An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels [07/07, 11:23 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍         *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* *Romantic Book ne, kuyi haƙuri sabida salon labarin ne ya zo a haka; babu yadda na iya.* _________________________ *BABI NA ƊAYA* _______________ *KADUNA ZARIA*             A garin Kaduna ƙaramar hukumar Zaria; anguwan tudun wada. Malam Iro me kifi, sana'ar sa kenan siyar da kifi. Gado ne da yayi wajen mahaifinsa marigayi, tun yana saurayi yake sana'ar wadda ta kai yanzu har Aure yayi a cikin sana'ar, kuma alhamdulillah yana samu dai-dai gwargwado kuma har ya rufawa kansa Asiri. Mahaifiyar sa tana raye kuma shi yake kula da ita tunda shi kaɗai ne ɗa namiji da suka haifa, sai ƙannin sa biyu mata waɗanda yanzu haka sun yi aure da jimawa, sai dai Allah ya yiwa ɗaya rasuwa a lokacin da zata yi haihuwar fari. Shi ya ci gaba da kula da matafiyarsu tare da nasa iyalan, wanda a lokaci ɗaya jinyan mutuwa ta tarar da mahaifiyar tace ga garin ku nan.               Shekaru da dama sun shuɗe, wanda har ga shi girma ya soma tarar da Malam Iro; amma har yanzu cikin sana'arsa ta gado yake. Yanzu haka Allah ya albarkace sa da Yara huɗu Mata; wacce matarsa Harira ta haifa masa. A cikin rayuwar Malam Iro akwai dogaro ga Allah da tsantsan tawali'u, duk abun da Allah ya ba shi yana ƙoƙarin karɓa da hannu bibbiyu sannan kuma ya yi mishi godiya. Sai dai kuma matsala guda ɗaya ce a rayuwar sa da yake samu, wanda kuma a yanzu ta zame mishi babbar matsala da yayi sanadin soma gurɓata rayuwar ƴaƴan shi Harira Mace ce mai tsananin son abun duniya, haƙiƙa duniya tana matuƙar ruɗanta wanda ta kai har ba ta iya bambance abu mai kyau da mara kyau a rayuwarta, ita burin ta kawai tayi kuɗi, me zata taɓa ya zama kuɗi? Sannan aina zata samo hanyar da zai kawo mata kuɗi? Shi ne tunanin ta a koda yaushe. Tun farko Harira irin matan nan ne kyawawa da Allah ya zuba musu kyau; kasancewar ta bafulatanan nan cikin Zaria cikin anguwan Fulani, tallen fura da nono take kawo wa nan cikin kasuwan tudun Wada, wanda har Malam Iro ya ganta kuma tayi masa a zuciya, babu ɓata lokaci ya bayyana mata irin ƙaunar da yake mata, to, itama bata ja zancen ba ta amince domin a lokacin kaf cikin samarin ta shi ne wanda take ganin yana da ɗan kyan gani da sura me kyau, duk da a rayuwarta ta taso da burin auren shahararren me kuɗi; kasancewar yanda ake ce mata tana da kyau, irin su masu kuɗi suko so, domin irin su ne ake ajiyewa a gaban mota, to, ga shi kuma har ta kai wannan lokacin babu wani me kuɗi da ya taɓa cewa yana sonta, tun tana saka ran zata same su domin ta ƙi aure tana jiran irin su, amma kuma shiru kake ji sai irin ƴan iskan samarin nan da suke kawo mata hari ko yaushe. Haƙiƙa ta ji daɗin shigowar Iro cikin rayuwarta, wanda babu ɓata lokaci ta ba shi dama ya tura gidan su, aka yi komai na al'ada aka sanya musu ranan aure.              Bayan lokaci yayi aka ɗaura musu aure ta tare a gidan su, tana zaune tare da mahaifiyar sa. Sai dai tunda aka yi auren ɗabi'un Harira waɗanda be san su ba suka soma bayyana, Mace ce fitinanniya ga shegen rowa, ko abinci tayi ba ta ba wa mahaifiyarsa, sai dai idan shi ya dawo ya nema mata abun da zata ci, sosai mahaifiyarsa take kuka da irin halin Harira saboda kasancewar ta Mace mai haƙuri, haƙiƙa tana ƙunsan baƙin ciki a wajen ta, ga shi ko kaɗan ba ta ganin girman ta har zagin ta take yi tayi ta gaya mata maganganu mara sa daɗi, shi kansa Iro haƙuri yake yi da ita sabida shima irin mahaifiyarsa ne, tun yana tanka mata yana tsawatar mata har ta zo ta fi ƙarfin sa yanzu, domin a yanzu ta sake kilewa rashin mutunci sai wanda ya daɗu a gunta, bare yanzu tayi ƙawaye matan masu kuɗi masu hannu da shuni, a wurin su take koyo duk wasu abubuwa da bata san su ba a baya, ita rayuwarta kawai tana hangen waɗanda suka fi ta ne shiyasa kullum fitina ba ya ƙarewa a gidan su, kullum da abun faɗan da zata yiwa Iro, ya gaji dai ya ƙyale ta ya fita harkan ta.              A haka rayuwa ta ci gaba da tafiya har Harira ta haifi ɗiyarta Mace ta fari, aka sanya mata sunan Ƙanwar Malam Iro da Allah ya karɓi abun sa, Nana Firdausi. A lokacin da Harira take da cikin ƙanwar Firdausi har ta kusa haihuwa, sai kuma mahaifiyar Iro ta rasu, sanadin da aka maida wa yarinyar sunan ta, Ummu Kulsum, suna kiranta da Ummu, ita dai Harira da sunan ta gatsau take kiran ta babu ko kunya. Bayan kamar shekaru huɗu sai ta ƙara haihuwar Mace, itama aka saka sunan uwar Harira, Fatimah suna kiranta da Zahra, sai kuma Auta da aka haifa bayan shekaru uku da haihuwar Zahra, sai dai fa tunda aka haifi yarinyar nan Harira ta ɗaura buri na duniya a kanta sabida ganin yadda yarinyar ta fita daban da sauran ƴaƴan ta, tsananin kyawun ta da kaf ƴaƴan ta basu biyo ta ba, duk kyawun Harira ta ninka ta a kyau nesa ba kusa ba, shiyasa tunda aka saka mata suna A'isha Humaira, sai ita Hariran take kiranta da suna Arab sabida tsantsan kyawun ta, kuma sunan ta ji shi ne a wajen wasu masu kuɗi da suka sanya wa ɗiyar su, shiyasa itama take ce mata Arab, shiyasa sunan ya bi ta har girman ta, wanda daga ita ne kuma bata sake haihuwa ba. A wannan lokacin Harira wacce yaranta suke kiran ta da Inna; babu irin sana'ar da ba ta yi don kawai ta farfaɗo da rayuwar ƴaƴan ta, kuma ta sanya su a inda zasu yi gogayya da yaran masu kuɗi, shiyasa tun suna yara makarantar kuɗi suke yi, ita take biya musu kuɗi da komai bata damu da sai Malam Iro ya bayar ba, wanda a yanzu shi kuma yaran suke kiran shi da Baba, sai dai idan ya samu kuɗi yana taimaka musu sosai tunda zuciyarsa bata mutu ba, bazai iya gani yaran sa suna rayuwa be da amfani a tare da su ba, sai dai bai da wani iko dasu tunda sai abun da Harira tace a gidan ake yi, tuni ta mallake shi domin har biye-biyen Malamai take yi yanzu.             Tunda yaranta suka girma bata da wani buri a yanzu sama da su samo mata masu kuɗi, kowanne iri ne idan yana da kuɗi; to, tana son yaranta su samu, shiyasa bayan sun gama secondary school; Ummu da Zahra, sai ta saka su a nan F.C.E Zaria, duk sanda suka je makaranta suka dawo zata ɗaura musu tallan shinkafa su shiga cikin kasuwa suyi talla, ita a ganin ta idan suna yawo kwararo-kwararo hakan ne zai sa masu kuɗi su gansu har su zo gare su Yayinda ita kuma Firdausi tana zaune a gida ta ƙi makaranta, sabida ita bata da buri sama da tayi aure, kasancewar rayuwar gidan su yana mugun ɓata mata rai, kwata-kwata ta tsani halayyar da Innarsu take shirin jefa su a ciki, shiyasa ita kaɗai ce ta fita zakka a gidan su, wadda ita ta biyo halayen Mahaifin su ne sak, shiyasa yake tsananin ƙaunarta saboda tana bin maganar sa, yayinda ita kuma Inna Harira ta tsane ta kuma ta fita harkan ta, dalilin da yasa tace, "baza ta biya mata kuɗin makaranta ta ci gaba ba tunda ba ta mata biyayya." Ita kuma dama bai dame ta ba bare ta saka hakan a ranta, duk da Babansu yayi mata alƙawarin, "idan har ya samu kuɗi a wannan shekaran zai saka ta sai ta riƙa bin ƴan uwanta". Amma ita furr tace, "ba ta so." Tace mishi, "ita aure take so yanzu, kuɗin da zai saka ta makarantar gwara ya siyan mata kayan ɗaki." Kasancewar tana da saurayin da yake neman ta tun tana secondary school, sun shaƙu da shi sosai. Ɗan Kaduna ne amma yana zaune da Kakarsa a nan To hakan ya yiwa Baba daɗi, shiyasa ya samu Nafi'u saurayinta yace mishi, "ya turo magabatan shi." Abu kamar wasa har aka sanya ranan aure kusan shekara biyu, a haka Baba yayi kurɗa-kurɗan shi har ya samu ya yi mata komai da uba yake yiwa ɗiyarsa Ba tare da ko sisin Inna ba, tunda ita tace, "ta ƙi bin umarnin ta sai abun da take so zata yi, to ta je tayi auren idan hakan shi ne zai fishshe ta." Haka kuwa aka yi auren lokaci yana cika. Aka kai Amarya gidan ta da ke can Kaduna, alhamdulillah Nafi'u yana da rufin asiri dai-dai gwargwado tunda yana aikin sa kala-kala. Haka dai ya fi ma Firdausi tunda tayi aurenta ta baro gidan su, su ma ƙannin ta tana fatan ace wata rana sun gane gaskiya su gane cewa Inna tana saka su ne a cikin *RUƊIN DUNIYA!* wanda hakan babu inda zai kai su sai dana-sani.         Ƙaramar ƙanwar su wato Arab, wacce a yanzu tana S.S 2 ne, ita kuma Inna Harira tana mata awara ne da yamma tana siyarwa a can bakin layin su. Gaba ɗaya yaranta ban da Firdausi ta ɗaura su a tirban da take buƙata, kuma su kansu sun tashi idanunsu a buɗe basu da buri sama da su cikawa uwar su burin ta, su kansu suna jin haushi musamman ganin su a gidan ƙasa gidan talakawa, ga ƙawayen su duk yaran masu kuɗi, shiyasa basu da aiki sai ƙarya, idan ka gansu baza kace yaran talaka bane sabida suturun da suke saka wa, kamar baza su taka ƙasa ba don yanga da iyayi. A duk cikin su ukun; Arab ta fi su fitsara da rashin kunya, domin ita halin mahaifiyarta ta ɗauka har ta zarta ta a son kuɗi, dalilin da yasa kenan ta soma ba wa maza kanta tun a wannan lokacin don kawai ta samu abun duniya, ga ta da samari ko ta ina, duk inda ta gibta sai ta samu saurayi, sai dai ita babu aure a tsarin ta a cewar ta, "sai nan gaba, sai ta gama karatu sannan zata yi aure". Dalilin da yasa take gara kan samari kenan, ga shegen wayon; sai ta ci kuɗin saurayi kuma ta hana shi abun da yake so sai ta gama jan mishi rai ko kuma ta gama wulaƙanta shi. Arab kenan yarinya mai zamani wacce take cin duniyar ta da tsinke a yanzu, a duk faɗin tudun Wada da kewaye babu wanda bai santa ba, har kirari ake mata da sunan, 'Arab Matar manya, kin fi ƙarfin Yaro'. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️                     Yau ma kamar kullum yanda Inna Harira ta saba yiwa Arab awara domin ta fita mata dashi; hakan ne yau tayi mata, sai dai na yau ya fi na kullum yawa saboda ganin yanda ake ciniki sosai, ba ta daɗewa yake ƙarewa idan ta fita dashi, shiyasa tace wa Arab ɗin, "Autana yau da yawa zan yi miki tunda naga kina dawowa da wuri yana ƙarewa." Arab tace, "ai kuwa Inna dama ina so in yi miki magana ki ƙara yawan shi don naga ba ya isan su suna son awara na wlh." Baki Inna Harira ta washe ita kuma tana cewa, "ai dole ne su so awaran ki sabida daɗi, Ni na san na iya ai, ko kayan da nake kashe wa wannan awaran dole su riƙa santin shi." Dariya daga Arab har Ummu da take jin su suke yi Ummu tace, "Inna ai Ni ina ganin hannun ki ne mai albarka, ko abincin nan da muke fita dashi ba ki ga yanda ake wawa ba wlh, mu ma idan za ki sake yin mana sai ki ƙara yawan shi, ki haɗa ma har da kunun aya don shima ana yawan tambayar mu." "To shikenan Allah ya kaimu goben za'a ƙara, dama ina ta tunanin siyan fridge wlh, to yanzu tunda kin ce haka kinga ban ga ta zama ba, yanzu ki taso ki shiga kasuwa sai ki siyo min abun kunun mu fara mu gani; Allah ya bamu sa'a." "Amin AMin." Duk suka amsa daga Ummun har Arab Sai Inna Harira ta kuma cewa, "yi sauri Auta ki shirya yanzu zan yanka miki ki wuce." "To Inna." Arab ta amsa tana tashi daga bakin ƙofan da take zaune tana yankan ƙumba, ta wuce cikin ɗakin su, kayan jikinta ta cire ta ɗaura zani daga iya ƙirjin ta, kana ta fito kanta babu ɗankwali ta kamfaci ruwa a rijiya ta shiga wanka. Ta jima kafin ta fito tunda dama haka ta saba yin wankan ta, bayan ta shiga ɗaki ta gama shiryawa ta fito wajen Ummu ta soma koɗata tana cewa, "iyen ba Ƙanwar mu, kin ga yanda kika tsatso kyau kuwa? Anya wannan baza ki haɗa gosilo a titi ba? Tirƙashi." Dariya kawai Arab ɗin take yi tana duba jikinta Yayinda itama Inna Harira sai washe baki take yi tana koɗa ta tana cewa, "ƴan matana ta fi na kowa kyau, iyee! Kin yi kyau sosai Auta na, na san yau akwai kasuwa kenan." Fari tayi da manyan idanuwan ta tana taunan chewing gum ɗin bakin ta, yayinda ta furta, "sosai ma Inna, sai mun dawo kawai kiyi min addu'a." "To Allah ya tsare Allah Ubangiji ya bada Sa'a, Allah yasa a samo mana rusheshen me kuɗi wanda zai kai Ni Makka bana." "Amin AMin innarmu." Duk suka amsa suna dariya "Ke ma tashi ki shirya ki wuce kasuwan nan kinga yamma tana yi." Tayi maganar tana kallon Ummu Ita kuma Arab ƙaton farantin da aka jera mata komai, kama daga kan; icce, matsama, ashana, kalanzir, kafi-tankiya da Robbern zuba awaran idan ta tsame, duk suna kan farantin saboda ƙato ne, sai ta riƙe Robbern awaran a hannu tunda shi mai hannu ne, irin bokitin nan ne fari amma ƙato sosai, ta yiwa Innan sallama ta fice a gidan tana ci gaba da taunan chewing gum ɗinta, ƙararas-ƙararas kawai ake ji tana tafiya kamar zata karye tsaban yanga. Sai da ta ɗan yi nisa da gida sannan ta hangi Zahran su a cikin wata ƙatuwar jib ita da saurayin ta, shiyasa ta nufi wajen don ta ƙi wucewa sai ta kwashi rabon ta, tunda ta hangi wannan motan to akwai maiƙo a wajen, shu'umin murmushinta ta saki har da cije laɓɓa; tana wani gyara tafiyar ta cikin tsananin yanga ta nufe su tare da rangaɗa musu sallama Gaba ɗayan su suka kalle ta suna amsa mata sallaman, Yayinda Zahran tace, "Ah har kin fito Auta?" Yatsina fuska tayi tana kallon ta tace, "eh wlh na fito, shi ne na hango ki nace bari in zo, dama Inna ce tace idan na ganki in amshi Naira ɗari biyu zan ƙara icce dashi, sannan kuma in siya yaji da sauran." Zahra tace, "to ai Ni bani da kuɗi, ban fito da kuɗi ba, sai dai ki koma..." Tun kafin ta ƙarisa zancen saurayin nata yace, "a'a Baby bari in bata." Sai ya sanya hannu a cikin Aljanu cikin sauri ya zaro kuɗi daga ciki, ƙirgawa ya soma yi Yayinda Arab sai zuba murmushi take yi har tana ƙara leƙawa tana lanɗe baki, idanunta suna ware a waje tana ganin yanda yake sarrafa hannayen nasa wajen ƙirga kuɗin, a zuciya kuma tana taya shi ƙirga Sai da ya ƙirga dubu goma cif kafin ya miƙo mata yana mata murmushi yace, "yauwa ƙanwata ga shi." Ta miƙa hannu cike da yanga ta amsa still tana murmusawa tace, "na gode." Murmushin ya kuma yi ko ƙyafta idanu ba ya yi a kanta yace, "babu komai ƴan mata yiwa kai ne, amma Baby ƙanwar ki ne da gaske?" Ya ƙare maganar yana mayar da idanun sa a kan Zahra "Eh ƙanwata CE love, ita ce take bina kuma ita ce ƙaramar mu." "Masha Allah gaskiya kyakykyawa ce, ga kama nan ma na gani sabida duk kuna yanayi ai." Dariya kawai Zahran tayi, Inda ita kuma Arab ta lanƙwashe murya tana sake mishi godiya Yace, "babu komai ki je kawai." Da haka ta wuce ta tafi; Zahra na mata, "sai ta dawo".          Tana wucewa saurayin yace, "Baby gaskiya duk ta fi ku kyau wannan ƙanwar taku, wow! Allah yayi halitta a nan." Haɗe fuska ita kuma tayi tana cewa, "to me kake nufi ne wai kake ta koɗata a gaba na?" Murmushi yayi yace, "Baby Sarkin kishi, ai saboda tana ƙanwar ki ce nake koɗata a gaban ki, amma babu wani abu a raina, yanzu mu je shan icce cream ɗin ko mu fasa?" Murmushi tayi tare da cewa, "mu je idan har baza a jima ba." "No Baby baza mu jima ba wlh, just thirty minutes ma ya isa." "Ok mu je." Daga haka suka rufo ƙofofin motan sannan ya ja suka tafi.       _In ana comments za a iya ganin posting koyaushe, so ku ba da haɗin kai please, idan kuma babu wani comments ba na bukatar ƙorafi don Allah, duk sanda ku ka ga sabon update shikenan._ [07/07, 11:26 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍        *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA BIYU* ______________Wayanta ne ta soma Ring, sai ta ɗan dakata daga tafiyar yauƙin da take yi, tare da ajiye Robbern awaranta ta soka hannun ta a cikin Aljihun doguwar riganta; tare da zaro wayanta tana kallon me kiran. Sunan Besty ne ya fito ɓaro-ɓaro a kai, ba tare da jan lokaci ba tayi peacking tana karawa a kunne da cewa, "ya dai Besty?" "Lafiya, ke nake jira tun ɗazu gani a wajen suyan ki, ko dai yau baza kiyi bane don naga time yana wucewa?" Yamutsa kyakkyawar fuskarta tayi cike da yanga irin nata tace, "No gani nan a hanya ai, ina zuwa." "Ok kiyi sauri da Allah, akwai labari wlh." "Haba nawan?" Tayi maganar tana ɗan sakin fuskarta kaɗan "You just have to come and see for yourself. " "Ok. I'm coming" Sai ta zare wayan a kunnenta tare da zura ta a cikin Aljihun, sannan ta ɗauki Robbern awaran ta ci gaba da tafiya. A haka tana yi kamar baza ta taka ƙasar ba har ta fita layin gidan su, duk inda ta wuce gungun maza kallon ta suke yi, majority wasu gulman ta suke yi, ƙalilan kuma suna mata magana kasancewar mutanen ta ne. Sai dai ta gaisa dasu kawai ta wuce har sanda ta kai babban titi inda take yin tuyan awara Da sauri Ibrahim her friend; ya taso daga saman wani benci da ke gaban shago a wajen; ya sauke mata farantin saman kanta yana dariya tare da cewa, "Oyoyo my Besty, I've seen you before everyone." Murmushi tayi tana ajiye Robbern tace, "uhm Ni ban ga alama ba, bayan yau kwata-kwata ban ganka ba sai yanzu, ina ka shige ne?" Ta ƙare maganar tana narkar da manyan idanuwanta a cikin nashi, tare da sauke mishi wani kallo da ke rikitar da duk wanda ta yiwa shi Shima ɗin kafe ta yayi da idanun yana cije leɓe cike da tsantsan sha'awar ta da ƙaunarta yace, "oh my Besty! Me kike ci na baka na zuba? Ai abun da yasa na kira ki kenan ki ƙariso don in shafa miki labarin abun da yake faruwa... Amma tukunna dai bari in soma hura miki wutan nan don naga time na gudu." Sai yayi saurin ɗaukar kafi-tankiyan ya ajiye sannan ya soma jera itacen a ciki, a haka ya gama ya hura wutan Ita kuma har ta saka kujera ta zauna suna magana a tsakanin su. Wani almajiri ta kira ta kalli Ibrahim ɗin tare da cewa, "Besty ba shi kuɗi ya ƙaro min icce, don wannan bazai ishe Ni ba." "Ok nawa kike buƙata?" Yayi maganar yana ɗago kai tare da kallon ta "Two hundred is ok." Sai ta kalli Yaron tace, "ka siyo min iccen ne na ɗari, sai yajin hamsin." "To." Yace yana amsar kuɗin a wajen shi Komai Ibrahim yayi mata hatta da ɗaura mai a wuta, sai da yayi zafi sannan ita ta soma jefa waran tana cewa, "My Besty bani labarin in sha na ƙosa." Dariya yayi yace, "Arab Sarauniyar son labari! Yanzu kuwa." Sai ya gyara zama a saman bencin da ya ɗauko Har zai soma maganar kuma sai wani saurayi ya iso wajen yana kiran sunan shi, tare da ba shi hannu suka gaisa, sai ya zauna a kan bencin shima yana kallon Arab tare da cewa, "Ƙin fi ƙarfin Yaro ya ne?" "Dai-dai Sa'id." Ta amsa shi batare da ta kalle shi ba tana ci gaba da saka awaran Shi kuma yace, "but yau ba ki fara suya da wuri bane? I think zan zo inga wuri ya cika sai na iske babu kowa, yanzu ma kika fara ai." Yatsina fuska tayi da cewa, "wlh kuwa. I did not start early." "Ok. tunda na zo da wuri yau dai na taki Sa'a, za'a ajiye min na ɗari uku ina dawowa, don Allah yanzu ba jimawa zan yi ba kar in dawo inga an cika wurin sai na jira layi." "Ba ka da matsala, kawo kuɗin sai in ajiye maka." Sa'id ɗin da ya miƙe sai ya narke fuska yana kallon ta, tare da cewa, "haba Arab sai kace ba ki sanni ba? Zan ba ki mana kar ki damu ki zuba min." Taɓe baki tayi sai a lokacin itama ta ɗago manyan idanuwanta tare da zuba mishi su tace, "ka san hali na, a kuɗi bani da mutunci ka san da sani, Allah bazan ajiye maka ba idan har ba ka bani kuɗi ba, Ni na dena wannan gangancin." "Ibrahim ka sanya baki mana, wai kamar bata sanni ba? Yawa ne wannan wlh, kin san hali na nima na san naki, bazan miki wasa da kuɗi ba, don Allah ki ajiye min yanzu babu kuɗin ne a hannu na, kuma idan nace sai na dawo zan siya zan zo in tarar da layi, ƙarshe in rasa, kuma so nake yi in wuce da wuri saboda akwai inda zan je." Tsaki ta ja da faɗin, "zancen kake so, bani da lokacin ka wlh." Ta mayar da hankalinta a kan abun da take yi bata sake bi ta kanshi ba Yayinda shi kuma yana ta roƙon ta tare da ce ma Ibrahim, "ya saka baki ta ajiye mishi don Allah, wlh zai bata kuɗin." "Kaima da tuni ka je duk inda zaka je ka dawo, ka san halin Besty tunda tace baza ta ajiye ba, to; baza ta ajiye bane, ka je ka dawo Ni zan ajiye maka." "Ok. Shikenan sai na dawo." Yayi maganar yana juyawa zai tafi tare da sanya hannu a aljihu yana zaro wayansa Sai da ya tafi Arab ɗin tace, "bar ɗan iska, wlh bazan ajiye ba sai ya bani kuɗi, da ma ace ban san halin sa bane." Dariya Ibrahim yayi yace, "ke ma ba ki da dama Besty a kan kuɗi." Tura baki tayi tana tsikaro ɗankwalin ta a gaba tace, "Ah to, wa ke wasa da kuɗi? Ai Ni duk inda aka ce kuɗi, to; ba na wasa dashi, a kan kuɗi zan iya yin komai." "Gaskiya ne Besty." Yafaɗa yana ƙyalƙyale wa da dariya, sai kuma ya sauko ƙasa ya duƙa setting kunnen ta yana raɗa mata, "kamu nayi miki fa, wlh wani babban Alhaji na samo miki me shegen maiƙo." Waro fararen idanunta tayi da cewa, "kai don Allah? Ba na son wasa fa me sunan Baba?" "Ah to, wanne wasa zan yi miki? Kin san bamu saba haka ba, wlh da gaske nake miki, irin waɗanda kike so, bari ki ga." Sai ya ciro wayansa ya danna kana ya nuna mata hoton wani ƙaton Mutum tulele wanda da ganin sa ka san ba ƙaramin Mutum bane, kuɗi ya zauna masa sosai, don ma a inda ya ɗauki hoton kana gani ka san waje ne na alfarma Amsar wayan tayi da sauri tana dubawa Sai shi kuma ya ci gaba da cewa, "a Abuja yake zaune, amma shi mutumin Bauchi ne, a can iyalan sa suke, ɗan hannu ne wlh sosai, nima ɗan small ne ya haɗa Ni da shi sabida ya san Mutumin, yace wlh ba ƙaramin kuɗi zamu samu a hannun sa ba idan har na tura ki wajen sa, shiyasa da gaggawa na amsa tayin nasa saboda Ni kaina sai da nayi bincike before in zo wajen ki." Ci je baki tayi tana ɗauke idanunta a kan hoton da ta kafa masa, ta mayar a kan Ibrahim tana cewa, "Ni ba wannan nake son ji ba. Ka tabbatar akwai samu a ciki sosai? Don ka san hali na ba na son harkan ƙaranta." "Haba tawan, kin san na fi kowa sanin halin ki, akwai nace miki, but kinga mutane sun soma yowa nan, ki bari zamu ƙarisa zancen idan kin koma gida, ko kuma muyi waya kawai." Baki ta washe cikin farin cikin da ya bayyana a kan kyakkyawar fuskarta tace, "ok. I would also prefer that." "Yauwa Besty na." Da haka suka ci gaba da magana suna dariya, yayinda wurin sai cika da jama'a yake yi, duk maza ne manyan samari da magidanta, har da masu kuɗi ƴan hannu zuwa siyan awaran nata suke yi don kawai suyi harƙalla da ita Nan da nan sai awaran nata ya ƙare ko kiran sallan magriba ba'a kai ga yi ba, shiyasa ta tattara kayanta ta ba wa wani almajiri yayi mata gaba da su, sannan suka tako da Ibrahim zai raka ta gida Wani saurayi ne a mota ya bi bayan su, ya tsayar da motan a kusa da su yana cewa, "ƴan mata ji mana." Tsayawa suka yi yayinda suka zuba mishi idanu. Gaba ɗayan su kallon yanayin tsarin zubin motan nashi suke yi tare da hasashen yanayin sa; kuma ba tare da tayi yunƙurin amsa shi ba Sai ya sakar musu murmushi tare da cewa, "Aboki na ɗan bamu wuri mana, zan yi magana da ƙanwar taka." Shima murmushin Ibrahim yayi tare da shafa kansa yace, "ok ba damuwa Alhaji." Sai ya kalli Arab yace, "Besty Ni zan wuce gida, zamu yi waya kawai." "Ok bye." Ta furta cikin yanga tana ɗaga masa yatsu Bayan wucewan sa ne sai saurayin ya buɗe mata ƙofan mazaunin banza yace, "shigo mana Gimbiyya." Sai da ta kalle sa ta tura baki cikin jan hankali kana tace, "a nawa?" Murmushi yayi yace, "duk farashin da kika yanka min Ni na amince." "But ban yi tunanin da sauƙi hakan ba." Tayi maganar tana kafe shi da kallon ta da ke rikita su Still murmushin yayi yace, "ai ke ce kin fi ƙarfin hakan, ko dukiyata kika ce in ba ki domin mallakar ki; da gudu zan aikata hakan." "Allah ko?" Tayi maganar tana zaro ido waje kaɗan mai nuni da mamakin maganar sa, yayinda fuskarta ke ɗauke da shu'umin murmushin ta da ba kowa yake iya gane ma'anar sa ba "Da gaske, kin wuce haka a wuri na, but na san tsokanata kike yi ke ma kin san da haka, ba Ni ne farkon faɗa miki ba." "No you were the first to tell me, in your mouth I began to hear, kuma kaga dole in yi shakkar amincewa da kai At the same time, bare yanzu da kidnappers suka yi yawa." Dariya yayi saboda yanda tayi maganar, cike da burgewa yake kallon ta yace, "haba Princess ban zaci haka a gare ki ba, anyway idan ba ki sanni ba Ni na san ki, cuz na daɗe ina bibiyan ki, kuma ina zuwa wurin nan sosai, but sai dai ba ki taɓa kula dani bane, but idan ma Ni kidnappers ne ai ba laifi bane, a kanki zan iya sace ki idan har hakan zai saka zuciyata ta samu natsuwa." "Ko?" Tayi maganar tana sake ware mishi kyawawan fararen idanuwanta a kanshi "Yeah, please ki shigo ba don hali na ba, wlh na ƙosa in ji ki a cikin motata, idan ba haka ba zuciyata zata fashe." Sai ya ɗaura hannun sa a setting zuciyar nasa tare da ƙarisa zancen da cewa, "saboda ba ki ji yanda take bugawa bane, saura ƙiris..." Sai ya cije leɓe yana sake faɗin, "wash Allana!" Dariya tayi kaɗan cike da jan aji, sai tayi wal da idanunta cike da yanga tace, "afwan kyakykyawar saurayi, bari in shigo." "Yauwa ko ke fa." Yafaɗa yana washe baki, "wlh bazan iya jure jan ajin nan naki ba, gwara ki taimaka min." Sai da ta shiga ta zauna before ta juya tana kallon sa da kyakkyawar murmushinta me shiga rai tace, "to kayi haƙuri na ce ai, gani na shigo." "To amma zan nemi wata alfarma." "Why not." Tace tana ɗage kafaɗa "Zan ɗan gyara parking sabida naga kamar a hanya nake." "Ok ba damuwa." Sai ya yiwa motan key ya ja zuwa gefe sannan ya faka, tare da juyowa kacokan yana kallon ta cikin tsantsan sha'awa da nuna zalaman sa, inda kyakykyawar murmushin sa ke gudana a kan fuskarsa While itama yanda yayi tayi, ta zuba mishi narkakkun idanuwanta masu shegen kaifi da ratsa ɓargon Mutum, wanda lokaci ɗaya suke sake zautar da ma'abocin kallon su Shiru suka yi babu mai cewa uffan a tsakanin su, inda suke sakarwa juna wani irin kallo me tattaro saƙonnin zuciyoyin su suna aikawa juna. Yayinda murmushin farin ciki ke kwance a kan fuskartasu cikin shauƙi; tamkar sun san juna da daɗewa a yanayin kallon da suke yiwa kansu Tsawon mintuna biyar before ya ja wani irin dogon numfashi yana lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kanta, sai ya buɗe baki cikin wani irin yanayi yace, "Gimbiyyata." Ɗan waro idanu tayi cikin salo da guntun murmushin ta tace, "har na zama taka?" "Eh mana, wace ce Gimbiyyata idan ba ke ba? Ai babu wata mace kyakykyawa a faɗin duniyar nan kamar ki, ba ki san jimawan da nayi ina bibiyan ki ba ko? Uhmm zuciyata ta jima da makancewa a kanki, ban yi tunanin zan iya kaiwa har wannan lokacin ban sanar da ke abun da ke raina ba, sai dai kuma ɗan wata tangarɗa da aka samu wanda ya hana Ni bayyanuwa a gaban ki, amma yanzu gani na dawo." Sai yayi shiru yana sake zuba mata idanu kamar yanda itama take mishi wani irin kallo me saka shi a wani irin ɓigirin da be taɓa tsintan kanshi ba, "na san za ki yi mamaki idan nace miki na san komai game da ke, Arab zuciyata ta makance a tun sanda idanuwana suka soma tozali da kyakykyawar fuskarki, na kasa natsuwa tun sanda na ganki, wlh ban taɓa jin wata ɗiya Mace ta shiga raina kamar ki ba, na so in jure amma na kasa, don Allah na zo da ƙoƙon barata ki taimaka ki amshe Ni a matsayin masoyin ki na gaskiya, ina ƙaunar ki! I love You A'isha Humaira, i love You with all my heart!" Lumshe manyan idanuwanta tayi sabida jin sunan da ya kira ta, ba kowa yake kiranta da sunan ba sai mahaifin ta, shi kaɗai ne ba ya kiranta da suna Arab sai A'isha Humaira. Buɗe idanun tayi ta zuba mishi tana kallonsa da shu'umin murmushin ta da a koda yaushe yake saman fuskarta. Bata yi magana ba illa kallonsa da take yi tamkar zata cinye sa babu wani ɗar ko jin kunya a tare da ita, hasali ma tsantsan gogewa ne irin nata na bariki Shi kuma sai yace, "kin yi shiru Gimbiyyata? Ko so kike yi zuciyata ta buga?" Wani guntun murmushi ta sauke before tace, "Ina wani tunani ne a raina that's the reason da ka ji nayi shiru." "Amma ba ki yarda da Ni bane? Wlh ina ƙaunar ki! Don Allah kiyi min magana ko ya ya ne inji daɗi." Sai ya saka hannayen sa biyu ya kamo nata da take faman shafa fuskarta dasu, ƙurawa junan su idanu suka yi na ƴan seconni before yace, "ina sonki! Me kike so in yi miki da za ki yarda?" Still murmushin tayi tana cije baki tare da sake narke idanuwanta tana wani luuu dasu tamkar zata rufe sai kuma ta buɗe su, cikin wani irin kallonta me sake zautar da duk ma'abocin da tayi masa tare da fitar dashi a wani yanayi lokaci ɗaya Wanda hakan ne ya soma tasiri a jikinsa har be san sanda ya sake damƙe hannayenta a cikin nashi ba yana wani irin murza mata cike da wani irin feelings da ya taso mishi Hakan yasa tayi murmushi kaɗan tana cewa, "har yanzu ba ka sanar da Ni kai wane ne ba balle in so ƙulla alaƙa da kai." "Haba idan har don wannan ne kar ki wani damu, na sha'afa ne, suna na Tariq... Tariq Muhammad Auwal, Ni mutumin Samaru ne, ina zaune tare da iyaye na da ƴan uwana, kuma abun farin cikin bani da Mata." Ya ƙare maganar yana mata murmushi Yayinda ita kuma ta saki dariya kaɗan wanda ya bayyana haƙoran ta, still idanuwanta a cikin nasa, sai kuma ta sake sakin murmushinta tana janye hannayenta a cikin nasa tace, "meyasa za ka taɓa min jiki ba tare da mun yi farashi ba? I'm an expensive girl." "Don't worry, I have the money to pay you until you say it's enough." "Really?" Tayi maganar tana ɗan waro idanu waje wadda ya zame mata ɗabi'a; kuma yake ƙara mata kyau ainun "Yeah. You just give me a chance." Leɓen ƙasan bakinta ta shigar cikin bakinta tana tsotsa cikin salo da jan hankali, sai kuma ta cire tana ɗage kafaɗa tare da faɗin, "fine. I answer you both hands." Dariya yayi cikin farin ciki tare da cewa, "gaskiya ke ta daban ce, na ji na ƙara sonki matuƙa, but yanzu kin bani damar taɓa hannun ki ko?" Ya ƙare maganar yana kashe mata ido ɗaya da murmushi a fuskarsa "Me kake ci na baka na zuba? kar ka damu, har sai ka gaji da taɓawa." "Haba idan ko haka ne bazan taɓa gajiyawa da taɓa kyakykyawar halitta kamar ki ba, ba ki san yanda kike da matsayi a cikin raina ba." Bakinta ta ɗan turo gaba before ta ja numfashi tace, "ok. Zan tafi, ka ga dare yayi." "To, babu ko ɗan kiss haka zamu rabu?" Ƙura masa idanu tayi tana kallonsa na ɗan wani daƙiƙu, sai ta saki wannan shu'umin murmushin nata kafin tace, "me kake yiwa sauri haka? Za ka samu abun da ya fi kiss ma, but not know." Langaɓe kai yayi, yayi mata fuskar tausayi tare da cewa, "Please Princess." "No. Zan ta fi." Ta furta tana ƙoƙarin buɗe ƙofan Sai yayi saurin kamo hannun ta da cewa, "haba Gimbiyyata kar ki tafi, I'm sorry to, na daina maganar." Hannunta ta zame tana kallon fuskarsa Sai yayi mata murmushi yace, "to ki bani Numban ki mana." "Ok." Kawai ta furta tare da karanto mishi numbern Sai ya rubuta sannan ya buɗe lockern motan ya ciro kuɗi 20k ya miƙa mata       Ta sanya hannu kuwa ta amsa ko jan aji bata yi ba, sai ga kyakykyawar murmushin ta ya bayyana a kan fuskarta, yayinda take bin sa da kallo me ban sha'awa tace, "tnx. Bye." "Bye dear." Sannan ya ɗaga mata hannu yana mata murmushi har ta fice, sai da ya ga tafiyar ta before ya ja motan ya bar wajen cike da farin ciki a zuciyarsa.              _Don't forget to follow me on Wattpad, and voted 🙏🙏. Tnx._ [07/07, 11:27 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA UKU* _______________A bakin ƙofan gidan su ta ci karo da mahaifinsu, wanda yake zaune tun dawowar shi masallaci sallan isha'i, ya shimfiɗa tabarma yana shan iska. Ganinta ne yasa ya kira sunan ta yana cewa, "A'isha Humaira daga ina?" Yamutsa fuska tayi tana ɗan sosa kanta tace, "Baba daga wurin saurayi na." Shiru yayi yana kallon ta don ya san halinta ba kunya ne da ita ba, bata da ɓoye-ɓoye abin da ke ranta shi take faɗa. Ganin zata wuce ciki sai yace mata, "dawo ban sallame ki ba." Dawowa tayi tana faman tura baki tare da ƙunƙunai "yanzu A'ishah Humaira abun da kika ɗaukarwa kanki kenan? Ban hana ku yawon dare ku kai war haka baku dawo gida ba?" "To Baba ai nace maka wajen saurayi na naje, ba fa yawo na je ba ina nan bakin layi." "Shikenan. Allah ya shirya, idan kin shiga ki kawo min abinci na in CI a nan." Wucewa tayi ba tare da ta amsa mishi ba ta shige gidan Yayinda shi kuma ya girgiza kansa a ransa yana takaicin wannan rayuwa na yaranshi, ya rasa yanda zai yi ya gyara su, ko yayi ma a banza tunda uwarsu tana warware wa, duk halin su ɗaya gaba ɗaya babu me kallonsa da wani ƙima, sun riga sun taso ba sa shakkar shi bare tsoron shi, tamkar shi ba mahaifinsu ba saboda yanda suka ɗauke shi, ko ince yanda uwar su tayi musu tarbiyya, Firdausi ce kawai ta fita zakka a cikin su, kuma duk hakan yana faruwa ne kasancewar sa me tsananin haƙuri kuma mara faɗa, yana da sauƙin kai ko kaɗan be iya faɗa ba bare ya ce zai ɗauki mataki a kansu, yana ƙaunar yaranshi shiyasa a kullum fatan shiriya yake musu, duk da abun yana matuƙar damun shi domin yanzu babu inda gidan shi bai zagaya ba a faɗin arean nan, kowa ya san yaran shi basu da tarbiyya, wasu ma don rashin ta ido har taren shi suke yi a hanya suna mishi zancen Yaran shi basu da tarbiyya, ya kan yi kuka wani lokacin saboda be san yanda zai yi ba, yayi nasihan duk wani abu da ya kamata uba yayi; yayi musu, amma uwar su ta ɗaure musu gindi, bai da wani fawa a gidan, bare yanda ta mallake shi sai abun da tace, shiyasa be da kataɓus a gidan, ko ya so ɗaukar mataki mummuna ba ya iyawa, sai dai ya zira musu idanu yana musu addu'ar shiriya, ya san wata rana Allah zai dubi maraicin sa ya shirya mishi su, fatansa kenan a rayuwa. Numfashi kawai ya ja yana ci gaba da jan carbin shi.              *******        Arab kuwa tana shiga gidan ko sallama bata yi ba Yayinda su Inna suna zaune a tsakar gidan a gindin bishiyar Mangwaro da ke dirke a tsakiyar gidan suna shan iska, kasancewar garin akwai zafi sosai. Daga ita har su Ummu suke zaune suna cin abinci a cikin faranti ɗaya, tunda haka suke yi a koyaushe, Inna Harira Mace ce mai tsananin ƙaunar yaranta, akwai sabo mai ƙarfi a tsakanin su, ta ɗauke su tamkar ƙawayenta ne, a rayuwa babu abin da take ɓoye musu nata haka su ma, suna rayuwar su ne cikin ƙaunar juna da tsantsan shaƙuwa a tsakanin su, tun farko haka ta sabar musu cin abinci tare a kwano ɗaya, sai dai idan ɗaya ba ta nan ne ko tayi dogon zango shine zasu ci babu ita, ko kuma su jira ta idan ta dawo su ci tare, amma duk runtsi dole sai kaga cikin su wasu sun ci tare, shiyasa shaƙuwa me ƙarfi ta shiga tsakanin su, su kansu yaran suna ƙaunar junan su matuƙa, kuma basu yarda wasu sun shigo rayuwar su ba, kaf ɗinsu babu mai ƙawa sai junan su, su ne ƙawayen juna su kashe tare su binne tare, shiyasa duk da babu tarbiyya a tare dasu amma suna rayuwar farin ciki a gidan su, basu damu da surutun mutane a kan rayuwar su ba, a ganinsu rayuwar su ne babu wanda ya isa ya hana su tafiyar da ita yanda suke buƙata, duk wanda yace zai taka su sai inda ƙarfin su ya ƙare, kaf ɗinsu basu da haƙuri suna rayuwarsu tamkar ƴan tasha, musamman Arab wacce duk ta fi su sheɗananta, ita abun kunya gaba ta ba shi ba baya ba, ba ta shakkan kowa sannan babu wanda zai mata a duniyar nan bata mayar mishi ba, komin tsufan shi komin girman shi, wannan sun sha a nonon uwar su ne. Domin idan wani ya taɓawa Inna Harira yara abu me sauƙi ne ta bi Mutum har gida ta ci mishi mutunci ta uwa ta uba, kowa ya sansu a kaf anguwan su har da maƙota, ba a taɓa su su ƙyale, an sha yin dambe da Inna a kan yaranta, bata da mutunci ko kaɗan a kan ka taɓa mata Yara, musamman zata saka wandon dambe ta bi ka har gida ku caku. Shiyasa yanzu da yaran nata suka girma wani lokacin tare suke zuwa ayi ta dambe ana faɗa a anguwa, in dai aka tayar da husuma a anguwan nan to kowa ya san ƴan gidan Malam Iro mai kifi ne, su ne ba sa barin anguwan ta zauna lafiya, an sha kaisu police station a kan husuma, su yanzu har sun saba da kowacce fitina ba sa tsoron ko wanne shege, bare yanda kaf ɗinsu Yaran suna da samari a station ɗin, ana kaisu za'a sako su, wani lokacin ma ƴan sandan ba sa jirgawa ko nan da can da su, a wajen zasu kashe maganar, shiyasa ma ƴan anguwan suke musu kirari da gidan Fitina. Wannan kaɗan kenan daga rayuwar iyalan Malam Iro.          Kai tsaye wajen su ta nufa tana cewa, "Inna wai Baba yace a aika mishi da abincin sa waje." "Ga yi can a ƙofar ɗakina ki ɗauka ki kai mishi." Gyalenta ta cire ta jefa a saman tabarman da suke kai, sannan ta nufi coolarn abincin Baban nasu ta ɗauka ta fita da gudu ta kai mishi. Tana shigowa nepa suka ɗauke wuta, dogon tsaki ta ja tana cewa, "ka ga ƴan iskan mutanen nan, daga shigowa kuma sai ɗauke wuta? Ga shi ina son saka caji." "Haka suke yi matsiyata, yanzu suka gama wasa dashi, ga shi kuma sun ɗauke, idan ba wasa ba kuma sai tsakar dare su dasu kawo wutan nan." Cewar Ummu bayan ta haɗiye abincin bakin ta Inna kuma tace, "Auta kunna mana Gen ɗin kafin ki zauna, Allah yasa ma muna da ishashshen mai a ciki." Wucewa tayi ta kunna sannan ta wuce ta wanke hannu ta zo ta zauna, ta saka hannu a abincin tana cewa, "wai Aunty Zahra aina kika samu wannan guy ɗin ne?" Zahra kallonta tayi tace, "wai Salisu? Ba ki sanni dashi bane? Shi ne fa wanda nace miki mun haɗu a bikin gidan Jamila ƴar gidan sanata da muka je mata, Ni ban ma san waye ya nuna mishi gidan mu ba, muna dai waya dashi kusan kwana biyu, sai yau kuma na ganshi ya zo." "To shi ɗan gidan waye ne? Ba ki bani labari ba Mamana?" Inji Inna tana washe baki Dariya suka yi gaba ɗayansu Yayinda Zahra take basu labarin Salisu da aikin da yake yi Itama Arab kuɗin da Tariq ya bata ta ciro ta miƙa wa Inna duka tana cewa, "nima kamun wani nayi wlh, duk da ban san ɗan waye ba amma da alamu yana da fararen." Ta ƙare maganar tana dariya cike da farin ciki Haka su ma suna taya ta Inda Inna tace, "ai na san ki Autana babu wasa a lamarin ki, sai dai idan ba ki fita ba, Allah yayi muku albarka baki ɗaya, haƙiƙa na haifi yara masu farin jini, hakan a jini na yake wlh, Ni na san da haka, duk wani me baƙin ciki sai dai ya mutu, ga shi yara mata suna share min hawaye." Dukkan su murmushi suke yi suna sauraron Innar tasu. Da haka suke ta hira abin su Yayinda Arab ta tashi ita ta nufi bayi, bata jima ba ta fito ta ɗaura alwala ta wuce ɗakinsu ta rama sallan da ake bin ta na magriba da isha'i. Sai ta zauna a ɗakin tana waya da Ibrahim A nan yake sake bata labarin Mutumin da ya samo mata, da komai nashi sai da ya faɗa mata, sannan yace, "ta kira shi su soma magana yanzu." Tace, "a'a sai zuwa gobe." Dariya yayi yace, "ai girman ki ne Besty na, ina jin daɗin jan ajin nan naki, gaskiya ke ta daban ce a cikin mata, har yanzu ban ga kamar ki ba, kina lokaci ƴan mata na, kin fi ƙarfin Yaro sai dai baban Yaro." Itama dariyan tayi tana cewa, "Besty kana fasa min kai da yawa." "Ai matsayin ki ne My Besty, ke ɗin ce ban san yanda zan kwatanta ki ba, amma wlh kin kere duk wata Mace da na sani a rayuwata, Allah ya barmu tare." "Amin." Tayi maganar tana dariya, "shiyasa nake ƙara sonka Besty na." "Nima haka Besty, i love You wujiga-wujiga, ba don kin fi ƙarfi na ba da tuni nayi wuff da ke." Dariya take yi sosai "Allah kuwa My Besty, yanzu meye tukuici na?" "Oh Besty! Ba ka yin abu don Allah fa na lura?" Kashe murya yayi tare da cewa, "haba dai, Ni na isa? Ai duk abun da zan miki don Allah ne, kin san Ni na sanki, Ni da ke ba ta ɓaci, Allah ne ya haɗa jinin mu, abun da kike so shi nake so, haka kuma abun da kike ƙi shi nake ƙi, ke ma kin sani ai.. kawai dai kwaɗayin nawa ne ya tashi wlh." "Uhmm shikenan. Let's meet tomorrow." "Ok. But ba ki bani labarin Mutumin da kuka haɗu ɗazu ba?" "Ai yanzu zan faɗa maka ka san ba na ɓoye maka komai." Daga nan ta ba shi labarin yanda suka yi. Basu jima suna wayan ba ta katse sabida ganin baƙuwar number tana kiran ta. Bayan ta ɗauka sallaman Tariq ya doki kunnen ta, rage murya tayi tana kwanciya a kan gadonta, yayinda ta juya baya ganin Ummu da Zahra sun shigo ɗakin. Haka tayi ta wayanta baza ka taɓa cewa waya take yi ba. Sun raba dare suna tare da Tariq before su yi sallama ta kwanta A time ɗin su Ummu su ma har sun yi barci.          Zuwa washe gari kuma suka ta fi makaranta. Dayake ita Arab text suke yi a school, saura two weeks su fara Exams, daga nan kuma sai su shiga S.S 3. Ƙarfe sha biyu ta dawo gida A lokacin Baba yana gida domin dawowar shi kenan daga wajen suyan kifin sa; yake sanar da Inna halin da Firdausi take ciki. Mijinta Nafi'u ya kira shi yace mishi, "bata da lafiya, yanzu haka suna asibiti an kwantar da ita, duk da dai yace jikin da sauƙi yanzu." "To Allah ya sauwaƙe." Cewar Inna tana wucewa cikin kichen tare da cewa, "Auta har kin dawo?" "Eh Inna." Ta furta itama tana shigowa tare da zama a kan kujeran zuƙuno, sai kuma ta kalli Babansu tace, "sannu Baba." "Yauwa Aisha Humaira. An dawo?" Fitowar Inna tana kallonta tace, "wai ba karatun ne kika dawo da wuri?" "Akwai mana, muna yin text ne kuma ba wani abu ake yi ba shiyasa na dawo." Baba ya kalli Innan yana cewa, "yanzu babu wanda zai je a cikin ku ne? Ai ya kamata ko ɗaya daga cikin yaran ne ya je ya zauna da ita, itama zata ji daɗi idan ta ga ƴan uwa, Mijin yace min idan da hali wata ta zo ta zauna da ita tunda kullum damuwar ta yaran nan ne, ta ce a tura mata ɗaya a ciki." Mitsitstsike baki Inna tayi da cewa, "a tura wa? Ai babu inda zasu je tunda kowacce ba zaman banza take yi ba, in ba iya shege ba ai ta san babu wanda zai je yayi mata bauta tunda ta san suna makaranta, kuma sana'ar nawa ubanta zai yi min?" Shiru Baba yayi be iya cewa komai ba illa kallonta da yake yi, sai kuma ya girgiza kanshi sabida takaicin Inna Arab tace, "Inna ni zan je domin dama ina son zuwa, yakamata ace ko sau ɗaya ne mun je amma har yanzu bamu ƙara zuwa gidanta ba tun auren." "To makarantar naki fa Auta? A'a babu inda za ki je." "Allah Inna zan je, ai Ni nace miki ina son zuwa, kuma makaranta bani da matsala da hakan tunda Exams ya rage kuma ba yanzu zamu yi ba, har zan je in dawo, zan mata kwana biyu sai in dawo." Baba washe baki yayi yace, "yauwa A'isha, ai zata ji daɗi idan ta ganku, to yaushe za ki tafi in ba ki kuɗin mota?" "Ka bar shi kawai Baba ina da kuɗi, idan rana tayi sanyi sai in wuce." Inna tace, "don dai kin matsa ne babu yanda zan yi amma wlh da baza ki je ba, har wani ciwon ne sai an je an ganta?" Sai ta ja tsaki tana wucewa Baba kuwa girgiza kansa kawai yayi, sai kuma ya kalli Arab da ta miƙe zata wuce yace, "bari in koma wajen sana'a na, kafin ki tafi zan dawo sai muyi sallama." "Sai ka ce wani tsiya za ka bata idan ka dawo ɗin? Aikin banza aikin hofi." Inna tafaɗa bayan ta fito daga ɗaki tana dallawa Baban harara Baba kuma bai ce komai ba ya wuce ya tafi "Arab ki zo ki ɗibi abincinki ki ci, sai ki zo ki amso min ƙanƙara wajen Lantana in sa a kunun nan. Na san yanzu zasu dawo tunda sun ce ƙarfe ɗaya zasu gama karatun." "To ina zuwa." Arab tafaɗa daga cikin ɗaki, kayan makarantarta ta cire ta saka wani doguwar rigan Abaya wanda ya fito mata da kyakkyawar shafe ɗin jikinta, sosai rigan ta kama ta saboda yanda aka matse mata dai-dai jikinta, sai ta ɗaura ɗankwalin Abayan a saman kanta da ke ɗauke da ƙananun kitso da aka yi mata, sun zubo har kafaɗunta, kana gani ka san ta haɗa jiɓi da Fulani saboda yanda gashin suka nannaɗe gunin sha'awa, sai dai ƙarshen kitson duk ya tsefe duk da kuwa kasancewar kwana biyu kenan da Ummu tayi mata, kasancewar ita tana son kitso shiyasa ko yaushe za ka ganshi a kanta duk da gashin nata ba ya zama da kitso, yanzu idan ma ta bar shi kafin sati ya tsefe da kanshi don da kanshi yake tugewa, shiyasa bata da wahalan ta sake wani kitson tunda tana da masu yin mata, har Inna tana yin mata, ita kaɗai ce me son kitso a cikin su, don su Zahra ma bai dame su ba sun fi son barin kansu a haka tunda su ma nasu gashin ba ya son kitso, ko sun yi warware wa yake yi, duk Innarsu suka biyo. Flat shoes ta saka a ƙafanta sannan ta fito Inna tace, "nace ki bari ki ci abinci sai ki wuce." "A'a ba na jin yunwa, bari in amso miki, idan su Aunty Ummu sun dawo sai mu ci tare." "To." Innar tafaɗa tana wucewa kichen ta sauke abincin siyarwan da take yiwa su Ummun Itama kuma Arab ta sa kai ta fice. Bata jima ba ta dawo tunda a maƙotan su Lantanan take Time ɗin su Ummu sun shigo su ma. Shiyasa suka zauna suka ci abincin tare A nan Arab take sanar da su, "zata je gidan Aunty Firdausi." Zahra tace, "ai da na bi ki kuwa, amma babu hali tunda karatu yayi zafi, sai dai ki gaishe ta, nima zan kira waya in Yi mata ya jikin." Itama Ummu tace, "Auta ki gaishe ta don Allah, ko zuwa weekend ne zamu zo, amma yaushe za ki dawo?" "Kwana biyu kawai zan yi, tunda kun ce zaku zo sai in tsaya mu dawo tare." "Eh hakan yayi, Allah ya kaimu Asabar zamu zo sai mu dawo a ranan." Inna dai na jinsu bata ce musu komai ba. Sai da ta gama abun da take yi sannan tace, "ga abincin nan na gama don Allah ku tashi ku wuce, kunga har biyu tayi." "To Inna." Duk suka amsa mata Yayinda Zahra CE ta soma tashi tayi alwala ta shige ɗaki Itama Ummu alwalan tayi; tayi sallan sannan suka shirya suka fita Arab tace, "Inna bari in Yi wanka kawai in wuce, ki bani dubu goma a kuɗin jiya saboda babu kuɗi a hannu na." "Ki shiga ɗaki ƙasan Matashi na suna nan na ajiye a wajen." "To." Tace tana wucewa. Sai da ta ɗauki kuɗin ta je ta saka a jaka sannan tayi wanka ta shirya. Riga da wando ta saka masu tsantsi, rigan milk color da flowers a dai-dai setting ƙirjin ta da aka yi da kalan maroon color kalan wandon, wanda shima ƙasan wandon aka yi flowers da milk color, kayan sun yi mata kyau ainun sabida kasancewar ta me sura me kyau wanda duk namijin da ya kalle ta sai kyawunta ya bizge shi, bare uwa uba yayi arba da kyakykyawar cuty face ɗinta, fuskar nan nata ta sha makeup me ɗaukan hankali, bakinta sai shaining yake yi, gyalen kayan ta ɗauka kalan milk ta yafa a kanta sannan ta jefa jelan a gefe da gefen kafaɗunta, sai ta saka takalmi masu shegen tsini white color, sai da ta jefa chewing gum a bakinta domin ita mayyar cin chewing gum ne, ya zama sabon ta ba ta rabo dashi, Hangbag ɗinta ta ɗauka na takalmin shima kalan fari ta rataya, sannan ta fito cikin yauƙinta ta wuce ɗakin Inna Inna na ganinta ta washe baki saboda farin ciki, "ga farar zinariya alkyabbar Mata, kin kerewa kowacce Mace sai dai su biyo bayan ki, kinga yanda kika haɗu kuwa?" Dariya tayi tana taunan chewing gum ɗinta ƙas-ƙas-ƙas, sai tace, "na san haka Innata, amma nayi  zam-zam ko babu wata mishkila?" Ta ƙare maganar tana juyawa a gaban Innar Inna tace, "babu abun da yayi saura, ai ke me kyau ce Autana, ko ba ki yi kwalliya ba komai yin miki kyau yake yi, Allah yasa ki samo mana wani me gwaɓi-gwaɓi wanda zai kai ni Makka da Madinah." Arab tayi dariya tace, "Inna kar ki damu insha Allahu zan cika miki burin ki wata rana." "Kai Allah ya amsa addu'ar ki Autana, amma ki kula fa don bazan so wani abu ya same ki ba, Allah ya tsare." "Amin Inna." Sai tayi dariya tana cewa, "to Inna ba ki ce in gaishe da Aunty Firdausin ba?" Taɓe baki tayi tace, "to har sai na ce? Ai ta san ina gaishe ta". Sosai Arab take dariya a wannan lokacin, tace, "Innarmu na Aunty, Allah ya bar ku tare, zan ce kina gaishe ta sosai, zan biya sai in Yi sallama da Baba a kasuwan. Babu wani abun da zan kai mata ne?" "To me nake dashi da zan ba ki? Gaisuwar ma ta isa." "To Inna na tafi, bye." Sannan ta fice ta shiga ɗakin su, jakarta da ta zuba kayan sakawanta ta ɗauka, ƙaramar Trolley ne, ta janyo ta fito. Har waje Inna ta raka ta suka sake sallama sannan ta tafi. [07/07, 11:29 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA HUƊU* _______________ *KADUNA STATE*             Bayan Arab ta sauka a tashan Kawo da ke Kaduna; sai ta kira Numban Nafi'u tunda sun san da zuwanta, time ɗin da Baba ya je kasuwa ya kira ya sanar mishi, "Arab na nan zuwa." Babu jimawa kuwa sai ga Nafi'u ya taho a motan shi, bai sha wahalar hango ta ba, sai ya faka motan nashi ya fito ya nufi inda take tsaye riƙe da waya a hannu tana faman latsawa, kanta na sunkuye tana tauna chewing gum ɗin da ke bakinta. Yana isowa yayi mata sallama Sai ta ɗago kai tana kallonsa da manyan idanuwanta da suka sha tozali suka sake haske tarr masu ɗaukar hankali, murmushi ta saki tace, "Yayanmu." "Na'am Autanmu. Barka da zuwa." Dariya tayi sai tace, "yauwa. Ina wuni?" "Lafiya ƙalau, ya mutanen gidan?" "Alhamdulillah duk suna gaishe ku." "Masha Allah muna amsawa. Mu je to ga motan can, kawo akwatin." Ya saka hannu ya karɓa sannan suka taho wajen motan suna magana suna dariya. Bayan sun shiga ne yake cewa, "bari in kai ki gida inyaso sai in je ɗauko Auntyn naki tunda an sallame ta ma." "A'a Yaya, mu je tare sai ka ɗauko ta." Murmushi yayi yace, "ke da kika sha hanya? Ki bari kawai in ɗauko ta ɗin kar ki sake shan wahala, suna tare da Ummana ne ma, bari in kai ki sai in je in ɗauko su." "Ok shikenan." Daga haka suka wuce gidan Nafi'un. Ƙaramin gida ne flat ya gina abun shi, bai jima da tarewa ba bayan auren da suka yi. Mahaifiyarsa kuma tana babban gidan su ne tare da kishiyoyinta; tunda Matan Baban Nafi'u su huɗu ne, kuma Nafi'un shi ne kaɗai ɗa a wajen Mahaifiyar sa. Bayan ya kaita ya sauke ta tare da bata makullin gidan, sai ya tafi asibitin Ita kuma ta shige ciki abun ta, a falo ta samu waje ta zauna tana zare gyalenta ta ajiye. Tsarin gidan take bi da kallo tunda yau ne zuwanta na farko, lokacin da suka kawo Firdausi a babban gidansu aka soma ajiye ta before ya gama ginin sa, babu laifi gidan ya ɗan birge ta, but sai yatsina fuska take yi tana tunanin, "idan ita ce baza ta iya zama a ciki ba, gida kamar kurkuku wai ace a nan zaka ƙare rayuwarka." Sai ta sake taɓe baki tana tashi tsaye ta nufi ƙofofin da ta gani, ta soma buɗewa tana leƙawa, da kichen ne da Toilet, sai kuma ɗakuna biyu masu kallon juna, ɗaya na Nafi'u ɗaya na Firdausi. Ɗakin Firdausin ta shige da akwatin ta, ta shiga toilet ta ɗaura alwalan magriba da aka kira, kasancewar bata yi sallan la'asar ba sai ta haɗa Tana cikin sallan ne suka dawo gidan. Daga Firdausi sai Nafi'u tunda sai da ya wuce da Ummansa gida sannan suka nufi nasu gidan. Kasancewar ya faɗa ma Umman nashi, "akwai ƙanwarta ta zo." Shiyasa tace, "to ya sauke ta a gida kawai." Jikin Firdausi da sauƙi sosai, dama ciki ne take dashi kusan watanni biyar kenan, kuma tunda ya fara girma sai ciwo ya sako ta a gaba, ko lokacin da yake ƙarami bata sha wahala irin yanzu ba, sosai take ciwo shi ne har aka dangana ga asibiti, kuma ta tashi hankalin ta tana kukan, "tana son ganin ƴan uwanta ko Innarsu." Gaba ɗaya hankalin ta a tashe yake musamman yanda suka yi watsi da ita kusan seven months basu zo sun ganta ba Dalilin da yasa Nafi'u ya kira Baba ya sanar mishi kenan. Kuma shi kansa bai yi tunanin zasu iya zuwa ba tunda ya san Innarsu ba ta son shi, amma kuma sai ga shi Arab ta zo Gaskiya sun yi murnan ganin ta sosai. Musamman sanda Firdausi ta shiga ɗakinta ta hange ta, ai sai ta washe baki tsaban farin ciki, bata taɓa yarda da gaske Nafi'u yake mata ba wlh, domin ta san ko kowa zai zo Arab baza ta zo ba, in fact ma Inna baza ta barta ba tunda ta fi ƙaunar Arab, baza ta so ta matsa a kusa da ita ba, bare ta san halin Arab sai abun da taga dama take yi, sai ga shi kuma ta ganta a ɗakinta. Da sauri ta nufe ta tana rungume ta tare da cewa, "Auta ke ce? Ashe za ki zo?" Sai ga hawaye sharr sun soma bin kuncinta Ita kuma Arab kallonta kawai take yi saboda yanda ta sauya mata, ta zama wata ƙatuwar Mata, ko don tana da ciki ne oho. Sai kawai ta ɗage kafaɗa alamun hakan bai dame ta ba, dariya tayi tace, "Aunty da kuka kuma? Kai! kai! Kar kiyi abun kunya a gabar ƙanwar ki mana." Yanda tayi maganar ne dole Firdausi tayi dariya tana kai hannunta ta ɗan buge ta, sai tace, "kin raina ni ko?" Murmushi ita kuma tayi tace, "a'a ina girmama ki, ke ce fa babbar Yaya, ina Ni ina raina ki?" Still dariyan Firdausi tayi sai tace, "idan na biye miki ko; za ki mayar dani mahaukaciya, ya su Inna da kowa da kowa? Ina su Ummu meyasa baku zo tare ba?" "Hhmm ke ma kin san Inna baza ta barmu gaba ɗaya mu taho ba, da ya ya ta bar Ni nima? Sai dai sun ce suna gaishe ki sosai, su Aunty Ummu ma zasu taho ranan Asabar sai mu koma tare." Sai Firdausin ta washe baki cikin farin ciki tace, "kai naji daɗi, Allah ya kaimu rai da lafiya, gaskiya kin faranta min da zuwan nan naki, wlh duk naji babu daɗi yanda ku ka manta dani, sai nayi tunanin ko Inna ne ta hana ku zuwa tunda ko a waya ba kwa nema na." "Ayya ba haka bane Aunty, kin san makaranta ga kuma sana'a, so bamu da lokacin kanmu." "Shi ne kuma har da lokacin ƴar uwanku baku dashi? Kar ki manta Ni fa ƴar uwanku ce." Tayi maganar cikin rauni har da hawaye suke son zubo mata Sai dai sallaman Nafi'u ne ya tsayar da Arab yin magana. Ya shigo ciki bayan sun amsa mishi, hannunsa da ledoji har guda uku yace, "to Autanmu ga abinci na siyo miki tunda me yi ba lafiya, ke kuma daga baƙunta baza mu wahalar da ke ba." Dariya tayi tace, "Ayya Yayanmu, wlh da baka siyo ba ka bar Ni inyi mana, ai ba wani abu bane don na shiga kichen." "A'a, gwara dai ki huta tunda yanzu kika zo." Sai ya kalli Firdausi yace, "kin yi sallah ne?" Girgiza mishi kai tayi da faɗin, "a'a." "To tashi kiyi mana sai ki ci abincin ke ma, kin san abun da likita yace ai. Bari inje falo idan kun gama sai ku same Ni." "To." Firdausi ta amsa mishi Sannan ya fice a ɗakin Kallonta Firdausi tayi tace, "buɗe ledan ki duba abun da ke ciki, bari in Yi sallah." "Ok." Arab ta furta tana ajiye wayan da ke hannunta, sannan ta jawo ledojin ta soma dubawa. Takeaways ne a ɗaya, sai kuma fruits sannan ledan tsire. Tana ganin tsiren ta ciro ta hau ci tana kaɗa kanta Firdausi da ta fito ta ganta a haka sai tayi dariya tace, "har yanzu kina nan da halin ki Auta, baza ki bar kwaɗayi ba." "To me ya fi hakan daɗi? Kowa fa na son daɗi Aunty sai dai idan bai samu ba, Ni duk abun da zai sa Ni jindaɗi a rayuwata shi nake yi bazan ƙwari kaina ba." Murmushi kawai tayi mata sai ta saka Hijab ta tayar da sallah Lokacin wayan Arab tayi ƙara, ganin sunan Besty ɗinta sai ta ɗauka tana cewa, "Ya ne Besty?" "Bazan amsa ba tunda kika yi tafiya ba ki sanar dani ba, na zo gida Zahra take sanar dani kina Kaduna." Dariya tayi tace, "oh! Sorry my Besty, wlh I have not forgotten you, right now I want to call you." Yace, "ai kin kyauta, kin san ba na fushi da ke, to ya Kadunan? Ya su Aunty Firdausin?" "Lafiya ƙalau. Hope kaima kana lafiya?" "Uhmm ina fa lafiya kin tafi kin bar Ni cikin maraichi, bayan kin san yau akwai alƙawari a tsakanin mu." Dariya tayi sosai tana siɗe hannunta, sai ta sauke ledan tsiren daga jikinta ta ajiye ma Firdausi, still tana ci gaba da wayan da cewa, "i Know. Amma ka san bazan manta da kai ba, Let me be with you when I return." "Fine. Ya na iya haka nan zan jira, but zan yi kewar ki sosai wlh, ba ki ga yanda ake tambayar ki bane yau a wajen sana'a, kowa yana tambayana ina kika je? Ni kuma sai na kira wayanki maybe network problem did not enter, after na je gidan ku ake faɗa min kin tafi KD." Taɓe baki tayi tace, "you just delete them and I don't have time for them. Ya labari?" Dariya yayi yace, "ok Gimbiyyar Mata, girman ki ne ai. But labari ke za ki bani, You have not spoken to Alhaji Bashir yet?" Yatsina fuska tayi sabida kallon da Firdausi take mata. Sai ta kawar da kanta tana kwanciya a kan gadon tare da cewa, "I spoke to him on WhatsApp, but I have not been able to go online again." "Haba Besty kina wasa da Mutumin nan ko? Zuwa yanzu yakamata ace har kun gama fahimtar juna, na san ki ba kya wasa da irin Alhazawan nan, amma da alamu har yanzu ba ki san ko shi waye bane." Murmushi tayi me sauti sai tace, "ka bari zamu yi maganar daga baya, yanzu ga Tariq nan yana kira na zan amsa call." "Ok when you're done I'll call you." Daga haka suka yi sallama ya kashe wayan "Kar ki ɗauki wayan nan please ki bari ki gama." Firdausi tayi maganar tana kallonta Itama sai ta ɗago tana kallonta. Sai kuma ta ɗage kafaɗa before tace, "ok." Ajiye wayan tayi ta sauko ƙasan inda Firdausi ke zaune tana cin abinci. Itama ta buɗe ɗaya takeaway ɗin ta sanya Robber spoon ɗin tana ci Sai da Firdausi ta ɗago ta kalle ta sannan ta kawar da kanta tana girgiza shi, ko kaɗan halayen ƙanninta ba sa mata daɗi, tana shiga ƙunci da baƙin ciki duk sanda ta tuna yanda suke rayuwarsu kuma bata da halin hana su, musamman ma Arab wacce take tsananin tausaya mata kasancewarta ƙaramar yarinya amma ta fi su hatsabibanci, ba ta jin magana ko kaɗan, yanzu tana buɗe baki don tayi mata nasiha zata iya jawowa kanta, sai ma tace mata, "zata koma gida tunda ita ba wa'azi ta zo tayi mata ba." Shiyasa tayi shiru ta ƙyale ta. Bayan ta gama cin abincin sai ta miƙe da gudan takeaway ɗin, sai drinks guda biyu tace, "idan kin gama muna falo, bari in kaiwa Nafi'u abincin shima ya ci."        "Ok." Tace mata kawai tana ci gaba da cin abincinta. Bayan fitan ta ne ta ɗauki wayan taga Tariq yayi mata three missed calls. Sai bata bi kiran ba ta miƙe ta shiga toilet. Bakinta ta kuskure sannan ta fito ta ɗauki wayanta zata fice sai kuma kiran Tariq ɗin ya sake shigowa. Zama tayi a bakin gadon tana amsa call ɗin. Sallama yayi mata ta amsa "Baby ina kika shige ne ina ta kiran wayan ki but ba ki yi peacking ba?" Ɗan muskuta zamanta tayi tana kwanciya sosai a kan gadon. A hankali cikin yanga tace, "ina cin abinci ne." "Oh. Har kin sa na ji sanyi a raina, nayi tunanin laifi nayi ko kuma babu lafiya. Yau ban ganki a wajen suyan wara ba? Allah yasa lafiya?" "Ƙalau. I just Traveling." "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!." Ya furta cikin wani irin yanayi da ya faɗarwa da Arab da gaba Da sauri ta furta, "lafiya dai?" Sai da ya ɗan ja numfashi before yace, "ina fa lafiya, shikenan Baby bazan samu ganin ki ba kin yi tafiya?" "Wai saboda haka ne kake jan wannan salatin?" "Eh mana. Ai babu abun da zai ɗaga min hankali a yanzu sama da rashin ki a tare da Ni, wlh ba ki san yanda na kwana da tunaninki bane jiya, na ƙosa yau tayi in zo in ga kyakykyawar fuskarki but sai ga shi na rasa ki, kuma kina faɗa min kin yi tafiya, yanzu shikenan sai yaushe zan ganki?" Murmushinta me kyau tayi kafin tace, "kana da abin dariya gaskiya, but I will be back soon, only four days." "Ki ce zan mutu kafin lokacin nan, Please kar kiyi min wannan horon na rashin ganinki, zan iya mutuwa ba ki san yanda na kamu da soyayyar ki ba ko? Please Aisha help me to give me a chance to show you how much I love you, ki bani dama don Allah in aure ki wlh I really love you." "Meyasa kake min maganar aure yanzu daga haɗuwar mu jiya? Ko nace maka zan yi aure yanzu ne?" "A'a, amma Baby ki fahimce Ni, ƙaunar da nake miki ne bazan iya jure tsawon lokaci ba na tare da ke ba, zan so ace Ni na mallake ki a matsayin Mata..." Katse shi tayi da faɗin, "kaga Malam Ni babu aure a gabana a yanzu, a tunaninka daga haɗuwar mu sai kawai in ba ka damar da zaka iya aure na? Duka-duka nawa nake da zan yi aure yanzu? Don haka ka dena min maganar aure yanzu sabida babu shi a raina kuma ban shirya yi yanzu ba, now ina gaɓar yarintana ban shirya tsufa da wuri ba, and sannan ba na son takura gaskiya idan ka san wannan maganar zaka riƙa min kar ka sake kira na." Sai ta ja tsaki ta kashe kiran. Ai kuwa ko ajiye wayan bata yi ba ya sake kira, kamar baza ta ɗauka ba sai kuma ta ɗaga Cikin sauri da tashin hankali da ya nuna a kan muryansa yake magana, "don Allah kiyi haƙuri, ban san haka zai ɓata miki rai ba, but I will not do it again." Yanda ta ji muryansa kamar zai yi kuka don har idanuwansa sun soma kaɗawa tare da ruwan hawaye, duk ya susuce yana ta roƙon ta, shiyasa tace, "is ok ya wuce." Ajiyan zuciya ya sauke me ƙarfi tare da furta, "thanks Baby, kiyi haƙuri don Allah, Ina sonki." "Ok. Ni zan kwanta, bye." Bata jira cewarsa ba ta katse kiran Sai ya bi wayan da kallo zuciyarsa babu daɗi, haƙiƙa yana tsananin ƙaunar Arab a zuciyarsa, tsaban ƙaunar da yake mata ya rasa inda ke mishi daɗi a yanzu, bai san haka take ba sai a jiya da ya soma mu'amala da ita, yayinda tarin ƙaunar ta me tsanani ya ninku a zuciyarsa wanda yana jin bazai taɓa iya rayuwa ba tare da ita ba, dole ko ta halin ƙa-ƙa ne ya mallake ta ta zama tashi ta har abada. Numfashi ya sauke yana ajiye wayan a saman kujeran da yake zaune, a hankali ya furta, "na zama mahaukaci a kan ƙaunar ki A'isha, bazan taɓa samun sukuni ba har sai kin zama mallaki na, ina sonki da yawa!" Sai ya kama setting ƙirjin sa yana shafawa a hankali tare da lumshe idanuwansa.               Ita kuwa tana kwance bata tashi a wurin ba sai ga Firdausi ta shigo Tace mata, "wai kina nan ba ki yi barci ba? I thought kin Yi barci tunda na ji ki shiru." "No ina nan ban kwanta ba." "Ok to ki kulle ƙofan, Ni zan wuce ɗakin Nafi'u sai in kwanta a can, sai da safe." "To." Kaɗai ta furta tana miƙewa daga kan gadon. Sai ta bi bayan Firdausin bayan ta fita ta kulle ƙofan. Toilet ta shiga taYi wanka sannan ta ɗaura alwala ta fito, bayan ta gama shiryawa ta sanya kayan barcin ta riga da wando sannan ta rama sallan isha'i da bata yi ba. After she's finished sai ta kashe fitila ta kwanta, a nan ne ta ɗauki wayanta tana ta faman latse-latse. Bata yi barci ba har kusan ƙarfe ɗaya, tana kan WhatsApp tana hira da samarin ta, ciki kuwa har da Alh. Bashir da suke charting dashi, tamkar sun daɗe da sanin juna yanda ta saki jiki suna ta hira. A ranan basu kwanta ba sai da ta ci kuɗin shi, don account yace, "ta tura mishi." Tana yin mishi sending ya tura mata 50k a account ɗinta, farin ciki ne ya cika ta sai murna take yi Yace mata, "yana buƙatar su haɗu, bazai iya jira har sai ya zo Zaria ba, amma ta biyo shi Abuja inda yake zaune."         Bata ja lokaci ba ta amince mishi zata zo, but sai dai tace mishi, "ya bari zuwa Sunday sabida yanzu tayi tafiya." Yace, "ba komai."     Haka suka jima suna chart daga ƙarshe ta tura mishi hotunan ta sannan ta sauka ta kashe wayan, bata jira ma reply ɗinsa ba. A ranan a cikin farin ciki ta kwana, ta tabbata zata samu kuɗi a hannun mutumin nan, har ta lissafa irin fantamawan da zata yi, yanzu burin ta zai cika, dole ne ta wanke shi iya wanka har sai ta mallaki mota a hannun sa, burinta kenan. A haka barci ya sure ta cikin tunane-tunane da mafarkin kuɗin da zata samu. [07/07, 11:30 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍          *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA BIYAR* _______________ Washe gari Arab ita tayi musu Breakfast suka ci gaba ɗayan su Ganin jikin Firdausi da sauƙi, sannan ga Arab a tare da ita shiyasa Nafi'u ya fita wajen aiki ya bar su Bayan fitan shi ne Arab ta wuce ɗakin Firdausin tayi wanka ta shirya cikin doguwar rigan atamfa fitet gwon. Sosai rigan ta zauna mata ɗas a jikinta ta fito mata da duk wata sura da Allah ya bata. Bata ɗaura ɗankwali ba sai ta zauna a bakin gado ta ɗauki wayanta ta kunna. Saƙonni ne suka soma shigo mata bayan ɗan wani lokaci da wayan ta gama daidaita, yawanci duk na samarinta ne sai na Ibrahim. Na shi ta soma buɗewa ta duba yana mata korafin, "meyasa ta kashe wayanta?" Bata yi mishi reply ba sai ta soma duba messages ɗin Alh. Bashir da taga ya turo mata. Murmushi ne ya bayyana a kan kyakkyawar fuskarta tana yi tana karantawa, ta san dama za'a rina dole zai susuce a kan hotunan da ta tura mishi, hakan take so dama. Wani irin shu'umin murmushi ta saki har da sautin shi, sai ta cije leɓen ƙasan bakinta tana wani turo baki, still akwai murmushin a kan fuskarta take ta faman karanta zafafan saƙonnin shi, har da korafinsa shima domin jin wayanta a rufe. Yana sanar mata ma, "bazai iya jurewa har tsawon wannan lokacin batare da ya kasance da kyakykyawa irinta ba, shi bai san ma haka take ba wlh." Kalamansa suna nuni da cewa ya gama susucewa da kyawun ta, hakan shi ne burin ta dama, yanzu ne wasan zai fara. Sai kawai ta danna airplane mode a wayan tare da ajiyewa, sai ta miƙe ta fice tana rera waƙar Isa Ayagi na "So ƙaddarar zuciya!" Har da murza jiki tsaban farin cikin ya kai mata Firdausi da ke zaune a falo da Cup ɗin tea a hannunta, duk da yanzu suka gama karin safe amma har ta haɗa wani tea ɗin tana sha, sabida ba ta jure yunwa tunda ta samu cikin nan. Tun fitowarta ta ɗaga kai tana kallonta Ita kuwa ko a jikinta tunda dama ba kunya ne a idanunta ba, rawan ta kawai take yi tana dariya sosai. A haka ta iso kujeran da Firdausi ke zaune ta zauna a kusa da ita cikin farin ciki da walwala wadda hakan ya nuna a kan fuskarta Firdausi tace, "Auta wannan murna haka me ya faru?" Kafaɗa ta ɗage da faɗin, "nothing. It was just something I remembered." "Ok." Sai ta shafa kanta tana sake kallon Firdausin da cewa, "za ki yi min kitso Aunty, kaina duk ya kwance." Ɗan waro ido Firdausin tayi da cewa, "haba Auta, Ni da ban da lafiya ai bazan iya ba, ko kin manta jinya kika zo?" Dariya tayi, sai kuma tace, "na manta wlh. Shikenan idan na koma sai in Yi, or when Aunty Ummu arrives she offers it to me." Ta ƙare maganar tana tashi ta ɗauko remote control da ke gaban t.v, and she came back sat down and started changing channels. Da haka suke hira da Firdausi zuwa ɗan wani lokaci sannan ta tashi tace, "bari ta ɗaura musu girki." Tana sane ta kashe wayanta saboda Alh. Bashir, tana son ta sake kama zuciyarshi don sai ta gama jan mishi aji before ta sake kula shi, haka tsarin ta yake, ba kowa ke samun Arab cikin sauƙi ba, yarinya ce me shegen wayau da shiga rai, musamman yanda kyawunta ke fuskar mutane shiyasa take da sauƙin kama zuciyar ko waye. Sai dai komai nata tana yi ne cikin class, She is not easy to deal with in her people, abu ɗaya ne yake saurin kama zuciyarta shi ne kuɗi, idan kana da kuɗi zaka ga tarairaya da ƙauna a wurinta, sai dai tana yin komai ne duk saboda kuɗi, tana da taurin zuciya wanda ba kowa ne zai iya shigan ta ba, duk yanda zata nuna maka ƙauna na ɗan lokaci kaɗan ne zata watsar da kai, ko kaɗan soyayya ba ta burge ta, koda wasa bata taɓa yi ba, in fact ma har yanzu ita bata yarda akwai wani SO ba, already ta sa a ranta komai kuɗi yana yi, farin ciki ne a soyayya, to ta tabbata duk sanda ta samu hamshaqin me kuɗi wanda take mafarkin samu a koda yaushe zata aure shi, shi ne kawai zai kawo mata farin ciki da soyayya a ranta, kuma har yanzu idanunta basu nuna mata wannan zaɓin ran nata ba, domin duk samarinta da ta taɓa yi kala-kalan masu kuɗi; har yanzu bata samu me kuɗin da zai iya siye zuciyarta ba bare har tayi marmarin auren shi. Sannan ita a rayuwa ba ta ƙaunar aure yanzu sabida gani take yi yanzu ta soma ɗiban duniyarta da tsinke, baza ta iya kashe kanta tun da ƙuruciyarta ba ta tarawa kanta matsalolin aure ba, tana da burika da yawa sai ta cika su kafin zata zaɓo namijin da ya cancanta ya mallake ta, sannan baya ga kuɗi tana son namijin da yayi suna a duniya ko iya Nigeria, wanda dai ya zama shahararre ne shi, irin kalan Mazan da take buƙata kenan.             Sai ku bi Ni masoya mu gani burin Arab zai cika ko kuwa? Wanne irin ƙalubale zata fuskanta sakamakon duniya da ke ruɗanta? Uhmm bamu fara ba fa, ku gyara zama kawai FAN'S 😍. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️                     *ABUJA STATE*             Kwance yake a bakin tafkin Swimming pool, a kan kujera mai kamar gado na katako, babban garden ne wajen wanda aka ƙawata ko'ina da green grass. Yana sanye da Singlet fari sol tare da gajeren wando kalan kore da ɗige-ɗigen ja. Yayinda ya ɗaura dantsen hannunsa ɗaya a saman goshinsa, ɗaya hannun kuma yana riƙe da wayansa yana kallo, inda kyakykyawar murmushi ya ƙawatu a saman beauty face ɗinsa, ga dukkan alamu ya shagalu da kallon fuskar wayan ba tare da ya ankare da zuwan wata budurwa ba Ita kam tana sanye da riga da wando matsatstsu da suka fito mata da halittun jikinta, sai ta saka baƙin gyale ta ɗaura a saman gashin attachment ɗinta da aka yi mata kwalliya dashi. Zuwan ta wurin ba tare da ya san da ita ba sai ta sanya hannu ta zare wayan daga hannunsa Yayinda shi kuma a lokacin sai yayi firgigit tamkar ya dawo a cikin hayyacin sa yana bin ta da kallo, kana kuma ya tashi zaune fuskarsa tana haɗewa lokaci ɗaya murmushin da ke kai ya ɓace ɓat Kafin ma yayi magana sai ita ta ɗago kai a fusace kasancewar ganin wata kyakkyawar yarinya da yake kallo a jikin wayan, wanda hakan ne ya ɗauke mishi hankali har bai san da zuwanta wajen ba. Hakan yasa zuciyarta tayi baƙi nan da nan fushi da kishi suka bayyana a kan fuskarta, inda ta kalle shi cikin wani irin yanayi tace, "What is this Malik? Who is this girl? What is your connection with her?" Ɗan waro idanusa yayi yana mata kallon mamaki, ba tare da ya amsa mata tambayoyin nata ba kuma sai ya ɗauke kanshi yana sake haɗe rai sosai Hakan ya sake fusata ta cikin tsawa da ɗaga murya ta sake cewa, "Malik, are you talking to you and keeping me quiet? I said who is this girl? Ka bani amsa idan ba haka ba wlh zan yi abin da zaka yi dana-sanin sani na." "Kiyi abun da za ki iya kinji ko? And bazan faɗa ko wace ce ba, dalla bani wayana." "Bazan bayar ba." Tayi maganar cikin tsiwa still a fusace wadda har ƙwalla sun cika mata idanu Shima a fusacen a yanzu yace, "Ke Nawwara ba na wasa da ke, i said give me the phone or..." Ta katse shi da sauri cikin muryan kuka da cewa, "wato amanata kake ci ko? Wlh tallahi ba ka isa ba Malik, baka isa ka wulaƙanta Ni ba, kayi kaɗan." Ta ƙare maganar cikin buɗe mishi idanu wadda a lokaci ɗaya ta fashe da kuka cikin ƙunan rai da ke nuni da tsantsan kishinta A dai-dai lokacin ne wani saurayi Black beauty ya iso wajen, tare da faɗin, "wai me ke faruwa ne a nan?" Dalilin da yasa Malik ya kasa yin magana kenan ya bi saurayin da kallo suna haɗa idanu Yayinda shi kuma saurayin ya mayar da idanunsa a kan Nawwara da ke faman kuka kamar wacce ranta zai fita, nan da nan har ta ɓata fuskarta da kwalliyan da ta caɓa. Kafin yayi mata magana har ta wurga wayan a jikin Malik ta ruga da gudu tana kuka sosai Da kallo suka bi ta har ta ƙulewa ganinsu. Inda Malik ya ja tsaki yana ɗauke kanshi ya mayar a kan wayan da ke jikinsa ya ɗauka While shi kuma saurayin sai ya taho ya zauna a saman carpet da ke shimfiɗe a wurin an jera drinks a sama. Zaman shi ya bi Malik da kallo yana cewa, "me kayi mata ka taɓo ta haka?" "Me kuwa nayi mata? Shirmen kishin ta take so ta nuna min haukansa a nan." Murmushi yayi yace, "Allah ko? Ni dai na san da abun da kayi mata shiyasa ka motsa mata, please tall me what did you do to her?" Ɗago kai Malik yayi ya kalle shi, sai ya ɗauke kanshi yana mayarwa a saman wayansa tare da duban hoton budurwan da ke jiki, bai san sanda murmushi ya suɓuce mishi ba yana faman shafa kan wayan a hankali Ganin haka ne yasa Abokin nashi ya amshi wayan yana dubawa shima. Arba da yayi da kyakykyawar halittar da ke gaban wayan, sai ya ɗago kai da sauri yana duban sa tare da faɗin, "wace ce wannan kuma?" Ya ƙare maganar yana sake duban wayan Shi kuma Malik yalwataccen murmushin ne ya sake suɓuce mishi, sai da ya kai hannu ya shafa ƙasumban shi kafin yace, "I don't know her." "Kamar ya?" Ya furta yana kallon sa Numfashi ya sauke yana ɗan cije leɓen ƙasan bakinsa. Sai da ya fuskance shi before yace, "Sinior ita ce yarinyar da ta hana Ni sukuni a tsakankanin wannan lokacin." "You mean. Ita ce wacce ta sanya ka a cikin wannan halin da kake ciki?" Gyaɗa mishi kai yayi Sai shi kuma Sinior yayi murmushi tare da cewa, "cab ɗijam! Kace ka taro match ne ba ka da ƴan wasa, ai dole Nawwara ta tashi hankalin ta ashe ta kama ka kana kallon wata ce, amma ya aka yi ban sanka da ita ba? Duk a cikin ƴan matan ka ban taɓa ganin kyakkyawa irin wannan ba, Guy aina ka samo ta domin ta haɗu wlh babu ƙarya?" "Ban santa ba nace maka, yanda ka ga hoton ta haka nima nake gani kullum, kuma a haka ne ta sanya ni a cikin wannan halin." "Wai ban gane ba fa, me kake nufi?" "Sinior I don't know her, nima tsintan hotonta nayi a facebook, wani ne yayi post a page na Arewa show. Tunda naga hoton wlh na susuce hankali na ya tashi, bani da buri sama da in Yi tozali da ita, amma abun ya faskara, yau tsawon sati biyu kenan na rasa sukunina na kasa cire ta a raina bare in manta ta, hasali ma ko sunanta ban sani ba, na bibiyi wanda yayi post ɗin but shima yace min bai santa ba, ya tsinci hoton ta ne shima yayi post a page ɗin." Sai ya ja wani dogon numfashi mai fita da huci, a hankali kuma ya ci gaba da cewa, "Sinior na kusa na rasa hankali na gaba ɗaya idan ban samu yarinyar nan ba, zan mutu wlh, bani da buri face in ganta in bayyana mata irin tarin ƙaunar da nake mata ba, wlh ban taɓa son ɗiya mace makamanciyar yanda nake mata ba, kai ko kwatan-kwata ban taɓa yiwa wata halitta ba kamar yanda nake jin nata soyayyar a zuciyata ba." Da kallo kawai Sinior yake bin shi dashi ba tare da yayi yunƙurin katse shi daga zantukan shi ba, haƙiƙanin gaskiya yake gani tsagwaronta a cikin idanunsa, wanda ya san waye Malik ciki da bai kuma ya san tabbas da gaske yake yi, babu shakka ko shi da ya kalli hoton yarinyar ya ji matsananciyar soyayyarta domin ita ɗin abun burgewa ne ga kowa, sai dai me, babu halin ya bayyana nashi soyayyar sabida Abokinsa ya riga shi. Numfashi ya ja shima yana mayar mishi da wayan nashi tare da cewa, "yanzu kana nufin duk tarin ƙaunar da kake yiwa Nawwara bai kai na wannan yarinyar da ba ka san wace ce ita ba?" "Bazan ɓoye maka ba ka san hali na Sinior, wlh da gaske nake maka ban taɓa jin irin soyayyar da nake mata a kan wata Mace ba, Ni kaina ina mamakin yanda zuciyata ta haukace da tunaninta, komai ba na iya yi yanzu sai da tunanin ta, wlh Sinior idan har zan samu yarinyar nan zan iya bada komai nawa domin in mallake ta, Ina sonta da gaskiya, kuma son da nake mata ba irin na sauran Mata da nake musu ba ne." Sai kuma ya fuskance shi sosai tare da ƙara faɗin, "wlh idan har zan samu yarinyar aurenta zan yi domin in killace ta a gidana, amma ban san ya zan yi ba, ban san ta inda zan fara ba." Jinjina kanshi Sinior yayi tare da faɗin, "lallai kam Malik, kana da babban aiki a gaban ka, ba wai nemo yarinyar da ba ka san inda za ka neme ta ba, a'a; matsalar yana ga wurin Nawwara, yarinyar da ka koya mata soyayyarka tun bata san kanta ba, yarinyar da ta so ka a rayuwarta ba ta jin maganar kowa sai kai, yarinyar da ta mallaka maka komai nata, yarinyar da ta fitsare jikinta duk saboda kai ta koma yanda take a yanzu, to ya zaka yi da ita? Da wanne ido za ka kalle ta? Ka san halin Nawwara ba sai na ba ka labari ba, a kanka zata iya kashe ko waye ne sai dai itama a kashe ta, ta sha yin dambe duk a saboda kai, ta sha zuwa cell duk a sabida kai, ta koma tamkar Matarka duk don ta faranta maka rai, sannan kai ma kayi mata alƙawari ba sau ɗaya ba; ba sau biyu ba a rayuwa, to ya za ka yi da ita?" Shiru kawai Malik yayi yana kallon Sinior yayinda ya kasa cewa uffan Sai shi Siniorn ya sake cewa, "kaga Malik idan ma mafarki kake yi to ka farka daga wannan barcin, duk da naga hoton yarinyar nan na san cewa ta fi Nawwara komai, bama za'a haɗa su ba idan kyawu ne, amma ba ka san inda take ba, ba ka san ta ina za ka fara nemanta ba, ba ka san cewa tana raye ko ba ta raye ba, to; ta ya zaka soma sonta bayan ba ka da hanyar da zaka iya nemanta? ba ka da wani takamaiman hanya ɗaya mai sauƙi da zai kaika gare ta, Malik ka dawo hayyacinka tun kafin ta shiga tsakanin ka da Nawwara, kaima abun da bazai taɓa faruwa bane." Malik yace, "na ji abun da kace, but ka sani wannan issues ne na rayuwata, soyayyata ne na gaskiya, bazai taɓa yiwuwa in cire abun da nake ji a game da yarinyar nan ba, ba Ni na sakawa kaina ba taya ya zan cire?" "Akwai hanyoyi da dama da za ka iya bi ka cire ta." "Which way is it?" Malik ya tambaye sa yana zura mishi idanu Sai yayi murmushi shi kuma yana cewa, "na farko dai na tabbata soyayyar yarinyar nan abu ɗaya zuwa biyu yasa ka kamu da ita, na farko kyawunta, Ni na tabbata kyawunta da sha'awarta yake ruɗanka Malik, baya ga haka babu komai Malik, kuma idan kayi yaƙi da zuciyarka ka nuna mata wannan ba irin Matan da kake samu cikin sauƙi bane zata fahimta, wannan baka santa ba, ba ka da tabbaci ma Mutum ce ita ko aljana domin kyawun nata yayi yawa..." Katse shi yayi da cewa, "yanzu kana nufin ba ka yarda cewa ina sonta har zuciyata bane? Taya kake ganin zan iya bayyana wannan magana alhalin akwai Nawwara a tare da Ni? Meyasa zan janyowa kaina fitina?" "Shikenan na yarda kana sonta, amma zaka iya cire ta ai, kaga Malik don Allah ka dena wannan maganar ma domin abun da bazai taɓa yiwuwa bane, da ace ka san inda yarinyar nan take to Ni zan iya goya maka baya ka aure ta, sai dai da sharaɗin zaka haɗa su su biyu da Nawwara, amma babu batun ka kawo wata wai kana so alhalin kuna tare da ita." "Ok." Ya furta yana miƙewa ba tare da ya sake cewa komai ba Sai Sinior ya bi shi da kallo yana cewa, "ina kuma zaka je?" "Zan shiga ciki." Yayi maganar ba tare da ya juyo ba yayi tafiyar sa Sinior shima ɗage kafaɗansa yayi before ya miƙe ya doshi hanyar fita gidan gaba ɗaya.           Malik na zuwa babban falon su ya ci karo da Mummyn su Ganin shi yasa tace, "Malik zo nan, me ya haɗa ku da Nawwara ne wai? Yanzu ta shigo tana kuka tayi ɗakin su Zainab." Yatsina fuska yayi, sai kuma ya taho yana zama a gefen Mummyn tare da cewa, "me tace miki nayi?" "Idan da ta faɗa min ai bazan tsaya ina tambayar ka ba." Tamke bakin sa yayi before yace, "a kan kishinta na banza ne, Allah yarinyar nan ta soma ƙure Ni, da abun da yakamata da wanda bai kamata ba duk sai ta hau kai tana nuna kishi, to ni wlh ta soma kai Ni bango bazan jure ba." Dariya Mummy tayi da cewa, "wai kana nufin Nawwaran naka ne yau ta soma kai ka bango? Lallai kam yau naga abun da ya fi ƙarfi na." "Uhm Mummy ki dena ɗaukar abun nan da wasa, wlh abun da take yi ya soma isata, yarinya sai bak'ar kishin jaraba sai kace ita kaɗai ce aka halarta min in aura?" "Tofa! Kace dai ka samu wata ce kake so ka juya mata baya? To ai da gaskiyarta tunda tana kishi ne a kan abinda take so, to bari kaji Ni kaina bazan taɓa goya maka baya a kan abun da kake shirin yi ga Nawwara ba, tunda har ka ɓata mata rayuwa ta zama yanda ta zama a yanzu dole ne ka aure ta." "Wai ban gane ba Mummy, na ɓata mata rayuwa kamar ya don Allah? Me kike nufi?" "Abun da nake nufi kaima ka sani, yarinyar nan dai tun tana ƙarama take tare da kai, ta ƙi kowa sai kai, ga shi yanzu har ta gama karatunta kuna tare, sai yanzu kuma da aka zo gaɓa ana shirin aurenku shi ne zaka zo da wani magana?" "To yanzu Mummy wanne magana na zo da shi ne?" Yayi maganar kamar zai yi kuka Hannu ta sa ta shafa kanshi before tace, "to idan baka zo min dashi ba ka faɗa min mene ne musabbabin abun da ya haɗa ku yanzu kuke faɗa? Sannan gaba ɗaya ka sauya a ɗan kwanakin nan ko fara'a ba ka yi, duk me ke damun ka ne?" Shiru yayi yana kallonta, kamar zai yi magana sai kuma yayi shiru yace, "ki bar zancen nan Mummy." "Shikenan tunda yau Ni kake ɓoyewa abun da ke ranka, idan yayi wari zamu ji. Ina maganar mu da nace zaka je Kano?" "Ki bari gobe sai in je tunda yanzu yamma tayi." "Ok Allah ya kaimu rai da lafiya, akwai saƙon Mai martaba da zan baka sai ka wuce mishi dashi." "To Mummy." Ya furta yana miƙewa tare da sake cewa, "Mummy bari in je in Yi wanka zan fita, but ki ce Zainab ta kawo min laptop ɗina tun kafin in karyata." "Kun fi kusa ai, idan ka karya ta kuma kai da Abban ku." Tayi maganar tana mayar da idanunta a kan t.v Yayinda shi kuma ya wuce ba tare da yace komai ba, ya haura sama inda ɗakin shi yake yana fito ya shige ciki Nawwara da ta fito cikin ɗakin su Zainab ƙannin Malik, sai ta hange shi ya shige shiyasa ta bi bayan shi ta tura ƙofan ta shige itama. [07/07, 11:32 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍* _________________________ *BABI NA SHIDA* _______________Har ya zauna a saman sofa ya soma latsa wayansa sai ya ji motsi, da sauri ya juya suka haɗa ido da ita, sai ya ɗauke kai yana sake tamke fuska ya ci gaba da abun da yake yi Ita kuma tana tsaye tana faman kallon bayan shi, sai kuma ta tako a hankali ta iso kujeran da yake ta samu waje ta zauna tare da kama hannunsa tana ƙoƙarin shigewa jikinsa Da sauri ya ɗago yana kallon ta yace, "stop it, I don't want you to be near me."     Ɗago idanunta tayi ta zuba mishi waɗanda a yanzu har sun tara ruwan hawaye, cikin sanyin murya tace, "me nayi maka?" "Tambayana kike yi?" "Yeah. Ban san me nayi maka ba." "Ok." Ya furta yana ɓanɓare hannunta tare da miƙewa zai wuce Da sauri ta tashi ta ƙanƙame shi ta baya tana sakin kuka me ban tausayi Take ya runtse idanuwansa sabida jin yanda ta manne mishi a jiki, bazai iya jurewa ba shiyasa yayi saurin soma ɓanɓaro ta a jikinsa yana cewa, "Nawwara ba na son wannan abun, Please sake Ni." "No bazan sake ka ba, wai me nayi maka ne kake so ka kashe Ni? Me nayi maka?" Tafaɗa cikin kuka sosai kuma ta ƙi sakin sa Tamke bakin sa yake yi yana wani karkaɗa kai, sai kuma ya ja jiki a hankali ya koma saman kujeran yana cewa, "is ok mana, mene ne na kukan kuma?" "Kai ne ai." "Me nayi miki?" Ya furta yana kamo ta sosai ya sake mannata a jikinsa tare da yunƙurin share mata hawayen Sai ta kawar da kai tana kallonsa tace, "wace ce yarinyar nan da na ganku tare? Kana nufin ka dena so na ne ko kuma ka gaji dani ne? Ka faɗa min mene ne alaƙar ku idan ba haka ba zan mutu?" Shiru yayi kawai yana kallonta, shi ya kan rasa wacce iriyar Mace ce Nawwara, idan da ace zata san waye shi a zahiri ba ya tunanin zata iya kai wa anjima bata mutu ba, sai dai kuma komai nasa yana yi ne da taka-tsan-tsan bai taɓa bari ta san halayyarsa na bin Mata ba, a komai nashi tana bibiyan shi ba yau ba ya san duk abin da take yi, kuma ya san muddin ta gane yana tarayya da wasu Matan akwai daru, shiyasa shima bai taɓa yin kuskuren da zata sani ba. But yau kuma ga shi ta kama shi da hoton wata yana kallo... Ya kasa magana sabida tunanin da ke addabar sa a lokacin, sai da ta taɓa shi sannan ya dawo hayyacin sa, sai ya ja numfashi yana kama fuskarta tare da cewa, "wai meyasa har yanzu kin kasa yarda dani ne a rayuwa? Sau nawa zan miki alƙawarukan da zai sa ki yarda dani? Bani da wata Mace da zan aura face ke, meyasa kike min irin haka ne?" "Na san cewa ba ka da wata macen da zaka aura bayan Ni, amma laifi ne don na tuhume ka a kan kallon hoton wata Mace bayan Ni ina da nawa hoton?" Murmushi yayi sabida maganar nata, sai yace, "Nawwara kin cika kishin jaraba, ke kaɗai ce fa a zuciyata, kin sani ke kaɗai na soma ƙauna tun ba ki mallaki hankalin kanki ba, ke ce kika fara ɗanɗana min zumar da tunda nake a duniya ban taɓa jin makamanciyar ta ba, to me kike kokwanto ne?" Shiru tayi sai kuma ta ɗan ja numfashi tana janye fuskarta daga riƙon da yayi mata, still tana kallonsa tace, "har yanzu ka ƙi sanar da Ni mene ne dalilin da yasa kake kallon hoton wata bayan Ni? Shi ne amsar da nake son sani." Ƙura mata idanu yayi, sai kuma yace, "saboda kawai naga hoton ta ne a social media shiyasa nake kallo, amma bayan haka babu komai, sannan ban santa ba; ban san ma inda zan ganta ba bare kiyi tunanin zata ƙwace miki Ni." Tura baki tayi gaba tana zare jikinta a nashi tare da cewa, "amma mene ne zai sa kana kallonta bayan ba ka santa ba? Meye haɗinka da ita?" "Nawwara." Ya kira sunanta yana tsare ta da kallo Sai ta kalle shi suka haɗa ido tayi saurin ɗauke kanta Hannunta ya riƙe yana ɗan mirzawa, sai kuma ya janyo ta sosai a jikinsa yana cewa, "da alamu kina kokwanto da irin ƙaunar da nake miki shiyasa har yanzu kike min irin wannan tuhumar." Ganin zata yi magana sai ya sanya hannunsa duka biyun ya matso da kanta ya haɗe bakunansu waje ɗaya. Bai saurara mata ba a haka ya ci gaba da tsotson bakinta cikin wani irin salo da yake saurin cin galaba a kanta, ko kusa ba ya ƙaunar ta ci gaba da wannan maganar don ya san halinta tamkar mayya haka take, shiyasa lokaci ɗaya ya soma birkita mata lissafi, cikin ƙanƙanin lokaci sun fita a hayyacin su Itama abun da take buƙata kenan, domin kusan sati biyu ba ta samun kulawa daga gare shi, shiyasa tayi tsananin kewar shi, hakan yasa itama bata saurara mishi ba sai da ta nuna mishi tsananin zalaman da take fama dashi a wannan lokacin. Sun shafe tsawon lokaci suna tare cikin wannan yanayin, until they were all satisfied sannan suka shiga cikin toilet suka yi wanka suka fito Duk wani hanya da Malik ya san zai bi domin ya mantar da ita maganar haka ya bi, ya ƙi bata ƙofan da zata sake dawowa da wancan tunanin, soyayya kawai suke sha domin daga ƙarshe ma rufe musu ƙofa yayi suka kwanta a saman gado manne da juna, still suna romance ɗin junansu tamkar zasu haɗiye juna, dama abun da ya san tana so kenan samun kulawan shi gaba ɗaya. Haka kuwa ya mantar da ita komai, har yana sanar da ita, "zuwa gobe zai je Kano sai ta shirya su je tare." Ai kuwa ba ƙaramin farin ciki ya cika ta ba, sai murna take yi sabida ta san bata taɓa samun wannan damar ba, basu taɓa yin tafiya tare ba, ta san cewa ita kaɗai ce a zuciyar Malik daga ita babu wata Mace, ita shi ne haka ma shi nata ne, kuma baza ta taɓa yin saken da wata zata shigo rayuwar shi ta raba su ba, idan kuwa hakan ta faru tayi alƙawari sai ta kashe ko wace ce; baza ta barta a raye ba.                    Sai da aka kira sallan magriba sannan suka rabu. Ta tafi ta bar shi ya sake wanka sannan ya wuce masallaci, lokacin ma har an idar da sallah. Daga can ne suka haɗu da Sinior suka wuce club.        ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️            *KADUNA STATE*           Ranar Asabar sai ga su Ummu sun zo kamar yanda suka yi alƙawari, wajen ƙarfe goma na safe yayi musu a gidan Firdausi Lokacin ma Nafi'u yana nan bai fita ba, sai da suka gaisa sannan ya fice. Bai jima ba kuma ya dawo musu da siyayyan da yayi musu na kayan abinci, sai fruits ya ajiye musu ya koma Firdausi tayi murnan ganin su ba kaɗan ba, har ƙwalla tayi a ɓoye don babu abun da ya fi mata ƴan uwanta daɗi, a haƙiƙanin gaskiya sun shaƙu matuƙa a lokacin da take gida. Sai dai kuma tun sanda suka soma zama ƴan mata ne ta gane ƙudirin Innarsu a kansu shiyasa ita Firdausi ta sauya ta nuna, "sam baza ta iya yin irin wannan rayuwar ba." Dalilin da yasa Inna ta tsane ta kenan, komai a sha'anin gidan ta cire ta tamkar ba ita bace babba, hatta da ƙanninta ta so ta shiga tsakanin su sai dai kuma akwai ƙaunar junansu, dalilin da yasa basu biye mata ba kenan suna mu'amala da Yayar tasu sai dai ba kamar baya ba, kuma ba wai bata girma suke yi sosai ba, tunda ko faɗa tayi musu a kan rayuwar da suke yi tana son ta nuna musu hanyar da Innarsu take ƙoƙarin tura su ba mai kyau bane, da yiwuwar zasu iya samun matsala, amma sam ba sa jinta, wani lokacin ma sai su kai ƙaranta wajen Inna, ita kuma ta kama ta ta jibga banza, haka Firdausi zata yi kuka ta share hawayenta babu mai rarrashin ta idan ba Baba ba.           Ummu da Arab suka yi musu girki, kasancewar Arab tana ƙaunar cooking shiyasa ta shiga suka yi tare. Shinkafa da miya suka yi tare da nama da Nafi'u ya fita ya siyo musu, sai suka yi juice kala biyu Basu gama ba Arab ta fita ta bar wa Ummu ƙarison. Tana shiga ɗakin Firdausi ta hangi Zahra na zaune ita kaɗai ta buga tagumi, sai ta nufe ta ta zauna a gefen ta tana cewa, "Aunty Zahra tunanin me kike yi ne haka?"    Ɗan ɗago kanta tayi tana jan numfashi, fuskarta ɗauke da damuwa ta kalle ta tare da cewa, "wlh akwai abun da ke damuna ne." "To faɗa min mana in abun da zan iya taimaka miki ne." Arab ɗin itama tayi maganar tana tsira mata ido Shiru ta ɗan yi na tsawon daƙiƙu before tace, "yau kimanin wata biyu kenan ban ga period ɗina ba Arab..." Sai tayi shiru kuma ta kasa ƙarisawa Arab da ko ƙyafta idanu ba tayi a kanta sai tace, "uhm ina jinki, to sabida me kenan?" "Ke ma kin sani an samu matsala wlh, na rasa wanda zan sanar mishi domin na tabbata ciki ne dani, wlh ina jin tsoro duk hankalina ya gama tashi." Dariya ne ya ƙwacewa Arab har da tafa hannaye tana ware manyan idanunta sosai a kanta, tare da cewa, "wai kina nufin kin ba wani ƙaton banzan jikin ki Aunty? To kin san da zuwan wannan ranan meyasa ba ki ɗauki mataki ba? Wannan ai ganganci ne." Hannayenta ta cire daga tagumin da tayi tana tamke fuska da cewa, "ba na son iskanci fa Arab, shawara na zo ki bani tunda naga wannan harkan naki ne ba nawa ba, nima akasi aka samu shiyasa amma wlh ban yi tunanin zan samu ciki ba." Wani dariyan ta tuntsire dashi har da ɗaura hannu a kan bakinta, but dariyan ya ƙi tsayawa, sosai take mata dariyan mugunta har da hawaye Wanda hakan ne ya fusata Zahra tace, "Wai ke meye haka? Wanne irin wulaƙanci kike min? Ba na son iskanci fa wlh, nayi dana-sanin sanar da ke sirri na, a tunani na ke ƴar uwata ce za ki rufa min asiri amma kuma kin zauna kina min dariya." Daƙyar a yanzu ta tsayar da dariyan da cewa, "to naji kiyi haƙuri, amma fa baza ki hana Ni yin dariya ba tunda dai baki na ne ba naki ba, abun naki ne da ban dariya, kina son daɗi amma ba ki shiryawa zuwan wannan ranan ba...." Shiru tayi sabida ganin Zahran ta miƙe zata fice, sai tayi saurin riƙe mata hannu tana murmusawa tace, "i said sorry ha'a, ki zauna sai muyi magana, yanzu ya kike so ayi?" Tsaki ta ja tana hararanta, kuma bata ce komai ba sai ta dawo ta zauna ɗin tana kumbura fuska "Ina sauraron ki sanar dani?" Arab tayi maganar tana ɗaura hannunta ɗaya a haɓarta "So nake yi in zubar dashi kafin mu koma gida, yanzu ki raka Ni muje tunda ke kika san yanda ake yi sai mu zubar don Allah." Arab tace, "Ni kar kiyi min sharri fa, taya za ki ce na san yanda ake yi? Ko na taɓa ce miki na ɗauki ciki ne?" "A'a ba ki ce min ba, Please be patient but help me." "Okay fine." Ta furta tana ɗage kafaɗa tare da taɓe baki, sai kuma tace, "Let's finish eating and go to the hospital." Daga haka suka bar zancen. Arab tashi tayi ma ta fice zuwa kichen ɗin Lokacin har Ummu ta jera komai a tsakar Falon. Suna tare da Firdausi da ta fito wanka a ɗakin Nafi'u, ta zo ta zauna Ummu ta zuba mata abinci Zahra itama fitowa tayi duk suka haɗu suka ci abincin suna ta hira suna dariya, abun gunun sha'awa idan ka gansu sabida yanda suke gudanar da rayuwar su, baza ka taɓa cewa ƴan ɗaki ɗaya bane domin tamkar ƙawaye haka suke yi, bare kuma dama ba wani tazaran girman jiki ne dasu ba, duka kansu ɗaya yanzu, har Arab ta kamo su a tsawo sun koma kai ɗaya, sai dai Firdausi ce yanzu da tayi ƙiba tunda tayi auren nan, but dukkan su ba wani jiki ne dasu ba sai diri da Allah ya basu. Shiyasa suka taso cikin shaƙuwar junan su, basu da ƙawaye sai junan su, basu yarda wata ta shigo rayuwar su ba sai dai zaman mutunci da suke yi da jama'a, ko kuma classmates ɗinsu, kuma ba kowanne suke sakar mishi fuska suyi ƙawance da su ba sai ƴaƴan masu kuɗi, don haka zai yi wuya kaga suna mu'amala da yaran talakawa a ganin su sun wuce ajinsu kamar yanda Innarsu ta koya musu wannan ɗabi'ar Sau tari tana sanar musu da cewa, "su ba sa'annin yaran nan na talakawa bane, sun fi ƙarfin su sun wuce da ajinsu, don haka su sai ƴaƴan manya, su yakamata suyi ƙawance da su, kar ta ji kar ta gani." Wannan shi ne huɗubar ta a ko yaushe, kuma a haka suka taso don gani suke yi sun fi ƙarfin kowa.           Sai da suka gama cin abincin suka yi sallah, sannan suka shirya Arab tayi wanka tunda bata samu tayi ba sai yanzu da zasu fita. Su dukka biyun shigan baƙar Abaya suka yi, iri ɗaya ce sai dai kwalliya da ya bambanta su, suka yi Rolling da gyalen shi, kana kallon su zaka san ƴan gida ɗaya ne tunda ga kama nan tsagwaronta, sai dai ita Arab duk ta fi su hasken fata ne da kyawu Suna fitowa Firdausi tace, "Ah ah ina zaku je kuma?" Zahra CE tace, "aunty ba daɗewa zamu yi ba, zamu ɗan je wani waje ne." "To ina ku ka sani a nan; kar fa ku je ku ɓace? Arab ke ma da ba ki fita ko nan da can ba taya zaku san gari?" "Shiyasa ai zamu je mu sha iska yanzu, kinga Aunty ba daɗewa zamu yi ba yanzu zamu dawo." Arab tayi maganar tana gyara agogon hannunta da ta gama ɗaurawa Ummu tace, "shi ne dan wulaƙanci baku sanar min ba in shirya mu tafi tare?" "Kuma yanzu ba jiran ki zamu yi ba tunda mun shirya, Aunty Zahra, let's go. Please don't waste time." Sai ta ɗauki jakarta a kan kujera da ta ajiye tana yin gaba Sallama Zahra tayi musu ta fice ta bar Ummu tana ƙorafin abun da suka yi mata, bata ma tsaya ta saurare ta ba tunda taga Arab ta fice Kai tsaye titi suka nufa suka samu abun hawa. Suka faɗa mishi, "ya kai su asibiti mafi kusa da nan." Yace, "ai suna da yawa asibitocin, amma na gwamnati ko na kuɗi wanne kuke so?" Arab tace, "kai mu na kuɗi." Sai da tayi maganar kuma sai ta kalli Zahra tana cewa, "ai kina da kuɗi ko? Don can zai fi tunda su basu cika tsawwalawa ba a kan irin wannan aikin." "Eh mu je, ina dashi, sai dai mu cire a POS. Driver aina zamu samu POS?" "Eh bari mu tsallaka can hanyar za'a samu." Can suka nufa suka cire kuɗin kamar yanda Arab ta faɗa mata adadin wanda zata cire. Daga nan suka wuce asibiti ya sauke su suka biya shi kuɗin shi. Suka taka zuwa ciki A reception suka samu wata nurse suka ce mata, "likita suke son gani?" Sai da ta gama musu wani kallo tana ganin yanayin su, sai kuma tace, "kun san dai ba haka kawai ake ganin likita ba sai an bi layi, don haka akwai waɗanda suke gaban ku sai ku jira." Jin hakan sai Arab tayi mata wani kallo, sai kuma ta taɓe fuska tana mayar da idanunta a kan Zahra tare da cewa, "ki bata 2k ta nuna mana Office ɗin da zamu ga likita, don na san abun da take buƙata kenan tunda ƴan maula ne." Maganar yayi ma nurse ɗin zafi, amma kuma ganin yanayin yadda Arab ɗin take gadara wajen yin magana kuma da yanayin zubin ta; sai tayi tunanin dole akwai abun da ta taka ne, shiyasa tayi shiru bata mayar mata da martani ba, bare kuma taji zancen kuɗi. Ai kuwa Zahra na bata kuɗin ta amsa tana wani yatsina fuska itama, sai kuma tace, "to mu je in kaiku." Tayi gaba Suka bi bayanta har zuwa wani Office "Ku shiga tana ci." Ta furta tana kallon su a lokacin da ta ja tunga a bakin ƙofan Office ɗin Basu ce mata komai ba Arab ta tura ƙofan ta shige ko nocking babu, inda Zahra ta take mata baya Kyakykyawar Mace ce a cikin Office ɗin sanye da rigan aikinta da ya ɗauke ta matuƙa, yayinda ta ɗaura baby hijab shima fari, tana rubutu ne ta ji ƙaran buɗe ƙofan, hakan yasa ta ɗago tana bin su Arab da kallo ɗaya bayan ɗaya ba tare da tayi yunƙurin yin magana ba Zahra CE ta soma yin magana cikin nuna girmamawa tayi mata sannu Sai ta amsa ta still bata cire idanunta da ke yawo a kansu ba. Kuma bata da ninyar basu umarnin zuwa su zauna Hakan yasa Arab tace, "We came to see a doctor and we were shown here." "Okay. You can sit." Tayi maganar tana nuna musu kujerun gaban table ɗinta      Zuwa suka yi suka zauna. Sai dai dukkansu sun yi shiru babu wacce ta iya magana Sai ita tace, "ehem ina jinku, me kuke buƙata? Hurry because I have a sick person to go to for a check-up." Arab tace, "Doctor we came for an abortion." "Abortion?" Ta furta da mamaki tana sake bin su da kallo sosai "Yerh." Arab ta bata amsa Shiru ta ɗan yi tana sake ƙare musu kallo, musamman ma Arab da ta kafe ta da idanu sai tauna chewing gum take yi alamun babu ko kunya a tare da ita, idanun nan ƙirr tamkar zata cinye ta. Sai ta ja numfashi da cewa, "dukkan ku ne za'a zubar wa da cikin?" "No ƴar uwata ce." Ta bata amsa tana kallon Zahra da kanta ke ƙasa Don ita kunyar matar ma take ji tunda bata saba wannan rayuwar ba, wannan time ɗin ta soma ba wa namiji damar da ya shige ta, tunda take bata taɓa aikata zina ba sai dai irin shafe-shafen nan da ya zama ruwan dare ga ƴan mata da samari suna ɗaukar shi wayewa, kuma duk a cikin samarinta mutum ɗaya ta taɓa ba shi kanta sabida ƙaunar da take mishi, kuma take fatan suyi aure a nan gaba shiyasa ta yarda, sai dai ko ba'a faɗa mata ba ta tabbata ciki ne a jikinta sabida canjin da ta samu a tare da ita Doctor kuwa a ranta duk mamakin waɗannan yaran ne ya cika ta, ko da ganin su ka san babu tarbiyya a tare da su duk da shigan nasu ba wani aibu bane, amma abun da zai bata mamaki yara ƙananu haka har sun san daɗin namiji? Ko a hasashe ta san Arab baza ta fi 16yrars ba, ita kuma Zahra tana kyautata zaton baza ta wuce 20years ba; daga gani kuma basu da aure, amma don ta tabbatar sai tace, "tana da aure ne?" "A'a." Still Arab ta furta tana wani ƙaƙas da chewing gum "Ok. Mu nan ba ma zubar da ciki tunda haramun ne, girman zunubin mu bai kai haka ba, so I will also advise you, ku ma yakamata ku yiwa kanku faɗa sabida wannan hanyar ba hanyar ɓillewa bane, Yara daku har kuke iya aikata wannan babban laifi haka?" Ta ƙare maganar tana bin su da kallo one after the other Sai Arab tace, "Doctor look ba wa'azi muka zo kiyi mana ba, babu abun da za ki sanar mana wanda bamu sani ba, abun da ya kawo mu shi za ki yi mana ba abun da bai shafe ki ba, idan kin san ba kwa irin wannan aikin meye na ɓata mana lokaci?" Murmushi Doctorn tayi tamkar maganar bai soke ta ba, sai tace, "amma a matsayina na ƴar uwanku musulma ai ina da haƙƙin da zan faɗa muku gaskiya ko? Laifi ne don na nuna muku hanyar da ya dace?" Rai a ɓace Arab ta miƙe, cike da rashin kunya irin nata har tana ɗaga murya tace, "eh laifi ne mana, mu bamu buƙaci wa'azi a wajen ki ba, ki bari idan mun zo muna buƙata sai kiyi, kin ganmu nan dukkan mu mun mallaki hankalin kanmu, zai fi kyau ki riƙe wa'azin ki don na san zai miki amfani tunda kina da Yara ke ma." "You better keep your mouth shut! Ni ba sa'an wasan ki bane." Doctor ta furta cikin tsawa Wanda hakan ne yasa aka buɗe ƙofan; wani dogon saurayi fari ƙal me kama da Doctorn sak ya shigo ciki, domin tunda yayi nocking a bakin ƙofa ya ji shiru bai shigo ba, but jin tsawar Doctorn ne yasa ya buɗe ƙofan da sauri ya shigo Sai duk suka bi shi da kallo har Arab da ta buɗe baki tana shirin maida wa Doctorn da martani, sai dai tuni ta ja ta tsaya tana zuba mishi idanun itama While shima hakan ne a wajen shi, ya zuba musu lulu eyes ɗinshi masu kalan brown da suke cikin medical eyes glasses. Cikin yanayin sa wanda ke nuni da rashin fara'an shi da rashin son hayaniya yake cewa, "Aunty What's going on here?" "Nothing Dacta." Ta furta before ta mayar da idanunta a kan su Arab tace, "ku fice min a Office." Tsaki Arab ta ja me ƙarfi har tana ture kujeran da ta zauna, sai ta kalli Zahra da ke zaune har yanzu tace, "zaman me kike yi da baza ki tashi mu bar wannan banzan Office ɗin ba?" Zahra sai ta miƙe bata ce uffan ba suna bin ƙofa zasu fice But wanda aka kira da Dacta yana tsaye ƙiƙam bai da alamun matsa musu, yayinda fuskarsa ta sake haɗewa fiye da yadda ya shigo da ita, babu inda idanunsa ke kallo face fuskar Arab yana sauke mata wani irin kallo da ta kasa tantance wanne irin kallo ne Da sauri ta ja ta tsaya itama tana bin shi da kallon ta kasa janye nata idanun daga cikin Brown eyes ɗinsa; wanɗanda suka yi mata matuƙar kwarjini da shegen kyawu Muryan Doctor ɗin ne ya ratsa kunnuwansu tana faɗin, "Dacta ka bar su su wuce." Maimakon ya matsa musu sai ma takowa da yayi a hankali cikin taku biyu ya isa gaban Arab, har numfashin junan su suke iya juyowa, cikin wani irin yanayin murya da idan har ka ji sai ta girgiza maka zuciya, a dake kuma muryan wadda babu alamun sauƙi a tare da shi yace, "wace ce ke?" Tambayar ya diran mata zuciya ne da wani irin bugawar gaban da yasa ta lumshe idanunta da sauri, yayinda ƙamshin turaren sa ya feso mata tamkar zai janye mata numfashi tsaban yanda ya ratsa mata ko'ina na cikin hancinta, hakan yasa ta ware manyan idanuwanta da sauri ta sake saukewa a kan shi but ta gaza yin magana, domin neman words ɗin bakinta tayi ta rasa "I said who are you to come to this office and say this nonsense?" Yayi maganar cikin tsananin tsawa da fushin da ya bayyana a kan fuskar shi. _Fatan zamu yi sallah lafiya ƴan uwa. Eid Mubrak._ 2022. [12/07, 12:01 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA BAKWAI* _______________Da sauri Doctorn ta tashi ta nufo wajensu sabida ta san halin ƙanin nata; yanzu sai a samu matsala, wurin ta nufa tana taran numfashinsa da yake yunƙurin sake yin magana a zafafe jin yarinyar ta raina mishi wayau ta ƙi magana, tace, "Aliyu please I told you to stop, let them go." Shiru yayi yana ɗauke kanshi ya mayar a kan Auntyn tashi, sai kuma ya ja numfashi yana haɗiye wani abu da ya wuce mishi ƙato daga maƙogwaro, har idanunsa sun soma juyewa sabida tsaban ɓacin rai, kasancewar akwai girmamawa sosai a tsakanin su shiyasa bai sake cewa komai ba; illa wani kallon banza na gargaɗi da ya saukewa Arab, kana ya raɓa ta ya wuce yana ɗaura hannunsa a yalwataccen gashin kanshi yana yamutsawa Daga Arab ɗin har Zahra sun kasa cewa komai sabida tsananin firgita da suka yi da mutumin, duk tsiwan Arab ta kasa cewa komai illa kallonsa da take yi, motsi ma sun kasa yi sai da Doctor ta sake ce musu, "i said out." Before su taka su fice jiki a saɓule Itama kuma ta iso ta koma wajen zamanta tana kallon Ƙanin nata wanda ya samu waje ya zauna a kujeran da Zahra ta tashi, sai faman sauke ajiyan zuciya yake yi har yanzu yana yamutsa tulin gashin shi da ya sha gyara ya fito da tsantsan kyawunsa da Allah ya ba shi, gami da kwarjinin sa. Sai da ta ɗauki daƙiƙu tana nazartan shi don ta san tunda ya shiga wannan yanayin ba ƙaramin ɓaci ranshi yayi ba, sau tari hakan yake yi shiyasa ta soma da ba shi haƙuri tana ce mishi, "ya kwantar da hankalin shi please ba ta son ganin shi a haka." Rikitattun idanuwansa ya ɗago su yana saukewa a kanta tare da cewa, "me ya haɗa ki da tsageran yaran nan da suka zo har Office ɗin ki suna son gaya miki magana?" Sai da ta sauke ajiyan zuciya tana ɗan kwantar da bayanta a jikin kujeran tare da cewa, "na saba ganin irin waɗannan yaran Aliyu, so ba abun tayar da hankali bane a matsayina na Likita, sun zo zubar da ciki ne nake sanar musu ba ma zubar wa, har ina son yin musu wa'azi but wannan ƙaramar take son gaya min magana." Shiru yayi yana sauke kanshi ƙasa tare da mirza yatsun sa "But ka share kawai ka bar maganar." "Ban ji daɗi ba yanda kika hana Ni koya musu hankali, da na nuna musu inda suka zo ba inda suka saba iskancin su bane." Murmushi tayi tana kallonsa tare da cewa, "Aliyu kenan! Ka dena irin wannan fushin Please, ba na son ranka yana ɓaci kaji ko? Ka san kai ɗan lele ne a wuri na." Wannan kalman ne yasa shi yin murmushinsa mai kyau yana kallonta shima, sai dai bai ce komai ba tunda shi ba kasafai yake son magana ba Sai ta sake cewa, "ina ta jiranka sai yanzu ka zo?" "Wlh kuwa, ban gama abun da nake yi bane Aunty." "Ok yaushe zaka koma?" Yace, "yau nake saka rai." "Kana nufin baza ka koma gidana bane?" Tayi maganar cikin waro ido Sai ya ɗan langaɓe kai da cewa, "to Aunty mai zan koma yi?" Hararansa tayi da cewa, "mu yi sallama mana." Sai yayi murmushi mai bayyana haƙora yana shafa suman kanshi yace, "to ai Aunty ga shi muna yin sallaman." "A'a Ni ban yarda ba, wai kana saurin meye ne?" "Aunty kin san na bar Dad, kuma kinga ban bar wa kowa drugs ɗinsa ba dole zan koma." "Eh haka ne, but ya jikin nashi?" "Da sauƙi sosai. Next week we'll be back in Germany to check it out." Murmushi Auntyn tayi tace, "alhamdulillah Masha Allah, haka nake son ji, amma don Allah kar ka tafi ka bari in tashi mu je gida tare." "Aunty akwai inda zan je yanzu, kuma ina son in ziyarci wani Aboki na da muka yi school tare, tunda na zo yakamata in je har gida mu gaisa before in koma, ban san ranan dawowana ba." Aunty tace, "shikenan bazan matsa maka ba tunda kace hakan, sai muyi sallaman a nan." "Or how long are you going to get up?" He speaks looking at her Tace, "by six insha Allah." "So I'll come and say goodbye when I finish what I'm doing, zamu haɗu a gidan." Washe baki tayi tace, "yauwa ɗan lele na, haka nake son ji." Murmushi sosai ya bayyana a kan fuskarsa sabida yana jin daɗin wannan sunan Itama murmushin tayi tace, "yanzu ina son duba person suna jira na bari in je." "Ok." Yace hakan yana miƙewa tare da sake faɗin, "bari in je nima aunty, sai na zo gidan." "To Ƙanina, ka kula da kanka." Murmushi yayi bai ce komai ba ya juya ya fice Itama kuma ta rufe file ɗin gabanta sannan ta ɗauki wani ta tashi ta fita; zuwa room ɗin da zata duba mara su lafiyan ta. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️         Su Arab da suka fita kai tsaye keke napep suka hau suka ce, "ya kaisu wani Asibitin." kamar yanda suka sanar da wancan Sai dai har wannan lokacin babu wacce tayi magana a cikin su. Kowa yana jajanta abun da ya faru tare da tunanin wannan kyakykyawar saurayin da yayi musu haka Musamman ma Arab wadda abun yayi matuƙar ƙona mata rai da bata mamaki, abun haushin yanda ta kasa buɗe baki ta mayar mishi da martani sabida tsananin shakkar sa da kwarjininsa da ya cika ta, tabbas ranta yayi matuƙar ɓaci saboda babu wanda ya taɓa gaya mata magana kamar wannan guy ɗin; bare har yayi mata tsawa a kai, sosai ranta ke ƙara ɓaci wanda ji take yi kamar ta koma tayi masa wulaƙanci, tabbas baza ta taɓa hucewa ba idan har bata mayar mishi da martani ba. Kanta ta kama ta riƙe sosai sabida ta rasa tunanin me zata yi don ta huce takaicin sa Zahra kuwa itama tunanin ne a ranta, sai dai ita nata ya sha bamban dana Arab, ba ƙaramin burge ta yayi ba, yanayin sa kawai take tunanowa fuskarta ɗauke da murmushi, idan da ace zata same shi fa. Haƙiƙa ya haɗu ga baiwar kyawu, Allah yayi halitta a nan, ga babu alamar tsoro a tattare da shi wanda ko wacce Mace ta ga halayyarsa sai ta afka mishi a soyayya. "oh Allah! Dama akwai saurayi irin sa a wannan zamanin?" Ta furta a ranta tana sake murmusawa, sai kuma ta kalli Arab ganin yanda ta kama kanta, sai ta taɓo ta tana tambayarta, "lafiya Auta me ya same ki?" Ɗago kanta tayi ta sauke mata manyan idanuwanta da suka soma sanja kala zuwa ja, sai dai bata ce komai ba ta mayar da kanta ƙasa ta duƙar Itama Zahra bata sake magana ba don babu shakka abun da Aliyu yayi musu shi ne yake damun Arab, ta san halinta kuma tayi mamakin yanda ta kasa mayar mishi da martani, amma ta san ya cancanci hakan ne tunda ba wanda za'a yi mishi wargi bane, wannan ya wuce tunanin su domin ko da ganinsa ba shi da wasa.                Tsayar da napep ɗin da Drivern yayi ne shiyasa suka dawo cikin hayyacin su a lokaci ɗaya, ganin sun tsaya a wani gini a saman an rubuta Hospital center shiyasa suka tabbatar an kawo ne. Sai suka fito suka ba shi kuɗinsa da ya sanar musu suka shiga ciki Wannan karon koda suka samu wata nurse basu tambaye ta kai tsaye Office ɗin Likita ba, sai suka bata kuɗi suka ce, "ta sanar musu idan ana zubar da ciki a nan? Nan suke nema." Ai kuwa ganin kuɗi har 5k. Farin ciki ya cikata tunda sun samu haɗamammiya dai-dai da wacce suke nema. Ta ko kai su wurin wani likita Christian Babu ɓata lokaci ya amince da buƙatar su bayan ya sara musu kuɗi mai yawa, wanda suka ciro ma bai ishe shi ba sai da ya caje su wani kuɗin But sai Arab ta ƙi ba shi don ita ta fi shi zalamar kuɗi, duk wani wayonka ba ka isa ka ci bati a wurinta ba duk da ba ita zata biya kuɗin ba. A nan tayi dabaru irin nata a matsayin ta na riƙaƙƙiya ƴar duniya wacce ta san yanda ake tafiyar da naMiji, ta kalallame shi da yaudaran ta a haka yayi musu sauƙi. Har da yin mishi alƙawarin, "zasu haɗu da shi a duk inda yake so." sannan ta amshi Numban shi Shi kuwa gogan ya ga zuƙa-zuƙan ƴan mata kuma ya samu banza a ɓagas, ai kuwa ya yiwa Zahra abun da zai mata ya cire mata cikin, sannan yace, "dole sai ta zauna ya ƙara mata ruwa tunda jikinta babu daɗi." Haka kuwa babu yanda suka iya sabida baza ta iya tashi ba, duk jikinta yayi weak sai jiri da take ji sakamakon yanda ta zubar da jini Kasancewar suna sauri ba sa son su jima sosai sai Arab ta matsa mishi, "ya sallame su kawai." Tunda ta ga leda ɗaya ya ƙare. Tace, "idan suka koma gida za'a saka mata wani." Yace, "kin tabbatar za'a saka mata?" "Yes Doctor I'm sure, muna komawa gida zamu samu Doctor ya ƙara mata." Baki a washe yace, "Me kyau ko za ki bani address ɗin gidan ku sai in zo in saka mata hakan zai fi ko?" Murmushinta da ke shagaltar da duk wanda tayi masa ta saki, tana wani yatsina fuska cike da yanga tace, "don't worry doctor, ba sai ka zo ba muna da likitan da zai duba ta, babu damuwa." "Yarinya mai kyau kin tabbatar?" Kanta ta gyaɗa mishi still tana sakar mishi kyakkyawar murmushinta "Ok. Let me give you the medicine she will take, her body will be much easier." "Ok thanks." Haka ya haɗa musu a kyauta kuma da kanshi ya amso musu. Ya basu ya raka su har haraban asibitin, tamkar kar ya rabu dasu yana ta ɗaga musu hannu yana washe baki cike da jin daɗi Su kuwa ko bi ta kanshi basu yi ba suka wuce gida Ai kuwa Firdausi da Ummu tuni sun soma tambayar su, "ina suka je suka daɗe haka?" Musamman yanda suka ga yanayin Zahra tamkar bata da lafiya tunda har a lokacin daƙyar take tafiya, fuskarta duk ta sauya Arab tace, "zaga gari nace muku zamu yi, kuma Aunty Zahra zazzaɓi ne ya rufe ta shiyasa." Nan fa suka ruɗe dukkan su. Firdausi har da cewa, "su je asibiti hankalin su zai fi kwanciya, gwara a duba abun da yake damunta." But Arab tayi saurin cewa, "sai da muka je daga can ma muke, ga maganin ta a hannu na, sun ce babu damuwa fever ne kawai, very soon zai sauka." Hakan yasa hankalin su ya ɗan kwanta Sai Zahran ta je ta kwanta a ɗakin Firdausi Nan Arab ta bi bayanta tana cewa, "ta bari idan sun koma gida sai a ƙara mata ruwan idan jikin bai yi daɗi ba." Sai ta juya ta barta ta koma Falo.                 Kusan ƙarfe biyar da rabi suka gama shiryawa zasu tafi gida. Wanda har lokacin jikin Zahra bai yi sauƙi sosai ba tunda bata da wani ƙarfi, sai a hankali dai zata warware. Sun yi shigan su iri ɗaya riga da skirt na material les, kowacce da nata style ɗin, sun yi kyau matuƙa tunda sun saba shiga iri ɗaya, kowa ya gansu sai ya ji sha'awar su shiyasa duk inda suka je a tare sai an kalle su kuma sai sun burge don daga gani ƴan gida ɗaya ne Firdausi kamar zata yi kuka ganin sun fito zasu tafi, sai tace, "don Allah kar su sake banzartar da ita, Please su dawo nan kusa kar su biyewa Inna su ƙi zuwa su duba ta, zata ji daɗi idan sun zo." Duk dariya suke mata ganin yanda tayi da fuska kamar zata yi kuka Arab tace, "to ke Aunty ke meyasa baza ki zo ba sai mu?" "To Auta kin san halin Innarmu shiyasa ma Nafi'u ya hana Ni zuwa har yanzu; sabida bai san me Inna zata yi mana ba, amma kwanan nan zan zo in duba ku ko ba a so." "To ai naga kina da Baba me ƙaunar ki meye na wannan maganar? Kawai idan za ki zo ki zo ba wai ki tsaya da hujjar Inna ba ta so ba." Arab ɗin ta sake faɗa tana taɓe baki Murmushi kawai Firdausi tayi sai ta sauya maganar da cewa, "to Ni dai don Allah ku zo ba sai na haihu ba." Ummu tace, "kar ki damu Aunty duk sanda muka samu hutun school me yawa zamu zo muyi miki kwana biyu, ki kwantar da hankalin ki kawai." Murmushin farin ciki tayi cike da murna tace, "yauwa Nagode, don Allah idan kun je ku gaishe da su Innan da kyau, ga wannan ledan sai ki bata, da saƙon Baba a ciki shima ki gaishe shi da kyau, idan kun koma zamu yi waya." Ta miƙo ledan da ke hannunta; Zahra da ke kusa da ita ta amsa Arab tace, "wai Aunty mu fa zamu tafi idan Mijin nan naki bai dawo ba, mun gaji da jira."    "Kai Auta kin cika ƙorafi wlh, yanzu fa kika ga na kira shi yace ga shi nan a hanya."    "To ai naga ba shi da alamar zuwa ne ya shanya mu sai kace bayin shi..."     Bata rufe baki ba sai ga sallaman shi sun shigo tare da Aliyu Abokin sa      A tare idanuwan su Arab da Zahra suka sauka a kan Aliyun da shima ya haɗa ido da su, sai kawai aka koma kallon-kallo da juna babu mai motsin kirki a cikin su, har shi Aliyun ya kasa jirgawa daga inda yake tsaye a bakin ƙofan hannunsa ɗaya a cikin Aljihun wandon sa. [14/07, 8:42 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA TAKWAS* _______________ Maganar da Nafi'u yayi mishi ne ya dawo da shi cikin tunanin sa, sai ya ɗauke kanshi a kansu yana isowa izuwa kan kujerun falon kamar yanda Nafi'u yayi mishi iso A cikinsu babu wanda ya motsa duk da akwai wajen zama amma duk sun ciccika wurin Arab da Zahra mamakin ganin shi kawai suke yi wanda yasa dukkan su babu me magana, yayinda suka ɗauke kai tuni Musamman ma Zahra wacce gaba ɗaya zuciyarta ke faman bugawa sabida abun da take ji a game dashi, bata taɓa tunanin zata sake ganin kyakkyawar saurayin nan da ya ƙi fita mata a rai ba ya tsaya mata cak Ita kuwa Arab tuni ta ɗaura ƙafa kan ɗaya tana wani shan ƙamshi sai kace bata san dashi ba; duk da kuwa itama tayi mamakin ganinsa tana tunanin meye haɗin shi da nan gidan? Sai dai maganar Nafi'u duk ya shafe musu wani tantama har shi. Inda yake musu bayanin cewa, "Doctor waɗannan su ne ƙannin Matata Firdausi." Sai ya kalli Firdausin yana murmushi da cewa, "wai kin gane shi? Aboki na da nake ba ki labari yana zaune a Abuja?" Murmushi tayi tace, "na gane shi mana tunda na san shi sau ɗaya." Sai ta gaishe shi cikin fara'a A lokacin ne ya ɗago kansa shima da ɗan guntun murmushinsa ya amsa mata yana tambayar ta, "ya jiki?" "Alhamdulillah jiki da sauƙi wlh." "Masha Allah. Allahumma ya ƙara sauƙi." Ya furta yana ɗaukar wayansa da ke ƙaran shigowar text Daga Firdausi sai Nafi'u suka amsa Inda Firdausin take cewa Ummu, "please Ummu ɗauko mishi drinks a fridge mana." "To." Tace tana miƙewa Yayinda itama Arab da ke faman shan ƙamshi har yanzu, fuskarta babu walwala ko kaɗan ta miƙe tana yatsina fuska da cewa, "please get up and let's go, ba a nan zamu zauna mu ƙare ba muna da abun yi." Duk kallonta suke yi sabida yanda take maganar da gadara tana wani ciccin magani, ba wanda bai san halinta ba But sai Nafi'u da wasa da dariya yace, "haba Auta ki jira muyi sallama mana, ai yanzu na dawo." "To wanne sallama bayan ga shi ka dawo? We will go, Aunty mun tafi." Sai ta suri jakarta tana cewa, "idan kun gama zaman ku taso mu wuce." Tayi hanyar waje zata fita, kamar an ce ta kalli inda Doctor Aliyu yake zaune, sai suka haɗa idanu, wani irin banzan kallo ta sakar mishi tana jan ƙaramin tsaki tayi waje da sauri Shi kuwa tsananin mamaki da al'ajabi ne ya cika sa har ya kasa yin magana, sabida ba kaɗan ba yarinyar tayi matuƙar ɓata mishi rai da irin kallon da take mishi, a ransa sai ya ji wani irin tsanarta yana huda mishi can cikin jikinsa, a rayuwa ya tsani ya ga Mace mara tarbiyya sheɗaniya, ko da gani wannan yarinyar bata da kunya. Koda Ummu ta kawo mishi drinks ɗin ya kasa sha sabida ganin yanayin yaran babu ko kunya a tattare da su, da idanu a tsakar ka suna yi tamkar karuwai, ko ba'a faɗa mishi ba zubin su ya tabbatar mishi da hakan. Abun ya dame shi har ya kasa sakin jikinsa koda suka tafi, yana mamakin ya aka yi Nafi'u ya je ya auro ƴar gidan mara su tarbiyya? Duk da cewa ya ga bambanci mai yawa a tare da Firdausin da su, ko da gani ba tarbiyyar su ɗaya ba amma abun ya ba shi mamaki don ya san halin Nafi'u.. daga ƙarshe ce mishi yayi, "zai wuce sabida a kan hanya yake tunda yana son komawa Abuja ne yau." A haka suka fito har haraban gidan Nafi'u ya rako shi, sosai yayi murna saboda yanda ya zo mishi ziyara, yana ta godiya a haka suka rabu cikin farin ciki cike da kewar juna Motansa ya hau ya wuce gidan Auntyn shi Hussaina wacce take aure a nan ɗin; tare da yaranta da mijinta. Su biyu ne kaɗai mahaifiyar su ta haifa kafin ta rasu, sai Dad ɗinsu ya auri wata Matar itama ta haifa yara uku duka Mata. Doctor Aliyu da Aunty Hussaina duk likitanci suka karanta. Yanzu haka Doctor Aliyu shi yake kula da mahaifinsu da bai da lafiya yana ciwon Sigar da Cancer da suka taso shi gaba, yau jikin da daɗi gobe babu haka suke fama. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️            Sai da aka kira sallan magriba sannan su Arab suka isa gida. Sallah suka yi sannan suka shantake a farfajiyar gidan suna ta zubawa Inna labari har Zahra da ba ƙoshin lafiya ta cika ba, sai ƙarfin hali da take nunawa don kar a gane halin da take ciki Baba ma da ya dawo yayi murna sosai, musamman da ya ji jikin Firdausin da sauƙi ba yanda yake zato ba.        Bayan kwana biyu da dawowar su ne Alhaji Bashir ya matsa wa Arab sai ta biyo shi Abuja tayi mishi ko kwana biyu ne. Ai kuwa yanda ya matsa ɗin ne shiyasa tace mishi, "tana nan zuwa." Ibrahim ta kira ta sanar mishi yanda suka yi. Shi ya sake kwaɗaita mata a kan, "ta je kawai ta wanki gara." Hakan kuwa ta kasance, tace ma Alhaji Bashir, "zata zo gobe." Tare da Ibrahim suka tafi super market ta yo siyayyan kayan da zata buƙata. Sai da suka gama suka tafi yawo tare, sai kusan magriba suka iso gida Tana zuwa ta hangi motan Tariq a ƙofar gidan su, dama ya kira ta duk bata ɗauka ba a yau ɗin, da alamu yana da takura ne shiyasa take ba wa banza ajiyansa, ita ta tsani a takura mata, sam ba ta ɗaukar hakan. Sallama suka yi da Ibrahim tace, "ya tafi kawai sai sun yi waya." Sannan ta wuce zuwa gidan ba tare da ta kula Tariq ɗin ba Yana ganin zata wuce sai ya fito da sauri yana kiranta, "haba Gimbiyyar mata kamar ba ki ganni ba?" Wani kallo ta watsa mishi lokacin da ta juyo ta kalle shi, sai ta taɓe baki da cewa, "ban ganka ba, ashe kai ne?" Murmushi yayi yace, "ko dai sarautar ne ya tashi? Don Allah ki zo mu shiga mota muyi magana, Please?" Ya ƙare maganar yana ɗan haɗe hannayen shi alamun roƙo Kamar baza ta motsa ba, sai kuma ta gama shan ƙamshin ta cike da yatsina ta taho ta buɗe motan ta shiga bata ce mishi uffan ba Shima sai ya shige ya rufo ƙofan yana kallonta da cewa, "wai Gimbiyyata me nayi miki ne kika share Ni kwana biyu? Kin hana Ni zuwa gidan ku tun sanda kika dawo bayan kin san da ƙishin ruwan ganin ki nake wuni a ko yaushe, ba na so kina min horo da rashin ganin ki zuciyata baza ta iya jura ba." "Ko?" Ta furta tana latsa wayanta ba tare da ta kalle shi ba, kuma babu wata alamar damuwa a tare da ita Hakan ne yasa ya ji babu daɗi, cikin kwantar da murya yace, "Arab wai don Allah me kike so in Yi miki da zai tabbatar miki da na damu da ke?" Ɗago kai tayi ta zuba mishi, sai kuma tayi murmushin gefen baki da cewa, "Yallaɓoi me kake so in Yi maka nima? Meye damuwar ka?" "Kin san ko meye damuwata Princess, kwata-kwata kin kasa bani dama na shiga rayuwarki sosai, ina so don Allah ki bani wannan damar ko kaɗan ne, tunda kin ce ba kya son ina zuwa gidan ku me zai hana mu samu inda kike buƙata mu tattauna?" "Why not." Ta furta tana ɗage kafaɗa still tana ci gaba da murmushin nan nata da ba kowa yake gane ma'anar shi ba Jin hakan sai shima ya yalwata fara'a a kan fuskar shi da cewa, "kin amince kenan?" "Yes, I agree. But tomorrow I will travel. We will talk when I get back."         Fuskarsa ne ta nuna damuwa, cike da rashin jin daɗi yace, "ina za ki je kenan?" Murmushi tayi tana ɗan kashe mishi ido da faɗin, "ba sai ka ji ba Yallaɓoi." "Kina kashe min jiki idan kina min wannan kallon, meyasa baza ki fahimce Ni ba? Ni mai ƙaunar ki ne wlh ina matuƙar ƙaunar ki." Ya ƙare maganar kuma yana kai hannunsa a hankali ya kama nata, yayinda ya zuba mata lumsassun idanuwansa da suke ƙoƙarin sauya kamannin su Ita kuma murmushi kawai take mishi tana ƙare mishi kallon ƙurilla, lokaci ɗaya ta gama saka shi a wani irin yanayin da ya soma ficewa a hayyacinsa, ba kaɗan ba ta san lagwon namiji musamman idan ta gama laƙantan shi.. sai da ta janyo shi jikinta yana ƙoƙarin haɗe bakin su sai ta hana shi damar hakan tana saka yatsarta ɗaya a setting bakin sa, still fuskarta na ɗauke da murmushin nan nata me zautar da duk wanda tayi masa, a hankali ta girgiza mishi kanta tana ɗan buga yatsan nata a laɓɓansa tare da cewa, "a'a Yallaɓoi mene ne kuma haka? Ka bari sai na ba ka damar yin wani abu dani." Sai ta saki dariya me sauti tana janye jikinta tare da zuba mishi rikitattun idanuwanta tana kashe mishi ido ɗaya Ya kasa jurewa shiyasa ya sake damƙo ta yana cewa, "haba Princess I need you, please kar kiyi min wannan horon, ko nawa ne zan iya ba ki domin in kasance tare da ke a yau." Harshenta ta sanya ta lashi kumatun sa tana dariya, sai kuma ta kafa mishi fingers ɗinta da suke zaro-zaro kamar na cin kare, sun sha jan lalle sun yi wani kyau na ɗaukar hankali a kan zara-zaran fararen yatsunta, hakan ne yasa ta hana shi ƙoƙarin kissing ɗinta da yake faman yi kamar wani maye, har ya soma yawo da hannunsa ɗaya a jikinta, sai tayi saurin cewa, "idan fa kana taɓa Ni farashin ka yana ƙara yawa ne. Wait until we trade." "So how much do you need? What do you want me to give you? I can give you wlh." Yafaɗa cikin rawan murya wanda tuni ya fice a cikin hayyacin sa sabida jin albarkatun jikinta manne da shi Janye jikinta tayi tana yatsina fuska, sai kuma ta ɗauki wayanta tace, "For my account number, send me the money before we talk." "Ok." Ya furta da sauri yana ciro nashi wayan tare da kwashe Numban nata da ta karanto mishi, bai yi wata-wata ba ya tura mata 50k a account ɗin Tana gani ta ƙyalƙyale da dariya, sai kuma ta dube shi cikin tsananin nuna soyayya tace, "But please be patient Malam, now I don't have your time, don haka idan kana so muyi wata harƙalla ka bari sai na dawo daga tafiya, sai abun da kace zan yi." Ta ƙare maganar tana cije leɓen ƙasan bakinta cikin wani irin salo me jan hankali Shi kuma jajayen idanuwansa ya zuba mata, tare da matsowa sosai wajenta, hannu yasa zuwa saman cinyanta yana shirin kware mata skirt din da ke jikinta, cikin marairaice fuska yace, "Please help me I can't stand it for a while, Princess I love you I need you in my life." Ɓata fuska tayi tana ɗaura dogon farin hannunta a saman nashi, tare da cewa, "kuɗin ka bazai yi min maganin komai ba Malam, idan ba ka amince da abun da nace ba zan dawo maka da kuɗin ka, ba na son takura." Ta ƙare maganar tana kwaɓe fuska kamar zata yi kuka Hakan yasa yace, "shikenan is ok, na amince Princess, but ko ɗan kaɗan ne ki bani dama in ɗan rage wani abu." Murmusawa tayi tace, "You don't agree with what I'm telling you?" "Na yarda but please, just 10mint." "Ok." Ta furta tana ɗan janye hannunta daga saman nashi hannun Hakan ne ya ba shi damar ci gaba da abun da yayi ninya cikin sauri da nuna zalamansa, they immediately clung to each other, at one point they began to romance tamkar zasu haɗiye kansu, kowannen su cike da ƙwarewa yake aikawa ɗan uwansa message Sai da ta ga abun yana son wuce gona da iri sannan ta janye jikinta, duk da dai sosai taji daɗin kasancewar su tare don ba kaɗan ba alamu ya nuna mata Tariq ɗan Love ne ya iya sarrafa Mace, ta san cewa duk sanda suka kasance tare zata ji daɗi ba kaɗan ba, sai dai kuma bata yi ninyar ba shi kanta ba a yanzu don ba shi ne a gabanta ba, shiyasa ta lallaɓa shi sannan ta samu ta fito ta wuce gida Shima ya tafi zuciyarsa na ƙara tsananin bege da ƙaunarta, bai san ya zai yi da mahaukaciyar ƙaunarta da sha'awar ta da yake fama da su ba, duk da dai ya san ita wace ce amma a zahiri da zai samu damar mallakar ta a matsayin Mata wlh sai ya aure ta, amma zai jure duk wani wulaƙanci domin ya mallake ta, shi dai ya san ya more idan ya samu zuƙeƙiyar yarinyar nan, bata da makusa ko ta'ina tayi mishi ɗari bisa ɗari, ya san idan ta zama mallakin sa dole zai hana ta mu'amala da duk wani namiji, ita ba irin matan nan da za'a iya yasar da su bane, sun san kan rayuwa kuma sun san yanda zasu bi domin su mallake zuciyar ɗa namiji, don haka shi babu ruwan shi don ita karuwa ce, shi dai ya same ta domun farin cikin zuciyarsa, ita kaɗai ce zata iya dashi.              Arab kuwa koda ta shiga gida ta tarar da ƴan uwanta a gindin bishiya ne zaune. Inna kuma tana ɗaki a lokacin, but tunda ta ji muryan Arab sai ta fito tana cewa, "Oh Auta wai ina kika je ne yanzu aka zo neman ki? Kinga baƙo a waje?" "Eh na ganshi Inna, mun je kasuwa ne Ni da Besty mun yi siyayyar tafiyana." "Tafiya kuma?" Cewar Innar tana isowa wajen itama ta zauna, yayinda ta bi kayan da Ummu take fitowa da su suna gani Zahra tace, "wanne tafiya kuma kika samu za ki yi?" Dariya tayi tana ɗaukar wayanta tare da latsawa tace, "Abuja zan je." "Abuja Autana? Ke kuwa me ya haɗa ki da Abuja da za ki je? Me za ki yo a can?" "Uhm ai Inna wani Alhaji na samu wlh me kuɗin gaske, ina faɗa miki idan har na samu shiga a wajen shi to kakar mu ta yanke saƙa, wlh ina tunanin ma sai dai in Yi wuff dashi don ina ji a jikina kin kusa zuwa Makka Inna." "Don Allah da gaske kike yi?" Innar tafaɗa cike da washe baki "Wlh kuwa Inna, shiyasa nake son in je saboda ya gayyace Ni, but ba wani daɗewa zan yi ba yakamata dai in je inga masaukin sa ne." "Kai wannan ganganci ne wlh, taya ya za ki bi mutum har wani uwa duniya don kawai yana son ki? Har yaushe farashin naki ya sauka haka haba Arab? To makarantar naki fa ko kin manta kuna da Exams ne?" Arab kallon Ummu da ke maganar tayi tana waro mata idanu da cewa, "lallai Aunty Ummu ba ki san waye Alhaji Bashir ba shiyasa kike wannan zancen, wlh ko ke ne kika samu damar nan sai kin je, to meye a ciki don na je can mun fahimci juna? Ba ki san irin kuɗin da ya tura min bane lokacin muna gidan Aunty Firdausi, wlh bazan zauna ba don na san arziƙi ke kirana." Baba da ya fito daga ɗakinsa domin duk yana jin abubuwan da suke tattaunawa a kai, sai ya tsaya daga bakin ƙofan yana cewa, "akul ɗinki A'isha da wannan banzar shirmen, wato abun naku ya kai har ki bi namiji wani garin tsaban gantali ko? To babu inda za ki je, baza ku mayar da Ni mutumin banza ba duk kun hana Ni saƙat a gari, ko ina zancen ku ake yi na gagari baku tarbiyya, wannan abun da me yayi kama? To zan ɗauki mummunan mataki a kan ku wlh idan har baku gyara ba, kowaccen ku ta samu Miji tayi aure don bazan iya wannan shirmen naku ba, na gaji wlh." Inna kamar jira take yi ya ajiye numfashi sai ta hayayyaƙo mishi tana cewa, "wlh bazai saɓu ba, ai zancen ka zancen banza ne tunda ba kai kaɗai kake da yaran ba, baka isa kayi musu aure a wannan marran sabida kana min baƙin ciki ba, na gode Allah ya bani ƴaƴa mata masu share min hawaye amma kai baƙin ciki yayi maka katutu kullum so kake yi kaga bayana, to wlh na rantse da Allah ba ka isa ba Iro, tun wuri ma ka canza tunani idan zugin ƴan gari zaka bi can ta matse maka, mu kuwa ba yau muka saba da su ba kuma maganganun su bazai mana komai ba, yara dai nawa ne sai abun da suka yi ninya zasu yi babu takura a rayuwar su, su ba Bayi bane balle ace za'a hana su ƴancin kansu, duk abun da suke so shi zasu yi tunda dai basu tarewa uban kowa hantsin gaba ba." "Yanzu Ni kike faɗawa haka Harira? Ni Mijin ki?" Yayi maganar yana nuna kansa "Yo yau ka soma ji dama? Ai idan har baka fita a harkan yarana ka dena takura musu a kan mutanen gari ba; wlh daga kai har su sai dai aniyar ku ta ƙare muku, yarana nan gari nan bari kurwan su kurr, kuma insha Allahu da su zan yi kuɗi, sai zaman anguwan nan ya gagare mu don mun fi ƙarfin zama a kwata." Kanshi kawai ya gyaɗa yana juyawa ya shige cikin ɗakin sa zuciyarsa kamar zata yi bindiga ta fashe, sai dai bazai iya amayar da abubuwan da ke ransa ba, Harira ta rigada ta fi ƙarfin sa bai san ya zai yi ba, bai san ta wanne hanya zai bi domin ya ceto rayuwar ƴaƴan shi ba, haƙiƙa yana kaicho da wannan rayuwar, yana tur da Allah wadai da samun Harira a matsayin Matar sa, ga shi yanzu ba shi da wani ikon da zai iya tsawatar musu a matsayin waɗanda suke ƙarƙashin ikon shi, bai da wannan fawan. Har hawaye yake sharewa sabida yanda ya ji sun ci gaba da shewa da maganganu wanda ko alamu bai nuna sun ɗauki zancen shi da wani muhimmanci ba, inda yana jin Inna tana sake zuga Arab ɗin sosai "Duk yanda za'a yi ta damƙo mutumin ta ɗaura shi a tafin hannunta, akwai ma maganin da zata bata zuwa gobe sai ta sake yin farin jini fiye da ko yaushe, kuma duk abun da ta buƙata ya bata sai ya bata a nan take, bari dai ta je ta ga yanda zai susuce a kanta." Ƙarshe dai rediyo ya sa a kunnen sa ya dena sauraron baƙin cikin da suke ƙunsa mishi.              Zuwa washe gari kuwa Arab tayi sammako ta gama shiryawanta tsab. Ibrahim ya zo da motan abokin sa zai kaita tasha ta samu abun hawa, tare da Ummu suka je tayi musu rakiya. Zahra kuma na gida suna aiki da Inna Bayan sun kaita tashan har ta hau Mota sannan suka juyo. [15/07, 9:25 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA TARA* _______________  *ABUJA STATE*             Tun shigowar Nawwara cikin falon Mummy ta washe baki tana cewa, "iyee ƴan matan Yayanta, wannan cancaɗi haka! Kwalliya yayi kyau." Dariya tayi tana isowa wajen, yayinda ta samu wuri kusa da Ikhlas ta zauna tana cewa, "Mummy good morning?" "Morning Nawwara, har kin fito? Ga shi mutumin naki har yanzu shiru nake ji ya ƙi fitowa." Ikhlas tace, "ai yanzu Mummy za ki ganshi, naga ya shiga part ɗin Abba but maybe ya fito." Sai kuma ta kalli Nawwara tana cewa, "Aunty kin Yi kyau wlh, sosai da sosai." Baki Nawwara ta washe tare da cewa, "thank you sister, Ina Zainab?" "Tana school, yanzu ta fita." "Ok Mummy bari in je in duba shi ko ya shirya." Nawwaran tafaɗa tana miƙewa Mummy tace, "to, but tell him don't waste time please, you should go now, gwara ku tafi da wuri zai fi ai.. Ikhlas tashi ki je ɗaki na ki ɗauko min baƙin ledan nan dana ɗaura a kan gado, ki riƙo da kyau fa kar kiyi min ɓanna." Miƙewa tayi da sauri tana cewa, "kai Mummy sai kace wata yarinya?" Sai ta ruga a guje kuma ta hau steps ɗin benen While Mummy na cewa, "ai na san halin ki ne tunda ba kya abu da hankali".                    *****          Nawwara kuwa tana shiga ɗakin Malik ta hange shi zaune a gaban gadon shi yana ƙoƙarin saka shoes ɗin sa Shima ɗago kai yayi ya zuba mata idanuwansa masu shegen haske da ɗaukar hankali, sai ya sakar mata murmushi kawai yana bin ta da kallo tare da ƙarewa shiganta kallo Doguwar riga ce a jikinta kalan ruwan hanta, me gajeren hannu da igiyoyi, rigan ta lafe mata daga sama har ƙasa babu wani shafe sai na jikinta, ƙam ta kama ta, stones ne kawai aka yi kwalliya dashi a gaban rigan while ta ɗaura farin gyale a saman attachment ɗin kanta; yayinda ya rufe mata har zuwa kafaɗun ta, kasancewarta fara rigan tayi mata matuƙar kyawu musamman yanda ta sha makeup a fuska, sai sheƙi fuskar nata take yi tana glowing, sai tayi using da farin hill shoes tare da Hangbag ɗinta me ɗaukar hankali While shima Malik farin yadi ya saka wanda aka yi mishi ɗinki dai-dai da jikinsa na zamani, yayi masa kyau matuƙa ya fito da ainihin kyawu da kamalansa, kyakykyawar fuskarsa yana zagaye da ƙasumba da dogon gemu da ya ƙara ƙawata face ɗin nasa, duk wata Mace idan ta kalle sa dole ta sake kallonsa sabida haɗuwar sa, kana kallon sa zaka hangi irin tsantsan tsaftar shi da gayun shi, shiyasa Mata suke mishi rubuti sabida ya iya wanka matuƙa Malik, duk inda namiji ya kai Malik ya kai, ga iya soyayya da ba wa Mata muhimmanci, shi dai a rayuwa yana bala'in ƙaunar Mata, ko ya ya suke yana matuƙar girmama su kuma yana jin daɗin mu'amala da su, shiyasa ba ya rabo da su a koda yaushe Nawwara tahowa wajensa tayi tana murmusawa tare da cewa, "Wow! My prince charming you look very well, honestly can choose." Hannu ya miƙa mata yana kama nata tare da cewa, "ai ban kai ki ba, anya zan iya tafiya da ke? Kar azo a samu matsala kuma wani yayi min ƙwace." Ya ƙare maganar yana ɗaura ta a saman cinyan sa, tare da kai fuskarsa kan nata yana shinshina ta cike da tsantsan shauƙi While itama haka, sai dai murmushi ne a kan fuskarta, inda ta sauke mishi hot kiss before ta janye bakinta tana cewa, "babu wanda ya isa ya ƙwace maka Ni, Ni an yi ni ne saboda kai kaɗai, I'm yours, don haka ka dena saka wani abu a ranka, idan ba kai ba sai rijiya, rijiyan ma mai kwalabe." Ta sake kai bakinta ta lashe saman laɓɓansa Shi kuma sai ya ɗaura hannunsa a ƙeyanta ya haɗe bakunansu waje ɗaya, tsawon lokaci suna kissing junan su before su janye wanda har sun soma fita cikin hayyacin su. Hakan bai ishe su ba sai da suka sake romance din juna sannan suka haƙura ganin suna shirin manta a inda suke da kuma abun da zasu yi Ita ta ƙarisa saka mishi takalmin sannan suka fito tare da ɗan ƙaramin Jakar sa kasancewar kwana zasu yi Mummy da Ikhlas har yanzu suna zaune a Falon, inda Ikhlas har ta kawo mata saƙon da ta aike ta Mummy tuni ta soma koɗa su don ba ƙaramin ƙaunar Nawwara take yi a ranta ba, tana matuƙar sonta da ɗanta saboda wayewanta da ƙaunar ɗanta da take yi, shiyasa take ganin kamar duk duniya ɗanta ya fi dacen Mace ta gari idan ya auri Nawwara Nawwara ɗiya ce wajen ƙanwar Abban su Malik. Gidan su a farkon anguwa ne duk da akwai nisa da gidan su Malik, but komai na rayuwar Nawwara a gidan su Malik take yin sa tun tana ƙarama, babu wanda bai san soyayyar su a family ba har dangin Mummy da suke Kano, kasancewar ita Mummy ɗiya CE wajen Sarkin Kano, ita ce ƴa ta biyu a yaranshi da ya mallaka, tana aure a nan Abuja tare da mijinta Alhaji Atiku Nera, shahararren ɗan kasuwa da yayi suna a faɗin Nigeria da kewayen ta, babu abun da bai mallaka ba sabida tsaban kuɗin sa, yaran sa uku Allah ya ba shi, Abdul Malik sai Zainab sannan sai Ikhlas mai sunan Mahaifiyar shi da ta rasu, Habiba Alh. Atiku su biyu ne iyayen su suka haifa, daga shi sai Mahaifiyar Nawwara. Itama a Abuja take Aure kuma abokin Alhaji Atiku ta aura. Nawwara kaɗai suka haifa ita kenan musu, suna sonta kamar ransu domin ba sa son abun da zai ɓata mata rai, shiyasa ta tashi cikin sangarta tunda ƴar gata ce gaba da baya, duk abun da take so shi take yi. Allah ya ɗaura mata ƙaunar Malik tun tana yarinya bata san meye rayuwa ba, shiyasa ya soma koya mata duk wani rayuwar wayewa da tanbaɗewa, kuma shi ya soma sanin ta a ɗiya Mace bayan yayi mata wayau ya amshe mata budurcin ta tare da yin mata alƙawaruka kala-kala, shiyasa take ganin babu wata Mace da ta isa ta mallake shi face ita, ita kaɗan ta, shi nata ne domin an yi shi ne don ita, tana da tsananin kishi zata iya komai domin shi Don haka shi kansa yana taka-tsan-tsan saboda shegen kishin ta, but hakan bai hana shi yin mu'amala da mata kala-kala ba duk da ya san halin ta, sai dai har a zuciyarsa bai taɓa son wata ɗiya Mace ba bayan Nawwara. Amma yanzu kuma ƙaddara tana neman canza mishi akala, duk da a baya yayi mata alƙawarin ita kaɗai ce matar shi a duniya, to bai taɓa tunanin zai iya cin karo da wata wacce zuciyar shi zata faɗa da kogin ƙaunar ta a nan take ba, sai dai abun haushin ma bai san inda zai ganta ba, a kullum da hoton ta yake kwana yake tashi, shi kaɗai yake gani ya ji daɗi a ransa, soyayyarta ta shiga cikin jikinsa ta zame mishi jini da hanta, abun da yake ji a kanta bai taɓa jin makamanciyar irin sa a kan kowacce Mace ba har Nawwara da yake tunanin yana matuƙar ƙauna, sai dai kuma bai san ya wannan soyayyar tashi zata kasance ba domin yana ganin makauniyar soyayya ce wacce zata iya kai shi ga halaka, bai san ya zai yi ba duk da yana fatan ace wata rana ya haɗu da yarinyar, koda hakan zai zama silan mutuwar shi ce sai ya mallake ta, dole ne ya mallake ta, sai dai idan Nawwara zata haƙura amma dole ne ayi ɗayan biyu, ko ya aure su duka biyun ko kuma ita kaɗai, amma babu fashi bazai taɓa iya cire soyayyar ta ba, kuma ko nawa ne zai iya kashewa don samun ta a cikin rayuwar shi, amma taya ya hakan zai faru? Abun da kamar wahala domin bai san ta inda zai soma ba, aina zai ganta bare har ya bayyana mata irin soyayyarta da ya kamu da ita? Tabbas idan aka ci gaba da tafiya da yiwuwar ya rasa tunanin sa gaba ɗaya saboda bege da tsananin shauƙin haukan soyayyarta.                  *******              Har suka gama sallama da su Mummy suka rako su haraban gidan, gaba ɗayansu har Abba da shima ya fito daga part ɗinsa. Sannan suka hau Mota suka tasarwa hanya ɗoɗar Duk da Malik ba ya cikin walwala sakamakon damuwa da tunanin yarinyar da take ƙarƙashin ransa, amma haka ya biyewa Nawwara da ke mishi hira, suna zantawa sama-sama yayinda yake kwasa gudu a titi. Wayan sa ne tayi ƙara sai ya ciro ta daga aljihu yana dubawa, ganin sunan wani friend ɗinsa sai ya ɗauka yana karawa a kunne. A haka suka ɗauki lokaci suna waya before ya kashe yana kallon Nawwara tare da kashe mata ido ɗaya yace, "ƴan Matana zamu wuce Zaria kafin mu je Kano, akwai Aboki na da zamu haɗu a can, yace min yana Zaria so ina son mu haɗu tunda muna kan hanya. I want to say hello because we haven't met in a long time." Murmushi tayi tace, "babu komai my Prince, ka san yau ina matuƙar farin ciki sabida kasancewar mu tare, so duk inda zamu je bazan gajiya ba Ni dai fatana mu kasance tare, ba don kar su Mummy su kira waya ace musu bamu ƙarisa ba da yau kawai mun hutawar mu a wani hotel, hakan zai faranta min rai sosai." Hannu ɗaya yasa ya kamo nata yana mata murmushi da cewa, "nima haka nayi tunani, but ki bari zamu samu time zamu kasance tare har sai mun gaji, duk sanda zamu dawo gida zamu yi yawon mu before mu koma." "Yauwa my prince, haka nake son ji, Allah ya barmu tare." Ta furta tana kai mishi kiss a kuncin sa Dariya yayi yace, "ki bari fa kinga tuƙi nake yi kar ki ja min matsala." Narke fuska tayi da cewa, "uhm kai ne ka san ba na gajiya da kai, ban ƙi ba mu dauwama manne da juna a koyaushe, ina matuƙar ƙaunar ka Malik, na mallaka maka komai nawa sai yanda kayi dani." Murmushi yayi yana sake tamke hannunta a cikin nasa, tare da sakar mata kyakykyawar kallo mai tsananin shauƙi da shiga jiki, a hankali cikin raɗa-raɗa da jan hankali irin nasa yace, "na san da haka Princess ɗina, nima ina tsananin ƙaunar ki, but baza ki gane hakan ba sai a nan gaba." Dariyan farin ciki ta saki itama tana mishi kallon soyayya. Cike da shauƙi da ƙaunarsa take ƙara narke mishi tana jan shi da hira me shiga jiki Cikin ƙanƙanin lokaci suka isa Zaria tunda yana zuka gudu, kafin karfe biyar sun kai. Sai ya kira Abokin nashi ya sanar mishi inda suke Babu jimawa abokin ya taho a motansa. Parking yayi ya fito ya isa wajen motan Malik Sai shima ya fito daga cikin motan nashi, da dariya a fuskokin su suka cafke hannaye cikin tsananin farin cikin ganin juna Itama Nawwara fitowa tayi tana kallon su ganin suna gaisawa Sai Abokin yace, "ah my Man wannan kuma kyakykyawar fa?" Murmushi Malik yayi yace, "Ƙanwata ce kuma wacce zan aura, Do you remember Nawwara telling you time muna school?" "Yeah! Yeah! I remember, kana nufin ita ce still?" "Yes ita ce. Nawwara ga Aboki na, my classmate his name is John." Hannu John ya bata don su gaisa. Sai ta miƙa mishi nata tana murmushi tare da cewa, "hello." "I'm glad to meet you. The truth is you are beautiful. My friend deserves to have you." Duk dariya suka yi, inda ita kuma Nawwara tace, "Thanks." Cike da farin ciki a fuskarta "Ok amma zaku je gidana ku huta zan ji daɗin hakan, yau ina da manyan baƙi." Yafaɗa yana washe baki Malik yace, "no John muna kan hanya ne, let sometimes we meet again, I will come especially for you but now we are in a hurry." "Ok babu yanda na iya ai, nayi farin ciki duk da haka ma." John ɗin yayi maganar yana murmusawa tare da ba shi hannu suka sake gaisawa. Daga nan suka yi sallama ya wuce nashi motan Su ma suka shiga nasu Malik ya ja suka wuce. "Bari mu nema abinci ko Baby?" Yayi maganar yana kallon Nawwara Sai ta gyaɗa mishi kai tana cewa, "Yes because I'm hungry now." Hannunta ɗaya a kan cikin ta tana shafawa "Ok ga bank can, let me withdraw money, I have no money in my pocket." Yayi maganar yana yin parking a gefen titi, "ina zuwa yanzu zan dawo." Ya buɗe motan ya fice zuwa tsallaken titi inda ya ga kamar wajen cire kuɗi ne. Yana zuwa ATM card ɗinsa ya zaro yana shirin tusa wallet ɗinsa da ta biyo baya, sai kuma ta faɗi a ƙasa, juyawan da zai ɗan yi ya ɗauka sai suka ci karo da Zahra da ta taho da sauri tana waya itama bata kula dashi ba, bata san zai dawo baya ba shiyasa suka ci karo har goshin su ya haɗe da juna. Da sauri suka furta, "oshhh!" Suna ɗagowa the same suka kalli juna. Waro idanu sosai Malik yayi yana kallonta saboda ganin yanda lokaci ɗaya tayi mishi kama sak da yarinyar da ya kamu da soyayyarta da bai san inda zai same ta ba, sai ga ta a gabanshi for surprise Ita kuma Zahra tuni tace mishi, "sorry." Tana ƙoƙarin janye jikinta ta wuce Sai yayi saurin dakatar da ita yana cewa, "ba ki ji ba don Allah." Lokaci ɗaya ya kai hannu ya kamo nata hannun ba tare da ya san yayi hakan ba Shiyasa ta tsaya tana kallon shi itama, sai dai bata yi yunƙurin janye hannun nata ba illa kallon kyakkyawar fuskarsa da take yi Murmushi yayi mata yana janye hannun sa da cewa, "kiyi Haƙuri na taɓa ki." "No babu komai." Ta furta itama tana murmushin har da canza tsayuwa cikin yanayin jan hankali Shi kuma sai a lokacin ya gama tantance ba ita bace domin suna da bambanci da wancan, amma tsananin kaman nasu yayi over a jikinsa yana ji duk yanda aka yi suna da alaƙa da juna, kamannin ta sak yake gani a jikin wannan dole suna da alaƙa, zai iya yiwuwa, shiyasa yayi saurin cewa, "idan babu damuwa ki bani Numban ki mana, don Allah kar ki ce na tsayar da ke a kan hakan, and ina son..." Shiru yayi sabida ganin Nawwara a gaban su tamkar kububuwa ko wacce aka hankaɗo    Lokaci ɗaya idanuwanta suka rikiɗe tsaban jaraba saboda duk abun da ya faru tana hange daga cikin mota, shiyasa lokaci ɗaya ta fito ta isa gaban su, kuma bata yi wata-wata ba ta kwashe Zahra da maruka har guda biyu, cikin tsananin kishi da ɗaga murya take cewa, "ke dan ubanki wace ce da har kika samu damar yin magana da Mijina? Karuwan banza karuwan hofi ba'a faɗa miki mijin wata bace...?" Tsawa Malik ya daka mata yana cewa, "ke Nawwara kina da hankali? Wannan wanne irin hauka ne?" A zuciye ta kalle shi tace, "hauka kace ko? Dama abun da kake son zuwa kayi kenan shiyasa ka taho damu nan? To asirinka ya tonu wlh zaka ga hauka yanzu." Kafin su farga har ta ciro takalmin ta me tsini ta kwaɗawa Zahra da ke tsaye ƙiƙam al'ajabin abun da Nawwara tayi mata ya cika ta, sai ji tayi ta sake buga mata takalmi a saman goshi Lokaci ɗaya ta saki ihu tana duƙewa a wajen; nan da nan jini ya soma tsatstsafo mata                Salatin mutane ya karaɗe wurin; har Malik da jikinsa lokaci ɗaya ya soma rawa tsaban ya rikice. [17/07, 10:35 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA GOMA* _______________Da sauri Malik ya duƙa yana kamo hannun Zahra cikin tashin hankali, yayinda ya kai dubansa kan goshin ta da ke fitan jini, ya kasa ma furta komai sabida halin da yake ciki illa bin wurin da yake yi da idanu Nawwara kuma na tsaye a kansu ta ƙi mayar da takalmin sai huci take yi Yayinda wasu daga cikin jama'ar wurin har sun iso sun tabaibaye su suna faɗin, "subhanallah.. meyasa zata yi mata haka? Me ya faru?" Duk laifin sun ɗaura a kan Nawwara tunda a kan idanuwansu suka ga komai, sai faɗa suke mata a kan, "bata kyauta ba, idan wani abun ya haɗa su ai ba sai ta kai ga haka ba." Sai dai ita bata damu da jama'ar ba kuma bata damu da surutun nasu ba, baƙin cikinta yanda Malik ya duƙa yana taimakon Zahra, shiyasa cikin zuciya da ya ɗebe ta kamar wata me Aljanu ta soma hauka a kan, "sai ya saki Zahra sun wuce, bai isa ya taimake ta ba wlh." Ta riƙe shi gam tace, "ta rantse da Allah bai isa su wuce ta a nan wajen ba sai dai su tafi su bar Zahra, bazai taimake ta ba." Har da kukan ta Abun fa ya ba wa mutane mamaki ganin kishin hauka ƙiri-ƙiri da ake yi a gaban su, tamkar bata da tausayi Shi kuwa Malik da ya san halin Nawwara kuma ya san me zata iya aikatawa, bai yi mamaki ba kwata-kwata, sai dai bai san cewa rashin imani da baƙin kishin nata zai iya rufe mata idanu ta aikata wannan haukan a kan abun da bai kai ya kawo ba, sai ya daka mata tsawa yace, "ta sake shi ko ya illata ta." But wlh ta ƙi, sai buɗe masa idanu tayi cikin nuna tijara tace, "na rantse da Allah babu inda zaka matsa da ita, baza ka taimake ta ba, kawai ka kama hanya mu tafi." Zahra taga abun da ya fi ƙarfin ta wajen wannan sheɗaniyar yarinyar, ita abun ma sai ya zame mata t.v don ta kasa kataɓus, yayinda zafin ciwon ma ya dena shigan ta sabida tsananin mamakin Nawwara, ikon Allah kawai take kallo a wajen ta. Ganin abin zai zame musu matsala sai ta ƙwace hannunta da Malik ya riƙe gam ta ratsa mutane ta wuce da sauri, domin idan ta zauna ganin wannan bala'in zuciyarta ce kawai zata buga jininta ya ƙare a banza, gwara ta soma taimakon kanta wajen tsayar da jinin before ya ƙare, a ranta sosai ta ji haushin Nawwara da ta kasa mayar mata da martani ko kuma ta rama abun da tayi mata, tabbas da ace kanta ba ya zuban jini da an kwashi ƴan kallo don baza ta taɓa ƙyale ta ba, faɗa da suke siyarwa ai ta zo gidan ta ne, sai dai kuma arzikin ta ɗaya Malik da yake ta bata haƙuri kamar zai duƙa mata, ba don shi ba wlh baza ta ƙyale Nawwara ba. Haka ta wuce ta bar su a wurin ana ta zagin Nawwara sabida abun da tayi Malik kuwa tuni ya wuce wajen motan sa ransa a mugun ɓace ya shige, yana ƙoƙarin tayar da motan ya barta a wajen don abun da yayi ninya kenan, amma sai tayi saurin shigowa sabida fahimtar abun da yake ƙoƙarin yi, bai bi ta kanta ba ya ja motan a guje ya bar wurin zuciyarsa na ƙara tafarfasa kamar zai ka dasu a hanya, baƙin cikinsa da bai amshi Numban Zahra ba Ita kuwa Nawwara ko a jikinta sai ma gyara zama da tayi tana kallon hanya, zuciyarta fari tass domin ta san koda wasa bazai ƙara mata irin haka ba, idan ma yana tunanin yi a gaba to dole zai tuna da abin da tayi mishi yanzu ya fasa, ta tsani a rayuwa ta ganshi tare da Mace kuma dole ne ta riƙa ɗaukar mataki, ita kaɗai ce tashi bai isa yayi mu'amala da wata Mace bayan ita ba Har suka kama hanyar Kano amma Malik bai yi mata magana ba, kuma bai tsaya a ko'ina ba bare su samu wani abun su ci Ita kuwa jin yunwa ya ishe ta sai ta soma mishi ƙorafin, "yunwa take ji." Wani kallo da ya watsa mata sai da hanjin cikinta suka kaɗa. Yana shirin yin magana wayansa tayi ƙara, haka ya ɗauka ya kara a kunne ganin sunan Mummy Tambayarsa take Yi, "har yanzu basu kai ba?" Saboda ta kira waya can an ce basu je ba Yanda yake jin mugun ɓacin rai daƙyar ya iya buɗe baki yace, "mun kusa kaiwa Mummy, motan CE ta samu matsala." "Ayya dama nayi tunanin haka, shiyasa nace ku hau jirgi da wannan wahalar, to yanzu ga shi kun samu matsala sai shigan dare yanzu zaku yi, yanzu da karfe tara ta wuce ko zaku samu wajen kwana ne Malik ba na son tafiyar daren nan?" "No Mummy mun kusa, ki ajiye wayan zan kira tunda ina tuƙi." Ya furta yana zare wayan daga kunnen sa, bai jira abun da zata ce ba ya kashe ya ci gaba da tsula gudu a kan kwalta. Bai sake kallon inda Nawwara take ba balle ya saurare ta Itama sai ta share shi tana cin magani tunda ta san ba laifi tayi ba, ai ya san halinta a kan kishin sa babu abinda baza ta iya ba, abun baƙin cikin nata ma yanda yake tambayar Zahra number wato yaga kyakykyawa shiyasa yake son ƙulla alaƙa da ita, ina ai baza ta taɓa bari ba, gwara da tayi musu haka bazai taɓa samun wannan damar ba.                 ********        Ita kuwa Zahra chemist ta wuce sabida yanda jininta ke zuba sosai, ga azaban zafi da yanzu ya addabe ta, shiyasa ta je aka yi mata treating wajen, dama kuɗi ta je ciro ma Innar su da za'a siya fridge dashi, sai kuma ga abun da ya faru, ƙarshe ma sai ta account ta biya me Chemist ɗin ta wuce gida tunda babu kuɗi a tare da ita Tana zuwa Inna da Ummu suka ga bandage a kanta suka hau tambayar ta hankalinsu a matuƙar tashe Tsaban takaici ma Zahra ta kasa yin magana, sai da suka ishe ta da tambaya sannan ta sanar musu abun da ya faru Ai kuwa tana rufe baki Inna ta hau ruwan bala'i, haka take zagin Nawwara ta uwa ta uba tana ƙunduma mata zagi, tace ma Zahran, "su koma wajen ko zasu ga matsiyaciya wlh sai taga uban da ya tsaya mata, sai tayi Shari'a da ubanta tunda ta taɓa ta." Zahra tace, "ba na tunanin za'a same su Inna don sun rigada sun tafi." "Ai duk da haka sai mun je, sai naga uban da ya tsaya mata, tashi maza muje ki kaimu wajen, ƴar iska matsiyaciya dan ubanta mu zata nuna ma hauka? Gidanta ta zo yau sai na kakkarya matsiyaciya inga uban da ya tsaya mata." Haka Inna ta tasa Zahra har Ummu suka fito suka tafi kasuwa inda abun ya faru. Sai dai koda suka je basu same su ba amma haka Inna take ta ruwan bala'i tana jifan su da alkaba'i har Malik ɗin, a cewar ta, "dama shi ya kawo ta don ta bugar mata ɗiya, da sun tsaya da sun gane shayi ruwa ne, Allah ya so su, amma duk ranan da tayi tozali da yarinyar komin daɗewa to Zahra ta sanar mata sai ta ɗauki mummunan mataki a kanta." Haka suka dawo gida Baba na tambayar inda suka je; don ya dawo bai same su ba shiyasa yake tambayar su Inna sai surfa bala'i take yi tana cewa, "to ko na faɗa maka mai zaka iya yi a ciki? Ga ta nan Zahra CE wata matsiyaciyar la'ananniyar yarinya da uwarta ta haife ta ba ta hanyar sunna ba; ita ta fasa mata kai, ai naso in same ta wlh da sai naga uban da ya tsaya mata, ƴar iskan yarinya kawai har ita ta isa ta fasa ma yarinyata kai? Ai kuwa ta tono tsuliyar dodo don wlh jafa'i da masifa sai ya ƙare mata, sai nayi ta jan mata alkaba'ai yana ƙare mata, in Allah ya yarda sai taga masifa da bala'i dan uban ta..." "Haba don Allah Harira ki sarara haka mana, mene ne haka ke ba ƙaramar yarinya ba? Kin tambayi ita Zahran ta sanar miki mai ya haɗa su ne haka kawai za ki yi ta zagin yarinya? Komai ai ɗan haƙuri ne mene ne a duniyar? Duka-duka nawa take? Kuma tsautsayi babu inda ba ta faɗawa..." "Eh dama ai haka zaka ce, shi tsautsayin dan ubanshi bai san inda zai faɗa ba sai a kan yarinyata? Kuma wancan Shegiyar ce zata fasa mata kai? Dama na daɗe da fahimtar ba ƙaunar yaran nan kake yi ba, da Allah Malam idan baza ka iya taimaka mana da komai ba kayi min shiru don ba na son wa'azinka na banza ƙara tunzura Ni yake yi." "Allah ya ba ki haƙuri." Baba ya furta yana yin gaba ya shige ɗakin sa Haka Inna tayi ta masifa Ummu na taya ta don sun ƙi haƙura da zancen sam, sai da suka gaji don kansu sannan suka sarara Ita kuwa Zahra takaici da baƙin cikin abun da Nawwara tayi mata duk sun hana ta saƙat; ko magana ta kasa yi, tana jin dama ace zata sake ganin Nawwara, uhm wlh sai ta kwantar da ita don ita nata mai sauƙi tayi mata, Chemist kawai ta je, but ita gadon asibiti za'a kaita, kuma ƙarshe sai ta ƙwace Malik ɗin a hannunta taga ƙaryan hauka, baƙin cikinta ɗaya bata san inda zata same su ba, ta cije yatsa ya kai babu adadi, da ace ta ba shi Numbanta da shikenan. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️                *ABUJA STATE*           Arab ta isa Abuja wajen gabanin magriba, sai ga Drivern Alh. Bashir ya zo ya ɗauko ta ya isa da ita hotel ɗin da Alh. Bashir yake zaune, kasancewar shima kasuwanci ne ya kawo shi nan Abuja but asalin shi ɗan Bauchi ne, a can iyalansa suke zaune but yawon gari-gari yake yi sabida harkan business ɗinsa, har ƙasashen ƙetare yana fita Alh. Bashir irin mutanen nan ne masu son Mata, har kawalai yake dasu waɗanda suke kawo mishi mata don kawai ya ji daɗi dasu, Matarsa ɗaya da yaransa biyu duka maza. Kasancewar matarsa ta mallake shi shiyasa ya kasa yin mata kishiya; but yana bin matan Banza a waje Tun da yaga hotunan Arab ya susuce da kyawun ta, ya gaza haƙura shiyasa ya buƙaci, "ta taho nan ta same shi." Daga shi sai Drivern sa wanda ya san sirrin sa shiyasa ya aike shi ya ɗauko ta Yana kawo ta hotel ɗin ya nuna mata Numban ɗakin da Alh. Bashir yake ciki, ta buɗe ta shiga tana bin ko'ina da kallo, nan idanuwanta suka sauka a kan Alh. Bashir ɗin da ke zaune a saman sofa daga shi sai gajeren wando Ƙaton Mutum ne don a shekaru zai haura sittin da biyar, Allah yayi mishi jikin girma don lukutete ne, ga shi baƙi babu zubin kyau ko kaɗan a tare dashi, tamkar wani basamude haka yake sai ƙaton tumbi a gaba. Yana ganinta nan da nan ya washe baki tare da miƙewa yana isa wajen ta, hannu yasa ya kamo nata a hankali ya janyo ta ya haɗe ta da jikinsa yana cewa, "welcome My Baby, sannu da zuwa, kin sha hanya." Murmushi tayi ba tare da ta furta komai ba illa tunanin yanayin Mutumin da take yi a ranta; da kuma yanda zasu kwashe. Yanda ya matse ta a jikinsa ne yasa ta ɗan ɗaga kai tana ƙoƙarin janye jikinta Hakan yasa ya sassauta mata riƙon tare da riƙe mata hannu gam ya wuce da ita saman kujera, sai da ya zauna sannan ya zaunar da ita a gefen shi yana washe baki cikin murna, "sannu da zuwa Baby; gaskiya ban taɓa tunanin kyawunki ya kai haka ba sai yanzu da na ganki a fili, kina da kyau Baby kin haɗu." Hannu yasa ya shafa fuskarta sai yace, "bari in Yi miki odan abun da za ki ci na san kin gaji, ki soma yin wanka before a kawo miki abinci, what do you want to eat?" Farr tayi da idanuwanta cike da salon burgewa, tana ɗan yatsina fuska tace, "Whatever is brought I will eat." "Ok to bari in kira waya." Yayi maganar yana tashi da sauri ya nufi wajen telephone, ɗaukowa yayi ya dawo ya zauna a inda ya tashi yana kiran wayan, babu jimawa suka ɗauka yayi odan abun da yake so su kawo mishi, daga nan ya ajiye wayan yana kallonta fuskarsa ɗauke da murmushi yace, "Are you going to take a shower now before you are brought in?" Bakinta ta tura gaba tana mishi wani irin kallo me shiga jiki, tare da gantsaro ƙirji cikin jan hankali tana zare gyalenta, a hankali ta miƙe tsaye tana cewa, "ina ne toilet ɗin?" Jikin sa na rawa ya miƙe yana cewa, "mu je in nuna miki." Yayi gaba ta bi bayan shi tana sake kallon ko ina har suka shiga cikin bedroom Nan idanuwanta suka faɗa kan damin kuɗaɗen da suke ajiye a saman gado a cikin wani ƙaramin jaka, an barbaza su da alamu ƙirga su yake yi, nan da nan zuciyarta tayi wani fari idanuwanta suka fito waje, haka take zazzare su a kan kuɗin cikin farin ciki a ranta, har wani lanɗe baki take yi ta shagala da kallon kuɗin sabida tsaban taga abun da ke faranta mata, masu kuɗin rana kenan, masu sanya Arab shiga shauƙi, a duniyar nan babu abun da ke faranta mata, babu abun da ke saka ta cikin tsantsan farin ciki da walwala irin kuɗi, tana son kuɗi fiye da komai, zata iya yin komai don su, su kaɗai ne soyayyarta, babu abinda take yiwa biyayya sama dasu Sai da Alhajin ya juyo yana kallonta don har ya kai bakin toilet ɗin ya buɗe mata ƙofa, sai ya juya ya ga bata biyo shi ba, nan ya hange ta tsaye idanuwanta na kallon wajen gadon shi, sai yace, "Baby taho mana, me kika tsaya yi?" Da sauri ta dawo cikin hayyacinta tana wayancewa ta ɗauke kanta tana kallonsa; sai ta saki wani malalacin murmushi wanda iyakan shi saman laɓɓanta, har wani sanja tafiya tayi wajen ƙarisowa wajen sa tana wani rangwaɗa kamar zata karye Lokaci ɗaya kuwa ta janye hankalinsa sai ɓashe baki yake yi, ya kama mata hannu suka shiga toilet ɗin ya haɗa mata komai na ruwan, sai kai mata cafka yake yi sabida ganin har ta cire kaya a gaban shi, ya kasa jurewa ya soma ƙoƙarin shige mata yana shafa ta But sai ta hana shi ta nuna masa, "yayi haƙuri tayi wanka yanzu zata fito, komai nata nashi ne sai yanda yayi da ita." Daƙyar ta turo shi waje ta rufe ƙofan. Nan fa hankalin ta ya dawo kan kuɗin da ta gani, lokaci ɗaya ta waro fararen idanunta waje tana washe baki, a fili ta furta, "Wayyo Allana! Kakata ta yanke saƙa, da alamu na zo gidan kuɗi, Wayyo daɗi." Ta ƙare maganar tana facal-facal da ruwa cikin farin ciki, sai kuma ta dakata tana sakin ƙayataccen murmushinta me kyau, yayinda ta saki huci tana cije leɓen ƙasan bakinta, a ranta kuma tana tunanin yanda za'a yi ta wanke mutumin son ranta, "Allah yasa mai sakin hannu ne, yo ko ba mai sakin hannu bane dole sai na wanke shi, meyasa ma bazan sace kuɗin ba kawai in gudu?" Ta furta tana wulla idanuwanta zuwa ƙofa, shiru tayi tana tunani, sai kuma ta tamke bakinta tana sakin killer smile da ita kaɗai ta san ma'anar sa, "Yes, haka zan yi". Still ta furta tana ɗaukar soso ta soma goga sabulu cikin farin ciki a fuskarta.    *Please share and follow me on Wattpad UmmuDahirah* [18/07, 10:07 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA GOMA SHA ƊAYA* _______________Wankan tayi ta fito ɗaure da towel da ta gani a rataye a toilet ɗin, sai dai tana fitowa idanuwanta suka faɗa kan gadon but babu Jakar kuɗin, tuni ya kwashe kayan shi ya adana, tsaki ta ja tsaban takaici, tana nan tsaye ta ji motsin shi zai shigo, sai tayi saurin nufan dressing mirror tana zama Yana shigowa ya hange ta zaune, sai ya taho wajen ta; baki a washe yana cewa, "Baby ga abincin an kawo miki." Murmushi tayi masa tana kallonsa da cewa, "ok bari in shirya sai in fito." "No Baby kinga yanda kika yi kyau a haka? Wlh na rikice ba na jin zan iya jira har wani lokaci, a hannu nake babyna ki gane mana." Sai ya sa hannu ya ɗago ta yana haɗa ta da jikinsa, tare da kai mata sumba cikin ƙwarewa yana sake cewa, "mu je a haka ki ci abincin a hannu nake Baby, zan fi jin daɗin ganin ki a haka." Murmushin yaƙe tayi tana kawar da kai sabida yanda taga yana lashe ta kamar maye, da alamu mayen ne wannan bazai ɗaga mata ƙafa ba, a ranta tace, "banza kawai, mutum ko fasali." But babu yanda ta iya haka ta bi shi a haka suka wuce Falo A saman cinyoyinsa ya ajiye ta; ya hana ta yin komai sai shi da kansa yake mata, abincin ma a baki ya bata sai shafa ta yake yi kamar zai cinye ta. Tun daga wajen wasan ya soma canzawa Ita kanta Arab sakin jiki tayi sosai ta jiyar dashi daɗi, ai kuwa ta sha ihu sosai, sai sambatu yake mata, tun tana jin daɗin abun har ta gaji tsaban ya ƙi ƙyale ta, ga shi yayi mata girma da yawa, sai can da dare ya tsala sannan ya haƙura da ita, daga nan barci ya ɗauke shi kamar kasa. Tsaki kawai ta ja ta miƙe ta shiga toilet tayi wanka don baza ta iya zama da najasa a haka ba, alwala tayi ta rama sallolin da ake bin ta sannan ta soma neman inda zata samu kuɗin shi, ta tabbata idan ta gani sai dai ya neme ta a daren ya rasa guduwa zata yi, but duk neman da tayi bata samu damar gani ba, da alamu ya rufe su a cikin drower ne kuma ya ɓoye keys ɗin. Duk ta duba bata samu ba dole ta koma ta kwanta Da asuba ya sake damun ta sai da suka ƙara yi, ta gane Mutumin shegen maye ne ba ya gajiya ko kwana zasu yi, duk da itama ɗin ƙwaruwa ce a harkan amma sam shi Mutumin ne bai yi mata ba, ga shegen girma da yake dashi da nauyi, shiyasa duk ya dame ta, amma haka nan ta haƙura take biye mishi suna shan Love; sabida ko a ranan sai da ya tura mata 100k a account. Sai murna take yi kamar zata haɗiye shi don daɗi Shi kuwa murmushi yayi yace, "ai wannan ma kaɗan ne Baby in har za ki kasance dani a duk sanda nake so, ban taɓa jin daɗin Mace kamar yanda nake jin ki ba Baby, gaskiya ke ta musamman ce, zan so mu kasance a ko yaushe domin zumar ki yana ruɗa Ni, ba ki da matsala da kuɗi Baby ko nawa ne zan kashe miki." Daɗi ne ya ratsa ta, sai ta sake shigewa jikinsa cike da kissa tace, "nagode Yallaɓoi, gaskiya naji daɗin samun ka nima Alhaji, Ni bani da damuwa idan har zaka sakar min kuɗi ko meye zan yi maka, bazan taɓa guje maka ba, ka saka a ranka Ni Arab taka ce sai yanda kayi dani ya Alhajjjj." Sai ta ja sunan kamar ta sha yaji tana kai harshenta saman bakinsa ta soma lashewa har zuwa saman hancin sa, inda tafukan hannun ta ke tallabe da fuskar tashi; tana mishi salo da zara-zaran ƙumbunan ta Ai kuwa kamar ta tsokano shi nan ya sake ƙanƙame ta yana laluba ta cike da tsantsan sha'awa. "Baby za ki kashe Ni don daɗi, ke ta musamman ce, ki faɗi duk abun da kike so ni kuma a shirye nake da in miki babyna." Sai da ta haɗe bakin su waje ɗaya ta tsotse shi son ranta before ta ɗago tana kallonsa, cikin farin ciki tace, "Allah ko Alhaji na?" "Eh mana faɗa min duk abun da kike so zan yi miki in bai fi ƙarfi na ba." Wal tayi da idanu cikin salon son burge shi tace, "Alhaji so nake yi ka siya min Mota sabida shi ne kaɗai burina yanzu." "Mota kaɗai?" Murmushi tayi masa tana kaɗa mishi kai tare da lumshe mishi idanu "Kin samu, baza ki koma gida ba sai da motan ki, zan sa a zaɓa miki mai kyau mai tsada, ko kuma zamu je ki zaɓa da kanki." Wani irin ihun murna ta saki tana ƙanƙame shi, ta hau mishi kissing ko ta ina, nan fa wasan ya sauya lokaci ɗaya ta soma shayar dashi madaran soyayyarta mai tsananin garɗi da tsayawa a rai A ranan wuni suka yi shayar da junan su daɗi ko nan da can basu fita ba. Dayake shima Alhaji babu inda zai je yau, haka suka wuni yin abu guda ɗaya Tabbas ya tabbatar Arab ƴar duniya ce kuma gogaggiya ce a wannan fannin, har manta kansa yake yi tsaban shauƙin da yake shiga, yana mamakin ƙaramar yarinya kamar wannan ta san kan harka, yanda zata tafiyar da Mutum cikin salon ta mai tsayawa a rai. Sun sha soyayya a ranan ko rabuwa na minti ɗaya ba sa iya yi sai idan abinci zasu ci Washe gari ma haka suka ɗaura suna manne da juna, sai da yamma ne ma ya fita sabida akwai inda zai je, but kamar ya shekara sabida yanda Arab ta tsaya mishi a rai, ta san kan lagwon namiji wanda idan har ta kama mutum to zai yi wuya ya manta ta, daɗin ta ya wuce misali ta san yanda zata iya tafiyar da namiji, irin su Arab ne idan aka same su a yawon duniya to Matansu ta banu, domin babu wani namijin da zai iya rabuwa da su sai idan an haɗa da addu'o'i. Lokaci ɗaya ta rikita tsohon nan, haka yake ta zuba mata kuɗaɗe a account, kuma yace, "ta shirya su je ta zaɓi motan." Ai kuwa suka fita tare ta darzo na miliyan shida sabuwa fill Kasancewar tace mishi, "bata iya mota ba." Sai yace mata, "zai koya mata idan har zata zauna dashi." Sai dai kuma bazai yiwu ba, dole tace mishi, "tana buƙatar komawa gida ko don jarabawan ta da zata yi wannan Mondayn." Yace, "bata da matsala yana da hanyar da zai sa ayi mata, idan ma tana son kwalin S.S.C.E ɗin ne zai sama mata." Murmushi kawai tayi tace, "no ya bar shi kawai, but zata zauna sai tayi mishi ko two weeks ne." Bai so hakan ba amma yanda ta nuna mishi, "suna tare a ko yaushe." shiyasa ya haƙura zai barta ta koma nan da two weeks A gida kuwa ko ɗarr Inna bata ji ba da Arab ta kira ta ta sanar mata, "Sai bayan sati biyu zata dawo." Bare yanda ta tura musu kuɗi gaba ɗayansu sun ruɗe sai murna suke yi Baba ne kawai yake ta faɗa daga ƙarshe haka nan yayi shiru tunda babu yanda zai yi, baza a ji maganar sa ba, sai dai shiriya da yake nema musu, amma abun yana damunsa matuƙa a rai babu yanda ya iya ne, Inna ta gama mallake shi bazai taɓa iya magana ba Arab kuwa na can Abuja an tare a wajen Alhaji, kullum da soyayyar da suke yi, ga shi har an fara koya mata motan kuma tana ganewa a hankali. Kullum da dare sai sun fita da Alhajin yawon shaƙatawa, a can ma sai da ta sake yin wani saurayin. Ana gobe zata tafi suka shiga super market da Alhajin ya dinga kashe mata kuɗi kamar hauka, kaf ƴan gidan su sai da tayi musu siyayya Alhajin ya soma fita sabida kiran shi da aka yi a waya ya fita amsawa Itama kuma tana tsaye wurin da ake ƙirga musu kaya, wayanta a hannu tana latsawa, long sleeve da jeans ne sanye a jikinta, sai flat Thoms a ƙafafuwanta, gashinta cikin ponytail. Maganar da mai ƙirga mata kayan yayi ne yasa ta ɗago kanta tana kallonsa, sai tace, "har ka gama?" "Yes Madam." "Ok." Ta miƙa masa ATM card ɗin Alhajin tace, "cire a ciki." Yana ƙoƙarin amsa ne sai ya faɗi ƙasa, shiyasa ta duƙa don ɗauka. Dai-dai kan wasu fararen ƙafafu da suke cikin Black flat shoes suka sauka, inda shi kuma ya take ba tare da sanin sa ba sabida already ya ɗaga ƙafan sa ɗaya zai ajiye; ATM ɗin ya shige ya taka, ƙafafuwan ta bi da kallo sabida tsananin kyawun da suka yi mata, har ta so shagaltuwa a kai tare da tunanin ya mamallakin ƙafafun zai kasance? gaskiya Allah yayi halitta. Ɗagowa tayi da zummar tayi mishi magana ya ɗaga mata domin da alamu bai san ya taka ba ma. Sai karaf idanuwanta suka haɗe dana Doctor Aliyu, kallon kallo suka yiwa juna sabida dukkan su sun gane fuskokin juna, da sauri ta janye idanuwanta saboda irin kallon da yake sakar mata, sam ba ta ƙaunar haɗa ido dashi musamman yanda idanuwan nasa suka kasance wani iri ga su kalan Brown, sai ta ɗan yatsina fuska tana ci je baki da cewa, "excuse me! ka ɗaga ƙafarka zan ɗauki ATM." Bai ce komai ba ya matsar da ƙafar yana bin ƙasan da kallo Ita kuma tuni ta sake duƙawa ta ɗauka ta ba wa mutumin. Sai ta kawar da kai bata sake kallon inda Aliyu yake ba Shi kuwa yana tsaye shima riƙe da kwandon da yayi siyayya a ciki. Fuskarsa babu walwala shima bai sake bi ta kanta ba, sai dai a ranshi mamakin ganinta a nan ɗin yake yi, but mamakin sa ya ƙare a sanda Alhaji Bashir ya zo wajen ta yana kiran ta da Baby yana tambayar ta, "ta gama ne su tafi?" Yana jin amsar da take ba shi, sai ya taɓe baki a ransa yace, "No wonder, ai ba abun mamaki bane don naga Karuwa a nan." Sai ya ja dogon tsaki yana ɗaura kwandon kayan shi ganin sun matsa daga inda suke Arab tana jinsa, har sai da ta juyo ta dube shi, hakan yasa suka haɗa idanu ya balla mata harara fuskarsa babu ko ɗigon fara'a, kasa ramawa tayi don abun ma mamaki ya bata, "lallai wannan mutumin." Ta furta a laɓɓanta ba tare da ta san zai fito fili ba Alhaji Bashir da ya ji kamar tayi magana, sai yace, "Baby are you talking to me?" "No ba da kai nake yi ba." Ta furta tana sakar mishi murmushi Cewa yayi, "su tafi." Sannan ta bi bayan shi suka fice ma'aikata na kwashe musu kayan Aliyu kuwa da harara ya raka su yana sake haɗe rai, ji yake yi ya sake tsanar yarinyar a ransa, ga ta dai ƴar ƙarama amma ta ɓata rayuwar ta, har mamaki yake yi wasu irin iyaye ne dasu da har suka bar ƙaramar yarinyar nan tana yawon karuwanci? Anya kuwa Nafi'u ya san ƴar gidan wa ya aura? Da alamu har ƴan uwan nata duk halin su ɗaya don basu yi kama da mutanen ƙwarai ba, tsaki kawai ya kuma ja cike da takaici a ransa, shi dai har ga Allah bazai iya auren ƴar gidan karuwai ba, Nafi'u ba shi da wata hujjar da zai iya auren Firdausi koda ita ba karuwa bace, but ai gidan su ɓata-gari ne, kuma kowa zai riƙa mata irin wannan kallon, yana ga kawai kyawu ne ya ribace shi har ya aure ta... Kayan sa ya ɗauka ya fice bayan ya biya kuɗin, yana fita kuwa ya hange su a cikin mota sai dariya suke yi, a gaban shi motan ta wuce Arab bata ma ganshi ba, the more yana kallon fuskarta the more yana sake jin tsanarta na sake shigan sa. Motan sa shima ya shiga ya ja ya tafi, yana kallon nasu motan a gaban shi a haka har suka yi nisa, sai ya ga sun shiga wani Hotel yayinda shi kuma yayi gaba abun sa, zuciyarsa abubuwa da dama take raya mishi a kan Arab, yayinda yake sake turr da ita a ranshi; tare da jin ƙyamar rayuwarta da halayyarta.                      Ita kuwa Arab sam ba ya gabanta, tunda suka fito ta manta da shafin sa, ta mayar da hankalinta a kan Alhajin ta sai nishaɗi suke yi. Suna tare a ranan har dare kamar chewing gum sabida ban kwana da suke yi zata tafi, shiyasa yake fanshe duk wasu kwanaki wai da zata yi ba tare da shi ba Ita kuwa sai dariya take mishi saboda yanda ya susuce a kanta ya ƙi haƙura, tace, "Alhaji kar ka damu in dai Ni ce sai ka gaji da kasancewa da Ni." "Ai ba haka bane Baby, Ni sam ba na so ki tafi ne, but idan kin yarda duk inda zan je zan riƙa tafiya da ke, zan sakar miki kuɗi har sai kin ce kin gaji, fatana dai ki kasance da Ni a duk inda zan je, zamu riƙa tafiya tare." "Oh! Alhaji kar ka manta fa Ni ina gaban iyayena ne, bazai yiwu mu riƙa kasancewa koda yaushe ba, nima bazan so hakan ba domin ba na son ka gundura da Ni, but zan riƙa ƙoƙarin zuwa a duk sanda ka buƙace ni amma ba ko ina ba, ka san ba zaman kaina nake yi ba, bambanci na da Karuwan titi kenan." "I know there is no problem that's why I said that baby, but shikenan tunda kin ce haka, amma idan zan riƙa yin nisa zamu tafi da ke don na fi son kasancewa da ke a kan kowacce Mace, wlh Baby bazan taɓa gajiya da ke ba don ke ta musamman ce, ko ba'a taɓa faɗa miki haka bane?" Ya ƙare maganar yana jan mata jelan kitson kanta da ke jiƙe sharkaf sakamakon wankan da tayi Ita kuma sai ta sake kwantar da kan nata a faffaɗan ƙirjinsa tana cewa, "na san da haka Alhaji, kaima na musamman ne a gare Ni don ban taɓa samun abin da na samu a wurinka ba a wajen wani." "Baby ai nace miki ba ki da matsalar kuɗi, zan kashe miki ko nawa ne kuma ko me kike so zan ba ki." Murmushi tayi na farin ciki, nan ta sanja salon hiran nasu. A haka suka kasance a ranan cikin nunawa juna soyayya   Zuwa washe gari kuma ya sa aka tafi mata da motan, an zuba kayan tsaraban da yayi mata a ciki, kasancewar bata iya motan ba har yanzu shiyasa yasa aka kai mata. Tana cikin motan Driver a gaba, a haka suka isa Zaria Arab na farin ciki sabida farar tafiyan da ta yo, ta samu kuɗi wajen Alhajin gaskiya ba kaɗan ba, ko yanzu da zasu taho 200k ya tura mata. [20/07, 8:39 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍    *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA GOMA SHA BIYU* _______________ *ZARIA CITY*                Lokacin da Arab ta koma da motanta; duk sun ruɗe sabida ganin motan Inna kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha don daɗi, bakin ta ma ya ƙi rufuwa faɗi take yi, "Wayyo daɗi Wayyo! Daɗin haihuwa kenan, yanzu idan ban haihu ba taya zan samu wannan arzikin? Allah na gode maka da ka bani Yara waɗanda zasu share min hawaye, farin ciki sai gudana yake yi a gidana, waɗansu kuwa hassada da ƙyashi yayi musu yawa sai dai su mutu wlh, ƴaƴana sun yi gaba nan gani nan bari mahassada sai dai su haɗiye zuciya su mutu, Allah ya yiwa ƴaƴana goshin arziƙi, wannan kaya haka? Nan gaba sai zuwa Makka a duk sati-sati, Allah na gode maka." Sai ta ɗaga hannayenta cikin farin ciki tana nuna godiyar ta ga Allah Yayinda Ummu da Zahra sai ɗaga kayayyakin da Arab ɗin ta yo musu tsaraba suke yi, suna murna su ma sabida ganin kayan masu shegen tsada, haƙiƙa ƴar uwansu ta kankaro musu girma. Sai tambayarta suke yi, "wannan wanne irin Mutum ne haka? Wanne irin kuɗi yake dashi? Sannan me suka yi a can da ina da ina suka je?" Ai nan Arab ta zauna tana ta ba su labari, abubuwan da suka yi da duk yawon da suka yi da Alhaji, sai dai bata sanar musu da haƙiƙanin zaman da suka yi a Hotel ba, kawai tace musu, "bikin Abokinsa ake yi." Duk da ƴan uwanta sun san cewa dole tana ba shi kanta ne don ita kaɗai ce a cikin su suka san tana wannan ɗabi'ar, su kawai iyakan irin soyayyar nan na shan minti ne ba sa wuce haka, daga nan sai su samu kuɗi abun su, but yanzu ne Zahra ta shiga sahun ta, don itama tana mutuwar son saurayin nata ne, ɗan gidan sarauta ne kuma shi take da burin aure, yayi mata alƙawarin aure but sai ta ba shi kanta, shiyasa ta ba shi kanta, sai dai tunda suka aikata wannan al'amarin ya bar ƙasar bai sake dawowa ba, kusan wata biyu kenan a na uku, suna waya har yanzu suna soyayyar su sai dai ba ya ƙasar ne yana can yana karatu, yayi mata alƙawarin duk sanda ya dawo zasu yi aure; don shima yana sonta sosai Ita kanta Inna itama duk a ganinta tsaban farin jinin yaranta da yanda ta koyar da su cin kuɗin samari shi ne yake tasiri, da kuma yanda take nema musu magani na farin jini saurayi ya sakar musu kuɗi, bata san cewa yanzu duniyar bani gishiri in ba ka manja bane, shiyasa duk abun da zasu yi baza ta hana su ba tunda ta san cewa basu taɓa aikata wani kuskure ba, suna yin komai ne don su wanki garori.          Baba koda ya dawo ya tarar da mota a waje bai ce musu komai ba, harkan gaban sa kawai yake yi domin tunda ya ga yanda suke duba kaya cike a tsakar gida ya san cewa Arab ne ta taho dashi, kuma motan ma ya san cewa nata ne tunda yana jin Inna tana magana. Shiru kawai yayi ya zubawa sarautar Allah ido; tunda ya ga abun yayi gaba sai dai idan Allah ya so ya shirye su, kuma zai ci gaba da musu addu'a tunda shi kaɗai ne abun da zai iya, Allah yasa su gane gaskiya idan masu shiryuwa ne fatan sa kenan a koda yaushe.       Arab kiran Ibrahim tayi tace, "ya zo ya ga mota." Ai kuwa babu jimawa sai ga shi, tare suka fita a motan yana tuƙa su, sosai ya taya ta murna sai koɗa ta yake yi yana cewa, "yanzu ne ta faso gari ta zama babbar yarinya, duk inda suka je yanzu ne za'a kalle ta da ƙima da mutunci." Dariya tayi tace, "shiyasa nake sonka Bestyna sabida yanda kake sanya Ni farin ciki, kaima kason ka na nan zan tura maka ta account; sabida ba don kai ba bazan samu wannan kuɗin ba, Ni kaina na san Yanzu ne nake ji nakai na cika Mace babbar yarinya." Ta ƙare maganar tana buɗe hannayen ta cikin farin ciki Dariya kawai yake mata ganin yanda ta koma tana rawa a zaunen. Sai ya soma rera mata waƙa suna dariya dukkan su Cikin farin ciki haka suka kasance a wannan lokacin, duk da dare yayi but sun ƙi komawa gida, ƙarshe wani restaurant suka je suka ci abinci suka siya ice cream da shawarma. Bayan sun gama ci sannan suka nufo gida A hanya ne Arab take ce mishi, "zai soma koya mata motan zuwa gobe." Yace, "bata da matsala ai, yana da time duk sanda take so zai koya mata." "Da yamma zai fi tunda Ni yanzu na dena tuyan awara, na zama big girl daga yau, zan sanar da Inna ma." Ihu yayi yana buga sitiyarin motan da cewa, "hihu! Babban yarinya Matar manya, kin fi ƙarfin Yaro sai dai baban Yaro! Gaskiya dama lokaci yayi da Yakamata ace kin dena fita talla, yanzu kina da sana'ar da ya fi wannan Babe, don haka ki share batun talla kawai, kwanan nan zamu riƙa out garuruwa za ki ga irin manyan mutanen da za ki samo wlh." Waro manyan idanuwanta tayi fuskarta da murmushi tace, "da gaske kake yi Besty?" "Wlh kuwa. Ai zaman ki a waje ɗaya ne shiyasa har yanzu ba ki san matsayin ki ba Baby, irinku ba sa zama a waje ɗaya, don wlh kwanan nan burin ki zai cika, kin san irin Alhazawan nan da kike buƙata celebraties irin su za ki samu, Ni na san irin wuraren da ake iya ganin su; don haka idan muka samu time zamu riƙa fita muna zuwa buɗe ido kawai, a can za ki yi kamu wanda suka fi Alhaji Bashir, zaki ce na faɗa miki, bare ke kyakykyawa babu namijin da zai ganki bai susuce a kanki ba, ke ta musamman ce Arab a kullum ina faɗa miki, kuma na san ba Ni kaɗai nake sanar miki da hakan ba, kin bambanta da sauran Mata, kina da bambanci da su sosai, abun da nake so kawai in sanar miki ki sake dagewa, ki gyara kanki da duk inda kike so ki shiga za ki shiga, wlh a lokaci ɗaya ke kanki sai kin zama celebraty ba wai ki zauna sai kin yi hurɗa da celebraties ba, za ki zama mai kuɗi the Yong lady. Babbar mai kuɗi." Bakinta ta washe zuciyarta cike da farin cikin jin zancen shi, tace, "Wow! Baka ji yanda nake ji a raina bane da ka furta wadannan kalaman, Allah ya tabbatar da zancen ka Besty, Ni na san kai me so na ne kuma bani da tamkar ka, ka taka rawa a rayuwata domin haɗuwa ta da kai alkhairi ne, shiyasa nake matuƙar ƙaunarka, kai nawa ne nima taka ce, ko aure nayi muna tare bazan rabu da kai ba." "Na fi kowa sanin haka Besty, na san kina ƙaunata haka nima nake ƙaunar ki, Allah ya barmu tare." Dariya suka yi har suna kashewa "Ka san wani abu, Mutumin nan fa ya dame Ni, ban taɓa ganin me naci irin shi ba, ya takura min wlh." Ta ƙare maganar tana yatsina fuska "Wanne Mutumi kenan?" Ya tambaye ta don bai fahimci wane ne ba "Tariq. Ka san ya takura min matuƙa, sabida shi na kashe wayana ina Abuja wlh ya takura min, yanzu kuma kaga shi yake kira, da ya san na dawo garin maybe da tuni ka ganshi, but zan ɗauki mummunan mataki a kanshi tunda na nuna mishi ba na so but bazai ƙyale Ni ba." Dariya yayi Ibrahim yace, "but a kan me za ki ɗauki mataki bayan na san hakan kika fi so? Kar ki manta fa shima daga ganin shi akwai maiƙo a wajen shi, kawai ki ajiye ajin nan naki ki ba da kai bori ya hau don na san kawai wahalar dashi kike yi har yanzu." "Baza ka gane bane Besty, na kula shi ba hakan yake so daga gare Ni ba, shi aure na yake so yayi." Sai kuma tayi dariya tare da cewa, "abun da bazai taɓa yiwuwa bane ai, Ni in Yi aure yanzu ai maganar ma bata taso ba, but duk bayanin da nayi mishi ya ƙi fahimta." Ibrahim yace, "ba ki fahimtar dashi bane shiyasa bai gane ba, ki sake gwada wa but Ni dai kar ki bar shi sabida nayi miki bincike a kanshi yana da kuɗi gaskiya, za ki more." Bakinta ta taɓe kawai tana mayar da hankalinta a kan wayanta ganin ana kira, sai dai bata ɗauka ba suka ci gaba da hiran su da Ibrahim har suka kai gida. Sai da suka yi sallama tukunna ta shiga gida da key ɗin motan ta, sai kuma tsaraban abubuwan da suka ci da ta kawo ma su Inna.          Washe gari sai ga Tariq a ƙofar gidan su Tayi mamakin ganin sa tunda bata sanar mishi ta dawo ba, hasali ma bata ɗauki wayan sa ba tun jiya. Ta fito kenan Inna ta aike ta nan maƙota taga motan shi. Tana sanye da shuɗiyar atamfa da kalan fari da ja a jikinta, ɗinkin riga da skirt ne sai dai an ci ma kayan mutunci matuƙa, duk shatin halittar da Allah yayi mata ya bayyana, kanta babu ɗankwali sai farin gyale siriri da ta yafa a kai, ƙafanta kuma flat shoes ne baƙi mai siraran igiya, face ɗinta babu makeup but ta sha jan janbaki sai glowing yake Yi bakin nata, tana yi tana taunan chewing gum irin na gogaggun ƴan duniyar nan Tunda ya hange ta ya fito daga motan ya nufo ta Tana ganin shi ta ɓata fuska, sai dai ta tsaya bata tafi ba illa kallonsa da take yi Haka shima kallonta yake yi har ya iso wajen, fuskarsa da yalwan murmushi yace, "ranki ya daɗe! Ashe kin dawo shine ba ki sanar min ba? Laifin me nayi miki da kika kasa ɗaukar wayana?" Yatsina fuska tayi kamar yanda ya zame mata jiki, cike da yanga irin nata tace, "ina da uzuri ne, yanzu me ya kawo ka gidan mu bayan ban ce ka zo ba? Ka san irin hakan ne na tsana ban buƙaci mutum ba ya tako inda nake." Idanu kawai ya zuba mata kamar zai cinye ta sabida yanda take sarrafa bakin nata yana tafiya da imanin shi, cikin rashin kuzari kamar zai yi kuka yace, "don Allah kiyi haƙuri tunda na san nayi laifi, but rashin ɗaukar wayana da ba ki yi bane, sannan kuma naji labarin kin dawo ba ki neme ni ba kamar yanda muka yi alƙawari, hankali na ya tashi a tunani na nayi miki laifi ne." "Babu laifin da kayi min, but yanzu dai ina da abun yi zan tafi sabida sauri nake yi." Da sauri ya sha gabanta ganin har ta wuce shi, "haba Princess haka za ki tafi ba ki ce min komai ba? Na san ke mai cika alƙawari ne kuma kin yi min alƙawari zamu yi magana idan kika dawo, but ga shi yanzu kin ƙi kula Ni." Kallonsa tayi tace, "shikenan. Ka bani address ɗin inda zamu haɗu zan zo." Washe baki yayi yace, "da gaske kike yi?" Kanta ta jinjina mishi bata ce komai ba illa kallonsa da take yi "Ok. Ina da guess house sai mu haɗu a can, hakan zai fi mana sirri ko?" Murmushi tayi masa tace, "why not, idan yayi maka ai shikenan." "Yayi min, a nan tudun Wada ne layin ƴan nono, but baza ki gane gidan ba zan zo sai in ɗauke ki mu tafi, yaushe ne?" Shiru ta ɗan yi, sai kuma tayi fari da idanuwanta cikin salo irin nata tace, "ok. Zuwa ƙarfe biyu sai ka zo, Ni na tafi bye." Da haka ta wuce bata jira cewarsa ba Shima yana mata ba-bye har ta ƙule masa, sannan ne ya shiga motansa ya ja ya tafi cikin farin ciki, ya san zai kasance da ita yau kenan, but da sannu zai mallake ta wata rana, amma ai yanzu aka soma zai ci gaba da bin duk hanyoyin da zai ja hankalinta ta ƙaunace shi har suyi aure, wannan shi ne burin shi don ya fi so gaba ɗayanta ya mallake ta ne sai yanda yayi da ita babu shamaki a taren su.               Zuwa ƙarfe biyu kuwa sai ga shi ya zo, yana yin parking ya kira ta a waya ya sanar mata Kamar shuɗewar mintuna goma sha biyar sai ga ta ta fito, sanye da riga da wando ƙananu, kayan sun matse ta matuƙa ko ina na jikinta ya bayyana sai rawa yake yi, fuskar nan nata tasha makeup da yayi mata kyau ainun, ta yafa ƙaramin gyale iyakan wuyanta, sai tayi using da hill shoes, tana taunan chewing gum kamar yanda ya zame mata ɗabi'a. Kai tsaye wajen motan ta nufa ta shige ya ja suka tafi Sai da ya ɗan soma tafiya before ya kalle ta fuskarsa da annuri yace, "kin yi kyau Gimbiyyata, gaskiya ke kyakykyawa ce." Murmushi tayi masa kafin ta fasa ƙwai tace, "na san da haka." Dariya kawai yayi, sai ya mayar da idanuwansa a kan titi, can kuma ya sake kallonta yana murmusawa, ji yake yi kamar ya haɗiye ta don daɗi, ya kasa ɗauke idanun a kanta minti bayan minti sai ya juyo ya kalle ta Ita kuma sai ta sakar mishi wani narkakken kallo mai tafiya da duk wani kuzarin mutum, ta tura baki gaba tana tsotsewa cikin salo na burgewa, a hankali cikin wani irin yanayi tace, "wai lafiya kake min wannan kallon? Halan na sanja maka ne?" Murmushi yayi yace, "no Gimbiyya, ai ke ce dole ne mutum ya kasa natsuwa idan kina gefen shi, ke ta musamman ce Arab, kina da kyawun da ba kowa zai iya samun natsuwa ba idan har yana kallon fuskarki, dole ne ya zauce a ƙaunar ki, idan har ba kin zama tawa bace hankalina bazai taɓa kwanciya ba, ina sonki matuƙa!" Idanuwanta kawai ta ɗauke a kanshi tana murmusawa Sai yace, "bari mu tsaya a nan mu siya wani abu, sai mu wuce dashi." Bata ce mishi komai ba, tunda ta ɗago ta kalli wajen ta mayar da idanuwanta a kan wayanta Yayinda shi kuma yayi packing ya fita ya je ya siyo musu ya dawo. Kai tsaye suka wuce gidan. Bayan yayi horn aka buɗe mishi tunda gidan shi ne a nan yake kwana. Ƙaramin gida ne amma mai kyau don ya haɗu kuma an kashe mishi kuɗi Tunda suka shiga Arab take bin ko ina da kallo tana ayyana yanayin tsadan komai. Da alamu gidan ya burge ta shiyasa sai zuba murmushi take yi Suna shiga falon ya bata masauki a kan kujera sai ya wuce kichen, babu jimawa ya dawo da Plates da cokali tare da cups, ya buɗe ledan ya sake musu gashashshen kazan da aka yayyanka, ya zuba mata yoghurt a cup sannan ya miƙa mata yana murmushi tare da cewa, "ga shi my princess, ki fara korawa da wannan." Hannu tasa ta amsa cikin yanga tana mishi murmushi, sai da ta kurɓa kaɗan sannan ta ajiye "Yauwa to, Bismillah, ga nama ga abinci duk wanda kike son ci." Yatsina fuska tayi tana ɗan kwantar da kanta a jikin kujeran, sai tace, "ba na jin yunwa gaskiya." "Haba Baby ko kaɗan ne ki ɗan taɓa tunda na siyo don ke ne." Manyan idanuwanta ta zuba mishi tana sakar mishi wani kallo mai shiga jiki, cikin yanayin shagwaɓa tace, "idan kana so in CI sai dai ka bani a baki." Da sauri ya miƙe daga inda yake yana dawowa kujeran ta, cike da farin ciki yace, "an gama ranki ya daɗe! Ai Ni ko yaushe biyayya nake yi a gare ki, zan fi kowa farin ciki ace Ni ne na ciyar da ke, don haka ba ki da damuwa." Sai ya soma ƙoƙarin ɗaura ta a jikin sa ya ɗago ta ya ajiye ta a cinyoyinsa, tare da sanya hannu ya zare mata gyalen wuyanta Ita kuma tuni ta kanannaye shi cikin salon ta na duniyanci, lokaci ɗaya ta soma zauta shi, maimakon ya bata abincin sai dai ya kasa saboda jin albarkatun jikinta a nashi, ga wani irin salo da take mishi duk ta narke a jikin sa Nan ya soma fita hayyacin sa ya soma ƙoƙarin wasa da ita yana shirin haɗe bakunan su But sai ta dakatar dashi wajen kara mishi zaro-zaron ƙumban ta da ya sha jan lalli a saman bakin sa, a hankali ta soma goga mishi yatsarta tana kallon shi ido cikin ido, fuskarta ɗauke da murmushi mai zautar da duk wanda ya gani, sai da ta cije leɓen ƙasan bakinta ta tsotsa kaɗan before ta buɗe baki a hankali bayan ta matso da fuskarta kusa da nashi ta haɗe waje ɗaya tana goga mishi, cikin raɗa da kuma shagwaɓa tace, "Ni fa yunwa nake ji, ka fara bani abincin." Uhmmn kawai yace don ya kasa yin magana sabida yanda yake jin shi, tamkar ya afka mata ya soma tsotson bakin nan nata da ya fi komai jan hankalin shi a tare da ita, but babu yanda ya iya haka ya soma bata abincin tana ci, sai dai tana yi tana cizon yatsan shi tana mishi wani salon da ke ƙara zauta shi yana ƙara mishi tsantsan sha'awar ta. Duk da haka bai ƙyale ta ba yana yi yana tattaɓa ta a haka har suka gama. Tun a nan wasan ya canza salo domin tuni ya murƙushe ta sun soma aikawa junan su da zafafan saƙonni, ba shi ba ba ita ba don da gani gaba ɗayan su gogaggu ne a wannan fagen, tuni sun zubar da kayan jikin su sun koma haihuwar uwar su. Daga ƙarshe ɗaukar ta yayi cak suka yi cikin bedroom ɗinsa ganin wajen bazai mishi ba, a kan makeken gadon sa ya dire ta suka hau romance ɗin junan su cikin ƙwarewa tamkar zasu cinye juna Yanayin yanda Tariq yake tafiyar da ita ba ƙaramin firgita mata lissafi yayi ba, ta kula shi ƙwaro ne a wannan fagen shiyasa itama ta dage sosai wajen nuna mishi nata ainihin ƙwarewan, lokaci ɗaya suka susuce suka manta a duniyar da suke sabida jiyar da junan su daɗi da suke yi A hankali kuma komai ya soma gudana ya soma ƙoƙarin kusantan ta Sai dai kuma lokaci ɗaya ta dakatar dashi tana jan jikinta gefe ɗaya Da sauri ya kamo ta yasa mata karfi ya danne ta yana aika mata da zafafan saƙonnin da dole zai fitar da ita a hayyacinta domin ta ba shi haɗin kai nan take, ko saurara mata ba ya yi haka yake aika mata da saƙonni kala-kala, sai da ya ga tayi tuɓus bata da sauran ƙarfin da zata iya hana shi, bare yanda yaga tana ihun daɗi kamar zata zauce, sai yayi saurin ƙoƙarin zura ƙwallo a raga sabida ya ƙosa ya ji irin daɗin da take dashi. [21/07, 9:26 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍    *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA GOMA SHA UKU* _______________Matse ƙafafuwanta tayi ta hana shi shiga, duk yanda ya so ya kusance ta abun ya gagara, cikin fitan hayyaci kamar zai yi mata kuka ya hau roƙon ta Amma sai ta nuna, "sam bazai kusance ta ba, ita gida zata tafi ma." Nan ta sauko a gadon tana ƙoƙarin ficewa Sai yayi saurin riƙe ta ya duƙa har ƙasa yana roƙon ta, "please be patient Princess, wlh whatever you want I can give you, haba sai da kika kawo Ni wannan limit ɗin kuma za ki tafi ki bar Ni? Za ki iya kashe Ni wlh, Please Princess help me." Taɓe baki tayi ta juya zata fice Sai ya miƙe da sauri ya kamo ta suna komawa kan gadon, hawa kanta ya soma yi amma sai ta dakatar dashi "Idan kayi yunƙurin yi min da ƙarfi zan ɗauki mummunan mataki a kanka." Tafaɗa ranta a ɓace Hakan da ya gani ne ya dakata, but har da hawayen shi a wannan lokacin yake cewa, "shikenan bazan miki da ƙarfi ba Princess, but please don't go and leave Me in this condition, ke kaɗai ce za ki iya gamsar dani a wannan lokacin saboda ke ce wacce nake kwaɗayi, ki faɗa abun da kike so Ni zan iya ba ki ko mene ne idan har za ki bani kanki, na jima ina kwaɗayin ki babe kar kiyi min haka bazan iya haƙura da ke ba. Please." Sai ya kwantar da jikin sa saman nata yana ƙoƙarin haɗe bakin su, duk ya gama fita hayyacin sa burin sa kawai ya ji shi a cikin duniyar daɗin ta Yanda yake manne mata ne yana taɓa ta sai ta miƙe zata sauka a kan gadon Ya sake kamo ta ta faɗa jikinsa ya ƙanƙame ta yana roƙon ta, sai kuma da sauri yace, "Give me your account and I will send you money." Jin hakan sai ta saki murmushi tana cije leɓe, tashi tayi zaune tana shirin gyarawa A tunaninsa tafiya zata yi, sai ya riƙe ta yana marairaice mata fuska kar ta tafi Murmushi tayi masa tace, "ba tafiya zan yi ba." "Ok to karanto min Numban sai in sa miki kuɗin." Yafaɗa jikinsa na rawa, ya ɗauki wayansa da ke saman drown gadon ya soma kofe numbern kamar yanda ta karanto mishi, a take ya tura mata 50k Ganin kuɗin ne yasa ta zuba murmushi sai ta kalle shi tace, "kana so mu fara mu tsaya ne ko? Wannan kuɗin kana ganin shi ne farashi na?" "No Baby, ai da kin faɗa min tun farko da bamu kai ga haka ba, ba ki yarda dani bane ko kina ganin bazan biya ki bane da kika yi min haka?" Baki ta taɓe tace, "a'a, ba na son dogon zance Ni zan tafi." He quickly said, "ok be patient, how much do you want me to give you?" Fari tayi da idanu da cewa, "ba na faɗa sai dai ka yanke da kanka, but iya kuɗinka iya shagalin ka." Take a nan ya sake tura mata 100k Tana ganin kuɗin tayi murmushi, sai ta kalle shi tace, "ranka ya daɗe! Da alamu kana hannu da yawa fa, babu damuwa mu ci gaba." Sai ta ajiye wayan nata Shima ajiye nasa yayi ya janyo ta jikinsa. Nan suka ci gaba da baɗalan su tsawon lokaci suna tare.               Sai gab da magriba sannan Tariq ya dawo da ita gida. Yana yin packing ya kalle ta yace, "kin wahalar da Ni Baby, ban yi tunanin samun ki zai yi min wahala ba, gaskiya ke ta musamman ce, nayi farin ciki da kasancewa da ke wlh, da ace na san haka kike tun farko da ban yi sanya da shiga gogin daɗin ki ba, ji nake yi tamkar mu koma mu ƙara." Ya ƙare maganar yana kai hannu saman cinyoyinta yana shafawa A tare suka saki wani numfashi mai ƙarfi, kowannen su yana jin wani irin sha'awa tare da shauƙi yana taso musu Ta kasa yin magana sabida irin salon da yake mata, sai ta lumshe idanu kawai tana sauraron shi Hakan da ya gani ne da alamu saƙon shi yana ratsa ta, sai kawai ya dawo kusa da ita tare da ƙara tusa hannun nasa ɗaya a can tsakanin cinyanta yana shafa mata ko ina, inda ɗayan kuma ya zura a riganta cikin salo yake raɗa mata, "Baby mu koma ki kwana min." Idanuwanta ta buɗe da suke ƙoƙarin sauya kala, sai ta ja numfashi tana cije leɓe a hankali, idanu suka ƙurawa junansu still yana mata yawo da hannayen sa a jikinta, ganin ya kawo baki zai haɗe bakunan su, sai bata hana shi ba ta buɗe bakinta suka soma tsotson juna, lokaci ɗaya suka rikice a cikin motan suna ta jiyar da junan su daɗi Sun jima a wannan yanayin tamkar baza su rabu ba, kuma ita ta ƙi yarda su koma duk da kuwa tsananin sha'awar da ya sake tayar mata, gaskiya ta kula Tariq na musamman ne, yana da bambanci da sauran Mazan da take mu'amala da su, ya san kan yanda zai tafiyar da ita ta ji daɗi, bata taɓa jin makamancin daɗin da taji a hannun sa ba yau, shiyasa duk jikinta yayi sanyi yanzu ta kasa hana shi ta biye mishi Tariq yana bin mata shima, sai dai ba kowa ba, ya jima yana wannan ɗabi'ar dalilin da yasa har yanzu bai yi aure ba, shekarun sa yanzu baza su gaza 33 ba, bare yanda yake da jini a jika saurayi mai tashe dole ne zai san kan harkan nan kuma ya san ta yanda zai tafiyar da ita, kuma ya ci nasara don bata yi zaton haka yake ba, ga shi duk da ya gamsar da ita sosai amma kuma sha'awar shi ya ƙi barin ta. Sai da tayi da gaske sannan ta sallame shi ta koma gida. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️        Fannin Malik kuwa tunda suka bar Zaria yake cikin baƙin cikin abun da Nawwara tayi mishi, shiyasa sam ya dena yin mata magana Tun tana ganin abun da wasa ne a tunaninta zata rarrashe sa but abun ya faskara, har suka gama kwanakin su a Kano suka dawo ya ƙi sakar mata fuska, abu kaɗan faɗa yake mata, ga shi ita tana tsananin ƙaunar shi duk ta ba shi haƙuri amma ya ƙi kula ta, duk yanda tayi ta kasa shawo kansa har suka dawo gida, yawon shaƙatawan da yayi mata alƙawarin zasu wuce before su koma; sai da ta tuna masa but yayi banza da ita Tunda suka dawo kuma sai duk hankalin sa ya koma tunanin zuwa Zaria, sabida ya san cewa dole a can zai samu yarinyar, duk yanda aka yi Zahra ƴar uwanta ce domin kaman nasu ya ɓaci, yana ji a jikinsa suna da alaƙa da juna, shiyasa yayi baƙin cikin rashin Numbanta, yanzu dole sai ya neme ta, koda ita ya samu ya tabbata dole zai samu yarinyar. A kwana biyun ya kasa samun natsuwa shiyasa ya sanar da Sinior halin da yake ciki, ya nemi shawaran shi saboda ba ya so Nawwara ta san inda zai je yana son komawa Zaria Sinior yace, "yanzu kai kana nufin a can take kenan?" "Haka nake tunani Sinior, na tabbata a can take, idan ma ba a can take ba in na gama bincike na in ban same ta ba fine." "Ok to yanzu taya zamu fara? Ka san Zaria ba ƙaramin gari bane, yana da faɗi, ya zamu yi mu nemo ta?" Shiru yayi, sai kuma ya ja numfashi before yace, "Ni dai zan riƙa kasancewa a can saboda ko Allah zai bani sa'ar ganin su dukka biyun, domin yanzu ba ita kaɗai nake nema ba, idan har zan samu wannan yarinyar da na gani zan ji daɗi gaskiya, in na bincika basu da alaƙa da juna dole zan ƙulla alaƙa da ita saboda kamannin ta da Babyna." Dariya kawai Sinior yayi yana kallonsa While shi kuma yace, "zaka raka Ni zuwa nan da two days sai mu je, ko hoton ta sai in nuna ma mutane wala'alla zamu samu wanda ya santa." Kafaɗa ya ɗage yace, "Allah ya kaimu." "Sai dai ba na son Nawwara ta san inda zamu je saboda na santa dole zata zargi wani abun, ka san halin ta." "Baza ta sani ba, zamu san yanda zamu yi, kaima na kula fushi kake yi da ita, don haka kafin nan yakamata ku shirya ko don kar tayi tunanin wani abun, hakan zai fi." "Shikenan." Malik ɗin ya furta yana kwanciya a saman gadon shi Shi kuma Sinior ya tashi yace, "Let me go. We'll call later." Ok." Da haka ya fice ya bar shi a ɗakin Shi kuma ya ci gaba da tunanin sa kamar yanda ya saba, gaba ɗaya tunanin Arab ne a ranshi zuciyar shi har tsinkewa take yi, soyayyarta tayi mishi kamun da bazai iya haƙura da ita ba, take ya fito da wayansa ya lalubo hoton ta ya ci gaba da kallo, sai kuma ya miƙe ya je ya kulle ƙofan sa don ya san zai iya ganin Nawwara at any time ta shigo cikin ɗakin. Nan ya kwanta ya ci gaba da sana'ar kallon hoton Arab wacce tana sanye cikin ƙananan kaya riga da wando, sun yi mata kyau matuƙa kuma sun fito mata da ainihin surar jikinta mai jan hankalin duk wanda ya gani, fuskarta babu kwalliya tana murmushi a hoton, ta sanya facing cap a kanta sai dogayen takalma masu igiya a ƙafafuwanta, tana riƙe da ƙugunta da hannu ɗaya, yanda tayi style ɗin tsayuwarta kanshi abun kallo ne, dole duk wani namiji mai lafiya sai ya susuce a kanta, haka shima Malik ɗin sai da sha'awar sa ya tashi tsaban yanda yake mata kallon ƙurilla, kuma ya kasa denawa sai da ya ga yana shirin fita hayyacin sa duk ya gama susucewa ya rasa yanda zai yi, ƙarshe kiran Nawwara yayi sabida ya samu ya kwantar da sha'awar tasa, idan ba haka ba da matsala, Allah yayi shi mai tsananin sha'awa ne, shiyasa ko ya ya ne idan Mace ta raɓe shi sai ta rikita shi, dalilin da yasa ba ya haƙura da mata kenan, kullum ranan duniya sai ya je club ya samu wacce zai huta, shiyasa idan ya samu Macen da zai huta da ita sai su wuce gidan Sinior, a can yake holewar sa wani lokacin har mata biyu yake ɗauka. Nawwara ce kaɗai yake cin ta a gida tunda ya san ita yar gida ce kuma babu mai saka musu idanu Mummyn shi ta san irin rayuwar da suke yi but bata taɓa damuwa ba, a ganin ta lokacin su ne sannan kuma da amincewar ita Nawwaran, don haka baza ta shiga tsakanin su ba tunda ta san ita zai aura, su kansu basu san cewa ta gane me suke yi ba idan suka shige ɗaki suka kulle Ga shi yanzu har Nawwaran ta koyawa Zainab bin Maza, don ta kwaɗaita mata daɗin abun shiyasa itama ta soma, tace mata, "idan ba tayi har yanzu bata waye ba, kallonta zaa riƙa yi tamkar bagidajiya, rayuwar yanzu sai da irin haka sai ana yi ana morewa, idan tace sai ta jira tayi aure ƙarshe baƙin ciki da damuwa zai kashe ta." Zainab kuma sai ta ɗauki huɗuban ta tayi amfani dashi tana ba wa samarin ta kanta, shiyasa yanzu ko karatun da take yi ba ta zuwa, sai dai ta fita da zummar zuwa makaranta but sai ta ɓuge a ɗakin saurayin ta, tana can suna holewar su, shiyasa ba ta gane komai yanzu don tuni ta jima da dena zuwa makaranta, sai dai idan tana son results mai kyau ta bi Malamai; sai ta ba su kanta sannan su bata result mai kyau, shiyasa sam ba a gane halin da take ciki Nawwara kaɗai ta sani don ita ce ƙawarta, ita kuma ba ta bin kowanne namiji idan ba Malik ba, shi kaɗai take iya ba shi kanta don shi kaɗai take so, baza ta iya tarayya da kowa ba sai shi, shima dalilin da yake matuƙar sonta kenan. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️        Zahra da Arab ne tafe suna dariya a kan hanya, sun dawo daga wurin Baban su da Inna ta aike su su je su amso mata kifi. Zahra ke riƙe da kifin don ita aka aika, sai suka haɗu da Arab wacce suke tare da Ibrahim a ƙofar gida, ita kuma tace, "zata raka ta." Shiyasa suka tafi a tare. Bayan sun je sun dawo ne Zahra take bata labarin Nawwara abin da tayi mata; tunda bata san komai ba basu sanar mata ba, kuma after ta dawo time ɗin an cire ma Zahra bandage ɗin da ke kanta har wurin ya warke Abun dariya ya ba wa Arab ma sabida jin wai har marin ta tayi, sai ta sake tuntsirewa da dariya tana cewa, "wlh kin bani mugun dariya, abun ne kamar almara, wai kina mene ne har ta zauna ta mare ki?" "Uhm baza ki gane bane Arab, Ni kaina nayi mamakin kaina saboda yanda na kasa ramawa, amma ta shammace Ni ne sannan ga mutumin da nake ba ki labari suna tare; yana ta bani haƙuri, Ni abin ma ya ɗaure mini kai yanda take nuna tsagwaron kishin ta." Arab tace, "kashh! Ban ji daɗi da ba na wajen ba, na rantse da Allah da ace Ni ta yiwa marin nan sai na sumar da ita, ban ga abun da zai hana Ni tayar da ƙura a wajen nan ba koda jinina zai ƙare ne." Zahra na dariya tace, "ke dai ayi sha'ani kawai, amma ai akwai alwashi a raina, sai dai kuma idan Allah bai haɗa mu ba." "Yo aina zai haɗa ku bayan ba ki san inda za ki same ta ba? But ni baƙin cikina da ba ki ba shi Numbanki ba, da shikenan dole zai neme ki kuma dole sai mun ɗauki mataki a kanta; domin wlh sai mun raba ta da saurayin nata da take taƙama dashi, har abada kuwa, sai ta raina kanta sai ta gummace bata aikata miki hakan ba." Sai ta cije baki tana kaɗa kanta "Ba ki kai Ni baƙin ciki ba wlh, ai nima na so ace na ba shi Numbata da na san dole zai neme Ni." "Ke bar kayan takaicin nan ki raka Ni shagon can in siya kati." Arab ɗin tayi maganar tana ƙoƙarin laluba aljihun rigan ta Zahra tace, "ok." Sai suka nufi bakin shagon yayinda Arab hankalin ta na kan ciro kuɗi Ita kuma Zahra suna gaisawa da mai shagon cikin faram-faram tunda sun saba, har tana tsokanar shi, "wlh sai ya ba ta chocolate ɗinta tunda ya taɓa mata alƙawari." Dariya yayi yace, "afwan Zahra, wlh yanzun ma bani dashi don ya ƙare, sai dai in canza miki da wani abun da kike so." "To shikenan, bani biscuit mai madara." Dariya kawai yayi yace, "to." Yana nufan cikin shagon zai ɗauko mata Ita kuma Arab tace, "Shu'aibu bani kati." "To wanne iri ranki ya daɗe!?" Yayi maganar yana juyowa da biscuit ɗin a hannunsa ya miƙawa Zahra Ita kuma ta amsa ta soma ƙoƙarin buɗewa tana cewa, "Allah yasa da daɗi." Arab tace, "MTN zaka bani, kana da ƴan ɗari biyar ne?" "Eh ina ga akwai." "Ok bani guda uku, but kuɗi na bai cika ba zamu haɗe a gaba." "Kai Matar manya akwai matsala fa idan na ba ki katin nan don na san halin ki." "Wai kana nufin bazan biya ka bane? Kaima ka san ba ma haka da kai tunda ban taɓa cin kuɗin ka na hana ka ba, da Allah miƙo min." "Shikenan zan ba ki, amma don Allah kar ki daɗe ba ki biya Ni ba sabida ba nawa bane nima, kiyi haƙuri ki taimaka ki biya Ni da wuri." Yayi maganar yana dariya ganin yanda take hararansa "Don Allah ka sallame Ni sauri nake yi, ka ga mutane sun soma zuwa kar mu tsare musu wuri." Sallaman wasu ƴan mata biyu ne ya hana Shu'aibu yin magana Yayinda wasu yara su ma suna tsaye duk sun zo siyayya ne, sai faɗi suke yi, "a basu kaza... A basu kaza..." Yayinda ƴan matan nan tunda suka zo suke hararan su Zahra ƙasa-ƙasa Ita Zahra ma hankalin ta na kan biscuit ɗinta tana ci tana tambayar ɗaya daga cikin yaran nan While Arab ta juya musu baya tana kallon Shu'aibu da ke ɗauko mata kati, sai ji tayi ƴan matan suna dariya da shewa, hakan yasa ta juya ta kalle su, ta gane su ƴan matan layin su ne, don ɗaya ma maƙociyar su ne, kanta kawai ta kawar tana amsar katin da Shu'aibu yake bata, sai dai bata kai ga sawa ba ta ji maganganun da suke yi wanda hakan ne yasa ta ɗaga kai ta kalle su Ɗaya tace, "ke bar zancen nan idan mun koma gida ma yi don naga munafukai sun soma saka mana idanu." Hakan ne yasa Arab ta tanka tace, "Ke Zaliha su waye munafukai a nan? Da wa kike yi?" "Da wa nake yi kuma? Kamar ya da wa nake yi? Wanda ya tsargu ko kinga na saka baki da ke?" Itama tayi maganar cikin ɗaga murya da tsiwa tana hararanta Daga wayanta har katin zura su tayi a Aljihun rigan nata tana cewa, "ƙwarai kuwa, domin duk wanda yayi zagi a kasuwa ya san da wanda yake yi, a nan dai mu kaɗai ne a wajen nan, sannan ba yau ba naga take-taken ki nema kike yi ki shigan mana hanci da ƙudundune, na rantse da Allah tsab zan faco ki domin ke ƙaramar alhaki ce ba ki isa in zauna ina sa'insa da ke ba, Ni na fi ki hauka jujun da suke kanki ƙanana ne a kan nawa, don haka ki kama kanki duk wani iskanci da kike ji da shi a tafin hannuna kike, na fi ƙarfin a zauna ana min shaguɗe a gabana in ƙyale ina kallo, kin san hali na ba na juran raini bare wulaƙanci." Har ta dire maganar Shu'aibu haƙuri yake bata yana cewa, "don Allah suyi haƙuri haka nan, Arab ta ƙyale ta." Don ya san ƙarshe mai zai faru, shiyasa yayi saurin shiga tsakani don a rabu lafiya But Arab bata san ma yana yi ba tsiya ya ci ranta sai rattaba zance take yi, don ƙiris take jira dama tunda tana da cikin Zalihan ba yau ta saba shiga harkan ta ba, yau kuma baza ta iya haƙura ba dole ne ta ɗauki mataki a kanta Zahra kuma dayake ba tsiyan ne a ranta ba; sai ta riƙo hannunta zata ja ta su tafi domin ta ƙi tankawa ma Amma ina Arab sabida jin maganganun da Zaliha da ƙawarta suke faɗi Har Zalihan na cewa, "yo ku da ku ka yi gadon iskanci waye bai san gidan ku ba? Dama dai ace ba'a san halin balbela bane sai tace daga Misra ta fito, to an san halin ku ciki da bai don kin nuna min ke tatacciyar Karuwa ce mai lasisi bazan damu ba...." Kafin ma ta ajiye maganar nata tuni Arab ta kafta mata maruka, fau fau haka ta sauke mata su cikin zafin nama da fusatan da tayi Nan da nan fa sai wurin ya rikice domin tuni Zaliha ta kai mata wawura itama sun soma kokawa While ƙawarta Jamila sai itama ta soma kai ma Arab ɗin duka suka taru mata Zahra da ke tsaye ai itama sai ta finciko Jamilan ta hau kima suka soma dambe har da faɗawa shagon Shu'aibu Ai tuni ya soma ihu yana faɗin, "kai kai zaku yi min ɓanna." But ko kaɗan ba sa jin sa don yanda suka cakuɗe sai bige-bige ake yi har da cire gyalulluka; ɗankwalai sun yi gefe ana ta tuman juna Ya rasa yanda zai yi don ya kasa taɓa su ganin mata ne, ganin dai da gaske suna ɓarar mishi da kaya nema suke yi su hargitsa mishi shago sai ya soma ƙoƙarin finciko su yana cewa, "wai meye haka ku fitar min a shago da Allah, zaku yi min ɓanna fa." Allah da ikon sa sai ga wasu samari sun faɗo shagon tunda suka ga mai ke faruwa, su suka yi ƙoƙarin raba su amma ina sun kasa fincike Arab a jikin Zaliha Ga shi ita ta fi shan wahala don har yaga mata gaban riga aka yi, babu ɗankwali babu gyalen ta a jikinta, kuma ta ƙanƙame Zalihan ta ƙi saki faɗi take yi, "sai ta koya mata hankali, sai ta nuna mata ita ba sa'ar wasan ta bane." Ƙarshe dai faɗa yayi tsamari waje ya cika maƙil da Maza sai zuwa kallon su suke yi, bare yanda suka samu abun kallo babu wacce jikinta bai bayyana ba, kar ma ace Arab ta ji, nata ma yayi muni da yawa amma ita ko a jikinta, burin ta kawai ta samu nasaran lallasa Zaliha amma hakan ya faskara don ta fi ƙarfin ta kasancewarta ƙatuwa Daƙyar wasu Maza suka raba su suka kama Arab ɗin ƙaƙam suka fito da ita a shagon da suka gama hargitsa mishi, nan fa ta soma zagin su tana cewa, "sai sun sake ta ta ƙaddamar mata, wlh baza ta ƙyale ta ba yau sai ta koya mata hankali." Babu wanda bai san jaraban gidan su ba musamman ma Arab don bata da mutunci ko kaɗan, ba yau suka saba ganin irin wannan damben na tada husuman gari ba, kar ma ace uwar su ta ji. Shiyasa aka yi saurin kiran ƴan sanda don idan ba'a yi hakan ba za'a samu matsala, su kaɗai ne zasu iya tsayar da rigimar nan cikin sauƙi tunda aka taɓo gidan jarababbu. [22/07, 11:38 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA GOMA SHA HUƊU* _______________Kafin ƴan sanda su zo har rigimar ta ƙara ta'azzara sabida yanda Arab take zagin mutanen da suka riƙe ta ta uwa ta uba Kankace me an samu wani wanda ya gwabgwabje ta sabida yanda take zagin su, ya kasa haƙura shiyasa ya same ta ya dinga duka, har da matse mata nonuwa tunda shima ɗan iska ne ya samu na banza a waje, a zuwan yana dukanta haka ya lallatse banza Ita kuma tun tana ramawa but ƙarfin su ba ɗaya ba, nan da nan yayi mata lilis daƙyar aka ƙwace ta a hannun sa But bakin ta bai mutu ba haka take ta zagin shi tana kuka. Daga ita har Zahra zagin shi suke yi but ita an riƙe ta ta kasa kufcewa Motan ƴan sanda na zuwa aka tattara su zuwa police station.            ***********       Wani yaro aka samu ya sheƙa da gudu gidan su Arab ya kai musu gulman ana faɗa da su Ai kuwa nan Inna tayi kiran Ummu tana cewa, "Ummu Kulsum.. Ummu Kulsum." "Na'am." Ummu ta fito daga bayi da gudu riƙe da buta "Maza ɗauko min wando na mu wuce station, wai ana faɗa da su Zahra an kai su can, maza-maza ɗauko min mu je mu ji ba'asin abun da ya faru." Da sauri Ummu ta nufi ɗakin Innan ta ɗauko mata wandon damben ta, dama hakan take yi sau tari idan ana faɗa da ƴaƴan ta da shirin dambe take zuwa wurin, idan ma damben ta kama haka zata tuɓe gyale aba hammata iska, sam Inna Harira bata da ta ido, kowa ya san ta a garin a kan ƴaƴan ta bata da mutunci ko na misƙala-zarratan Haka suka fice daga ita har Ummu suka tafi station. Suna zuwa kuwa suka hango yanda aka yiwa Arab, duk an farfasa mata baki an ji mata ciwuka, a wurin ma bakin ta bai yi shiru ba shiyasa aka ce cell za'a jefa ta. Dai-dai nan su Inna suka iso wajen Da gudu ta riƙe Arab ɗin tana cewa, "Ah ah ya haka DPO? Ya za'a yi ka jefa min ƴata cell a kan wanne dalili? Su sauran shafaffu da mai ne da baza a saka su ba sai ita?" "Ke! Ki kama kanki nan fa ba wajen wasan ku ba ne, ya za'a yi ku zo ku mayar mana da station filin dambe? Muna da maganin ku wlh don kun ishe mu, case ɗin ku yayi yawa a wajen mu zan ɗauki mummunan mataki a kanku." "To ai naga dai ba wani abun muka yi ba, a kan haƙƙin ƴaƴana nake magana, wlh bazan bari a saka ta a cell ba sai an faɗa min abun da tayi, bazai taɓa yiwuwa ba." Kallon yanda take kumfar baki kawai yake yi tsaban tsiya ya ci ranta, ya san matar nan bata da mutunci tunda ba yanzu suka saba sa'insa da ita ba idan aka kawo su nan, don haka yace, "yanzu za ki tsaya ayi sulhu ne ko kuma so kike yi mu nuna miki ƙarfin mu? Duk wani tsiya naki ba shi ne zai ƙwace ku a nan ba, don haka ki kama kanki tun kafin raina ya ɓaci." Hakan ne yasa Inna ta sassauta ganin yanda taga fuskarsa babu alamun wasa, don ta san tsab zai iya kulle mata yara tunda shima ba kirki ne da shi ba Kiran wani Corporal yayi yace, "ya je ya taho da sauran duk wanda zancen ya shafa." Haka suka shigo mishi Office gaba ɗayan su har Shu'aibu mai shago, don yace, "wlh bazai yarda ba shima sai an biya shi kayan shagon shi." kuma ya san nan ne kaɗai zai iya samu a ƙwatan mishi haƙƙin shi Nan DPO ɗin yace, "a sake mayar da maganar, kuma ayi masa daki-daki yanda zai fahimta." Shu'aibu ya soma bayar da labarin abun da ya faru tunda shi aka ce yayi maganar since a gaban shi aka yi komai tun farko. Ai kuwa ya soma rattafa zancen komai yanda aka yi Bayan an gama ne sai DPO yace, "to kin gani, ai har da laifin ƴarki tunda ga abun da aka faɗa a gabanta ta musa idan ƙarya ne." "Eh babu zancen ƙarya a ciki, amma babu yanda za'a yi wata ta zo har inda nake ta taka Ni, meye laifi na don na ɗauki mataki? Idan don gaskiya za'a yi ai su ne da laifi tunda su suka zo suka taƙale Ni." "Dalla rufe min baki mara kunya, ke dama ai ba a ka dake a zance, kina wannan halin ma baza kiyi shiru ba, to wlh idan na sake jin bakin ki za ki ganki a cell." Tura baki gaba Arab tayi tana ƙunƙunai Sarai yana jin ta shiyasa yayi ƙwafa ya mayar da hankalin sa a kan sauran Inna tace, "to Ni ban ga aibun abun da Arab tayi ba tunda su suka soma taƙalan ta, don haka tun a nan wlh sai an yi musu tsakani kafin mu bar nan wurin, kuma dole ne a hukunta ta a kan kira min yara da tayi da karuwai, na rantse da Allah sai an ɗauki mataki don nima bazan yarda ba..." "Ya isa haka Hajiya." DPO ya katse ta yana ɗaga mata hannu, "ki bari mu yanke hukunci ba ke za ki yanke mana ba." "Ai naga nima maganar haƙƙina ake yi, wlh tallahi bazan yarda ba sai an hukunta ta tunda ta kira Ni da karuwa, zan ga idan ubanta ne ya taɓa ci na da take kira na da kalman." Arab tayi maganar tana kaɗa jiki don har ta manta da riƙe wurin da aka yaga mata gaban rigan, ta sake shi ana ganin breasts ɗinta Da sauri DPO ya kawar da kanshi yana cewa, "ke shashashan yarinya ce ko? Ban hana ki magana ba? Zan ɗauki mataki a kanki kuwa yau. Kai kama ta ka saka min ita a cell." Ya ƙare maganar yana kallon inda Corporal din nan yake, duk suna tsaye da su Shu'aibu idanunsu yana kan Arab suna kallon t.v suna haɗiye yawu Ita kuwa ko a jikinta. Sai ma jin da tayi za'a kama ta a saka ta a cell take faɗin, "ita wlh ba'a isa a saka ta a cell ba." Nan fa ta ɗaga musu hankalin wurin da hayagagan ta Itama Inna ta riƙe ta gam tace, "baza a shiga da ita ba." Ga shi shi DPO ba ya son kallonta sabida ganin albarkatun ƙirjin ta a buɗe, amma ganin suna son raina musu hankali sai ya cire kunya yayi musu jan ido yace, "a saka ta a cell." Haka kuwa suka tura ta har ƴan sanda biyu suka saka ta kamar yanda DPO ya basu umarni, babu ɗankwali bare takalmi, har gyalen ma duk an watsar da su tun a can wurin dambe; ga riga a ɓarke Wurin fa ya karaɗe da faɗan Inna, tace, "Sam sai an sako mata ɗiya baza ta taɓa yarda ba." Bala'i dai kala-kala da tijara haka take sauke musu, tana yi su Ummu suna taya ta Sai da DPO ya sake yin musu jan ido ransa a mugun ɓace yace, "ya rantse sai ya haɗa su duka ya kulle idan basu bar mishi wurin nan ba." Hankalin fa Inna ya tashi sabida ganin an ƙi ba ta Arab, bare yanda taga duk an farfasa mata fuska a damben da suka yi; shiyasa take ta musu haukan, "idan ɗiyar ta ta mutu ba'a bata sun tafi asibiti ba kaf ɗinsu sai tayi ƙaran su." Haka suka bar wurin suna tijaran nan sai kallon su ake yi Domin su kansu ƴan sandan abun ya zame musu t.v ne tunda sun saba ganin hakan a wurin su, abun ma ya wuce a kansu har da ogan su ake yi yau. Duk da dama wani lokacin suna zuwa station ɗin ake sakin su tunda sun samu dai-dai dasu ƴan iska, shiyasa suke sakin su tunda zasu kewayo su ɗibi rabon su a wajen su Amma yau DPO ne da kansa kuma shi ba irin halin shi bane shiyasa suka samu matsala yau, ransa ya ɓaci dalilin da yasa ya hana belin Arab kenan, kuma yace, "sai yayi maganin su." Haka ya sallami sauran bayan ya kashe Case ɗin, yace ma Shu'aibu, "ya je ya ƙirga duk asarar da aka yi masa masu damben zasu biya shi, daga su Zaliha har su Arab ɗin".                *******       Duk yanda su Inna suka so a saki Arab abun ya faskara, don DPO ya hana belin ta. Daƙyar da suɗin goshi aka samu ta fito a daren ranan domin a cikin Samarin Ummu ne wani ya fito da ita, tunda yana da hanyar manyan ƴan siyasa sai ya je ya roƙe ɗaya; shi ya saka baki aka sake ta Daga can station ɗin ne ma aka wuce da ita asibiti tunda Inna tace, "sai an je an duba lafiyarta." Suka je aka yi treating ɗinta sannan suka koma gida Baba sai faɗa yake yi amma nan da nan ta hau kansa, ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, a kansa ta ƙare haushin ta, don ma dare yayi ne shiyasa ta bar zancen a iya gidanta, amma ta sha alwashin goben nan a gidan su Zaliha zata dira kaf sai ta ci uban su, sai tayi musu iyaka da gidanta. Ai kuwa duk abun da ya faru a station bata hankalta ba; gari na wayewa ta yiwa gidan su Zaliha mikiya wai ta zo wa uwarta jan kunne, "ta ja ma ƴarta kunne ta fita harkan ƴaƴan ta, duk sanda aka ce ta sake zagin su ta rantse da Allah kotu ne zai raba su domin tsiya daga nan har Mahadi ya bayyana." Tana yi su Ummu suna yi don tare suka zo gaba ɗaya sukai ta tijara Ga shi Maman Zalihan irin matan nan ne masu haƙuri, ta kasa tanka su don hankalin ta a tashe yake, musamman abun da ya faru jiya, sai da ta saka Yayan Zalihan yayi mata dukan tsiya, tace, "idan ta sake taƙalo mata faɗa da gidan to sai dai ya ƙare mata can ita kaɗai." Ta san za'a rina don ba mutunci ne da su ba baza su bar maganar ya tafi iya nan ba, ilai kuwa ga shi nan sun biyo ta gida suna mata ɗiban albarka, babu kowa a gidan sai ita, Allah-Allah take yi su tafi ba tare da ɗaya daga cikin ƴaƴan ta sun shigo ba, don ta san su ma baza su bar su haka nan ba sai sun tanka su, ƙarshe kuma abu ya ƙara rincaɓewa tunda su tsiya gaba suka bata ba baya ba, kowa ya san jaraban gidan su Ana haka sai ga Zaliha ta faɗo gidan, tsautsayi ya dawo da ita tunda makarantar hadda ta tafi, kuma sai aka yi rashin Sa'a an kore su kuɗin makaranta tun a Gate. Haka ta shigo gidan ta tarar da abun da ke faruwa, ai kuwa nan ta saka baki ganin yanda suke yiwa uwarta ɗiban albarka Nan da nan sai suka rufe ta da duka daga ƴaƴan har Innar. Suka yi mata lilis duk da haƙuri da shiga tsakanin da Maman Zalihan tayi basu barta ba Arab sai da ta huce kaf haushin ta suka yi mata jina-jina Maganar ma ta so komawa police station don rigima aka yi raga-raga, yayyin Zaliha suka ce, "baza su yarda ba sai sun ɗauki mataki." Mamansu ta hana su tunda ta san faɗa da su Inna da jaraban su bazai taɓa ƙarewa ba, ƙarshe idan aka je wurin ƴan sanda a kasa amsar musu haƙƙin su, tace, "idan dai ta isa da su to su bar zancen, tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan duka, ita Zalihan da ta taƙale su faɗa gobe sai ta ƙara." Sun ji haushi yayyin da ta hana su ɗaukar mataki, haka dai suka bar zancen ba a son ransu ba, amma kowanne yana ƙullace da su da burin ɗaukar fansa wata rana, sa'an su ɗaya akwai Mahaifiyar su a tsakani da su ma sai sun ga ƙarshen jaraban su, don wlh baza su haƙura ba dole ayi ta ta ƙare Ita kuwa Inna faɗi take yi, "sun ci dubu sai ceto, kowa ya kwana lafiya shi ya so, babu wanda ya isa ya ɗaga mata yatsa a garin nan bata karya shi ba, bare a taɓa mata yara sai inda ƙarfin ta ya ƙare, yanzu suka saka ƙafar wando ɗaya da duk wani shege ko shegiya a garin nan, idan har ba'a dena saka musu ido ba wlh fitina yanzu aka soma, sai ta tayar da garin a kan taɓa mutuncin ƴaƴanta".                Baba kasa fita yayi a ranan sabida kunyar abun da Matar shi da ya'yan shi suka janyo mishi a gari, ko ina yi da su ake yi don kaf anguwansu har da kewaye zancen faɗan nan ake yi Su kuwa ko a jikinsu don tuni yawon su suke yi a gari, kuma ƙiris suke jira wani ya tanka su fitina ta dawo sabo Arab ce kawai babu inda take zuwa tunda duk an suntuma mata fuska. Ƙarshe duk wanda ya zo neman ta sai dai tace mishi, "ba ta nan." Ibrahim Abokinta ne kaɗai yake shigowa har gida tunda shi sun saba ya zama kamar ɗan gidan ne tsaban yanda yake wuni a gidan wani lokacin       Kwanan ta biyu ta warware ta ci gaba da harkan gabanta. Ranan ma da ta soma fita suna tare da Tariq a gidan shi, can ta wuni suna ta aikata masha'an su. Sai bayan Sallan isha'i ya dawo da ita gida after sun shiga kasuwa ya jibgo mata siyayya, bayan sun ajiye magana gobe zata raka shi bikin Abokin shi Kaduna. _Happy juma'at Mubarakh. Enjoy your weekend._ [25/07, 9:05 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA GOMA SHA BIYAR* _______________Washe gari kusan karfe goma na safe su Arab suka nufi Kaduna. Kafin su fita Zaria ne Tariq ya shiga wani gidan mai zai sha mai A dai-dai lokacin su ma su Malik sun iso cikin gidan mai ɗin, zuwan su kenan motan su take yunƙurin tsayawa, Allah yasa akwai gidan man a kusa shiyasa suka shiga ciki, motan su tana setting na su Tariq ne, sai dai kasancewar akwai tied a glasses ɗin ba a ganin su sosai. Idanun Malik kuwa yana a kan motan nasu yana kallo duk da hankalinsa ba a kai yake ba, ya fito da hannunsa ɗaya waje kasancewar ya sauke nasa glass din suna magana da Sinior yana ta dube-dube a waje, kuma duk cikin binciken sa ne a zuwan ko Allah zai sa yayi tozali da ita Abun da yasa Sinior yake ta mishi dariya kenan yana tsokanar shi While Tariq kuma da suke cikin mota yana ba wa Arab haƙuri a kan tsayuwar su a wurin. Kasancewar akwai layi zasu ɗan ɓata lokaci a wajen Murmushi tayi tace, "don't worry, I don't mind." Sai ya riƙe mata hannu yana kashe mata idanu ɗaya tare da cewa, "baby gaskiya ina mugun sonki da yawa! Na ji daɗin yanda za ki bi Ni bikin nan don ina bukatar dama abokanai na su ganki sabida su san wacce zan aura, but we will stay there for two days so that we can have a rest and enjoy ourselves ok?" "Yes, I need that too." Tayi maganar tana lumshe lumsassun idanuwanta saboda yadda take ji a jikinta sakamakon shafa mata jiki da yake yi, har nishi take saki tsaban daɗin abun da yake mata Ganin yanda take amsar saƙon nasa sai ya burkito ta ya dawo da ita jikinsa yana zame mata gyalenta, yayinda ya sanya hannu yana ƙoƙarin zuge mata zip ɗin riganta da aka yi mata ta gaban Ita kuma sai ta buɗe idanu tana kallonsa, hannunta ta saka ta dakatar dashi don har ya fara buɗewa, a hankali cikin shagwaɓa tace, "what can you do?" "Haba Baby zamu ɗan yi wasa ne kafin layi ya zo kanmu, na kasa jurewa ne wlh bazan iya ganin ki kusa dani in kasa taɓa ki ba, kin san ke ta musamman ce, Please baby help me let me have peace of mind, I really miss you!" Ya ƙare maganar yana lashe mata fuska kamar tsohon maye, cikin salo yake tafiyar da ita lokaci ɗaya ta sakar mishi jikinta tunda a hannu take itama, tuni ya zage zip ɗin ya saka hannu ya soma wasa da albarkatun ƙirjinta Lokaci ɗaya suka rikice a cikin motan tamkar zasu cinye juna Malik da hankalinsa ya sake zuwa wajen motan, sai ya tsira ma wurin ido don gani yake yi kamar yana kallon inuwar mutanen ciki, kuma alamu ya nuna akwai abun da suke aikatawa tunda yana ganin motsin su, sai kallonsu yake yi sai kuma abun ya ba shi dariya ya taɓo Sinior yana cewa, "kai zo kayi kallon Film a nan, da alamu mata da miji ne a nan kaga sai hutawar su suke yi babu ruwan su." Shima leƙawa Siniorn yayi, shima yana hangen komai sai dai baza ka gane sosai bane sai idan ka kula dasu, kuma baza ka gane mutanen ciki ba sai inuwar su, dariya yayi shima yace, "da alamu a hannu suke fa tunda suka kasa haƙura, kalle su kamar zasu haɗiye juna don sun zama abu ɗaya ma." "Uhm har sun sa nawa ta motsa ina buƙatar kasancewa da Mace, gaskiya muna tashi a nan Hotel zamu wuce in nemi wacce zata rage min zafi." "Kai dai masifan ka yayi yawa, shiyasa nace babu wacce zata iya da kai sai Nawwaran tunda itama ka koya mata wannan shegen jaraban taka, Yakamata dai ku samu kuyi aure ku huta haka nan." Dukansa Malik yayi yace, "kai me ya hana ka auren dan ubanka? Naga dai halin mu duk ɗaya ne ba finka nayi ba." "Wlh ƙarya kake yi Ni ban kaika wannan jaraban ba, kai da kullum sai ka ci mata fiye da biyu a rana, har haɗa su kake yi a lokaci ɗaya fa. Haba dai ina zaka haɗa Ni da kai kaima kayi ƙarya." Uhmmn kawai yace yana lumshe idanuwansa yana wani ƙanƙame jikinsa, sai kuma ya buɗe idanun da suka soma canza kala sabida jaraba yana kallon motan, haka ya tsira musu ido ko ƙyaftawa ba ya yi Sinior kuwa sai dariya yake mishi yana cewa, "kar dai ka je ka janyowa kanka dan Allah ka dena kallon su, ka bari mu bar nan lafiya kar ka rikice min ka janyo min abun kunya." Hararansa yayi yace, "me ka mayar dani ne wai?" "No babu komai, Ni dai maganar gaskiya na faɗa maka ka dena saka musu ido." Malik tsaki ya ja yana mayar da idanunsa a kansu yana aiyana abubuwa a ransa Sai da layi ya zo kansu sannan Tariq ya fito daga cikin motan Da sauri Malik ya taɓo Sinior yana cewa, "kai kaga shegen ƙwallon can ya fito a yamutse, ashe dai abun da suke aikatawan kenan." Dariya kawai suke mishi sabida ganin rigan shi duk a yamutse, kuma su sun san me ya aikata shiyasa suke ta gulman shi Har Sinior yana cewa, "da ace itama zata fito muga idon shegiya, tana fitowa zamu gane idan matar shi ce don daga gani wannan da budurwa yake wannan aika-aikan; idan matar sa ce ai baza su zo titi suna wannan iskancin ba, duk da dai sun san babu wanda zai gansu mu ma shegen bin ƙwaƙƙwafin mu ne idanun mu ya ja mana." Dariya Malik yayi yace, "wa yace yayi? Ina ruwan mu?" "To yi gaba Malam mota ta matsa muyi-muyi." Time ɗin ne Arab ta kalle side ɗin su, nan idanuwanta suka sauka a kan Malik sai ta kasa janye idanunta a kansa saboda ta shagaltu da kallon kyakkyawar fuskarsa da surar jikinsa, musamman yanda ya tara ƙwanji a jikinsa gunun sha'awa, daga gani zai yi ƙarfi ne har taga yanda zai taka rawa a bed idan da ace zata same shi, lashe laɓɓan bakinta tayi tana shirin zuge Glassess ɗin tunda bata ga fuskarsa sosai ba But lokacin shi kuma tuni ya ja motan sun ƙara gaba sun tashi a side ɗin Hakan yasa koda ta buɗe ta dena hangen sa, har leƙa kai tayi amma bata hango shi ba sai dantsen hannun nashi. Jin motsin shigowar Tariq ne sai ta mayar da hankali a kansa tana tambayar sa, "har an zuba mishi?" Yace, "Yes. Now we will pass." Motan ya kunna ya ja suka bar wurin Idanun Malik har yana kai wa wajen motan, nan ya hangi Arab kuwa tunda bata mayar da glass ɗin ba, ba ya ganin fuskarta sosai but yana hango white skin ɗinta da ya tsole mishi ido, har leƙa kai yake yi yana sake juyawa don samun ganin fuskarta, kaɗan ya ganta sai dai bazai iya gane ta ba, a ransa yace, "yarinyar kyakykyawa ce daga gani, zan so ganin fuskarta gaskiya don ba ƙaramar beauty bace, She has cute skin and glowing." Ɗauke kansa yayi yana kallon Sinior da ke waje yana ma me zuba man magana, dayake su ne a kan layi yanzu Ana zuba musu ya shigo ciki ya ja suka tafi. Kai tsaye hotel ɗin suka wuce kamar yanda Malik ya matsa mishi sai sun je, suna zuwa kuwa suka kama ɗaki, a nan Sinior ya shiga wanka Shi kuma Malik ya fita zagawa ko Allah zai sa ya samu wata Macen, but duk jimawan da yayi bai samu ba, dole ya dawo ciki yana faman jan tsaki tare da maganganun cewa, "matsalar ka zo garin da baka sani ba kenan, yanzu da a can Abuja ne da tuni na kira su sun zo, amma yanzu a nan wa na sani?" Sinior sai dariya yake mishi yana tsokanar shi A haka ya shiga wanka ya shirya shima, suka ci abinci sannan suka fita zagawa a kan aikin da ya kawo su. ********* *KADUNA STATE* Su Arab sun isa Kaduna a cikin ƙanƙanin lokaci, a hotel suka sauka, bayan sun yi wanka suka yi odan abinci sannan suka kwanta suka huta, sai bayan la'asar suka farka suka yi sallah suka sake ɗaukar wanka Tariq ya kira Abokin shi ya tambaye shi, "suna ina ga shi ya shigo gari?" Ya sanar mishi, "yanzu haka suna gidan su ya zo ya same su a can." Hakan ne yasa yace ma Arab ɗin, "ta jira shi zai je ya dawo." But sai ta nuna sam a'a tana ta narke mishi sai ya je da ita Nan yace, "haba Baby ba na son zuwa da ke sabida kaf abokanmu ne a wurin." "But kai kace zaka gabatar da Ni a wajen su ai." "Ba irin wannan gabatarwan ba Baby, gobe ne bikin a wajen party nake son mu je tare sai in gabatar da ke, amma yanzu gaskiya ina kishin ki bazan so su ganki ba gaskiya, kuma mu da muke hidiman biki ina zan ajiye ki in kin bi mu?" Tura baki tayi tace, "sai ka kai Ni wajen Amaryan sa mana nima in zauna a can." Hannu yasa ya janyo ta jikinsa yana cewa, "haba Babyna ki gane mana, kishin ki nake yi bazan bari su ganki ba gaskiya, ki dai bari goben zamu je bikin tare zan kai ki wajen Amaryan sai ki zauna a can, idan za'a yi partyn sai ku wuce tare a can zamu haɗu in gabatar da ke." "No worries since you said, I will stay." Hugg ɗinta yayi tightly yana mata kissing a kumatu, sai ya ɗan ɗago ya dube ta tare da cewa, "Allah yasa Princess ɗina bata yi fushi ba? Kin amince in tafi ko babu komai?" Kallon cikin idanuwansa tayi tana murmusawa sai ta manne a jikinsa tana zagayo da hannayenta ta bayan shi, cikin salonta tana goga mishi ƙirjinta tare da narke murya tace, "to ya zan yi? As you say I will do, sai dai kar ka jima idan ba haka ba zan yi kuka." "Oh! Baby I promise you soon zan dawo, but idan kina min wannan shagwaɓar naki ji nake yi kamar kar in bar ki, sake rikita Ni kike yi." Dariya tayi tana lashe bakinta, sai ta ɗago kanta tana ɗaura gemun ta a ƙirjin sa yayinda narkakkun idanuwanta suke kallon nashi tana ɗan murmusawa, a hankali ta furta, "kar ka damu ai Ni taka ce muna tare a kodayaushe, ka je ka dawo sai mu kasance tare domin nima ina buƙatar ka." Cike da farin ciki ya haɗe bakin su yayi mata hot kissing, before yayi mata alƙawarin, "bazai jima ba zai dawo." Sai ya tambaye ta, "me take so ya taho mata dashi?" Ta sanar mishi sannan ya fice ta raka shi har bakin ƙofa. Yana fita ta koma saman sofa ta kwanta tana ɗaura ƙafafuwan ta a saman jikin kujeran; ta ɗage su tana latsa wayanta, chart take Yi da samarin ta shiyasa sai murmusawa take yi tana cije leɓe. Momentarily tana juya kwanciya sabida daɗin chart ɗin, yawanci maganganun batsa ne shiyasa lokaci ɗaya ta fita hayyacin ta, shiyasa kawai tayi off ta koma hira da Ibrahim kawai, video call suke yi yana kwantar mata da hankali, har kaya ta cire suna sex video. Sai da ya gamsar da ita sannan suka haƙura da juna ta shiga ta sake yin wanka, riga da wando ta saka English wear, rigan blue mai gajeren hannu da wuyan love, sai ta saka jeans baƙi da flat Thoms, hula ta ɗaura facing cap a kanta ta zura wayanta cikin Aljihu ta nufi waje a haka, baza ka taɓa cewa musulma bace a wannan shigan da tayi don komai nata juyawa yake yi sabida yanda kayan suka matse ta, shiyasa tunda ta fito mutane ke kallonta ba Mazan ba ba matan ba idan har idanun su ya kai kanta, Allah yayi ta da jikin Mata mai kyau, komai nata abun sha'awa ne bare yanzu ta sake cika komai Masha Allah; babu namijin da zai iya yin mata kallo ɗaya ya ɗauke ido komin kamewan sa kuwa. Kai tsaye wajen Swimming pool ɗin cikin hotel ɗin ta nufa ta samu kujera ta zauna tana latsa wayanta da ta zaro Ko minti uku bata yi ba wani matashin saurayi ya ƙariso wajen ya zauna bayan yayi mata sallama Kallo ɗaya tayi masa ta karanci yanayin sa ta ɗauke kanta, Allah yayi ta da wannan baiwar idan har Arab zata kalli namiji tana gane wanne kalan Mutum ne shi? A haka take gane kana da maiƙo da kuma kai ɗan hannu ne wadda zata iya mu'amala da kai, tana da karatun Maza sosai a kanta sabida mu'amala da su, ta san su kamar yunwan cikinta. Duk da yayi mata magana bata kula shi ba sai da ta gama jan ajin ta Shi kuma ganin zai iya rasa ta idan yayi wasa don ya kula ba ƙaramar yarinya bace, tana da class sosai ga baiwar kyawu da Allah ya bata mai ɗaukar hankali, nan ya buƙaci waiter ya kawo musu drinks da abinci. Masu tsada ya siya aka ajiye musu, sannan ya kalle ta yana murmusawa yace, "babe ki taɓa wani abu cikin nan tunda naga kin zauna haka nan babu komai a tare da ke, ina fatan za ki amshi tayi na da nayi miki?" Ɗago kai tayi ta kalle shi, sai ta harɗe ƙafafu ba tare da ta janye idanuwanta a kanshi ba, ta sakar mishi kyakykyawar murmushin ta da lokaci ɗaya yake tafiyar da zuciyar Mutum, cikin salo da tsantsan yanga irin nata tace, "to na gode Yallaɓoi, sai dai har yanzu ban gane manufar ka ba a kaina? Me kake nufi?" Dariya yayi kaɗan before yace, "a zamana a nan na karanci ke babbar yarinya ce, so bazan yi tunani da gaske ba ki gane manufata ba, na san kin fahimta sai dai idan jan aji kike min, ki bani dama mana mu ƙulla Abota tare, a jikina ina jin ke ta musamman ce, zan so ace mun zama abu ɗaya kuma ina fatan ace hakan ya ci gaba har zuwa wani mataki da nake burin ki kasance." Murmushi kawai tayi tana ɗaukar drink ɗaya ta zuba a glass cup ta soma sha, har yanzu ƙafafuwanta suna harɗe bata sauke ba, har wani lumshe idanu take yi tsaban yanda daɗin ya kai mata ga sanyi yana ratsa ta Hakan yasa matashin saurayin ya haɗiye yawu har da lanɗe bakinsa, yayinda yake bin ilahirin jikinta da kallo cike da sha'awa, a hankali ya furta, "kin shiga raina baby, ki bani dama na shiga rayuwar ki domin ina jin zuciyata ta kamu da ƙaunar ki lokaci ɗaya..." Dariya ta sakar mishi wanda yasa ya dakata da maganar lokaci guda yana kallon zubi da kyawun da Allah ya bata, dariyan ba ƙaramin mugun kyau yake ƙara mata ba, shiyasa har ya shagaltu da kallonta yana bin bakinta yanda take magana tana sarrafa shi cike da sha'awa Idanunta itama suna kanshi take cewa, "to Malam Ni zan wuce saboda ina tare da wani a nan ne, but zan baka Numbata sabida naga kamar zaka yi min amfani." Sai ta saki murmushin gefen baki tana sake cewa, "thanks da siya min lemu duk da ban buƙata ba." "Haba kar kiyi min godiya mana girman ki ne ai, gaskiya ke kyakykyawa ce domin ban taɓa ganin wacce ta taɓa min kyau kamar ki ba, you are very beautiful and your voice is so sweet, ga ki sweet baby girl irin wacce ake yayi; I love you! I really enjoyed the meeting." "Mee too, I will go." Sai ta ɗauki wayanta zata tashi He quickly stopped her saying, "You forgot to go and you didn't give me the Number." "Oh! I forgot, but kai kuma abun na ranka ko?" Tayi maganar cikin smiling Shima murmushin yayi yana miƙewa, cikin wani irin kallo da yake mata yake cewa, "ai dole ne in tuna tunda shi ne kaɗai hope ɗina da zai sada Ni da ke, ga shi za ki tafi ko sunan junan mu bamu kai ga sani ba ina zan yi sake?" Juya idanuwanta tayi tana miƙa masa wayanta tace, "Give me your number I'm in hurry." "Ok." Ya amshi wayan da sauri ya saka mata sannan ya kira nashi, yana shiga ya katse yana kallonta. At the same time, they smiled at each other, "suna na Shahed, I'm lives here." "Nice. I'm A'isha. A'isha Humaira, but you can call me Arab, I like the name more." Tayi maganar tana amsar wayanta Shi kuma yace, "Wow! Suna mai dadi, ashe shiyasa na ganki kyakykyawa? Duk A'isha dama haka suke kyawawa irin ki." Murmushi tayi masa sai dai bata ce komai ba kasancewar ganin kiran Tariq ya shigo wayanta, sai ta kalle shi tace, "zan tafi, see you next time." Sai ta ɗaga mishi hannu ta wuce bata jira cewarsa ba, a hanya ta amsa call ɗin While Shahed ya bi ta da kallo har ta ƙule masa, shafa kansa yayi yana murmushin farin ciki, sai ya koma ya zauna yana kurɓan drink ɗin da ta ajiye ta setting bakinta, yayinda ya tsira wa waje ɗaya idanu yana tunanin ta; still da walwala a kan face ɗinsa, har da sakin guntun murmushin sa sabida tuna wani abu. _In babu comments sosai, zaku sake jina shiru insha Allahu._ [26/07, 8:57 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA GOMA SHA SHIDA* _______________Gab da zata shiga room ɗinsu ta ji ana mata magana, tana juyawa ta ga babban Mutum a tsaye a bayanta Murmushi yayi mata yace, "Baby ɗan tsaya mana, if not worries I want to talk to you." "Why not." Ta ƙare maganar tana ƙare masa kallo; yayinda take karantar yanayin sa cikin hikima, a kayan jikinsa kaɗai ya tabbatar mata kalan sa, shiyasa ta saki fara'a a kan kyakkyawar fuskarta tana mishi kallon nan nata mai shiga jiki da ƙara nutso a shauƙin ta Tuni Alhajin ya sake ruɗewa saboda kallon ido ciki ido da suke yiwa juna, narkakkun idanuwanta ba ƙaramin sake tafiya da shi suka yi ba, tare da sake nutso a tafkin ƙaunarta da sha'awar ta, jiki na rawa ya zaro wayansa yana cewa, "I look like you're in a hurry, but if you don't mind, give me your phone number; We'll talk later." Bata ɓata lokaci ba ta karanta mishi Numban Sai yace, "ban yi tunanin kina da sauƙin kai haka ba, kin haɗu sosai, Allah yasa zan samu karɓuwa duk sanda na kira ki?" "Don't worry Alhaji, whatever you want you will find in my place." Tayi maganar tana cije leɓe cikin salo irin na gogaggun ƴan hannu, waɗanda lokaci ɗaya da salon su suke janye Mutum, har wani gantsaro ƙirji take yi tana karkaɗa mishi fararen manyan idanuwanta masu shegen kyau da ɗaukar hankali Shi kuwa tuni ya washe baki yana cewa, "yauwa na gode, ki sanar min da sunan ki bazan so in bar nan ba sai naji sunan ki duk da nima ina sauri ne, but Ni suna na Alhaji Sammani, what about You?" Before ta ba shi amsa ne Tariq ya fito daga ɗakin don ganin shiru bata shigo ba bayan tace mishi, "ga ta nan." Ya kasa haƙura shiyasa ya leƙo don ya duba ta, karaf idanuwansa suka faɗa a kansu, da sauri ya fito daga ɗakin daga shi sai gajeren wando da Singlet yana kiran sunanta Hakan yasa ta juya ta ganshi don bata ji buɗewar ƙofan nashi ba tunda ta juyawa ƙofan baya "Me kike yi a nan kuma? Waye wannan?" Yayi maganar da damuwa a kan fuskarsa yana sake kai duban sa kan Alhajin da ke tsaye wanda a ƙalla zai kai shekaru 50 a duniya, duk da hutu da jin dadi ya ɓoye shekarun nasa sai zallan ƙuruciya da ya bayyana a kan fuskarsa, baza ka taɓa cewa babba bane kuma ba shi da jikin girma sosai ɗan dai-dai ne Murmushi ne ya suɓuce a kan fuskarta, tana riƙe masa hannu ta saƙala nata cikin nashi, cikin salo da yaudara irin nata nan da nan ta kalallame murya tana narke mishi da cewa, "haba Sweetie mene ne kuma na kishi? Kaga fuskarka kuwa?" Sai ta shafa fuskar tana ɗan zizira mishi tsinin ƙumban ta cikin jan hankali tace, "wannan ɗan uwan Mamana ne ai, na zo shiga ciki ne muka haɗu muna gaisawa." Sai ta kalli Mutumin da cewa, "Kawu Sammani wannan shi ne wanda muka zo nan ɗin tare ai, kuma shi ne wanda zan aura." Da sauri Alhaji Sammani ya washe baki yana cewa, "Ah ah ashe shi ne surukin namu? To Masha Allah! Allah yasa za'a yi damu." Tuni Tariq kunya ya kama shi har yana sunne kai ƙasa, kana ya gaishe shi cikin girmamawa yana cewa, "Kawu ina wuni." "Lafiya lau Yaro, ban san tare kuke ba shine nake tambyar ta me ya kawo ta nan? Amma babu damuwa tunda ta gaya min akwai abun da ku ka zo yi." Sai ya kalli Arab ɗin ta kashe mishi ido; sai yayi murmushi yana cewa, "to bari in je nima sauri nake yi, ki gaishe da Maman naki kinji ko?" "To Kawu." Ta furta tana murmusawa A haka ya wuce ya bar su a wurin, sai suka shige cikin ɗakin su Suna shiga Tariq ya janyo ta kan jikinsa yana cewa, "wai da gaske Baby za ki aure ni? Ni ne wanda za ki aura ɗin?" Yaudararren murmushinta ta sakar mishi tana shafa fuskarsa idanunta cikin nasa, cike da kissa tace, "me zai hana Yallaɓoi? Idan muna tare ai zan iya auren ka, ka haɗa komai fa da Mace take burin mallakar ɗa namiji, baka da makusa ko kaɗan, don haka bani da dalilin ƙin amincewa da kai." Wannan kalaman nata ba ƙaramin faranta ranshi suka yi ba, nan ya matse ta a jikinsa yana cewa, "ban taɓa tunanin ina burge ki har haka ba Baby, naji dadin kalaman ki matuƙa, i love You Baby, har a cikin zuciyata ina jinki can ciki, i will never be happy every day idan na rasa ki, i love you so much and so much!"            Dariya tayi; sai ya haɗe bakinsu waje ɗaya ya soma tsotsa tamkar zai cinye ta, lokaci ɗaya suka soma cuɗa junansu cikin ƙwarewa da tsantsan sha'awar da ke addabar su. Sai da suka gama gamsar da junan su a falon sannan suka shiga wanka, a can ma sai da suka yi taɓe-taɓen su tamkar baza su rabu ba, ko kaɗan ba sa gajiya musamman ma Arab da abun ya zame mata jiki yanzu, mintuna kaɗan ba ta iya jurewa idan babu namiji a tare da ita Shi kuma tsantsan iya soyayyarta da ƙwarewanta na iya tafiyar da namiji hakan ne yasa Tariq ba ya iya gajiya da ita, bai taɓa cin mace sau ɗaya sau biyu ya sake na uku ba, hasali ma shi ba kasafai yake wannan harkan ba sai idan ta motsa mishi, amma kuma yanda yake jin Arab a zuciyarsa bazai taɓa iya haƙura da ita ba, kullum da zai samu damar su kasance tare yana so, ba ya gajiya da ita ko kaɗan, tana da daɗin da duk yawan mata zai yi wuya a samu kalanta da yawa, bare tana gyara jikinta sosai, duk wani abun da zai kawo mata ni'ima tana yin shi da hannunta, bata yarda da abubuwan siya barkatai ba, da kanta take haɗa kayanta ta sha iya shanta, shiyasa idan har kana tare da ita zai yi wuya baka manta kanka ka mutu a gogin ƙaunarta ba, duk wanda yayi tarayya da ita yana jinta daban ne matuƙa, bare ƴan bariki sun fi shiga rai fiye da matan gida, su kaɗai suka iya tafiyar da kowanne irin namiji babu ƙyama bare kunya, duk da ya san wace ce ita amma burin sa ace ta ba shi damar da zai mallake ta ya killace ta a cikin gidan sa, tana da kyan da ba kowanne namiji bane zai iya haƙura da ita duk da ya san wace ce ita, sai dai yayi fatan ta zama tashi shi kaɗai a nan gaba.        Abinci suka ci sannan suka kwanta manne da juna babu kaya a jikinsu. Washe gari kuma suka tashi suka shirya tsab, inda Tariq ya sanya ƙananun kaya da suka yi mishi kyau matuƙa, don dama shi mutum ne mai son gayu, ga shi kyakykyawa farin sa mai kyau mai ɗaukar hankali Ita kuma sai ta sanya bak'ar material da ya ɗauki beauty white skin ɗinta, doguwar riga ce tunda yawanci shi ta fi ƙauna, musamman idan an yi mata aljihu zaka ga ta saka wayanta duk karikitanta a ciki, babu ruwanta da jaka don bata cika using dashi ba. Ɗankwalin kayan ta ɗaura tayi ture kaga tsiya fuskarta da light make-up, sai ta jefa chewing gum a baki kamar yanda ya zame mata ɗabi'a, ga shi ta iya taunan chewing gum ɗin don nata salon na daban ne, da wannan taunan nata kaɗai take iya janyo hankalin namiji, duk wanda ya kalle ta sai ya sake. Takalma ta saka mai tsini sannan suka wuce zuwa mota A haka suka isa anguwan da ango yake. Yana yin parking sai ya kira Angon yace mishi, "ga su a waje." Babu jimawa ya fito kuwa, ganin su tare sai yace, "Ah ah Mutumina Ina ka samo wannan mai zafin haka? Daga zuwa garin mu har kayi kamu?" "No da abata na zo ai, tana masauki ne shi ne dalilin da yasa nace maka bazan kwana a nan ba ai." "Haba dai? But meyasa baka sanar min ba? Masha Allah amma kun dace matuƙa, kayi dacen kyakykyawa, sannu ko." Ya ƙare maganar yana kafawa Arab ɗin idanu Wacce ta ɗauke kai tunda tayi mishi duba ɗaya, tana taunan chewing gum cikin yanga tana latsa wayanta. Jin yayi magana sai ta ɗago itama ta kafa mishi idanuwanta da babu alamar kunya a cikin su, a buɗe suke kyar na zubin ƴan duniya; masu shiga jikin duk wanda ta zuba mishi su sabida kyawunsu. Murmushi tayi masa tace, "sannun mu, ya kake?" "Lafiya lau, kin zo lafiya?" Ya furta cikin washe baki "Alhamdulillah." Kaɗai ta furta ta sake ɗauke nata idanun tana shan ƙamshi irin nata na big girl wayayyu Tariq yace, "yauwa abun da yasa na kira ka ban shiga ciki ba; don ba na son kowa ya ganin min ita ne, ka san yanzu zamani ya sauya." Dariya yayi Angon yana cewa, "shege baaba, kuma haka ne fa, gwara kayi tattalin abun ka don wannan Allah ne ya kashe ya baka." Ya ƙare zancen yana sake kallon Arab don ba ƙaramin kyau tayi masa ba, ba hassada ba ya san abokin nasu ya kere ma sa'ar su idan ya mallaki wannan, ko shi ace za'a musanya mishi da ita wlh da gudu zai amshe ta, ta tafi da duk wani imanin sa, ko jirgawa da idanuwansa ba ya yi a kanta tsaban yanda ta haɗu ta ba shi sha'awa, ga ta yarinya sharaf ko a ido aka kalle ta za'a gane hakan Tariq ya katse mishi zancen zucin shi yana cewa, "ina son ka haɗa ta da Amaryan ka ne sai ta zauna a can wajen ta, hakan zai fi tunda bazai yiwu muna yawo tare ba mu ba zama zamu yi ba sabida harkan biki." "Eh wannan ba matsala bane ai, bari in shiga gida sai in kira Ƙanwata ta raka ta zuwa gidan, zan kira Lailan in sanar mata." "Yauwa nawan." Tariq yace hakan yana ba shi hannu suka kashe Shi kuma sai yayi dariya yana cewa, "bari in zo ina dawowa yanzu." Sai ya juya ya shiga gidan su. Babu jimawa ya dawo da wata ƙaramar yarinya da baza ta wuce 10years ba. "yauwa to ga ta nan zata kaita." Tariq yace, "Gidan da nisa ne ko mu je kawai a mota?" "Eh babu wani nisa, amma ku je a motan zan jira ka a nan, idan ka dawo sai mu shiga ciki." "Ok." Yarinyar baya ta shiga suka wuce bayan sun sake sallama da Arab. Babu nisa kuwa tunda tafiyar mintuna biyar ya kaisu kofar gidan, sai da yarinyar ta fita suka yi sallama tare da kissing ɗin juna before ta sauka ya ja motan ya tafi. Su kuma suka shiga gidan Akwai mutane sosai a gidan wanda zai tabbatar maka da sha'ani ake yi, ga mata nan sai tuƙa tuwon biki suke yi ana ta hayaniya. Yawanci basu kula da shigowar Arab ba tunda kowa harkan gaban shi yake yi, wasu kuma hankalin su ya je gare ta har suna ta kallon ta sabida farin ta ma kaɗai zai iya jawo hankalin ka gare ta bare kyanta Hakan ne yasa ta gaishe su suka wuce ciki Har ɗakin Maman Amaryan ta kaita suka gaisa, take ce mata, "in ji Yaya Umar ne yace a kawo ta wajen Aunty Laila." Maman tace, "ai tana gidan su Safara'u, maza ki kaita can Fatima." "To." Ta amsa tana miƙewa suka fice tare da Arab ɗin. Can ta kaita kamar yanda Mamansu tace mata, tana zuwa ta hangi Lailan cikin ƙawayenta tunda gidan su kaɗai ne, a nan suke taron su Suna zaune a falo sai hayaniya suke yi ana ta gardaman ɗaura girkin da ba'a yi ba. Shigowar su Arab da sallaman su duk sai hankalinsu ya raja'a a kanta; suka bi ta da kallo kamar sun samu t.v Arab babu ruwanta sai taunan chewing gum ɗinta take yi itama tana tsatstsare su da ido kamar yanda suke bin ta da kallon, a ranta tana ayyana wace ce Amaryan tana yatsina fuska; kasancewar yanda ta gansu ba wasu gogaggun ƴan mata bane sosai, kuma duk babu sa'an ta tunda sun girme ta sosai, zasu yi sa'annin Ummun su a yanda ta fahimta Fatiman ce ta yiwa Lailan bayani sannan ta tafi Itama Laila ta gane ta tunda yanzu suka gama waya da Umar ɗin yake sanar mata, har tana tsokanar Ƙawarta da tun jiya da suka haɗu da Tariq ta nuna tana sonshi, har sanar mishi tayi don ta kasa haƙura, amma bata samu fuska ba, take ce mata, "yanzu budurwan sa zata zo." Ita kuma budurwan mai suna Zubaida tace, "zasu ga yanda take ma; idan ta fi ta ne yake mata shan ƙamshi, kuma wlh zai ga wulaƙanci idan ta raina wayon ta." Ƴan ɗakin sai dariya suke yi Safara'u na cewa, "ke dai Zuby ban da cika baki sai ta zo muga idanu suna ƙwal-ƙwal don ta fi ki, kin san ƴan Zarian nan akwai iya zaɓen Mata, bare yanda Tariq ya haɗu ko a yanayin sa ma ba kowacce karikitai bane zai iya kulawa." Suna cikin musun ne kuma suka koma kan abincin da zasu girka kasancewar duk a cikin su an kasa samun masu tashi su ɗaura tukunya, kowa son jiki yayi mishi yawa duk da sun gama tanadar komai hura wuta kaɗai ya rage Ganin Arab ba ƙaramin shiga taitayin su suka yi ba, don wasu da zummar yin mata shaƙiyanci suke jira. But tun da suka ganta sai suka kama kansu gaba ɗaya don ba wanda zai nuna mata wani abun da ya fi nata, a komai ta kere musu ga kyawunta da ya ɗauke musu hankali, ko a suturan jikinta da yanda take walwali hutu ya zauna mata komai ya ji na surar jikinta; baza ka taɓa cewa ƴar gidan talakawa bane Laila CE kawai tayi ƙarfin halin yin mata magana, cikin fara'a tace mata, "ta zo ta zauna." Ita da kanta ta kawo mata drinks ta bata Babu abun da ta sha sai faman yatsina da take yi kamar ta ga kashi, sai ta ciro faskeken wayanta da ya tsole musu idanu sai dannawa take yi tun da ta ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya Babu mai bakin magana a cikinsu, tamkar ta kashe musu jiki, kuma babu wacce bata burge a cikinsu ba, daga masu satan kallonta sai waɗanda suka zuba mata idanun ƙura-ratan While Zubaida sai ta raina kanta sosai don ko kusa baza ta haɗa kanta da Arab ba, ta kerewa sa'ar ta Laila kuwa sai nan-nan take yi da ita tunda taga kalanta, nan da nan ta soma shige mata har tana tambayar sunan ta? Murmushi kawai Arab tayi tace mata, "Arab suna na." "Masha Allah suna mai daɗi, na samu ƙawa gaskiya, zan so ki zama ƙawata don Allah don kin yi min sosai." "Babu damuwa ai." Ta furta ba tare da ta kalle ta ba Da haka dai take ta janta da hira duk da ita Arab ɗin ta nuna sam basu a gabanta, maganar ma bai dame ta ba sai taga damar amsa mata, but haka nan take shige mata bata damu ba Su kansu ƙawayen sai suka soma neman hanyar da zasu shiga jikinta tunda kowa so yake yi ta zama ƙawarta Babu laifi ta saki jikinta musamman yanda suke ta shishshige mata. Amma dai a yanayin yanda take musu magana zai tabbatar da wulaƙanci da raini a tattare da ita, amma su sam ba sa ganin hakan, a tunanin su don ita ƴar masu kuɗi ne dole ta ja aji tunda class ɗinta ne, musamman da suke tunanin balarabiya ce tunda suka ji sunanta. Har aka gama abinci aka sawo mata ta kasa ci, ƙarshe Laila ta aika aka siyo mata tsire da yoghurt da kayan maƙulashe, ai kuwa ta amshe ta lanɗe kayan ta, da hayaniya ya cika ta komawa wani ɗaki inda Laila ta kaita tayi zaman ta A can sukai ta waya da Tariq har yake ce mata, "zai kawo mata kayan da zata saka a dinner, but zai shiga super market ɗin zai kira ta video call sai ta duba wanda yayi mata." Har yana cewa, "ko kuma ya zo ya ɗauke ta ta zaɓo?" But tace mishi, "a'a ba ta jin fita, idan ya je zasu yi videon kawai." Da haka suka yi sallama ta hau WhatsApp suka soma chart da Alhaji Bashir. Shiyasa hankalinta ya ɗauke bata sake fita cikin ƙawayen ba Duk da ɗakin da take a nan ake yiwa Amarya kwalliya in zata canza kaya, babu mai shigowa sai ita Amaryan da mai kwalliya, sai kuma Safara'u tunda gidan su ne, ita take shigowa ɗaukar wani abun jefi-jefi Can daga baya kuma sai Arab ta canza shawara ta kira Tariq ta sanar mishi, "ya zo ya ɗauke ta zuwa anjima sai su je ta siyo, daga can hotel zata shirya don ta gaji da zama a nan, baza ta iya kaiwa har dare ba." Dalilin da yasa ƙarfe biyar da rabi sai ga shi ya zo, ya kira ta ya sanar mata Bayan ta fito ne take sanar da Laila, "zata tafi." Laila kamar zata yi kuka tace mata, "baza ta zauna su tafi wajen partyn tare ba? Daga can ne za'a kaita sai su tafi tare ta kwanan mata." Murmushi Arab tayi tace, "kar ta damu zata dawo insha Allahu, but bata yi mata alƙawarin zata kwana ba amma zata kasance a wajen partyn, yanzu haka jiranta ake yi." Daga haka suka yi sallama ta rako ta har ƙofar gida ita da sauran ƙawayenta da suke ta shigewa Arab ɗin. A nan suka ga Tariq a cikin motan, sai suka ƙarisa har wajen suka gaishe sa. Sai da suka ga tafiyan su kafin suka dawo ciki suna tsegunta ma Zubaida, "Tariqa ne ya zo ɗaukar ta." Zubaida duk haushi ya cika ta shiyasa ta bar musu wurin don ta gaji da jin zancen yanda suke koɗa Arab da dacewar ta da Tariq ɗin. Tace, "su bari ba ta so." Amma sun ƙi bari sai shewa suke yi suna tsokanar ta.               ******             Arab kuwa tunda suka fita kai tsaye super market suka wuce, a can ta zaɓo rigan da zata saka a partyn, komai sabo ta siya wanda zata yi amfani dashi, daga nan suka wuce Hotel. Bai jima ba shi ya tafi tunda ana jiran shi, ya ce mata, "zai zo ya ɗauke ta idan an fara." Tunda ya tafi ta kwanta a saman kujera tana ta chart ɗinta, har ta Kira su Zahra suna ta hira cike da nishaɗi Sai bayan sallan isha'i sannan ta tashi tayi wanka ta haɗa sallan da ake bin ta ta rama A lokacin ne Tariq ya dawo yayi musu odan abinci suka ci sannan suka shirya Arab doguwar riga ne a jikinta light blue, Robber CE kuma tsukakkiya daga sama har ƙasa, hakan yasa ta kama ta ta fito mata da duk surar jikinta da dirinta, babu kwalliya a rigan sai dogon hannu da take dashi siriri, wuyan v ne da ita wadda bakin wuyan aka sanya bakin leshi baƙi, sai tayi using da baƙin takalma masu shegen tsini da igiyarsu, ƙaramin gyale kawai ta ɗaura baƙi shima; sai ta jefa jelan gyalen a gefe da gefe na kafaɗun ta, ana iya ganin kanannaɗaɗɗen gashin kanta irin na Fulani da aka yi mata kitso kuci-kuci ta gaban goshin ta. fuskarta da makeup mai ɗaukar hankali da ya ƙara fito da ainihin kyawun ta, bakin ya sha lipstick tamkar zai zubo, sai ta jefa chewing gum a bakinta Tunda ta fito sai Tariq ya kasa ɗauke idanuwansa a kanta, ta tafi dashi ainun don daƙyar yake iya haɗiye yawu, sai da ya ji jikinsa yayi wani irin yamm tsigan jikinsa ya tashi tsaye saboda ganin zubin halittan ta da ke kaɗawa, zuciyarsa har hautsinewa take yi yayinda jikinsa na faman rawa ya nufe ta da sauri ya haɗa ta da jikinsa, ɗaura hannu yayi a ƙugunta ya sake matse ta a jikinsa while suna kallon juna ido cikin ido cikin wani irin shauƙi na zallan sha'awa, hannunta ɗaya na a kan ƙirjinsa ta dafa shi. Cikin wani irin yanayi yace, "Baby bazan iya barin ki a haka ki fita ba saboda tsantsan kishin ki da nake yi, kinga yanda kika yi kyau kuwa? Da alamu ina barin ki kika fita zan iya rasa ki don naji hakan a jikina." Murmushi ta saki wanda har fararen haƙoranta da suke ƴan ƙananu masu ban sha'awa sai da suka fito, sai ta soma murza hannun nata da ke kan ƙirjinsa tana mishi yawo dashi a jikinsa, cikin salo take mishi wani irin kallo wanda ke ƙara tsulma shi a gogin tafkin ƙaunarta da sha'awarta, duk wucewar second ɗaya yana jin wani irin feelings ɗin da bazai iya misaltuwa ba, sauke hannunta tayi saman fuskarsa tana zagaye mishi ƙaramin sajen sa da faɗin, "mene ne aibun shiga na after all you know I didn't start today? Ina da tarin samarin da kai ka san cewa ba kai kaɗai bane, Ni allura ce a cikin ruwa har yanzu mai rabo bai ɗauka ba, kuma shigana ba shi ne zai sa ka rasa Ni ba..." Sai ta ja wani irin numfashi tana hura mishi iska a kan fuska, inda ta ɗaga kanta sosai tana kallon cikin idanuwansa cikin wannan shu'umin murmushin nata ta sake cewa, "abu ɗaya na sani, kai ne ka kawo Ni nan, don haka muna tare da kai a kodayaushe; I will never pay attention to anyone, ka kwantar da hankalinka sweetie ba na son ina ganin damuwa a kan fuskarka..." Bata ida maganar ba ya haɗe bakin su waje ɗaya yana mata wani irin tsotso tamkar zai cinye mata baki; sabida kawai bakin nata ne ya fi ɗaukar mishi hankali a time ɗin Duk yanda ta so ta ƙwace bakinta ta kasa haka ta bar shi yana ta sarrafa ta son ransa, ganin yana son wuce gona da iri ne sai tayi ƙarfin halin zare bakin nata tana kwantar da kanta a ƙirjinsa saboda baza ta iya tsayuwa da ƙafafuwanta ba a halin da ya saka ta Shi kansa ya kasa haƙura shafa ta kawai yake yi yana sake ƙwaƙume ta kamar wacce za'a ƙwace mishi ita, a hankali ya raɗa mata cikin wani irin hali da yake ciki yace, "Baby mu fasa zuwa don Allah, ina tsananin buƙatar ki bazan iya fita a haka ba." Zare jikinta tayi daga jikinsa tana shirin wucewa Sai ya damƙo hannunta yana kiran sunanta tamkar zai yi kuka Kallonsa tayi tana ɗan nazartan shi, sai kuma tace, "I don't run I am always with you, but I want to go to the party because I want to be there." "So how do I do it? After all I want to be with you? I can't go out like that." Guntun murmushi tayi tace, "idan Abokin ka kuma ya ji shiru fa? Kar ka manta ka zo nan ne don bikin sa sannan ka kasa halartan biki, and nima ka saka min rai Ina son zuwa wajen; because it will make me very happy." "Shikenan zan haƙura." Ya furta yana lashe bakin sa, yayinda ya janyo ta kusa da shi yana ƙara cewa, "but you promise me we will be together today without sleep." Fari tayi mishi da manyan idanuwanta tace, "kaima ka san hali na, Let's go time is running out." Bai barta haka nan ba sai da ya sake laluba ta duk ya ƙarisa lanɗe mata lipstick ɗin bakinta before suka fice ba tare da ta sake saka wani ba Sai a cikin mota ne ta sake shafa wani ta gyara kwalliyan nata. Yana ta mata ƙorafi but bata saurare shi ba har suka kai. Time ɗin ma an ɗauki mintoci da farawa. [28/07, 9:06 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝‍♀️* PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️*         _________________________ *BABI NA GOMA SHA BAKWAI* _______________Yana tsayar da motan kiran Umar ya shigo, nan yake tambayar sa, "har yanzu basu zo ba an fara?" Sai yace mishi, "ga su nan a waje, yanzu zasu shigo." A tare suka fito suka shiga Hole ɗin da ake taron. Lokacin party yayi zafi ana ta cashewa gunun sha'awa, su kansu wurin ya burge su don an shirya wajen ya haɗu But yawancin mutanen wurin sai da idanuwansu suka koma kan Arab domin ba ƙaramin burge su tayi ba, musamman yanda take wani karairaya cikin yanga da jan aji sai idanu ya koma kanta, ga rigan da ta sanya dashi da babu duk ɗaya Tariq kuma yana manne da ita don ganin idanun mutane yayi yawa a kansu, ya san bazai wuce Arab ce ta tsole musu idanu ba. Ai kuwa suna zama Abokan Ango suka soma mishi tsiya wai, "aina ya samo wannan tsaleliyar?" Dariya yayi yace, "da abata na zo ai, dama nace sai a nan zan gabatar muku da ita, ita ce wacce zan aura." Farin ciki suka taya shi kowannen su ya kasa ɗauke ido a kan Arab, zuciyarsu cike da sha'awarta da tsananin birge su da tayi, sai dai babu daman faɗin abun da ke ransu tunda ga gwaninta a tare da ita, sai dai sun yabe ta suna ta mishi murna Shi kuwa washe baki yake yi yana ƙara tarairayan abar sa. Komai tare suke yi cikin wayewa da nuna gogewan su Musamman ma Arab wacce take sake shan ƙamshi tana karairaya. Har wurin Amarya ta je suka gaisa sai kallonta ake yi don majority idanun mutanen wurin yana kanta tunda sun samu t.v, shigan jikinta ya sa da yawan maza susucewa, babu Macen da suke gani idan ba ita ba, duk ta rikita su, sai ma lokacin da ta shiga rawa tana takawa tunda tana son rawa sosai. Zo kuga yanda ake liƙa mata kuɗi ana shewa Sai da Tariq ya je ya janyo ta don kishi ya hana sa sukuni, musamman da ya ga ita kaɗai ake kallo, kowa idanuwansa na kanta, shiyasa ma yace, "gwara su tafi gaskiya." Haka suka koma masaukin su ba'a gama taron ba ma Arab kuwa dariya kawai take mishi, don abun nasa ma dariya yake bata, idan tayi ninyar kula wani a wajen bai isa ya hana ta ba, sai dai duk a cikinsu babu wanda yayi mata ne, don ita ba ta harka da ƙananan mutane sai dai manya, ta fi son inda zata samu maiƙo sosai ba ɗan gutsiri ka tsoma ba, ita babbar Mace ce ba kowa yake iya shiga rijiyar ta ba sai mai Rabo, ta fi ƙarfin ƙananan Yara. Amma ganin yana son wuce gona da iri sai wani ciccin magani yake yi don haushi da kishi ke ɗawainiya dashi, sai ta taka mishi burgi da cewa, "ka ga Malam, Ni fa ba matarka bace da zakana min irin haka, Ni budurwan ka ce baka da ƴancin hana Ni kula wani idan na so, but abun naka yana son wuce gona da iri don na sanar maka ba na son takura. Please don't do this to me or we will get into big trouble." Yanda ya ga ta tayar da jijiyar wuya ranta na son ɓaci sai ya koma bata haƙuri tamkar wani wawa, domin ko kusa ba ya ƙaunar ace sun ɓata har wani saɓani ya shiga tsakanin su, soyayyarta ta rigada tayi mishi zurfi a zuciya har ba ya son ganin ɓacin ranta. Dole ya lallaɓa ta daga nan kuma zance ya juya Kusan ranan basu runtsa ba sai gab da asuba. Ƙarshe sai goman safe suka tashi suka yi wanka sannan suka rama sallan da basu yi ba, bayan sun karya ne suka wuce gidan Firdausi don Arab tace mishi, "tana buƙatar zuwa kafin su koma." Ai kuwa tayi murnan ganinta don bata yi zaton zuwan nata ba, farin cikin ta ba ya misaltuwa, nan da nan ta tarbe su da lemuka da snacks sannan ta zauna suka gaisa sai kallon Tariq take Yi Arab da ta kula sai tace, "oh! Ban gabatar miki dashi ba, saurayina ne." "Allah Sarki!" Inji Firdausin tana murmusawa, duk da a ranta ta san cewa bazai wuce samarin ta irin waɗanda ta saba tarawa bane, don ta san halin ta, shiyasa tace, "yanzu tun daga gida ku ka zo nan gaishe Ni tare? Ko dai dashi ne za'a yi?" Ta ƙare maganar tana dariya Shima Tariq murmushi kaɗai yayi yana sunne kai ƙasa Ita kuwa Arab dayake ba kasafai take ɓoye gaskiya ba, abun da ke ranta shi ne a zahiri, shiyasa tace mata, "biki suka zo nan ɗin, kuma ba ta son ta tafi bata zo sun gaisa ba tunda Allah ya kawo ta garin." "Biki? Bikin wane?" Firdausin tayi tambayar da mamaki Tana kurɓan juice ta bata amsa da, "Abokin Tariq ne, shi ne na rako sa." Shiru Firdausi tayi bata iya cewa komai ba illa kallon Arab ɗin da take yi Ita kuwa tuni ta canza zancen nata ko a jikinta; ta mayar da hankalinta a kan Tariq tana ce mishi, "wai baza ka ci komai bane? Nan fa ba baƙon waje bane gidan Babbar Yayar mu ce, don haka ka saki jikinka ko Mijinta ne bazai hana ka abun da kayi ninya ba bare ita." Tariq murmushi kaɗai yayi yana jinjina kansa; tare da mamakin halin Arab, kowa dai bata bari ba, a ɗan zamantakewar su ya soma fahimtar halin ta, ko meye a ranta faɗi take yi, ba ta da shakku ko tsoro, iskancin ta a fili ne ba ta tsoron uban kowa Itama Firdausin bata ce komai ba jin abun da Arab ɗin tace, don ta san zata iya faɗan abun da ya fi haka tunda ba kunya ta cika ba, sai dai ranta babu daɗi sabida ganin Arab ɗin tare da saurayin ta wai sun zo biki, har yanzu baza su canza halin su ba, abun ya kai har Inna tana barin su zuwa wani waje da saurayi, "Allah Sarki Baba! Na san kana nan kana kwana da baƙin cikin Inna, Allah ya kawo maka mafita..." "Wai Aunty lafiyan ki ina magana kin yi shiru?" Arab ta katse mata zancen nata ganin hankalin ta ya ɗauke tana magana bata ji ta ba Da sauri ta dawo hayyacinta tana kallonta tace, "me kika ce ne?" "To ina kuwa za ki ji kin zauna kina saka tunani a ranki? Ga ciki a gaba amma baza ki bar zuciyarki ta huta ba, shiyasa ciwo ke kwantar da ke, Allah dai ya raba lafiya mu kam zamu tafi." "Tun yanzu Arab? Ki bari ku kai anjima ko Nafi'u zai dawo sai ku gaisa." "A'a Aunty, yanzu zamu tafi tunda ba wani abin zai bamu ba, ki gaishe shi dai in ya dawo." Tayi maganar tana tashi tare da rataya gyalenta Babu yanda ta iya tana ji tana gani suka yi mata sallama ta raka su har bakin ƙofa, sai da ta ga fitan su gidan before ta dawo ciki zuciyarta cike da fatan shiriya gare su.              A ranan su Arab suka dawo Zaria, don tace, "baza ta kwana ba ta gaji, kewar ƴan uwanta take yi." Dole suka dawo gida cike da niƙi-niƙin kaya da ya kashe mata kuɗi. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️            Su Malik duk yawon da suka yi don neman Arab but basu yi nasara ba, domin kuwa duk inda suka nausa sai sun nuna hoton ta ko zasu dace, duk da ita ba ɓoyayyiya bace don babu wanda bai san su ba a arean su, amma kasancewar ba wurin suka yi ba basu samu waɗanda suka santa ba, wasu kuma sun nuna sun santa sai dai basu san gidan su ba, sai dai a fuska sun santa har sukan ce, "suna yawan ganin su ta nan. Ko a waje kaza". Dole ba don sun so ba suka dawo gida tunda kwanan su biyu a Zaria, shiyasa suka koma Abuja da zummar bayan wani lokaci sai su sake komawa tunda gobe Monday ranan aiki ne Sai dai kuma baƙin cikin sa tunda suka koma gida Abban su yace, "za'a tsayar da maganar auren sa da Nawwara, dama ya gaji da ganin su haka nan basu yi aure ba, don haka ya yanke shawaran dukka zai yi musu aure har Zainab itama ta fito da mijin." Farin ciki wajen Nawwara ba a magana, kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, duk wanda ke tare da ita ya san tana murna da wannan albishir ɗin da Abba yayi musu Shi kuwa gogan ko kaɗan ba ya farin ciki, bai san dalili ba amma ko kusa ba ya son Auren yanzu, amma kuma babu yanda ya iya don ko a fuska bai nuna yanda za'a fahimta ba Tunda aka tsayar da rana nan da wata ɗaya sai Nawwara ta matsa mishi, "sai sun yi party." Babu yanda ya iya ya biye mata suka shirya gagarumin taro a gidan su Malik ɗin, kuma duk ƴan uwa sun zo komai an tafiyar dashi cikin girma da arziki Zainab ma an tsayar da ranan auren nata duk tare za'a yi, wani Ustaz ta samu zata aura don dama ya jima yana neman ta, tunda ta yiwa sauran Samarin ta maganar auren suka gudu don babu wanda yake fatan ta zama matar shi, Macen da suka gama sani a waje ita ce zasu aura? Haka suka guje ta kuwa kowa ya ƙi auren ta, don haka ta dawo ta lallaɓa Ustazun da ya nuna yana ƙaunarta ba tun yanzu ba amma kullum wulaƙancin yau daban na gobe daban, tayi mishi cin kashin duniya but ya ƙi haƙura da ita ya nace mata Shiyasa a sanda ta sanar mishi yayi farin ciki matuƙa, bai taɓa zaton zai iya samun ta ba don ya cire rai, sai dai zuciyarsa ne ta hana sa rabuwa da ita, sai ga shi Allah mai jin roƙon bawan sa ne ya tabbata addu'ar da yake yi ne Allah ya amsa mishi, cikin murna ya sanar da iyayen sa suka je nema masa auren ta, aka sanya rana wata ɗaya tare da na su Malik. To Allah yasa yana da abun yi don Malamin secondary ne kuma har da islamiyya yana dashi, yana samun kuɗi ta hanyoyi daban-daban a sana'ar sa don baza a ce mishi talaka ba, har gida yake ginawa Amma dai Zainab tayi kuka sosai tunda har ga Allah ita ba ta ƙaunar Ya Sheikh; wanda ɗalibansa suke kiran sa da haka. Amma kuma haka nan ta ɗauki shawaran ƙanwarta Ikhlas wanda tace mata, "ta fito dashi kawai tunda ta rasa wanda zata nuna, idan ba haka ba Abba bazai bar maganar ba tunda har yace mata ta fito da Miji." Shi matsalar sa ba ya magana biyu, idan zai yi abu yana yin shi ne a lokacin da ya yanke, kuma babu wanda ya isa ya sauya mishi zance, idan ma bata fito dashi ba zai iya zaɓo mata wani a ƴan uwa tunda ya sha yin zancen, "shi yana son auren zumunci." Shiyasa auren Malik da Nawwara ya fi komai faranta mishi. Ya so ace su ma su Zainab sun samu mai son su a cikin ƴan uwa, don wani lokacin har kwatance yake yi, "da ace wane zai nemi Zainab; ko wane da wane." Ire-iren maganar nan yana yawan yin shi To itama ta so hakan a yanzu, sai dai kuma ta san halin su duk a cikin wanda yake lissafowa babu wanda bai kama ta a club ba, duk sun san halin ta shiyasa suke yaɓa mata magana ba sa shiri da ita ko kaɗan, maganganun ɓatanci da musguna wa shi suke jifan ta dashi, ta san duk sanda ta sake ta faɗa gidan ɗaya daga ciki kashin ta ya bushe, gwara ta lallaɓa Ya Sheikh tunda ta san yana ƙaunarta, ga shi kyakykyawa ba shi da wani makusa, kawai dai Allah bai sa mata soyayyar shi a zuciyarta bane, amma gwara shi sau dubu a kan su tunda shi bai san tana da wannan halin ba Shiyasa tunda aka sa ranan suka soma gyara ita da Nawwara. Ita Nawwara nata mai sauƙi ne tunda wanda zai aure ta ya san wace ce ita sannan kuma tare suke iskancin su. Amma ita Zainab ita ce a tsaka mai wuya, tunda zata shiga gidan da ba'a san tana aikata zina ba, ya Sheikh bai taɓa sanin wannan mummunan halin nata ba, Nawwara ta kaita ta baro ga shi ita damuwar abun da zai biyo baya ya cika ta, tun ba'a je ko ina ba samarin ta sun guje ta ina ga tayi auren? Da wanne idon zata kalli Ya Sheikh ta sanar mishi ba ta tare da budurcin ta? Ganin ta damu sai Nawwara tayi ta kwantar mata da hankali tana nuna mata, "babu wani ganewar da zai yi, idan aka je aka ɗinke ta ta ci gaba da shan magungunan mata nan da nan zata haɗe, duk da lokaci ƙanƙani ne amma ya ishe su ta gyara kanta ciki da bai bazai taɓa ganewa ba, abu ɗaya kawai zata yi ta nisanci kowanne namiji daga yanzu, ita kanta itama baza ta tafi gidan Malik a haka ba sai ta matse ta koma budurwa, zai sha mamakin ta." Shiyasa suka shirya suka tafi asibiti aka ɗinke su kuwa. Suka soma shan magunguna kala-kala duk don su matse Wannan dalilin ne hankalin Zainab ya ɗan kwanta ta saki jikinta tunda tana ganin an sami solution ɗin matsalarta.       Please share and voted 🙏 28/July/ 2022. [29/07, 8:33 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍    *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️*    _________________________ *BABI NA GOMA SHA TAKWAS* _______________Tun dawowar Arab Alh. Bashir ya matsa mata, "sai ta zo ta same shi." Har a cikin ranta ba ta son tafiya sabida yace mata, "yana Lagos ne yanzu haka." Amma kuma yanda yayi mata alƙawarin kuɗi har wasu ya tura mata ta account shiyasa duk ta ruɗe ta amince mishi Already yanzu motanta dukkan su suke hawa, tare da su Zahra ake koya musu kuma duk Ibrahim yake koya musu, ko a sanda take Kaduna yana fita tare da su Zahran ya koya musu, da ta dawo kuma sai suke fita tare, yanzu ita hannunta ya faɗa duk da ba wai sosai ta iya ba, amma ta fi su Ummu since ita an daɗe da soma koya mata. Yanzu haka ta samu wurin ajiye motanta don ba ta ƙaunar ajiye ta a waje dama, yara suna taɓa mata duk da ba ta ganin su but idan ta zo ta duba sai taga alamun ana taɓa mata, shiyasa tayi tunanin kai ajiya gidan wata Amarya da aka yi a layin su, kasancewar duk layin babu wani gida mai Gate sai sabon gidan da aka yi, sun tare kusan sati ɗaya kenan, a gidan motan take kwana yanzu; tunda ta je ta tambayi Matar gidan, "zata riƙa kawo motan idan babu damuwa?" Ai kuwa ta amince mata don yarinya ce itama Amaryan baza ta wuce sa'ar Zahra ba, amma kuma kasancewar Arab ta shiga ranta lokaci ɗaya suka yi sabo da juna, har da su Zahran ma suna zuwa gidan suna gaisawa Kuma Mijin ba shi da matsala bai hana su ba tunda dai akwai filin ajiyewa, duk da yana jin raɗe-raɗin mutane da suke hana shi barin Matar shi tayi mu'amala da su Arab, ana yawan faɗa mishi, "karuwai ne kawai zasu ɓata mishi Mata ne, gwara ya raba su tun wuri." To shi dai bai hana su ba tunda suna gaisawar mutunci suna mishi kirki, ya dai ja kunnen Matarsa tayi hankali da su duk da yana ganin yanayin su da shigan da suke yi sam ba na masu tarbiyya bane, amma kuma wannan ba shi ne dalilin da zai hana taimaka musu ko ya hana matar shi mu'amala da su ba, idan za'a yi zaman lafiya shikenan, idan kuma abun zai juye a samu matsala sai ya ɗauki mataki Ita dai Arab tunda ya amince ya bar su suna ajiye mota hakan ya fi mata komai daɗi, idan zasu hau suna zuwa su ɗauka, kuma baza su mayar da ita gidan ba sai dare. Koda ta tashi tafiya Legos ba da motan tayi ninyar tafiya ba, zata bi jirgi kamar yanda Alh. Bashir ya turo mata kuɗin da zata biya, ai wannan abun ba ƙaramin faranta ran Arab yayi ba, wannan ce rana ta farko da zata hau jirgi a rayuwarta, farin cikin ta ba ya misaltuwa, tana ganin girman ta da matsayin ta ya ƙara ƙaruwa Dayake Inna ba ta hana su duk abin da suka yi ninya, bata damu ba da Arab ta sanar mata tafiyan, farin ciki ma tayi sabida jin zata koma wajen Alhajin nan, ta san zasu samu tagomashi ne shiyasa take murna, tunda duk abun da za'a ce kuɗi to magana ta ƙare, duk ita suka biyo ta koya musu son kuɗi da neman sa ko ta halin ya ya ne Ranan Alhamis suka yi sallama da Tariq don a can gidan shi ma ta wuni. Yana ta mata ƙorafin tafiyan duk da bai san me zata je yi ba, kuma ta ƙi sanar mishi tunda ba kasafai ta cika ƙarya ba, ƙiri-ƙiri zata bayyana wa Mutum, "ba hurumin ka bane." Idan kuma zata faɗa maka to kai tsaye zata sanar maka don babu ɓoye-ɓoye a tare da ita, sai idan ta so ne take iya yin ƙarya, amma komai nata ƙuraratan ne don ba ta shayin ko waye ne Shi kansa ya san halin ta a wannan ɗan ƙanƙanin lokacin da suka yi, shiyasa bai ja zancen ba tunda ta ƙi sanar mishi, kuma ya buƙaci, "zai bi ta can ɗin, su je tare." But tace, "a'a ba ta buƙata." Dole ya ƙyale ta suka sha love ɗinsu, sai dare ya mayar da ita gida Washe gari kuma ta wuce Kaduna daga can ta hau jirgi zuwa Legos. Ta sauka da la'asar; kamar yanda wancan suka zauna a hotel wannan ma a can ne masaukin su. Gaskiya ta ji daɗin zuwa Legos ɗin don ba kaɗan ba rayuwar can yayi mata daɗi, irin rayuwar da take so kenan, shiyasa kullum sai sun fita, ko basu fita da Alh. Bashir ba zata fita ita kaɗai, a haka ne yasa ta samu friends irin gogaggun ƴan duniya asalin karuwan can, don har club take zuwa a can ta haɗu da su, zamanta a can ɗin ya sa ta sake wayewa idanuwanta sun buɗe sosai. Shiyasa bata so suka bar can ɗin ba sabida zaman yayi mata daɗi, musamman yanda suke fita outing da Abokanan ta, ga samari ƴan duniya masu hannu da shuni da ta sake cin karo da su. Kwanan su goma sha biyar suka wuce Jigawa, duk da ta so komawa gida amma Alhajin ya hana ta komawa, sai da ta ci kuɗi sannan ta amince mishi suka tafi Koda suka je can ɗin ma kullum cikin hutawa suke da Alhaji tunda kullum yana gida suna manne da juna, sai yayi kwana biyu ma bai fita ba tunda meeting ya zo yi dama, kuma meeting ɗin ya ƙi ƙarewa ana ta cin lokaci A ɗan wannan satikan da Arab tayi cikin hutu da jin daɗi ba ƙaramin canzawa tayi ba, ta sake yin ƙiba ta murmure hutu ya zauna mata tunda tana jin daɗi sai abun da tace tana so, bata da damuwar komai kullum cikin hutu take, sai dai ta aika wa su Inna da kuɗaɗe su ma su dangwali arziƙi Babu abun da ya shalli Inna tunda burin ta ya cika, suna samun kuɗi sun fi ƙarfin komai, har kayan ɗakinta ta canza komai da komai, aka soma gyaran gidan ana ta canza filasta da penti, duka har su Ummu duk babu wanda ba ya taimakawa tunda su ma suna samun kuɗin samarin Baba dai nashi ido ne tunda yanzu ba sosai yake fita wajen suyan nashi ba sakamakon jikin sa babu wani daɗi, ba komai yake tsinana musu ba domin shi kansa sai Inna ta dafa ta ba shi ya kan samu Shiyasa kullum cikin gori take mishi, tayi ta tsiya bakin ta ba ya shiru ko kusa ba ta tausayin shi, wai, "kullum a haka zai ƙare zuciyarsa ta mutu yana gida ba ya tsinana musu komai sai dai ya ci, shi bai ji kunya ba ma ace Matarsa ce take ciyar dashi ko Yaranshi?" To ta fi ƙarfin shi ba ya da bakin ma mayar da martani tunda ya san halin ta, amma kuma yanzu dai yana ɗan lallaɓawa ya fita ko ya ya ne ya samo duk da nashi ba a bakin komai yake ba, idan ma ya bata kuɗin sai dai ta amsa ta ajiye ba dashi zasu yi girkin ba Ta kance, "uban me wannan kuɗin zai yi musu? Ta dai amsa don raba mugu da makami ibada ne; amma ba don wai zata yi amfani dashi ba." Wannan jaraba na Inna Harira kullum gaba yake yi kwata-kwata ba ta tausaya wa Baba, duk wani ciwo ma da yake yi baƙin cikinta dana Ƴaƴanta shi yake haifar mishi, tunda kullum cikin damuwa da tunani ba shi da sukuni, a haka kullum yake shiyasa yau ciwo gobe lafiya abun ya ci ƙarfin shi, asibitin ma ba ya iya zuwa tunda ba ya dashi sai dai ya je chemist ya siya magani, Inna bata taɓa damuwa da damuwar shi ba ita dai idan bai kawo ba ta dinga jaraba kenan har sai wunin ranan ta gushe, ƙarshe sai dai ya bar mata gidan Ko kuma tace, "ya ga don yaran suna samu ne shiyasa yake wani langaɓe wa a gida yana son dena fita nemowa, amma ada har dashi yake musu baƙin ciki da hassada yanzu kuma ya zo yana ci, ai da yayi zuciya ya barsu su ci kayan su kawai".               **********              Yau Arab ita kaɗai ce sabida Alh. Bashir ya fita tun safe, dayake yau ne zasu ƙaddamar da meeting ɗinsu na ƙarshe wanda suke sa ran samun matsaya a kan kasuwancin nasu da suke ƙoƙarin haɓaka shi, zuwa gobe ko jibi kuma sai su wuce Arab kaɗaicin ya ishe ta shiyasa ta tashi ta zura dogon Hijab Robber purple a saman kayan jikinta, dayake kayan shan iska ne gajeren wando blue Black, sai vest pink color mai taushi da siraran hannu. Komai na jikinta ana gani duk da ta saka Hijab ɗin; don da shi da babu duk ɗaya ne, albarkatun jikinta tamkar a waje suke don yanda suke kaɗawa dole ne duk wani namiji mai lafiya ya ruɗe, but ita babu ruwanta haka ta fice tana kaɗa jiki cikin tafiyanta na yanga da ɗaukar hankali, duk inda ta wuce kuwa kallonta ake yi don majority mutanen da zata haɗu da su a hotel ɗin idanuwansu yana kanta. Ita kuwa hankalinta yayi gaba wajen waya da Bestyn ta, sai dariya take yi cikin nishaɗi har tana sanar mishi, "yanzu ne ma ta fito zata ɗan sha iska don ta gaji." Yayi dariya yace, "ai na faɗa miki kin samu duniya yanzu babban yarinya, yanzu sai hutu da jin daɗi kike ba ki da wata matsala, Ni na ƙosa ma ki dawo don nayi kewar ki sosai, yaushe ne za ki dawo don Allah?" Ya ƙare maganar cikin narke murya da salon jan hankali Dayake already ta fice daga hotel ɗin, ta fita zuwa bakin titi tana kallon mutane sai ta jingina da wata mota da ta gani, a nan ta tsaya tana ci gaba da waya dashi suna ta dariya da nishaɗi; wanda hakan ya ɗauke mata hankali har tana hayewa saman motan Ashe na wani Alhaji ne yana ciki a zaune, kasancewar wurin akwai irin manya-manyan shagunan nan; yana tare da Matarsa ta tsallaka siyayya, hawa motan da tayi ne ya ja hankalinsa gare ta, sai ya fito daga cikin motan da ninyar yin mata masifa, amma yana yin tozali da ita ta ja hankalinsa, zuciyarsa nan da nan ta kwaɗaita da ita tunda shima ɗan hannu ne, har wani haɗiye yawu yake yi tsaban jaraba. Wajen ta ya nufa yayi mata sallama Dalilin da yasa ta katse kiran tana mayar da hankalinta a kanshi tare da kallonsa sama da ƙasa       Shi kuma yayi mata murmushi yace, "sannu ƴan mata." Murmushin itama ta maida mishi tana dirowa daga kan motan tare da amsawa Yace, "But here you are or you will pass?" "No, Ina nan ne. I am in this hotel." Abun da yake son ji kenan shiyasa nan da nan ya washe baki yana cewa, ""If you don't mind, give me your phone number. I often come here; or we will meet together." Dariya tayi mai jan hankali, sai ta ɗage kafaɗa tace, "ok fine." Daga nan ta soma karanto mishi Numban Ashe fitowar matar shi tana hango su, kuma ita ga ta akwai shegen kishi, tunda ta hangi Arab nan da nan hankalinta ya tashi zargi ya ɗarsu a zuciyarta, tsaban kishi ya ci ranta tana zuwa wajen ta zubar da kayan hannunta bata yi wata-wata ba ta cakumi wuyan Arab Basu an kare da zuwan nata ba shiyasa sai ganin ta suka yi Kafin Arab ta farga Matar ta wanka mata mari tana cewa, "dan kutmar ubanki me ya haɗa ki da Mijina? Dan ubanki nace mai ya haɗa ki da Mijina iyee karuwan Banza?" Da sauri Alhajin ya soma ƙoƙarin fincike hannunta yana cewa, "Ke.. ke Lubna mene ne haka? Ba ki da hankali ne?" Ita kuwa Arab tunda taga Matar ta sake ta sai itama ta wanke ta da marin cikin zafin nama, tare da cewa, "uban ki ne ya haɗa Ni da mijinki dan durun uwar ki." "Ni kika mara? Ni?" Matar ta furta cikin tsantsan mamakin Arab ɗin, musamman yanda ta ganta ƙaramar yarinya a kanta, but har ta cire hannu ta mare ta bayan ita tayi mata laifi Hankalin Alhajin ya tashi don ya san halin matar shi, shiyasa yayi saurin shiga tsakani yana jan hannunta da cewa, "dama kin saba ja min magana Lubna, yanzu ma a nan sai kin kwance min zani a kasuwa? Ki wuce muje da Allah." "Wlh bazan tafi ba, kana ganin yanda ta mare Ni kake cewa in tafi? Tunda ba ka da gaskiya mugu azzalumi ai dole ka ce in tafi." Sai ta fashe da kuka tana ƙwace hannunta Ita kuwa Arab tana tsaye a wurin don ko gezau bata yi ba, kuma ba ta shakkar duk abun da zai faru, tana gani yanda mijin yake lallaɓa matar don su tafi amma ina ta kafe sai ta ci uban Arab; shi kuma ya hana ta ya shiga tsakani Cikin baƙin ciki ta nuna Arab da yatsa tace, "wlh tallahi sai na ɗauki babban mataki a kanki karuwan Banza karuwan hofi, sai na nuna miki Mijina ya fi ƙarfin ki dan uwar ki, shegiya asararriya wacce iyayen ta suka tsine mata suka ce ta je zata gani." Dariya Arab tayi ko a jikinta tace, "ok haka kika ce ko? To nima zan nuna miki Ni cikakkiyar karuwa ce mai lasisi, Mijin naki zan raba ki dashi har abada, kuma Ni da mijinki sai dai ki haɗiye zuciya ki mutu babu mai raba Ni dashi, Ni Arab zan nuna miki tantiranci na." Ai kuwa ba ƙaramin fusata matar tayi ba, duk da yawan jama'ar da suke wurin an taru haka ta cire gyalenta ta ɗaure tana ta ƙunduma wa Arab zagi, mummunan zagi kuwa wanda kare bazai ci ba, ga shi ta kasa ƙwace wa a hannun Mijin, tace, "wlh sai ta ga bayan Arab, sai ta kashe ta idan har bata rabu dashi ba." Daƙyar Mijin ya samu ya saka ta a cikin motan duk ranshi ya jagule, jikinsa ɓari kawai yake yi don sosai yake jin tsoron matar tashi, ba ya ƙaunar fitinan ta ko kaɗan Arab kuwa sai dariya take mata tana ƙara mata kayan takaici, kuma ta ƙi tafiya a wurin sai da taga sun tafi, sannan ta taɓe baki ta juya zuwa wani shago ko a jikinta, ko kallon ma mutanen da sukai caa a wurin kamar sun samu t.v sai hayaniya suke yi; bata bi ta kansu ba ta wuce ta siya ice-cream ta koma room ɗinsu. Baƙin cikinta ɗaya ba ita ta amshi numbansa ba; da tun a yanzu ta soma kiransa ta maida mata da martani, but tana nan tana jiran duk lokacin da ya kira ta wlh sai ta koya ma Matar nan hankali, sai ta raba ta da Mijin har abada, sa'arta kawai kar ya soma ya kira ta, but idan ko ba haka ba sai ta shayar da matar nan mamaki, sai ta nuna mata ita karuwa ce; mai lasisi kuwa Tana gama shan ice-cream ɗinta tayi ɗai-ɗai a kan gado ta shari barcin ta Sai da Alh. Bashir ya dawo sannan ya tashe ta, da jaraban sa ya tashe ta daƙyar ya bari tayi wanka sannan suka tsulmiya gogin soyayya. Sai da suka gamsar da junansu son ransu sannan suka sake yin wankan suka shirya, abinci suka ci daga can ma wasan ya juye sai romance ɗin juna suke yi tamkar zasu haɗiye kansu, kwata-kwata ba sa gajiya musamman Alhaji da shi sam ba ya ƙoshi da Arab, ita dai tana biye mishi ne kawai don kuɗinsa don ba wani daɗin azo a gani take ji ba, sai ta tuna da Tariq wanda shi kaɗai ne idan zasu yi sex take iya gamsuwa ɗari bisa ɗari, ya iya tafiyar da Mace ba kaɗan ba, har kewarsa tayi ta ƙosa su koma Dukkan su babu wanda yayi Sallah a cikin su sai bayan sallan isha'i sannan suka haɗa daga la'asar har isha'i suka rama. Sannan suka ƙara mannewa da juna, sai da suka raba daren sannan suka yi barci Washe gari kuma suka fita suka yi siyayya sannan suka shirya tsab, daga nan suka rabu Arab tayo gida, shima ya wuce Bauchi inda yake. [30/07, 10:28 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA GOMA SHA TARA* _______________Ana ta shirye-shiryen bikin su Malik, sai dai shi har yanzu hankalin sa ya ƙi kwanciya, tunanin Arab tamkar zai kashe shi, ya kasa cire ta a ransa ya kasa haƙura da ita Tun Sinior yana kwantar mishi da hankali yana faɗa mishi, "ya manta da ita, ya dena saka damuwa a ransa tunda ba lallai ya ganta ba, sannan ko ya ganta bai zama dole ya same ta ba, ta iya yiwuwa ma Matar aure ce ko kuma ita ta ƙi shi." But bai taɓa yarda da zancen sa ba, ya kan ce, "shi ya fi ƙarfin Mace ta ƙi shi, kuma ko Matar aure ce wlh bazai bar ta ba, sai dai abu biyu ya faru, ko Mijin ya sake ta ko kuma su zama Mijin ta su biyu, don dole ne sai yayi rayuwa da ita." Dariya kawai Sinior yake yi idan yana jin wannan zancen, sai yace, "wlh kana bani dariya Malik, an gaya maka kowa irin ka ne ɗan iska? Yanzu kana nufin idan har ba ka same ta ba zaku yi rayuwar bariki a ɓoye? Cab ɗijam.. idan kuma ita ba halin ta bane fa?" "Uhm ko ba halinta bane zata fara a kaina, zata san daɗin irin wannan rayuwar duk idan ta haɗu dani, wlh ko ta rabu da mijin ko kuma dole ne sai ta bi zaɓi na, don duk yanda zan yi sai na yi ta zama tawa, bazan taɓa barin ta ba. Hmm kaima ka san hali na Sinior ka san me zan iya aikatawa." Kafaɗu ya ɗage alamun, "he can see".               Kasancewar bikin na gogaggun ƴan duniya ne; kuma ga kuɗi a ƙasa, shiyasa aka yi wadaƙa kuma aka zubar da su, an yi ƙarya ba Ni da ƙarya ba, almost two weeks ana shagulgulan biki, kuma kowacce rana akwai event ɗin da ake aiwatarwa. A ranan Asabar kuma aka ɗaura auren sannan aka yi dinner bayan an kai kowacce gidan Mijinta Duk ustazancin Ya Sheikh babu yanda ya iya sai da ya halarta duk wani events da aka yi, tunda dai ba shi ya shirya ba daga gidan Amarya ne, and kuma babu daman ƙin zuwa sabida ba ya son ɓacin ranta Bayan an gama daga can ne kowacce aka mayar da ita gidan ta. Babu wacce aka kwana mata kowacce daga ita sai Angon ta Fannin su Malik sun sha soyayyar su tamkar zasu cinye juna. Musamman ma Nawwara da farin cikin wannan rana daban ne a wurin ta, yau Allah ya cika mata burinta ta mallaki Malik ɗinta a matsayin Mijinta, ya zama nata ita kaɗai kamar yanda take fatar ya kasance. Babu ɗaga ƙafa haka suka kasance a wannan ranan Shi kansa Malik ya kasa gane ko canza mishi ita aka yi, sabida yanda ya ji ta zam-zam ga daɗin da ta ƙara sakamakon gyaran da suka yi, ta koma mishi tamkar yau ya soma ɓare ta a leda shiyasa yayi farin ciki walwalan sa ma daban ne, har kasa haƙura da ita yayi haka suka kwana kamar zasu cinye juna.               Fannin Zainab ma abun da ya faru kenan. Ya Sheikh bai taɓa sanin wata ɗiya mace ba a rayuwarsa, sannan babu wacce ya taɓa so face Zainab ɗin, hakan yasa bai gane komai ba tunda dai ya ji ta daƙyar yake shiga, bai ga wani bambanci da ya saɓa da na budurwa mai budurci ba. Sai dai abu ɗaya yanda ya sha mamakin Zainab, kasancewar ta gogaggiya a wannan fannin kuma ta san Maza shiyasa ta nuna mishi ƙwarewar ta ba tare da ita kanta ta san tayi ba, domin daɗin da ke ratsa ta musamman yanda ta ji Ya Sheikh daban da sauran Mazan nata, ga shi ya iya tafiyar da Mace, hakan yasa itama ta nuna ƙwarewanta ko kaɗan babu kunya irin ta Amare bare nuna raki da suke yi. Hakan ne yasa mishi wasi-wasi da shakkar ta. Har daga baya yake tambayar ta, "shin ko ta taɓa yi ne wai ya ganta haka da son abun? Shi yayi mamakinta tunda ya san cewa duk wata budurwa dole ta guji daren farkon ta na aure." Jin wannan zancen sai da gaban Zainab ya faɗi, ta rasa mai zata ce mishi ma duk alamun rashin gaskiya ya nuna a bayyane da ita Hakan ne ya sake ɗarsa mishi zargin ta, cikin yanayin damuwa yace, "Zainab don Allah ki faɗa min gaskiya, taya kika iya wannan abun bayan ke ba ki taɓa aure ba? Alamu ya nuna kin saba tunda har kika nuna zaƙewar ki kuma babu tsoro na a tare da ke." Cikin dabaran da ya faɗo mata a nan take ta sakar mishi kuka, babu shiri ta tashi da sauri ta nufi Falo Sai ya bi ta cikin tashin hankali yana kiranta. A zaune ya ganta a saman couch tana ta kuka, sai ya zauna gefen ta cikin yanayin damuwa da tsantsan ruɗewa yake cewa, "dan Allah Zainab ki dena wannan kukan naki yana ɗaga min hankali, ki sanar da ni abun da ke faruwa da ke kar zuciyata ta buga Please." Sai ya sanya hannu ya ɗago ta zuwa jikinsa yana ƙoƙarin share mata hawayen Amma sai ta buge hannunsa tana shirin tashi still ta ƙi dena kukan Janyo ta yayi sosai ya hana ta damar ƙwace wa, cikin lallami yake sake bata haƙuri tare da tambayarta abun da yayi mata take kuka? Cikin kissa da nuna tsantsan shagwaɓarta take cewa, "ba kai ne ba kake zargi na don kawai na nuna maka irin soyayyar da nake maka gami da farin cikin da nake ciki, har kake iya kallo na ka furta min wannan zancen, nufin ka kenan ina bin Maza a waje? Kenan ba ka yarda ma ina tare da mutunci na ba? To wlh bazan taɓa zama da kai ba dole sai ka sake Ni, bazan iya zama da wanda yake zargi na ba, tun ma ba'a yi nisa ba kenan dama halarcin da zaka yi min kenan ko?" Sai ta fashe da wani sabon kukan tana sake narke wa a jikinsa Duk ta gama kashe masa jiki; tare da ƙara dulmiyar dashi cikin tsantsan tashin hankali gami da ruɗu da jin zantukan ta, nan da nan ya gama ruɗewa ya hau rarrashin ta yana ce mata, "ba haka yake nufi ba, amma tayi haƙuri ta gafarce shi wlh bazai sake ba." Haka ya dinga rarrashin ta har yana duƙa mata, don babu abun da ya fi firgita shi irin cewa da tayi, "zata tafi ta bar shi sai ya sake ta." Daƙyar ya samu ta haƙura tace, "zata zauna. Amma duk ranan da ya sake gaya mata makamancin irin wannan maganar wlh sai ta bar gidan sa, dama ta ɓoye mishi irin ƙaunar da take mishi ne sai a wannan ranan zata bayyana mishi, amma kuma sai ga shi yana zargin ta don kawai ta ba shi haɗin kai wajen jiyar da shi daɗi, to idan ba ta ƙaunar shi taya zata amince ta aure shi? Duk samarinta ace shi kaɗai ne zata iya nuna wa wanda zata aura; duk wannan ba so bane?" "Wlh na yarda Sahiba, na yarda kina matuƙar ƙaunata, yau na gane haka, tunda Ni kaina ina ta mamakin ya aka yi kika zaɓe ni a cikin dubu duk da irin halin da kike nuna min? ba ki taɓa bani dama ko na minti biyar ne mun yi magana da ke ba, kullum cikin hantara na kike yi, Ni kuma na ƙi yin zuciya na kafe sai ke, duk da na san cewa kin fi ƙarfi na amma gani nake yi kamar wata rana za ki zama rabo na, ashe hakan ne kuwa tunda ga shi Allah ya nuna min wannan ranan, wlh Zainab ban taɓa tunanin kina so na ba sai yanzu, ashe duk da gangar kike yi min haka?" Dariya tayi masa tana sake shigewa jikinsa tare da ɓoye fuskarta, cikin nuna kunyarta tace, "Ina sonka Ya Sheikh, sai dai na kasa nuna maka hakan ne saboda in gano irin soyayyar da kake min, amma duk abin da nake maka wlh da sani na nayi maka, kuma ga shi yanzu na goge maka tantamar ka, na zama taka yanzu." "Godiya ga Allah maɗaukakin Sarki." Ya furta cike da farin ciki yana sake rungume ta, "na ji daɗin wannan rana Sahibata, bazan taɓa manta wa da wannan karamcin da kikai min ba, kuma zan nuna miki Ni masoyin ki ne na gaskiya, Allah ya bar mu tare." "Amin." Ta furta tana dariya, yayinda cikin zuciyarta farin ciki da hamdala take yiwa Allah da ya rufa mata asiri, har ga Allah a yau ne take jin zuciyarta tayi sanyi da tsanar Ya Sheikh, har tana jin cewa zata iya zama dashi har ƙarshen rayuwarta, kuma baza ta sake aikata makamanciyar rayuwar da tayi a baya ba, haƙiƙa Allah na sonta tunda ya rufa mata asiri ya bata Ya Sheikh a matsayin Mijinta, don haka dole ne ta gode masa, ba don haka ba ta san da tuni a yanzu suna tsiya da mijin ko kuma ya sake ta a kan abun da tayi na rashin zuwa da budurcinta, gwara da Allah yasa bata auri sauran Samarin da take bi ba; Allah ya musanya mata da Ya Sheikh, ga shi a yau kaɗai ya shayar da ita farin cikin da bata taɓa sanin zata samu daga hannun sa ba, har ta fi jin gamsuwa ɗari bisa ɗari fiye da sauran ranakun da ta aikata sauran masha'an ta, kuma daɗin da ta ji ya fi na kowanne namiji da ta sani Shi kuwa Ya Sheikh tunda ya ga ya shawo kanta sai ya ja ta suka koma ciki, sai da suka ƙara shayar da junan su daɗi before suka kwanta rungume da juna cikin tsantsan farin ciki a ransu.                    Bayan kwana biyu da auren ne su Malik suka wuce New York, a can ne zasu yi Honeymoon ɗinsu, daga can kuma zasu sake zaga wasu ƙasashen, basu da matsalar komai tunda a Campanin Mahaifin Malik suke aiki. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️            Yau su Arab suna zaune a tsakar gidan su, Inna ta fita zuwa PZ canzo fridge; tunda wanda suka siya yayi ƙarami shi ne Arab ta bada kuɗi tace, "a canza babba zai fi." Su uku ne kaɗai a gidan a yanzu, Zahra da Arab suna bakin bishiyar gidansu suna hira. While Ummu tana kwance a ɗaki barci ya sure ta tun sanda suka dawo school ita da Zahrah. Labari suke yi a kan saurayin Zahran; Haidar wanda yake ƙasar waje yana karatu, ita Zahra abun ya soma damunta kasancewar tayi masa alƙawarin baza ta taɓa bari wani ya kusance ta ba bayan shi, ga shi tunda ya tafi ya ƙi dawowa, kuma yanzu lamarin yana son ya zame mata matsala tunda a yanzu dai tana matuƙar buƙatar namiji tunda ya ɗanɗana mata abun da ake ji, duk da tana rage zafi da samarin ta amma ta kasa ba wa kowa damar da zai kusance ta idan ba Haidar ba Shiyasa yanzu Zahra tace, "gaskiya ita ta gaji wlh aure take so, tayi-tayi Haidar ya dawo suyi aure amma ya ƙi, ya zata yi dashi ne?" Arab kuwa dariya tayi tana cewa, "ke wlh banza ce, meye na wani jiran Haidar ya tafi can ya manta da ke? Ke kin san me yake yi ne a can? Ni ban taɓa ma tunanin ke sakarya bace idan ba yau ba." "Ni kike kira sakarya?" Zahran ta furta tana ban ka mata harara "To idan ba sakarya ba mece ce?" Arab ɗin ta sake cewa tana ware mata idanu da dariyan shaƙiyanci, "kinga fa, Ni ba na tunanin wannan Haidar ɗin zai iya auren ki wlh, kwata-kwata zubin shi na ƴan yaudara ne, zai ci moriyar ganga ne kawai ya yasar da kauren ta, to ban da abun ki ma meye na tunanin aure yanzu? Na san dai abun da kike buƙata bai wuce ɗa namiji ba, kuma kina da su sai wanda kika zaɓa ya jiyar da ke daɗi. But you are still talking about Haidar and you are not sure if he will marry you or not." "Hmm Arab kenan! Baza ki gane bane, wlh ina matuƙar ƙaunar Haidar, idan ba shi ba ba na jin zan iya auren wani namiji a duniyar nan, sai dai Mutum ɗaya da nake tunanin a cikin su idan na same su tabbas na more, har ga Allah har a cikin zuciyata ina son in Yi rayuwar aure da su." Arab tace, "Ok kina ma da wani bayan Haidar ɗin kika zauna kina jiran sa? Kin san fa irin gidan Sarautar nan wlh ba lallai su amince da ke ba, ko shi yace zai aure ki iyayen sa baza su yarda ba, tunda zasu ce za'a ɓata musu gida ne, bare kin san yanda muka yi tambari a anguwan nan, ana zuwa za'a basu shedar duk wani halayyar mu, shawaran da zan ba ki kawai ki bar shi ki nemi ɗayan; don na san zai ɗan fi gwaɓi-gwaɓi a kan Haidar." "That's what you think, bayan shi wannan ɗin ban ma san inda zan same shi ba, ban san komai a kanshi ba, maganar ma da nake miki bai ma san ina yi ba." Sakato Arab tayi tana kallonta, sai kuma ta kawar da kanta tana ƙoƙarin soka earpis a wayanta tare da cewa, "To wannan kuma daga ina kika samo shi?" Sai da ta buga tagumi kamar zata yi kuka tace, "ina wannan Likitan Abokin Nafi'u Mijin Aunty Firdausi? wanda muka je asibiti muka haɗu da shi a Office ɗin Doctorn nan?" Da sauri Arab ta ɗago kanta tana kallonta, yayinda ta furta, "wai shi kike so?" "Eh. Shi zuciyata ta mutu a ƙaunar shi, Ni kaina wlh mamaki nake yi sabida yanda na kasa manta fuskarsa, abun da nake ji a kan Haidar haka shima nake ji a kanshi, tunani na da burina kawai in ganshi a yanzu, abun farin cikin kuma sunan su ɗaya..." Dariyan da Arab ɗin ta kwashe dashi; shi ya tsayar da ita daga zancen da take yi. Yayinda ta furta, "haukan Banza, wai wannan Mutumin kike so Aunty Zahra? Ki rasa wanda za ki so sai shi? Amma gaskiya zuciyar ki bata yi miki adalci ba, shiyasa kwata-kwata na tsani soyayya don na san abun hauka yake zama." Sai ta ƙare maganar tana dariya sosai; yayinda ta sanya earpis a kunnenta tana ƙoƙarin latsa wayan da cewa, "to yanzu aina za ki ganshi kenan?" Shiru Zahra tayi mata tayi banza da ita   Sai ta ɗago ta kalle ta tana cewa, "ya na ji kin yi shiru?" "To ba dole in Yi shiru ba kin mayar da zance na wasa? I'm telling you my problem but ke kamar bai dame ki ba." Murmushi tayi tare da zare guda ɗaya earpis ɗin a kunnenta tana cewa, "to na ji, na dena dariyan, amma maganar taki ce akwai ban dariya da kayan haushi, wannan mutumin wlh ba shi da mutunci ko da ganin shi, sannan ma kin san inda muka haɗu dashi taya kike tunanin zai so ki?" "Leave this conversation alone; tunda dukkan mu bamu san shi ba." Dariyan rainin hankali Arab ta saki tana cewa, "ke ce ba ki san shi ba, amma Ni kallo ɗaya na gane waye shi, ba kalan Mazan nan da kike tunanin za ki samu cikin sauƙi bane, ban ba ki labari ba ma? Zuwana Abuja da nayi sai da muka haɗu a wani ShopRite." Zahra cike da ɗoki tace, "haba dai? Don Allah da gaske?" "Zan miki ƙarya ne?" Arab ɗin tafaɗa tana hararanta Kafin Zahran tayi magana; suka ji sallaman Yaro yana ta kwaɗawa ko jingirta wa ba yayi Hakan ne yasa Arab ta ƙunduma mishi zagi tana cewa, "dan uwarka ba kaga mutane bane kake mana ihu aka? Uwar me ka zo yi?" "Wani ne ya aiko Ni a waje, wai ana kiran Arab." Arab tace, "wane ne? Kuma a me ya zo?" "A mota ne." "Ok. Je ka kace ga Ni nan." "To." Ya amsa da sauri yana juyawa "Bari in je in duba waye ne, duk da ban yi da wani zai zo ba. Ina zuwa." Sai ta ajiye wayan tana miƙewa tare da zura slippers ɗinta da ke wurin, ta zari mayafin Zahra da ke jikinta ta rufe kanta kasancewar babu komai, daga ita sai doguwar riga Robber brown color; ta fice ta nufi waje. Tana fita ta hangi wata dalleliyar mota har wani sheƙi take yi tsaban kyawu da sabunta, da kallo ta bi motan tamkar idanuwanta zasu faɗo, zuciyarta tana me aiyana, "waye wannan?" Nan da nan sai ta sauya tafiya ta nufi motan kanta tsaye babu ko tsoro bare tunanin wani abu, yayinda ko ƙyafta idanu ba ta yi wajen kallon motan da santin da take yi har da haɗiyar yawu. [01/08, 8:53 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA ASHIRIN* _______________Koda ta isa wurin motan sai da ta gama zagaye ta har tana leƙe-leƙe, sai dai ba ta ganin kowa sai na ciki ne zai ganta Tana cikin dube-duben ne wani matashin saurayi ya fito daga ciki yana murmusawa tare da yin mata sallama Ta amsa tana kallonsa tare da ƙare masa kallo, "lafiya Malam? Kai ne kake kira na?" Ta furta da mamaki sabida ganin yanayin saurayin kuma a cikin wannan motan, wacce a ƙiyasinta duk da bata gama sanin ire-iren waɗannan tsadaddun motocin ba; amma tabbas wannan zata iya kai wa miliyan takwas ko goma Saurayin ne ya sake magana sabida ganin tayi shiru hankalin ta ma ba ya wajen sa Hakan ne yasa ta ɗan yi firgigit tana ɗan waro kyawawan idanuwanta a kansa, tare da ƙirƙiro wannan Shegiyar murmushin nata tana cewa, "ina jin ka Malam, mai kace ne?" Murmushi yayi yace, "ba suna na Malam ba, suna na Ahmad, kuma Ni ɗan saƙo ne wajen ki, aiko Ni aka yi." "To fa. Wane ne ya aiko ka?" Tayi maganar tana ɗan gyara tsayuwar ta, tare da ƙara kafa mishi idanuwanta ko ƙyafta su ba ta yi "Kar ki damu za ki sanshi ai, sai dai shi bai bani damar bayyana miki kansa ba, abun da ya aiko Ni kawai na zo yi, shi uban gidana ne shi ne yace in kawo miki wannan." Sai ya buɗe motan ya ɗauko wata ƙatuwar jaka ja mai kyau da burgewa a ido, ya zagayo yana miƙa mata Ta saka hannu ta amsa tana bin Jakar da kallo, kana kuma ta mayar da kallonta gare shi While shima idanuwansa a kanta yana cewa, "wannan shi ne saƙon, sannan akwai waya a ciki idan kika kunna za ku iya magana a ciki don zai kira ki." Sai ya miƙa mata key ɗin mota ya ƙara da faɗin, "sannan wannan ma shi yace in ba ki, motan nan taki ce." "Ban gane ba?" Ta furta tana zare idanu tare da shiga ruɗu da jin zancen nasa Murmushi yayi shi kuma yace, "kar ki damu za ki gane ai, Ni dai abun da aka ce in Yi kenan, kuma na aiwatar da aiki na, Ni zan tafi sai kuma wani lokacin." Da kallo ta bi shi har ya juya ya wuce a ƙafa, ta kasa motsawa sabida mamakin da ya cika ta tare da tunanin waye wannan? Wane ne ya aiko sa? Amma kuma tuna furucin sa na ƙarshe da cewa motan nan nata ne; tuni fuskarta ta sauya nan da nan ta washe baki ta soma zagaye motan tana shafawa, cikin wani irin farin cikin da ya tabaibaye ta har jikinta rawa yake yi ta juya gida da gudu. Tana shiga gidan ta soma kwaɗawa Zahra kira Zahra da ke wurin inda ta bar ta tana shan waƙa, sai tayi saurin zare earpis ɗin da ta sanya saboda yanda taga ta sukwano wajenta a guje. "Lafiya mene ne?" Arab ta kasa ma magana sabida yanda bakin ta ya ƙi rufuwa tsaban daɗi, sai yarfa hannu take yi tana son yin magana but ta gaza. Daƙyar ta natsu ta furta, "wlh na yi kamu.. na yi goshi.. na yi kasuwa ne ina tunani." "Faɗa min mana me ya faru ne don Allah? Kin saka Ni a cakwakiya." Zahra itama ta furta cikin zumuɗi da son sanin abun da ya faru "Mota... Mota... Mota ce wani ya kawo min Alkur'an, kin ganta ne kuwa? Wayyo Allana! Daɗi zai kashe Ni wlh." Tayi maganar cikin tsantsan farin ciki tare da tura mata Jakar tana cewa, "kinga har da wannan ya bani." Sai kuma ta soma ƙoƙarin buɗewa Zahra na taya ta da faɗin, "wai wane ne? Waye zai ba ki mota?" "Nima ban sanshi ba, amma yace min..." Sai kuma tayi shiru sabida ganin abun da ke cikin jakar Gaba ɗayansu suka ɗauke wuta ganin wannan maƙudan kuɗaɗen da ke cikin jakar. A tare suka kama baki suna zare idanu Hannu na rawa Arab ta sanya tana shafa kuɗin, yayinda take ɗauka tana mayarwa tare da zaro kwalin wayan da ke ciki. "Kuɗi.. kuɗi ne..." Ta furta cikin ihu da tsananin murna Wanda hakan ne ya farkar da Ummu da ke cikin ɗaki, ta fito da sauri tana hamma da cewa, "wai ihun me ake yi ne a wurin nan?" "Zo ki gani, zo ki ga abun mamaki." Zahra ta furta itama tana kai hannu kan jakar kamar zata taɓa sai kuma ta janye hannun, don ta tsorata da ganin wannan kuɗaɗen, don babu shakka ƙila ɗan yankan kai ne ya aiko mata da kuɗin Itama Ummu zuwa tayi wajen tana durƙusa wa tare da zaro idanu tana mamaki da faɗin, "wannan kuma daga ina? Aina wannan kuɗin ya fito?" "Wlh Arab ce, Arab ta zo da su." Zahra ta furta cikin tsoro Arab tace, "Wani ya bani, nima bai faɗa min ko waye ba, yace min idan na kunna waya mutumin zai kira Ni, sannan ya bar min mota a waje yace nawa ne." "Mota? Amma waye wannan?" Cewar Ummu cikin sake shiga mamaki, sai kuma ta miƙe tana cewa, "mu je mu ganta." Zahra tace, "wai kun tabbatar ba ɗan cin kai bane? Kar fa mu shiga uku, Ni a tsorace nake wlh." Tsaki Arab ta ja itama tana tashi da cewa, "ɗan cin kai kuma? Ke ana maganar arziki kar ki kawo mana ta tsiya mana. Uban ɗan cin kai ɗin." Sai ta dubi Ummu tace, "Aunty Ummu mu je ki ganta." Suka fita a tare da sauri tare da barin kuɗin a nan wurin Itama sai Zahran ta tashi ta bi su. Sun sha mamakin ganin zazzafan motan nan, tare da mamakin wanda ya aiko da su? Abun ya ɗaure musu kai; musamman da suka shiga ciki suka duba kuɗin wanda ƙiyasin su ya tabbatar musu da One million ne, sannan ga babban wayan da ke ciki ƙirar Samsung, har da simcard a ciki. Koda suka kunna babu komai a ciki bare su kira Number. Sun kasa kataɓus don a wurin suka zauna suka tasa kuɗin a gaba, kowa na kawo nashi tunanin a kan mutumin da ya aiko kuɗin Ita Arab farin ciki kawai take yi, sai da ta tashi ta taka rawa don daɗi, ita a wurinta ko waye ne wanda ya aiko mata da kuɗin babu ruwanta ko ɗan cin kai ne wlh, kuɗi dai ya zo hannunta baza ta taɓa mayar wa ba, a kan kuɗi babu abun da baza tayi ba, burin ta ma kawai ta ga kiran Mutumin, don ta ƙosa ta san waye ne me yake nema a wajen ta? Me yake so ta ba shi? Amma shiru babu kiran sa            Har Inna ta dawo suka shafa mata wannan daddaɗan labarin, ai daɗi kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha don babu wanda ya fi ta farin ciki, ita gani take yi ƴarta ne tayi goshi, duk yanda aka yi babban Mutum ne wanda ya aiko mata da wannan kuɗin, Shiyasa take ta sake musu huɗubar tsiya ta ci gaba da ɗaura su a kan keken ɓera, tare da sake ba wa Arab shawaran, "duk yanda za'a yi kar tayi sake da duk wane ne ma mutumin? Domin tana ji a jikinta arzikin su ne ya zo, tun yanzu ma sun tashi a sawun talakawa. Ai arziki kashi a wurin su yanzu." Sai dariya suke mata sabida yanda take ta santi har tana kasafa kuɗin yanda za'a yi dashi Ita dai Arab ta amshi dubu ɗari biyar a ciki ta ɓoye kayan ta, zuwa gobe zata kai banki ta zuba a account ɗinta. A ranan kasa barci tayi don daɗi, bata taɓa shiga farin ciki kalan wannan ba, Allah-Allah take yi mutumin ya kira ta don ta ƙosa sosai ta san waye shi? Amma shiru har safe tayi babu kiran shi. Tun tana zuba ido haka ta haƙura ta dena tasa wayan a gabanta; daga ƙarshe ta koma harkokin ta Kusan ƙarfe biyu na rana suka fita da Ibrahim a sabon motan nata, sun sha yawo babu inda basu zaga ba. Sai yamma suka dawo gida suka rabu a kan zai dawo anjima su fita zuwa club. Akwai wani Abokinsa da suke party a can, bayan ya bata labari shi ne tace, "zata bi shi." Da dare nayi kuwa ya zo ɗaukar ta. Ta ci wanka ta saka riga da wando matsatstsu tace ma su Inna, "zata je party da Bestyn ta." Haka ta fice babu wanda ya damu bare ya saka mata ido Baba ma bai san da fitan ta ba tunda yana ɗakinsa a lokacin A sabon motanta suka wuce zuwa club ɗin. Tun a waje za ka tabbatar da wurin babu ɗan kirki Maza ne da mata suka cakuɗe kowa da shigan banza a tare da shi, daga masu shaye-shaye sai masu casu, haka wurin ke tashin kiɗa ana ta iskanci, duk ƴan duniya ne gogaggu mara sa tarbiyya su ke wurin Yanda wurin ya haɗu kowa na harkan gaban shi ya burge Arab. Nan fa jikinta ya tsumu tunda ta ji kiɗan nan sai da ta shiga ta taka Daƙyar Ibrahim ya janyo ta suka fice zuwa wajen Abokin nasa, a nan ya gabatar da ita a cikinsu Duk babu wanda bai yabe ta ba a ciki yana koɗa kyanta. Sai dariya suke yi da nishaɗi, inda aka kawo musu kayan maƙulashe da su kwalaben giya kowa ya ɗauki abun da yake so Har Deen wanda shi ne ya haɗa partyn yake zolayan Arab ganin ta ɗauki drink tana sha, yace, "ba girman ta bane shan drink kaɗai, ga win na irin su shi Yakamata ta sha." Tayi murmushi tace, "no ba na buƙata gaskiya, wannan sai irin ku don ba ya burge Ni." "Oh! ba ki san daɗi ba Baby Gaskiya, Ibson guy yakamata ka nuna mata fa'idan shan shi, akwai dad'i." Dariya kawai Ibrahim yayi, dayake shi yana sha shiyasa yake ta kurɓan abun sa To cikin wannan yanayin ne duk samarin wajen bayan sun fita cikin hayyacin su suka ja ƴan matan su suna ta holewar su Ita dai Arab tana tare da Ibrahim suna zaune suna hira. Hankalin ta ma yana a kan waya tana chart, jefi-jefi suna hira da Ibrahim ɗin. Ganin dare ya tsala sosai tace mishi, "ya tashi su tafi." Shi ne suka tashi suka yi musu sallama suka wuce. Time ɗin duk Ibrahim ya soma fita hayyacinsa don sai sambatu yake mata sabida giyan da ya kwankwaɗa Abun da ta tsana kenan Arab ta ga Mutum ya shiga wannan halin, shiyasa sam giya ba ya burge ta don ba ta ƙaunar hankalin ta ya riƙa gushewa. Musamman yanda ta ga Ibrahim yana ta maganganun hauka, daƙyar ta tura sa a cikin motan ta shiga tana ƙoƙarin ja Amma ya hana ta, ƙarshe janyo ta yayi jikinsa ya soma ƙoƙarin romance ɗinta, yana ta mata sambatu yana gaya mata irin daɗin da take dashi idan suna tare, sai lashe ta yake yi kamar wani tsohon maye Haka ta biye masa tunda itama yanda take ji a lokacin gaba ɗaya ya tayar mata da tsumin ta. Sosai suka gogi juna kamar zasu cinye junan su, sai da kowannen su ya gamsu sannan ta tayar da motan suka wuce gida. A ƙofar gidan su tayi packing sannan ta taimaka mishi suka wuce gidan su Ibrahim ɗin, tana kai shi ƙofar gida ta dawo. A wani lungu ta ji an fizgo ta babu zato aka shige da ita cikin lungun, lokaci ɗaya aka danne mata baki sabida ƙoƙarin ihu da ta soma yi, cikin tsoro da firgita ta ɗaura hannunta a saman wanda aka ɗaura a bakinta tana ƙoƙarin cire wa, amma ina ta gaza sabida alamu ya nuna ba Mutum ɗaya bane masu kokawa da ita, suna ƙoƙarin danne ta a ƙasa zasu cire mata kayanta. [02/08, 9:24 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA ASHIRIN DA ƊAYA* _______________"Baaba wannan Shegiyar yarinyar nan ce fa ƴar gidan Iro mai kifi, shegiya tana ƴar hannu amma tana ƙoƙarin yin mana gardama, gwara ma ki tsaya mu mori rabonmu mu bar ki kafin ki ja muyi miki illa, banziya kawai." Ɗaya yayi maganar yana ƙara tale ƙafafun Arab da ta dage baza su buɗe ta ba Samu tayi ta gantsara wa ɗaya cizo a hannun da ya rufe mata baki, ta kwatsa ihu tana ƙoƙarin fincike jikinta Amma basu bar ta ba sai danne ta suke yi suna ta cikiniyar zare mata wando, ɗaya kuma ya matse mata nonuwa haka suke ta kokuwa da ita suna latsa ta Daƙyar ta samu ta ƙwaci kanta don yanda suka shawu duk ƙarfin su ya ƙare. Tana ƙwace wa ta ruga aguje sai gida, sai da ta ji ta a cikin zauren gidansu sannan ta samu natsuwa ta tsaya tana nishi; don ba ƙaramin gudu ta sha ba. Wayanta ta zaro a cikin Aljihun ta tana dubawa, Allah yasa bata yi komai ba don ta fi jin wayan a kan komai, sabida sabuwar wayanta ne da aka bata, ganin bata yi komai ba sai ta saki ajiyan zuciya a fili ta furta, "wlh da sun ci kutmar uban su da wayan nan tayi wani abu, matsiyata tsinannu kawai." Ta ja tsaki cike da azaban da ke ratsa ta sabida yanda duk suka sa ta ƙuƙƙuje a garin ƙwatan kanta, ciki ta shiga ta wuce ɗakinsu don har su Inna sun kulle ƙofa, nasu ɗakin kuma an sakaye shi but ba'a rufe ba Dukkansu babu wacce tayi barci sai chart suke yi Tana shigowa ɗakin Ummu tace, "ashe za ki dawo? Nayi tunanin a can za ki kwana ai." "Uhm ku dai bari, wlh daƙyar na sha." "Me ya faru?" Suka tambaye ta a tare suna tashi zaune "Ƴan iskan gari na samu suka so min fyaɗe, daga na je raka Besty gida suka tare Ni, wlh daƙyar na ƙwaci kaina har na hango yanda za su yi min." Dariya suka saka mata su kuma Inda Ummu tace, "kuma yanzu ƙyale su za ki yi? Sun raina miki wayau wlh, nan gaba ma za su sake kwatanta hakan in dai ba'a ɗauki mataki ba." "Nima tunanin da nake yi kenan, but babu wanda na gane a cikin su wlh da a gobe a cell za su kwana, domin ƴan sanda zan kira musu, sai dai kuma yanzu bani da tabbacin waɗanda suka yi min wannan abun, amma dole zan ɗauki mataki." "Gwara dai, don matsiyata ne mutanen nan, ta yiwu irin ƴan shaye-shayen nan ne da suke yawo kango-kango, da yanzu sun samu arhanki sun ci banza." Zahra tafaɗa tana dariya While Arab ta tashi tana shinshina kayanta, tare da cewa, "ƴan iska tsinannu waɗanda uwayen su suka tsine musu, duk sun zuba min warin su dole sai nayi wanka wlh." Ta ja tsaki tana tuɓe kayan a wurin Zahra CE kaɗai take bata amsa tana dariya Ita kuma Ummu tuni ta mayar da hankalinta a kan wayanta ta ci gaba da abun da take yi Sai da Arab tayi wanka sannan ta zo ta kwanta. Ta ɗauki wayanta itama ta hau net. A haka ta raba daren cikin chart da samarin ta, har su Ummu suka yi barci da daɗewa ita tana nan tana sana'ar nata, don in dai wajen chart ne ta ƙware sosai, yawanci duk sex chart take yi da su, wasu ma har video take musu ta tura musu, ko kuma ta ɗauki jikinta duk ta tura musu, ba ta wannan abun sai idan zata mori kuɗin ka, don ita a kan kuɗi babu abun da baza ta iya yi ba. Sai gab da asuba barci ya ɗauke ta Babu wanda ya tashe ta tunda su rayuwar su kowa yana yin shi yanda yake so ne, babu mai takurawa wani Shiyasa sai wajen goma ta farka, tayi wanka sannan tayi sallah, time ɗin ma su Zahra sun shiga school, ita dayake bata rigada ta koma makarantar ba duk da an koma tun last week. Yau ma haka ta wuni jiran kiran Mutumin nan amma shiru babu kiransa babu alamar sa, sai can da yamma ne ma ta samu saƙon sa, ta sha mamakin abun da ya rubuta Wai, "ta jira saƙo yau da dare za'a kawo mata, kar ta tayar da hankalin ta shi mai sonta ne, amma zata san shi bada jimawa ba." Daga haka babu abin da ya ƙara, kuma da ta kira Numban switch off ake ce mata. Duk ta sanar da ƴan gidan su suna jiran su ga abun da zai kawo Ai kuwa sai ga Ahmad wajen ƙarfe biyar da mintuna araba'in, ya kira Numban ta tunda Ogan nashi ya ba shi, idan ya je sai ya kira ta. Ai kuwa tana fitowa suka gaisa faram-faram da shi, sannan ya bata takardun gida wanda ogan ya siyan musu a can GRA, yace, "su koma can da zama saboda bazai iya zuwa wannan anguwan ba, shi babban Mutum ne ba ya buƙatar sa ido." Sun rikice da ganin gidan da aka kai su, don ita Inna ta kasa haƙura sai da ta tasa su suka je suka ga gidan tunda Ahmad yayi musu kwatancen gidan, kuma suna zuwa suka ga shi ne tunda da keys a hannun su. Babban gida ne makeke da ya ruɗa su ya saka su a wasi-wasi, suna tunanin wanne irin Mutum ne haka da yake kashe musu wannan maƙudan ƙuɗin? Me yake so a wurin su? Tsaban murna sun kasa barci a wannan ranan. Gari na wayewa suka ɗibi kayan su suka koma sabida zumuɗi Har da Baba babu yanda ya iya dole ya bi su tunda sai abun da Inna tace, kuma bazai yiwu ya bar iyalan shi ba idan ma yace, "bazai je ba." Ai kuwa ranan ƴan anguwa sun sha habaici da yaɓa magana wajen Inna, tana faɗin, "yanzu kuma sai su yiwa uban su tunda sun fi ƙarfin su yanzu, sun tashi sun bar musu anguwan, masu saka wa yaranta idanu sai suyi da uban su matsiyata, a haka zasu ƙare babu ci gaba, ita kuwa tayi musu fintinkau har abada baza su taɓa kamo ta ba, dama hassada ga mai rabo taki ce." Babu wanda ya kula ta tunda sun san jaraban ta, ƴar hau ce yanzu sai rikici ya kaure tunda ba mutunci ta cika ba, kowa Allah ya kyauta yake cewa don son kuɗin Inna yayi yawa, suna mamakin hali irin nata A wancan gidan da suka koma kowacce da nata ɗakin, kuma har da Toilet a ciki Sai abun da yayi gaba yanzu a wajen Arab, ta ƙaro wulaƙanci tunda komai tana dashi, babu abun da masu kuɗi zasu nuna musu wanda su basu dashi, su ma sun tashi a talaka sun koma masu kuɗin waɗanda sun fi ƙarfin raini, ga motocin ta duk a gidan, ɗaya take hawa ta bar wa su Zahra ɗayan. Yanzu ko school ta dena zuwa don yanzu bata da lokacin sa ma, ba don lokaci ya ƙure ba da tuni ta zana S.S.C.E ɗinta tunda yanzu abun da tayi tunani kenan, but ta bari zuwa next year ɗin sai ta zana, yanzu komai kuɗi nayi ko bata je ba zata samu kwalinta a hannu shaidar ta gama school, yanzu iskanci a wajen ta sai abun da yayi gaba, ba ta kula ƙananun yara sai manya, kuma idan har zaka ganta a wuri sai irin manya-manyan wurin nan inda sai masu hannu da shuni suke zuwa, shiyasa yanzu samarin ta duk irin manya-manyan Alhazawan nan ne; sai dai ta ci kuɗinsu son ranta Har yanzu suna tare da Besty don tare suke tsula tsiyan su. Tare suke yawon ta-zubar ɗin su duk inda akwai casu da holewa can zaka gansu, yanzu ta kai har ba ta kwana a gida sai idan ta so, wata rana ma sai dai su bar garin gaba ɗaya sunan sun tafi biki ko wani party, babu mai hana ta tunda Inna tana goyon bayanta. Yanzu ba Alhaji Bashir kaɗai take bi duk inda ya so ba, kowanne Alhaji idan ya kira ta tana bin shi ya kwana da ita, zai ɗauke ta tsawon kwanakin da zai yi idan tafiya yayi, zata zama ita ce tamkar matar shi har sanda zai dawo, shiyasa yanzu Arab ba ƙaramar mai kuɗi bace don ta fi ƙarfin komai, ta fi ƙarfin Yara kamar yanda take faɗa a koyaushe yanzu burin ta ya cika, babu inda sunan ta bai zaga ba in dai ana zancen gagga-gagga kuma tatattun ƴan duniya ne waɗanda suka shahara a iskanci. Duk wani babban ɗan iska ya santa kuma yana mu'amala da ita. Ta sake sauyawa tayi ƙiba na samun hutu da jin daɗi, ga jikinta da ya ƙara buɗewa ta zama babbar Mace komai ya ji, ƙirjin nan nata sun yi fam breasts a tsatstsaye suna tsole idanun Maza tare da ruɗan su, haka ma zubin dirinta, baza ka taɓa tunanin ƴar 17years bace tsaban yanda ta haɗa waɗannan kayan, sai dai a fuska ne kawai idan ka kalle ta za ka tabbatar da yarinya ce sharaf tunda fuskar Yara gare ta, fuskarta ƴar tsut ce da kyawu da Allah ya bata, tana da circle ɗin fuska da kuma kufan gashi, don duk fuskarta gashi ne har saje take dashi, gashin giranta kuma har sun kusa haɗewa; ga manyan idanu masu ban sha'awa da ɗaukar hankali farare sol a lumshe irin masu shiga jikin nan idan ta kalli Mutum, bakinta ɗan ƙarami sai dogon hanci, skin ɗinta kuma irin mai kyau ɗin nan ne don fara ce sol irin mai ɗaukar hankalin nan, ta ko'ina Arab ta kai Mace wacce kowanne namiji fatansa ace ya same ta, tana da kyau na fizgar hankali shiyasa suke ruɗewa idan suka ganta, ga ta da saurin shiga rai saboda yanda ta iya sarrafa jikinta, tafiyarta ma kanta abun kallo ne idan tana sarrafa jikinta, ga shegen iyayi da yanga kamar ta karye tsaban ta ƙware a bariki. Sai dai kash! Duk wannan kyawun; kyawun ɗan Maciji ne..... Uhmmm mu je zuwa, yanzu ne za a fara kafta wa.....             **********             Alh. Ƙasim Ali, shahararren mai kuɗi ne wanda yake zaune a garin Kano, tsohon ɗan siyasa ne wanda ya ci jiya ya ci yau; kuma yana saka ran gobe ma a dama dashi, yanzu haka kujeran senator yake kai, but yana neman takarar gwamna wanda yake son ya zama gwamnan jahar Kano a wannan shekarar. Shi mutane suka sani a yanzu kuma sunan shi babu inda bai zaga ba, Mutum ne mai facaka da kuɗi da taimakon talakawa da nuna musu shi na gari ne don samun jama'a, kuma Allah ya ba shi ɗin don yana da farin jini, duk abun da zai yi yana yi ne don jama'a su yabe shi su kuma so shi. Shi ne wanda ya bayyana a matsayin Mutumin da yake aiko wa Arab da maƙudan kuɗaɗe da kuma duk hidiman da yake mata da sunan yana sonta Ba ita kaɗai ba, kaf ɗinsu sun yi matukar girgiza da jin Sn. Ƙasim Ali ne wanda yake yiwa Arab duk wannan hidiman, kuma yake burin ya aure ta. Ai su shar abun su domin wannan babban dama ce a gare su Barin ma Arab da ta watsar da duk wani makamanta na ƙin yin aure yanzu sai a nan gaba, to ta san idan tayi sake da damar ta zata iya kufce mata, namijin da take buƙatar aure ne a yanzu ya zo gare ta, burin ta dama bai wuce ta auri shahararren mai kuɗi ba kuma wanda yayi suna domin itama ta kasance ana damawa da ita; sunan ta ya shiga ko ina ta nunawa duniya itama celebraty ne, kuma shi ne wannan ta samu tunda ga shi kujeran Gwamna sulluguda yake nema, nan gaba kaɗan zata iya zama First Lady, me ya fi mata wannan? Baza ta taɓa wasa da damar ta ba, dole ta amince mishi jiki na rawa, duk da har yanzu bai tako ya zo wajenta ba a cewar sa, "aiki yayi mishi yawa, yanzu haka ma ba ya ƙasan." Ita babu ruwanta wannan bai shafe ta ba tunda bata damu da sai ya zo gare ta ba, in dai zai aure ta to ita mai sauƙi ne tuni ta sallama mishi Sun sake ruɗewa a sanda ya sake musu wani babban kyautar. Ya biya wa Baba da Inna aikin Hajji wannan banar da ta rage sauran watanni kaɗan. Yanzu ma haka shirye-shiryen azumi ake yi. Yace, "nan da bayan azumi za'a yi musu aure da Arab." Kuma har Inna ta amince tunda ita ce a kan komai yanzu, Baba ma bai da lafiya sosai yana kwance a gida, sai dai a taimaka masa. Kuma a cikin azumin ne dukkan su zasu wuce Umrah Uhm daɗi har da kuka. Inna faɗi take yi, "yau burinta ya cika, dama ta sani wata rana a ƙashin arzikin ƴaƴanta zata je Makka ta fita ƙasarta na haihuwa, ga shi Allah ya cika mata burin ta, yau haihuwa tayi albarka ga shi ta samu surukin da ya ɗauki duk wani ɗawainiyar su albarkacin ƴarta." Azumi na zuwa kuwa suka wuce gaba ɗayan su har Baba, tunda ya ɗan ji sauƙin jikinsa, a sanda zasu wuce ne SN. Ƙasim ya zo garin Arab tayi mamakin ganin tunda ya zo ya tafi kwanansa biyu a Zaria; bai taɓa tunanin taɓa ta ba, don tunda ya sauka yasa aka ɗauko ta ta zo gidan da yake zaune, sai dai suyi hira yana faɗa mata wasu abubuwa nashi amma bai taɓa riƙe ta ba, lokaci ɗaya ta saba dashi tunda Mutum ne mai sakin fuska, har bata labari yayi a inda ya taɓa haɗuwa da ita, tana tare da wani Abokin sa a nan Adamawa zuwan da ta taɓa yi, tunda ya ganta ya kasa sukuni shi ne sai da ya bincika aka nemo mishi ita. Ta sake mamaki sosai musamman yanda ta gane ya san komai a kanta, ya san irin Rayuwar da take yi amma a haka yake son Auren ta, shi kuma ga shi tamkar mutumin kirki ba ya ko yin mata maganar banza, ba ya ƙoƙarin taɓa ta, burinsa kawai suyi hira na nishaɗi ta yanda zata saki jiki da shi. Ai kuwa tamkar sun shekara da sanin juna sun saba sosai, don har waya ya bata suka gaisa da matarsa ta gida, hakan ne yasa Arab ta sake sakin jikinta sosai musamman yanda ta ga matar ta nuna mata kulawa da kirki, itama ga ta kalar shi mai faram-faram. Arab bata da damuwa tunda ba wai don soyayya zata aure shi ba, zata aure shi ne kawai don kuɗinsa da kuma sunan da yayi, amma ita soyayya ba ta gabanta tunda har yanzu bata yarda akwai ta ba, kuɗi na siyan komai a wurinta, komai zata iya samu kuma ga shi tana kan samu ɗin Sai dai matsalarta ɗaya da ta so samu a wajen Tariq, ya saka ta gaba tunda ya ji zancen auren ta, har kwantawa yayi a asibiti don jin zancen, gaskiya itama ta tausaya mishi kuma ba ta ƙaunar rabuwa da shi saboda kulawar da yake bata, shi kaɗai ne yake iya gamsar da ita tana matuƙar jin daɗin harka dashi, sai dai tace mishi, "gwara ma yayi haƙuri don baza ta taɓa auren sa ba, yayi haƙuri kawai su ci gaba da yanda suke a haka, tayi masa alƙawari suna tare koyaushe, aure bazai sa su rabu ba, duk sanda yake buƙatar ta ya zo inda take zata san yanda zata yi su kasance tare." Ganin bazai same ta ba tunda da gaske take yi zata kuɓuce masa, dole ya amince da hakan tunda burin sa ace suna tare ɗin, musamman da ta ƙara ƙarfafa masa gwiwan, "wata rana zata iya fitowa ba dauwama zata yi da auren ba, don ita ba ta jin zata iya zama waje ɗaya, in dai da takura to zata fito, idan kuma babu takura zata ci gaba da rayuwarta yadda ta saba yi." Hakan ne yasa ya ji sanyi a ransa har ya haƙura.                           Bayan sun dawo daga Umran ne aka tsayar da ranan aure nan da sati biyu masu zuwa, a cewar sa, "komai shi zai yi musu". [04/08, 8:39 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA ASHIRIN DA BIYU* _______________Ana saura kwana tara bikin Arab; Firdausi ta haihu, ta haifi ɗa namiji Duk a cikinsu babu wanda yayi tunanin ya je ya duba ta, don hidimar biki ya sha musu kai, tunda aka sanar musu babu wanda ya sake bi ta kanta, su Zahra sun dai yi mata waya har suka nemi ta tura musu hoton Baby Ita kanta bata so haihuwar nan yanzu ba don ta so zuwa gidansu, tunda tayi aure bata taɓa zuwa ba, kullum Nafi'u sai dai ya bata haƙuri yace, "ta bari zuwa wani lokaci, shi wulaƙancin da za'a yi musu ne ba ya so, kar ya zo su je Inna tayi musu koran kare, kuma bazai jure ganin ƙunci a tattare da ita ba, gwara ta bari duk sanda suka tashi zuwa ya zamana Inna tana buƙatar su kuma tayi kewar su a sannan ɗin." Da wannan daɗin bakin ta amince ta haƙura ta zauna, musamman idan ta tuna da Baba shima ya kan ce mata, "tayi zamanta kawai." Amma ganin ta haihu har ana saura kwana uku suna babu wanda ya leƙo mata sai kuka take yi, duk ta tashi hankalin ta, nan ta kira Baba tana sanar mishi, "babu wanda zai zo mata ne?" Shi ne dalilin da yasa ya roƙi Inna a kan, "a tura wata ta je wajenta don Allah." Amma furr Inna ta ƙi, tace, "babu wanda zai je, ai su ma sha'anin biki suke yi, ta ƙarata can tunda ita ta zaɓi haka." Su kansu ba sa son zuwa tunda ana biki, amma ganin har da hawaye Baba yayi shiyasa Ummu tace, "zata je, amma ranan sunan zata dawo don bata yi alkawarin wuce wa ba." Inna bata ce komai ba tunda ita da kanta ta so zuwa ba wani yayi mata tilas ba Haka Ummu ta wuce Kaduna. To sai a lokacin ne Firdausi ta ɗan ji dama-dama, ko banza ta samu ƴar uwanta ta zo A washe gari kuma sai ga ƙanwar Baba itama ta je, dayake yayi mata waya ya faɗa mata halin da ake ciki, duk da ita sam ta fita harkan gidan Yayan nata, musamman a kan ƴaƴan Inna Harira sam babu ruwanta, amma yanda ya kira ta ya nuna mata damuwarsa shiyasa ta shirya suka wuce ita da ƴarta wacce ta aurar, sai kuma budurwan yarinyar ta wacce take gabanta, sa'ar Arab CE, ita kuma wacce ta aurar sa'ar Zahra ce amma ta girme ta da watanni, Ƙannin Malam Iro su biyu ne, daga Nana Firdausi sai Samira. Nana Firdausi ita ce wacce Firdausi ta ci sunanta, kuma ta rasu tun haihuwar fari da tayi, yarinyar ce take wurin Samira, kuma ita ta raine ta har tayi mata aure, sai dai ita yarinyar sa'ar Ummu ce, tayi aure a can wani ƙauye gaba da inda Gwaggo Samira take aure tunda itama a ƙauyen take da zama. Tsiya da fitinan Inna ne yasa kaf ɗinsu ba sa ƙaunar zuwa wurin Baba, sabida sun san halinta bata da kirki bare mutunci ko ƙalilan Har ƴan uwanta sun fita harkanta sabida tana da ƴan uba tunda ita kaɗai aka haifa a ɗakinsu. Sun fita harkanta tunda sun ce, "ba wani abun kirki take basu ba illa jaraba da zasu kwasa." Bare sun fita samu sun fita hutu da jin dadi, amma tunda suka ga yanda Allah ya mayar da ita a wannan gaɓar shiyasa duk suka sako jiki suka zo wannan bikin na Arab Ai kuwa sun ga wulaƙanci da gori, sai dai dama matsiyaci wanda ba shi da zuciya; in dai a kan kuɗi ne sun rigada sun yar da zuciyarsu kare ya ɗauka, sam sun ƙi tafiya duk da gorin da tayi musu, a haka akai ta biki da su suna nane Duk wani events da aka yi babu wanda SN. Ƙasim ya halarta, tunda ba shi da lokaci a cewar sa, gidan Amarya kawai suke kiɗan su suke rawan su, ai kuwa Arab tayi ƙarya a bikin nan ba kaɗan ba, an kashe kuɗi sanunu domin ƙawata bikin nan, ko ina ka je sai zancen bikin ake yi sabida yanda yayi matuƙar haɗuwa A ranan da aka ɗaura auren kar ku so kuga jama'ar da suka halarta, manyan mutane ne masu hannu da shuni har da gidan sarauta, kama daga na Kanon har na nan Zarian, sannan ga ƴan siyasa waɗanda suka yi fice sosai. Bikin nan an nuna ƙarya gaskiya, musamman yanda sadakin Arab ya kasance Naira miliyan biyu da mota Mercedes Benz sabuwa fil tana walwali, motan a ƙiyasin ta zata kai 13million Hmm babu bakin magana sabida farin cikin wannan ranan, sun sake tsinkewa da lamarin Senator Ƙasim, kuma lamarin nashi ya soma basu tsoro, amma dayake abun da suke so kenan babu wanda ya damu bare yayi tunanin wanne irin kuɗi ne haka dashi da zai riƙa musu ɓarin shi? Sun san dai Mutum ne ɗan siyasa dole a samu kuɗi a wurin shi Mutane an samu bakin gulma, sai dai babu damar yi a gaban Inna, domin dai-dai take da ƙugun kowacce shegiya, yanzu sai ta raba halin ta ba damuwar ta bane Komai na bikin a hotel aka yi odan shi, kama daga abun sha da ci har inda aka sauke baƙin a can hotel aka yi musu masauki, sai da zasu zo ɗaurin auren ƙofar gidan su Arab ne sannan suka fito An ci an sha an ƙoshi kuma an watse lafiya. Sai Allah ya kaimu gobe za'a ɗauki Amarya. Kar ku so kuga yanda ta koma, babu wanda idan ya san Arab zai iya gane ta a wannan lokacin sabida haɗuwar da tayi, ta sha gyaran Amarya ciki da waje, har wani ɗaukar ido take yi idan ta zo wurin jama'a, tana fita daban ne kawai kowa ya ganta ya san amarya ce, ga ƙyalli da tsantsi da fatarta ke yi duk wanda ya kalle ta sai ya so ya dauwama yana kallon kyawu da tsarin halittar ta, bazai so ace ko da wasa ya ƙyafta ido a kanta ba. Da yawa ta tafi da imanin jama'a a bikin nan Su kansu Abokan Ango abun ya ɗaure musu kai; ya aka yi Senator ya samo wannan yarinya ƙarama haka mai zubin larabawa sabida tsantsan kyau da Allah yayi mata? Sai dai yayi dariya yace, "rabon sa ne kawai." Sun taya sa murna sosai. Don su ma su Ummu babu wanda bata samu Saurayi a cikin su ba, domin tuni sun shige musu Zuwa washe gari suka wuce Kano da su Zahra kaɗai. An sauke su a babban katafaren gidan Senator Ƙasim. Gida ne mai hawa uku tsaban girman sa tamkar baza a mutu ba, side ɗin Arab daban na uwar gida Jameema daban. Sun sake susuce wa da suka gansu a wannan gidan Arab bakinta ya ƙi rufuwa tsaban daɗi, mafarkin da take yi a kullum kenan ga shi Allah ya cika mata burin ta, ko zama bata yi ba ta hau zagaye ilahirin part ɗinta Haka su ma su Ummu suna biye da ita suna taya ta, sai ɗaukar hoton gidan suke yi suna yin video a tiktok. Sun yi santin gidan tamkar kar su taho su bar ta, bare yanda komai yin musu ake yi wanka ne kaɗai ba a yin musu, hatta kayan da zasu saka kawo musu ake yi, abinci kuwa sai sun ture sabida yawan shi Kwanan su biyu aka zo da mota aka ɗauke su, tare da kyautar dubu ɗari biyar biyar da Jameema ta kawo musu a matsayin nata tsaraban, suka yi mata godiya sosai don ba ƙaramin burge su tayi ba sabida yanda ta kula dasu a zuwan nasu, kullum tana part ɗin tana tambayar matsalolin su, ko sun ce ba sa son abu sai ta kawo musu Ita kanta Arab ta yaba da hankalin Matar kuma ta shiga ranta, har Aunty take kiranta dashi a lokaci guda, sabida Matar babba ce zata iya kai wa arba'in a shekaru, ga kuma yanda take kula dasu tamkar ƙannin ta shiyasa nan take ta bata girmanta Bayan an kai su Zahra gida ne a nan me motan ya basu kyautar da Senator Ƙasim yace, "a basu." Motan cike fam da kaya sai murna suke yi Tun tafiyar su Jameema take kula da Arab, don wani lokacin ma a part ɗinta take wuni, dayake ba sa aikin komai an wadata su da masu aiki ko ta ina, sai dai su zauna suna hira suna sake sanin juna, ko kuma suyi kallo sai dare sannan Jameema zata tafi. Har kuma wannan lokacin Arab bata sake ganin Senator ba, ita sam bai dame ta ba tunda ga ta a cikin daula, tana cin abun da take so ta bar abun da bata so, lokaci ɗaya ta sake kilewa kamar ba ita ba, tamkar ka taɓa ta jini ya tsillo Jameema bata taɓa mata maganar Mijin nasu ba sai sau ɗaya da tace mata, "aiki ne yayi mishi yawa ba ya kwana a gida, kin san zaɓe ya kusa bare shi da yake neman babban kujera." Murmushi kawai Arab tayi tunda bata damu ba, amma kuma yau da gobe tunda ta saba a koda yaushe ana cinta bata taɓa kwanaki babu namaji ba; sai abun ya soma damun ta, dalilin da yasa ta nemi abokan harƙallan ta a chart take samu har ta biya wa kanta buƙata, shiyasa ta ɗan rage zama da Jameema wuni tana ɗaki tana charting da ba ya ƙare wa, sai da taga tamkar zata mutu abun yayi mata yawa don har ta kai ba ta jin daɗin biyan buƙatarta da kanta, namiji kawai take buƙata, ga shi tsawon sati biyu ana shiga na uku babu Miji babu alamar sa, shiyasa tace ma Tariq, "ya zo kawai ya same ta." Ita ta tsara mishi komai yanda Plan ɗin su zai kasance. Har kuma ta sanar da Jameema a kan, "ɗan uwanta ne zai zo gidan sabida akwai kasuwancin da zai yi a nan Kano; shi ne zai zo su gaisa." "Jameema tace, "ai babu komai ya zo nan ma ya zauna, suna da ɗakuna birjik sai inda ya so ya zauna." Farin ciki ne ya cika Arab sabida dama hasashen ta kenan, kuma ga shi ya tabbata, har tsallen murna tayi a wurin Yayinda Jameema take ta faman kallonta kamar wata mayya tana mata murmushi Hakan ne yasa Arab ta ji kunya tana bin jikinta da kallo sabida shigan da tayi, daga ita sai farar shimi da iyakansa cinya, komai na jikinta ana gani tunda mai tsantsi ne rigan, sannan bata saka komai a ciki ba sai iya rigan, ga kanta yau a tsefe wadda bata saba barin sa ba, ya sha gyara yana tufke sai shaining yake yi sabida kyau da ya ƙara mata, ta fi kyau fiye da in ta kitsa kan nata, duk da ba yawa ne da gashin ba amma mai ɗaukar hankali ne kasancewar har saje take dashi saboda kufan gashi ko'ina a jikinta Jameema kuwa dariya tayi da ta fahimci hakan, sai tayi saurin ɗauke kanta tana cewa, "kiyi haƙuri na dame ki da kallo ko?" Murmushi tayi ita kuma tace, "a'a wlh Aunty, bari in je in shirya don ya kusa zuwa." "To shikenan, nima idan ya zo sai ki kira Ni." "Tom." Arab ta amsa tayi gaba har tana ƙara tsallen ta don ta manta da wata Jameema a wurin Ita kuma sai kallonta take yi har ta shige; sai faman haɗiyar yawu take yi, daga ƙarshe ta tashi ta shiga ciki zuciyarta cike fal da tunani kala-kala.              **********        A sanda Tariq ya zo sai da aka ba shi wajen zama yayi wanka ya shirya sannan aka kawo shi babban falon su Jameema ta soma zuwa ta tarar da shi, suka gaisa faram-faram har tana tambayar shi mutanen gida? Ya amsa cikin fara'a da jin kunya shima Tana shirin magana ne sai ga Arab ta fito cikin shirin ta na riga da skirt masu ɗaukar hankali, gaba ɗaya zubin jikinta ya bayyana tana tafiya ko ina nata yana motsawa ne sabida yanda ta cika tayi fam sai ɗaukar ido take yi abun sha'awa Su kansu sun saki baki suna kallonta ne babu wanda ya ankare da ƙarisowarta Musamman Tariq da kamar zai zubar da yawu tsaban kallon da yake bin ta dashi, duk ta sauya mishi a ɗan ƙanƙanin lokaci haka, tamkar wata tarwaɗa haka yake ganin ta sabida mugun kyawun da tayi mishi Har sai da ta zauna tana zuba murmushinta mai ƙara mata kwarjini da tsantsan kyau, ta soma gaishe da Tariq ɗin Sai a nan ne suka dawo duniyar da suka shuɗa, kowannen su ya ja ido cike da kunya Tariq ya amsa cikin rawan baki yana ƙara bin ta da kallo Ita kuma murmushi tayi masa tana cewa, "ya su Innan?" Ya amsa da, "lafiya lau, suna gaishe ki ai." Sai satan kallonta yake yi, idan ya kalli fuskar Jameema ya ga ba ta kallon shi sai ya sakar mata wani kallo mai kama dana tausayi yana langaɓe kai kamar zai yi kuka Ita kuwa sai murmushi take yi tana share wa kamar bata ganshi ba Jameema tace, "su tashi su je su ci abinci kar su bar Baƙo haka nan maybe yana jin yunwa." Haka suka tashi ita ta fara yin gaba Daga bayanta suna biye da ita, nan da nan ya matso kusa da Arab ɗin ya riƙe mata ƙugu yana shinshinan ƙamshin ta har da wani lumshe ido Bata hana shi ba illa murmushi da take masa tana kallon fuskarsa Sun kusa isa dainning area ɗin; sannan ya yi saurin kama mata breasts yana faman matsa wa. Lokaci ɗaya suka saki wani irin numfashi da ƙiris ya rage Jameema ta jiyo ta gansu Sai dai ɗan tuntuɓen da tayi da three steps ɗin da ke wurin; ya sa ta dakata tana salati Dalilin da yasa suka janye jikinsu suna matsowa kusa da ita tare da yin mata sannu Ta ɗago da murmushi a kan fuskarta tace, "babu komai ai, mu je kawai." Suka ƙarisa kan dainning ɗin suka zauna. Sannan tayi kiran Mai aikin su ta zuba wa kowa abun da yake son ci suka fara ci, babu mai magana a cikin su illa su Arab da suke ta kallon junan su suna murmusawa cike da shauƙi Ita kuwa Jameema tunanin ta ma ya tafi wani wajen, jefi-jefi itama tana ɗago kai ta kalli Arab ɗin da bata san ma tana yi ba Har suka gama suka tashi suka koma Falo. Sai hira suke yi kamar sun daɗe da sanin juna da Jameeman da Tariq ɗin, don sosai ya saki jikin sa suna ta hira Jefi-jefi Arab take saka musu baki while hankalin ta yana a kan t.v tana yi tana canza channels, ɗaya hannunta kuma ta matse pilow har guda uku a jikinta, ɗaya tsakanin cinyanta ta jera su har kusa da ƙirjinta; tare da matse su sosai tana ta faman lumshe idanu, sosai take jin sha'awa saboda ganin Tariq ɗin, shiyasa maganar ma ba ta son Yi, ga shi Jameema ta ƙi tafiya ta bar su, duk haushi ya cika ta, daga ƙarshe tashi tayi tace musu, "zata je ta kwanta." Jameema tace, "lafiya dai ko? Naga yanayin ki ya sauya ne." "Babu komai." Ta furta tana ɗan ƙaƙalo murmushin dole. Sai kuma ta kalli Tariq tace, "Yayana bari in shiga in kwanta, in zaka tafi ka shigo sai muyi sallama before ka fita." "Ok Ƙanwata." Daga haka ta wuce. Suka bi ta da kallo suna ganin yanda jikinta ke juyawa musamman ma mazaunan ta wanda ya fi komai ɗauke musu hankali, sai da ta ƙule sannan suka juyo suna sauke ajiyan zuciya mai ƙarfi, duk kallon juna suka yi sai kuma suka wayance suka ci gaba da hiran Sai da aka kira sallan magriba sannan Jameema tace, "bari ta tashi ta koma part ɗinta, amma zuwa bayan sallan isha'i yayi ƙoƙarin zuwa suyi dinner tunda yanzu tare zasu riƙa cin abinci." Yace, "zai zo insha Allahu." Daga haka ya tashi ya nufi ƙofa kamar zai fice. Yana ganin ta ƙule ya dawo da sauri ya nufi inda ya ga Arab ta bi, sai dai bai san hanyar da zai bi ba, ya tsaya yana dube-dube kawai ya ji an ƙanƙame shi ta baya kamar za'a shige mishi jiki, har sai da ya saki ƙaramin ƙara yana faɗin, "Washh!". [05/08, 8:53 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/           *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA ASHIRIN DA UKU* _______________Shaƙar ƙamshin ta da yayi daga cikin hancinsa shi ya tabbatar mishi da Arab ce, hakan ne yasa ya janyo ta zuwa gabanshi ya rungume ta ƙaƙam suna sauke ajiyan zuciya, nan da nan ya soma shinshina ta yana ƙoƙarin haɗe bakunan su waje ɗaya Sai ta janye jikinta tana kallonsa itama a cikin wani mawuyacin hali, a hankali ta sa hannu ta janyo shi suka nufi upstairs zuwa ɗakin kwanan ta, tun a tsakar ɗakin suka soma kai wa juna wawura, lokaci ɗaya suka rikice burin su kawai su jiyar da junan su daɗi, ba ƙaramin kewar juna suka yi ba a yanda suke zalama babu ko sassauta wa, bare yanda Arab tayi satikai ba tare da taji daɗin namiji ba Haka suka kasance a wannan lokacin ba sa ji bare gani har sai da suka gama gamsar da junansu babu sauran wani sha'awa, sai a lokacin suka dawo cikin hayyacinsu suna ma junan su kallo cikin farin ciki, sai dai bugun ƙofan da suka ji daga can ƙofan shigowa yasa suka dakata babu mai magana a cikin su Daƙyar Arab ta miƙe ta ɗauki bargo ta lulluɓa a jikinta tana nufan bakin ƙofan da tambayar, "waye ne?" "Ni ce, Aunty ne tace in zo in kira ki kuyi dinner." Cewar Mai aikin da aka turo Jin hakan yasa tace, "ok, gani nan." Daga haka ta juya tana kallon agogon ɗakin, har takwas da rabi tayi. Hakan yasa ta dubi Tariq tace, "mayar da kayanka ka zo ka tafi, idan ka je can sai kayi wankan." Haka ya miƙe yayi kamar yanda tace mishi, bai bar ɗakin ba sai da ya ƙara tsotson ta before ya tafi cike da kewar juna Yana fita ita kuma ta faɗa toilet, har ta tuɓe ta ji motsin shi Sai ga shi ya faɗo mata Toilet ɗin yana cewa, "ban gane hanya ba Princess..." Maganar nasa ne ta ƙaƙale sabida ganin surar jikinta, nan da nan abun sa ta harba ya nufe ta da sauri ya haɗe jikinsu lokaci ɗaya ya soma shafa ta yana ƙoƙarin haɗe bakin su Ta dakatar dashi tana cewa, "please Tariq ka san jira na ake yi, kar ka tona mana Asiri mana, ka je don Allah ba guduwa zan yi ba, yau muna tare fa har sai ka gaji." "Da gaske kike yi?" Yayi maganar kamar ɗan maye ba tare da ya dena shafa ta ko ta ina ba, sai goga mata jikinsa yake yi Ita kanta numfashi take sauke wa cike da wani irin sha'awa da ya turniƙe ta, ta sa hannu ta kama mishi ƙeya tana ƙara shigar da shi jikinta sosai sabida daɗin abun da yake mata, tamkar zata zauce haka take ji, lokaci ɗaya ta biye masa suka soma romance ɗin juna cikin zafi-zafi tamkar zasu cinye juna, har ƙasa suka kai suna baɗalar su sun cakuɗe wuri ɗaya, babu mai saurara wa ɗan uwansa. Sai da suka sake jin muryan Jameema a cikin bedroom sannan lokaci ɗaya suka dawo hayyacin su, duk sun gama ruɗewa Arab ma ta kasa amsa kiran sunanta da take yi. Daƙyar ta amsa a karo na uku muryanta a shaƙe "Lafiya dai A'isha babu abun da ke damun ki?" "Eh Aunty, Ina wanka ne, amma yanzu zan fito." Ɗan jim Jameema tayi sabida jin nishi da kuma yanda ta ji muryan Arab ɗin yana fita, kamar ta leƙa haka take ji sabida ganin ƙofan toilet ɗin a buɗe, amma sai ta daure tace, "ok kiyi sauri ina jiran ki, sannan ki kira Yayanki don na aika a kira shi babu shi a ɗakin, Allah yasa ba ya rasa hanyar dawowa bane." "To." Arab ta furta tana jin zuciyarta na sanyi ganin asirin su bai tonu ba, da sauri ta miƙe jin Jameeman ta fice daga bedroom ɗin, "ka gani ko za ka ja mana a banza a hofi, don Allah mu je in raka ka ka fita." Tayi maganar tana janye hannunsa da ya ɗaura mata a breasts sai faman matsawa yake yi kamar tsohon maye. Duk abun da take ji haka ta haƙura ta tasa shi gaba bayan ya mayar da kayansa; itama ta saka towel sannan suka fice, ta wani ƙofa ta nuna masa wanda ba sai ya je ta babban falon ba. Tana ganin fitan sa ta koma da sauri tayi wankan a gaggauce, ta zura doguwar riga mai ruwan zuma; ta rufe kanta da hula ta fice ko tsayawa busar da gashin bata yi ba. Tana fita Falon ta tarar da Jameeman zaune a kan couch Jameema tace, "har kin fito?" "Eh Aunty, sannu na bar ki kina ta jira." "Babu komai wlh." Ta furta tana bin ta da kallo ko ta ina Hakan yasa Arab duk ta tsargu, sai dai bata ce komai ba ta zauna tana ɗauke kanta zuwa kallon t.v Jameema tace, "kira Yayan naki mu ji inda yake." Murmushin yaƙe tayi, bata ce komai ba ta ɗauki wayanta tayi dialing Numban Tariq, "Hello Yaya kana ina?" Daga can Tariq murmushi yayi yana rage murya a hankali yace, "ina nan cikin shauƙin daɗin ki da har yanzu bai sake Ni ba." Murmushi ita kuma Arab tayi da cewa, "Ok ka zo muna jiran ka." Daga haka ta kashe wayan tana kallon Jameema tace, "ga shi nan zuwa." "To Masha Allah tunda ya dawo, nayi tunanin sai an je nemo sa a hanya ne ai." Tayi maganar cikin zolaya Dariya kawai Arab tayi bata ce komai ba Daga haka suka yi shiru har sanda Tariq ɗin ya zo Shima sai da ta tsokane shi tana cewa, "ashe ba ɓace wa yayi ba? Tayi tunanin ko anguwan nasu ne ya rikitar dashi." Sai da ya kalli Arab a sace before yayi murmushi yana cewa, "a'a Aunty, Ina masallaci ne na tsaya yin shafa'i da wutri shiyasa ban dawo ba." Sai da Arab ta kalle shi jin abun da yace, murmusawa kawai tayi ta sake ɗauke kanta. Tana jin amsar da Jameema take ba shi, wai, "gwara hakan ai." Murmushi kawai ta sake yi a zuciyarta tana faman cije leɓe Daga nan ne suka tashi zuwa dainning area suka ci abincin. Wannan karon Jameema ta soma musu sallama ta tafi Su kuma hakan ne yasa suka wuce kai tsaye ɗakin Arab ɗin suka garƙamo ƙofa.            Washe gari ma sun more abun su tunda Jameema bata fito ba, kasancewar tayi baƙin ƴan mata kusan su biyar suna can a part ɗin ta, har can Arab ta je ta gaishe ta shi ne take ce mata, "su karya kawai ita baza ta fito ba sabida akwai baƙin da take jira." Arab bata damu ba sai ma farin ciki da tayi, tana komawa ɗaki ta kira Tariq suka ci gaba da holewar su, sun ji daɗin ranan don tare suka kasance har yamma babu Jameema, cin abinci kawai yake fitar dasu Suna nan zaune a falo ne sai ga Jameeman ta fito tare da ƴan matan, tace musu, "zata je ta dawo, zata iya kai wa dare idan sun ji shiru kawai su ci abincin su su kwanta." Suka ce, "to." Cike da farin ciki Ita kuma ta sa kai ta fice ƴan matan na biye da ita duk babu mai suturan mutunci a jikinsu, ɗaya ce ma kawai ta saka Hijab sai dai daga gani ba kayan kirki bane a jikinta sabida yanda komai ya nuna na halittar ta. Sai kallon Arab suke yi kamar zasu haɗiye ta Ita kanta ta tsorata da wannan kallon kuma ta sha jinin jikinta, tunda suka gaisa sai ta ɗauke kai a kansu, amma duk idan ta ɗaga kai ta dube su sai ta ga irin kallon da suke mata kamar wasu tsofaffun Mayu, har a ranta tana tunanin ko dai Mayun ne? hakan ne yasa bata sake bi ta kansu ba har suka fice   Da sauri Tariq ya janyo ta jikinsa yana cewa, "Wow! Na ji daɗin tafiyar Matar nan wlh, shikenan ta bamu fili muyi abun da ranmu ke so." "Na fi ka jin daɗi ai." Ta furta tana kai mishi sumba a fuska Lokaci ɗaya ya kama kanta ya manne bakin su wuri ɗaya ya ƙi saki, haka suke ta tsotson juna tamkar zasu haɗiye juna, nishin su kawai ake ji mai fita da ƙarfi, don da ace akwai mutum a wurin dole zai ji, sun manta ma a inda suke don a babban falon gidan ne, haka sukai ta aika wa junan su saƙo cikin shauƙi da bege. Daga baya ne suka tashi suka koma ciki, a nan ma sun jiyar da junan su daɗi kamar baza su rabu ba, kwata-kwata ba sa gajiya, suna gama wa suke sake tsulmiya wa wata gogin tafkin daɗin sabida yanda suke maganganu na batsa masu sake tayar musu da sha'awa, har Fingnaring ɗinta yake yi tana ihun daɗi Sai da can kusan ƙarfe tara na dare nan suka dakata da abun da suke yi, wanka suka shiga a tare suka ɓata lokaci a ciki, daga ƙarshe suka ci abinci babu wanda ya damu da sallan da basu yi ba a ranan, suna zaune a ƙaramin falon Arab ɗin sai hira suke yi suna dariya, suna wasa a tsakanin su tana zaune a saman cinyar sa, duk idan ya bata abincin kaɗan sai ya latsa mata nonuwa before ya ci gaba, ko kuma idan ya saka mata a baki sai ya haɗa da nashi bakin ya cinye, ya gama tsotse ta tas before ya ƙara bata wani. Daga ƙarshe suka tashi suna wasan tsere Ita Arab daga ita sai farar shimi iya cinyanta, saman an yi ado da less baƙi, da rigan da babu duk ɗaya sabida ko hannun kirki babu, irin siraran hannun nan ne ga shi sai zamewa suke yi rabin ƙirjin ta a waje, tuɓur-tuɓur haka take gudu komai na jikinta yana motsa wa gunun sha'awa Hakan ne yasa Tariq lokaci ɗaya wani sha'awar nasa ya tashi, nan da nan abun sa ya miƙe yana faɗa mata, "ta tsaya haka nan shi ya gaji, gwara su je su sake koda sau ɗaya ne zai iya zauce wa a yanda yake ji." But ta ƙi tsayawa tace, "sai ya kama ta sannan zata ba shi." Ai kuwa haka yayi ta bin ta yana gudu, gaba ɗaya ya ɓalle bottles ɗin rigan sa yana bin ta kamar maye don ya zaƙu ya kama ta. Yana cafke ta kuwa ya manne gabansa a jikinta ya kama mata ƙugu yana shinshina ta cikin salo raɗa-raɗa yake cewa, "ga shi na kama ki, yarinya babu mai ƙwatan ki yau sai nayi miki cin da sai kin kasa tashi, ba dai Ni kika wahalar ba?" Ƙoƙarin gudu take yi tana dariya Ai kuwa ya ɗaga ta sama yana wulwula ta kamar ƙaramar yarinya A dai-dai lokacin kuma Senator Ƙasim ya buɗo ƙofan ya shigo ya tarar da su a haka. _Please more comment, idan babu sai bayan kwana biyu. enjoy your weekend._ [07/08, 8:39 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/          *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA ASHIRIN DA HUƊU* _______________Dukkansu sun dafurce ganin Senator a gabansu, tuni Tariq ya sake ta yayi ƙasa da kansa jikinsa har rawa yake yi; dukkan su sun gaza motsin kirki Shi kuwa idanu ya kafa musu, sai da ya gama ƙare musu kallo before ya tako cike da izza irin na masu kuɗi ya zauna, tare da sake kallonsu yace, "ashe kuna nan?" Ɗago kai Arab tayi jikinta na rawa don bata san ya zai ɗauki abun da ya gani ba, baza ta so ya zarge su ba bare ya sake ta, shiyasa duk ta kasa natsuwa maganar ma ta kasa yi sai ɗaga mishi kai da tayi Murmushi yayi shi kuma yana cewa, "sannu ɗan samari, wannan shi ne ɗan uwan naki kenan? Jameema ta sanar min da zuwan shi." "Eh... Eh shi ne." Ta furta tana sakin murmushin yaƙe murya cikin rawa While shima Tariq tuni ya soma gaishe shi cikin girmamawa ko ɗago kai ba ya iya yi Ya amsa cikin fara'a yana tambayar sa ayyuka da mutanen da ya baro? "Alhamdulillah kowa lafiya." Ya amsa mishi still cike da nuna kunya, kana kuma ya ɗan ɗago kai ya dubi Arab yace, "bari in je akwai inda zan je." Sai ya yiwa Senator ɗin sallama sannan ya fice Ita kuma Arab duk ta rasa abun yi tana tsaye tana cakuɗa hannayen ta duk jikinta a sanyaye. Sai da taji yayi mata maganar ta kawo mishi ruwa sannan ta wuce da sauri ta buɗe fridge, ta zuba masa ta kawo masa Ya amsa yana mata murmushi tare da cewa, "zauna." Ya nuna mata kusa da shi A hankali ta ɗofana mazaunan ta cikin ɗar-ɗar Hakan ne yasa da ya gama shan ruwan yace da ita, "ko akwai abun da ke damun ki ne?" Da sauri ta girgiza mishi kanta tana murmusawa Sai yace, "kiyi haƙuri da barin ki da nayi tsawon wannan lokacin ban zo gare ki ba, ayyuka ne suka yi min yawa kin san zaɓe ya kusa, kwata-kwata bani da time, yanzu ma haka daƙyar na samu wannan time ɗin nace bari in zo in duba ki, mun Yi waya da Jameema tace min baza ta dawo gida ba zata kwana a inda ta je shiyasa nace ni kuma bari in yi ƙoƙarin dawowa mu gaisa." Sai ya kama hannunta yana kallon fuskarta ya ƙara da cewa, "ba kiyi fushi da Ni ba ko?" Murmushi tayi tana duƙar da kanta tare da cewa, "a'a ban yi ba." "To na gode, na san dai ban kyauta miki ba ki sake haƙuri da Ni komai ya kusa wuce wa." Sai ya ja numfashi yana cewa, "mu je ki haɗa min ruwan wanka in na gama sai na ci abinci, na ga dare ma yayi." Ya ƙare maganar da duba agogon hannunsa Tashi tayi suka wuce bedroom ɗinta, a nan yayi wankan sannan ya wuce nashi ɗakin da ke part ɗinta ya shirya A time ɗin tuni Arab ta saka an shirya musu abincin a dainning. Yana fitowa suka wuce suka ci abincin, yana jan ta da hira har suka gama, nan da nan har ta saki jikinta ta ma manta me ya faru, sai da suka taɓa kallo before suka koma ɗaki suka kwanta Abun da ya ba wa Arab mamaki ganin bai yi mata komai ba haka suka kwanta, shiyasa take tunanin to ko lafiya? But bata damu ba dai ta juya kai itama tayi barcinta tunda yau bata da matsalar komai already Tariq ya kawar mata da kwaɗayin ta Zuwa washe gari sai kusan ƙarfe biyu sannan Senator ya bar gidan, lokacin ma Jameema ta dawo sannan ya tafi. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️           Yanzu haka su Inna suna ta shirye-shiryen wuce wa Saudiya ne tunda lokaci yayi, sai dai kuma jikin Baba ya ƙi daɗi a ɗan kwanakin nan, har sanadin hakan ne yasa aka kwantar da shi a asibiti Inna dai babu ruwanta don tace, "wlh baza tayi jinyar sa ba, can ta matse mishi lokaci yana yi zata tafi Saudiyyan ta, yanzu ba tashi take yi ba." Sai su Ummu ne suke zaune dashi, idan wannan ta kwana yau gobe sai wancan, sun sanar da Arab halin da yake ciki har ta turo musu kuɗi, kuma matsalar ga shi Senator ba ya zama a gida bare ta sanar mishi, idan ta kira wayansa ba ya ɗauka, shiyasa ta sanar da Jameema Ita kuma tace mata, "ta shirya kawai ta je ta gaishe shi." Sannan ta bata kuɗi tace, "tayi hidiman asibitin dashi." Arab ta amsa tayi mata godiya sosai don ba ƙaramin farin ciki tayi da kuɗin ba. Haka ta shirya suka wuce da Tariq don shima a lokacin ne zai koma sabida ayyukan sa.        Bayan sun sauka a Zaria ita ta wuce gida Inna tayi farin cikin ganin ta ba kaɗan ba tamkar zata goya ta, haka ma Ummu tunda a time ɗin ita tana gida Zahra na Asibiti. Sai murna suke yi haka itama ɗin, farin ciki duk ya cika ta don ba kaɗan ba tayi kewar ƴan uwanta tamkar yau ta taɓa yin nesa da su, but wannan daban ne tunda aure ne Haka Inna na rawan jiki tayi ta kula da ita, ta ɗauko mata wannan ta ɗauko mata wancan, duk a tunanin Inna ciki Arab take dashi saboda ganin yanda ta sake sauya wa a ɗan ƙanƙanin lokacin nan, tamkar ba ita ba, kowa ya ganta ya ga Matar manya sabida tsaban kyan da tayi, har wani ɗaukar idanu take yi, sosai ta sauya ba kaɗan ba komai nata ya sauya tayi dam da ita gunun sha'awa, ko maganar ta ma ta sauya salon ta tsaban yanda take yanga da kwarkwasa Sai da ta huta sannan suka wuce asibitin tare da Ummu a motanta, motan da Senator ya bata ranan bikin ta tunda a shi suka zo ita da Tariq, dayake shi lokacin da ya je can motan haya ya hau, motocin ta na gida kuma guda biyun yanzu Zahra da Ummu kowa yana amfani da ɗaya ne. Koda suka je asibitin haka suka rungume juna da Zahra sai murna suke yi suna dariya, kowacce fuskarta cike da farin ciki Jikin Baban da sauƙi don a lokacin ma ya samu barci ne har tashi yana iya yi ya zagaya. A lokacin da ya farka ya ji daɗin ganin Arab kuma ya nuna murnan sa sosai, haka yayi ta sanya musu albarka yana musu nasiha Duk jikinsu yayi sanyi sosai a yau ɗin, sun zauna suna ta sauraron shi domin ji suke yi tamkar wasiyya yake musu sabida yanda nasihan nasa yake ratsa musu zuciya Sai dare sannan suka wuce gida, aka bar Ummu ita zata kwana dashi Bayan sun koma ne sai ga kiran Senator Ƙasim ya kira. Ta ɗauka suka gaisa yana tambayar ta, "ya mai jiki? Jameema ta sanar mishi but tayi haƙuri sai yanzu ya samu ya kira." Murmushi kawai tayi tace, "babu komai Alhaji, ai jikin ma da sauƙi." "To Masha Allah haka ake so." Sai kuma yayi ɗan shiru before ya ci gaba da cewa, "ki zauna zuwa lokacin da kike son dawowa sai ki dawo, zan tura miki saƙo ta account sai ayi hidimar asibitin dashi." "To." Kaɗai tace mishi jikinta duk a sanyaye, har suka gama wayan bata yi wata magana sosai ba Zahra da ke kusa da ita dariya tayi tace, "kina sha'anin ki ƙanwata, gaskiya kin more da yawa da samun wannan Mijin naki, kinga yanda kika sauya? Anya bazan bi ki mu tafi tare in Yi kwana biyu a can ba? Dama ina son zaman Kano wlh." Murmushi Arab tayi tace, "zan ji daɗin hakan gaskiya tunda nima na gaji da zaman Ni kaɗai, kullum kana zaune kamar wani maye." Zahra tace, "haba kina nufin kishiyar taki yanzu babu ruwanta da ke ne ko kuma Mijin ba ya zama ne?" "Hmm baza ki gane ba." Arab ta furta tana ajiye wayanta a saman cinyanta tare da ɗaura hannunta ɗaya a saman fuskarta tana shafa wa "Ki sanar da Ni zan gane, ko akwai wata matsala ne?" Kallon fuskarta Arab tayi before tace, "babu wata matsala zan iya cewa; tunda ban rasa komai ba a gidan, sannan Aunty Jameema tana kula dani sosai yanda kika san ɗiyarta, matsalar har yanzu Mijin bai taɓa kwana dani ba, ke in faɗa miki ma tunda aka yi auren sau ɗaya na taɓa ganin shi ya dawo ya kwana a gidan, kullum ba ya gida, Ni kuma gaskiya bazan iya ba duk da dai zuwansa da rashin sa bai dame Ni ba, amma bazan iya zama a haka babu namiji kusa da Ni ba, shiyasa kawai na kira Tariq ya zauna dani a can." "Me?" Zahra ta furta da sauri tana ware idanun ta "Ƙwarai kuwa, kiran sa nayi kuma a gidan ya zauna a matsayin ɗan uwana, babu wanda ya zarge Ni ya maye min gurbin Mijina tunda shi ba ya tani." "Tab ɗijam... Kin yi auren ma baza ki bar wannan rayuwar ba Arab? me kike nema ne da yanzu ba ki samu ba? Ina jiye miki abun da zai faru a gaba." Taɓe bakin ta tayi ko a jikinta tace, "me zai faru? Babu abun da zai faru, ke bari ki ji Ni fa ba nayi auren nan don wani abu bane face kuɗi, kuma dama ban taɓa saka wa a raina zan dena rayuwar ƴanci na ba, sana'a ce a gare Ni idan har zan samu dama sai na dama wlh, bazan takura in hana kaina jin daɗin rayuwa ba, duk da kuɗi dai alhmadulillah sai dai na ba wani amma bazai yiwu na cuci kaina wajen hana zuciyata abun da take so ba, tsoho na aura fa, a haka zan ƙare rayuwata?" Zahra tace, "lallai ina jiye miki lokacin da asirin ki zai tonu Allah kuwa, aure kuma ba abun wasa bane Arab, shiyasa nima nake son yin auren nan don na gaji da zama a haka ina cutuwa, Haidar ya dawo har mun yi magana zai turo, kin san fa tunda ya ji labarin Alhaji Abubakar yana nema na shi ne duk ya damu wai kar in ƙara kula sa, yanzu tunda ya dawo yace zai turo muyi auren." Arab ta kalle ta tace, "amma ke wawiya ce wlh, kina nufin za ki bar Alhaji Abubakar ɗin; ki auri Haidar? Kin kuwa san waye Alhaji Abubakar? Wlh wlh ya fi Mijina kuɗi domin da kanshi Mijin nawa yake faɗa min yanda suke, kuma yace duk wasu kasuwancin su shi ya ɗaura sa a kansu." "To ai hakan ba shi zai sa in aure shi ba don yana da kuɗi, Ni farin cikin zuciyata nake so, kuma da kike cewa yana da kuɗi ai shima Haidar ɗin ba matsiyaci bane kin sani, sannan jini ne na Sarauta, wlh ya fiye min shi a kan in auri tsohon nan, Allah ya kyauta sam bazan iya ba, yanzu ke ma kike faɗa da bakin ki baza ki iya rayuwa da tsoho ba babu jin daɗin rayuwa." Tsaki Arab ta ja tace, "wani zubin ke doluwa ce Allah, ana nuna miki ga Annabi kina runtse ido." Hannu Zahran ta sa ta taska mata duka a cinya tana cewa, "ya ishe ki fa wlh, uwar waye doluwar? Allah Arab kin raina Ni Ko kina manta Ni Yayar ki ce?" "Ban manta ba, gani nayi sam ba ki da wayau." Tayi maganar a fusace saboda jin zafin dukan ya shige ta, kana ta ƙara da cewa, "Bari zan faɗa ma Inna sai ta nuna miki gaskiya tunda ke sam ba kya gane wa." Ta ja tsaki tana tashi zata fice Zahra tace, "wannan kuma ke ta shafa, zan gani idan za'a yi min auren dole ne." Itama ta ja tsakin tana tashi ta bi bayanta Arab kuwa na fita wajen Inna ta je ta faɗa mata Itama Innan bata goyi bayan Zahran ba Amma ita Zahra sam tace, "baza ta iya auren tsoho ba Haidar ne zaɓin ta, gwara ma su dena zancen." Haka dai suka haƙura suka bar ta tunda ta ƙi gane abun da suke nufi.             **********       Arab tayi zaman ta a gidan su tunda ga abun da mijin yace, iyakan ta kira Jameema suyi waya, yawo kuwa babu inda ba ta zuwa don ba ta zama a gida, daga tana can da wannan namijin sai a ganta da wancan, tamkar bata yi aure ba don manta wa take yi da wani Aure a kanta tsula tsiyanta kawai take yi, ta ƙi komawa ne sai idan Inna ta tafi Saudiya tunda lokaci yayi ana ta kiran Alhazai Jikin Baba kuma babu sauƙi dole sai dai ya haƙura tunda yana jin jiki, idan yayi kamar zai warke sai kuma jikin ya tashi, dole aka hana sa zuwa tunda baza su bar shi ya tafin musu a haka ba A ranan da Inna ta tafi washe gari jikin Baban ya sake tsanani sosai, shiyasa Arab ta ƙi tafiya sai ma canza mishi asibiti aka yi don gani suke yi kamar ba ya samun kulawa a asibitin gwamnati, sai aka mayar da shi na kuɗi, haka yake shan jiki tunda ciwon already ya ci jikinsa kafin ya kwantar da shi, duk damuwa ne ta haifar mishi da ciwukan nan har da hawan jini, baƙin ciki da damuwan da yake saka wa ransa a kan abubuwan da Inna Harira take mishi, ga damuwar halin da yaransa suke ciki ya kasa sanya su a kan hanya, ciwo ya ci ya ci jikinsa har ya taɓa mishi zuciya Kwana uku da kai shi asibitin ma Allah ya amshi abun sa Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un... Tabbas mutuwa wata aba ce mai girma wanda komin taurin zuciyarka idan har mutuwar ta shafe ka dole ne sai ta taɓa ka, duk yanda su Arab suka kai da rashin biyayya ga mahaifin su; da kuma rashin ɗaukar sa da muhimmanci a rayuwar su, sai da suka yi kuka, sun sha kuka sosai domin a zuciyarsu babu wacce ba ta ƙaunarsa, bare tafiyar da yayi ya tafi ne baza su sake ganin sa ba, mutuwar ta shige su sosai kuma tasa jikinsu yayi sanyi matuƙa, ko magana ba sa iya yi, duk wanda ya gansu sai ya tausaya musu tamkar ba su ba Barin ma Firdausi wacce ta fi su shiga wani hali, a daren da ya rasu washe gari ta zo gidan, ta sha kuka ba kaɗan ba duk ta fita a hayyacin ta, haka suka haɗe kai suna ta kuka kamar zasu bi shi Baba ya ga jama'a gaskiya ba kaɗan ba, shi kansa Senator Ƙasim mutane da yawa ya zo dasu jana'izar Haka Matar shi Jameema itama a ranan ta zo, tana tare da su Arab tana faman rarrashin su, gaskiya ta tausaya musu domin mutuwar mahaifi babban illa ne ga rayuwar kowanne Mutum, tamkar ka rasa wani ɓangare na jikinka ne, rashi ne babba.           Inna tana can Saudiyya mutuwar ya riske ta, duk yanda ta kai ga musguna wa Baba itama mutuwar ya matuƙar girgiza ta har sai da ta zubar da hawaye, shiyasa gaba ɗaya aikin hajjin tana yin shi ne cikin rashin walwala, nan take hankalin ta sai ya tashi burinta kawai ta koma gida, hankalinta duk yayi gida duk da ta san ko ta koma baza ta same shi ba, amma yanda mutuwar ta shige ta ne duk ta ruɗe a can; ba ta iya yin wani abun kirki Kwana uku da rasuwar shi sannan Jameema ta koma gida, while Senator shi tun a ranan ya tafi bayan ya danƙa ma Arab kuɗi mai yawa wanda zasu kula da jama'a ƴan gaisuwa Yawanci duk a ranan mutane suka watse, dama ba wasu mutane bane illa su Firdausi, itama a ranan uku ta wuce, sai Jameema da ta tafi itama a ranan, sannan sai Gwaggo Samira, duk a ranan suka wuce Arab ce kaɗai tare da su Ummu a gidan, sai ranan bakwai sannan suka tattara su duka suka taho Kano; kasancewar Arab tace, "su biyo ta kawai idan Inna ta kusa dawowa sai su dawo." Haka kuwa suka bi ta babu musu Kuma a can ma babu wanda yace don me? Domin Jameema ma murnan ganin su tayi, sai haba-haba take yi dasu tamkar zata goya su, duk da akwai ƴan aiki amma komai ita take musu, musamman zata ce, "su shirya su fita yawo." Wani lokacin ma har gidan su take kai su, wato gidan sarauta kasancewar ita ƴar can ne, mahaifinta ƙani ne wajen Sarki. Duk sun saba da jama'ar gidan su babu wanda bai sansu ba. A cikin ƴan uwa ma har su Zahra sun samu samari don har biyo su suke yi gidan su Arab su sha soyayyar su But sai dai su ɗin babu wacce take son su don Allah sai dai don a rage zafi, domin already kowacce cikin su tana da wanda take fatan aura. Zahra ta tsayar da Haidar a wanda take burin aure da zaran Inna ta dawo za'a yi magana. Haka itama Ummu sabida akwai wani saurayi da yake son ta Shima kyakykyawa ne duk da ba wani kuɗi sosai da sosai yake da shi ba, irin ƴan ƙaryan nan ne duk abun da take so yana mata, ga shi ya iya wanka na jan hankali da iya tsara kalaman soyayya, lokaci ɗaya ya samu zuciyarta sabida gaba ɗaya ta susuce a kansa, duk abun da ya faɗa mata ita yarda take yi dashi don yace mata, "ba a nan yake aiki ba, yana ƙasar England ne yana aiki, suna yin aure can zasu wuce." Ita abun da take hangowa kenan, shiyasa duk ta amince dashi, yanzu sun yanke shawaran duk tare zasu yi aure bayan Inna ta dawo za'a tsayar da rana   A can Kano su Zahran suka yi babban Sallan su. Bayan kwana biyu da yin sallah suka koma gida sabida gyare-gyare da zasu yi na dawowar Inna, tunda ba wani daɗewa za'a yi ba zata dawo. [08/08, 9:34 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/          *P.W.A✍️ _________________________ *BABI NA ASHIRIN DA BIYAR* _______________Jameema ce tsaye a dainning area tana ba wa masu aikin su umarnin yanda zasu shirya kan dainning ɗin, mutane biyu ne masu shirya wurin while biyu kuma suna kwaso coololin da suka shirya komai a ciki suna kawo wa Arab ta fito daga ɗaki wanda barci ne ya sure ta har rana tayi bata farka ba, fitowan ta sai ta iso wajen tana cewa, "Aunty Barka da aiki." Jameema wacce sai a yanzu ta ganta ma sai tayi murmushi tace, "yauwa Ƙanwata barkan ki, kin tashi ashe?" Murmushin itama tayi tana cewa, "eh, I don't know when I fell asleep but now I wake up, until time is up." "Ƙwarai kuwa, na shigo na ganki kina ta sharan barci nace bari in bar ki kar in tashe ki, dama na shigo sanar miki ne akwai baƙi da zan yi, ɗan Aunty na ya zo shi ne zasu shigo gaishe Ni da Matarsa." "Ayya ashe baƙi zamu yi? To bari in je in shirya before su zo." Jameema tace, "sai kin dawo, nima yanzu zan shiga in watsa ruwan." Daga haka Arab wuce wa tayi ta koma part ɗinta. Wayanta ta tarar tana ƙara shiyasa ta ɗauka ganin Besty ɗinta ne, sun jima suna waya before ta kira Zahra suka gaisa tana musu ya hanya kasancewar tun tafiyar su jiya basu yi waya ba, sun jima suna wayan har da Ummu before ta shiga wankan.                A lokacin ne motan Malik ta shigo gidan, bayan yayi parking suka fito shi da Nawwara, sun yi kyau matuƙa cikin shaddar da suka yi anko kalan maroon, ko da gani ka san kuɗi da hutu ya zauna musu don har wani ƙiba suka yi Tun tafiyar su yawon Honeymoon suka ƙi dawowa a can suka yi azumi da ƙaramar sallah Sai da Abban Malik ya nuna musu ɓacin ransa yace, "maza su dawo kafin ya taho inda suke ya saɓa musu." Sannan ne suka dawo Yanzu kwanan su biyu da zuwa Kano, shi ne suka zo gaishe da Jameema tunda a matsayin ƙanwar Mummyn su Malik take Itama sai da tayi musu mita tace, "wlh idan basu zo ba zasu ga fushin ta tunda sun manta da ita." Suna shiga falon Jameema ta tarbe su don tana zaune a Falo tana jiran shigowar su. Rungume juna suka yi da Nawwara tana cewa, "sai yau Allah yayi zan ga idanun ki Nawwara, kika biye wa Abdul kwata-kwata ba kwa ƙaunar zuwa wuri na, ko me nayi muku oho? Tun auren ku fa baku zo nan ba." Dariya Nawwara tayi da cewa, "kiyi haƙuri Aunty, wlh muna ta sa ranan zuwa Allah bai yi bane, bayan mun dawo kuma ayyuka sun yi yawa, Abba ya tsare mu yace babu inda zamu matsa sai mun gama aikin Office, to sai da wannan sallan ya zo ne muka ɗan samu damar fita muna zagaya dangi." "Ai yayi min dai-dai tunda alamu ya nuna babu mai hankali a cikin ku, daga zuwa hutu kun je kun shantake a can, ke kuma kwata-kwata kika biye masa kika ƙi dawowa." Tayi maganar tana jawo kunnen Malik da ya zauna a gefen ta Shagwaɓe fuska yayi kamar zai yi mata kuka yace, "kai Aunty don Allah kar ki katse min kunne, please ki sakar min." "Bazan saki ba har sai ka faɗa min dalilin da yasa ba ka son zuwa gidana, wato kuna ma garin ba don mun yi waya da Mummyn ka ba bazan sani ba? So ku kayi ku tafi ban san da zuwan ku ba." "Wlh Aunty a'a, ya za'a yi mu zo bamu zo nan mun ganki ba? Allah zamu zo." Nawwara na dariya tace, "ai Aunty kar ki yarda da daɗin bakin shi, tun farko sai da nace mishi mu zo mu gaishe ki First; but yace a'a, kuma Ni na san dole zai ce ya manta mu tafi bamu zo ba, shiyasa tun farko nace mu fara zuwa." "Hohho! Ka ga gaskiya ta bayyana, ai kuwa zan yi punishment ɗin ka, a nan zaku ƙarisa kwanakin ku har ku koma Abuja, zan kira Mai martaban in faɗa masa." Murmushi Malik ɗin yayi tare da faɗin, "da girman kujeran ki Aunty, tuba nake, amma..." Sai ya kalli Nawwara ya harare ta zai yi magana      Jameema ta hana sa da cewa, "kar ka ce komai ka dena hararan ta, gaskiya dai ta faɗa min kuma na gama yanke hukunci, a nan zaku zauna har ku tafi, yanzu bari in sa a kawo muku drinks ku fara sha before mu je mu ci abinci, nan jiran ku muke yi bamu ci komai ba sai kun zo; don nace tare zamu yi lunch ɗin." Sai ta koma kiran ƴar aikin nasu Babu jimawa sai ga ta ta fito da gudun ta tana cewa, "Aunty gani." "Kinga baƙi kuma sun zo ba ki kawo musu drinks ba? Bayan nace kar kiyi nisa da nan, maza haɗo musu snacks ki kawo musu, sannan ki kira min A'isha a ɗakinta." Cikin girmamawa ta amsa mata before ta tashi ta tafi da saurin ta Su kuma suka ci gaba da hiran su cikin raha da dariya; har sanda mai aikin ta kawo musu abun taɓa wa, suka ɗauka suna ci still suna hiran su Malik yace, "Uncle ba ya nan ne wai?" "Ba ya nan, amma na san nan da kwana biyu zai dawo sabida hidindimu sun yi mishi yawa ne ma." "Maybe zamu tafi ma bai dawo ba kenan?" "Ku yaushe zaku tafi?" Ta tambaye shi tana kallon sa "Nan da two days din mu ma insha Allah." Tace, "ok zaku haɗu ma kafin ku tafi tunda kuna tare da Ni." Ta ƙare maganar tana murmusawa Su kuma sai suka yi dariya kawai While Malik yana cewa, "wai Aunty ina Amaryan naki da aka yi miki?" Nawwara da ke shan juice tayi saurin ajiyewa tana cewa, "Ni fa wlh Aunty da biyu na zo gidan nan fa, don wlh tunda aka ce an yi miki kishiya abun ya baƙanta min rai, gaskiya Uncle bai kyauta miki ba, yanzu mene ne abun ƙara aure kuna a wannan shekarun? Su fa Maza na lura basu da tabbas wlh." Baki Malik ya saki yana kallonta While Jameema sai dariya take yi sabida ta san halin Nawwara akwai ɗan banzan kishi, duk wanda yake tare da ita dole ne ya san halinta. Bata kai ga yin magana ba sai ga Arab ɗin ta fito, takunta suka ji shiyasa duk suka waiga ga turaren ta da ya bugi hancin su lokaci guda Saukowa take yi daga matattaƙalan benen cikin taku irin na isa da tsantsan wayewa irin nata, tana sanye da bak'ar riga mai santsi har iya gwiwan ta, sai jan leggings tare da hill shoes red color, gashin kanta tayi parking ɗin shi sannan ta ɗaura hula mai tuntu wanda rabin gashin nata ta gaba a buɗe yake sabida style ɗin da tayi, tayi kyau matuƙa saboda yanda kayan suka halittu a jikinta suka bayyana kyakkyawar surar jikinta, duk da fuskarta babu makeup amma ta shafa lipstick mai maiƙo sai glowing yake yi bakin nata; daga nesa ma ana iya hango shaining ɗin sa Wani irin shock Malik ya shiga da ganin fuskar Arab a wanann lokacin, bai yarda cewa ita bane shiyasa ya kasa motsi tunanin sa ya tsaya cak illa idanunsa da suke yawo a kanta While Nawwara kuwa ita kanta kyawun Arab ɗin ya ruɗe ta har ta kasa ɗauke ido a kanta tsaban yanda tayi mata mugun kyau, tamkar hawainiya saboda yanda take sarrafa jikinta Ita kuwa Arab ko kaɗan bata damu da irin kallon da suke mata ba, don itama ɗin idanun ta zuba musu musamman Malik, amma cikin jan aji sai ta ɗauke idanunta sabida ganin ta iso wajen, ta ƙariso da murmushi a fuskarta tace, "sannun ku da zuwa." Tana zama a kujeran da ke kallon wanda suka zauna, tunda duk suna kan three sitter ne sun sanya Jameema a tsakiya Jameema tace, "wannan ita ce A'isha Matar Uncle ɗinku, ita ce Abokiyar zama na." "Me?" Cewar Nawwara da ta kasa riƙe mamakin ta Malik kuwa har miƙe wa yayi tsaban yanda maganar ta buge sa, tabbas Arab yake gani a gabansa wacce yake fatan ace yau Allah ya haɗa su, amma kuma mummunar maganar da ya ji Jameema ta furta sai da yasa lokaci ɗaya ya firgice ya shiga wani hali zufa na keto mishi Da sauri Nawwara ta kalle shi tace, "mene ne haka Dear? Lafiya?" Itama Jameeman tambayar da tayi masa kenan While Arab na kallonsa ba tare da ta furta uffan ba, sai dai mamakinta yanda yake mata wannan kallon ƙurillan kamar maye Shi kuma zama yayi yana kama kanshi ya kasa furta komai duk ya rikice har jikinsa rawa yake yi Shiyasa hankalin su ya tashi don a tunanin su wani abun ne ya same shi, ga shi ya ƙi musu magana bare su san me ke faruwa Nawwara miƙewa tayi ta dawo wurinsa duk ta gama ruɗewa itama, dafa shi tayi tana kiran sunan shi kamar zata yi kuka, "wai lafiya Dear me ke faruwa da kai ne?" Daƙyar ya iya furta, "babu." Yana ɗago kansa tare da zuba wa Arab idanunsa da suka soma canza kala "Wai me ke damun ka Abdul? Ya za'a yi kace babu komai bayan muna zaune lafiya yanzu?" Inji Jameema cike da damuwa a fuskarta itama "Babu komai Aunty, kaina ne ya ɗan sara min." Ya furta a hankali yana runtse idanunsa Jameema tace, "Ayya sorry, Allah ya baka lafiya, bari in samo maka magani ina zuwa." Sai ta miƙe da sauri ta wuce While Nawwara sai sannu take mishi tana tattaɓa shi duk ta rikice Arab kuwa taɓe baki kawai tayi don ita haushi ma yake bata ganin yanda yake ɗago kai yana kallonta a sace kamar wani tsohon maye, amma kuma wai ba shi da lafiya, alamu ya nuna mata akwai wani abu a ransa ne saboda kallon da yake mata, "ko dai ya sanni ne?" Wata zuciyar ta kawo mata wannan tunanin, sai kuma ta taɓe baki tana ɗage kafaɗa bata damu ba Jameema na dawowa ta ba shi maganin ya sha sai sannu suke mishi Ya so ya bar wurin amma bazai iya ba, domin ganin Arab ya fi mishi komai a yanzu, bazai taɓa iya jirgawa a wurin ba bayan ya ga yarinyar da yake burin gani a rayuwar sa, ga ta a gabansa tamkar mafarki, anya dai ba mafarkin yake yi ba har yanzu? Zuciyarsa ta hautsine gaba ɗaya don bai taɓa tunanin ganin ta ba, murna zai yi ko ihu? Ya rasa wanda yakamata yayi tsaban farin cikin da yake ji a cikin ransa, sai dai abun da ke ruguza mishi farin cikin a nan take idan ya tuna kalaman Jameema na cewa ita ce Matar Uncle ɗin su, wannan wacce irin mummunan ƙaddara ce? Yau ga ta ya ganta amma wai a matsayin Matar Uncle ɗin shi? Shikenan ya rasa ta kenan? No bazai taɓa yiwuwa ba domin yayi ma kansa alƙawari ko tana da aure sai ta zama tashi, ba ya da sukuni ko kaɗan a wannan lokacin, ya kasa ma furta komai hankalin sa kacokan yana kanta duk da ba ya fahimtar me ke faruwa a wurin Ita kanta Arab ta gama tsarguwa da wannan shegen kallon da yake mata, bare itama tana jin kamar ta taɓa ganin mai kama da shi, maybe ya santa ne, shiyasa ta miƙe zata bar wurin Amma sai Jameema tace, "ta tsaya tunda abinci zasu ci." Haka ta basu umarnin tashi su je su ci abincin Babu musu suka miƙe su duka suka wuce wurin, Nawwara na manne a jikin Malik ɗin ta hana shi saƙat sai kula take yi  dashi, ita tayi save ɗinshi ta tura mishi abincin a gabansa, sai kuma tace, "ko ta ba shi abincin da kanta tunda ta ga ya ƙi ci?" Jameema tace, "oh wa ya ga masoya, a gabana ma sai kun nuna min kenan?" Arab ta soma tashi tace, "ta ƙoshi." Sai ta koma Falo ta zauna Shima sai Malik ɗin ya tashi tsalan yace, "ya ƙoshi." Da mamaki Nawwara ta kalle shi tace, "Dear ba ka ci komai ba fa? Ka zauna ka ci ko kaɗan ne don Allah." "Ba na ci, bazan iya cin komai ba yanzu baki na babu daɗi, zuwa anjima zan ci." Yayi maganar yana yin gaba zuwa Falon Nawwara ganin ya zauna a Falon tare da Arab, sai kawai ta miƙe ta koma wurinsa ta manne mishi tana jan shi da hira don ɗauke mishi hankali Amma sam bata san cewa ba ta ita yake yi ba, hankalinsa yana a kan Arab wacce ta duƙufa tana latsa wayanta tunda ta ga zuwan shi wurin A sace yake kallonta ba ya son Nawwara ta gane, shiyasa yake ɗan biye mata don kar ta zargi wani abin tunda ya san halinta da shegen kishi yanzu sai ta iya gano wani abun Ana haka Arab ta ɗago kanta saboda a jikinta tana jin irin kallon da ya tsare ta dashi, shiyasa ta ɗago itama ta zuba mishi idanu, suna haɗa ido ta sakar mishi harara tana yatsina fuska While shi kuma sai ya sakar mata da singnal yana ɗan mata murmushi da wani irin narkakken kallo da ya jefa mata Tuni Arab ta gane manufar sa; kasancewar ta ƴar hannu domin in dai akwai abu a ran Mutum zaka iya fahimta ko daga irin kallon da zai maka, itama ta fahimce shi shiyasa ta saki guntun murmushi kawai tana ɗauke kanta saboda zuwan Jameema wurin, sai ta miƙe tace, "Aunty bari in shiga ɗaki zan yi Call." Bayan ta amsa mata ne sai tayi gaba kamar zata tafi kuma sai ta sake haɗa ido da Malik ɗin suka sakar wa juna murmushi a tare; don ita burge ta yayi bare yanda ta ganshi mai kyau da alamu yana da tsananin tsafta koda kallon yanayin sa, komai nashi kamar ka sace musamman jikinsa na ƙirar ƙarfafa, shi ya fi ruɗanta, har kwaɗayin sa ta ji tana yi Tunda ta tafi bata sake bari sun haɗu ba don ta ƙi fitowa bare su ga juna Shi kuwa Malik duk ya zuba ido ya ga ta fito amma shiru, suna zaune sallah kaɗai yake tayar da su suna hira Ga shi Nawwara ta dame su da hiran Arab ɗin, sai sukan ta take yi sabida wai, "a kan me Jameema zata yarda a auro mata wannan ƴar shilan yarinyar ruwan Larabawa? Gani take yi kawai ta zo musu wayau ne don daga gani idanunta a buɗe suke, zata raba ta da Mijin ne ya zama nata ita kaɗai, don irin su basu da mutunci bare ace ta haihu da uncle, sai abun da tayi dashi kenan." Malik yace, "ke dai ba ki da wani tunani sai na kishi, ki dena haka da Allah, haka kawai ba ki san yarinya ba ki kama ki riƙa kwatanta ta da abun da bai dace ba." Sosai Nawwara tayi mamakin yanda ya fitittike yana faɗa alamu ya ji haushin maganar nata, shiyasa tace, "wai tsaya dear meye haɗin ka da yarinyar nan da kake son kare ta? Ban fa gane ba me kake nufi?" Jameema ta katse su tace, "ya isa haka don Allah ba na son wannan maganar nima, Nawwara ba yanda kika ɗauki A'isha haka take ba, tana da kirki kuma muna zaune lafiya, Ni ban damu ba don Alhaji ya kawo min ita a kishiya saboda Ni na ba shi goyan bayan ya ƙara auren." "Gwara ki faɗa mata Aunty tunda ba kowa bane irin ta, kishi yana rufe mata idanu gaba ɗaya sai ta manta abun da yake dai-dai." "Tab ɗijam... Wlh tallahi a kanka sai dai kace min mahaukaciya Malik, Ni dai ace kayi min kishiya gwara in mutu da inga bak'ar ranan nan bare ace Ni da kaina na buƙaci haka, gwara ma idan akwai hakan a ranka tun wuri ka cire don Ni ba irin sauran matan nan bane da zasu iya sadaukar da mijin su ga wata, kai nawa ne Ni kaɗai babu wata Mace da zata shigo cikin mu." Jameema tace, "lallai Nawwara na yarda kishi ya rufe miki ido, amma kafin hakan ta kai ga faɗa gwara mu bar zancen nan don Allah, don naga alamu ba ki da sauƙi a kan hakan." Da haka suka bar zancen sukai ta hira Amma Malik ya ƙi sakin jikinsa, ƙarshe ɗakin da aka basu a nan downstairs ya shige ya kwanta a saman gado, ya kasa kataɓus sabida damuwar da ta taru tayi mishi yawa, taya zai ɓullo wa al'amarin don yana gani dai bazai iya ƙyale Arab ba, zuciyarsa baza ta taɓa haƙura da ita ba bare ace yanzu da ya sake jin tsananin soyayyarta ya ƙara nunkuwa a ransa, bai taɓa tunanin haka take ba domin sosai ta sake sauyawa fiye da yanda yake ganinta a hoto, ta ƙara girma ba kamar a cikin hoton ba, tabbas ita ce domin ko ya ta koma bazai taɓa kasa gane ta ba, komai nata mai kyau ne Allah ya bata komai, ga suna mai daɗi, "A'isha." Ya furta a laɓɓansa cikin farin cikin da ba ya misaltuwa yana murmusawa. Ya rasa wanda zai iya faɗa ma wannan tsantsan farin cikin da yake ji a ransa saboda arba da yayi da wacce yake jin soyayyarta daban da kowacce Mace, haƙiƙa yau babbar Sa'a ce a gare sa, dole ya ɗauki waya domin kiran Sinior ya bayyana mishi, but sai ya dakata sabida shigowar Nawwara Har dare ya kasa sukuni don ƙiri-ƙiri barci ya ƙi ɗaukar sa a daren, bazai iya haƙura batare da ya je gare ta ba, amma taya ya? Can cikin dare da ya tabbatar da Nawwara tayi barci sannan ya lallaɓa ya fice, sama ya haura tunda ya tabbatar a nan ɗakin su yake, amma abun damuwar bai san ina zai nufa ba, ɗaya part din ya bi tunda ya san Jameema ce a wancan part ɗin, dole zai kasance ita tana wancan ne, shiyasa ya lallaɓa ya shige cikin ƙaramin falon da ya ji a buɗe, duk babu haske a ko ina tunda duk an kashe glop ɗin sashin, sai da ya dudduba sauran ɗakunan bai ganta ba sannan ya nufi wadda take ciki, ai kuwa yana shiga ya hango ta a cikin ɗan hasken fitilan da ta bari Tana kwance tayi male-male a saman gadon, daga ita sai wata figigiyar rigan barci mai ruwan orange, da ita da babu duk ɗaya domin komai na jikinta ana gani, ga shi ta yaye can sama cinyoyinta duk a waje suke, da alamu tayi nisa a barcinta don yadda take sakin numfashi mai ɗan ƙarfi Wani irin ajiyan zuciya ya sauke lokaci ɗaya ya kwaɗaitu da ganin kyakykyawar surar jikinta, gaba ɗaya jin sa yayi cikin wani irin feelings ɗin da bai taɓa jin makamancin sa ba, a hankali ya ɗaura hannunsa a saman marar sa yana wani sauke numfashi a kai -a kai, bazai iya haƙura da abun da zuciyarsa take kitsa mishi ba, shiyasa nan take ya nufi kan gadon cikin wani irin yanayi da ya kasa control ɗin kansa. [11/08, 10:14 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍     *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/          *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA ASHIRIN DA SHIDA* _______________A hankali ya isa kan gadon ya hau yana kai hannunsa jikinta, jin tattausan skin ɗinta sai da ya sake shiga wani irin hali lokaci ɗaya ya sauke numfashi, gaba ɗaya ya soma ficewa a hayyacinsa sabida yanda ya soma shafa jikinta while ƙamshin turaren ta yana ƙara shige masa hanci kamar zai ɗauke masa numfashi, shiyasa daƙyar yake fizgo numfashin yana ƙara shige mata cikin salo yana sarrafa ta Yayinda Arab kuwa sosai ta sha mamakin jin kamar Mutum a jikinta, lokaci ɗaya ta farka sabida jin ya damƙe mata breast yana ƙoƙarin fito mata dasu daga riga, lokaci ɗaya ta buɗe ido ta zuba mishi tana shirin ƙwalla ƙara domin ba ƙaramin tsorata tayi ba, kwata-kwata bata gane kowaye ba Jin ta saki ihu hakan ne ya dawo dashi cikin hayyacin sa da sauri ya kai hannunsa saman bakinta yana cewa, "shiiii! Baby Ni ne." Ya furta a hankali yana kallonta Itama kallon shi take yi zuciyarta na tsananin bugawa sabida har yanzu a tsorace take, da sauri ta miƙe zaune tana janye jikinta cikin mamakin ganin shi, but ta gaza buɗe bakin ta bare ta furta wani word Shima sai ya miƙe zaunen yana ƙoƙarin kama hannunta da cewa, "Baby kiyi haƙuri na tsorata ki ko?" Hannunta ta buzge cikin jin haushi tace, "wannan wanne irin hauka ne? Me ka shigo min a ɗaki?" "I'm sorry, don Allah ki rage murya muyi magana na fahimta." Tsaki ta ja tana sauka daga kan gadon tare da gyara rigan ta, ta shige toilet ta bugo ƙofan Shiru Malik yayi ya rasa abun da ke mishi daɗi, shi kansa bai san meyasa ya aikata wannan aika-aikan ba, idan kuma ta tona mishi asiri fa? Meyasa yayi wannan gangancin batare da ya soma tunkaran ta ba? Wayyo... Shiru ya ji bata fito ba sai ya miƙe jiki a sanyaye ya soma zagaye a wurin, yana ta kallon ƙofan toilet ɗin kamar ya shiga haka yake ji, duk ya gama susucewa ga tsananin sha'awar da ya taso mishi, burin sa kawai ya ji shi a jikinta, gaskiya bazai iya fita ba dole ne sai yayi ko ma mene ne in dai zai samu cikan burin sa. Fitowar Arab ɗin; shi ya tsayar dashi daga inda yake tsaye tare da bin ta da kallo yana son karantan yanayinta Ita kuwa fuskarta ta wanke koda ta shiga toilet ɗin, tana fitowa kallo ɗaya tayi mishi sannan ta haye kan gadon ta zauna, sai ta bi shi da kallo fuska babu walwala tace, "So what do you want in my place What are you looking for? Meyasa ka shigo min ba tare da izni na ba?" "Kiyi haƙuri, I'm very sorry, na kasa jurewa ne, and I love you so much!" Ya furta hakan cikin wani irin yanayi yana tsaye a wurin ba tare da ya motsa ba While ita kuma sai ta sake ɗaure fuska da cewa, "I don't understand what you mean? Ina Matar aure kake so na?" Tahowa yayi a hankali zuwa wurin gadon, sai ya samu wuri ya zauna yana fuskantar ta, "na kasa jurewa ne Baby, wlh son ki ne yasa na aikata hakan, kuma bazan taɓa iya sukuni ba har sai naga na mallake ki sannan, na san ba ki san Ni ba but Ni na san ki da jimawa, kuma tun ba yanzu ba nake tsananin ƙaunar ki." Murmushi ne ya suɓuce mata before tace, "you mean you already know me, ehem fahimtar da Ni don ban gane ba?" "I have known you for a long time, and since I have been looking for you but I have not seen you, now I see you in this house. Gaskiya bazan iya haƙura da ke ba that's why I came here to tell you how much I love you, ko me zai faru bazan iya haƙura da ke ba dole ne in sanar miki idan ba haka ba ina ji mutuwa zan yi, sonki zai kashe Ni, wlh bazan taɓa iya haƙura da ke ba!" "Lallai kam kana da ƙarfin hali, anyway yanzu kaga Ni Matar aure ce bai kamata ace kana so na ba, tunda yanzu ka sani sai ka haƙura kawai ko?" Tayi maganar tana murmusawa tana mishi wani kallo mai shiga jiki Sosai ta sake saka shi a wani irin yanayi, shiyasa yace, "A'isha bazan iya haƙura ba, a kanki nace zan iya yin komai wlh, bazan taɓa iya fita ɗakin nan ba har sai kin amince da Ni, ina sonki da gaskiya, ina tsananin buƙatar ki a cikin rayuwata, wlh ko nawa ne zan iya ba ki idan har za ki kasance da Ni, na yarda ko ba ki kashe auren ki ba idan har zamu kasance tare Ni na yarda zan iya zama da ke, Ni dai burina ki zama tawa Ina matuƙar ƙaunar ki, na san watarana zan iya mallakar ki ko ba yanzu ba, amma dai yanzu ina buƙatar ki a cikin rayuwata, ina son mu kasance tare." Shiru ta ɗan yi kamar tana tunani, sai kuma tace, "ok na yarda, amma da sharaɗi..." Da sauri ya ƙara matsowa kusa da ita cikin zumuɗi yace, "wanne sharaɗin ne? Ko meye zan iya bi idan har za ki amince." Dariya tayi sabida yanda ta ga yana rawan jiki, sai tace, "kai kyakykyawa ne gaskiya Matarka tayi Sa'a, ko Ni zan so ace kai ne Mijina ba wannan tsohon ba, to amma..." Sai tayi shiru kuma tana wulla idanunta cikin salo, murmushi ne ɗauke a kan fuskarta tace, "Ni ba Mace ce mai sauƙi da kowanne namiji zai samu a banza ba, ina da farashi mai yawa, idan har ka shirya nima a shirye nake. I will be with you whenever you want." Ta ƙare maganar tana lakutan mishi kumatu cikin salo da jan hankali, while tana wani banƙaro ƙirji cike da tsantsan duniyanci irin nata Lokaci ɗaya kuwa ta tsulmiya shi a wani hali, dama daƙyar yake iya riƙe kansa, da sauri ya kai mata cafka yana ƙoƙarin haɗa ta da jikinsa Sai ta dakatar da shi da cewa, "bamu gama magana ba fa, idan bamu gama ba babu abun da za ka samu a wurina." "Bani da matsala da kuɗi Baby, ko nawa ne zan ba ki, ki sanar da Ni farashin ki." Ya furta yana ci gaba da shafa mata jikinta "Kai za kayi min farashi, idan bai yi min ba zan iya neman ƙari." Hannu yasa a hankali ya soma ƙoƙarin zare mata rigan jikinta tare da yin murmushi, cike da farin ciki yace, "ke mai tsada ce a wurina ai, ko nawa ne kamar yanda nace zan iya ba ki, bani da matsala da kuɗi, kowanne tarayya da zamu yi I will give you 1m." "Wow!" Ta furta cikin zumuɗi da farin ciki, nan da nan ta sakar masa jikinta sabida bata da wani matsala kuma tunda ta samu abun da take so, dama a matse take tana bukatar namiji, lokaci ɗaya ta sauya mishi tunaninsa sabida shayar dashi zumar soyayyarta da tayi, gaba ɗaya ta gama fitar dashi a hayyacinsa sai sambatu yake mata, ga alƙawaruka da yake furta mata kala-kala, nan kuwa daɗi kamar ya kashe ta, ita kanta ta ji daɗin kasancewa dashi, don lokaci daya ta gane ɗan hannu ne Shima haka a fannin sa, already ya fahimci ƴar hannu ce itama, duk yanda aka yi sai da ta gama biye-biyen Maza sannan uncle ɗinsu ya aure ta, shi bai da matsala da wannan domin hakan kamar taimaka mishi tayi tunda ya same ta yanda yake so, itama ƴar hannu ce babu matsalar komai. Babu ƙarya ta sarrafa shi wanda bai taɓa jin wata Mace a tarayyan su ta shayar dashi wannan daɗin ba, gaskiya ita ta musamman ce domin ta kerewa dukkan Mata, har kukan daɗi sai da yayi domin daƙyar ya iya haƙura da ita, sai da asuba yayi sannan ya bar part ɗin, shima don yana tsoron Nawwara ta gane ba ya ɗakin ne shiyasa ya tafi, amma kuma gaba ɗaya ya gama firgicewa motsi kaɗan Arab yake gani da abubuwan da suka gudana a tarayyan su, fuskarsa gaba ɗaya ta nuna irin tsantsan farin ciki da annashuwan da yake ciki yau Su kansu su Jameema sun ga sauyi a tare da shi, sai dai duk tambayoyin da suka yi mishi bai basu wata ƙwakkwaran amsa ba Ce musu yayi, "kawai yau ɗin yana jin walwala ne sabida bai da matsalan komai." Arab na fitowa farin cikin sa ya ƙaru, lokaci ɗaya suka sakar wa juna murmushi yayinda ya kashe mata ido ɗaya yana wani lanɗe bakin sa, duk wani moment ɗinta a kan idanunsa ne, ko kaɗan ba ya ɗauke ido a kanta but komai yana yi da taka-tsan-tsan ne Ita kanta ta ƙi tafiya tana tare da su koda suka gama Breakfast, duk da tana ganin yanda Nawwara take wani shashshan mata ƙamshi tana wani shige ma Malik ɗin duk don ta nuna wa Arab iyayi da kisisina ita ga mai Miji, dariya kawai take yi a ranta tana cewa, "wawiya! Mijinki tuni ya daɗe da zuwa hannuna".           **********              Almost two days ɗin da suka yi suna tare da juna, kullum dare sai Malik sun kasance da Arab, lokaci ɗaya suka shaƙu sosai kamar sun daɗe da sanin juna. Koda zasu tafi kamar kar su rabu, barin ma Malik da ji yake yi kamar ya saka Arab a jaka ya gudu, dole ne ma ya dawo nan kusa domin su sake kasancewa da juna domin bazai iya jimawa ba tare da ita ba, tarayyan su yasa ya ƙara nutso a soyayyarta, ko a baya bai ji zai iya rabuwa da ita ba; bare a yanzu da ta shayar da shi madaran ƙaunarta. Yanzu ma bai yi ninyar tafiya ba don kwanan su uku a gidan suna tunanin Ko Senator zai dawo su gaisa, but har suka tafi bai dawo ba.               Kwana biyu kenan da tafiyan su babu labarin Senator Ƙasim, ita kanta Arab mamaki take yi wanne irin siyasa ne haka da bai da lokacin ta? Tunda ya aure ta bai taɓa bata haƙƙinta ba, to ina ya zauna ma bare wani abun ya haɗa su, ko dama haka ake yin siyasan basu da lokacin Matansu? Idan ko haka ne tabbas tana ganin ƙoƙarin Jameema, but ita ina zata iya, wlh da ace ba ta bin kowanne namiji babu abun da zai zaunar da ita a gidan nan tunda babu amfanin auren ma, duk da bata wani damu ba a ganinta rayuwarsa ne yayi ta zama, abun da take nema tana samu amma hakan bai sa ta yiwa Jameema maganar cewa da tayi nan da kwana biyu zai dawo ba, amma shiru kake ji, shiyasa tace mata, "ita ta ji shiru ko lafiya?" Jameema tayi murmushi tace, "kiyi haƙuri kin san halin siyasa, amma zai dawo kamar yanda yace ɗin, na san wani abun ne ya tsare shi." Taɓe baki tayi ko a jikinta, tausayin Jameeman ma take ji tunda a ganinta bata da wani wanda zai ɗebe mata kewa dole sai Mijin nasu, amma shi ta rayuwar shi yake yi, ya fifita siyasan shi a kan auren shi, wani abu ɗaya da Arab ta fahimta, tun kwanan da yayi da ita a kan gado ɗaya bai nemi komai daga gare ta ba, sai tayi tunanin tabbas ba shi da lafiya ne, kuma tana ji a jikinta haka ne don bata taɓa ganin namijin da ya kwana a gefen ta bai nemi komai ba, ita cikakkiyar Mace ce wacce babu namiji mai lafiyan da zai iya kwana da ita bai neme ta ba, sai dai ko idan bai da lafiya, ita ba irin Macen da za'a iya kawar da kai ba ne, shiyasa kawai ta share zancen bata ƙara tunanin dawowar shi ba ta shiga sabgar gabanta. Tana komawa ɗaki ta kira Besty ɗinta sabida baza ta iya zama a haka ba, gwara shi ya zo ya ɗebe mata kewa ko kuma Tariq, don wlh in dai zargin ta ya tabbata dole ne ta nemi mafita don baza ta iya ba, abun farin cikin ta ma babu matsi a gidan, don haka nan zata kawo su su riƙa shan soyayyar su babu ruwanta. Wannan shawaran shi ta yanke a ranta shiyasa ta kira Besty saboda tana kewar shi matuƙa, zata kira shi ya zo yayi mata sati biyu. Hankalinta kwance suke wayan tunda yayi mata alƙawarin zuwa nan da kwana biyu sabida ba ya gari ne, duk da bata ji dadi ba but haka nan zata jira shi har nan da kwana biyun. Daga nan wayansu suka ci gaba da yi duk batsa ne don basu da aiki sai waɗannan maganganun domin su kwantar wa junansu da hankali, har cire kaya Arab tayi suka sha video call, tsawon daren nan suna nan suna baɗalar su sai daga ƙarshe ta je tayi wanka ta zo ta kwanta ko rigan barcin ma bata samu ta saka ba yana gefen ta, illa abun rufa da tayi amfani dashi ta rufe jikinta, barci mai daɗi ya sure ta cike da mafarkin ana saduwa da ita. Ai kuwa can cikin dare ta soma jin ana laluban ta, a tunanin ta mafarki ne ga daɗin abun da take ji shiyasa take ta sake shigewa jikin wanda bata san ko waye ba, abubuwan da ake mata wani irin daɗi ne ke fizgar ta musamman da ta ji an saka mata yatsa a ƙasan ta, nan take ta farka ta sauke idanuwanta a kan.....  [12/08, 8:51 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/          *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA ASHIRIN DA BAKWAI* _______________Mamaki ne ya kusa kashe Arab ganin Jameema a jikinta, babu ko kaya tana mata murmushi, yadda ta shiga shock ne yasa ta kasa furta komai kuma ta kasa motsawa Ita kuwa Jameema fuskarta ɗauke da murmushi babu ko damuwa a tare da ita, illa ma shafa face ɗin Arab da tayi tana cewa, "na san za ki yi mamakin ganina a nan a kuma wannan yanayin ko? Ba abun mamaki bane A'isha domin na daɗe ina kwaɗayin ki, yau na kasa jurewa ne shiyasa na zo gare ki domin ɗauke miki kewar Mijinmu. Don haka ki kwantar da hankalin ki babu abun da zai same ki idan kika bani haɗin kai, ki bari mu more daren mu kinji ko?" Ta ƙare maganar tana sauke hannunta a saman ƙirjinta Ƙiris ya rage Arab ta hantsala ƙasa saboda yanda ta ja jikinta da sauri tare da mugun mamakin abun da ke shirin faruwa da ita, "kar dai ace Jameema ƴar less ce?" Bata kai ga samun amsar ba taji ta taro ta tare da matse ta a jikinta "Kar ki ji ma kanki ciwo a banza mana, A'isha na sanki na san ke wace ce, don haka don na nemi wannan ƙaramin abun ba laifi bane, bazan iya haƙura da ke ba ki bari kawai mu ji daɗin rayuwarmu sabida na san kina buƙatar namiji, but hanyar nan ta fi wacce kike bi daɗi da gamsarwa, ina tare da ke ki bari kawai mu ji daɗin rayuwarmu, zan ba ki duk abun da kike buƙata a duniyar nan, komai da kike nema za ki samu wlh, kawai ki aminta da Ni." Ko kaɗan Arab bata taɓa tsammanin haka daga gare ta ba, shiyasa duk ta ji zancen wani iri bambaraƙwai, domin bata saba haɗuwa da kalan su Jameema ba, musamman yanda ta hayayyaƙe mata a dole sai tayi amfani da ita ta ƙarfi da yaji, duk yanda Arab ta kai da iskancin ta tana matuƙar tsoron irin wannan rayuwar, ace Mace ta bi ƴar uwanta Mace don su ji daɗin rayuwa? To wanne irin daɗi zasu ji in ban da wahala? Ita a ganinta babu wani dadi da ya fi na Mace da namiji, ita ƙyama ma abun yake bata, musamman yanda ta ga ta haɗa jikinta da nata tana jagula ta, sai kawai ta ture ta tana miƙewa da sauri, gaba ɗaya ranta a ɓace yake duk da tana shakkarta amma hakan bai sa tace mata, "Ni sam ba na ƙaunar wannan rayuwar, don Allah ki fitar min a ɗaki ba na buƙata, iskanci na bai kai wannan wurin ba." Dariya Jameema tayi tana ƙoƙarin tasowa ta zo inda take Fahimtar hakan ne yasa Arab ta ruga aguje ta shige Toilet ta kulle kanta, jikinta sai rawa yake yi duk da taso ta ɓoye tsoro da firgicin da ta shiga, wai yau ita Mace take bi a kan lesbian? Kuma Macen ma Jameema, sam bata zata hakan daga gare ta ba, tana matuƙar tsoron irin wannan ɗabi'ar sabida ta sha jin yanda masu yi suke ƙare wa, duk iskancin ta bazai yiwu ace ta ba Mace kanta ba, to meye riban hakan? Wata zuciyar tace mata, "to amma ai ke kika ce komai za ki iya yi idan har za ki samu kuɗi?" Sai tayi saurin girgiza kanta kamar da wani take yi, a fili ta furta, "sam ban da wannan rayuwar, idan har in haɗa jikina da Mace ko a neme Ni ta baya wlh bazan taɓa yarda ba, haka kawai in kai kaina makasa? Ina sam ba mai yiwuwa bane na san ciwon kaina wlh bazai yiwu ba, ko nawa zata bani na rantse da Allah bazan yarda ba." Ta ƙare maganar tana sake danne ƙofan don gani take yi kamar Jameema zata buɗe ta shigo, duk da tana jiyo muryanta tana roƙon ta a kan ta buɗe, but tayi banza da ita sai ma jan tsaki da take yi, gaba ɗaya zuciyarta zafi take mata, duk wani ɓurɓushin girma da take gani na Jameema ya zube a nan take, "an yi Babbar banza, duk wayon ta ta ɓata shi a banza a hofi, ga ta kamar Macen ƙwarai ashe lamo tayi, Maybe ma Matan da suke shigowa wurinta duk neman su take yi, za'a rina wlh don koda ganin fuskar su tsinannu ne." Haka take ta sambatu ita kaɗai ta ƙi fitowa daga ban-ɗakin, sai da ta ji ta dena jiyo motsin Jameema sannan ta fito ta rufe ƙofan ta, riganta ta mayar ta zauna a gefen gado duk ta rasa abun da ke mata daɗi, dole ne ma tayi hankali daga yanzu domin an ce Mata masu irin wannan halin Mayu ne, ta san dole zata sake bibiyanta, sai ta ji duk gidan ya fitan mata a rai, to, mene ne amfanin zaman ta a gidan ne wai? Mene ne dalilin auren ta tunda Mijin bai taɓa kusantan ta ba? Sannan ba ya zama ma bare su haɗu, abu ɗaya ta san tana ƙaruwa da shi; shi ne kuɗi, wanda ta san tana samun su ba kaɗan ba, abun da yasa kawai baza ta iya barin gidan nan ba kenan Tashi tayi tayi wanka don da kanta ƙyamar kanta take ji, musamman idan ta tuna yanda Jameema take shafa ta har tayi ƙoƙarin saka mata yatsa a farji, sai tsigan jikinta duk ya tashi, sai da tayi wanka sannan ta kwanta, but ta kasa samun sukuni bare wani barci ya ɗauke ta, dole ta ɗauki wayanta ta hau online ta soma chart da Abokan iskancin ta, sannan ne fa hankalin ta ya ɗauke har ta manta abun da ke faruwa. Sai gab da asuba barci ya sure ta, ta sha barci kafin ta tashi don kusan ƙarfe 11 ta farka, wanka tayi ta shirya cikin riga da skirt, kayan sun zauna mata ɗas kuma sun yi mata kyau ba kaɗan ba, kwalliya tayi sannan ta yafa gyale a kanta ta fita, duk da bata yi ninyar fitan ba amma kasancewar yunwan da take ji yasa ta fita A falonta ta zauna don ta ƙi fita babban falo gudun haɗuwar ta da Jameema. Sai kuma ta miƙe ta shiga kichen ɗinta wanda bata taɓa amfani dashi ba, domin tunda ta zo gidan bata taɓa girki da kanta ba, komai yin musu ake yi ko'ina akwai masu aiki. Tana cikin ɓuruntu a kichen ɗin taji motsi, da sauri ta leƙa don a tunanin ta Jameema ce, don wlh shakka da tsoronta ne ya kama ta, tana gudun abun da zai sa ta ƙara kawo mata farmaki, sai dai akasin hakan ɗaya daga cikin masu aikin su ne. Sai ta sauke ajiyan zuciya tana kiranta. Tana zuwa tace mata, "ta haɗa mata Breakfast ta kawo mata bedroom ɗinta." Yarinyar tace, "ranki ya daɗe! Ai ga yi can mun haɗa muku komai a babban falo, kuma tun ɗazu Aunty Jameema ta bar gidan tace mu ajiye miki duk abun da kike so." Jin hakan yasa ta sake sauke ajiyan zuciya before ta wuce ba tare da ta sake furta mata komai ba. Kai tsaye falon ta fita sabida jin an ce mata babu Jameema a cikin gidan, sai ta kwantar da hankalin ta Ita kuma Yarinyar dama gyaran part ɗin ya kawo ta, kasancewar ta gyara ko ina sai bedroom ɗin Arab da ya rage mata, shi ne ta zo duba wa ko ta tashi sai ta shiga ta gyara. Shiyasa sai ta fara aikin nata kamar yanda ta saba Arab kuma na kan dainning a babban falo tana karyawa. Har ta gama babu Jameema shiyasa ta sake sakin jikinta, but bata zauna a Falon ba ta dawo nata, ta ɗauki waya ta ci gaba da latsawa. Daga ƙarshe da ta gaji ta koma cikin ɗakinta ta kwanta, babu abinda ke tayar da ita sai sallah, sai kuma da sukai waya da Ibrahim yake sanar mata, "gobe yana kan hanya." Ta ji daɗi sosai tunda gaskiya a matse take. Abincin rana ta ci ta sake dawowa ta kwanta, can anjima har barci ya fizge ta taji motsi, kafin ta tashi sai ganin Jameema tayi sun shigo tare da wasu ƴan mata biyu waɗanda a girme sun bata shekaru huɗu zuwa biyar. Sai kawai ta dauke kanta tana ɗaure fuska tare da miƙewa zaune Jameema kuwa murmushi tayi tace, "Barka My sweetheart, yau kin ƙi tashi da wuri na leƙo na ji ƙofan a rufe, ko duk tsoron nawa ne ya sanya ki hakan?" Bata kalle ta ba kuma bata ce komai ba illa sake tamke fuskarta da take yi Sai Jameeman tazo ta zauna a gefen ta tana kai hannu ta shafa mata fuska Da sauri Arab ta miƙe tana sakar mata harara da cewa, "meye haka don Allah? Kar ki shiga hurumin da ba naki ba..." Sai ta katse ta da cewa, "wa ya faɗa miki ba hurumina bane?" Tayi maganar da murmushi, sai kuma ta ƙara da faɗin, "A'isha guje-gujen ki ko ƙin amincewar ki bazai yi amfani ba, shiyasa na soma bin ki da lalama domin ki amince ta ruwan sanyi, idan kuma ba haka ba zan yi miki dole, ki kwantar da hankalin ki duk abun da kike so za ki samu daga gare Ni, zan ba ki komai da kike buƙata, kin ji na rantse miki, ina matuƙar ƙaunar ki bazan taɓa haƙura da ke ba." Cikin tsiwa da rashin kunya Arab ɗin ta nuna Jameema da yatsa, tare da cewa, "kar ki gaya min maganar banza a nan, ana yi dole ne? Na ce ba na buƙata bazan taɓa amincewa ba ko dole ne? Da Allah ki fitar min a ɗaki ko in shuka miki rashin mutunci, ƙiris ya rage in nuna miki ainihin kalata don wlh bani da mutunci ko kaɗan, kuma babu sanayya da zai sa in raga miki, ki fita nace." Ta ƙare maganar tana daka mata tsawa tare da nuna mata hanyar fita "Ni kike wa wannan koran?" Sai tayi dariya tana kallon ƴan matan da ke tsaye har yanzu basu ce komai ba, ta nuna musu Arab ɗin tare da cewa, "ku danne ta in nuna mata nima ainihin kalata."       Take kuwa suka bi umarnin ta, kafin Arab tayi wani motsi sun cafke ta sun ɗaura ta a gadon da ƙarfi da yaji, duk yanda ta so ta ƙwace amma inaa ta kasa, domin ƙarfin su ba ɗaya ba tunda sun fi ta girman jiki Haka tana ji tana gani suka soma tuɓe mata kayan jikinta. Lokaci ɗaya Arab ta gama ruɗewa, ƙiri-ƙiri tana gani za'a yi mata fin ƙarfi, shiyasa cikin sauri batare da ta nuna ta karaya ba tace, "wlh if you do anything to me sai na tona miki asiri, sai na nuna wa duniya abun da kike yi, sai nayi sanadin da auren ki zai mutu, kuma bazan taɓa ba ki haɗin kai ba." "Kar ki damu Sweetheart, ban damu da haɗin kanki ba kinji?" Jameema tayi maganar tana dariya kaɗan, kana ta tashi itama ta cire kayanta ta hayo kan gadon Ganin da gaske dai murƙushe ta zata yi sai ta fashe da kuka, kukan baƙin ciki tunda tana gani wata ƙatuwa zata ƙwaƙule ta bata da hanyar ƙwatan kanta, ga shi gaba ɗaya sun tale ta sun riƙe ta gam ko motsin kirki ba ta iya yi Hannunta Jameema ta sanya a kyakykyawar fuskarta da ta soma jiƙewa da hawaye, "alamu ya nuna kina da taurin kai A'isha, da kin amince da buƙata ta da duk hakan bata faru ba, amma kuma duk da haka dole ne ki shigo cikin mu, kina ga zan iya ƙyale ki ne bayan yanda Allah yayi miki surar nan mai ɗaukar hankali? Uhm bazai yiwu ba, A'isha kin haɗa komai da komai a rayuwa, daga yanzu kin zama tawa Ni Ni kaɗai, babu mahalukin da ya isa ya raba mu, kuma gidan nan kin shigo ta kenan babu fita har sai kin zama ƴar hannu." Ta kwanta a jikinta tare da ci gaba da shafa ta Ita Arab tsaban baƙin ciki ne yasa ta kasa magana, kukan ma ta dena sai hawaye da ke fita a idanunta, nan da nan sai idanun suka sauya kamanni abun ka da manyan idanu tuni sun ƙara luhu-luhu da su sai hakan ya ƙara musu kyau ainun. Tana ji tana gani take ta shafa ta duk ta inda take so, tana sarrafa ta babu yanda ta iya, musamman wurin da ta zo ƙwaƙule mata ƙasan ta, sai ta ji kamar tana mata da mugunta, duk iskancin ta since after fitan budurcinta yau ne kaɗai zata iya cewa ta ji zafi da raɗaɗi a ƙasan ta don wani yana kusantanta. Tana ji tana gani tayi bidiri a kanta ta gama bata da ƙarfin ƙwatan kanta, domin koda basu riƙe ta ba yanda jikinta yayi laƙwas baza ta iya ƙwatan kanta ba Jameema sallaman ƴan matan tayi tace, "su je sai zuwa gobe zasu sake haɗuwa, yau dai tana tare da Arab." Haka suka fice bayan tayi musu kiss one by one. Ita kuma sai ta mayar da hankalinta a kan Arab ɗin tana kai mata sumbata a kumatun ta tare da ɗaura hannayen ta saman breasts ɗinta tana matsawa cikin salo da jan hankali, da murmushi a fuskarta tace, "My sweetheart gaskiya kina da daɗi, ko Ni na shaida hakan, yanzu ba a son ranki nayi ba amma ji be yanda kike zubar da ruwa." Sai ta kai hannunta ta shafa mata ƙasan ta tana sake cusa yatsarta ciki tare da caccaka mata, "I love you! I don't feel I can get tired of you, we are here together until tomorrow, yanzu bamu da wani aikin da zamu riƙa yi kina nan tare da ni koda yaushe." Sai ta ƙara haye wa kanta ta danne ta tare da ƙoƙarin haɗa bakin su wuri ɗaya while tana mirza jikinta a nata Amma sai Arab ɗin ta tofa mata yawu a fuska cike da tsantsan tsanarta da fushin da ya turniƙe ta tace, "kutmar uban ki da ke da muna taren, wlh if you don't lift me up I will kill you! sai na kashe ki dan uwar ki". Dariya Jameema ta saka saboda ganin yanda Arab take kiciniyar ƙwace wa amma ko gezau ta kasa, to ƙarfin su ba ɗaya ba, ita Jameema da take ƙatuwar Mace mai shekaru taya zata haɗa ƙarfin ta da nata? Shiyasa take ta mata dariya tare da ƙara matse ta ta kai bakin ta ta haɗe da nata, duk yanda Arab ta ciccije ta but ta ƙi sakinta kamar wata mayya, da alamu ma cizon ba ya tasiri a kanta don sai da ta manne bakinsu sosai ta yanda baza ta iya ko motsi ba, sai ta soma mata tsotso cike da mugunta don ladabtar da ita, domin ta kula idan bata nuna mata ainihin kalanta ba ta koya mata hankali baza ta saduda ba. _Na gaji tunda ba kwa comments sosai, zamu sake zuwa hutu, sai kun ji Ni._ [14/08, 9:17 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍       *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/          *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA ASHIRIN DA TAKWAS* _______________Ba ƙaramin jigata Arab tayi a hannun Jameema ba, yau ta bambance aya da tsakuwa, don yau Mace ta wahalar da ita fiye da zaton ta, duk taurin ran Arab sai da ta sha kuka sosai Ga ta kamar mayya ta ƙi barin ta ta huta ko na misƙala zarratan, tsawon lokacin nan tana kanta tana yin duk abun da ta so da ita Tun Arab tana da ƙarfin jayayya da son ƙwace kanta, har ta gaji ta haƙura ta zura wa sarautar Allah ido, kukan ma ta dena yi sai hawaye, hawayen baƙin ciki da ke zuba a idanunta. Tana ga tamkar Jameema ba Mutum bace saboda yanda take mata ko gajiya ba ta yi, ga shi ba daɗin abun take ji ba amma babu halin ƙwatan kanta Ƙarshe ko jirgawa kusa da ita ta ƙi yi, a haka suka kai dare ko sallah basu yi ba Ita Arab baƙin ciki da ƙunci ya hana ta roƙonta a kan ta barta zata yi sallah Ita kuma dama Jameema ba ta yin sallan ko kaɗan, bata damu tayi ba. Sai daga baya ne tace mata, "ta tashi ta shiga toilet tayi wanka ko zata ji dadin jikinta." Sai ta shafa fuskarta tare da cewa, "kyawun fuskarki ya fi komai bani sha'awa a jikinki Baby, bari in je in samo mana abinci, ki shiga toilet ki tsaftace jikinki ko zamu fi jin daɗin harkan, na san kin sha wahala kina buƙatar gashi." Lumshe idanunta Arab tayi tana zub da hawayen wahala, motsi kaɗan azaba take ji daga ƙasanta sabida mugun ƙwaƙulan da Jameema tayi mata "Ki tashi mana Baby, ko kin fi son in shiga in Yi miki da kaina ne?" Wani mugun kallo ta watsa mata, sai dai ta kasa yin magana sabida bata da ƙarfin da zata iya buɗe baki ta furta wani word, bata da karsashin yin hakan, tarin tsanar Jameeman ma bazai barta ta sake furta wata magana ba, domin ji take yi tamkar ana soka mata wani ƙarfe daga ƙahon zuci saboda ƙuncin da ya taru yayi mata yawa Itama kuma tuni ta miƙe sabida ta san baza tayi mata magana ba, dariya kawai tayi har ta kai bakin ƙofa bayan ta saka doguwar riganta, sai kuma ta dawo tace, "gwara ma ki dena wannan taurin kan ki sallama wa kanki, domin wahala za ki sha wlh, Ni ina tausaya miki ne saboda ina ƙaunar ki, amma dole ne kiyi biyayya idan kina son jin daɗi a gidan nan, if not kuma..." Sai ta taɓe bakinta ta kwashi wayoyin Arab ɗin tare da system ɗinta zata fice A nan ne Arab tayi ƙarfin halin buɗe baki tace, "ina za ki je min da wayata? Ki dawo min dashi, wlh idan har kika bari na samu kuɓuta a hannun ki sai kin yi dana-sanin sanina a rayuwarki, sai kin sha mamakin abun da zan miki, muguwa azzaluma kawai..." "Shiiii! Ya isa haka nan, har yanzu bakin ki bai mutu ba ko? Shikenan zan yi maganin ki." Sai ta juya ta fice fuskarta babu walwala. Tana jin yanda Arab ɗin take ta zaginta tana tsine mata albarka amma bata kula ta ba, sai da ta rufe ƙofan ta bar key ɗin a ciki sannan ta wuce Arab kuma sai ta fashe da kuka, kuka tayi sosai kafin tayi yunƙurin tashi daga kwancen da take, daƙyar ta miƙe zaune tana matsan hawaye zuciyarta na ƙuna, ji take yi da zata samu Jameema wlh babu abun da zai sa bata kashe ta har lahira ba, sai dai a kama ta a hukunta ta, har addu'a take yi Allah ya dawo da Senator Ƙasim ko zata samu kuɓuta daga sharrin Matar nan... daƙyar ta rarrafa ta nufi toilet sabida zafin da take ji, ruwa ta haɗa mai zafi ta shiga ciki ta gasa jikinta, ta jima tana wankan kafin ta fito A lokacin ne Jameema ta shigo ɗakin ɗauke da Plate a hannunta, still fuskarta babu walwala tamkar bata taɓa dariya ba, ta kalli Arab ɗin tace, "ki gaggauta cin abincin nan kafin in dawo, don in kika sake kika ce za ki yi min gardama wlh yau sai na wahalar da ke fiye da yanda nayi miki, sai na gana miki azaba." A fusace Arab tace, "in kin fasa kin raina uwarki da ubanki, don Allah kar ki bar Ni da rai kinji ko? Kuma ba ki isa ki ƙara min komai ba domin bazan taɓa bari ba." Ajiye mata Plate ɗin tayi ta juya ta fice ba tare da ta bi ta kanta ba, kuma ta rufe ta tabar falon Arab sosai ta zuciya itama, tana tunanin matakin da zata ɗauka a kan Matar nan, idan bata yi mata hauka-hauka ba tabbas zata ci galaba a kanta, dole ne ta kufce mata. Abincin ta ɗauka ta ci sabida yunwan da take ji, cikin sauri-sauri ta shirya cikin riga da wando na barci masu kauri, sai ta shige Toilet ta rufe kanta a ciki, baza ta sake bari ta ci galaba a kanta ba dole ne ta gudu. Tana nan a cikin toilet ɗin taji motsinta, sai da cikinta ya tsarga na tsoro, amma ta daure tayi shiru tana jin bugun da Jameeman take yi, sai kuma can ta ji shiru ashe ta je ɗauko safayan key ne Haka ta zo ta gwada ƙofan toilet ɗin bai buɗe ba, kasancewar tabar key a ciki bazai yiwu wani key ɗin ya shiga ba, sai tayi dariya tace, "ba ki sanni ba ko? Gwara ma ki fito tun kafin in fito da ke da ƙarfi, haɗuwar mu baza tayi kyau ba." Arab tana jinta ta ƙi magana tamkar ba ta ciki, nan kuwa tana nan zaune cikinta yana ta ɗuran ruwa, ta soma tsorata da Matar nan gani take yi komai zata iya aikata wa, amma hakan bai sa ta buɗe ƙofan ba Ita kuma Jameema tuni ta wuce part ɗin ta, a cikin masu aikin gidan Maza ta saka ɗaya tace mishi, "ya je ya nemo mata masu ɓalla ƙofa." Batare da ta damu da daren da yayi ba Yace, "ai shima zai iya in dai kwance abun ƙofan ne." Ai kuwa tare suka dawo ta ba shi umarnin cire wa Haka ya soma kwance abun cikin ƙwarewa, nan da nan sai ga shi ya buɗe Godiya tayi masa tace, "ya tafi." Yana fita ta buɗe ƙofan ta shiga sai ga Arab a inda take tsaye ko motsi ta gaza Amma Jameema na kai hannu zata taɓa ta sai ta kai mata naushi a fuska da iya ƙarfin ta, ta nemi arta wa a guje but tuni Jameema ta riƙo ta "Lallai yarinya kina son wahalar da Ni ko?" Sai tayi ƙwafa kawai ta jawo Arab ɗin tayi mata ɗaukar jarirai ta jefa ta a saman gado, duk yanda Arab ta so ƙwace wa but bata ba ta damar hakan ba, kakam ta danne ta sannan ta ɗauki waya tayi kira, babu jimawa aka ɗauka tace, "Ramcy kuna ina ne?".... Ban ji mai aka ce a can ɓangaren ba sai ta sake cewa, "ok ku taho gaba ɗayanku ku same Ni ɗakin Amaryata, yau zamu yi mata cin hauka ne zamu koya mata hankali, tana da taurin kai." Sai kuma tayi dariya tare da kashe wayan. Kallon Arab tayi da ke zaginta tana ta ƙoƙarin ƙwacewa, bata kula ta ba har ta gama hargagin ta tayi shiru don dole Sai ga wasu ƴan mata su huɗu sun shigo dukkan su babu mai kayan kirki a cikin su "Kamar kuna hanya? I see you are in a hurry." Jameema said looking them Dariya Ramcy tayi tace, "ke kuwa taya zamu yi sanya bayan mun san ƴar kyakykyawar nan ne abun harin mu? Ba ki san yanda muke kwaɗayin ta bane tunda kika furta hakan nace su taso mu zo, already muna gidan su Salma ai." "Ai kuwa yau sai kun more da ita saboda ina son koya mata hankali, nan gaba idan an ce tayi jayayya da Ni baza ta iya ba, ta ƙi bada kai bori ya hau gwara ku koya mata hankali na rana ɗaya don ita ɗin tawa CE Ni kaɗai, bazai yiwu ina sharing ɗin ta ba." Dariya suka yi suna cewa, "an gama ranki ya daɗe! Duk yanda kika ce haka zamu yi". Daga nan kowaccen su ta tuɓe ta nufo kan gadon. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️          *ZARIA CITY*      "Wai har yanzu wayan Arab bai shiga ba?" "Wlh kuwa, ga shi nan ina ta try ni har na gaji ma." Ummu ta furta hakan tana ajiye wayan Zahra da ke kallonta, sai ta taho ta zauna a gefen ta tana ajiye tea cup din da ke hannunta, tare da furta, "to ko dai babu lafiya ne? Kinga fa ita tace mana zata zo tun ana kwana biyu but ga shi gobe Inna zata dawo amma shiru." "To Allah kaɗai masani, amma mu bari zuwa gobe idan bata zo ɗin ba ta yiwu akwai matsalar kenan, Allah yasa lafiya dai." Zahra ta amsa da Amin tana ɗaukar tea ɗinta ta soma sha. Tare da sauya hiran da suke yi yawanci duk a kan dawowar Innan ne a gobe, da kuma abun da zasu girka mata Sai da suka raba daren kafin suka kwanta. Washe gari suka tashi suka sake gyara gidan fes. Sannan suka shirya da zummar fita kasuwa domin siyo abubuwan da zasu buƙata na girkin A lokacin ne Firdausi ta zo tare da jaririn ɗanta Khalil mai sunan Babansu, dayake sunan shi aka saka Sun yi murnan ganinta shiyasa suka daka tsalle suka rungume ta Ummu ta amshi Khalil ɗin tana mishi kiss tare da cewa, "welcome My Dady, fatan ka zo lafiya?" Zahra kuma tace, "Aunty yanzu fa muke shirin fita, mun yi tunanin ma baza ki zo ba." Murmushi Firdausi tayi tace, "mai zai hana? Ai ko datsa Ni Inna zata yi sai na zo wlh." Dukka dariya suka yi Sai ta sake cewa, "ina Autan? Ko bata zo bane ita?" "Wlh kuwa, kuma wayanta kwana biyu ba ta shiga bamu san dalili ba, I thinks matsalar network ne, amma jiya da dare a kashe wayan, yau ma mun gwada still a kashe." Ummu ta bata amsar hakan "Allah Sarki Auta! Allah yasa dai lafiya babu wani abu, koda yake haka aure ya gada ai, ku ma shiyasa nake muku fatan ku samu Miji nan kusa kuyi aure ku huta, wlh na ji daɗin auren Auta don ban taɓa tunanin zata yi aure yanzu ba, sai ga shi ta bamu mamaki." "Hmm aunty kenan, mu ma mun kusa auren nan fa, jiran Inna kawai muke yi ta dawo a tsayar da maganar, kar ki damu mu ma muna hanya." Cewar Zahra tana wucewa wurin fridge ta ɗauko mata drinks Firdausi tace, "to Allah yasa, na yi farin cikin jin hakan wlh, gwara ku dena biyewa Inna ku samu Miji kuyi aure shi ne mutuncin ƴa mace, yanzu karatun ma ai kun kusa gama wa ƙariso ne." Ummu tace, "Haka ne, watanni suka rage mana yanzu." Sun ɗan taɓa hira kafin suka ce, "zasu shiga kasuwa su siyo abubuwan da zasu buƙata." Firdausi tace, "to su tafi kawai zata tsare gidan." Tare da Khalil suka wuce Yaron yana hannun Zahra a yanzu, while Ummu kuma tana tuƙi suka bar gidan. ✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️              *KANO STATE*          Arab bata sake sanin inda kanta yake ba tunda ƴan matan nan suka soma bidiri a kanta, tuni numfashin ta ya ɗauke daga gangan jikinta bata farka ba sai washe gari, washe garin ma kusan ƙarfe goma na safe sannan ta soma dawowa cikin hayyacin ta, sai dai ta kasa tantance mai ke faruwa da ita saboda tsaban wahalar da ta sha, ta fi awa ɗaya a kwance duk da tana farke ne but ba ta gane komai, ji take yi kamar ba a duniyar take ba sabida yanda komai nata ya sauya jikinta kamar ba nata ba duk yayi tsami, ga azaban da ke ratsa ta shiyasa ta dena gane komai. Sai daga baya ta soma dawowa dai-dai har tayi yunƙurin miƙewa zaune, kuka kawai take yi a wannan lokacin tana ta furta, "ta shiga uku!" Ji take yi kamar ana ɗaɗe mata ƙasanta sabida zafi, da sauri tayi yunƙurin miƙewa domin ta shiga toilet sabida fitsarin da ya matse ta, daƙyar ta iya ɗaga ƙafafunta tana yi tana kuka wi-wi, haka ta kai kanta cikin Toilet ta haɗa ruwa ta shiga, ta jima a cikin ruwan tana ta gasa jikinta amma ji take yi kamar an yi mata amfani da barkono tsaban azaban da ke shiganta, babu tantama ma sun zuba mata barkono don yanda take jin azaban ya wuce misali, shiyasa ta dinga leƙa ƙasanta tana ƙara fashewa da kuka. Sai da ta gaji da zaman sannan tayi wanka ta fito a daddafe, zama tayi a gefen gado ko towel bata sa ba, har yanzu kukan take yi idanunta a kan ƙofa, ko bata taɓa ƙofan ba ta san a kulle ne, babu yanda zata yi ta fita, sai ta kifa kanta a saman gadon ta ci gaba da rera kuka, shikenan ta kawo kanta mahalaka, taya zata yi ta kuɓutar da kanta? Matar nan bata da imani wata rana kashe ta zata yi. Ko kaɗan ba ta gajiya da kukan domin ta kasa yin shiru, tun tana yi da hawaye har ta koma jan numfashi kawai take yi tana gurnanin kuka, ga yunwa da ke addabar ta kamar zata mutu, tana riƙe da cikinta ta rarrafa ta ciro kaya ta saka a jikinta, riga da wando na fakistan ta saka, a nan ta hangi abinci an ajiye mata a can ɗaya side na gadon, da sauri ta nufa ta ɗauka ta soma ci. Sai da ta gama sannan ta kwanta ta rufe idanunta cikin ƙunci, fatan ta Allah yasa kar Jameema ta sake dawowa, idan ta dawo mutuwa zata yi.          **********       A wannan lokacin kuwa Ibrahim ya zo gidan, duk da ya kira wayan Arab koda ya zo garin Kano, amma bai samu ba, dayake ya san kwatancen gidan shiyasa da tambaya ya kawo kanshi, sai dai koda ya buga ƙofan mai gadi ya fito suka gaisa, yace mishi, "wajen Arab ya zo." Mai gadi yace, "Arab kuma? A nan gidan?" "Eh Arab Amaryan gidan nake nufi." "Au too. Ai kuwa ba ta nan, tayi tafiya ita da mai gidan." Da mamaki Ibrahim yace mishi, "but mun yi magana da ita ta san da zuwana fa, idan zata yi tafiya ai baza ta gayyato Ni nan ba." "Ka ga Malam tayi tafiya nace maka, ko zan yi maka ƙarya ne? Jiya da dare suka yi tafiya da Alhajin, sai dai ka je ka dawo duk sanda itama ta dawo gidan." Mai gadi ya furta tare da juyawa ya shige gidan, don dama haka Jameema tace mishi ya riƙa faɗa duk sanda wani ya zo da zummar neman Arab, yace musu, "ba ta nan sun bar ƙasar ma." Yace, "to shikenan an gama ranki ya daɗe!" Bai tsaya yin jayayya da ita ba tunda ba hurumin shi bane; bare kuma yana samun kyauta a wurin ta         Shi kuma Ibrahim yana tsaye a wurin ya kasa tafiya, sai kiran wayan Arab yake yi but a kashe ake ce mishi. Dole da ya gaji da tsayuwa ya tafi tunda ba shi da yanda zai yi.              **********      Tun safe Jameema ta bar gidan shiyasa Arab bata ganta ba, ga ta tana kulle a ɗaki babu inda zata iya zuwa, tun karyawan safe bata sake saka wani abu a cikinta ba, yunwa ya ci ya cinye ta amma babu Jameema babu labarin ta, duk da ba ta ƙaunar zuwanta amma baza ta iya zama da yunwa ba Tana nan kwance daƙyar take iya numfashi tsaban yunwa ya galabaitar da ita, ba abun da take yi daga tunani sai kwanciya sai shiga toilet. Ga shi har yamma tayi ana shirin magriba, can ta ji kamar motsi a Falon nata amma bata tashi ba tana kwance sai ma rufe ido da tayi kamar tana barci Jameema ce ta shigo, domin dawowarta kenan da wasu ƴan mata su biyu, tana shiga part ɗinta ta bar su a can sai ta fito ta nufi dainning aria, tana tune da Arab da ta barta a ɗaki a kulle ba'a bata abinci ba, kuma tayi ma masu aikin gargaɗi, "kar su sake shiga part ɗin, idan tana buƙatar su shiga ita da kanta zata neme su," shiyasa suka bi umarninta basu shiga ba, sai yanzu da ta dawo ta sa ɗaya ta haɗa abinci a kan faranti, bayan ta gama sai ta amsa ta wuce dashi sashin Arab. Tana buɗe ƙofan ta hange ta a kwance tamkar mai barci, itama a tunaninta barcin take yi shiyasa ta ajiye farantin a ƙasa, kana ta zauna a gefen gadon ta soma tashin ta Arab tana ji amma tayi biris da ita, sai can daga baya sannan ta buɗe idanunta da suka gama canzawa sabida yunwa da damuwar da ta ɗaura wa kanta "I'm sorry Baby, kiyi haƙuri na manta na bar ki da yunwa kin sha wahala. I'm so sorry." Tayi maganar cike da tausayinta tana shafa mata fuska har zuwa goshinta inda kwantaccen gashin kanta ya kwanta a wurin Mayar da idanuwanta tayi ta rufe bata ce mata komai ba, kuma alamu ya nuna baza tayi maganar bane, amma kuma yadda fuskarta ta nuna tana cike da tsantsan tsana da kuma haushin Jameeman Ita kuwa bata damu ba sai murmushi da tayi, tare da cire hannunta daga goshinta tana cewa, "ga abinci nan ki ci zan dawo yanzu." Bata jira cewarta ba ta miƙe ta fice bayan ta datse ƙofan Kamar baza ta tashi ba tun bayan fitan nata, sai dai kuma ta miƙe ta sauka ƙasa ta soma cin abincin cikin sauri sabida azaban yunwar da take ji, zuciyarta na cinkushe da baƙin ciki da tunanin mafitan abun da yakamata tayi, bazai yiwu ta dauwama a haka ba dole tayi wani abu... Tana nan zaune bata motsa ba sabida tunanin da ya ɗauke mata hankali, sai ji tayi an buɗe ƙofan, ta bi wurin da kallo suka haɗa ido da Senator Ƙasim, da sauri ta miƙe har jikinta na rawa wajen nufan shi, tana zuwa ta rungume shi tare da fashewa da kuka Hannunsa ya ɗaura a saman kanta alamun rarrashi tare da ɗago kanta yana kallonta yana mata murmushi A lokacin Jameema ta shigo cikin ɗakin itama tana zuba nata murmushin tare da cewa, "Alhaji kaga yanda take ko? Ta ƙi kwantar da hankalinta bare ta bada haɗin kai, maybe idan kayi mata bayani zata fahimta." Wannan kalaman na Jameema su ne suka sa Arab ta kasa furta komai, tayi shiru tana kallonta tare da tunanin ma'anar maganar nata While shi kuma hannun Arab ɗin ya kama zuwa bakin gado ya zauna, itama ya zaunar da ita a gefe, kana ya kalli Jameema yace, "itama ta zauna." Zama tayi a stool ɗin gadon tana kallon Arab Haka itama ɗin kallon nata take yi tana tunanin irin makircin da zata lanƙaya mata, don da alamu ta soma gane me Jameeman take nufi, ko ma me zata faɗa sai ta tona mata asiri a yau ɗin nan, zata san ta taɓo ta "A'isha." Senator ya kira sunanta yana kallonta Sai itama ta mayar da hankalinta a kanshi batare da ta amsa ba tana shirin jin ta bakin shi Yace, "a ganin ki mene ne dalilin da yasa na aure ki ko? Na san wannan tambayar yana nan a ranki duk da ba ki fito fili kin faɗa min ba, amma na san dole za ki yi tunanin nan; duba da yanda na ajiye ki a gidan bani da wani lokacin ki." Murmushi yayi before ya ci gaba da cewa, "auren ki da nayi yana da manufofi da dama a wurin mu; don bazan ce manufa kaɗai ba, amma dole za ki ji wasu a yanzu wasu kuma sun girmi tunanin ki. A cikin rayuwar siyasata dole zan buƙace ki domin kai ga ci, Mace irin ki muke buƙata sai aka yi Sa'a ke ce wacce tayi dai-dai da kwatancen da Malamina yayi min, na aure ki ne ba don komai ba sai don cikan burina na siyasa, tun lokacin da aka aura mana aure na sake ki domin ba ki zo gidan nan da igiyoyin aure na ba; sabida ba a buƙatar kasancewar mu a ma'aurata, don haka ko mai za ki gani ki kwantar da hankalinki idan har za ki yi mana biyayya, ko nawa ne zan iya biyanki ko mene ne kike so, buƙata kawai kiyi mana biyayya, na san Matata ta fara biyan buƙatarta a wurinki kuma kin gane manufarta, haka nima zan riƙa biyan buƙatata ta baya( Homosexual/Luwaɗi) a duk sanda nake so, don haka sai ki shirya don ko da amincewar ki ko babu zamu yi abun da muke so da ke; tunda na siye ki ne." Tunda yake maganar; bakinsa kaɗai take kallo har ya dire zancen nasa ta kasa furta wani word; sabida gani take yi kamar a mafarki ne tsaban yanda maganar tayi mata wani irin duka, ta hautsina mata duk wata natsuwa nata, ta sanya mata firgici gami da kaɗuwa; wadda ko a fuskarta kaɗai zaka tabbatar da halin da take ciki. [16/08, 10:05 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/          *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA ASHIRIN DA TARA* _______________Har suka ƙarike maganganun su suka tashi zasu tafi bata furta komai ba. Sai da ta tabbatar zasu bar ɗakin sai tayi wuff ta miƙe kamar wata mahaukaciya, hawaye ke zuba a idanunta jikinta na rawa ta zube a gaban su, cikin muryan kuka tace, "don Allah kuyi hakuri ku bar Ni in tafi bazan iya wannan rayuwar ba, ku nemi wacce zata iya Ni bazan iya ba." Dariya suka yi su dukka While Senator yace, "bayan duk sonki da kuɗi ace wani abin ya gagare ki? Na sanki fa sosai kuma na san yanda kike matuƙar ƙaunar kuɗi, ɗan wannan abun shi ne baza ki iya ba? Kar ki manta zamanki billonia a ɗan ƙanƙanin lokacin nan mafarkin ki zai cika, mai kike tsoro ne? Kuma batun mu sauya wani bazai taɓa yiwuwa ba, kin san sirrinmu baza ki taɓa fita a gidan nan ba, zan yi magana da masu tsaron gidan babu ke babu fita, don haka kiyi shawara rayuwarki ko kuma kuɗi. Mu je Hajiya." Yayi maganar yana kallon Jameema. Kana suka fice a ɗakin suka barta a nan Sai ta kwatsa ihu tana faɗin, "na shiga uku Ni A'isha! na kawo kaina inda zan kashe kaina da kaina." Sai kuma ta tashi cikin rawan jiki sabida ganin ƙofan a buɗe, bata yi wata-wata ba ta fice da gudunta, tana taɓa ƙofan falon nan ma a buɗe ta ji, sai ta fice da gudu jikinta na rawa sosai, har zata sauka kan benen sai ta hango su a ƙasan falo suna magana, sai kuma ta ga shi ya nufi ƙofan waje riƙe da waya, ita kuma Jameema ta bi hanyar part ɗinta, da sauri ta gangara ta sauka itama ta bi bayansa, tana ganin ya nufi haraban gidan yana waya, ita kuma sai ta lallaɓa ta jikin flowers tana ta tafiya a duƙe a hankali yanda baza a ganta ba, duk da akwai duhun dare amma gidan tarwai yake da fitilu masu haske, still jikinta sai rawa yake yi duk a tsorace take, burinta kawai ta samu kuɓuta daga gidan nan. Tana jin sanda ya gama wayan ya soma kiran securityn gidan har mai gadi, dole ta dakata sabida ganin sun nufo wurin, kuma idan tace zata yi ƙoƙarin fita dole zasu ganta sabida ta kai ƙarshen flowers ɗin. Daga inda take tana jin maganganun da yake faɗa musu Yana basu umarnin, "kar su bari ta bar gidan, idan suka bari ta bar gidan daga yau kashin su ya bushe." Sai da ya ja ma mai gadin kunne domin shi ne a bakin ƙofa Mai gadi yace, "an gama ranka ya daɗe! Yanzu ma zan soma aiki na, babu mai shiga da fita sai da iznina domin kwaɗo zan sa a ƙofan." Jin hakan shiyasa ta lumshe idanunta tana sake buɗewa tana kallon tazaran inda take da Gate ɗin gidan, tabbas idan ta bari ya sallame su bata bar gidan nan ba shikenan kuma bata da damar fita, gwara tayi shahada idan Allah yasa zata iya tsallakewa. Shiyasa ta fito a guje ta nufi ƙofan fita, zuciyarta na wani irin tsalle da bugawar da take tunanin ƙiris ya rage ta fito daga ƙirjinta, tamkar zata ci kai sabida irin gudun da ta kwasa a wurin Tuni sun hange ta. Nan da nan Senator ya basu umarnin, "su kama ta kar su bari ta fita." Hankalinsa a matuƙar tashe don ba ya fatan ta bar gidan basu kama ta ba Tuni sun bi umarninsa daga su har karnukan gidan suka bi bayanta Sai da ta kai bakin ƙofan Gate ɗin tayi wani irin zamewa fuskarta ta bugi jikin Gate ɗin. Bata tsaya tunanin wani abu ba bare buguwan da tayi, burinta kawai ace ta fice daga gidan, tuni ta saka hannu ta buɗe ƙofan tayi wuff ta fice. Gudu take yi kamar zata tashi sama, gudun ceton rai. Ko waiwayan bayanta ba tayi duk da tana jin gurnanin karnuka a kusa da ita, amma inaa ta ƙi tsayawa da iya ƙarfin ta take gudun Ga layin masu kuɗi ne babu kowa, sai haushin karnukan da suke biye da ita da kuma na cikin gidan mutane, garin yayi duhu sosai duk da akwai hasken fitila na sauran gidaje da ya haska wurin Wani siririn hanya ta gani ta shige da gudunta, nan da nan ta ɓilla ta wani ƙaton kwalbati, bata tsallaka ba sai ta bi hannun dama, juyawa tayi ta ga basu ɓullo ba sai ta faɗa kwalbatin kawai ta ɓuya, hannunta duka biyu a bakinta ta danne saboda nishin da take saki, ƙarfin nishin dole ne zai tona mata asiri, shiyasa ta ɓame bakin tare da runtse idanu; zuciyarta na wani irin bugawa tamkar zata faɗo ƙasa saboda tsoron kar su ganta, ga numfashinta kamar zai cire daga jikinta sabida yadda ta liƙe bakinta magudanan iska ba ya shiganta sosai Ai kuwa suna ɓullo wa wurin karnukan suka tsaya suna ta haushi mai firgitar wa. Su ma tsayawa suka yi Ogansu na cewa, "duk yanda aka yi tana wurin nan dole mu bincika kafin mu bar wurin..." Wayansa da tayi ƙara shiyasa ya dakata daga maganar ya ɗauka, "Hello Ranka ya daɗe!" Dayake a handsfree ya saka shiyasa maganar Senator Ƙasim ya fito duk suna ji; har Arab da ke cikin kwalbati ta kasa motsawa tsaban yadda ta tsorata jikinta nata rawa Tana jin muryan shi yana basu umarnin, "duk inda take su kamo ta, kar su bari ta bar garin Kano basu dawo da ita cikin gidan shi ba, and duk yanda zasu yi su tura wasu su riga ta zuwa can gidan su, tana zuwa don't let her into the house su kama ta..." Iya abun da ta gama ji kenan ta soma rarrafe a cikin kwalbatin, bata damu da irin abun da zai same ta ba, burinta kawai ta tsira, sai da tayi ɗan nisa kaɗan kafin ta fito ta ruga aguje, haka ta dinga canza hanya har sai da tayi nisa daƙyar take iya ɗaga ƙafarta tsaban galabaitar da tayi, a wani lungu ta rakuɓe inda baza a iya ganin ta ba, dirshan ta zauna a wurin tare da dafe ƙirjinta tana ta faman haki, har ƙwallan wahala tayi tsaban jigata, sai da tayi ta ƙaƙarin amai kamar zata amayar da abun da ke cikinta, amma babu abun da ya zuba sai yawu, ga idanunta da suka kaɗa suka yi jawur. Daga ƙarshe kwanciya tayi a wurin tana jin duniyar tana juya mata; domin tunda take bata taɓa ganin bala'i irin wannan ba, gudun da tayi ba shi da maraba da bala'i, don idan aka ce tayi baza ta taɓa iyawa ba sai dai bala'in da ta gani dole yasa tayi Tayi kusan mintuna ashirin a wurin tana hutawa tare da mayar da numfashi sama-sama tamkar zata shiɗe, daƙyar ta tashi ta bar wurin sabida gudun kar su biyo wurin su kama ta, don ta tabbata zasu iya riskar ta idan har suka biyo hanyar da take, da sauri ta dinga tafiya duk da dare yayi yanzu sosai amma ana ganin abun hawa suna wuce wa, sai kuma fitilu na kan hanya, shiyasa ba ta bari hasken ya haska ta; can gefen titi take tafiya da sauri da sauri tana dafe da cikinta. Ko yanzu suka biyo ta ta tabbata baza ta iya gudu ba a halin yanzu sabida azaban da take ji a cikinta, wanda gudun nan da ta sha shi ya haddasa mata hakan, ko iya tashi tsaye sosai ba tayi, ga azaban da ke ratsa mata gwiwoyi da fuskarta da ta faɗi ta buge, ta rasa inda zata je ga babu shaguna a buɗe, dole ta soma tare abun hawa domin barin wurin da hanzari, gwara tayi nesa da wurin ta samu mafaka idan ba haka ba zata koma gidan jiya. Ta fi kusan mintuna sha biyar tana tafiya tana tare abun hawa amma ba sa tsayawa, ko don dare yayi ne ko kuma don ganinta a haka kamar wata mahaukaciya ne oho, daga ita sai riga da wandon jikinta na Fakistan da ta sanya tun safe, babu takalma bare ɗankwali a kanta, gashin duk yayi baja-baja ya tuttuge daga ribom ɗin da ta ɗaure, ga kwatan da ya ɓata mata jiki, daga ƙafafunta har wandon ta zuwa gwiwanta da ƙasan riganta ya jiƙe sharkaf da kwata, haka ma gwiwowin hannayen ta duk sun ɓaci, ita kanta warin jikinta take ji amma bata bi ta kai ba, fatanta kawai ta tsira. Daƙyar ta samu wani mai napep ya tsaya, bata yi wata-wata ba ta shige ciki tace, "mu je Malam." Shima bai tsaya tambayarta ba yayi gaba, sai da ya soma tafiya before ya tambaye ta inda zai kaita Shiru tayi tana tunani don bata san inda zata je ba, koda gigi baza ta iya komawa gida ba tunda ta ji wayan nan da suka yi, kuma zamanta a garin Kano tamkar ta gudu bata tsira bane, Senator Ƙasim ba ƙaramin attajiri bane, komai zai iya yi domin ya nemo ta, ko don sirrinsu da ta sani zai iya kashe ta ma, wannan tunanin kawai take yi a ranta yayinda take ƙara shiga cikin tashin hankali da tunanin mafita Har mai keken ya gaji ya sake tambayarta jin shiru bata yi magana ba, "Malama ke fa nake tambaya? Ina zan kai ki kina ɓata min lokaci? haka kawai ma bamu yi ciniki ba kin kame kin shige min mota; ga shi duk kin cika min wuri da wari." Sai ya ja tsaki yana mitan, "bai ma san dalilin da yasa ya tsaya ba." har a ransa tsoro ya fara ji yana dana-sanin ɗaukar ta tunda bai ga alamun gaskiya a tare da ita ba, shiyasa ya soma ƙoƙarin tsayar da keken, gangarawa yayi gefen titi Sai a lokacin Arab tayi magana daƙyar da cewa, "ah ah ya za ayi ka tsaya kuma?" "Kinga saukar min a mota ki nemi wani, Ni iyakana wannan kwanan daga nan zan tsaya, bani kuɗi na." Fita tayi daga cikin keke napep ɗin, sai ta dube shi duk da ba wani ganin shi sosai take yi ba; haka shima ɗin, tace, "bani da kuɗi." "Ba ki da kuɗi kuma? Kin san ba ki da kuɗi taya za ki hau min keke?" Bata ce komai ba tayi mishi banza tana kalle-kalle don tunanin hanyar da zata bi "Ke ki sallame Ni in tafi mana kina ɓata min lokaci." Dawo da kallonta gare shi tayi da cewa, "bani da kuɗi nace, idan kuma baza ka haƙura ba ka sauko ka ci na kuɗin ka sai ka ware." "Kamar ya?" Yafaɗa yana zubura cike da mamakin furucin nata "Eh kamar yanda ka ji nace, ai na san ka gane tunda ba kurma bane kai, sai dai ka fanshe kuɗin ka a jikina ka biya buƙatarka na kuɗin ka domin Ni bani da kuɗi." Sai ta ja tsaki tayi gaba ba tare da ta bi ta kansa ba Shi kuma sai ya tayar da keken yana zaginta da cewa, "shegiya ƴar tasha, an gaya miki kowa ma irin ki ne ɗan iska? Can ki je ki samu abokan shashancin naki, banziya jaka ƙazamiya, sai wari take yi ashe Karuwa na ɗauko." "Ka zagi uwarka Ni ban rama ba." Tayi maganar da ƙarfi yanda zai ji domin har ya ja keken shi ya tafi Cikin anguwa ta shiga duk da bata san inda zata je ba, tafiya kawai take yi, sauƙin ta ɗaya tana haɗuwa da mutane jefi-jefi kasancewar cikin anguwa ne. Wani teburin mai shayi ta hango ta nufa ta je ta zauna kasancewar babu kowa a wurin, hannunta ɗaya dafe da cikinta tana zazzare ido sabida tsoro, har leƙe-leƙe take yi idan ta ji kamar motsi ana tafiya, sai kuma ta juya ta ga babu kowa Machine ne ya zo ya tsaya a wurin ya sauke wata budurwa. Ta ciro kuɗi a jaka ta miƙa mishi sannan ya tafi, ita kuma sai ta taho zata wuce ta kalli inda Arab ke zaune, dayake sanda suka sauka hasken Machine ya gama haske ta tass, so ta ganta shiyasa tayi mata sallama tare da cewa, "baiwar Allah lafiya kike zaune a nan?" Arab tace, "Ni baƙuwa ce, ina buƙatar wurin da zan zauna ne da safe sai in tafi." Shiru budurwan tayi, sai kuma tace, "amma wa kike nema a nan arean da kika zo cikin dare kika zauna? Kin san mutane ba abun yarda bane, nima don naga kamar kina buƙatar taimako ne." "Eh ina buƙatar taimako, wasu suka biyo NI kuma Ni ba a nan nake ba, ina buƙatar wurin fakewa idan kina da ki taimaka min." "Shikenan, mu je ai Ni ina da wurin ajiye ki, tashi muje." Hakan yasa ta miƙe suka wuce, tana biye da ita a baya duk da tana a cikin tsoro amma baza ta ƙi tayin da tayi mata ba, a haka ta bi bayanta suka shiga cikin wani gida Babban gida ne domin ɗakuna ne a ciki sun kai ashirin, koda ganin tsarin gidan ka san gidan Karuwai ne. Babu kowa a tsakar gidan duk da wasu ɗakunan a buɗe ne, kuma ana jiyo surutan mutane a ciki; wani ɗakin ma har shewa ake yi Kai tsaye ɗaki mai number takwas suka shiga, sai da budurwan ta tura ƙofan sannan suka shige Arab na biye da ita a baya tana ta kalle-kalle Ƴan mata biyu ne a cikin ɗakin sa'annin budurwan, dukkansu babu mai kaya a cikinsu, ɗaya ta ɗaura zani ɗaurin ƙirji, ɗaya kuma breziya ce a jikinta sai guntun skirt na ciki tana waya Mai ɗaurin ƙirjin ne take kwance tana latsa waya, ita ce wacce ta soma magana ganin shigowar su tace, "Ke da wace ce haka Shahy?" Ta ƙare zancen tana leƙen fuskar Arab Wacce itama kallonsu take yi, but tana tsaye a bakin ƙofa ta ƙi ƙarisa shigowa Shahy kallon Arab ɗin tayi tace, "shigo mana ki zauna." A hankali ta tako ta shigo amma ta ƙi zama sai bin ɗakin take yi tana yatsina, duk da ba wani abu ta gani ba a ciki, komai tsaf yake a muhallin sa "Wai Shahy aina kika samo ta? Wace ce ita?" Wacce tayi mata tambyar ɗazu ta sake yin mata bayan ta tashi zaune a yanzu Haka itama wacce take wayan tuni ta kashe tana kallon Arab Shahy zama tayi tana zame Hijabin jikinta, sai ga ta daga ita sai wata ƙaramar riga da leggings a jikinta, gashin kanta kuma an saka attachment mai kalan ja. "Nima kun ganni ban santa ba, ganinta nayi a waje tana zaune shiyasa nayi mata magana, kuma tace tana buƙatar wurin kwana ne shiyasa na kawo ta. Ki zauna mana ko tsoro kike ji?" Ta ƙare maganar tana kallon Arab ganin har yanzu tana tsaye Zama tayi ba tare da tace komai ba, tana zaune a kan carpet ɗin ɗakin, while su kuma suna zaune a saman ƙaton katifan da ya mamaye rabin ɗakin Sai Shahy ɗin tace, "ki saki jikinki babu wanda zai cutar da ke a nan, Ni sunana Shahida, but ana ce min Shahy ko ƴar lalli, wannan kuma Sha'ira, ita kuma wannan Walida, tare muke kwana a ɗakin nan, za ki iya zama har lokacin da kike son tafiya, ke kuma ya sunan ki?" Ta tambaye ta dukka idanunsu a kanta A taƙaice ta bata amsa, "Arab." "Masha Allah, shiyasa na ganki kyakykyawa, alamu ya nuna ke balarabiya ce kenan?" Shahy tayi maganar tana murmusawa Ita kuma sai tayi yaƙe batare da tace komai ba; bini-bini ta bi ɗakin da kallo Walida ce tace, "amma gaskiya kin san akwai matsala Shahy, Magajiya idan ta san da zuwanta ba tare da an faɗa mata ba zai zama wata fitinar, kin san halinta ai, bare akwai ƴan sa ido duk da ba zama take yi ba zasu faɗa mata." "Haka ne, zan faɗa mata bari tayi wanka ta canza kaya, kinga tana buƙatar yin wanka kayanta ya ɓaci, idan ta gama sai in je in faɗa mata." Sai ta kalli Sha'ira tace, "ina butar ruwan zafin nan in saka mata ruwan wankan?" "Ga shi can saman drower." Ta bata amsa tana nuna mata da hannu Ita kuma ta tashi ta ɗauko tare da fita, sai ga ta ta dawo da ruwan ta jona a socket tunda akwai nepa Suna ta surutu amma Arab tana jinsu bata ce komai ba, sabida ganin ba ta son magana shiyasa su ma basu sake tambayarta ba, har ruwan yayi zafi Shahy ta sake mata ta kai mata bayin ɗakin. Ita kuma ta shiga tayi wankan Bayan ta fito Shahy ta bata kayanta tace, "ga shi nan ki saka waɗannan, kiyi haƙuri da yanayin kayanmu; duk da ban sani ba ko kina sa irin su." "Ba komai." Cewar Arab ɗin tana amsan kayan, riga da wando ne duk da basu kama ta sosai ba kasancewar Shahy ta fita girma da shekaru Tunda ta saka kayan suke bin ta da kallo sabida yanda suka yi mata mugun kyau, musamman yanda suka sake ganin diri da tsarin halittar ta da ya ruɗa su "Wow! Gaskiya ke kyakykyawa ce, Allah ya ba ki kyawu, kin burge Ni." Shahy ta furta tana mata murmushi Itama murmushin tayi sai dai ta ƙi magana Sha'ira tace, "amma ga shi ba kya son magana, zamu so mu san inda kike, ko kuma mai ya fito da ke daga gida?" Zama Arab tayi tana kallonsu, sai tace, "Ni ƴar Zaria ce, na zo Kano ne sai kuma wasu mutane suka biyo ni, daƙyar na samu na ceci kaina." "Allah Sarki! Maybe irin waɗannan ɓata garin ne, koda yake sun ga kyakykyawa." Walida tayi maganar tana dariya Su ma duk dariyan suka yi ban da Arab ɗin da tayi murmushi Sha'ira tace, "gwara ki je ki sanar da Magajiya kar wani magulmacin ya riga ki zuwa wurin ta." "Ai babu wanda ya ga shigan mu ma, ina zuwa bari in je in dawo." Tayi maganar tana miƙewa ta fice a ɗakin. Bata jima sosai ba ta dawo tana kallon Arab da cewa, "taso mu je in kaiki wurin ta, wai zata ganki." Miƙewa Arab tayi ta bi bayanta suka fita "Ki saka takalman nan." Shahy ta nuna mata wasu takalma da ke bakin ƙofa Haka ta zura suka wuce ɗakin Magajiya da ke can ƙarshen gidan. Suna zuwa suka shiga ciki Wata Mata suka samu a zaune a kan kujera, gabanta kuma da ƙaramin faranti tana zuƙan taba tana kakkaɓe tokan a ciki. Shigowar su sai ta ɗago kai tana kallonsu a kaikaice tana hura hayaƙin bakinta Arab kuwa tuni ta rufe hancinta da bakinta har ta soma tari; sabida yanda hayaƙin taban ya cika mata baki ya wuce mata ta maƙogwaro, ɗakin gaba ɗaya ya kaure da hayaƙin ko ganin Mutum ba a yi sosai "Aunty Magajiya ga ta nan na kawo miki ita, kwana ɗaya tace zata yi gobe zata tafi shiyasa na taimaka mata." Cewar Shahy tana kallonta Hankalinta na a kan taban tana kashewa tace mata, "ta basu wuri." Fita tayi a cikin ɗakin kamar yanda ta buƙata Ita kuma Magajiya sai da ta gama kashe taban tana kore hayaƙin da ya gauraye ilahirin inda take, shiyasa ko gani sosai ba tayi, sai da ta gama hure wurin yayi ɗan sauƙi sannan ne ta ga fuskar Arab da ke tsaye liƙe da hanci har yanzu, "ke ce baƙuwar da Shahy ta kawo?" Shiru tayi mata sabida ta ƙi buɗe hancinta da bakinta da ta liƙe bare tayi magana Tasowa Magajiya tayi ta ɗage labulen sannan ta dawo kusa da Arab tana ƙare mata kallo, sai ta sanya hannu ta cire mata hannun da ke fuskarta ta sake ganin fuskarta da kyau, ita kanta ta jinjina da ganin kyawun Arab ɗin, musamman da ta kama hannunta ta ji taushi, ko da kallon yanayinta ka san akwai hutu da jin daɗi a tare da ita, uwa uba kyawun da take dashi. Sai ta riƙo ta suka zauna a saman kujera tare da cewa, "amma ke bafulatana ce ko?" "Eh." Ta amsa mata a taƙaice tana zame hannunta a nata domin ji tayi gabanta na faɗuwa sakamakon tunawa da Jameema, kar ya zo itama Magajiyan haka take shiyasa ta sake ja baya cike da fargaba Murmushi tayi ita kuma tace, "kar kiji tsoro babu abun da zan miki ai, sai dai zubin ki ya nuna min ke ƴar gidan masu kuɗi ne, babu wahala a tare da ke amma kika fito yawon karuwanci?" Kallon da Arab ɗin tayi mata ne yasa ta sake cewa, "ko ƙarya nayi ne? Ai duk Macen da kika ganta a nan gagaran iyayenta tayi ta taho nan, ke ma ga shi kin taho da alamu guduwa kika yi daga wurin iyayen ki, dama mun sha ganin ire-iren ku da suke zuwa neman mafaka, daga ƙarshe muna basu wuri shikenan sun zama cikin mu, sai su kama haya mu haɗa su da customers, Ke kuma ga shi kin zo a Sa'a domin yau insha Allahu zan haɗa ki da wanda za ki samu kuɗi ba kaɗan ba, Allah yayi miki diri mai kyau, ko Ni Mace na susuce da kyawun halittar ki bare namiji." Sai tayi murmushi ta kama hannun Arab ɗin tare da cewa, "kar ki wani ɗaga hankalin ki domin ke kyakkyawa ce, na tabbata shigowar ki cikin mu tamkar ɗaukaka ce a wuri na, idan kin amince anjima kaɗan idan ƙarfe sha biyu ta cika akwai wani Soja da zai aiko a ɗauke ki, a rana ɗaya 30k yake ba da wa, kawai buƙatar sa a kai mishi Mace ya kwanta da ita, da asuba zai sallame ki da kuɗinki ki dawo, dama irin ku kyawawa yake so na tabbata zai ji daɗin harka da ke, ƙila ma ki samu kuɗin da ya fi haka daga gare shi." Shiru Arab tayi ta kasa cewa komai but tunani ne a ranta Sai Magajiyan ta sake cewa, "kin amince kina bukata ko kuwa? Baza ki samu damar da ya fi wannan ba, in dai irin su ne ina da mutanen nan masu kuɗi da yawa, kuma zan haɗa ki dasu, kin kwanta min a rai shiyasa na ji ina son taimaka miki, daga yanzu ma ɗaki na za ki dawo da zama, zan ɗaukaka ki a gidan nan fiye da yanda kike zato." Arab gani take yi tamkar dama ce ta same ta, duk da ta raina kuɗin amma a yanzu tana buƙatar su, gwara ta amince idan yaso daga can inda za'a kaita sai ta ƙara gaba, baza ta taɓa dawowa gidan nan ba tunda ita irin zaman gidan Karuwai ba burge ta yake yi ba, hasali ma baza ta iya sharing gida da mutane da yawa haka ba, kuma ba ka da ƴancin kanka kana ƙarƙashin wani sai abun da aka ce kayi, ta fi ƙarfin hakan domin ita ba ƙaramar yarinya bace, tana da kuɗin da zata kama gidan kanta ita kaɗai babu takura, sai dai tana buƙatar kuɗi domin barin garin nan, musamman idan ta tuna babu wayanta bare ATM ɗinta a hannunta, komai yana gidan Senator, sannan bata da damar cire kuɗin ta dole sai ta koma banki domin samun mafita yanda zata iya ciran kuɗin ta. _Tom mai zai faru? Wacce ƙaddaran kuma Arab zata sake koma wa? Yanzu ne za a fara._ [17/08, 9:43 am] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍      *RUƊIN DUNIYA!* 🌍🌍🌍🌍🌍🌍 *NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL* _UMMUDAHIRAH_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝🏼‍♀️* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                   *P.W.A✍️* _________________________ *BABI NA TALATIN* _______________"Na amince." Arab ɗin ta furta tana kallonta Murmushi Magajiya tayi tace, "yauwa ko ke fa, bari in ɗauko miki kayan da za ki shirya saboda lokaci ya kusa, babu jimawa za ki ga ya turo a ɗauke ki, kar ki bani kunya kinji ko? Duk da dai kin yi ƙanƙanta amma na san zai ji daɗin ganin ki, don Allah duk abun da yace kiyi mishi ban da gardama, da sannu za ki saba, Shahy zata koya miki komai abun da yakamata kiyi, zan kira miki ita ku tattauna." Sai ta tashi ta fita daga ɗakin Arab ta bi ta da kallo kamar wata sokuwa, sai kuma tayi murmushi kawai, wai yau ita ce za'a koya wa barikanci da yanda zata tafiyar da naMiji? Sai ta kalli kanta kawai tana mamakin meyasa ta kira ta da ƙanƙanuwa? taɓe bakinta tayi tana lashe ƙasan bakinta Magajiya tare da Shahy suka dawo tare Magajiya tace, "ki tabbatar kin ɗaura ta a hanya kuma kin shiryata da kyau, na san yanzu Soja zai aiko a ɗauke ta." "To Aunty." Shahy ta amsa mata da girmamawa. Tana fita daga ɗakin sai ta matso kusa da Arab ta zauna tana cewa, "Arab kina sane cewa wurin wani za'a kaiki? Ko dama kin fito yawon Bariki ne?" Girgiza kanta tayi tana taɓe baki batare da damuwa a fuskarta ba "To ke da za ki tafi gobe kuma shi ne za'a kaiki wurin wani? Gaskiya rayuwar bariki bai dace da ke ba Arab, ina ganinki tamkar ƙanwata ce domin kin shiga raina matuƙa, zan so ace muna tare da ke a gidan nan amma Ni ban ga amfanin zaman ki a nan ɗin ba, sabida za ki ɓata rayuwar ki a banza ne, kinga mu bamu da inda zamu zauna ne dole sai nan, dukkan mu da kika ganmu yaudaran ɗa namiji yayi sanadin fitowar mu gida, iyayen mu suka kore mu muka shigo duniya bamu da inda zamu je, sai da wannan rayuwar zamu iya kula da kanmu, amma ke kina da iyayenki sannan kwana ɗaya kika ce za ki yi ki tafi, ban san mene Magajiya ta faɗa miki ba har kika yarda da ita, kin amince ki siyar da mutuncinki a kan ɗan ƙanƙanin kuɗi? Kar ƙaramin kuɗi ya ruɗe ki kiyi tunanin zama a cikin mu." Murmushi Arab tayi wanda har haƙoranta suka bayyana, maganar Shahy ɗin ne ya bata dariya, inda ta san ita wace ce da bata zauna tana mata wannan ɗan guntun nasihar ba, tun tana ƴar shekara sha biyar ta siyar da mutuncinta, a bariki babu kalan iskancin da bata iya ba, idanunta a buɗe suke sosai fiye da zaton mutane, ita iskancin nata ma ba kalan nasu take yi ba domin sheɗanantan ta ya wuce nasu Shahy ganin tana murmushi sai tace, "kamar ba ki damu da maganar da nake miki ba, duk da ban san ko ke wace ce ba amma alamu ya nuna min kamar ba ki san komai a harkan nan ba, kar daga taimako na jefa ki cikin bala'i sabida bazan so ta sila na ki shiga bariki ba." "Kar ki damu babu wata cutarwa a gare Ni, ina buƙatar kuɗin ne domin akwai abun da nake so in Yi dasu, kuma sai ta wannan hanyar kaɗai zan iya samun su." Arab ɗin ta furta mata still tana mata murmushi Shahy tace, "idan kuɗi ne zan ba ki in har baza ki jefa kanki cikin matsala ba, kuɗin komawa garin ku ne ba ki dashi ko mene?" Girgiza kanta tayi tace, "a'a ba kuɗin komawa garin mu nake buƙata ba, zan...." Shigowar Magajiya cikin ɗakin ne yasa Arab tayi shiru suka bi ta da kallo Ita kuma tace, "ya naga kuna zaune ba ki shiryata ba Shahida? Wannan wanne irin iskanci ne bayan kin san yanzu za'a aiko a ɗauke ta? Maganar ne baza ku iya yi kina shiryata ba sai kun zauna?" "Kiyi haƙuri Aunty yanzu zan shiryata." Shahy ta furta da sauri tana tashi "To kuyi sauri ga shi nan ma har ya zo." Tafaɗa tana amsa kiran da aka yi mata a waya, basu ji mai aka ce mata ba sai tace, "ka ƙara haƙuri yanzu zata fito, tana shiryawa ne." Riga da wando ne sababbi Arab ɗin ta saka, kasancewar kayan Robber ne duk sun ɗame mata jiki, gashinta kuma an gyara mata shi tare da kama mata da ribom, Shahy tayi mata light make-up sannan ta yafa siririn gyale, ko ina na jikinta sai da Magajiya ta bi ta shafa mata turare. Tamkar wawuya haka Arab take bin su ba ta cewa uffan, komai su suka yi mata har suka gama aka bata takalma ta saka Sannan Magajiya ta ja hannunta suka fice. Cikin gidan shiru sabida kowa ya kwanta a yanzu, duk da wasu ɗakin sakayo ƙofa suka yi amma ba a jin motsin komai kasancewar dare ya ratsa, haka ma waje babu kowa sai haushin karnuka Motan da aka zo ɗaukar ta tana can nesa da gidan kasancewar wurin lungu ne baza ta shigo ba. Shima Drivern da alamu soja ne domin kayan jikinsa kakin aiki ne, shi ya buɗe mata bayan motan ta shiga sannan suka tafi Sai da Magajiya ta ga tafiyansu sannan ta koma cikin gidan ta rufe ƙofan Su kuma tafiya suka yi ɗoɗar a kan titi. Ko tsoro Drivern ba ya ji domin babu wani halitta a waje, maybe don shi soja ne shiyasa, sannan Ogan nasu babba ne shima a soja babu ruwansa duk sanda yake buƙatar Mace a daren za'a je a ɗauko mishi ita, babu ruwan su tunda jami'ai ne su ma bare a tsare su A wani babban gida ya dakatar da motan yayi horn. Aka buɗe masa Gate sannan ya shige ciki Arab sai kalle-kalle take yi tana ƙare wa gidan kallo, domin babu ƙarya gidan ya burge ta, ko da gani mamallakin sa yana da kuɗi gaskiya, ya haɗu sosai gidan domin tamkar ginin Turai aka mishi, flat ne mai faɗi. Ba ka jin ƙaran komai a gidan sai kukan tsuntsaye ko ina akwai flowers, har da bishiya da irin masu bin gini kamar macizai. Akwai jami'an tsaro a haraban gidan kowanne riƙe da bindiga suna ta zagaye Drivern shi ya buɗe ma Arab ƙofan sannan yayi mata jagora har cikin makeken Falon. Suna shiga ya nuna mata wani ƙofa yace, "ki shiga wancan ɗakin yana ciki, sannan kar kiyi wani abun da zai sa mu kama ki, kowanne wuri akwai Camera CCTV; abun da ya kaiki kawai shi za ki yi, ba ma son shishshigi, zuwa asuba zan zo in buɗe miki ƙofa ki bar gidan." Har ya gama maganarsa bata ce komai ba; sai kallonsa da take yi kamar ta samu t.v Shi kuma ya juya ya tafi batare da ya damu ba, domin shima ba ya son yayi wani abun da zai yi laifi a wurin Ogan su. Umarnin da yake ba shi kenan ya ɗauko Mace ya kuma kawo mishi ya fita Rufe ƙofan da yayi ne yasa Arab ta ɗauke ido a kan ƙofan, tare da taɓe bakinta ta soma bin ko ina da kallo. Ta ɗan ɓata lokaci a wurin tana ƙare ma falon kallo, kana ta nufi wurin fridge da ta hango, buɗewa tayi ta ɗauki ruwa a ciki ta sha, sai da ta sha sosai kafin ta rufe ta mayar ta nufi ɗakin kanta tsaye cikin tafiyarta na jan aji. Ƙofan ta murɗa ta ji ya buɗe, sai ta zura kai ciki kawai ba tare da tunanin wani abu ba. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels