maryam nayi komai. Wanan karon bai sai kayan tsaraba ba kudi muka tsara zai bayar idan yaje sai abincin da zai sai ma iyayyen shi don rage ma mahaifin shi nauyi. Da yamma lis suka isa kaduna don haka ya wuce gidan shi bai shigo wurin su hajiya ba sai da safe bayan ya karya ya shiga gaida su. Sai da yagama gaida abokan zaman hajiya suka wuce nata part din dake daga can ciki yana fuskantar part din mommy. Sai dai tsakanin su akwai dan filin tsakar gida da shuke shuken filawoyi a gurin da wani babban icen ambrale dake basu innuwa a gidan. A kofa su kai sallama ta amsa masu daga ciki suka shigo ko ina na falon tsab yake sai kamshin turen wuta dake tashi a falon. Tana zaune tare da kannen shi Binta da zainab su uku a falon gaida shi kannen nasa keyi ya amsa masu a tsatsaye tare da zama saman center capet din falon shi da Yusuf. Gaida hajiyan sula farayi a cikin ladabi inda hajiyan ke nuna farin ciki da ganin su tare da fara,a a fuskanta. Tana man kamar yadda take a cikin gyaran ta ko yaushe atamphar super ne ja a jikin ta babu wani alamar tsufa ko girma a tare da ita hutu da jin dadin da mijin su ke basu ya kama ta. Cike da kula take amsa masu tare da tambayan da Nafisa suka zo ne Yusuf yace su kadai suka zo don Nafisa cikin ta ya fara girma yanzu. Tace cikin mamaki ciki ke ga Nafisan bamu sani ba mu tana kallon su cike da kulawa Yusuf yace wallahi hajiya ai cikin ma yanzu zai kai wata shida ko bakwai. Ikon Allah to Allah ya raba lafiya ashe da baka fada yanzu ba da sai dai muji haihuwa kawai. Yace ba akai ga haka ba ai hajiya zakuji ne don dai ba a tare ne Affan ne ya shigo falon bai mai da hankali shi wurin su ba sai fada ma hajiyan dayayi a jiki yana fadin wai yaji ciwo a waje. Tace baka ga Abban ku bane Affan daba gaida su ba yaron ya dan kara lafewa a jikin kakan nashi Yusuf yace malam Affan kuna lafiya ina daddy yake ? Hajiya ke fadin maza ka gaida Abban ka da baban ku daga jikin kakan yace ina wuni bazakaje kusa dasu ka gaida su ba in ji Binta dake dagawa daga inda take zaune zainab ko sai charting take a wayan ta. A dadare yaron ya isa gurin su yana kara gaida su Yusuf ya jawo yaron a jikinshi yana tambayan shi dan uwan shi yace yana gurin mommy su. Hajiya tace ai shi wanan dan lake ne tunda uwar tabar gidan ga ta koma gidan su kullun yana can like da ita. Da sauri Yusuf din yace hajiya Fati ta koma gida ne kuma tace to mu rike ta ne nan tunda abin yaki ci yaki karewa haka. Ai gara dai ta koma gida ko hankalinta zai kwanta a can anan taki ta sake sai rama da takeyi kullun Abdul ya mika hannu yana tambayan yaron labarin makaranta. Yayin da Yusuf da hajiya ke magana akan komawan fati din gidan su yace zamu lekata kagin mu koma abin ne sai an hada da hakkuri. Don Fati taki tayi hakkuri da yanayin Nafisa amma ai ita ta zabi ta zauna nan kaduna cewan ta hankalin ta yafi kwanciya da nan din. Wayan zainab dake gefe ne yayi kara ta dauka tana fadin Khadija Adamu wallahi nayi fushi dake ai tana mikewa ta shige dakin su. May wanan yarinyar ta bugo ta fada ma zainab yanzu ko dai komai da sanin su take aiwatar wa yace a zuciyar shi sai ga khadijan ta fito tana hajiya ga khadija na son gaida ke. Ta amshi wayan da faraa a fuskan ta muka fara gaiswa da ita ba wani dogon magana bane gaida ita kawai nayi tana sa min albarka. Ta mikama zainab wayan ta ta sake shigewa ciki shiru falon yayi sai hajiyan ne ke fadin yar albarka yariyar na da hankali sosai wallahi. Ta juya tana fadin yarinyar nan da nasa ku rage ma hanya wani lokaci da zaku koma abujane Yusuf yace oh khadija tana da kirki sosao wallahi. Ai nikan dan leka ta wani lokaci mu gaisa idan na samu lokaci tace ka kyauta haka ake son mutum ya zaba ma kanshi abu na gari. Yace hajiya babu komai a tsakanin na da ita wani dai ma yake raayin ta yanzu haka don yabawa da hankalin ta da yayi har lokacin hira yake da dan shi dabai sake jiki dashi ba. Ya dago kai yana fadin hajiya ko Abba ya fito yanzu mu gaisa dashi kafin ya fita tayi murmushi tace ai yanzu Alhaji ya rage fita kasuwa don yanayin girma da kuma jikin shi yana gida koda yaushe. Binta ta kwala wa kira tazo ta kira mata mommy a dakin ta don tai masu iso gurin Alhajin mommy ta shigo tare da Binta dataje kiran ta hajiya ke fadin dan ki zaki wa iso gurin Alhaji wai. Mommy tana murmushi tace kai hajiya sai kace wani bako a gidan Alhajin yana nan falo ya fito yanzu ma na baro wirin sa ta juya ta fita zuwa fada ma Alhajin zuwan su. Sai lokacin ya dubi hajiya yace wanan karon ban riko komai ba yana sa hannu a cikin aljihun shi yace ga dai kudi a kasa fa aba su mommy dubu daridari sai yaran nan a raba masu dari biyu ke kuma ki dauki sauran ya zube kudin a gefen mahaifiyar sai kuma abinci da anjima za a shigo dashi. Ta kasa boye farin cikin ta nan ta shiga saka mai albarka mommy ne ta dawo dakin tana fada masu su shiga yana jiran su har mommy ta juya hajiya tace . Mommu yara da alama adduan mu ya fara kana dan ki yanzu ga kudi ya kawo a raba ga kuma kayan abinci a tafe. Komawa mommy tayi dakin tana fadin kai madallah Allah mun gode maka da dan mu ya fara dawowa gare mu. Haka ake so wallahi amma da babangida kamar wanda baida kowa a duniya da gatan ka zaka bari shedan yana rudin ka. Ga dan uwaka nan Suraj sai shine ke bamu talafi bawai don bamu dashi ba don nemawa kansa albarkan mahaifa kawai don Allah aci gaba da kula da hakkin mahaifa dana. A da ya tsani mommy sosai don yana ganin nuna mashi kulawan da take kamar duk a munafunci ne sai yanzu yake fahintar halinta ne kawai a hakan ga yaran gida musanman na hajiyan su da takan nuna nata ne. Ita mommy Allah bai bata haihuwa da yawa a gidan ba daga Sadiq danta na fari sai salma kuma ba wasu manya bane sosai yanzu ma suke a secondary. Yace mommy in sha Allahu za a gyara kwanan nan ma zaki tafi abuja wurin mu don Nafisa ta kusa haihuwa ke nake son kije tare da iya na zaria ku zauna a gidan. Ba mommy ba har hajiya sai da tayi mamakin jin wai yau Abdul ne da kansa ke fadin wani nasa yaje gidan shi ya zauna don matar shi da zata haihu. Kirikiri a baya tace bai yarda kowa nasa yaje gidan shi ba don suna zuwa suna tayar kashi da hankali a gidan shi haka Nafisa ta fada mai a baya. Hajiyan su ce tace yar ikon naka tasan da haka kuwa yace haba hajiya sai ta san da hakan mahaifana da yan uwana zasu zo gidana. Idan na gama shiri zan aiko a dauke su yanzu idan na shiga gurin Abba zan sanar dashi bukatan hakan don ba zan so ta haihu babu wani dan uwana a kusa ba. Allah ya kaimu mommy tace da murnan ta fita daga dakin cikin farin cikin canjin da suka gani gareshi. Wayan shine yayi kara ya mike yana amsawa ya bar Yusuf a gurin hajiyan Yusuf yace hajiya muna bukatar adduan ki kamar kulun yanzu haka akwai yarinyar da Abdul ya fara so ina ganin zata iya zama da Nafisa. Duk wanan shiri nane don ba mace matsoraciya bane zata iya gwabzawa da halin nafisa ba don haka a tayamu da addua akan zancen in lokaci yayi nasan zakifi kowa farin ciki da zancen. Hajiya tace ashe ba batun mayar da Fati kuke yi ba ku wani tashin hankalin kuke shiri daukowa yace hajiya wanan shi kadai ne nake ganin mafita ga alamarin. Tace to shike nan addua dama kulun munayi Allah yasa hakan shine saukin abin amma dai wanan yarinyar ta cuta muna da yawa a rayuwan mu. Babu komai hajiya komai ya kusa zuwa karshe insha Allahu Allah yasa tace ya mike tana mashi godiya ya fita ya samu Abdul din a waje suka wuce wurin alhajin shi. Da sallama suka shiga dakin na Abba yana zaune saman kujera yana duba wayan shi ya dago kai yana amsa sallama tare da kallon su ta cikin farin glass din shi idon na medical. Kasa suka zube suna mika gaisuwa ga Abban girma da kuma ciwo ya ramar da Abban don mutum ne mai jiki a da yanzu ko girma da ciwo yasa duk ya zube. Sun gaisa sosai sabanin da da in yazo gaida Abban yake amsa mai a dadafe ba wani saki a fuskan shi. Ya aje wayan tare da mayar da hankalin shi gare su magana yake irin na dattako yana tambayan su yaya aiki da iyali suka amsa da lafiya kalau Abba Alhamdullahi. Kallon da yake masu ne yasa suka san da magana a bakin Abba din jikin Abdul yayi sanyi yana tunane a ran shi may kuma yayiwa Abba din yake mashi kallon tuhuma a yanzu. Yasan dai ba wuce maganar yar aminin shi ba da yake ganin yayi mata ba daidai ba shi dai Fati taja mashi kiyayya a gun mahaifan shi yanzu komai yake masu baya fari a gare su. Gyara zama yayi yana kallon Abba din don jin abinda zai fada masu Abba yace Yusuf zan iya cewa yanzu Alhamdullahi a yadda naga abokin ka yana waiwayan mu akai akai. Ko ba a fada ba alama ya nuna cewa yanzu ya fara samun kwanciyar hankali a tare dashi shidai Abdulsamad ya zuba ido yaji karasan magana shi. Abba yace ya na dade ina jiran wanan ranan tun ban mutu ba ranan da zaka gano gaskiya ka dawo a cikin hankalin ka irin haka. Wanda nasan ba yin kan ka bane don ba haka muka tarbiyarta da kai ba da farko don haka nake son ka kara natsu ka tsayar da ibadan ka duk wani abinda zakayi kada ka manta da yawan addua a tare da kai don shine jagoran rayuwa ko ba haka ba ya tambaye su. Lokaci guda suke kada ma Abban kai tare da fafin hakane Abba , murmushi Abban yayi masu yace to yanzu saura maganan iyalin ka zan so inga ka hada kan iyalin ka a wuri daya. Kamar yadda ka taso ka gani a gidan nan kasan hakan shine cikar kamalan ko wani magidanci aga yana ba ko wace mace hakkin ta daidai gwargwado. Suka ce hakane Abba, Abban ya dan tsura masu ido yayin da kanun su yake a kasa suna sauraren shi Abban yace kai kuma Yusuf na dawo gare ka mai kake jira har yanzu baka maye gurin matar ka da ta rasu ba shikenan kana nufin ba zaka sake aure ba a rayuwan ka ko may. Yusuf din ya dago da sauri yana fafin ba haka bane Abba zan sake insha Allahu da zaran an gama na Abdulsamad dake tafe. Au Abdul din aure zai karane kuma Abba ya tambaya sai Yusuf yayi kasa da kai yana fadin insha Allahu Abba basu gama daidaitawa bane da yarinyar shi yasa bamu gabatar maku ba tukun. To madalla ka nuna ka gado gida ke nan to yaya maganan Fati kuma fa may ake ciki game da alamarin ta ? Abba insha Allah zata koma daki ta ba da dadewan nan ba akwai abinda muke tsarawa a kai ne yanzu to Allah ya bada sa a sukace amin ya kara da fadin a kula da hakkin akai dai. Insha Allahu suka fadi suna mikewa ta ciro kudin da ya ware na Abba ya nufe shi yana aje mai a gefen kujeran da yake zaune a sama. Suna fita dakin Abba suka sallami mutanen gidan suka fice a gidan Abdul yace Yusuf yaya zakai min haka kace wa Abba wai aure zan kara kwanan nan ? Idan ba haka na fada mai ba kana ganin iya abinda zai fada muna ke nan a yadda yake kallon mu din nan shine kawai mafita ai kai kasan ba auren zaka kara yanzu. Bai yi magana ba ya bi bayan shi yana murmushi don yasan ya kulu dashi sosai da yamma motar kaya ya tsaya a kofan gidan Yusuf yasa akai ta shiga da kayan cikin gida. Kowa na gidan sai farin ciki duk da zaman kishi dole na ciki na ciki a ransu ganin sauyin da yayi hakan bai hana a kebe gefe ai gulma ba tsakanin ummi da anty Amarya. Nafisa da madam murnan tafiyan shi kaduna a satin sukayi don dama kafan zuwa ondo take nema don Abdulsamad ya hanata tafiya yanzu ko ina. Tafiya sukayi sosai tun suna na dadin rai har ta fara galabaita ga tafiya don dan karan nisan da garin ke da tsakanin shi da Abuja. Bata dauka nisan shi yakai haka ba sai da suka fara hanya duk wanan bakar wahalan bai sa ta janye kudirinta na zuwa wurin wanan bokan dataji ana yabon aikin sa ba. Ko da suka isa ondo da safe wani motar suka kara bi zuwa kauyen da bokan bayaeraben yake zaune sun isa a wahalce don har amai da zazzabi sai da tayi a hanya. Sun isa dajin mai kama da gari da baifi yan gidaje a kirga ba sai da suka huta kafin su samu ganin bokan don ranan suke son su koma Akure su shiga motan dare su koma abuja. Bayan ta gama fadin abinda take son yai mata nan boka ya fara surukule shi ya dago yana kallon ta na dan lokaci. Sai duk suka tsargu da irin kallon da yake masu wanda ke nuna akwai magana kai ya girgiza sanan yace aikin ta akwai dan wahala a cikin sa. Don yanzu haka mijin ta yana tare da wata yarinya sai dai bai hango soyayya tsakanin su ba amma akwai aure har da haihuwa a ciki. Kirjin ta ta doka tana fadin ta shiga uku ita samad zaiwa kishiya wacece zai aura har su haihu ? Sam ta mace da Fati ma mallakin mijin ta ne har da diya shi boka Allah bai bashi ikon tsafin shi ya hasko ni ba nan tasa ai mata aikin da za a raba tsakanin shi da ko wacece . Akuma fitar da ranshi ga ko wace mace a rayuwan shi sai ita kadai ya kara yin saddabarun shi na bokayen da suka gwane da tsafi yace ya ga wata mace sai dai baiga gaban ta sai bayan ta kamar tana son shiga rayuwar mijin ta amma dai bari ya mata aiki akan wace ta baiyana in yaso daga baya aikin da zaiyi zai gusar da waccan matar da yaga bayanta din. Tace tana son koda kashewa ne a kashe mata wace aka gani ko a haukatata gaba daya kowa ya huta. Yace an gama sai dai aikin ta na da tsada sosai tace kada yaji komai indai aikin zaiyi kyau nan ya shiga hada mata irin nashi surukulle da bayanun yadda zatai amfani dashi ba tare da kuskure ba. Yace ba mijin ta ba wata mace da zai duba a duniya muddin tayi abinda ya fada mata daidai suka kama hanya komawa gida bayan ta cika shi da kudi. Sam bata san Abdul kwana biyu zaiyi a kaduna ba lokacin da Abdul ya iso gida ya neme ta sai cewa sukayi ta tafi unguwane. Har ya shiga ya huta ya dan kwanta bata dawo ba ran shi ne ya baci sosai da ita yaji yana son fita don haka ya shirya ya fito dan yasan kafin ya dawo ta dawo gida a lokacin. Sai dai abinda ke bashi mamaki baifi ganin motocin shi duka dayayi ba a gidan yana tambayan kan shi da wace mota nafisa ta fita ? Yana fita batare da sanin inda zai tafi ba har ya yanke shawaran zuwa wurin Yusuf sai ya fasa don ya san yanzu shima hutawa yake a gidan shi kada yaje ya damay shi. Sai kawai ya yanke shawaran ya leka khadija don ya kwana biyu da ganin ta hanyar hostel din mu ya dauka sai da ya iso ya kira waya gashi abakin hostel. Nace da yamman nan yace na koma ne nace gani fitowa yaja iska ya kashe wayan na fito ina tako dadaya wanda ni ban san inayi ba ma. Na karaso wurin motar cikin yar murya na nace dashi sannu da zuwa baki maraba da zuwa na bane ko may ? Murmushi nayi tare da fadin naga baka fita a wanan lokacin ne kawai har ina da lokacin fitane na daban da ban sani ba yace shigo mota mana. Ina shiga sai kawai ya tayar da motar nace da sauri sata na zakayi ko may ? Bai bani amsa ba yaci gaba da kallon titi may zan sata anan, nace mutum, dariya yayi yace kan nan naki kuwa zaiyi kudi sosai nace ai kafin ka sai da nawa ka fara sayar da na buzuwar ka ita bakuwar haure, Kuff naji yake ma bakina dan bugu da sauri na dafe bakin nace saboda buzuwa ka dukar min baki ? Yace ban san hadinki da wanan buzuwar ba nace halinta halinta bai mun bane don tana da ji da kai da son wullakanta mutane. Ita abi kyama ba a kyamace ta ba sai itace zata kyamace mutane matar tawa ce abin kyama khadija ? Ba ita duk buzaye abin kyama ne gare mu yan Nigeria sai iri kune dake mai dasu mutane kawai baku kyaman su don su din ba abin yarda bane mazan su da matan su. Sai mutum ya yarda dasu daga baya su zo su yaudare shi yaudara a wurin su ba abin kunya bane don su din basu da kunya ko kadan. Shiru yayi yana tunane a ran shi bai bani amsan magana na ba nace kuma gasu da son raba mutum da yan uwan shi su cika gida da nasu yan uwan. Ga kazatar tsiya da son mamaye komai ya koma nasu su kadai koda kuwa sun samu wasu mata ne a gidan shiru nayi don na dauka bai saurare na a lokacin. Sai naji yace uhmm go on yaya kikai shiru ba labari kike bani ba nace au na dauka baka sauraro na ai gasu da dan banzan bin malamai da bokaye basu yarda da kowa ba sai kan su suna iya yiwa yan uwan su yankar baya su zauna da mijin yar uwar su. Zasu iya ketarowa da auren su suzo su auri wani anan alhalin duna da mazan da suka baro a gida sai lokaci lokaci suke lekasu. Kai bazaye muggan mutane ne sosai wallahi duk wayon ka zasu san yadda suka juya ka indai na miji ne ji nayi ya tsayar da motar da karfi yace bari inyi sallah please sai kici gaba da bani labarin ki. Fita yayi a motar ya nufi wani gu sai yanzu na duba naga ashe massalaci ne a wurin shiga yayi a ciki na mayar da kaina akan sit din motar ina kallon mutanen da ke gurin. Ya dan jima a ciki ya fito ya shiga motar ya kama hanya mun dan taba tafiya ba tare da nasan ida zamu nufa ba. Yace bissimila cigaba da labarin ki nace labarin yai ma dadi ke nan kwarai kuwa ina jin dadin labarin sosai nace toba zan kara fada ba. Don may ko don kar naji halin buzaye nace ba wanda baka sani ba a cikin wanan kai da ke da ita a gida may ya rage da baka sani ba. Ina ga saura bani kuddi baba ko a yaye ka kafa ka wayi gari ka samu ta ketara kasan su da dukiyar ka. Yace da taci rabon ta ashe idan ta iya ketara kasa da dukiyana duka eh tunda a banza kake samun kudin yace haka kike zato ashe ? Ni ba ragon namiji bane ko da yaushe ina tsaye da kafana wurin neman na kaina zaune a office din nace mai. Au haka kike dauka na ni ko a gidana nake ina neman na kai na nace gun buzuwa ke nan kai ya girgiza min. Koda yake dama abinda kuke nema a wurin su na daban ne da sauri ya juyo yace may muke nema a gun su nayi shiru tare da kawar da kai gefe. Fada min may muke name muka aure su nace su mana tunda irin su ne ku din jara, , , , shiru nayi karasa mana ina jin ki. Hannu yakai yana kamo min baki nayi saurin rike hannun nashi a karo na farko dana taba taba jikin shi da sauri na sake hannun nashi. Na kawar da kai na gefe hannun nashi ya duba a hankali sai naga ya sauke murmushi a fuskan shi yace how lucky you're ? Ke ce mace ta uku da na taba hada jiki da ita a duniya nace nima ina regreting din hakan da nayi wallahi. Shiru mukayi yaci gaba da tuki wani guri ya shiga da motar mai yawan ginene gine da sasa da yawa yace kin san wanan gurin tsoro ne ya kama ni dana kalli gurin sai na dauka ko hotel ne. Kai na girgiza alaman tsoro ya kamani sai naji yace nan ne ma,aikatar mu wanda daga MD din mu sai ni a gurin. Da sauri na kalle shi yace ko kina bukatan shiga kiga gurin da sauri na girgiza kaina nace a,a don Allah ka mayar dani hostel inda ka dauko ni. Ai bamu gama ba don baki ban amsata ba da sauri nace tamay yace irin mu da kika fara fadi baki karasa ba nace maganar yawuce ai. Yace a gunki ya wuce ni a wurina bai wuce ba sai naji karasan maganan ki ko mu kwana a nan da sauri na dago ina kallon shi don Allah dai kayi hakkuri ka mayar dani inda ka dauko. Maimakon yayi abinda na nace sai naga ya gyara set din motar ya kwantar dashi tare da sa hannayen shi yayi matashi dashi yakai kwance. Muna wurin shiru ba wanda yai magana a cikin mu sai tsukin da nake ja can yace a kasalance kada ki kara jamin tsuki a mota yanzu na fitar dake na wuce. Kayi hakkuri don Allah ka maidani hostel ina da exam next tomorrow ban son in fadi wani mutum ne ya dun faro inda muke yana haska toci a hannun shi. Ni dake zaune nake iya ganin mitumin dake tafe nace ga wani nan yana zuwa gurin nan fa bai damu da abinda nace ba yana kwance abinshi yadda yake. Har mutumin ya karaso ko ya sheda motar shine sai naga ya dan tsaya daga nesa damu yana fadin barka da dare yallabai an wuni lafiya cikin harshen turanci. Ya dago yana amsa mashi da lafiya kawai sai mutumin ya juya ya koma ciki ban san na firgice ba sai bayan wucewan mutumin yace lafiya kika shige min a jiki haka ? Ko kina son jin abinda buzuwa ke ji ne ajikina ta leke min da sauri nayi kokarin jaye jikina dana dan manna da nashi sai naji ya riko ni. Ta yadda har muke iyajin saukar numfashin junan mu a lokacin ka sake ni don Allah wai may kake nufi da nine haka wai ? Fada min amsan tambayana mubar aurin nan kada masu gadin nan su dauke ni dan iska nace sake ni in fada ma to yace sai kin fada jin irin rikon da yaimin yana kara manna ni a jikin shi nace jarabbabu irin su mana. Sake ni yayi ya daga bai ce komai ba ya tayar da motar muka bar gurin sai da naga mun hau titin da zai sada mu da hostel din mu hankalina ya kwanta dashi. Don yadda a lokaci daya naga canjin yanayi a gare shi ya firgitani ainun sai da muka dauki hanyar hostel din yace ki shirya shiga cikin jarababbun mutane daga yanzu. Ban iya magana ba bukata na shine inga kafata a kasa yanzu a wani shago ya tsaya ya shiga har ya dan dade sai gashi ya fito ina hangen shi tun daga nesa na raya a raina Allah yayi halitan namiji a nan . Baya ya bude aka saka mai kayan a ciki ya sallami yaron ya shiga muka tafi bakin hostel din mu ya tsaya bai bude motar ba niko a kage nake da in fita daga motar. Yace zan yi tafiya may yuyuwa baza mu hadu ba sai idan na dawo Allah ya tsare hanya nace dashi tare da kallon shi ya bude min motar. Kina level nawa yanzu a karatun ki nace two a takaice yace yayi nisa da yawa gaskiya nace ai ni ke yi ba wani ba ban ga amfanin karatun ba a guna amma ai naga su Binta da zainab sunayi suma ? Wanan matsalar su ne ni nawa matsalar na sani bata wani ba su ya shafa wanan bani ba amma kai mugu ne ko ? Zaki iya ba kan ki amsa idan kin so ko wani kalar nake ya bude min motar tare da miko min ledojin dake bayan motar ina karba na fice ina fadin mugu kawai da karfi. Girgiza kan shi yayi ya tayar da motar ya tafi sai da ya fara tafiyane tunanen Nafisa ya zo mashi a rai yana tunanen ko ina taje dazun ya dawo bai samay ta a gida ba. Ya iso gidan ya shiga a falo ya samu su Hadiye zaine suna hira suna ciye ciye gaishe suke da dawowa yace Nafisa ta dawo sukace bata dawo ba ya shige ya barsu a gurin zaune. Ya shiga ran shi a bace ya dubi lokaci yaga tara da wani abu na dare goma saura kadan wanka ya shiga yana tunanen Nafisa a ranshi har ya fito ya kwanta shiru ba Nafisa. Ni na fado mashi a rai jarababu irin ku murmushi ya danyi yana rufe idon shi kamshin turen oud dina yake tunowa daya shaka. Ya lumshe idon shi tare da gyara kwanciyar shi yana lumshe ido yaji dadin kasancewa mu a tare yau hiran da nake mai na buzaye ne ya dawo mashi a rai. Ba abinda na raga daga halin da yasan Nafisa dashi zai iya cewa kila wani ya fada min kadan daga cikin halinta daya fahinta. Sai dai abinda ya tuno inda nace suna barin mazan su a gida su zo duniya su auri wani mijin na daban sunayi suna zuwa ziyarar mazan nasu. May wanan maganan yake nufi kodai shiyasa Nafisa take yawan ziyaran gida akai akai bai sani ba da sauri ya kawar da wanan zancen kada zargi abinda bashi ba yashiga zuciyar shi. To wai ma ina Nafisa taje ne uban may tafitayi da tun safe har wanan lokacin bai ta dawo ba yaja tsuki yace zan gwada ma Nafisa matsayin ta na mace a gidan nan. Goma, sha daya shabiyu saura ya mike zubur hankali a tashe ya mike yana zura riga a jikin shi ya sauko zuwa kasa komai na falon a kashe yake . Su hadiye sun shige dakunan kwanan su kayan da sukaci abinci gurin babu kowa a wurin tsuki yaja ya fita waje ya nufi gurin maigadi yana tambayan shi ko yaushe nafisa tafita a gidan. Maigadi yace rabon shi da ita tun shekarajiya da kawar ta tazo suka fita komawa yayi ciki yana tunanen tun shekaran jiya da kenan Nafisa dama bata gidan tun lokacin da shima yayi tafiya ko may ? Kamar zai tayar dasu hadiye ya tambaye su sai kuma ya fasa ya koma ya kwanta suna barin mazan su a gida su je wani guri su kara aure suna yi suna ziyarar su. Abinda ya fado mashi a rai ke nan karfe daya agogon da ya kalla ya nuna mai da sauri ya mike zaune biyu saura na dare yaji ana buga gidan maigadi ya bude kofa motar ta shigo sai ganin nafisa yayi ta fito daga motar ta dan tsaya suna magana da ta cikin motan. Ta shigo gidan a gajiye take kafafuwan ta har sun dan kunbura saboda zaman motan da tayi mai tsawo dakin su hadiye ta fara zuwa. Ta samu suna barcin su hankali kwance ta ta da ita a cikin magagin barci tace kin dawo da yare tace na dawo bata gane komai a guta ba ta juya zata shige tace Alhaji ma ya dawo dazu da safe. Dam taji gaban ta ya fadi da sauri ta fita zuwa dakinta ta kayan sihirin da ta dawo take kokari boyewa a wardrobe din ta sai taga an kuna wutan dakin ta. A fusace ta juyo sai ganin Abdulsamad tayi tsaye yana kallon ta da sauri ta kara gare shi sai yayi saurin juyawa ya fice daga dakin . Boye kayan ta karasa yi ta rufa mai baya ta murda kofan dakin a rufe taji shi gam ta juya zuwa dakin ta ciki da fargaba da tsoro a ranta. Washe gari ta samay alokacin ya gama shiri zai fita yana daura agogo a hannun shi yana gani ta ya daure fuska tankar bai taba dariya ba a rayuwan shi. Rudewa tayi tama rasa may ta fada mashi can dai tace Samad kayi hakkuri na san ban kyauta ba na fita ba da sani ka ba. Jakar laptop din shi ya dauka zai wuce ta zube kasa gaban shi tana fadi ka yafe min gurin buki naje shine naka wanan lokacin ban dawo ba. Nasan nayi laifi fita in dade baka nan amma kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa ba insha Allahu. Yace don gani saunar na miji ki fita gida na kwana da kwanaki yanzu kizo kice inyi hakkuri haka kai tsaye bayan kin gama yawon gantalin ki a can. Kin kwaso kafan ki kin dawo min gida ki koma inda kika fito zai fi maki sauki na baki minti awa daya ki fice a gidan nan da kowa naki. Samad kayi hakkuri ka yafe min ba zan sake ba yace rufa min baki munafuka wace bata san ciwon kan ta da darajan aure. Ya sure jakkar shi ya fice a dakin da kyat ta iya mikewa tsaye daidai lokacin ya dawo yana fadin fita min daga daki zan rufe abina ne . Ta bishi da kallon mamaki a kofan tana tsaye ya rufo dakin shi karo na farko a gidan abin ya mata zafi saidai cikin ranta tana fadin yi abin ka a hannu na zaka dawo kwanan nan. Ya fice ta bishi da kallo tare da juyawa ta wuce zuwa dakin ta tana mai jin haushin shi. Kutayani da addua yan uwa ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Washegari da safe ban tashi da wuri ba don fashin sallah da nakeyi sai da naji motsin daddy ya dawo na fito don in gaida su har lokacin a cikin damuwa nake. Daddy yana zaune a cikin dan karamin falon mu ga abin karyawa a gaban shi mama tana gefen shi ta motsa mashi kunun da ta aje mai a gaban shi sai kamshi kosai ke tashi a falon. Daga kofa na tsuguna ina gaida su daddy yace a a baby na shigo mana daga ciki na tashi na karasa shigowa cikin falo har lokacin na kasa sakin jiki dasu kamar kullun. Daddy yace ya karatu nace daddy Alhamdullah yace babu matsalan komai ko nace daddy ba matsalan komai na fada tare da sunkuyar da kaina kasa. Ina kokarin mai da hawayen da ya ke shirin silalowa a idona nace daddy sai dai wanan mutumin da ya hado ni da kayan nan wallahi ban san ya sakasu a mota ba sai da muka zo nan taimakon shi nayi shine ya saka min da haka. Ido duk kan su suka tsura min da nake masu bayanin daddy yana kallona yana yaba hankalina don yasan ba zan boye masu komai dake faruwa ba. Saboda karya ba halina bane kai tsaye nake fadin gaskiya ga mutum yace dakata khadija kin mashi alheri kin shirya shi da iyayyen shi. Shi kuma yaji dadin hakan ya saka maki da alheri ko kamar yadda yace na gyada kai nace hakane daddy. Mama tace ina kika hadu dashi haka khadija nace mama a wurin da aka tura mu aiki ne na hadu dashi ya samu matsala da iyayyen shi da yan uwanshi. Shine na basu shawara ya nemi shiri da yan uwanshi da mahaifar shi ta hanyar aikata masu alheri daya jaraba hakan sai suka shirya dashi. Shine yazo yace zai saka min da alheri akan abinda nayi mashi tace khadija shine ya kashe maki wanan uban kudin daga taimako kawai irin haka ? Nace mama wallahi ni ban san haka zai min ba daga ta Hussai yace ma mama kin san ni ya kamata in dauki zafi akan maganan nan fiye da kowa. Amma sanin halin ya ta danayi yasa na yarda da bayanin mutumin nan tunda ya rantse min da bata roke shi ba kuma ba da wani manufa yayi mata haka ba. Yai min bayanin da hankalina ya sa na yarda dashi da ita sai dai yanzu ba yadda muka iya tunda kayan nan sun riga sun shigo gidan nan. Kiga ba komawa zasu yi ba tunda dai ba rokon shi tayi ba sai dai khadija a gaskiya nayi mamaki da wanan abin don ba karamin kudi ya kashe ba ga kayan abincin nan. Da sauri nace daddy ba kayan abinci bane kawai har da na sakawa da kudi sune a cikin wanan akwatin da ga gani jiya. Ido maman mu ta fitar waje tace khadija anya ba dan yankan kai bane kika hadu dashi kada fa watarana ya gama zolayar ki da abinduniya mu nemiki mu rasa. Dariya maganan ta yaso bani sai na dake nace mama ba dan yankar kai bane don nasan kowa nasa na kuma san matar shi. Share kawai duk wanan tunanen nayi shi a daren jiya har nafila sai da nayi akai banga wani abin cuta ba daga gare shi sai tarin alheri da na hango ga wanan alamarin. Shiyasa kika ga ban wani damu ba da hakan sai da ita din ta kula da kanta da mutuncin ta da irin tarbiyar da mukai mata zan sake yin yau na gani don ni kaina abin ya daure min kai sosai. Mikewa nayi na dauko kudin da kayan na turo zuwa dakin nan na fara fitarwa ina masu bayani yadda kayan suke nima mamakin yawan kayan nake yi a cikin macewa jiki. Daddy yace aje kayan zamuyi sai na nemi yar uwarki a waya naji shawaranta akai da yadda za ayi da kayan. Zan dage da rokon Allah don ina jiba jikina kamar akwai alheri ga haduwan khadija da wanan mutumin sai dai mu bar ma Allah sanin shi. Koda yakira ya Amina yayi mata bayanin abinda na dawo dashi wanan karon tare da fadin ta sake binkice na tsakani na da wanan mutumin don a gono gaskiyar maganan. Ta kira ni lokacin ina kwance mara na yana damu na da ciwo na dauki wayan ina gaida ita bata tsaya amsawa ba sai cewa tayi Deeda make faruwa ne daddy ya kirani yana fada min wani magana da safen nan. Shiru nayi sai da ta kara maimaita maganan ta nace cikin kuka wallahi ya Amina ba halina da kuka sani da na canza yanzu. Nima ban san da kayan nan ba sai da muka shigo garin nan na gani nan dai na koro mata bayanin komai don ba zan iya boye mata ba ita. Tace khadija kina nufin dama Abdulsamad ne ya yi maki wanan alherin ban sani ba khadija baki jin tsoron buzuwa ta san wanan labarin ta yi maki illar nace ya Amina yaya zanyi ni ban roke shi ba shiya bani. Tace dama khadija kece kika saka yayi wanan alherin da yayiwa iyayyen shi ashe dama duk kece sanadi ni ba komai nake ji wa ba sai buzuwan matar nan tashi wallahi. Takira daddy tayi mai bayanin komai yace shi zancen buzuwan matar shi bai damay su ba tunda ta sheda ba mugu bane. Nema ne idan naga zan iya sai in yi dashi wanan ba komai bane Allah yasan abinda ya hada a tsakanin mu ya kawo hakan sai dai mu saka ido a kan yar mu don har yanzu khadija yarinyar ce karama. Ya Amina tace gaskiya ne daddy zan shigo kafin ta koma dayardan Allah anan suka rufe maganan tare da taya ni addua ga wanan lamari tunda daddy yace abarwa Allah sanin shi a tsakanin mu. Maryam ta kirani nake mata bayanin abinda ya faru dani maimakon ta tayani jimamay sai naji tana min dariyan shakiyancin da ta saba min tace shike nan ya nuna maki wayon manya ya gabatar da kan shi ke nan gare su. Nace wai ke maryam don Allah may yasa kike irin haka ne sai a na maganan gaskiya sai ki dauko wani zance daban tace shike nan yanzu mubar zancen a haka dai. Nace zai fi sauki muka dauko maganan karatu bayan mun gama wayan ne barci ya dauke ni a wurin wanda nasan barcin da ban samu bane a daren jiya. Nan dai na kwashi barci na sosai a ranan sai wani lokaci na tashi don mama taki sake min fuska yasa ban son fita a tsakar gidan sam. Wayana yayi kara na dauka Dan Baiwa nagani a rubuce wani haushin shine ya kamani a raina nayi banza da wayan nashi bandaga ba har kiran ya katse. Ya sake kirana da kyat na iya daga wayan don har yanzu ina fama da ciwon mara dake cina jin murya na da yayi yasa shi saurin fadin. May ya samay ki baki da lafiya ne may ke damun ki ne khadija haka yadda naga ya rude ne nace banda lafiya ne . Tun yaushe nace tunda safe daddy na gida naji ya tambaya nace yana waje turo min da layin shi may zakayi da layin shi nace dashi. Ban number shi nace maki ya fada a dake nace ban san number shi OK zan kira a bani number yar ki in karba a gurin ta yace da sauri nace a a din Allah ni dai kada ka kirata naji sauki. Dole na bashi layin daddy din don naga yana niyar kashe wayan bayan na bashine ya kashe wayan bai fi minti goma ba sai ga daddy ya shigo gidan yana fadin ina khadijan take ne wai ashe bata da lafiya bamu sani ba. Sai da wanan yaron ya kirani yanzu yake fada min khadija bata da lafiya a kaita asibiti wai zai turo da kudi kamar shine ya haife ta. Mama tace ni tunda jiya da ta dawo na ganta kwance ban san may ke damun ta ba, har dakina daddy ya shigo ya samay ni kwance sai dai ba barci nake yi ba. Zama yayi saman tsohowar kujeran dake falon yana fuskanta na yaga yar raman da nayi yace baby na may ke damun ki ne yanzu wanan mutumin ya kirani wai baki da lafiya. Sai dai ban san ida ma yasamo lambata ba ya kira nace niyace in bashi na tura mai yanzu amma ban san kiranka zai yi bz ai daddy yace zai turo da kudi wai kije asibiti nace ya barshi bayan kudin da ya turo muna zai kara dawainiya kuma. Daddy yayi murmushi yace kin san may yace dani na girgiza kai cewa yayi wai dawainiyar ki yanzu akan shi yake. Nace daddy kada ka yarda da maganan shi wallahi ni ba komai a tsakanin mu yace naji sai dai yadda yake ya nuna min da fuskan gaskiya yazo maki don bai bar abin a tsakanin ku ba ku biyu ya sakomu mu iyayyen ki a ciki bai boye muna ba. Yanzun dai yace a tura mashi da account number da zai turo kudi kije asibiti nace daddy nifa ba komai a tsakanin sai mutunci kawai yace yaji. Sai ga daddy ya shigo zuwa sha biyu yana fadin ya turo dubu hamsin in tafi asibiti nace nasha magani naji sauki daddy dama ciwon mara ne kawai ke damu na. Yanzu yaya kike son ayi da kudin da ya turo maki kasa kasa da murya nace kayi amfani dashi kawai daddy. Sai yamma ya kira yana tambaya ko naje asibitin nace eh yace sun baki magani nace eh nasha har naji sauki sosai yace ashe period kike yi kike wanan raki haka ? Shiru nayi banyi magana ba yace duk wata haka yake maki nace ban sani ba yace kan ki ga Yusuf ku gaisa. Kunya naji sosai jin har da Yusuf yasan ina period yanzu muka gaisa yayi min yaya jiki nace da sauki yace ki sha magani kin ji sauki ko nace eh yayana . Sai shiru ya biyo nace Yusuf batare da fadin yayan da na saba kiran shi dashi ba yayi makin jin hakan daga bakina sai ya dake yace yaya akayi yar mama ? Nace kayiwa mutumin nan fada mijin buzuwa akan abinda yayi min bai kyauta min ba don may yake son saka iyayyena su zarge ni. Yace zargi kuma khadija akan may nace yanzu haka tunda na dawo mama sai fushi take yi dani akan abin da ya saka a motar da naje gida dashi. Saboda shi take fushi dake nace wallahi ni na rasa may zanyi akai suna ganin kamar ban kama kaina bane a Abuja ina hurda da mazan banza ne a can. Sai daddy ne kawai daya fahinci komai da taimakon ya Amina na samu ya dan sausauta min bai fishi dani muryan shi naji yana fadin why mama zata yi fushi dake akan dan abinda na tura masu. Mama bata yarda da tarbiyan da sukai maki bane ko may in haka ne kuwa zan shigo da kaina in mata magana da zata fahince ni ita ma. Ban saka ba haka ka hadani dasu dazun daga na fada ma banda lafiya ka fadawa daddy yazo yana yi min fada balle maman mu da ta hau dani. Ba matsalan ki bane nasan abinda zance da ita idan nazo nayi saurin fadin bansaka ba dai ka barni da ita zamu shirya wataran. Bayan na kashe wayan na mike na shiga wanka na fito na canza kaya jikina zuwa dogon riga nayi kyau sosai a cikin rigar lokacin yamma yayi sosai nace zan je gidan su hafsat kawata da tai aure ta haihu bani gari. Kallon da mamaki min ne yasani tsarguwa sai daga baya na fahinci rigar da na saka ajikina ne yasa take min wani kallo da bashi ba. Sai na dawo tace min batare da ta kalle ni ba na fita jiki a sanyayye zuwa gidan hafsa din dake bayan minna minicipla coucil. Hafsa kawa ta ce tare muka taso da ita kasancewar unguwar mu ba nisa da karatuna ya dawo minna na hadu da ita muna zuwa girl day dake a bayan old airport tare kusa da tsohon makarantar wtc na mata. Bayan mun gama ta samu wani guy ta aura dan kabilar Nufe dake tashen kudi a lokacin . Na fito gida a hankali nake takawa iskan marance yana kadawa inda nake ganin fuskokin wa yan da na sani muna gaisawa jefi jefi dasu a hanyan. Har na isa gidan na samay ta tana girkin abincin dare tana gani na ta tare ni da murna muka gaisa ta nufi falon su dani ina biye a bayan ta. Sai bayan na zauna ne ta dauko min baby ta har yaron ya fara wayo sosai ta miko min shi sai bina take da kallo wai na sauya gaba daya na zama wata big girl dake nace kai haba dai hafsat har dake cikin fadin haka. Tace wallahi gaba daya kin sauya ma sani na ne khadija nace yanayi ne kawai wallahi yazo a haka ba wani abu may ye sunan yaron na tambaye shi. Muna hira tana duba girkin da takeyi har ta karasa takawo min nace wallahi hafsat a koshe nazo gidan nan watarana zanci. Mikewa nayi saboda magariba daya kawo jiki sosai na bata asai ma yaro takalma ina shirin fitane mijin ta ya shigo gidan. Allah ya gani jini na bai hadu da mijin ta ba tun farko asali ma nice ya fara cewa yana so sanin shi da nayi dan duniya mai wayan yan mata da kyale kyali yasa ban bashi fuska ba. Naje hutu kaduna kafin in dawo na samu sun dinke da hafsa har sukai aure yanzun ma da ya shigo gidan ya samay ni sai da ya daga min gira ba tare da sanin hafsa ba. Harara na watsa mai na fice gidan tare da yi mata sallama nadan yi nisa naji muryan shi a baya na yana fadin khadija ji mana. Juyowa nayi fuska a daure ina kallon shi nace lafiya dai ko ya washe baki yace don Allah sorry to distub you kin boye fa da yawa ban san kin zo garin ba ai dana kawo maki gaisuwa. Dan murmushi nayi nace ba komai ai gashi mun gaisa yanzu dama boye nazo gani na ganshi har yayi wayo. Yace in ba laifi ki bani layin ki akwai maganan da zamuyi kin san dai yanzu ba da bane zaki iya fahinta na har yanzu ba kin fita raina bane. Auren hafsa Allah ya nufa sai munyi da ita amma ni ke ce choice dina tun farko hafsa dai ta shishige min har na aure ta. Dakata Adam kada ka kara taro na da irin wanan maganan ko da hafsat bata gidan ka kai ba choice dina bane ka sani ban hurda da maza irin ku da kafan su bai tsayo a guri daya ba. Ke kizo kici arziki kibar arziki kawai don yanzu arzikin bana yaci uban na da zan iya daukan lalurar ki da komai naki wallahi. Wani kallo na watsa mai na up and down nace a haka din kake tunanen zan iya cin amanar kawata aminiya ta nace Allah ya tsare ni da masu irin halinka. Na wuce na barshi tsaye a gurin yana bina da kallon zalama irin ta yan iskan maza yana sosa kan shi baida mu da mutanen dake wuce ba a saman titin. Na shigo gida ana kiran sallah magariba dakina na nufa sai da mama ta gama alwala ta kwada min kira na fito inyi sallah lokacin sallah yayi. Nace mama kin manta bana sallah ne ta ce oho ta shige dakin ta sai bayan sallah isha,i daddy ya dawo gidan suka zauna a dan falon mu har kanne na ciki suna kallon NTA dake labaran marance. Daddy ya duba bai ga na shigo ba yake tambayan ina nake mama tace ina dakina kafin yace wani abu wayan shi ne yayi kara ya dauka bayan sun gaisa ne yayi mai magana yana son magana da mama ne daddy yasa handfree din wayan yadda zai ji abinda yake fadi. Sun gaisa yace mama don Allah a dan sasauta ma khadija da takurawa tace na saka kuna zargin ta da aikata ba daidai ba ni kuma nasan idan har kun yarda da tarbiyan da kukai mata ba abinda zaisa ta canza daga baya kuma. Mama kiyi hakkuri khadija na nan a yadda kika santa alheri kuma yanzu na fara maku kuda ita muddin ina raye sai abinda yafi karfina ne bazan maku ba. Alherin yar ku gare ni ne ya jawo maku hakan ba ina nufin Khadija da wata manufa bane sai alheri don ta cancanci haka a gare ni so kuyi hakkuri a sake mata fuska babu komai sai alheri ga haduwana da khadija. Bayan sun gama waya da mama ya gama daure ni a gaban su da ban gane manufar maganan shi ba daddy ya kwala min kira daga falon. Da sauri na shigo dakin har lokacin shigan da na fita gidan hafsat ne a jikina ban cire ba na samay su a zaune falon. Gaidasu na fara yi tare da samun wuri na zauna mama tace khadija yaushe ne kika canza haka wai ? Nace cikin dago kai da mata kallon mamaki nace mama wanin abin nayi kuma again tace yanzu bamu da shakat a gidan nan dan abu kadan sai ki kai karan mu ga saurayin ki. Da sauri nace mama wane saurayina kuma danakai karan ku gare shi tace wanda kika jajibo a Abuja mana wanda ya fimu sanin zafin ki a yanzu. Mama ni ba saurayina bane wallahi ba wani abinda ya taba shiga tsakanin mu na soyayya har yau tace in babu yaya kika kai karana wurin shi wai na saki gaba a gidan nan tunda kika dawo. Kai kai innalillahi haka yace maku mama fada nayi mai fa akan abinda yayi min nace kina zargina ga abinda kika gani ya bari ban so. Daddy sai dariya yake muna ni da mama don yasan duk iya binciken shi bai gano wani abu da nake aikatawa a bayan su. Tun daga wanan ranan mama bata kara daure min fuska ba muka koma daidai a gidan kamar yadda muke a baya. Wayana gaba daya na kashe sai zan kira nake kunna wa don ban son wani abinda zai haifar min da matsala kuma tsakani na da iyayyena a gida. Ya rage saura kwana biyar mu koma makaranta sai ga kamal mai bi mun ya shigo da kaya wai ya Amina ta shigo gari. Da gudu na kwasa nayi waje ina masu sannu da zuwa tana sallaman driver da ya kawo ta gida na rungumay ta na sake ta naja hannun yaran na rungume su a jikina. Ciki muka shiga gaba dayan mu bayan ya Amina ta huta taci abinci tana zaune a falo na shigo da karamin dan ta a hannu na tace dada hutu ya kusa karewa dai nace wallahi ya Amina. Nakai zaune kusa da ita tace dama ina son in zo gida in samay ki kafin ki koma ne nace tau wani abin nayi ya Amina ? May ye ma baki yi ba khadija ina ke ina Abdulsamad mijin buzuwa fati da mijin ta ta barshi dole don wanan buzuwa ke yanzu kike kokarin jefe kan ki ciki. Kai ya Amina kuna bani mamaki wallahi wai ya fada maku muna soyayya dashi ne halan na san dai shi ba zai fada ba. In kuma don wanan abinda yayi ne kuke zaton muna tare ne da bakin shi ya fada ma daddy gaskiya ba sona yake ba. Haka kike tsamani ke ko azaton ki duk wanan alaman da yake gwada maki ba so bane hakan wani namiji zai samay ki yace bai so ki. Kin fi buzuwa durin na ya mace sai dai fari da gashi zata gwada maki ko farin ma ba wani can ba don ke ma ba baya ba. Sai yanzu nake gane maganan baban boy da yake cewa ke din matar manya ce watarana ina ganin kamar fadi dai yake yi. Abin mamaki ne yadda har Abdulsamad ya fada tarkon ki abinda ba wanda ya taba tsammani zai iya sai gashi lokaci guda har kin fara canza shi da naki sallon soyayyan. Mama da ta shigo dakin dauke da kwanon da ta tuka muna tawaska ta aje tana cewa ke ma dai kya fada idan anyi magana tace an matsa mata ba soyayya suke da shi ba ko takai karan guri shi. Shi ko ba kunya gare shi ba ya kira mutane yana rokon su akan a daina matsa mata don Allah ni daddy ku har mamaki yake bani yarda ya yarda da mutumin nan a lokaci daya. Da ban san halin shi ba sai ince ko don kudin shine yake son shi ya Amina tayi sauri cewa a a mama ba halin daddy bane haka da yana bin kudi da ba zan auri Abban su boy ba. Mama tace nasani ai shine abin ke ban mamaki yanzu ai tace yarda ne kawai wallahi in badon buzuwar matar shi ba ai Abdulsamad mijin aure ne ga ko wace mace ta samay shi. Nan ya Amina ta fara ba mama labarin shi da rayuwan su har karshe nace wai ku may yasa kuka damu da wata buzuwa can ne. Kowa tashi tafishe shi amma ni bata cikin tsarina ni dai kawai bai min bane ina zan jefa kaina ga family man mai iyali da yawa haka. Wanan duk ba matsala bane tunda yana da abin kula da koda mata nawa yayi niyar yi abin damuwa shine kishi da wanan buzuwan da bata da imani ko kadan. Balle idan taji ba barin shi zatayi ya aure ki ba kuna tana iya yima rayuwan ki illar yada taiwa fati ko sunan ta baya son ji yanzu. Allah bai bata iko a kaina nace ke don Allah rufawa mutane baki ana baki kina roko may kika taka da kike fadan haka nace mama Allah. ZAINAB IDRIS MAKAWA 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Mommy wayayir mace mai haba haba da jamma irin matan nan ne masu fara,a a fuskan su kuma ita har cikin zuciyar ta haka take da kowa sai dai bata daukan raini. Abin ta bai rufe mata ido ba tana da ilimi na boko wadattace don duk matan na Abban su Abdulsamad suna da ilimin su ya aure su in ka debe ummi wace iyakarta secondary kadai tayi har hajiya mama mahaifiyar Abdulsamad a gidan shi ta hada karatun ta na NCE wanda dama koyarwa take koda ya aure ta. Ita anty amarya ma da aikin ta ya auro ta wanda yanzu ta daina duk ya hana matan nasa aiki ya tsaya ga bukatun su kuma. Mommy ne zaune tare da Abban yana karyawa hajiya mama wadda yaranta ke kira da hajiyan mu ko hajiya mama ta shigo falon. Akan maganan tafiyan mommy da Abdul din ya bugo yana mata tuni a daren jiya don sun fara tatauna maganan sai Abban bai bada goyon baya akan haka ba. Yanzu shine ta shigo ayita akaare idan zai yarda shigowan mama yayi daidai da shigowan hajiya ummi da anty Amarya data kira kaffinta shigo. Sun sami wurin sun zauna tare da fuskantar shi yasa yasan da magana sukazo mai ummi ce ta fara maganan amma sai anty amarya ta dan saka larin kishi a ciki tace ni naga ai ba sai taje ba ya mayar da matar shi mana zaifi sauki. Ummi da wanan kkaron bata goyi bayan maganan anty amaryan ba tace a a Sadiya tunda har kika ji wanan yaron ya bukaci hakan ai sai mu gode ma Allah da har wanan tunanen yazo mashi a rai. Ko ba komai ya kamata ace sanin halin ita Nafisa ya kamata wani daga cikin mu yaje ya zauna kamar yadda ya bukata din don ace mai daki shiyasan ida ruwa ke yoyo a dakin. Nidai kunsan ba lafiya ke gareni ba ba zan iya zuwa ba ita dai suwaiba din ya dace ta tafi don ita dai zainab din ya dace taje ta zauna dasu ta saka ido tunda da iyan bawa zasuyi tafiyan. Murmushi Abban yayi yace ke nan dai kun gama magana kuna goyon bayan dan ku ko ummi tace ba hakana bane Alhaji. Ganin dai dacewan hakan mukayi yasa muka goya baya ga maganan shi da kan shi babangidan ya fara tuntubana da wanan zancen da yazo na bashi goyon baya akan haka. Sai anty amarya ta kalle ta ta rausaya da kanta gefe daya bata kara magana ba har lokacin da Abba ya gama ja ma mommy kunne akan zaman da zatayi a gidan dan nasu. Suka bar mommy dashi a falon kowa ya kama gaban shi tun wanan ranan mommy ta fara shirin tafiya Abuja gidan Abdulsamad wanda suke kira da babangida kasancewa sunan mahaifin maigidan su ke gare shi. Abdulsamad bai fada ma Nafisa zuwan mommy ba gidan sai cin karen su ba babbaka suke ita da yan uwanta a gidan banza ta fadi masu kasa gasasa dama haka aladansu yake yar su ta auri mai arziki dangi su kwaso a taru aci arzikin ta. Mommy bata boye ma Anty Fati zancen tafiyan ta ba inda ta kirata ta fada mata da bakin ta tare da cewa zatayi iya kokarin ta taga ta shirya tsakanin ta da mijin ta kafin ta bar Abuja din. Allah ya kiyaye hanya Fati tai mata tare da cewa mommy amma fa sai kin hada da hakkuri don kun san Nafisa bata kaunar taga kowa ya rabi yaya Abdulsamad. Abinda yakai ni shi zanyi idan tayi ba daidai ba dole ne in fada mata gaskiya koda kuwa bata so dariya tayi don sanin halin Nafisa da tayi kamar yunwar cikin ta. Tsaye yake tsakar falon inda yake umartan masu aikin da ya shigo dasu da su gyara part din Fati yana masu kwatance yadda yake son gyaran. Nafisa da ke barci a dakin ta Yanyala ta shiga mata da maganar cewa may ke faruwa ne taga ana gyaran dayan part din da tace na uwar gidan ta ne. Kamar ba cikine a jikin ta ba ta diro saman gadon ta fito inda masu aikin su nan ta hausu da fada wayasa su aiki a gidan ta ba a fada mata ba. Daga bayan ta ya bata amsa yana saukowa daga sama yace nine nan maigidan na basu aiki suyi in biya su wani irin kallo mai kama da kai asuwa ta aika mashi. Bai tsaya kulata ba sai kokarin shiga dakin da yake yi tasha gaban shi da sauri ta tsare shi may kake nufi ne samad da wanan gyaran da akeyi ? Yace abinda kika gani Nafisa shi nake nufi don gida nawa ne ba naki ba kamar yadda kika fadi yanzu. Nan hankalin ta ya tashi sai ta fara surutu ita may yake nufi da ita da zai mata haka yace don yaga zata haihu zai dawo da fati da yaranta gidan shi. Tace nasan dama kule kulen da ake shiryama ke nan kake yawan zuwa kaduna akai akai yanzu dama ba so na yan uwanka keyi dani ba . Shi dai bai mata magana ba don mazan dake gidan suna aiki ya fita batunta basu raba hali a gaban su ba. Hankali tashe ta kira madam tana fada mata abinda ke faruwa madam tace kika sani ko watace zai dauko ya saka a dakin ba Fati ba ? Nan hankalin ta ya kara tashi sosai tace Nafisa dam wanan tunanen baizo min ba sai da kika tunatar dani haka yanzu. Madam tace to zauna nan kina fada akan fati wata tazo ta shige dakin kina gani saboda sakaci irin naki in zaki mike ki mike tun yaushe muka gama da wata fati can. Wacce hudi daya mukai mata muka fitar da ita a gidan har diyan ta sai tarihin su yanzu har kike tunanen ita zai mayar dakin ta. Ke kasar ku fa zaki koma aiki kaifi sai Niger nan kusa kafin ma mu dawo aiki ya kankama ko mu huta da ko wacece ma ke son muna kutse haka cikin ruwan sanyi. Nafisa tace madam kin san ba zuwan ba kuma ba kudin nake jiwa ba don zan iya saida da duk wani kaddara da nake da akan wanan aikin tunda yanzu na rasa gane kan shi. Matsala daya ne shine mutumin nawa yanzu kin san matsi yake min tun wanan tafiyan da mukayi ondo ya kara burge min a gidan nan baya sake min har yanzu ga kuma lalurar cikin nan dake jikina yanzu. Madam tace ke dai kawai tawa ki nemi kudi in ma bai barki ba sai ni inje maki manene amfanin zaman mu tare da ba zan iya maki komai ba. Ai kawai ki daina damun kan ki mu za a gwadawa hanyar boka ko malam kuma ko latsandan ne gaba da lahira indai ana zuwa zamuje shi. Sai lokacin Nafisa tayi ajiyan zuciya taji dadi a ranta tana ganin aduniya bata da kamar su madam dake tsaye a kan ta yanzu. Tace uwar dakina Allah dai yaja muna nisan kwana tare ni nasan banda kamar ki a duniyan nan yanzu. Da wanan shawaran hankalin Nafisa ya kwanta nan ta shiga buga waya gida Niger ko an samu wani bakon boka ko malami mai tashe a kasan. Sai da ya ga komai ya kankama yadda yake so ya bar gidan bayan ya sallami mutanen da sukai mashi aiki duk da yawan samari yan uwan Nafisa a gidan ba wanda zaiyi bugun gaba dashi yayi mashi aiki alhalin biyansu yake duk wata dasunan aiki suke mai a gida. Bayan kwana biyu su mommy sun gama shirin su tsab ya tura Yusuf ya dauko su zuwa garin Abujan mommy a gutin hajiya mama ta bar yaran ta tazo ita kadai sai iyan Bawa da suka zo tare da wata yar mai masu shara budurwa don taimaka masu da wani abin. Mommy sunyi waya da Ya Amina tana sallaman ta tace zata gidan Abdulsamad wanda matar shi watan haihuwan ta ya kama zasu dan kwana biyu acan . Ya Amina sai sulbul da baka tayi tace mommy ashe zaku hadu da Khadija na ke nan mummy tace banda abinki khadija dake makaranta ina zan ganta ni ? Sai dai idan sawa zanyi a dauko min ita ko akaini in gano maki lafiyan ta idan na samu lokaci dariya kawai ta Amina tayi don ta san gidan su Abdulsamad basu san komai ba a tsakanin mu dashi. Tafiyan rana sukayi don haka sai da yamma lis suka shigo garin Abuja din direct gidan shi suka nufa yana gida a lokacin don yana dakon zuwan su. Nafisa wace ke falo tana shan iska ga yan uwanta a kewaye da ita kowa na shaanin gaban shi sai sallaman su mommy da su iyan bawa suka ji . Gaban tane ya fadi da ganin su mommy din gidan don bata taba zaton zuwan su ba don a wautan Nafisa ta gama da kowa nashi yanzu babu mai marmarin zuwa inda yake. Zuwan su mommy ba karamin faduwan gaba yasa ta ba sai take ganin ai zancen auren da take zato ko dawowan Fati gidan gaskiya ne. Shiya fito daga daki bayan sunyi waya da Yusuf ya sheda mai sun iso ya fito da yar fara, a a fuskan shi yayin da ko kallo su mommy basu ishi Nafisa da yan uwanta dake falon ba . Shi da kanshiyayi masu iso dakin da zasu sauka din bayan dun gaisa sun mashi yaya gida ya fito tare da Yusuf da ya shigo da kayan su ciki da taimakon wani saurayi. Falon ya dawo inda suka samu Nafisa da yan uwanta sun juye harshe cikin yaren su na buzanci suna maganan zuwan su. Fuska a daure ya kalle ta yace Nafisa baki san mommy bane da gwago na iyan bawa da baki tare su da zuwa ba ? Tace a yatsune na san su mana ba matar mahaifin ka bane ita yace OK cikin wani irin kallo har ya fara tafiya sai ya juyo yace tunda kin san ta kin san kuma matar mahaifina ne baki iya taron su ba nima haka ban son in fita yanzu in dawo in samu wa yan nan yan uwan naki a gidan nan yanzu. Yana fadar haka ya juya ya fara tafiya tace wallahi baka isa ba don zuwan su zakace yan uwana su bar maka gidan ka yanzu yace zaki san na isa idan yan sanda dun shigo sun fitar min dasu. Idan akwai abin da yan Niger sukaki jini shine dan kakin Nigeria don basu yi masu da wasa idan sun farmake su. Nan Yanyala ta fara magana tace haba Allaji ai bin baikai can ba daga dan wanan magana har zaikai ka kira muna polizawa kawai dai jira muke su huta mu mika masu gaisuwan mu. Ya fice zuwa nemo ma su mommy abinda zasu ci a gidan don yasan ba zasu iya taba cin abincin da suka dafa ba. Bai dauki lokaci ba ya dawo dauke da ledoji iri na restaurant dauke abinci dasu ruwa a ciki ya bayar aka shigo masu dashi har dakin. Mommy ta idar da sallah sai ga yaron shi isyaka yana shigo da kayan ciki tare da gaba tar masu da abincin. Sunka ce har da dawai niya zuwa sayo abinci kuma nan dai iyan bawa ta kasa hakkuri tace zainabu may kika fahinta ga wanan zaman ? Murmushi mommy tayi tace ke dai iyan bawa ai ayi shani kawai wai ancuci na kauye wanan matar bata da hali ko kadan. Kin dai fara ganin makasudin zuwan mu garin nan ke nan don fitar shi kunyan abokan shi nasan halin matar nan tashi dakilace na gani a fada. Ba zamu sakar mata fuskan da zata kawo muna raini ko wulakanci ba don nasan tun zuwan mu batayi farin ciki da ganin mu ba. Sunci abinci sun huta sai ga Nafisa ta shigo tayi wanka ta saka sutura a jikin ta yan uwan ta suna mara mata baya suka shigo dakin. A falo suka samay su nan ta ja ta tsaya bata zauna ba tana fadin kunzo lafiya ya hanya da mutanen gida ? Mommy tace lafiya duk suna gaida ku yaya nauyi Allah ya rabaku lafiya tace amin sauran suka shiga gaida su da yi masu ya hanya suka fice daga dakin ba wanda ya zauna. Shiko bayan ya mika sakon wuri na ya nufa kamar yadda ya saba zuwa man koda ya kirani muna tare da maryam da zarah a dakina kiranshi ya shigo min. Mutumin ki ne halan yazo maryam take tambayana nace cikin tabe baki shine ai kin san bai tashi zuwa min sai wanan lokaci. Maryam tace ai kuna daidai dashi in kin isa ki fadi a gaban shi yana da amsan baki indai wanan yaya in love din kine. Kai maryam kina da wuyan sha,ani wallahi na fada maki ba soyayya a tsakani na dashi sai amin taka kawai na damuwa. Zarah ta dago kai tace min wani guy kuke magana muje in gani idan ya min in saka shi a layi mu shiga sha,ani dashi. Zarah wai ke baki jin kunyan fadin fitsrane haka tace in banda abinki wake ta wani wasa da so yanzu khadija bari kiyi wasa da daman ki yanzu yan jami,an nan suyi maki wuf dashi. Idan banda abinki an fada maki kowane yan matan jamia ke iya wuf dashi kai daya zarah wanan ya wuce sanin ki wallahi. Dariya tayi tace muje inga guy din nan dai da kuke wani zuzutawa haka dai murmushi nayi kawai don ba zan so a ganni da ita ba. Duk da ba wani shiga na yi ba amma suna ta yaba kyau da nayi wai na hadu zarah na fadin ashe zaki zama yar hannu haka khadija. Tare muka fito dasu sun zo su gaida shi tunda muka tunkare shi zarah ta tsunke da ganin motar da yazo da ita tana fadin tun ban ga guy din ba wallahi nasan zai hadu ko don motar nan da nagani how lucky you are da kika iya canko wanan zukeken guy haka. Mun iso yana ta faman ansa call a wayan shi sai da zarah ta kare mai kallo ta dago bayan ya gama wayan suna gaida shi bai wani sake fuska ba ya amsa gaisuwan. Tare da kawar da kanshi gefe daya zarah tace dama na sani sai irin wanan guy din khadija wanan jan ajin naki yayi yawa wallahi har ta gama ta wuce bai yi magana ba suna shiga maryam ta nufi dakin ta. Maganar shi ta farko bayan wucewar su shine ina kika samo wanan kawar kuma ? Nace a inda ka gan mu yanzu yace No ba girman ki bane da mutuncin ki yawo da irin wayan nan nace kawatace fa tare mukazo karatu daga gida. Na fada maki bana son in kara ganin ki tare da ita please na juyo ina kallon shi ido cikin ido nace tana da aibu ne komay ? Au ke baki ga aibu ta ba wanan bata da kamun kai ba girman ki bane yawo da ita nace ka taba ganin mu a tare ne ko yanzu ma daurowa tayi ka gan mu da ita. Har ya bude baki zaiyi magana sai kuma yayi shiru nima shirun nayi ba wanda yayi magana daga cikin mu. Can naji yace idan na fada maki wani abu zaki yarda dani ? Zaki yarda gaskiya nake fadi. Murmushi nayi nace idan maganar ta kama gaskiya mai zai hana nayarda tunda nasan gaskiya ka fada. Kin yarda dani khadija ? Nace na yarda dakai mana yaya Abdul fati da mijin buzuwa ina fadi ina mashi dariyan shakiyanci cikin gatse. Shima murmishin ya dan yi wanda sai wanda ya sanshi zai iya fahintar hakan daga gare shi yace kin san kamun kan ki yasa muke tare da ke har wanan lokacin. Kasan ni ne da zaka wani ce ina da kamun kai bayan iyakar mu dan wanan haduwan da muke yi. Na tsinci muryan shi yana fadin niko na sanki khadija you are classic baby da na taba haduwa da ita a rayuwana. Katse shi nayi da fadin may ke faruwa daksi haka ne wai ke irin wanan magana yanzu a kai na ko last zuwa da kayi haka ka dinga min wanan maganganun. Ya girgiza min kai tare da fadin ba komai cikin lumshe idanuwa shi sai kuma ya bude su ya sani gaba yana kallo na. Shirun motar na kawar da fadin yau ba fita ke nan yace ina kike son muje nace inda ka saba zuwa mana mu zaga gari kawai kana barnan man motar ka. Haka kika dauki fitan namu dama nace hakane mana tunda ba wani guri muke zuwa ba. Ke ce baki fahinci muhinmancin fitar namu ba kila amma ni yana da ma,ana masu yawa a gare ni matuka khadija. Don kasan cewan mu a tare you have change me now na fahinci su abubuwa da dama da ban taba fuskantar su ba a baya. Maganan gaskiya yau kin dawo min da farin ciki rayuwana har iyayyena sun zo gida da sunan kwana biyu a wuri na. Da sauri nace cikin murna wai da gaske kake yi yace kwarai kuwa deeda don yanzu haka mommy da gwagona iyan bawa na gida maganan nan da muke yi dake. Taya kike ganin bazan maki godiya a wanan kangin da nake ganin kin fitar dani wanda a da nake dauka da shirmay irin naki na yara kike yi. Sun kuyar da kai nayi kasa ina tunane hankalina yayi nisa bani jin abinda yake fadi tsoro na daya ne kada mommy tasan ina tare dashi ta fasara haduwan mu a wata manufa. Ban sauri maganan shi ba na katse shi da fadin zan roke don Allah kada ka bari mommy tasan kana zuwa inda nake don bansan da wani ido zan kallesu ba har hajiyan ka. Ya lura da irin rudewan da na shiga sai dai baice min komai ba ganin bai yi magana ba yasa nace please yaya Abdulsamad ka boye wanan a matsayin siri a tsakanin mu don Allah. Kallo na yayi ya sauke murmushi yace saboda may kike son kada su san ina tare dake nace dashi wayyo Allah kana son su dauke ni yar cin amana ne ko may ? Cikin sanyi murya nace kasan su ba zasu gane mutunci ke tsakanin mu ba sai su dauka muna tare da wani manufan da bashi ba. Hakan kuma yana nufi na ci amanan su ke nan gama yadda suke son Fatin ka a gidan yanzu kuma sai su gan mu tare yaya kake ganin zasu dauki abin. Kai tsaye yace zasufi kowa farin cikin da hakan na sani tunda sun san ki sun san halin ki zasu yi farin ciki da hakan. Daga yau magana ya kare ba sauran wani abu a tsakanin mu tunda bukatar mu ya biya ka shirya tsakanin ka da yan uwan ka. Mamaki magana na ya bashi yace juyo yana kallo na sai can yace ai deal namu bai kare ba tukun ko kin manta baki karasa aikin ki ba akan fati ? Na amsa da fafin kwarai bamu kai nan ba cikin takaici nace wana kuma yanzu ya rage gare ka sai kasan yadda ka shirya da matarka. Ba wani sauran magana yanzu a tsakanin mu kuma na fada cikin tsiwa ya juyo da kyau ya kalle ni yace don mommy tazo duk kike fadan wanan magana ko may. No ba don tazo ba in ma don tazo din ne haka ne bana son su dauki abinda wani fassarane kawai. Ya zura min idon sa yana kallin yadda duk na rude yace a ranshi ashe karyan rashi kunya nakeyi a da gashi yanzu daga jin mommy tazo duk na bi na birkice lokaci daya. Motar tayi tsit kowa da abinda yake tunane a ran shi sai da ya shafa kan shi naji yace relax deeda wace dake mommy zata san da wanan maganan dake tsakani mu wai ? Wata zuciyane ta bashi shawaran ya min wayau kawai don yadda na rikece din nan daga jin mommy tazo zai iya sa komai ya faru idan ya biye min. Kawar da zancen yayi da fadin zuwa nayi ki ban shawara yaya zan yi da Nafisa don batai farin ciki da zuwan nasu ba yanzu haka. Da sauri na dago kai na kalle shi da idona da suka sauya kala nace baka fada mata zancen zuwan su bane dama , ? Kai ya girgiza min yace ban fada mata zasu zo ba tunda ba itace ta aje ni ba yan uwan ta dake zuwa ai ba fada min take yi ba itama. Kada kaga laifinta a yanzu don kai kai sake har haka ya kasance tun farko saboda tsoron ta da kake nuna kanayi da farko. Ba tsoran ta nake yi ba deeda kaunane kawai na tsakanin miji da mata wanda ita ta dauka tsoron tane yasa nake mata hakan. Sai yanzun kasan da wanan yana iya faruwa ka manta a lokacin da take saka abu kana mata shi koda kuwa baka son abin ? Ya gyara zama yana fadin shine babban kuskure dana tabka a farko wanda nake nadaman yi shi a yanzu haka. Duk abinda zakayi ko zatayi kada ka bari rainin matarka yakai ga iyayyen ka don ko zaka iya canza mata amma ba zamu iya canza iyayye ba. Wai ke wake koya maki wanan hikimar haka nr ya tambaya cikin son in bashi amsa nace baka son maganan ke nan. Yace No idan ban so ai ba zan fada maki zuciyana na ba a yanzu don da zuwan su abinda tayi masu yaci min rai sosai ba zan boye maki ba don yanzu ke ce abokiyar shawarata shiyasa nazo maki da zancen. Yaya zanyi khadija ina son in fita daga cikin dana shiga a bayane gida na yanzu bana son su mommy su fahinci sakaci na a gida na. Nace na yaushe kuma saidai kada a kara muma makwabta ku mun sanni balle su mommy dake gidan tare ku. Ina son mata na khadija shiyasa har haka ya faru da ni kallon shi nake cikin mamakin kalamin shi na wai yana son matan shi da yace. Shin shi wani iriin mutum ne wai nace nafisa dai kake so amma baka son fati kowa ma yasan da hakan ? Haka kuke tunane ya fadi cikin zafin zuciya amma ita ai tasan ina sonta halin ta ne kawai baizo daya da nawa ba shine matsalan mu. Kalon shi nake sororo kamar na samu tv da alama yarasa yaya zaiyi da damywar shi ne ya tsinci kanshi cikin fada min sirin zuciyar a matsayi shi na mutum mai shekaru kamar shi. Tausayi ya bani don na fuskanci bayan Yusuf da suke tare baida wani wanda zai fada ma zuciyan shi ya fahince shi shiyasa yazo gare ni. Nace wallahi rayuwan ka na cikin hadari ya kamata ka koma ga Allah kayi abinda Allah yace shine kawai mafita a gare ka. Lokaci ya duba yace zai tafi lokacin sallah ya gabato zai dawo gobe tunda ba school mu karasa tataunawa mukai sallama ya tafi ya barni cike da tausayi shi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Tunda ya je office ya kasa aiwata komai a office din ga Yusuf bai shigo ba har lokacin ranshi ke kara baci idan ya tuna da kalaman nan daya dana fada shi yafi bata mashi rai ko yaushe. Shigowan Yusuf office din tun daga nesa ya karanta zuciyar abokin nashi ya karaso gaban tebur din shi yana fadin wani abu ya faru ne na ganka haka. Tsuki yaja tare da juya kujeran da yake zaune sama yace may ye ma bai faru ba Yusuf wai kasan matar nan bata gida tun ranan da muka tafi kaduna. Ba ita ta dawo ba sai karfe biyu da wani abu ta shigo gida jiya da sauri Yusuf yace ina taje haka ko da sanin ka ta tafi yace idan na sani abin zai damay ni haka ne ? Kai wai may yasa wasu matan samun wuri ke sa su wuce limit din su ne na mata akan may mace mai ciki zatayi irin wanan tafiya haka ba tare da sanin mijin ta ba. Bata tsoron wani abu yaje ya samay ta a can yace ma Yusuf ni ba wanan ne damuwa na ba damuwa na shine ina taje ? Jiya jiyan nan Khadija taban wani mugun labari wai buzaye sukan baro mazan su na gado su shigo nan suyi auren bugi don kudi ni wanan abin shi abinda ya tsaya min a rai na. Ita Khadija ta fada ma hakana sosai kuwa jiya muna tare da ita tana zayano min halin buzaye sai naga babu abinda ta rage daga cikin halin Nafisa har ma da wasu da ban sani ba takara min haske akai. Lalai Khadija jarumar gaske ce tunda har ta tsaya ta iya fahintar dakai wanan abin yace ka san hauka irin nata ita bata dauka maganan ai zaiyi tasiri a raina ba haka. Yanzu fa har na fara zargin yawan tafiyan Nafisa kasan su akai akai da takeyi tunda gashi har yakai ta fara satan tafiya haka. Da fa shi yayi yace kada ka zargeta da wanan don ta fadi haka ba lallai ne haka ya zamo gaskiya ba akan Nafisa din sai dai idan wasu sun su suna yin hakan bance a a ba don son kudin su yayi yawa. Kai ina bazan yar da ba Yusuf ko na yarda da komai ba zan yarda da wanan gantalin da Nafisa ta dauko yi ba dole ne in dauki mataki a kai. Tunda ta fara haka maganin abin kawai ya kamata kayi don tana ganin ita kadai ke gare ka yasa take abinda taga dama a gidan. Yanzu zabi biyu shine nake ganin mafita a gare ka na farko walau Fati ta dawo ko nabiyu ka kara aure don ganin da takeyi ita kadai ce yasa take wa yan nan abubuwa haka. Ido ta kura wa Yusuf dake magana sai da yayi shiru yace Fati ita ta kasa zama saboda rashin hakkurin ta. Kai ya girgiza mashi yace ka daina fadin Fati bata da hakkuri halin Nafisa dai ya kori Fati gidan ka wanda a lokacin baka ganin haka kai. Zaka iya bata wani daman a yanzu ko abin zai gyaru a tsakanin ku amma fa sai ka jajirce wa hakan kafin komai ya zama dai dai don Nafisa shuumace ta kwarai. Ba zata taba bari kuyi zaman lafiya da Fati kawai a gidan ka dole sai da wace mace a tsakani mai kwato mata nata hakkin idan kun cuta mata. Bai iya magana ba sai jawo file din gaban shi yayi ya fara aiki ba tare da ya san abinda yake yi ba. Fita yayi ya bar mashi office don yasan halin tunda yayi haka ba amsan maganan shi zai samu ba a lokacin. Ya kai wani lokaci yana aikin da zuciyar shi raki sakewa don haka ya rufe files din ya mike tare da nufar hanyar fita office din. Gida ya nufa kai tsaye lokacin sha biyu da wani abu na rana tun daga kofa yake jin tashin sautin wakan yan yaren su cikin harshen buzaci ya karade gidan. Bai ko kali gefen da suke zaune ba ya hau sama ya shige dakin shi tare da rufo kofan da karfi zuwa yanzu sun fara isan shi a gida. Mutane haka ba kimsi ko kadan sai bakin ci da ihu yau ma don samun wuri kidan suka sake mai haka a gida anya ma suna wani cikaken ibada kuwa tunanen da yake kenan Nafisa ta turo kofan dakin ta shigo. Sau daya ya kalle ta ya kawar da kanshi gare ta ta karaso kusa dashi da shi ra tsaya cikin murya da maida hankali gare shi tace lafiya yau kadawo a wanan lokacin haka ? Kallon ta yayi ya kawar da kan shi gefe daya ta sake cewa magana fa nake maka wai may ke damun ka ne haka ? Ya dago ido ya sake kallon ta da idanun shi da sukayi jawur yace ban son damuwa a wanan lokacin tace haba mai gida ai wanda duk ya ganka a wanan lokacin yasan akwai damuwa a tare da kai. Matsalar ki ce ta isheni Nafisa in ma ina da damuwa bai wuce halin ki ba tace halina na kamar yaya wani abin nayi maka ko may ? Au baki ma san abin da kikai min ba ke nan kike nufi tace don kawai na fita na dade shine zai zama matsala haka ? Fita nayi kuma gani na dawo lafiya sai may da zaka dauki wanan a babban matsala kuma ko nace ka barni in fita na san ba barina zakayi ba inje inyi lalurar gabana. Ina kika je har kwana biyu baki gidan nan tayi shiru tana tunanen karyan da zata yi mashi ya yarda da ita a lokacin. Ya sake tambayan ta sai tace na tafi bukin kawata ce da ta haihu a jos don ko na fada ma ba zaka yarda in tafi ba. Duban ta yayi cike da zargin ta sannan yace wata kawa kike da ita haka a jos da ban santa ba har zaki iya zuwa ki kwana biyu a bukin ta ? Ta dan zaro idanu tace dole ne sai ka san kawaye na duka wai yace da kyau Nafisa wanan halin da kika dauko a yanzu sam ba zan dauke su ba . Tunda har kika iya tafiya na kwanaki don kawai bukin wata kawa taki buki nawa akayi a gidan mu sau nawa kika taba zuwa? Sam yanzu zuciya ta ta soma zargin ki da aikata wani abu akaina da ba daidai ba sakamakin hurda da matan barikin da kike a yanzu. Zargina ka fara ne Samad akan may ba zan rage ki ba halayen ki gaba daya yanzu sun gundureni baki zama gida ba yar aiki ba ba wata yar kasuwa ba amma ke kenan kulun yawo fita. Gaba daya kin shiga rayuwana kin hana min farin ciki kin hana mata na ta zauna dakinta ke kuma ba kula nake samu a gurin ki ba. Au matar ka kace kace dama matar ka kake son ta dawo kawai kake wanan kamay kamay haka idan zata dawo zaki hana ne ko may ? , Ta dube shi a hasale to ta dawo din mu gani mana sai may yadda ta dawo haka zata koma da kafan ta. Yace haka kika ce tace na fada sai may ? Baya ya bata batare da ya kara juyawa kanta ba ta tsaya tana ta jidali wai ai dama ta sani zuwa kadunan da yakeyi yanzu saboda fati yake zuwa da yaran shi. Mamaki yayi sosai da ta iya karfin halin furta hakan lallai yasan ya cuci Fati da yawa ita da tazo daga baya ta iya fadan haka ? Ina ga Fatin da zaman gidan ya gagare ta da yaranta dole suka bar mata gidan har diyan shi ita ko tana zaune yan uwan ta da yarta a cikin salama. Lalai ya tabka babban kuskure a rayuwan shi dole kowa nashi ya tsane shi yanzu don sam shi bai taba hango wanan abin ba sai yanzu da taimakon Yusuf da khadija suka ganar dashi gaskiyar hakan. Ido ya rufe kamar yana barci don bai son hayaniya ko kadan gashi ya jawowa kanshi yar hayaniya a rayuwan shi bai taba nadamar auren nafisa ba sai wanan karo. Mikewa yayi ya shiga ban daki ya dauro alwala yazo ya tayar da sallah azahar ya gama ya dade zaune a gurin anan wayan Yusuf ya shigo mai yana tambayan shi yana ina ne ? Yace gida sai ya kashe wayan yasan damuwa ce taimai yawa yasa ya koma gida yasan ko a gidan ba wani sauki zai samu ba, don ko yasan Nafisa ba zata kyale shi ba. Sai dayayi sallah karfe hudu ya fito daga gidan kai tsaye ya yanke shawaran zuwa guri na don irin shammatan junan da mukeyi yana sashi nishadi a ranshi haka yasa ya nufi inda nake. Bai faye son zuwa wurina tare da Yusuf ba yanzu don idan sunje tare hiran kan koma tsakani na da Yusuf ne don bai iya sake jiki yayi komai a gaban Yusuf di yanda ya samu dama a zuwan karshe. Ya iso bakin hostel din sai da ya kare ma gurin kallon yadda mutane suke ta faman shige da fice ya daga waya ya kirani kamar kullun gani kofan hostel din ku yace ya kashe wayan. Muna zaune girki na gama muna muna ci kiran shi ya shigo min kalon maryam nayi nace wai may wanan mutumin ke nufi ne maryam jiya fa ce min yayi zai yi tafiya ba zamu sake haduwa sai ya dawo yanzun kuma may zo nema nan ? Dariya tayi tace ke mana don Allah tashi kije kada ki bata mai lokaci dan hararan ta nayi nace na kirashi ne ? Sai da na tsaya shirya nasa wasu material a jikina din kin buje da riga akai min wani zuwa kaduna da nayi maron colour dinkin yadan matse min jiki kadan don dan jikin dana kara yanzu. Sun kama min jiki tam sai kitson da mukayi satin nan na ghana wiving ya kara fito min da fuskana shar ga matsiyacin kamshin dake tashi a jikina wanda ke tafiya da imanin wanda ya shaka. Tun daga nisa ya zuba min ido yana karewa shiga na kallo har na karaso inda yake kofan motar ya bude min wai nashiga. Naki nace cikin girgiza mashi kaina yace common shigo don Allah mu tafi rakiya zaki min wani guri da sauri nace a hakan zan tafi wani gu. Ko banza kuma ba zan shiga motar ka ba again agogon hannun shi ya duba yace cikin dakewa kina bata min lokaci ki shiga mutafi. Tunda muka fara tafiya ba wanda yai magana a motar sai shi dake tuki a hankali cikin wani irin yana yi yana yi yana wani furzo iska daga bskin shi lokaci lokaci. Sai can ya juyo inda nake yace zakici wani abune kaina yana a waya na da sauri na dago kai nace wani sai kuma ja girgiza mashi kai nace ni a koshe nake. Ok rakani inci wani abu tun safe banci abinci ba da sauri na zaro ido nace azumi kayi ne ? Dashi nayi ma da zai fi min sauki yace ba tare da ya dube ni ba na mayar da kaina ga titi ina kallo sai kuma can kamar an tsunkule nace matar ka tayi tafiya ne ? Bai bani amsa ba sai karya kan motar shi da yayi zuwa wani restaurant din abinci mai kyau gurin da daukan ido ya parke a wurin . Mun shiga naga tsarin wurin yana da kyau sosai da alama yasan wurin da kyau don wani ke bebben wuri naga yana nufa a cikin wurin. Min zauna masu aiki gurin suka zo suna tambayan shi mai za a kawo muna ne yace ferfesu kawai zai sha bayan an mika mai dan takarda ya duba. Koda aka kawo mai bai wani sha da yawa ba naka ya aje cibin yana goge bakin shi tare da fadin tashi muje kawai nikan mike wa nayi nabi bayan shi. Sai da ya biya su kudin su muka fice muka bar gurin ina mamaki a raina nace yaya mutum kamar shi baici komai ba sai a wurin cin abinci zaici kuma bai tsaya yaci wani abin kirki ba. Kasa hakkuri nayi nace amma wanan ba girman ka bane cin abinci a waje alhali kana da iya li kuma a gari. Kamar bai jini ba yana tukin shi sai dai ban san ida muka nufa ba can naji yace dani yaya kike son inyi khadija in banci abinci a waje ba ? Kamar yaya kuma kana da mata a gida zaka ce haka yaya Abdul yace sunana Abdulsamad ko ke ma zaki bata min suna ne ? Yi hakkuri bani na kashe karen ba ratayan buzu ba zai zama nawa ba in bai zama naki ba wace ki dauki karen ? Naci yau kana da magana ke nan yace da yawa khadija iam not in good mood at all. Ayyah sorry Allah ya sauwa koma maye yayi maka mafita a kan shi yace amin na gode da adduan ki gare ni yaci gaba da tuki. Matsala a gun aiki ne ya taso maka yace matsala a gida na yake subbahanallahi nace dashi tare da dan kallon fuskan shi. Yace khadija dole in ci abinci a waje ko in zauna da yunwa ko zaki taimaka ki dinga bani abinci in dinga zuwa wurin ki ina ci idan na taso office. Kai don Allah ka daina zolaya abincin yan makaranta ne zakaci wanan ai sai mu da yazama muna dole muci shi. Badai ke kina ci ba nace sosai kuwa yace to ni mai zai hana inci tunda ke kika iyaci sai dai idan rowa zaki min kuma beside ke kika ce na daina cin abincin waje. Nace matar da ran ta da lafiyan ta zaka wai ni na dinga dafa ma abinci kamar wata wacce ka aje da zaman banza. Bai kara magana ba sai horn da yayi a bakin wani gida aka bude mai muka shiga dayan motar da suke zuwa wuri na da farko ne na gani a gidan. Maigidan na ciki ya tambayi mai gadi ya na gaishe shi bai amsa ba ya jefa mai tambayan shi sai maigadin yace yana nan bai dade da shigowa gidan ba. Fita yayi daga motan ya zagayo ya bude bangare da nake zaune jin ya tambayi mai gidan yasa banji wani tsoron shiga gidan ba. Sanyin A C ne ya tari fuskana da kamshin air freshner da falon ya dauka falon ya tsaru komai akwai a ciki ga wasu manyan kujeru da aka kawata falon dasu. Yana waya koda muke shiga gidan yana fadin kafito gamu a falon gidan ka yace a wayan baifi second ba naji ana bude kofan daga cikin gidan sai ganin Yusuf ya fito yana saye da kayan shan iska irin ta maza wando dogo tare da yar riga armless a jikin shi. Yana gani na ya bude baki da mamaki yace kace yau ina da babban bakuwa a gidana ina kafito da yar mama da yamman nan haka ? Ya nuna mun kujera da hannu yace bissimillah zauna mana khadija bamu hadu ba sai yau nace ina wuni ya amsa da lafiya kalau ya kike ? Ina nan lafiya yace Alhamdullahi yau sai gaki a gida na kwatsam na gan ki ba tsammani nace wallahi ga wanda ya dauko ni nan bai fada min ida zamu zo ba yace dai wani guri zan raka shi. Yayi maki wayan manya kenan don ya baki mamaki dan hararan gefen da yake nayi mikewa Yusuf yayi yana fadin barin kawo maku abinsha sai dai kiyi hakkuri kin san gidan gwauro kika zo. Da sauri na dago kai ina kallon shi da mamaki nace baka da aure ne dama yace eh baki sani bane yar mama ? Ashe mutumin bai fada maki komai game da ni ba yace ma Yusuf din an fada ma kowa irin ka ne mai zuba a lokaci guda. Yusuf yana dariya ya wuce inda fridge din shi yake ya dauko drink a ciki tare da kofuna ya kawo gaban mu ya aje nidai ido nake binsu dashi kawai. Ya aje tare da zama yana fadin bissimillah kusha lemon shi yasha nin ban sha ba gani nake kamar plain ne suke shirya min in fada ciki. Yayi yayi dani don insha nace wallahi na gode mai zai sa ka damu haka idan bata sha ba yace mai kasan bakuwa tace ita dole in damu idan tazo gida na bataci wani abu ba. Daukan cup nayi na tsiyayya kadan na dan kurba na aje cup din ina fadin na gode shima tunda ya kurba sau biyu ya koma ya jingina da kujera tare da dafe kanshi da hannun shi . Yaya dai Abdulsamad lafiya ko dan tsuki yaja tare da kara dafe kan nashi fuskan shi ya nuna alamun bacin rai da damuwa. Juyawa yayi guri na yana fadin may ke faruwa ne khadija nace nima haka naganshi wallahi ko maganan da nayi mai ne yasa shi bacin rai ban sani ba ? Ni kuma gaskiya na fada mai ba girman shi bane cin abinci a waje ban san ranshi zai baci da kalamina ba na fada mai haka. Dariya ya dan yi tare da fadin see you akan dan wanan maganan zan bata raina ai gaskiya kika fada bai dace ba nima na san da hakan. Watau khadija mutumin naki yana da matsala ne a gidan shi wallahi wana abin ya dade yana damun mu muma. Ace mutum kamar wanan ba abinda ya nema ya rasa a duniya amma cin abincin gidan shi ya gagare shi sai na waje ? Shiru nayi ina kallon shi yace ya zama dole mu samu mafita akan wanan matsala kada abin yazo yai yawa na yaushe kuma ? Ko sau daya aka ganka a waje kana magidanci kana cin abincin sayarwa ai girma ya fadi ko a wurin mutane sai dai a gyara don gaba. Yarinya kamar tsuhuwa wurin iya tsara magana haka ashe shiya take karatun lauya ya fada a ranshi. Khadija ni na rasa samun mafita ka wanan matsalar wallahi don ko nafisa ba gyarawa zatayi ba tunda in ita batayi ba bata bari kuma ya dauko yar aiki irin namu na nan wace ta iya saidai yan uwan ta zasuyi. Wanan kuma shi ya daukar mata don shi yaga zai iya zama a haka don may ba zai dawo da matar shi hala tsoron ta yake yi ? Sai lokacin ya cire hannun shi da ke saman kanshi yace tsoro tsoron wa nace ka alamu nan sun nuna kuwa buzuwa ta shiga gaban ka. Ke fa baki da kunya din kikan wuce limit din ki nayi saurin fadin wurin fadin gaskiya ba haka nan Ya Amina na ke fada min wai banda tsoron fadin magana ga kowa. Ni kuma naga idan gaskiya tazo a fadeta komai dacin ta kuwa dayake baki da kunya ba zaki iya fadin maganan da wani bai iya fadi ai . Ciki ciki nace a nan zaka zare idanu agida ko a zare maka idanu matsorancin banza kawai. Ban yi aune ba na gan shi a gaba na waye matsoraci yace cikin zare min idanu Yusuf nace ni gaskiya na fada ai Yusuf ne yace daga fadin gaskiya sai leifi ? Laifin ka ne mana kaima ka sani ai in ba tsoro ba ka dauki mataki mana a kan haka mugani nace aishi na gani walla, , , Hannu shi yake ya kamo bakina yana fafin wanan wanan baki sai nayi maganin shi wataran zai shiga hankalin shi. Don Allah ka bari bana son namiji yana taba min jiki wallahi kin dauke ni dan iska ke nan ashe nace bai da kyau yin haka ka sani. Yusuf yana dariya yace ina zuwa ya barmu a gurin zama yayi a kusa dani yana fadin bari ma yau in nuna maki dan iskan nake. Tsoro ne ya kamani yadda ya zauna a kusa dani din nace may ye haka malam ? Malama iskancin nake son nuna maki kalan tawa ki gani ya rankwafo inda fuskana yake har muna iya jin hucin numfashin juna a lokacin. Cikin sanyi murya nace ka dai san hakan bai dace ba a addinance ai kin san ban san addini ba ni yace wanan ba gaskiya bane don gidan ku kaf hazifai ne kuna karatun addini tun kuna kanana . Sai naga ya maida kanshi saman kujera yana zaune kamar yadda yake bai daga kusa dani ba yace khadija ina cikin matsala wallahi ina son in gyagyara wasu abubuwan da suka baci min a yanzu. But i don't know how to make things easy ? Tausayi ya bani nace ka yawai ta addua da sadaka ga dukan al,umurorin ka sai kaga Allah ya kawo maka mafita a ciki. Sai ya mike daga hannun kujeran yana fadi n muje in mayar dake yamma ya fara yanzu saurin mike wa nayi ya kira yusuf a waya yana fadin mun tafi. Yafito da sauri tare da fadin har kun gama hiran ta masoyana zaku tafi kai haba yayana firan masoya kuma a haka ? Har ya fara tafiya shi muka mara mai baya yusuf ya bani hakkuri akan bai bani komai ba gashi na kawo mai ziyara. Ba koma nace muka kama hanya na tsaye sai da yaga wucewar mune ya sauke murmushi tare da fadin ikon Allah komai yana da sanadin shi. Wanan karamar yarinya kuma Allah ya jefo a rayuwan Abdulsamad mutumin da magana da mace a wurin shi aiki ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Gidan ya nufa kai tsaye tare da sayayyan da yayiwa bakin shi na abubuwan bukatun su ya nufi part din fati dashi. Babu kowa a falon sai yake mamaki yau ina mutanen gidan su shiga haka duk da basu ciki hakan bai hana falon nashi jin tashin yanayin da jikin su ke dashi ba a falon. Hakana har ya isa gurin su mommy zuciyar shi cike da tambaya da tunane ya samay su a zaune suna hira yarinyar da suka zo da ita tana cin abinci. Sai da ya aje kayan a gaban mommy ya zauna lokacin ya fara gaida su suna kara mashi yaya sula samay su yace mummy lafiya sai hamdala. Nan dai ya zauna dasu suka dan taba hira har wani lokaci sai ga Nafisa ta biyu shi har dakin dags kofa ta tsaya ta kira sunan shi. Bayan ya amsa kamar ba zai tashi ba sai kuma ya mike ya tafi sude su mommy kala basu ce ba suna kallon ikon Allah kawai. Ya fito ya samay ta zaune falo tana ganin shi ta mike da kyat ta fara fadin muje sama ina da magana dakai ne ta juya ta fara tafiya yana biye da ita a bayan shi. Ko da suka hau sama bai tsaya bin ta nata ba don har ta juyo da nufin tayi mai abinda ta kulla a ranta sai hango shi tayi yana bude kofan dakin shi kai tsaye. Ido ta bishi dashi tana fadin samad maganar nakira ka muyi zaka shige kuma yace baki san dakina bane ko a kan hanya kike son maganan da ni ? Sai lokacin ta dan juya ta dubu wurin da suke tsaye din sai kuma tayi shiru don ita bata ga komai a nan ba don sunyi magana ai gidan su ne. Dakin ta samay shi tsaye yana rage kaya a jikin shi ta fado dakin babu ko sallama ya dan juyo ta kalle ta ya kawar da kanshi gefe yaci gaba da abinda yake yi. Bayan shi ta tsaya tana kama baya tare da fadin Samad wai may wanan mutane suka zo yi ne a gidan nan ? Yaushe zasu koma don ban son sa ido da takura a gida na sai da ya gama cire kayan ya rage daga shi sai boxes a jikin shi yace cikin duban ta ina fatan wa yan nan mutanen da nace su bar min gida na yau sun bari ? Tsaye tayi sororo tans kallon shi ta shige ban daki ya barta a wuri tsaye tana mamakin yau wai itace samad ke ba amsa haka daidai da nata tambayan. Da dane da yanzu ya fara matairaice mata yana bata hakkuri akan zuwan su mommy din itako tana cika tana batsewa tare da kafa mashi sharudda dole ya bi ya juye mata makudden kudi yana lalashin ta. Yanzu ko da yake kokarin kwato kanshi daga sherin ta sai take ganin wasu ne suke kokarin bata mata aikin ta ta baya. Tunda ya shiga bayin taja kafanta ta zuwa bakin gadon dakin ta zauna tare da tin tagumi don ta fahinci ba maganar da zatai sanyi bane dashi sai da yanzu cikas din ta shine cikin da ke jikin ta don bai bari tayi yadda take so sam. Da mamaki samun ta wurin yake kallon ta da ya fito daga ban dakin don yayi zaton tuni ta tafi dakin ta ta kwanta sai ganin ta yayi zaune cikin damuwa. Samad wai may kake nufi danine yanzu da ke tsiro da wasu halaiya na daban da ban san ka da su ba a da don may zakace sai na sallami yan uwa na gidan nan ? Yace saboda ba gidan yar uwasu bace su bari idan kin kaiga naki gidan sai su kwaso gaba dayan su su dawo inda kike ba dai nan gida na ba. Da bakin ka kake fada min haka Samad yaushe ka tashi ga samad din da na sani mai so na da tausayina da son duk wani abinda nake so a rayuwa na. Da ke nan Nafisa a lokacin da ban fahinci koke wacece ba amma yanzu da na fahinta yasa kike ganin sauyi daga gare ni haka . Ban taba yarda da halin ki ba sai yau Nafisa da har mahaifa na zasu zo gida na ki tsare ni kina tambaya na wai yaushe ne zasu koma ? Alhalin ke ga yan uwan ki nan a gidan sun hana ni shakat dani da gida na ba daman in huta in samu natsuwa a ciki ga dan banzan kazanta da kuka bata min gida dashi ya koma wani iri. Samad mune kazamai dani da yan uwana kake nufi ko may yanzu ne kasan da kazantan mu din ko may yace da na dauka idan idon ki ya bude zaki daina Nafisa ashe abin ba haka yake ba a gun ki. Komai ai zaka iya fada a kaina tunda kaga yanzu banda moriya a gareka yadda kake so a da, da kake yawan naci a kaina da banda komai. Wanan ne tunanen ki ashe kike min yadda kikaga dama bakin ce in dauki matakin da zan dauka ki gani ba ranan to matakin ne yanzu na fara daukar wa kaina. Su mommy kuma da kika gani nan sun zo gidan nan ke nan harsai kin haihu kinyi arbain zasu koma gida. Ido ta zaro waje tace ina zasu zauna din yace a inda kika gan su and bari kiji idan naji wani rashin mutunci ya fito daga gare ki zan baki mamaki sosai a gidan nan. Mamaki ne ko rudewa ya kamata a wanan daren na Abdulsamad wanda take gani karfin haline irin nashi daya iya fada mata wanan magana haka babu ko dar a idon shi. Bai kara kulata ba ya shiga gyaran jikin shi ya barta zaune a gurin cike da mamakin shi fita yayi ya duba ko an rufe gidan ya samu ko ba a rufe ba shi da kansa yaja kofa ya rufe yasa mashi key. Washegari mommy da wanan yarinyar da suka zo mai suna Aisha bayan sunyi sallah basu kara kwantawa ba suka fito falon gidan suka gyara tas ta saka turaren wuta dana tsunke a ko ina na gidan. Take gidan ya dauki kamshi da sanyin Ac kitchen suka koma sai da gaban mommy ya fadi ganin yadda kitchen din yake kamar ba mata ke amfani dashi ba. Nan kuma suka shiga aiki a kitchen din gyara can gyara nan take kitchen din ya koma na macen da tasan kan ta girki suka dora na abinda zasu ci a gidan. Sai da suka kusa gamawa ne matan dake gidan jin kamshin girki yasa suka fara fitowa daga dakunan kwanan su daya bayan daya. Suna lekawa kitchen din suna masu ina kwana don tsaron mutuncin su ga maigidan. Bayan sun gama girki mommy ta zuba masu nasu taba Aisha nasu ta shige masu dashi ciki tabar saura da mutanen dake gidan zasu ci. Yanyala ce ta shiga dakin Nafisa take kwarmata mata abinda ke faruwa a gidan da fushi Nafisa ta sauko kasa zuwa kitchen din don taga abinda ke wakana mata a gida. Komai na gidan neat yake yau ya samu gyaran da ya dace daga bakin su ta shiga kitchen din taga yadda suka gyara komai suka jera shi a inda ya dace. Fita tayi zuwa sama ta samu Abdulsamad ya gama shirin fita tsab ta fado dakin da fushi tana fadin ban san may kuke nufi ba kaida wa yanda kake fadi wai iyayyen ka ne ? Ya juyo yana fafin kamar ya fa tace don may zasu zo min gida suna min abinda suka ga dama a ciki suna matsayin baki a gare ni. May sukai maki ya tambaya cikin bata lokacin shi yana sauraren amsa daga bakin ta tace a hasale yanzu ya dace ace sun shiga kitchen sunyi abinda suke so haka ? Sai da ya dubeta dakyau yace kada ki manta gidan dan su suka zo suna da ikon yin komai da suke so a gidan nan. Dansu ko dan ta da sauri ya kalleta yace may kike nufi da wanan maganan naki tace dashi gani nayi itama arziki tazo ci kawai a gidan nan do ba itace ta haife ka ba. Au dama wanan ne tunanen ki ke nan dama raba daya biyu a gida to bari kiji mommy tankar hajiya mu take gare ni don matar mahaifina ne ita ma kamar hajiyan mu don haka nake daukan su daya. Yanzu ke baki jin kunya baki tashi kin tare su da abin karyawa ba sun tashi sunyiwa kansu har kike fadan akan haka don baki da kunya ? Tace ba zan yarda da wanan wuce wurin ba irin nata dama na dade da sanin halin ta tun shigowa na cikin ku do haka kayi saurin taka mata burki a hakan. You're very stupid ya fada da karfi sai data razana yace kada ki fara kice zaki saka masu ido a gidan nan ko bayan fitana ne don zan saba maki sosai kuwa. Fita yayi daga dakin ya barta cike da mamaki tana ganin wankin hula zai kai ta dare wai itace samad din ta keyi wa abubuwa haka yanzu. Lalai duniya na shirin juya mata baya idan batayi da gaske ba tin yanzu dakin ta ta koma ta jawo wayan ta cikin tashin hankali take fada wa madam abinda ke faru da ita. Sai da ta gama sauraron ta tace Nafisa sai kin hada da hakkuri fa yanzu don ni a gani na akwai ida aiki ki ya samu matsala ko kuma don cikin dake jikin ki ne asiri ya daina kama mijin ki yanzu. Ina cikin wani hali walahi haka na nufin yan uwan samad zasu dawo gare shi suyi yadda suke so gidan nan ke nan wanda ba zan taba yarda ba sai dai duk abinda zai faru sai dai ta faru. Madam tace Nafisa kibi sannu fa ba kullun ne ya zama dole mutum yayi nasara ga abinda yake so ba kowa kika gani sai yanayi yana hadawa da hakkuri da kuma kissa bawai ga magani kawai muka dogara ba. Madam ni abin ne yazo min a bazata wallahi tace yanzun dai ki kwantar da hankalin ki mubi komai a sannu. Tace na ji amma duk da haka zan nuna masu gidana suka zo ba zan bari suyi min abu gaba gadi ba haka tace kiyi a sannu dai na fada maki. Shiko yana fita tun a falo ya fara ganin sauyin da gidan nashi ya samu da zuwan su mommy din ga gida ya koma neat a lokaci daya a falo ya hango su hadiye suna kuskus a cikin yare suna ganin shi suka shiga gaida shi. Fuska a daure take amsa masu ya wuce part din su mommy din wanda anan fati da take zaune da yaran ta ganin haka yasa ya tuna da abubuwa da dama na rayuwan su a baya a gidan. Kagin zuwa yanzu da komai ya hargitse mashi haka wanda kan shi yanzu ya dorawa laifin kasancewar haka kamar yadda na fada mai. Ya samu su mommy sun yi wanka suna karyawa a cikin tsanaki ya shigo da sallama ya gaidasu tare da masu ya gajiyan hanya. Mommy tace gajiya ai yabi lafiya don mun zama yan gari yanzu ko yace mommy duk ku kukai wanan gyaran haka a gidan nan ? Tace ba dole ba babangida gida ya koma kamar ba mata a cikin sa kasan mu mun saba mijin mu baya son ganin kazanta ko kadan. Iya bawa tace mai ni ina mamaki gida da mata haka ace bai samun gyaran da yadace mace ta yi a gidan ta wanan matar taka akwai bakin son jiki ne da ita. Ciki ai bai hana ka gyara muhalin ka sai dai dama idan gyaran bai damay ka ba can amma yaushe ne mace kirki zata bar gidan ta haka ? Mommy tace ga abin kari can a kitchen idan ta fito sai ta raba maku ka karya kafin ka fita yace mommy zuba min zanci anan gurin ku don bata fito ba ko ina sauri ne. Anan ya zauna ya karya tare dasu yana mai jin dadi a ranshi yaushe rabon da ya karya a gidan shi haka cikin dadin rai. Bayan ya gama yayi masu sallama tare da tambayan ko akwai wani abinda suke bukata a gidan ya sayo masu idan ya fita. Mommy tace sai kayan kitchen din da taga sun soma lalacewa saboda rashin amfani dasu da ba a yi akai akai yanzu dole a sayo wasu yaje matar shi tai mashi lissafi don gudun su shiga mata hakkin ta. Bai koma takan Nafisa ba ya fice gidan inda ya samu Sani driver yana jiran shi a waje suka dauki hanyar zuwa office din su. Barci nake a dakina tun dawowana class wayan shi ne ya tayar dani daga barcin da nakeyi nayi mamakin kirana a wanan lokacin da yayi. Bayan na karba mun gaisa ne yake tambayana idan maryam tana nan don Allah zai aiko Sani driver shi mu taimaka mu sayo mai abin girki a gidan shi. Da sauri nace mai kaga malam bafa zaman ka nake a garin nan ba da zaka dora min nauyi irin haka a kaina ina matar ka kaje ka tura ta ta sayo ma mana . Don Allah kiyi hakkuri ku taimaka min for today only naji nace na kalli maryam dake barci nace yanzu yau friady muna hutawan mu ya dauko wahala ya dora muna kuma. Ban sake komawa barci ba motsina ya tayar da maryam nan nake fada mata abinda ya bukata da mu tace to may ye a hakan khadija ? Ai taimako ne kin san matar shi ba wani wayewan kaine da ita ba kuma kin san gata da ciki baki yanzu nace wanan ai ba excuse bane. Son dorawa mutane wahala kawai yake yi don kada a zauna lafiya muna zaune kalau zai dauko wahalan gidan shi ya dora muna. Kin san may khadija nace aa cikin kada kaina tace walahi sai nake ganin wanan Abduldin yana bukatan taimako a rayuwan shi. Bai samu macen da ta dace da irin halin shi bane har yanzu yasa komai yanzu yake bukatan taimakon ki ban san yaya zaiyi ba ranan da zaku rabu dashi tunda kince ba soyayya bane a tsakanin ku. Nace ai ke kin fi kowa sanin hakan shiya san yadda zaiyi don ni bashi ne a gabana ba karatuna ne ya damay ni inga na kammala Allah yaban sa,a in samu aiki da wuri. Duk da haka khadija akwai matsala ranan rabuwan ku kan inda ran mu zamu sha kallo nace in babu sai abaku labari ai. Tace labarin taimako ya juye ya zama soyayya haushi maganan ta yabani ban samu bata amsa ba naso ta biye min kada muje ko ina ya karata can da halin shi shiya sani. Karfe uku bayan an fito sallah jumma,a sai ga malam sani driver yazo daukan mu nan yaban kudin yace wai zamuyi waya dashi. Muna hanya ya bugo min yana fada min duk wani abinda muka sani ana amfani dashi a fannin girki har nama da kaji da sauran su mu sayo mommy ne ke bukata a gidan. Kai dama duk wanan abin ba a saya a gidan ka may kuke ci a gidan silly girl ya fada ya kashe wayan shi naja tsuki. Mun shiga kasuwa maryam tayi kaca kaca da kudin komai mun hada sai yamma lis muka baro cikin kasuwan inda ya fara sauke mu a hostel ya wuce bayan hilux din su acike muka bashi sauran kudin shi ya kai mashi canji. Wanka nayi tea kawai nasha da nai sallah muka samu wuri muka kwanta don gajiyan da muka debo a kasuwan bamai taimaka wa wani a cikin mu duk a aikin sa kai da mukayi. Barci yana batun dauka na wayan shi ya shigo min jin murya na yasa yace har kin fara barci ne ko may ? Nace ba dole ba yau an samu wahalan da ba namu ba lada ba zunubi sai tarin gajiya khadija ke wace irin yarinya ne wai da ba tsoron fadin magana a bakin ki ? Yanzu dai ba wanan ba don may kuka ba sani ragowan kudin da ya rage yakawo min kuma ya fada min komai baku sayo wa kan ku ba ku. Saboda ba hakkin mu bane yasa muka bashi yakai ma kudin ka don Allah barni na huta malam gara da kai kana da madafa. Murmushi naji yayi yace ina dashi tunda ina da matar da zan runguma inji sanyi ke ko sai dai ki kama filon ki ko ? Kaidai ka sani nace mai sai da safe yace ba zaki tsaya nayi maku godiya ba zaki kashe min waya ?nace ai ba don ka gode muna muka taimaka maka ba na kashe wayan gaba daya. A gidan shi ya iso da kayan akai ta shiga dasu ciki shi kanshi yayi mamakin yawan kayan da muka sayo din ya kira Nafisa kafin ta sauko ya kira mommy da kanshi kan tazo idan akwai abinda babu sai a sayo gobe. Nafisa na zuwa mommy tana fitowa tare dashi yake tambayan ta ta duba ta gani ranta a bace tace komai yayi sai mommy tace komai an sayo sayayya haka kamar na mace. Nafisa da ta juya zata tafine ta juyo da sauri ta kara kura ma kayan ido tana kallo kayan da bata kalla ba da farko saboda idon ta ya rufe da masifa a lokacin. Maganan mommy ne ya tsaya mata a rai da tace sayayya kamar mace tayi komai an saya yadda ya kamata ta kira hadiye da yanyala wai su kawar da kayan wurin tana daure fuska gata mai gida. A daki ta samay shi zaune lokacin muna waya tace gurin ka nazo ya aje wayan da na kashe yana kallon ta ta samu guri ta zauna da kyat. Tausayi ta yaji ya dirka mai a zuciya tace may kake nufi da baka shawarce ni ba ka sayo wanan kayan haka sai da kasayo abinka zaka kirani. Yace saboda baki damu da asaya din bane yasa na sa a sayo min tace wace yar iska ce ta sayo ma cikin kura mashi ido da son jin amsa daga gare shi. Wanan ba matsalsn ki ba ne ke dai kiji da kanki ya fada mata yana kokarin mikewa tsaye samad mai kake nufi dani ne wai ? Da akayi may kuma yanzu tace ban fa gane inda ka dosa ba gaskiya da irin wanan halin naka yace saboda baki son gaskiya ne yasa na canza nima. Kana nufi nice mai laifi yanzu aike ma kin sani idan kina son mu shirya dake to ki canzs ke ma yaushe rabon da na karya a gida na in ba yau ba da mommy tazo. Dama nasan abinda ya kawo su ke nan ai hadin fada a tsakanin mu in bashi ba may zai sa su kwaso kafan su suzo nan wai sai na haihu. Yace saboda ina dan su kuma ni na bukaci haka a gare su tunda ke baki san komai ba sai bakin yawo da lalaci kawai da kashin kudi. Nice mai kashin kudi murushi yai mata yace ko yanzu ma nasan amsan kudin ne ya kawo ki ai ba wani abu ba tunda baki damu da damuwa na ba. Kaine dai ai naga kamar kana gudana yanzu nan dai suka shirya ranan ace tsakani miji da mata sai Allah suka manta da komai a ransu. Washe gari mommy ta sake hada masu break fast mai rai da lafiya tasa Aisha ta gyara dining din aka jera kkmai a yadda ya dace ta aikawa su hadiye da nasu. Tare suka sauko suka karya a tare sai hadiyan abincin take ba kunya ko wani nauyi a tare da ita bayan sun gama ya fita zuwa wurin aiki. Sai lokacin Nafisa ta kalle gefen dakin da su mommy ke ciki ta kira hadiya ta rufe mata kofan kitchen da store din gidan gaba daya. Da rana mommy ta turo Aisha ta gyara mata kitchen din sai ta samu gurin a rufe ta koma ta fada ma mommy. Mamaki ne ya kama mommy ta kira hajiya mama tana fada mata abinda Nafisa tayi masu ita kuma mama ta kirashi inda take shiga ba nan take fita ba tace maza ya dawo dasu gida tunda yasan gidan shu ba a hannun shi yake ba ya dauke su. Hakkuri ya fara bata yace zai dauki mata hakan tace ya yake son yi idan Abban su ya samu wanan baki labarin dama abinda yake ma gudu ke nan ya hana su zuwa tu farko. Hakkuri ya dinga bata har ta saurara mai tace tana jiran taji matakin da ya dauka a gidan idan ba haka ba zata fada ma Abban su abinda ke faruwa kada yaji a gurin wasu. Yusuf yana zaune yana sauraren su yana kashe waya ya dago idon shi da suka kade sukai ja yace wai may Nafisa take nufi da nine ? Guri ta samu take wanan abin mana Yusuf ya bashi amsa yace in bashi ba rashin mutuncin nata har yakai ga su mommy kuma yanzu. Mommy ne zata rufewa dakin girki bata girka ta basu ba basu damu ba suna yi kowa kuma yaci har zata rufe kada suci su kwana da yunwa komay ? Tasan yadda Abba yake ji da iyalin shi kana zaton da ba mommy bace in anty amarya ce Abban zata kira da kan shi ta fada mai kasan ko yau ba zata kwana gidan ka ba. Wallahi idan zaka kara aure ka kara shine kawai mafita ga wanan shu,umar mace da ka dauko wai mata bazata taba ganin darajan ka ba idan ba ta bude ido tagan ka da wata mace ba a gidan. Idan tana zama ta zauna in bata zama kuma ta kara gaba dama ba akirata ba kutse ne da sa kai irin su ta kallamay kada dadin baki da komai ta aure ka. Kai yace tare da bugun tabur din gaban shi ya mike cikin fushi Yusuf yace ina zaka kuma yanzu ? Gida yace cikin wani irin murya kamar mau zazzabi shima mikewa yayi ya bishi a baya tare suka fita daga office din shiya jasu don Abdul din bai da karfin haka a yanzu. Suna tafiya yana dafe da kanshi ba tare da ya kalle shi ba Yusuf din yace ba irin ku masu sanyin hali ne ya kamata ya auri irin Nafisa ba. Sun fi daidai da irisu wa yanda zasu caja junan su a zauna lafiya amma ai dama ita haka suke so su samu wanda suke juyawa son ran su. Yanzu ai ta fara koya min iya magana ita da wanan yar matsalan khadijan din nasan idan an auna ni za a samu VP dina ya hau wallahi Yusuf damay Nafisa take son inji ne wai ? ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Yau take son ta gwada abubuwan da aikin boka dan Ondo wanda ya ja mata kunne da gujewa aikata kuskure tace zata tsare in sha Allahu. Ya shigo bai jima da dawowa ba ya fada wanka Nafisa ta shigo dakon kai tsaye tasamu yana ban dakin gurin wanka nan ta zauna a bakin gadon cike da jiran mijin nata. Ya fito daga ban dakin ta taso ta karbi duk wani abinda yake ma jikin shi tana mai gama daga goge jiki da shafan mai da saka turare da sauran su. Shidai ido kawai ya saka ma ta yaga iya gudunta don zuwa yanzu ya fara gano shirin ta sam bai yarda da wanan abinda take mashi ba . Ya gane sai tana son abu take mashi ladabin shegu a lokacin yake miji da zaran ta samu abinda take so shike nan ta koma ma halinta na I don't care da ta saba dashi. Zama yayi a bakin gado yana jiran yaji ta inda zata bullo mashi ta dan yi dariya tare da karasowa wurin shi ta zauna itama. Sai bayan ta zauna ne tace samad a ranshi yace nasan da wanan kan tace wai yaushe ne zamu tafi shopping ga ciki ya fara girma haka ? Yayi mata kyar da ido sai kuma ya sake guntun murmushi a fuskan shi yace ban san da wanan maganan ba ai. Ita ko tayine don tana ganin shi ne zai fi saka shi farin ciki har ta samu ta sake da ita ta aiwatar da nufinta gare shi sai kuma taji sabanin hakan a bakin shi. Sai ta dan tsuke fuska tare da fadin gaskiya ya kamata ace ka shirya wa tafiyan mu zuwa yanzu don kada nazo nayi nauyi da yawa kace ba zan fita ba. Abdulsamad ya tsura mata ido yana mamakin rigimar Nafisa yanzu bata aje kanta a kusa ba shi kayan bany ko a nan gida Nageria za a samau su ai. Ya cikin daure fuska kin fi kowa sani komai nake so zan iya odan shi a dan kan kanin lokaci ya iso gare ni ballanta na babu dan da aka haifa a gidan nan da na fita waje na sayo mashi kaya. Ranta ne taji ya baci don may zaya danganta sauran diyan shi da abinda ke cikin ta a yanzu da ta san tafi karfin kowa ma nashi. Shikan gado ya hau yana gyara kwanciyan shi don yasan ba tayin abinci zai samu a gurinta ba duk dako yana son saka wani a bakin shi yanzu. Nafisa kuma bataji dadin haka ba don tana gani idan ta kyale shi bazata samu yadda take son komai ya tafi ba har ya sadu da ita don ta riga ta shafa maganin da boka ya bata tayi amfani dashi. Tabo shi tayi tana kwantawa a jikin shi da sauri ya juyo gareta yana fadin barni banda lokacin aiwatar da wani abu yau a tsakanin mu. Tace aiko tunda ni ina da bukatan ka tare dani dole zaka daure ka biya min bukatana haka nan yasan ta da son ya kusance ta akai akai wanda a baya yakan biye mata. Kara kwanto mashi tayi ya kara daga ta ajikin shi karo na biyu yace ki barni please na fada maki ina bukatan kasancewa ni kadai ne duk iya nacin ta dole ta barshi tafita kamar zatayi hauka take jin kanta a lokacin. Ta jefeshi da harara ya karkace kai yana mamakin tace ba laifin ka bane tunda kai kana fita waje yanzu kana samun inda ke sauke nauyin ka acan. Sheri zaki min yau kuma Nafisa tace amma kasan baka kyauta mi ba nima idan kai min haka yau don ina bukace dakai a yanzu yace ki hakkuri nace yau ba zaki samu ba ya gyara kwanciya yana fadin hakan. A yadda ta rude sai ta bashi tausayi amma bai iya aiwatar da komai a yadda yake jin gabanshi yana faduwa mai. Jin fitan ta a fusace bayan ta gama mashi mita ta fice daga dakin ya girgiza kanshi ya gyara kwanciyan shi sai barci acikin barcin ne yayi mafalkin mara dadi da Nafisa wanda ya tayar mashi da hankali. Tunda ya falka bai koma barci ba tunanen mafalkin da yayi ne ya tsaya mashi a rai mikewa yayi ya dauro alwala ya gabatar da sallah tare da samun sauki alamura a gare shi kamar yadda mahaifan shi ke koyar dashi ko wani lokaci. Washe gari ta tashi gaban ta yana fitar da wani irin kaikayi dake damun ta sam bata kawo cewa aikin boka da ta sakane ya jawo mata hakan ba. Tunda ya watsa ruwa ya fito yana shiri zuciyar shi cike da tunanen abubuwan da suke faruwa dashi ya yanzu din. Sai da ya biya dakin ta ya dubata kamar yadda yayi mafalkin a haka ya samay ta tana ta faman da soshe soshe don kaikayin dake damun ta. Yace may ke damuwan ki haka ne kike wanan soshe soshen haka cikin bacin rai tace dama ai haka kake so dani tunda na bukace ka kashere ni. Banga dalilin da zaka daukoni karabo ni da kasata ba kazo yanzu kana nuna min gazawanka a kaina inda take shiga banan take fita baya ya ciki da irin kalaman da take fada mai. Hannu ya daga mata tare da fadin ya isheki haka na kada kine me ki fada min maganan banza an fada maki ni banda abinyi ne sai na kwanciya da mace kullun , ? Kallon shi take da mamaki don bata dauka zai fada mata wanan magana haka ba yace kinje kinyi biye biyen ki kin dauko wa kanki cuta kiike son aza min. Kuka ta saka mai tan , aza mai kururuwa bai kulata ba ya fice daga gidan kai tsaye kukan ta ne ya jawo hankalin yan uwanta gare ta suka shigo dakin. Har yaje office bai iya tsinana komai ba da yamma koda ya dawo ya samay ta a hargitse ya dawo har ya dade ta bishi dakin shi ta samu ya fito wanka yana daure da dan karamin tawul a jikin shi. Tunda ta shigo mai daki ya dago ido ya kalleta ya kawar da kan shi gefe daya yaci gaba da abinda yake yi din tazo gaban shi tace. Allah kuwa sai ka fada min abinda yasa ka tsiro yimin wullakanci haka ko dan kaga ina dauke da ciki ne a jikina yanzu yasa har kake guda na. Ya jefeta da wani muggun harara har sai da taji tsoro ta dan ja bays kadan yace look Nafisa idan dan dai kina son mu zauna lafiya dake sai kin aje kanki a matsayin da na dauko ki a gidan nan na mata. Macen kwarai itace wace ta san damuwar mijin ta da cin shi da shan shi da gyara mai makwacin sa da sauran su. Amma duk ke baki san yin wanan ba sai dai kici arziki ki wadatar da yan uwan ki ba tare dani kin dubi nawa da komai daya shafe ni ba. Don haka kodai ki gyara halin ki ko kuma in karo wata a gidan nan ku zauna tare wacce zata dinga kyautata min. Ya na kaiwa nan yaja dogon tsukiy ya dauki key din motar shi ya fice dakin ya barta tsaye tana kurma ihun bakin ciki. Wanan halin da Nafisa keyi wani lokaci kamar zautata sai daga baya kuma idan ta samu abinda take wa haukan ta dawo ta gyagije kamar ba ita ba. Iyanzu ya fahince ta idan tana bukatan abu bai mata shi ba babu sauran zaman lafiya a gidan tsakanin ta dashi shiyasa da zaran ta bijiro da bukatatun ta yake saurin biya mata akan lokacin. Wanda ita kuma take ganin aikin bokayen tane da mahaukacin son da yake mata yasa yake biya mata bukatanta a haukace kamar ba gobe. Wanda tayi believing da baka da malamai ta ne aikin su yake ci a gareshi da kuma kyau da zati wanda take gani dashi take rudan shi ba zai taba samun mace kamar ta a cikin matan hausawan Nigeria ba sai dai kalan matan mu na nan. Burin mazan Nigeria ne su malki mace mai kyau koda bata da hali na gari adai ce matar shi ta gwada wa tsara ne a gari. Bata san Nigeria akwai wanan akwai kuma la,akari da ilimi tare da wayen mace da tarbiya ga mazan da suka san kan su. Yau ma kamar jiya tashigo mai tana bukatan su kasance tare amma fir yaki amincewa ya biya mata bukatan ta kamar jiya haka ta wahala da wanan dan banzan kaikayin na gaba da tadamay ta. Yanzu kan ya gama sakankancewa a ranshi mafalkin shi gaskiya ne inda ya ganta dauke da wani mugun abu tana goga ma gabanta. Washe gari har ya shirya bata tashi ba daga barci tana ramuwar barcin da bata samu tayi ba a daren shiya tsaya ya tayar da ita cike da tsanar halin ta na rashin son yin ibada. Idonta da sauran magagin barci bai gama watsakewa ba tace har ka shirya fita ke nan yace idan ma ban fita ba wani abin zaki min ne tunda ba abin kari zaki hada min ba. Cikin bacin rai ga maganan shi tace ba muyi wanan alkawarin da kai ba na cewa nice zan dafa ma abincin da zakaci na dauko masu dafa ma kace basu iya ba don haka banda matsala ga wanan. Yace yana daukan jakar Laptop din shi tare da sabawa a kafadan shi Nafisa zakiyi nadaman wanan maganan da kike fada min don ya zama dole idan baki canza ba in dauko wace zata bani kulawan da nake so a gidana. Maganan shi Ya bata mamaki kwarai don bata zaton zai iya fadin wanan magana a gabanta ba kai tsaye sai gashi yau yana fada mata da bakin shi wai zai dauko mai kula dashi a gidan. Wai ina kudin da take narkawa malaman ta yake shiga ne haka gashi ta dalilin bin bokaye da malamai dasa gaba yanzu ta daina kai kudin da suke kaiwa gida duk wata ana amfani dashi. Ya bata mamaki kwarai ta samu ta danne zuciyar ta don ta san yanzu akwai sauyi a tare dashi ta dago ta kalleshi yana shirin fita daga dakin. Fuskan shi a daure yake har lokacin gabata ne ya kara faduwa sosai dole sai ta hada da kissa da kisisinan mata yanzu. Tace kayi hakkuri don naga yanzu magana kadan sai ka dauki zafi dani haka yace ai kece zan bawa hakkuri keda ban san na dauko ki kawai ne gidana don ki ji dadi ba. Ta sada kai kasa tace ba laifina bane ka sani don ba girki zan iya yi yadda kake so ba bai sake yin magana ba yaci gaba da shirin shi bayan ya gama ne ya dago ya kalle ta yana fadin ki tashi ki sallah don lokaci ya gama kure maki ko. Ya fice daga dakin bayan ya gama fadin haka bishin shi tayi da kallo har ya bacd ma ganin ta sai lokacin ta saukar da ajiyan zuciya. Tace lalai da sake ya zama dole ta canza halin ta idan ba haka ba wankin hula zai iya kai ta dare wanan wani irin mutum ne da magani bai saurin kamashi. Shin shi ba kamar sauran mazaje yake bane da take jin mata na hiran yadda suke samun kan maza je nasu suke juyasu ne ? Yazama dole duk wani abu da zatayi taga ta samu ya sauko kamar yadda malam yace ta bi komai a sannu kada alamarin ya juye mata gashi ko taga abubuwa na shirin juyewa da ita. Wai shin ko da gaskiya ne asiri baya kama mutum idan mace nada ciki ko ta haihu dole ne ta jirkinta har ta haihu ta bishi a yadda yake so ta nuna mashi ta kwanta yanzu. Alaadan shine idan ya fita office zai mata kira uku ko sama da haka amma sai take ganin sabanin haka yanzu tun yana mata kira daya har yakai yau ya bai kirata ba ki daya. Haka yasa ta fara zargin dama dalili yake nema da ita ai sunsha yin fiye da haka dashi amma bai sa ya daina kulata ba sai wanan kawai zai dauka da zafi haka. Har tayi wanka ta fito falo wurin yan uwanta da ta samu suna shayen shayin su bata daina tunanen halin da take ciki da mijin ta ba. Gaida ita suka farayi ciki harshen buzaci tana karba masu da kyat yanayin ta ya nuna ba ta cikin dadin rai. Yar dattijuwa daga cikin su ne tace yau ba zaki fita bake nan ta amsa tare da yamutse fuska tana fadin ba inda zanje yau suko sunfi sin tana fita a gidan don sun fi sake jiki suyi yadda ransu ke so idan bata gidan. Matar tace yanzu ya kamata ace kin fara natsuwa guri daya saboda cikin ki da ya fara girma don kina bukatan hutu. Ta dan lumshe ido tare da jan tsoki ta dafe kan ta tace wani irin hutu Yanyala, ni da abubuwa suke son rikewa a gidan nan yanzu. A lokaci daya suka zaro ido tare da mayar da hankalinsu gare ta suna sauraren ta tace ya zama dole dukkan ku ku gyara a gidan nan. Yace mun bata mashi gida bamu gyara ba ai mai girkin da na dauko ku da sunan masu aiki a gidan saboda haka nake son kowa ta dan fara aikin ta. Yanyala ta fidda idanuwa waje tana mamaki tace garin yaya har kika bari haka ya faru a tsakanin ku tace wallahi ke ma shedace ina iya kokarina don ganin haka bai faru ba amma hakan bai samu a gare ni. Yanyala tace gaskiya ya kamata ki fara tura kaya gida tun yanzu ko za a watse dai kin riga da kin debi rabin ki ko ke. Dama bazan Nigeria ai basu da tabbas ba kowane ke kamuwa yadda ake so ba don haka muke daukan su kamar wurin cin kasuwa a gare mu. Don ko da kasuwa zata watse dan koli yakasa ya kwashe rabon shi nan dai sukai ta shawaran abinda zasu yi akan sauyin da ta ke gani ga mijin nata yanzu. Idan da sabo na saba izuwa yanzu haka kawai zai zo ya dauke ni a mota sai dai mu zagaya gari ya dawo dani ya aje ya wuce makaranta. Yau ma da yai kwana biyu bai zo inda nake ba komai na tafiya a guri na normal sai dai zan iya cewa haduwa na dasu ya bude min wani sabon babi na rayuwane. Duk da nake yarinya kuma mace ban yarda na fara hurda dasu ba sai da na karanci rayuwan su nagane zama dasu ba yana nufin jefa ni a gurbataciyar rayuwa bane. Yauma ina daki kwance ni kadai ina nazarin wani littafi don sabon da nayi da yawan karatu sai dai ance sabo turken wawa ne don har na dan fara shiga damuwan rashin ji daga gare shi kwana biyu. Waya na da yai ringing na juya ina kallon mai kirana a lokacin ganin sunan shi a screen din wayan yasa na dan sake murmushi sai da naja mai aji na dauki wayan. Da sallama na fara magana ya amsa min yace kina hostel ko kina cikin makaranta ne nace ina hostel yanzu fito ina waje yace ya kashe wayan shi. Na shirya cikin wani dogon riga mai dan hannu shara shara riga yana dan matse kadan daga saman shi kasan shi a bude. Kai tsaye daga inda yake zaune a motar yana sana,an shi na hango shi cikin motar ya mayar da hankalin shi sosai ga abinda yake yi. Tun da ya dago kai ya hangoni tafe ya daina abinda yake yi ya tsura min idanuwan shi masu kashe min jiki da zuciya haka ya sake min su tankar wanda ya samu tv har na iso gare shi. Daga waje na gaida shi kamar wanda baiji ni ba yayi sai bude min motar yayi da alaman in shiga kai na daga na kalle shi carab muka hada ido dashi. Nan nace dashi karatu nake fa yallabai ka kirani yanzu yace shiga mu tafi na sani ai. Tambayan shi nayi da ina zamu tafi tare da kashe shi da idanuwana dasu ke rikitashi idan ya kalla. Sayar dake zanyi yace murmushi nayi nace ai dako kayi babban kamu yau galleliyar yarinya kamata ba karamin kudi zaka samu ba ko. Nace yanzu ya kamata ace kana wurin aiki ka ko gida kana hutawa dan murmushi ya sauke tare da fadin. Bazan iya zama gida ba ne yanzu. To ka koma office yanzu mana tunda lokacin aiki bai kare ba don nima karatu nake yi yace don Allah ki shigo mu tafi kona fito na daukeki in sa a mota. Nayi saurin nuna kaina nace ka dauke ni sai kace wata yar tsana ko matar ka can da zaka dauke ni. Don Allah shigo mu tafi kin sa mutane suna kallon mu na dan juya naga wasu yan mata dake gefen mu sun kura muna ido. Dole na bude motar na shiga ya tayar da motar muka bar gurin sai da mukai nisa ne naji yace may yasa duka mata wani lokaci halin ku daya ne wai ? Na bata fuska tare da dan kallon shi nace haba mijin buzuwa da alama yau baka cikin dadin rai kake hango matsalan gidan ka ga kowa. Kada ka danganta abinda ya hada ka da matar ka dani don bai shafeni ba ko kadan yanzu ma banga abinda nayi da zaka fadi haka ba. Yace nima ban san dalili kawai dai ina hango hakane gun ko wace mace kamar halinku duk dayane wani lokaci. Nace baka canka da kyau ba malam ai kaji ance mata suna suka tara . Ya kalle ni ya girgiza kai yace bazan iya tabbatar da haka ba sai na gwada don naga biyu halin su daya basu damu da damuwan mutum ba kansu kawai suka sani da son abinduniya. Wow i am impress dama haka ka dauki mata a ranka ashe ? Yes sai dai ban sani ba ko kamar yadda kika fada inke din ta daban ce don na dan ga alama haka. Shiru mukayi duka a motar sai can yace cikin langabar da kai please khadija kiyi hakkuri ki fahince ni don yanzu bani da zabi sai wanan tunanen. But sai dai ban san may yasa ba nake yawan son in kasance a tare dake muna irin wanan tafiya tare da shammatan junar mu. What na fada cikin mamaki da rashin fahintar maganan shi tare da fadin me ye maanar hakan a gare ka may yasa sai nice zaka ji dadin fada dani ranka yai maka dadi. Don haka kaje ka dauko ni a lokacin da nake a tsakiyan karatuna don kawai son fitina kace wai kana son muyi ta shammatan juna kana jin dadi. Murmushi yayi yana fadin bazaki gane ba ne khadija hakane kawai farin ciki na a yanzu a take na daure fuska tare da fadin maidani inda ka dauko ni don Allah. Haba mana khadija may kike fadi haka ke nan baki bukatan ganin farin ciki na ne komay yanzu fa kika gama fadin mata suna suka tara da bakin nan naki. Nace da ban dauka farin ciki kaka samu daga yin haka da nake maka ba ai na dauka bacin rai nake sakaka. Hummm yace sai ya juyo ya kalle ni yace to indai ina da wani matsayi a gare ki yanzu dai ki zauna mu tafi. Ba yadda na iya haka na koma na zauna tare da kawar da kaina gefe daya yace yanzu na fara sanin ashe suna kuka tara. Tunda gashi na roki alfarma a gurin ki kin yi min abu biyu ke nan na fahinta a gare ki yanzu zaman mu tare da ke. Nace wanan bata min lokaci na kawai kake son yi a banza bayan kasan ina da abinyi a gaba na yanzu. May yasa zan so bata maki lokacin ki haka bayan nafi kowa sanin amfanin abinda kike yi yanzu. Yanzun dai mubar wanan magana may kadauko ni yi a yanzu ne don Allah na tambaye shi tare da kura mai ido ina son jin amsa na. Wanan lokacin da wanan yanayin yafi min ko wani lokaci jin dadi a rayuwa na yanzu matukar ina tare da ke khadija. Kece mace ta farko da nafi jin natsuwa idan ina tare da ita khadija ya juyo ya kalle ni tare da fadin kin san may yasa nace haka ? Kai na girgiza mai cikin sanyin jiki alaman ban sani ba sai ya fada dai zan sani daga gare shi. Yayi murmushi ya kalleni yace kin san yadda zakisa zuciyar mutum ya sake ba tare da an rabu cikin bacin rai ba khadija. Ina jin dadin hakan da kike min ke ta daban ce da sauran matan zan iya yarda a yanzu saboda wasu dalili da na kafa akan ki. Wani dalili ne haka na tambaya da sauri tare da kallon shi yace baki taba rokona wani abuba khadija alhali nasan kina da bukatan abubuwa da dama tunda kin san ina da halin shi. Na nuna kaina nace ni in rokeka kuma akan may zan roke ka bayan nasan rabo ne idan rabona ya ratsa a kan ka zaka bani ko ban roka ba. Good girl tafiya zatai dadi a tare dake kuwa tunda kin san haka she nayi saurin fadin ashe kai marowaci ne ke nan ga mata ? Ya dan lumshe ido yace ko daya wallahi na dai fi son inyi abinda ba sai an roke ni bane sai dai ina haduwa da matan da basu da hakkuri ne khadija. Ban san lokacin da baki na ya bude ba nace kana nufin har da anty Fati haka take yaushe ma ta samu gurin roko a wurin ka kai ? Ya na tukin shi hankali kwance ya murmusa yace kin ga yanzu ma kin fada da bakin ki yaushe na kula ta balle ta samu tambaya na ? Haka kowa ke gani khadija shiyasa manya sukace tsakanin miji da mata sai Allah wanan abin na bar wa kaina sani kawai. Daga ya mayar da kanshi ga titi yana ta tuki a hankali tare da shakan isakan dake kadawa a lokacin may hade da kamshi kasa wanda ke nuna dama na son sauka a lokacin. Ba wani guri mukaje ba sai yawata garin da mukayi kawai ya dawo dani hostel ya aje ba tare da na tsaya ba na shige kai tsaye yaja motar shi ya tafi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU 1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Suna shiga gidan su Nafisa ne zaune a falo da yan uwanta sai wata bukuwa da tazo mata a lokacin wace bai san ko wacece ba. Sun fara gaida shi sai dai ita bata dago kai ta dube su ba ganin su tare da Yusuf da taki jini da tayi don a cewan ta Yusuf ne ke kulla mashi duk wani shawara a gamay da ita. Shima Yusuf din bai tsaya ta kan su ba ya wuce dakin da su mommy suka sauka dauke da ledan take away da suka sayo masu a hanya. Nafisa may ne hujjan ki na rufe kitchen da kikayi yau tace saboda gida nane yasa na rufe don ina da ikon yin hakan ko ? Idan abinci yayi saurin karewa wa zaka tambaya yadda akayi dashi ai naga da kawo abincin sai da ka kirani ai in gani ko ba haka na bane ? Nafisa lalai wuyan ki ya yi kauri a gidan nan har da zaki iya rufe ma iyayyena wuri kada su dafa abinda zasu ci ko suyi amfani dashi. Amma ba laifin ki bane laifina ne da na sakar maki wan har kike ganin kin isa kike son wuce gona da iri a gidan nan da rayuwa na. Baki dafa kin basu ba sun dafa ma kansu kuma kinyi bakin ciki da haka da suke yi ko kin mata nan din gidan dasu ne halal malal suna da iko da komai yadda suke su. Ai ban sani ba sai yanzu da ka fada a gaban kowa nasan yan uwanka sun fini muhinmanci a gare ka yace da may kike daukan kanki ne. Tace ai sai su fito mu zuba dasu a gidan bansan ka kawo su nan bane don su kara dani tsawa ya daka mata cikin kiran sunan ta da karfi. Mikewa tayi da kyat itama tana fadin ban san sun isa da kai ba sai naga muna raba kwana a gidan nan dasu. Haka kike ce tace an fada din yace bada su zan raba maki kwana ba amma ki sani zan kawo wace ta dace in raba maku kwana gidan nan wace zakuyi daidai da fitsaran ki. Su wa yan nan iyayye nane yanzu na kawo amma mai zuwa in raba maku kwana tana tafe kwanan nan. Madam ne dake zaune ta mike tana fadin Nafisa kina da hankali kuwa kin san may kike shirin aikata ma kan ki yanzu ? Ta figi jakkanta dake aje gefen kujeran da ta zauna tana fadin ni na tafi tunda baki da wayo yace bata san bata da wayo ba yanzu ne zata sani. Waya ya ciro daga aljihun shi ya fara fadin hello inspector kana jina wasu froriners nake son kazo ka kwashe a gida na yanzu don Allah. Jin haka duk suka mike tsaye don da a zaune suke gefen guda sun zuba masu ido suna sauraren su madam ce ta fara bashi hakkuri da fadin. Assha Alhaji ai a bin bai kai haka ba basai ka kira hukuma a cikin zancen iyalin ka ba anan akayi sai a sasanta shi a nan Nafisa kin yi kuskure ki bashi hakkuri ke kuma. Bani taiwa laifi ba su da ta bari da yunwa tun safe ne za ta ba hakkuri tace ni ban masu komai ba balle in basu hakkuri. Yace da kyau mommy da suke daki da Yusuf suka ji hayaniya yai yawa a gidan yasa suka fito daga dakin gaba dayan su. Sun fito daidai lokacin da take fadin batai masu laifi ba bazata basu hakkuri ba mommy tace Nafisa kinyi kuskuren ki ba mijin ki hakkuri mu namu mai sauki ne. Don shi muka zo gidan nan kuma da bakin shi yasa muzo ba wai haka kawai muka kwaso kafan mu zuwa nan ba tunda mun san baki son wani nashi ya rabe shi yasa kowa ya sallama maki shi yanzu. Shigowan inspector din da wasu polisawa uku ne ya ruda Nafisa da da ta dauki abin da burgan maza yake mata sun gaisa ya nuna su Yanyala da su hadiye yace gasu nan . Yar uwar su na aure suka zo suka tare min a gida ban san dalilin su nayin haka ba sai ku tambaye su hankalin kowa a falon ya tashi ya juya gurin su mommy ya fara basu hakkuri. Mommy tace mu bakai muna komai ba don wurin ka mukazo dama ba wurin wani ba macen police din ne ta fara ingiza keyan su hadiye gaba. Samad kayi hakkuri don Allah ba sai ka wulakanta min yan uwa ba don ni suka zo gidan nan sai ka hada dani duka kace a kwashe mu. Bissimila yace idan haka yafi maki yan uwa na daine dole na a yanzu gidan nan na kuma gwada maki haka kina iya binsu ga hanya nan a bude ya juya gurin police din yace ku tafi dasu duka. Samad ni zakai wa haka ni zaka fada a kwashe mu a tafi damu babu ko nauyin haka a bakin ka kake fada. Ke uwata ce ko may ko ajeni kika yi a gidan mara mutunci kawai ya juya zai fara tafiya da sauri tasha gaban shi tana fadin kuskure ne nasan nayi ba daidai ba don Allah kayi hakkuri. Madam tace tun farko da haka kikayi da abin baikai haka ba ya nuna su mommy yace su zaki ba hakkuri bani ba ai. Mommy kiyi hakkuri kisa baki a maganan nan don Allah mommy tace naji zan bashi hakkuri amma haka ya zama ishara a gare ki gaba. Nan Abdul din ya dage sai idan ta basu hakkuri zai jaye maganan tace cikin dukawa mommy kuyi hakkuri nayi kuskure don Allah. Iyan bawa tace amma ke kan anyi mutumiyar banza a nan yanzu baki ji kunya ba don Allah ga yan uwan ki ko ina a gidan baki bakin ciki da cin su ba sai mu da mukazo zama daku na dan lokaci. Dan mune fa mai dukiyan da kike kadagi dashi din har kike ganin kowa ba kowa bane a gurin shi sai ke da yan uwan ki keda iko komai dashi. Nan suka kaita fada mata abinda suke so a cikin nasiha tace ayi hakkuri zata gyara yusuf ne ya sallami yan sanda suka wuce. Ranan dai anyi ta ba dadi a gidan tayi nadama tayi bakin ciki abinda Abdulsamad din yayi mata a gaban kowa ya nuna bata da wani power a gare shi yanzu ga madam ma tayi fushi da ita ta tafi tana fadin ta bashe su a idon duniya. Ta kula wanan ta kwance wancan haka na ta wuni da sake sake a ranta a kan sai ta rama abinda yayi mata akan su mommy din da suka zo gidan don ganin bayan ta. Ita sam bata dauka don dan su da taimakon ta suka zo ba har yanzu don idon ta ya rufe da son bata kaunar taga wani wanda ba nata ba ya rabe shi saboda tsananin kishi da take dashi irin na buzaye. Ta kira madam ta bata hakkuri har suka shirya take anan kuma suka fara sabon shirin da zasu aiwatar a kan kowa ma daga bangaren shi. Shiko a bangare shi ranan daki ya shige bai son yawan hayaniya da kowa don haka ya ke be kan shi a daki ba abinda yake sai tunanen hanyar da zai samu mafita ga alamarin Nafisa. Saboda yasan ba canza halin ta zatayi ba kwanto kawai tayi a yanzu tana nazarin ta idan zata biyo mashi ne. Allah ya gani yana son ya kara aure kamar yadda Yusuf yasha fada mai shine kawai mafita gare shi akan Nafisa to amma wa zai aure din da zasuyi daidai da Nafisa a zauna lafiya. Khadija ina khadija karama ne sosai ga Nafisa da halinta ba zai dauko yar mutane ya jefa a matsala ba ya cuta mata don yanzu yana jin yarinyar a wani bangare na rayuwan shi . Don haka ba zai cuta mata ba ta wanan hanya na hada aure a tsakanin su wani abu yazo ya samu yar mutane a hannun shi. Ga mahaifin ta ko yaushe sukai waya yana mashi godiya akan kyautatawan da yake ba yarsu wace kamar kauna take a gareshi. To amma kuma ga shakuwan da sukayi taya zai iya rabuwa da khadija a yanzu nan tunanen irin rayuwan da suke yi da khadija din ya fado mashi a rai abinda ya sa shi dan murmushi ke nan kadan ya gyara kwaciya yana lumshe idanuwan shi. Wayan shi ne ya yi tsuwa alaman kira na shigo mai ya dan juya ya daga wayan Queen of matsala ya gani da sauri ya daga kiran nawa. Tambayan shi nayi lafiya kake kuwa yau ? May kika gani ya bani amsa dashi sai na rasa abinda zan fada mashi karya na samu kaina da yi nace kawai dai sai nake tunanen hakan . Fada min kewa na kikayi ko may kika kirani a cikin wanan daren haka baki san ina da mata bane ni Family man ne idan kika hadani fada da mata na fa ? Wayan na kashe ina ci gaba da tunanen mafalkin da nayi dashi a yanzu daga dan barci ya dauke ni sai wanan mafalkin yazo min gaba daya na saka waya na a off na gyara kwanciya cike da zullumi ina tunanen mafalkin. Can dai barci ya dauke ni na manta da zancen mafalkin koda na tashi naci gaba da alamura na shima kuma bai kira ba don haka na kara share shi. Nafisa ko hankalinta bai kwanta ba gida Niger ta kira mai mata aike a can da kukan ta wiwi matar tace may ke faruwa Nafisa ko sakin ki mijin ki yayi ? Tace bai sake ni ba serah sai dai gaba daya ya canza min yanzu nan dai ta koro mata bayanin abinda ke faruwa cikin kuka. Serah tace share hawayen ki Nafy murde dan iska zamuyi ya koma sai yadda kika ce a gidan ki bai isa ba wallahi yanzu dai ki daure kibi yan iska yan da suke so daga yau zan shiga in fita zaki gannin nan da kwana uku kedai turo min da kudi kiga aiki da cikawa. Tace serah har kin kwantar min da hankali na wallahi don yanzu ni damuwa na bai wuce cikin nan dake jikina ba don cewa ake wai idan mace nada ciki ko jinin haihuwa wai komai nata baici. Serah ta katse ta da fadin da ke nan wanan zancen yanzu may ye kudi baiyi Nafy ina nan shigowa nan da kwana uku kada kiji komai. Bayan sun gama wayan ta zauna ta zabga ta gumi ta rasa ta ina zata fara da shi zata fara ko da iyayyen ko wanan mugun abokin nasa da ta tsana. Zaman gidan yanzu haka ake yin shi ba ruwan wani da wani sai gaisuwa a tsakanin su dasu mommy kowa na harkan gaban shi. Shiko yana tsananin basu mommy girma da kulawan da ya dace a gidan wanda hakan keyi wa Nafisa ciwo matuka ta rasa yadda zatayi dasu a gidan. Kunci cikin zuciyar ta ba a maganan shi har yakai bata iya boyewa hakan yasa ma ta daina yawan saukowa kasa inda zata gan su ko wani abinda sukeyi shiko sam bai kula da halin da ta jefa kanta a ciki ba yanzu. Kamar yadda serah tayi alkawari haka ya faru tazo da kule kule da sihiri kala kala tun a ranan suka fara aiwatar da komai kamar yadda suke so ya tafi. Nafisa sai gani take har aiki ya fara ci saboda yarda da tayi da maganin don irin labarin da Serah ta bata yadda ta shiga kungurumin dajin kasan su wurin samo mata wanan asirin mai amfani da ci da sauri ga wanda akaiwa. Haka kawai yake ji kwana biyu yana jin haushin kowa a gidan inbanda Nafisa da yanzu yake jin wani irin so da kaunar ta yana shigan shi. Mommy dake da kaifin basira ta fahinci abubuwa suna sauyawa a gidan don haka ta fara tuntubar Iyan bawa akan abinda da ta fara hangowa ga dan nasu don tun zuwan Serah mommy tasha jinin jikin ta da ita don tsarin ta da zubin ta yafi kama dana yan duniya ta irin mutanen su. Batai kasa a gwiwa ba ta sanar da mahaifiyar shi hasashen ta amma tace kada ta bari kowa ya fahinci abinda ta fada mata ta dai taimaka mashi da addua. Hajiya mama tayiwa mommy godiya bayan sun gama tataunawa akan zancen sukai wa juna sallama aka aje wayan. Sosai hankalin hajiya mama ya tashi da maganan mommy haka yasa ta kira yayan ta da suke uwa daya uba daya a zaria tana neman shawaran shi. Yace ta bari zai ga wani malamin shi a nan cikin garin zaria da zancen don rayuwar Abdulsamad da wanan matar tashi yana bukatan addua sosai. Haka suka bar zancen akan zai kira ta taji duk yadda sukayi da malamin nashi idan ya dawo daga wurin shi. Ban san mun shaku da shi ba sai wanan karon ga jerabawa ya na gaba to muna ga zancen zuci dake damuna haka ya dan sani rama kadan. Karshe nabawa kaina shawaran abinda ka fisheni na watsar da komai na rugumi karatu na gadangadan ina yi tare da share zancen su gaba daya a raina. Ranan muna zaune da Maryam a dakin ta tsifar kaina na ke da ya kitso ya tsufa min zan je in wanke kai na wayana yayi tsuwa na duba Yusuf ne a kan layin. Nayi mamaki kwarai da ganin kiran shi a wanan lokacin na dauka da sallama tare da gaida shi ya amsa yana fadin kanwa ta ina kika shige haka ? Kai yaya Yusuf ina nan inda nafi karfi mana na bashi amsa yace ko dai mutumin nawa ya boye muna ke ne ban sani ba ? Wa ke nan kake magana nima na tambayeshi yace abokina mana kuma ogana a wurin aiki nace wai mijin buzuwa kake magana ? Dariya ya kyalkyale dashi yace kai khadija baki da dama wallahi har yanzu dai mijin buzuwa aiko zaku kwasa dashi idan ya jiki. Nace ina ruwa na dashi balle balle ya jini . Yace ke ko keda ruwa dashi khadija yar mama amma dai baki da kirki Abdul din ne zaki ce yau ina ruwan ki dashi da bakin ki kike fadin haka . Tsuki naja na tabe baki kamar yana gani na a lokacin nace ni na fita batun shi yanzu banda lokacin shi. Yace subbahanallahi may yai zafi haka ne a tsakanin ku kuma keda mutumin naki khadija ? Mutumi na ko naka yaya na kai nifa ko wancan lokacin da nake kula shi albarkacin ku ya samu a gare ni har na biye mashi amma ba don shi ba. Kai haba yar mama bai dace ki fadi haka ba tsakanin ki dashi yanzu ai kunyi nisa sosai bai kamata aji wanan maganan ba a bakin ki. Taimako fa kikace zakiyi sai da abu ya kusa kai karshe zaki ce ba ruwan ki dashi yanzu ai ko kece mai ruwa har da tsaki akan shi yanzu. Mu dai bar wanan zancen nace dashi da sauri yace akan may zamu bari idan na tambaye ki zaki fada min gaskiya ? Nace akan may ke nan yace akan mutumin naki mana nace idan na sani may zai sa na boye maka kuma ? Yace Yaushe rabon da yazo gurin ki ko kuyi waya dashi when last kukayi koda waya ne please kada ki boye min komai just feel free with me khadija? Dan jin nayi sai can nace gaskiya mun kwana biyu dashi don ba zan iya tuna zuwan shi gurina ba na karshe ko wayan shi a yanzu. Yace abinda nake son ji ke nan daga bakin ki sai dai zan ari bakin aboki na inci mashi albasa Abdulsamad yayi tafiya two weeks ago amma dai yanzu ya dawo. Sai dai ko a yanzu da bukata nazo maki a kan shi don gaba daya khadija ba zan boye maki ba Abdulsamad ya canza ga komai cikin yan kwana kin nan. Gashi matar shi na shirin haihuwa watan ta ya tsaya tun last month sai dai har yanzu bata haihu ba yana gida ko wani lokaci tunda ya dawo like da ita. Katse shi nayi da fadin ni may ye nawa a cikin zancen nan kuma can su karata shi da ita tunda shi ba tsayayyen namiji bane ko yaushe. Namiji ne mana khadija ai shiyasa na kiraki don ki sheda mai cikin wanan wasan da kuke yi don ya farga ga abinda yake yi din. Ni tsoro na shine kada su mommy daya dauko gidan shi su fahinci susucewar shi a kan wanan shuumar matar tashi sugane gazawan shi a gaban kowa. Shiya sani mana tunda shi ke ji a jikin shi ba wani ba yayi saurin fadin a a khadija ba haka zamu yi ba daurewa zakiyi mu fitar dashi daga wanan kangin don Allah. Ni haba yaya Yusuf ni may zan mai kuma shiya sani don Allah khadija dakata ki saurare ni don Allah nace ina jin ka ai. Zaki iya hakkuri ki daure ki kirashi a waya ki fada mai magana daya wanda zai shi ya natsu ya dawo cikin hankalin shi yanzu don ke ce kawai mafitar da nake dashi bayan Allah. Ni kuma why sai nice mafita akan haka yace saboda ban taba ganin wani ko wata dake fada mai magana yadda kike fada ba azauna lafiya kuma yai amfani da abin da kika da mai a zauna lafiya. Dan jin nayi ina tunane yace kada ki karaya khadija don nasan zaki iya ki taimaka muna please wanan taimako ne indan kin yarda. Yaya Yusuf wanan ya zama na karshe da zan ma wani alfarma akan wanan mutumin don gaskiya baida niyar canza halin shi nake gani . Khadija ba laifin shi bane shu,umar mace ya hadu da ita take juya shi yadda take so nace har da halin shi a haka. Kin yarda zaki taimaka muna ke nan nace naji zan gwada don Allah don kai amma da ba haka ba babu abinda zai kara damuna da rayuwan shi. Nagode kwarai da hakan da zaki min don wanan ne kadai hope din da nake dashi yanzu akan wanan matar tashi. Ina aje wayan maryam dake zaune ta kura min ido tana sauraren maganan da muke yi din tace kai wasu maza suna haduwa da shu,uman mata wallahi. Koda yake ba abin mamaki bane ga wanda yasan mazajen da ke auren irin yan yaren buzaye zai san mazan ne a kasa matan suna sama. Sai abinda sukace komai su mamaye na miji yazama nasu su raba shi kuma da kowa nasa sai su da yan uwan su zasu dinga bushasha da shi da dukiyan shi. Sai dai kima sam basu son auren mazan yaren su don irin bakar wahalan da suke sha wurin su amma namu mazajen su ke kwadayin matan buzaye saboda bakar jaraban da suka iya. Yanzu dai kira shi muji yadda zaku kwashe a tsakanin ku don nasan akwai drama nace ni wanan daure ni suke son yi maryam. Ban san may yasa suke cewa wai sai nice zan iya masu haka ba bayan yana da kanne mata da yan uwa da zasu iya. Su iya may khadija ai abin sai da hikima ke fa ba yar uwan su bace kin ga yadda kuke moved dashi kamar saurayi da budurwa ne. Ke komai zaki iya fada mashi a zauna lafiya wani dan uwa idan yafa da sai inda karfin shi ya kare ke ko sai ki fada mai a wasa bai dauki abin da zafi ba. Wayan ta na karba ta hanyan yi mata karya wayana ba kudi a ciki tace ai bai san layi na ba don haka ba lale bane ya dauki kiran . Bari dai mu gwada mu gani idan bai dauka kiran har ya kusa karewa ya daga tare da fadin hello nace dole zama da yan haure ya kowa ma wani akidar banza. Wake magana please ya tambaya nace wata buzuwa ce ko kana son kari su zama biyu a gidan ka murmushi yayi yace khadija nace ba ita bace. Kina zaton muryan ki nan zai bace min ne nace marya na yana kama da na buzaye ne ? Yace ai kamar ma ta baci baki ganin zubin ku daya dasu sai dai yaren da baki ji nasu kai malam ni kiran ka nayi naji ko mommy ta koma ne? Don nasan ba lale bane buzuwan gidan ka ta barsu su dade a gidan yace idan kina son sani kije gidan ki duba mana. Ban tashi ba ne da zanje yace ya kike nace ina nan yarda ka sanin a baya ke ba a maganar girma da arziki dake ne ? Nace banson don ba gaisuwa na kira ka muyi ba ko tambayana yaya ni yace ai kogi ba ki dadi ba ko nace . Wani kogin ke nan dai wani ko wani ruwa ne ya shige shi in ba nasa bane amansa yake yi don haka ba gaisuwan ka nake nema ba. Yace becareful nace a nan ko sai kaga mutum har mutum amma a gidan shi sai ka rena mai wayo idan kaga abinda yake yi. Ta yaya bakin haure har zasu shigo su samu mutum a gidan shi in ba samun wuri ba suce sai abinda suke so zasu mai ni wallahi na dade da raina aya don tsakuwar ta. Yau hausa kike ji ke nan nace daurowa ne hakan adai ji tsoron Allah kada mutum ya zauna mace ta mayar dashi saniyar tatsan ta . Ba mai ci sai ita da yan uwan ta kadai yace kina son wani abu ke nan nayi saurin fadin haram wallahi adai ci lafiya. Ga yan ketare nan suna taya ka ci idan ka wawuro su kuma sai su cafke ranan na zuwa da zan maka irin ku kotu masu ba bakin haure makafa suyi yadda suke so da dukiyar kasan mu. Yace magana kike ji ke nan dai nace ba wani magana sai fadin gaskiyan da na saba kulun idan naga anyi ba daidai ba. Ya Abdul ace mutum baiwa kansa adalci kulun sai abinda mace ta dora shi a kai yake bi yace wai may kike nufine don na rasa gane ida maganar ki ya doso har yanzu. Mafalki nayi naga ka susuce kazama bawan mata sai goyon su kake yi a bayan ka ka manta da kowa na naka sai masu jajayen kunne kasa a gaba. Murmushi yayi yace ki fito fili kice kin yi kewa na kawai kin tsaya kina dora wa wani laifi kuma ko na kulata ba mata na na kula ba na kula matar wani ne ? Mata wai mata matar namu duka dai inji manya mata kan tana kaduna ka barota can wanan ai ta bugi ne . Khadija you are very stupid matar nawa kike aiban tawa a gaba na nace ko a idon ka sai na fada don gaskiya ake fadi. Namiji kamar mace baida say a gidan shi sai na mace macen ma abin kyamatar mu gaskiya ka gyara halin ka sai anjima nayi saurin kashe wayan batare da najira amsan da zai fada min ba. Wanan yarinyar ta ci uban rainin wayo wallahi yace Yusuf da ke zaune gefen shi yana murmushi yace khadija ce halan ? Wa kasan zai min wanan idan ba ita ba ban san mayeatsalar ta da Nafisa ba ko da yake su mata haka suke dama ko Nafisan da tasan da zancen khadijan Allah kadai yasan iya boren da zatai min. Kana zuwa gurin ta ke nan har yanzu ya danja tsuki yana fadin wallahi na dade ban ganta ba tunkan naje Lesvegan rabo da na ji daga gare ta. Yusuf yace ai gashi yau ta kiraka ita yace ta kirani taci min mutunci ba sai nayi maganin yarinyar nan wallahi ta raina ni da yawa I don't know why take min abinda taga dama haka ? Kun fi kusa ai bani shiga tsakanin ku yanzu ai wani kallo yaiwa Yusuf din yace tunda ka gama hadawa ba ai ka fadi haka yanzu ? Au ni ma hada ke nan ashe wa ya manna min wanan chewing gun din idan ba kai ba ina zaune kalau abina. Amma ai tayi muna rana ba kadan ba kasan da hakan dai ? Tsuki yaja yace ban san ya nakoma ba wallahi yar karamar yarinya ta shige min na kasa yin komai akan hakan ? Kun dai shige ma junan ku yanzun ne kuma kake neman maraba da ita ko why zaka so ka rabu da khadija bayan kasan tana da amfani a gare ka ? Amfani fa kace Yusuf yana kallon shi da idon shi da ya kafa mashi sai da Yusuf ya rausaya kai yace kafini sanin haka malam. Kada ka bari shedan ya rudeka kaiwa kan ka hasara zukekiyar yarinya kamar khadija may kake fadi ne wai Yusuf ? Kiran kawun shine ya katse masu magana da mamaki a fuskan shi ya furta kawu habu yau lafiya kawu ya kirani haka ? Ya dauka suka fara gaisawa da kawun nashi wan mahaifiyar shi cikin kunya da nauyin kawun nashi yake amsa mai gaisuwan. Don ya manta yaushe rabon shi daya kira shi ya gaida shi a matsayin shi na wan mahaifiyar shi da take ji dashi a cikin yan uwanta. Bayan sun gama gaisawa ne kawun nasa yace dama na kiraka ne idan da hali ina son ka shigo kaduna a cikin wanan satin . Da mamaki ya tambayi kawun nasa yace kawu lafiya ko yace a, a lafiya kalau sai alheri akwai abinda nake son kayi ne idan kazo amma fa idan ba takura. Haba kawu ba komai in sha Allahu satin nan zan shigo ranan jumma, a asabar zan karaso zaria in gan ka kawun nashi yace nagode Allah yayi maku albarka ya kara tsare muna ku. Ya amsa da amin kawu na gode ya aje wayan yana mamakin maganan da kawun nashi ke dashi akan shi Yusuf dake gefen shi ne ya tambaye shi ko lafiya. Yana mai da kan shi bayan kujeran da yake zaune sama yake fadin wallahi ban san abinda yasa yake nema na ba a yanzu. Zamu tafi karshen satin nan don haka sai ka shirya muna tafiyan yadda ya kama sai dai ban so tafiya yanzu ba a yadda Nafisa take haka haihuwa yau ko gobe. Zamu iya zuwa muyi kwana daya idan hakane sai mu juyo idan ka gama ganawa da kawun. Yace hakan za ayi Allah ya kaimu lafiya gaba daya har ya manta da zancen wata khadija ko don mantuwan da yake fama dashi a yanzu. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels