An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* *Mallakin* ⬇️ *OUMMU IMAM* *Da Sunan ALLAH Mai Rahama Mai Jin Kai* *Ya Rabbi ina rok'on ka da sunayenka kyawawa masu tsarki yadda ka bani ikon fara rubuta littafin nan,ka bani ikon rubuta abunda zai amfaneni duniya da lahira da al'umma baki daya,ka tsare man hannuwa na daga rubuta abunda zai cutar da ni da al'ummar Annabi(S.A.W).Yadda na fara rubutun nan lafia cike da farinciki ya Allah ka bani ikon kammala shi cikin farinciki da koshin lafia,Amin Ya Mujib.* *Wannan littafi sadaukarwa ne ga family na wato MUNHIZAFA FAM,Allah ubangiji ya kara hada kawunanmu ya kuma kara rufa mana Asiri fiddunya wal akhira da sauran Al'umma baki daya,Amin.* *Labarin wannan littafin kirkirarran labari ne,idan suna,hali ko yanayi sunyi kamanceceniya arashi ne bada nufi ba.* *Gaisuwar Ban Girma* *Ga mahaifiyata,Allah ya kara girma da nisan kwana,MY FIRST LUV❤️.* *TUKUICI NE* *Ga Hafsat Bature Muhd(Boss Lady) Allah ya kara mana basira da hazaka baki daya Amin.*🤝 Sabuwar Marubuciya wadda ta dade tana yi maku tanadin tsararrun labaran da zasu Ilimantar da fadakar daku,uwa uba kuma nishadantar daku, Littafin *A SANADIN MAKWABTAKA* Na dauke da labari mai cike da barkwanci,tausayi,da kuma tsabtatacciyar soyayya mai ta6a zuciya,kada ka/ki bari ayi tafiyar ba ki/ka. Littafin nan na kudi ne,da zarar nagama sakin free pages sai wanda ya biya ne kawai za'ai tafiyar dashi🤝 *Free Page1️⃣&2️⃣* KATSINA STATE Unguwa ce mai dauke da Manya manya had'i da K'ananun Gidaje,sai dai kana kallon yanayin gidajen zaka fahimci cewa ba tsohuwar unguwa bace,don sam gidajen basu ji jiki ba,wasu gidajen Sababbi ne yayin da wasu kuma baza'a kira su da sabbi ba,ba kuma tsofaffi bane,akwae Manyan gidaje masu kyau wad'anda da ka kalla zaka fahimci masu gidajen nada arziki,yayin da wad'ansu kuma ke nuni da masu su,masu rufin asiri ne.Yanayin layin ba hayaniya sosai akwae mutane jefi-jefi,kallo daya zakae ma layin ka fahimci akwae masu arziki had'i da masu rufin asiri a wurin. Wata mota ce k'irar Corolla S Navy blue ta shigo layin da matsakaicin gudu, K'irrrrrrr! Motar taci burki batare da shiri ba sakamakon wasu yara mata da basu wuce shekara 13 zuwa 14 ba, da suka shigo hanyar da gudu daga Lungun dake a bangaren dama,d'aya cikinsu na dauke da farin matsakaicin Bokiti mai d'auke da wani abu ciki hakan na nuni da tallah take yayin da dayar da ta biyo ta ita bata dauke da komae,lungun da ke opposite da wanda suka fito suka shiga a daidai nan kuma d'ayar yarinyar ta samu nasarar kamo hijab din yarinyar dake dauke da bokitin talla,tura ta tayi jikin bango tana kokarin 6arar mata da abunda take sayarwa, ita kuma ta rik'e bokitin gam, Shi kuwa na cikin Motar still yayi da alamun bacin rai a fuskarsa yadda yaran suka fad'o masa all of a sudden,ba don Allah yasa bai gudu sosai ba da horrible accident ya faru a wurin don gaba dayan su zai dauke su da motar watakil ma ya take su,dan tsaki yaja"Mtsww"A hankali ya waiwaya yana kallon lungun da yaran suka shiga,hango su yayi sai faman kici kici suke alamar dai fad'a suke ga d'ayar yarinyar mai sanye da riga da skirt na atampa kanta d'aure da kallabi wanda daga bayan kallabin yayi tudu sosai alamun dai tana da gashi mai yawa ga gyalenta kuma daure a k'ugunta sai faman kokarin ganin ta 6aro da bokitin dake kan dayar yarinyar da ta matse a bango take, Ganin yadda ta dage bilhakki sai ta 6arar ma d'ayar abunda ke cikin bokitin yasa shi sauke gilashin motar a hankali,"ke,ke" Ya fara k'okarin yima yarinyar magana sai dae ko waiwayo inda yake batayi ba,tunani yayi kilan bata ji shi ba hakan yasa ya k'ara dan daga murya duk da bai so hakan b "Kee sake ta!" ya kara fada,tana jinsa tayi burus da shi,yarinyar mai talla ce tace"ke Fatuu baki ji wancan mai motar na cewa ki kyale ni bane"kara k'ankame bokitin tayi ita kuwa wadda aka kira da Fatun ganin ta kasa 6aro da bokitin yasa ta fara dukan yarinyar don tasan in tayi hakan dole ta saki bokitin ai, Ganin hakan yasa mutumin cikin motar fitowa,Wow! Masha Allah, Wani Kyakkyawan Mutum ne mai dan tsayi sai dae ba irin tsawon nn sosae b, sai dai kana kallonsa zaka shaida dogo ne,kalar fatar sa kuwa fara ce irin farin nan mai kyau mai tafia bai d'aya ba wai irin wanda zaka ga wani wuri yayi dan ja-ja ko yalo-yalo ba,gaba daya fatar shi sumul take,yana da matukar kyawun Fuska wadda da idanu sun kalli fuskar zasu shaida hakan,sumar kansa nada dan tsawo wadda take a nad'e yayin da daga tsakiya ta dan fi gefe da gefen tudu,sam bai tara kasumba ba sai dai akwae sumar kad'an zagaye da fuskar har zuwa saman dan madaidaicin bakinsa wanda labban sa suke kalar peach mai duhu,sanye yake cikin Suit Navy Blue yayin da yar cikin take Black color,Wuyansa na sanye da Necktie kalar suit din wato navy blue wanda yake kwance ak'asan bakar collar din yar cikin,k'asan necktie din kuma an rufe shi data saman ta hanyar sa Ma6allan rigar wad'anda suke bakake masu kyan gaske,hannunsa na sanye da Wrist watch silver mai d'an duhu kai da gani kasan zai yi kudi Agogon, yayin da K'afafunsa kuwa ke sanye cikin wasu dakakkun Takalma cover shoe bak'ak'e, ba k'aramin haduwa yayi ba,ba kamar da kalar fatar sa take fara sai yayi kaman ba irin mutanenmu ba na nan,yadda suit din suka amshi jikinsa cib ya bayyana sam ba ramamme bane yana da cikar kira ba kaman Kafadunsa da suke da fadi,da ka kalli kayan jikinsa da kuma motarsa zaka fahimci yayi shigan da ake kira too match, Ya mayar da Kofar motar ya rufe da hannunsa daya tafiya ya fara yi majestically,da ganin yadda yake tafiyar za kai tunanin irin mutanen nan ne masu ji da isa,gefen su ya tsaya fuskar nan a tamke cikin dan daga murya ya fara yima yarinyar magana"Sake ta!"burus tayi sai ma k'eya da ta kara juyo masa,cikin 6acin rai da daga murya yace"Am i not talking to u, idiot." ya fada a dan harzuke,jin yace mata idiot yasata juyowa a fusace ta fara magana cikin masifa"Ni ba idio......sam ta kasa k'arasa maganar sakamakon hada ido da mutumin dake a tsaye fuska a d'aure,kwarjini yayi mata sosai, "Get your hands off her"ya fada fuska a daure,a hankali ta saki Yarinyar mai talla da alama ta ji abunda ya fada da turanci,d'an ja da baya tayi kad'an,kasa-kasa tace "Don kana da kyau zaka wani daure ma mutane fuska ni ba ruwana da kyaun ka ehe" Still yayi yana kallon yarinyar don yaji duk abunda tace,lallai yarinyar bata da kunya ya ayyana a ransa,"Wuce kibar wurin nan before I slap ur face"ya fada tare da nuna mata hanya da hannu,A hankali ta fara tafia cikin lungun tana turo baki tana waiwayen su,kallon yarinyar da ke dauke da bokitin talla yayi"Wuce ki tafi" ya fada yana nuna mata hanyar da suka fito "To",ta fada tana gyara Yellow din hijabinta da ta cukwikwiye ta fara tafiya,shima juyawa yayi ya nufi inda motarsa take, "Wayyo Allahna! ta 6arar man da Awara...!" Yarinyar ta fasa kuka tana fadi da sauri mutumin ya juyo,da wani irin expression yake kallon yarinyar da ta 6arar da awarar,Ashe ba tafiya tayi ba tana ganin ya nufi motarsa ta fito da sauri tasa hannu ta ture bokitin Awarar,ganin yadda yake mata wani irin kallo yasata jin tsoron shi rugawa tayi a guje cikin lungun ita kuwa mai awarar muryar ta kawai ake ji sai faman ihu take tana fadin"Wllh bazan yarda ba sai an biyani gidanku zan biyo ki,Muguwa,Azzaluma kawae"d'aukko bokitin tayi wanda ya rigada ya fashe ganin haka yasa ta sakin wani sabon kukan, A hankali ya juya ya koma inda take tsugunne tana d'ibar awarar tana zubawa cikin bokitin sai faman kuka take,tsayawa yayi a kanta,d'ago kanta tayi cikin kuka tace"kagani sai da ta 6arar mn da awarar ko,kuma wllh bashin waken soyan da mai Innarmu ta amso sai na sayar za'a kai kudin gashi ma har bokitin ya fashe wllh gidansu zani sai an biya ni" ta k'arasa maganar da matsanancin kuka. "Is okey,just leave the rest" Ya fada,dagowa tayi tana kallon shi da alama bata fahimci mi yace ba,"tashi kibar sauran, baki ga yayi k'asa b" Ya fad'a gently, mik'ewa tayi tana ta sheshsheka cigaba da magana yayi a hankali"Miya hada ki da ita? "Wllh ba abunda nayi mata kanwata ta tare rannan wai sai ta bata alakoro ita kuma tace bazata bata b,shine ta buge ta,kuma ta d'ebi awarar,da Innarmu taji shine taje gidansu da kanta don ayi mana tsakani don ba lokacinne na farko ba da take taremu tace mu batan,to shine aka bugeta yau tana ganina tace tunda Innarmu tasa aka bugeta sai taja mata asara sai dai in tasa a kasheta,ba yad........"its okey"ya katse ta, da alama ya gaji da sauraronta,"Ina ne gidan ku? ya tambayeta a takaice,"Acan layin baya muke gidan Alhaji Sani karofi anan babanmu yake gadi cikin gidan muke acan baya"takae maganar tana goge kwallan idonta. "Shi abun naki na nawa ne? ya tambaya."Awarar dubu da dari biyar ce gashi ta zubar da ita duka yar kadan ce bata baci da k'asa ba,inaga ma ko ta d'ari biyu bata wuce ba,wllh gidansu zanje sai anbiya mu ta k'ara fashewa da kuka,da alama taji zafin abun sosai, Sigh yayi kafin yace"You know what,ku kyaleta kawae tunda bata jin mgn in kun k'ara zuwa kun kai karanta zata k'ara zubar maki da abu,calmly yayi maganar,Hannu yasa a cikin aljihun wandon suit din jikinsa bak'ar Wallet ya fiddo mai kyaun gaske ya bude,Kudi ya kirgo sababbi fil kamar lokacin aka buga su,mik'ama yarinyar yayi wadda ke tsaye ta kafe sa da idanu tasa hannu da sauri ta kar6a,aje fasassan bokitin tayi a kasa ta fara kirga kudin dubu ukku ta gani da tsananin mamaki ta d'ago lokacin har ya juya da sauri tace"Yallabai kudin sunyi yawa ai" Hannu yad'an daga ba tare da ya juyo ba yace"ku siya sabon bucket da sauran" ya cigaba da tafia wurin da motarsa take, Mai tallan kuwa har lokacin juya kudin take da mamaki hakanan bai santa ba ya bata har dubu ukku da sauri tabi bayansa tana fadin "Yalla6ai,yalla6ai..." lokacin har ya kama k'ofar motar zai bude jin yadda take ta faman kiransa da yallabai yasa shi juyowa"What again? Ya tambaya da kosawa,"umm dama².... ta kama inda-inda sakamakon kafeta da ido da yayi,ya lura da yadda ta dabarbarce,dan sakin fuska yayi yace"Uhum ina jinki dama me? Dama so nike in tambayeka in innarmu ta tambayi wanda ya ban kudin wa zance mata? ta k'arasa maganar tana sunnar da kai k'asa"just tell her wh....ki fada mata abunda ya faru kawai"ya juya zai shege cikin motar, da sauri tace "ai tana iya cewa k'arya nike ni na tsara hakan kullum tana ce mana kar wani ya bamu kud'i bamu san shi b,ko yace zai siye mana yayi mana abunda bai dace ba"ta gama maganar kanta a kasa, d'an murmushi yayi na gefen fuska wurin ya lotsa alamar yana da dimple,yaji dadin maganar da tayi ko ba komai hakan ya nuna rashi ne yasa suke tallan ba wai ra'ayi ko son kudi na wasu iyayen, Juyawa yayi yabude motar ya shige ya jawo kofar ya rufe,tana dai ta kallonsa don gaba daya komae yayi burgeta yake sai da yayi ma motar key kafin ya bude Glove box din gaban motar kudi ya kirgo dubu biyu juyawa yayi ya mik'a mata da d'an murmushi a fuskarsa yace "ki hada da wannan ki kai ma Mom din naki" Maida hannunsa yayi ya murza key din jikin motar tana dai ta kallonsa da tsananin mamaki sai da motar ta tashi sannan glass din murfin motar ya fara rufewa sama a hankali juyawa yayi ya kalli yarinyar da har lokacin take tsaye tana ta faman binsa da idanu "Ki ce ma Mom din naki dan gidan HAJIYAR SENATOR ne ya baki" daga haka ya ja motar fuuuu, "Hajiar Sanata! Yarinyar ta maimaita da mamaki had'i da rike ha6arta da hannunta daya,sai kuma ta saki wata irin dariar farinciki da sauri ta juya komawa tayi inda sauran Awarar ke a zube k'asa tace "bari in kara dan kwashe wadda batayi k'asa sosae ba da ansa cikin mai k'asar zata fita ko mu sai muci" a saman marfin bokitin ta zuba mai kasar,mikewa tayi da dan gudu-gudu ta koma cikin lungun da suka fito tun da farko. Yarinyar data 6arar da Awarar ce ta lek'o da kanta daga cikin zauren gidan da ta 6uya,round face gare ta mai dauke da madaidaicin hanci mai dan tsawo tana da dan kumatu,idanuwanta kuwa suna da dan girma sam baza'a kira su da k'ananu ba,tana da gashin gira wanda yake kwance lub haka kuma gashin idonta nada tsawo gazar-gazar bakinta madaidaici ne le6anta na k'asa nada dan fad'i sosae,kalar fatar ta kuwa fara ce sai dai ba sol ba,Amman kana kallonta zaka kirata da fara, sai da ta waiwaya hagu da dama ta tabbatar ba kowa kana ta fito,cikin sand'a take tafiya tana yi tana waiwaye har ta iso bakin lungun daidai inda ta 6arar da awarar,tsayawa tayi tana kallon sauran awarar dake a k'asa, Kafarta tasa tana tattake awarar tana cewa"Gobe ma ta kara sawa a doke ni" ta fada a fili tana mummurguda bakinta gefen kumatun ta na lotsawa sosae alamar tana da dimples, jin k'arar mota ta taho a bayanta yasa tayi saurin juyawa hadi da d'an tattare Skirt dinta da hannayenta biyu tana shirin rugawa ganin ba motar mutumin d'azun bace yasa ta saki skirt dinta tace "In ma shine yazo banjin tsoron sa koda kuwa Aljani ne ehee" ta fad'a lokacin da ta fara tafia ta miki hanya tana yi tana waiwayen bayanta tana watsa hannuwa gami da turo baki, Yar tafiya tayi kafin ta iso bakin wani Gida wanda keda shafen plaster ba fenti a jikin bangon gidan daga gaban gidan akwae k'atuwar kwata wadda ke zagaye da gaban gidajen layin saidai a rufe take da slabs daga d'an gefen kofar shiga gidan akwae Kiosk a saman rufaffiyar kwatan gaban gidan,shiga cikin zauren gidan tayi wanda keda K'ofa da kuma Window a cikinsa da alama irin d'akin zauren nan ne, A bakin kofar shiga cikin gidan ta tsaya,dan leka cikin tsakar gidan tayi wanda yake wayam ba kowa,dawo da kanta tayi cikin zauren ta rik'e habarta da hannunta na dama tunani ta shiga yi "Ba'a kawo karar tawa bane?kodai sun zo har sun tafi" jinjina kai tayi a fili tace"Inma an kawo k'arar tawa nasan abunda zance,cewa zan yi tsokanata tayi,ta kuma yiman daria harda gwalo wai sun sa an bige ni" ta k'arasa maganar tana faman mummurguda baki dimples dinta na lotsawa, A hankali tasa k'afa cikin gidan mai dan matsakaicin girma wanda kasan shi ke malale da siminti gaba daya,d'akuna biyu ne a cikin gidan wanda kofofin su na kallon juna,dakin da ke a bangaren dama babban daki ne yayin da na bangaren hagun k'arami ne a jikinsa kuma kicin yake wanda shine a farko in ka shigo gidan daga bangaren hagun,sai dan fili wanda da gani wurin yin Wanke-wanke ne a gefe daga tsakiyar filin akwae yar Bishiya,daga nan kuma sai Band'aki da ke a can gefe bangaren da kofar shigowa take, Shiga tayi cikin gidan a hankali tana yin sand'a "Daga ina kike? Aka jefo mata tambaya daga bayanta,cikin yar razana ta juya,wata farar dattijuwar mata ce mai dan tsayi,sam bata da jiki sai dai ba siririya bace sosae tana da tsagun yan baka a bakinta,tsaye matar take da buta a hannunta da alama daga band'aki ta fito "dake nake Fatuu" ta k'ara fada da muryarta irin ta fulanin da suka ji hausa sosae,in'ina fatun ta fara yi,ta rasa mi zata ce don tunani take ko an kawo karar abunda tayi ma mai tallar Awarar nan,"Halan kina can wurin jawo man fitinar da kika saba ko" ta k'ara jefo mata tambaya,da sauri fatun tace "A'a gwaggo.." tana ta faman zare ido "to ki fadan ina kika je don na lek'a neman ki da kaina baki a waje" Goggon ta fada ta kafe ta da idanu,"Umm... gidan Hajiyar Sanata naje gaishe ta" taba gwaggon amsa da alamun rashin gaskia a fuskar ta,"Allah yasa da gaske kike don banga ranar da garin Allah zai waye har rana ya fadi baki jawo mun fitina ba" jin hakan yasa fatun gane ba'a kawo k'arar abunda tayi ba" da karfin gwiwa tace "Allah gwaggo daga can nake fa" gwaggon tace"to wannan d'amarar da kika ci da gyalen ki ta mene?" "ba komai kawai gyalen ne ya ishe ni yana ta fad'uwa shine na kulle shi anan" tayi maganar tana kokarin kwance gyalen daga kugunta, gwaggon taci gaba da magana"Ai in ance kisa hijabi sai ki k'iya sam bakya son sa hijab ke kinfi son gyale gashi ko yafawar ma baki iya ba kullum yana ruke a hannu ko daure a k'ugu,to ina amfanin hakan in anyi magana kice ke baki saba sa hijab a kauye ba" ta karasa maganar tana shiga cikin gidan, "Allah gwaggo hijab din shak'e ni yake fa, ni ban saba sawa ba,acan ruga fa wani lokacin ko gyalen ma ba sawa muke ba" ta karasa maganar da sigar shagwa6a tana bin bayan gwaggon "Ai sai ki tayi tunda anfad'a maki nan ma kauyen ne, da kina son sa hijab din ai da yanzu kin saba dashi yaushe rabon ki da kauyen kusan shekara ta ukku kenan fa, kawae dai kin fi son kisa gyalen yadda zaki ji dadin nemo man fitina,Kullum cikin daukko man magana kike nikam na fara gajiya wllh kuma zan yi maganin ki indai baki bari ba tunda na lura sam duka bai maki" ta k'arasa maganar lokacin da ta iso bakin kofar dakin da ke a bangaren dama, d'aga labulan kofar tayi ta shige harda butar da ke a hannunta,ita kuwa fatun labulan kofar da ke kallon wadda gwaggon ta shiga ita ma ta daga ta shige,dakin baida girma sosae, akwae Gado irin na karfe mai spring yana da bakin fenti da katifa wadda aka rufe da tsohon zanin gado,A bangon dake kallon gadon kuwa wardrobe ce mai gida biyu da kananun gidaje a kasa suma guda biyu,ta dan ji jiki sannan yar madaidaiciya ce ba mai tsawo ba,a samanta akwae jakunkuna,daga gefen ta kuma dressing mirror ne kalar ta shima karami ne wanda hannuwan drawers din jikin shi wasu duk sun balle haka mirror din jiki dan guntu ya rage,akwai leda shimfide a dakin wadda ta ji jiki don duk wasu wurare sun farfashe,Saman gadon ta fada hadi da fadin "Washh" sai kace wadda tayi wani uban aiki banda neman rigima,tunani taci gaba da yi "ko sai yaushe zasu kawo kara tan..." k'wafa tayi a fili tace"Allah yasa su kara sawa a doke ni wllh nasan abunda zan yi masu...."Muryar gwaggon tace ta katse ta"fatuu fito ki tankade man garin can na cikin kicin yamma tayi in samu in daura girki......,Fatuu ko bakya jina ne wai? cikin d'aga murya tace "Ina ji fa,gani nan fitowa.." mik'ewa tayi ta nufi k'ofa sai faman k'unkuni take tana jujjuya kai alamar bata son yin abunda aka sata yi. *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* *STORY* & *WRITTEN* BY *OUMMU IMAM* *Free page3️⃣&4️⃣* Da d'an gudu gudu ta shiga gate din gidan wanda Babban gidane irin na masu hali wata yar hanya dake a gefen tank'amemen Flat din ta bi sai gashi ta 6ullo bayan gidan,gini ne dan dogo mai dauke da dakuna biyu a jere sai kuma kofofi biyu dake opposite da juna k'ananu,akwae baranda da ta lullu6e d'akunan kana kallon yanayin ginin zaka fahimci BQ ne da ake yi a gidajen masu kudi,BQ din yadan ji jiki saman Ceiling din barandar duk yadan farfashe haka fentin ginin duk ya k'oke,ga damsa kuka duk tayi baki-baki a k'asan bangon ginin, Yara ne bi da bi a tsakar wurin suna ta wasa,yayin da wata mata ke can gefe ak'ark'ashin ginin da ake daura tankin ruwa tana ta faman hura wuta wurin duk yayi baki da gani a nan suke yin girki,yarinyar na isowa wurin wani Yaro ya buda murya yana cewa "Lah inna ga Jamila har ta dawo daga tallan" da sauri uwar ta su ta waiwayo daga cikin inda take ganin jamilar rungume da bokiti ga awara a saman shi da gani 6arin ta tayi,yasa uwar fitowa ba shiri tana fad'in "Jamila mi zan gani haka badae 6arar da awarar kika yi ba..."Salati ta shiga yi lokacin da ta k'araso taga awarar saman marfin duk k'asa cikin tsananin tashin hankali tace"yanxu jamila abunda kika yi man kenan kina sane da cewa ko kudin kayan da akayi awarar nan ba'a biya ba shine kika........" Jamilar ce ta katse ta da cewa "Wllh innarmu bani na zubar da awarar ba" "to ubanwa ya zubar da ita kuma kina aikin mi" ta tambaya a hasale "Fatuu ce ta 6arar man da ita wai don kin kai k'ararta an buge ta" nan ta bata labarin yadda ta bita har ta zubar da awarar, Kwafa Innar tayi a hasale tace "to wllh bazata sa6u ba bindiga a ruwa,dole a biyani awara ta,yarinya ta bi ta addabi kowa to wllh bazan d'auki asara ba dole a biya ni" ta karasa maganar tana shirin juyawa ta daukko Hijabi bata karasa juyawan ba sakamakon kudin da jamilar ta miko mata sabbi fil,zaro ido uwar tayi lokacin da tasa hannu ta kar6i kudin tana jujjuya su "Wannan kuma na miye?"ta tambaya da mamaki a fuskarta "kudin awarar ne inna" jamilar ta bata amsa, "kudin awara kuma,da mamaki innar tasu ta tambaya lokaci guda kuma ta fara kirga kudin,da sauri ta d'ago ido a waje tace "na shiga ukku ni Saratu,jamila ina kika samu kudi haka da yawa? Jamilar tace "Mutumin da abun ya faru agaban sa ne yabani ya....."bata k'arasa maganar ba innar ta katse ta"ya baki kamar ya ya? hakanan bai sanki ba kawai don an 6arar maki da awara ya dauki kudi har dubu biyar ya baki a wannan halin rashin da kowa ke fama,ke jamila ki gayan gaskia kodae wani ya miki wayo ya baki,shine kika tsara man karyar Fatuu ta zubar maki!"ta karasa maganar idanu a waje tana cikin tsananin fargaba,hannu tasa ta fizgo yarinyar har awarar dake a saman marfin bokitin na zubowa tace "gaya man ina kika samu kudin nan ko in yanka ki a wurin nan" jin ance za'a yanka jamilar yasa sauran yaran tasowa suka yi cirko cirko suna kallonsu,da sauri jamilar tace"a'a inna wllh ba wanda yayi man wayo mutumin dana gaya maki anyi a gabansa ne ya bani kuma ma sai da na tambaye shi wa zance maki ya bani in kin tambaya....da sauri uwar ta katseta ta hanyar tambayar"to waye shi yace maki? Har lokaci tana rike gam da hannun yarinyar "cewa yayi ince maki dan gidan HAJIYAR SANATA"yarinyar ta fada cike da kwarin gwiwa don tasan gaskia take fada, "Hajiyar Sanata! Innar ta maimaita lokaci guda kuma ta saki hannun jamilar da mamaki a fuskarta sai maimaita sunan hajiyar sanatan take "to ke kinsan shine dama" ta tambayi Jamilar "a'a Innarmu ni yau ma na fara ganin shi wllh"nan ta shiga fadi mata yadda sukayi dashi bayan an 6arar da awarar,innar tace "To waye wannan mutumin mai kirki haka,lokaci guda ta rike ha6arta da alamar tunani take...... taci gaba"Ni dai a tunani na Hajiyar sanata bata da wani d'a ko d'iya a gabanta gaskia,sai dai danginta da ke yawan kawo mata ziyara da kuma mutanen gari tunda gidanta gida ne na al'umma ko don taimakon da take ma mutane tunda mace ce mai kirki ga taimako gashi kuma d'anta babban dan siyasa ne shiyasa gidan bai rabuwa da mutane kala kala,Oh to shi wannan ko waye?"ta k'arasa maganar da sigar tunani, Jamila ce ta katse ta da cewa"gaskia nidai ce man yayi dan gidan ne shi,kuma da gani haka ne,don baki ganshi ba innarmu Kyakkyawa ne sosae wllh wani irin fari mai kyau gare shi,ga gashin kanshi kaman na yan kasan waje ni wllh innarmu banyi zaton ma ya iya hausa sosae ba sai da yana man magana nayi ta kallon shi,kuma kin san mi inna? "A'a" innar ta bata amsa a inda take tsaye Sototo "Kalar kayanshi irin kalar motar da ya hawo ne,ina irin kayan nan na turawa masu igiya a wuya...tasa hannu tana kwatanta ma innar,ita kuma ta gyad'a kai alamar ta gane kayan"to sune a jikinshi kinga takalmanshi irin rufaffun nan ne masu kyaun gaske kai wllh Mutumin mugun dan gayu ne innah" ta k'arasa maganar tana yarfa hannu, Ajiyar zuciya uwar tayi tace"to kam ina tunanin daya daga cikin jikokin hajiyar ne,don jikokinta tubarkallah akwae kyau sosae wllh don kwanaki can da dadewa munje kar6ar tallafi a gidan naga wani Matashin Saurayi mai kyaun gaske har muka gaida shi ya amsa mana kamar baison amsawar..."inna wllh kilan ma shine,shima wannan fa kamar dan dole yake maganar baki gani ba yana wani haka,ta d'an yamutsa fuska ita ala dole yadda yake magana take kwaikwaya gaba daya suka sa Daria harda Kannenta,Innar ce tace"hakan duk cikin gayu ne ai,kinsan su yan gayu komae nasu na daban ne wllh,kai Allah muma yayi mana arziki mai Amfani" ta d'an daga hannayenta sama, "Amman anya shine kuwa wannan fa anyi shekara biyu koma fi dana ganshi kilan dai dan uwan shi ne,kai koma dai waye nagode kwarai wllh Allah ya taimakeni ta silar shi,da bansan ya zanyi in biya kudin Waken nan da Mai ba dama sai da aka ja man rai aka bani,kai Allah ya taimake ni wllh",hannu ta daga tana k'ara gode ma Allah cikin tsananin farinciki,gaba daya yaran suma suka dauka"Allah mungode ma² suna yi suna tsalle ganin Mahaifiyarsu na farin ciki,kar6ar bokitin awarar tayi tana dubawa"Kai yarinyar nan anyi yar....ko da yake inma na zage ta kanmu abun zai k'are,don ba'a son mutum yana abu ana aibata shi da mugayen kalami,to kara lalacewa yake kuma mutanen da ke tare da shi su abun ke shafa,Allah ya shiryata dai damu baki daya" "Amin"yaran suka amsa da karfi" amman duk da haka ji nake kaman inje in fadi ma gwaggon tata don abun Yarinyar yayi yawa wllh" jamila tace"innarmu ki kyale ta kawae shima Mutumin daya bada kudin cewa yayi kar in bita gidansu don in an kara dukanta zata kara 6arar mani tunda bata jin Magana" hakane gara mu kyaleta tunda ma sanadin abunda tayi mana ji bi abun arzikin da muka samu" ta kara sa maganar tana k'ara kirga kudin, wani yaro ne cikin yaran yace "Inna muzo mu karbi sauran mu cinye tunda an samu kudi" yayi maganar yana d'an noke kai gami da yar daria da sauri Innar tace"ehh maza kuzo ku kar6a" tsalle yaran suka fara yi suna murna,marar k'asar ta babbasu Jamila ce tace "Inna don Allah tunda ansamu kudi zaki ban in siyo hoda mai madubin da na tambaye ki kwanaki kika ce sai kin samu kudi" ta karasa maganar tana sussunna kai kasa,da fara'a a fuskar innar tace "Kwarai kam zan ba ki tunda Allah yasa ansamu kudin,ko dama can abunda yasa ban baki ba kudin ne ba isa suke ba sam kina dai ganin yadda ake ta fama,kinga da kika yi hakuri ba gashi Allah ya kawo ba, shiyasa in aka ce ma Mutum yayi Hakuri to yayi din don mataki ne na nasara rashin yin hakurin kuma ba abunda yake ja ma Mutum face asara da dana sani" cikin washe baki jamila tace"Eh hakane Inna" "to sakamakon hakurin da kika yi harda na siyan jan baki zan baki sai kije ki siyo harda sabon bokitin tallan" tsallen murna jamila ta fara yi tana ta faman daria tana shima dan gayu mai mota daya bata kudi Albarka,itama Innar tasu Albarkar take sa ma mai motar yayin da ta nufi daki don adana Kudin. * * * * * * * * * * * * * * * * * Wani irin Katafaren Gida ne mai tsananin kyau wanda da ka kalla zaka gasgata kyawun gidan,Fentin gidan ya matukar kayatuwa wanda Peach colour ne mai dan duhu had'i da milk colour,Katangar gidan na dauke da peach din fenti yayin da Pillars din dake a jikin katangar ke dauke da Milk din fenti,gaba daya katangar na zagaye da hadaddan Fence wanda ke dauke da farin fenti,daga saman fence din yadan yi tsini kamar mashi anyi mashi adon fenti Golden mai salk'i,cikin fence din kuwa shukan Flowers ne masu kyau da gani suna samun kulawa sosae,gasu a tsare mai tsawo sai ta gabanta gajera haka suke jere gwanin sha'awa,can saman katangar ma zagaye yake da Electric fence bak'i,A k'arshen katangar gidan gaba daya kuwa Masallaci ne mai kyau da girma komai nasa kalan na gidan ne ga Tankunan ruwa manya har biyu a sama da kan Famfuna a jikin ginin da aka d'aura su Yara nata dibar ruwa. Gate din gidan kuwa ya d'an shiga lungu ta yadda in mota ta taho daga bangaren katangar gidan ta dama ko hagu zata shiga gidan sai andan karya kwana, A daidai gidan mutumin ya juya kan motan ya tunkari Dank'areren Gate din gidan wanda shima yake da farin fenti daga saman shi anyi design irin na fence din,ajikin bangon da ke kallon hagu in an shigo kwanar gate din kuwa wata dakakkiyar Kofa ce a rufe itama da farin fenti mai salk'i da kwalliyar irin design din fence din wanda akayi ratsi da golden paint mai daukan ido. Wasu Jami'an tsaro ne guda biyu dake zauna a saman bencin karfe shima da farin fenti suka mike ganin motar ta tunkaro gate din kowannansu na sanye da Uniform,daya uniform din yansanda ne jikinsa dayan kuma na civil defence had'i da Bindigu rataye a kafadunsu,daya ne ya kama gate din yana Sliding din shi right yayin da dayan ya matso kusa da motar yana washe baki,a hankali gilashin motar ya dan bude "Welcome sir" jami'in ya fada baki washe. Mutumin ya juyo fuska adan sake yace"Thanks Officer,how work" cikin sauri officer din yace"Aiki Alhamdulillah gamu a cikinsa,har lokacin bakin shi a washe yake,"Ok,Allah ya taimaka" mutumin ya fadi a lokacin kuma yaja motar fuuu don angama bude masa gate din,da sauri dayan Jami'in ya daga masa hannu alamar sannu da zuwa lokacin da motar tazo saitin da yake a tsaye,Horn na cikin motar ya latsa alamar ya amsa,Parking Spot ya shiga wanda ke dauke da karafa masu farin fenti anyi masu design mai kyau yayin da saman wurin ke rufe da Alminium roofing sheet yana da girma don yana da wurin parker mota shidda,akwae motoci guda hudu a ciki akwai Hilux mai dauke da tambarin NGO,sai Vibe,peugeot 406,da kuma wata Had'addiya wadda na kasa gane sunanta,a kusa da ita ya parker motar a can karshe kuma wani hadaddan k'aton bak'in Bike ne ajiye, daga gaban parking space din wani dan daki ne wanda ba'a sa kofa ba,daga saman wurin shiga an rubuta GENERATOR ROOM,a gefen ginin wata kofa ce ta k'arafa wadda zata kaika cikin masallacin dake jikin gidan. Wani matashin saurayi ne rik'e da tiyo yana ba Flowers ruwa yana sanye da wani kodaddan Crazy Jeans da bakan T-shirt itama dai ba sabuwa b,kanshi anyi mashi aski irin na gayu,yana ganin motar ta tsaya ya saki tiyon ruwan ya nufo ta da yar sassarfa ya tsaya a gefe yana ta faman washe baki sai da aka dauki wasu seconds kafin na cikin motar ya bude yana kokarin fitowa,da sauri saurayin dake a tsaye ya kama k'opar ya idasa bude ma Mutumin,fitowa yayi a hankali yasa hannu yana gyara necktie din dake wuyansa,saurayin ne yace "Barka da zuwa yalla6ai "yana ta faman washe baki, fuska adan sake ya kalli saurayin daga sama zuwa kasa da alama shigar da yayi yake kallo kafin ya tsaida fuskarsa akan tasa yace " Yauwa T.K Babban Yaro,yayi maganar ta sigar tsokana, Cikin dan jin kunya T.k din ya sunkuyar da kansa yana murmushi yace "Ah haba yalla6ai wane mu Almajirai".Murmushi mutumin yadan yi kafin ya bude back door din motar yadan zura hannu ya fiddo da Briefcase din sa,da sauri T.K ya mik'o hannu ya karbi jakan shi kuma yayi gaba,T.k yasa hannunsa daya ya rufe duka kofofin motar ta gaba da ta bayan kafin yabi bayan mutumin. Wata corner suka shiga wadda ke a bangaren dama inda gate din gidan yake, tafiya Mutumin yake cikin corridorn a nutse, yayin da T.k ke binsa a baya rungume da jakar har suka iso wata kofa ta karafa wato Fence door daga can gaba kuma akwae bayan wata kofa wadda ke a rufe tana kallon bangaren da fence door din da suke k'okarin budewa take da alama bayan hadaddiyar kofan nan ne dake a waje kusa da gate,hakan na nufin in kabi ta kofan zaka fito wajen gidan kwanar da gate yake. T.k ne ya dawo gaban Mutumin da sauri yasa hannu ya zare kubar da ke rufe jikin Fence door din yasa hannu ya tura kofan ciki ya dawo gefe ya tsaya saida mutumin ya shiga sannan ya bi bayansa,dan Flat ne mai kyaun gaske wanda kasan ke malale da Interlocks ga Flowers jere masu kyaun gaske girman su daya,gaban flat din na rufe da fence mai dauke da glass wanda ke dauke da zanen flowers ajikinsa hakan ya bada area din da ake kira da Bolcany. Sai da Mutumin ya wuce saman wurin kafin T.k ya bi bayansa da sauri T.k ya murd'a handle din Dakakkiyar kofar shiga flat din ta bude ya dan ja gefe guda yaba mutumin wuri ya shiga kafin yabi bayansa,Ya Allah!ba karamin had'uwa Parlorn yayi ba wanda gaba daya Fentin cikinsa fari ne mai salk'i,haka Tiles din da ke malale a kasa ma fari ne kar da ratsin baki,kujerun ciki kuwa Leather chairs ne L-Shape bakake wanda ke kewaye a tsakiyan parlorn a samansu akwae Throw pillows Red color masu kyau a jere,daga gefen dama kuwa in ka shigo akwae Armchairs guda biyu suma leathers ne amman red color saman kowacce akwai T-pillow bak'i,daga bayansu kuma wani Had'addan Desk ne manne da bango wanda ke dauke da Drawers gefe da gefe fari ne kal sai faman salk'i yake a samansa akwai Table Lamps (fitilu) guda biyu jajaye kowacce a k'arshen desk din,a tsakiya kuma bakin telephone ne ajiye daga dan gaban desk din tangamemiyar Window ce wadda ke rufe da farin Blinds (irin labulen nan mai yanka yanka,wanda aka fi yawan amfani dashi a office),A tsakiyan kujerun parlon dakakken Carpet ne mai laushin gaske baki dauke da ratsin kwalliya ja da fari a samansa kuwa wani hadaddan Center Table ne na glass fari mai kaurin gaske,daga can bangon dake kallon inda jajayen kujerun suke wata Window dince itama rufe da bak'in blinds,a bangon dake kallon duka kujerun parlor din kuwa wani irin PoP Casting ne manne da bangon mai dauke da Manyan gidaje anan kuma madaidaiciyar Plasma T.V ke manne a gidan tsakiya daga kasanta kuma gidan da Sound systems suke ne da DVD player da reciever,a gidajen dake a gafe da gefen bangon da saman inda T.V din take kuwa,Hotuna ne dasu Agogo da Frames na zane wato Artworks ba karamin kyau wurin yayi ba.A gefe kuma d'an corridorn da bedrooms suke ne,a kofan corridor din flower vases ne bakake dauke da Red flowers masu ratsi da farin kananun flowers,a Angles (sako) din dake a bangon kuwa 6arin hagu Standing A.C ce babba a angle din dama kuwa madaidaiciyar Freezer ce a wurin,a tsakiyan pop ceiling din parlon akwae chandelier babba (irin fitilar nan mai adon sarkoki) kwan fari sol yayin da sarkokin jikinta bakake ne,ba k'aramin haduwa parlorn yayi ba ga sanyin A.C hadi da kamshi mai sanyaya rai da ya gauraye ko ina,da ka shigo parlorn zaka ji gaba daya yanayin ka ya canja koda kuwa kunci kake to tabbas ranka zai yi sanyiii. Mutumin na shiga ya nufi inda bakar kujerar take ya dan fada samanta hadi da aje wayarsa wadda take slim mai dan tsawo bayanta sai shining yake a gefensa,ya kwantar da kansa jikin saman kujerar don bayanta baida tsawo sosae,T.k kuwa yana shigowa yad'an lumshe ido hadi da jan dan dogon numfashi alamar sanyayyan kamshin ya kai masa karo,shiyasa a koda yaushe yake son abunda zai kawo sa part din Mutumin koba komae ka samu natsuwa.Wucewa yayi bayan Red Armchairs din parlorn ya daura jakar saman farin desk din dake wurin kafin ya zagayo tsakiyar parlorn ya tsaya saitin Mutumin yace"Yallabai akwae wani abu? A nutse yayi maganar,Mutumin bai dago ba yana a yadda yake yadan daga mashi hannu hadi da fadin "Thanks T.k,u can go" t.k yace "To a huta lpy" ya kama hanyar fita batare da ya jira amsar Mutumin b,don yasan ma b lalle ya kara cewa komae ba, Yana fitowa yaji wani zafi ya bugi fuskar sa a fili T.k yace " Kai masu kudi dai sun ji dadin su,da ace part din nan yazama nawa ai wllh fitowa sai dole"Ya k'arasa maganar hadi da wurga kafa yace "qur'an kau" a daidai lokacin ya fita daga Part din Mutumin. Ya dau tsawon mintuna a haka da alama dai ya gaji ne sosae kafin ya mike ya tunkari hanyar da zata kai shi Bedroom dinsa har zai shiga cikin koridon ya tsaya cak sakamakon karar da Telephone ke yi,a hankali ya juyo gami da kai idonsa saman desk din da telephone din yake yanata faman kara alamar ana kira,tafiya ya fara yi a hankali saida ya zauna saman daya daga cikin Armchairs din dake gaban teburin sannan ya mikar da hannunsa ya dauko kan telephone din,da murmushi a fuskarsa ya kara shi a kunnansa da alama yasan mai kiran nasa cikin murya mai tattare da gajiya ya fara magana"Hello sweetheart" dan saurarawa yayi kafin yaci gaba da magana "Ok ganinan zuwa yanzu" daria yayi har Hakoransa masu kyau da tsari suka bayyana cikin jaddada abun da ya fada ya k'ara cewa "Don't worry, I'm coming right away" yana fadin hakan ya maida telephone din ya mike har lokacin fuskansa da dan murmushi,Corridorn ya shiga kofa biyu ce a ciki daya tana kallon mutum in ya shiga wurin,dayan kuma na a bangaren bangon dake dama,sai da ya tsaya ya cire takalmin kafansa ya daura sa saman Shoe rag din dake ajiye a wurin anyi mashi design mai kyau da daukan hankali yabar safar dake a kafarsa bai cire ba kafin ya tura kofan dake a bangaren dama ya shiga,masha Allah Bedroom ne mai kyau da tsari bai da hayaniya Italian Bed ne da Bedside drawers din shi sai Dressing mirror wanda ke dauke da yan kwalaben turare da yan mayukan shafawa saidai da gani masu tsada ne don jikinsu kadai abun kallo ne,a bangon dake kallon gadon kuwa Wardrobe ce gaba daya bangon wadda ke rufe ruf a iya hangena nakasa gane yadda ake budata don banga hannun da za'a kama a bude ta ba, gaba daya Furniture din Coffee brown ne masu duhu sosai don inba ka shigo sosae ba zaka yi tunanin kayan bakake ne,haka Labulen dake a jikin katuwar Window din d'akin ma coffe ne mai kyaun gaske ga kauri wanda tsakiyan sa ke a tsage anyi hanging din bari daya,a Angles (sako) din bangon da gadon yake kuwa Floor lamps (dogayen fitilun kasa) ne dogaye ko ina an aje daya. Gaban dressing mirror din ya tsaya ya cire agogon hannunsa ya daura a saman wurin kana yasa hannu cikin Aljihun wandon sa ya fiddo da wallet dinsa itama ya daura ta a wurin ya juya ya tunkari wata kofa dake a rufe da alama kofan Bandaki ce,kofan na budewa na tsaya kallon Ikon Allah don kuwa ba toilet bane wani dan daki ne mai tsawo sai dai bai cika fadi ba akwai Wall Cabinet (durowar bango) a jikin dogon bangon dakin wadda ke a bude ga kaya nan iri iri wasu a sagale a jikin hangers wasu kuma a ninke daga gafen cabinet din kuma madaidaicin injin wanki ne wato Washing Machine a jiye.a bangon dake kallon inda cabinet din take katon Madubi ne manne da bango daga kasan shi kuma wurin d'aura mayuka ne dasu Shampoo da sabulai kala kala da alama wurin laundry ne,wato wurin wanki dasu kayan dauda,tsayawa yayi gaban tangamemen madubin wurin yana kallon fuskarsa kafin yasa hannu ya ciro wipe daga cikin wani kwali mai kyau a hankali ya fara goge Fuskansa da ita,nikam zuru nayi ina kallon ikon Allah,ya gama goge ko ina ya jefa ta cikin dustbin sannan ya tunkari Wall Cabinet din ya fara cire kayan da ke jikinsa tun daga kan rigan saman zuwa ta cikin da safar dake a kafafunsa yayi hanging dinsu jikin hangers din Cabinet din ya rage daga shi sai Vest da Short acan sama cikin wani gida ya mika hannunsa ya dauko wani abu dake a linke fari sol cikin kayan da ke wurin da alama Bathrobe ce wato rigan wanka wadda duk jikinta gashi gashi ne mai laushin gaske daga haka ya tura kopan Toilet din dake cikin wurin ya shige. *💖ASANADIN MAKWABTAKA💖* *By Oummu Imam📲* *Free Page5️⃣&6️⃣* Sanye da Bathrobe din da ya d'auka ya fito,sai da ya cire Slippers din dake k'afar sa a bakin kofan toilet din yasa wasu flip-flops dake a waje cikin laundry din,K'arasowa yayi gaban Mirror din dake a Laundry room d'in ruwa na dripping daga cikin sumar kansa da alama wanke kan yayi,Juyawa yayi ya d'aukko d'an farin towel a cikin Cabinet din bangon ya dawo gaban mirror din yana tsane ruwan cikin sumar kafin ya jawo Stool ya zauna ya rataya towel din a wuyansa a can gefen mirror din ya mika hannunsa ya d'aukko Hair dryer wadda dama a jone take ya fara busar da sumar tasa yana dan jujjuya ta da d'ayan hannun yan mintuna ya dauka yana busar da sumar kafin ya maida dryer din inda ya d'aukko ta,Hair Oil ya matsa a tafin hannunsa ya shafa ma sumar sannan ya bude robar da Cotton buds suke ya zaro daya yana kwalkwale Kunnansa ya gama goge duka kunnuwan ya jefa abubuwan wadanda ba wani dirty a jikin su cikin Wastebin. Daga haka ya mike ya nufi kofar shiga Bedroom din har lokacin Bathrobe din na a jikinsa,gaban dressing mirror ya tsaya ya fara matso mayuka yana shafe jikinsa bayan ya gama wardrobe d'in dakin ya tunkara wadda na k'osa inga ta yadda ake buda ta gefenta na dama ya tsaya,sak'a hannunsa gefenta yayi ya latsa sai ga shi ta fara zugewa da kanta,Iko sai Allah ashe Sliding ce,a tsakiyan murfin ta akwae tsaga wadda ta raba marfin biyu daidai,in ta daman aka bud'e sai ta zugo ta rufe ta hagun haka ma in ta hagun aka bud'e,komai dai na masu arziki na daban ne,Allah kai mana Arziki mai Amfani,Amin. Kayan sawa ne birjik a cikin ta wasu a rataye jikin hangers,wasu a ninninke gasu nan a tsare abun gwanin burgewa. Kowane kaya da wurinsu,Jeans,Shirts,Suits,Shaddoji,Yadiddika,wasu ma kayan a cikin leda suke alamar sabbi ne,ga Underwears suma wurin su daban tsarin kayan dai kaman Boutique,fiddo kayan da zai sa yayi had'i da underwears sannan ya latsa jikin marfin daga ciki ta fara rufewa ya juya ya nufi gefen gadon ya d'aura kayan....... Bayan ya gama sa kayan wanda T-Shirt ce coffe brown da bakin wando tracksuit wanda yad'an tsuke daga k'asa gafe da gefensa akwai zip wanda sai ka k'ura idanu zaka gani,rigan kuwa ta zauna cib ajikinsa hannun rigan ya kama cinyar hannunsa wadda take a murd'e da gani yana Bodybuilding,gaban Dressing mirror ya koma ya matso wani hadaddan mai ya shiga mutsitsika ma tafin hannuwansa,bayan ya gama ya dauko Hair Spray ya fesa ma gashin kansa sannan ya daukko turaren jiki wanda kwalbar shi kanta abun kallo ce ya faffesa ma jikinsa maida kwalbar yayi ya daukko wata itama mai matukar kyau ya fesa.....saida ya fesa turare kala ukku kafin ya dau Comb yana sharce kanshi wanda yake nad'e ko ba'a sharce ba bai yamutsewa,Drawer chest ya jawo ya fiddo da wani kwali mai kyau da k'yalli ya d'aura shi gaban mirrorn sannan ya bude,wasu irin agoguna ne masu kyaun gaske designers kala daban daban kowacce a dan gidanta ya fiddo mai fata kalan rigarsa ya daura sannan ya dauki wadda ya cire d'azun ya maida ta ciki ya mayar da kwalin hadi da rufe drawer. A corridorn ya tsaya ya ciro takalma Slide Sandals bak'ake daga cikin Shoe rag kafin ya fito parlor a daidai nan kuma telephone din ya sake fara ringing,dan girgiza kai yayi yana murmushi bai kalli inda yake ba yasa hannu ya dauki wayarsa da ya aje dazun ya fice. Ta Corridorn daya bi dazun ya fito cikin farfajiyar gidan mai girman gaske cikin natsuwa yake tafiya ya tunkari k'aton flat din dake a cikin farfajiyar wanda sak fentin shi kalar na gidan ne,Wani farin d'awisu ne ya fito daga bayan flat din ya bude jikin shi yana kuka gwanin burgewa,bansan lokacin da ni mai rubuto maku labarin na furta"lah kuga wani hadaddan dawisu,abun ka da ba'a saba gani ba,shi kau yalla6an ko kallon shi bai yi ba ya shige Entrance din,a wani dan corridor ya tsaya ya cire takalmansa da alama nan ake aje takalma kafin ashiga main Parlour din don akwai wasu takalman jere a gefe,shiga yayi cikin parlon wanda yake mai girman gaske fentinsa milk colour yana dauke da Royal Sofas masu kyau yadin su Maroon design din kwalliyarsu golden mai kyau ga Table dinsu aje a tsakiya daga can bayan kujerun kuwa dining area ce mai dauke da dinning table da kujerun shi irin design din kujerun parlorn, gaba kad'an da dining din kofa ce ke kallon su wadda corridor ne anan kuma kofofin bedrooms suke,Pop Casting din dake a bangaren da kayan kallo suke irin na d'akin mutumin da ya shigo ne sai dae hotunan dake wurin sunfi yawa har a sauran bangarorin bangon parlourn duk an kafe hotuna manya manya,hotunan wata dattijuwa sunfi yawa wasu tayi da family dinta wad'anda suke kyawawan gaske,wani kuma tayi da turawa akwai wanda tayi da Governor yana bata Award,da kuma wanda tayi da mutananmu na nan da alama a wurin aiki ne,akwae wanda take ita kadai ta nad'a lifaya fuskanta sanye da glasses tayi daria har hak'orin makkan ta ya bayyana daga kasa an rubuta sunanta,HAJIA HAUWA ADAMU ZAKEE,Akwae hotunan wani babban mutum wanda yayi suna gaisawa da shugaban k'asa,wani kuma tare da dattijuwar matar ya riketa fuskarsu d'auke da fara'a,akwae wanda kuma yake zaune a majalissar tarayya wato National Assembly k'asan hoton an rubuta sunan shi,SENATOR ALI ADAMU ZAKEE. Akwae flowers a Angles din parlorn da A.C manne a jikin bango,Labulayen cikin parlorn kuwa maroon ne da ratsin golden masu shegen kyau. Zaune saman kujera 2 seater dattijuwar matar dake jikin hotunan parlon ce gafenta telephone ne ajiye hannunta rike da magazine yayin da idanunta ke cikin glasses da alama Medical glass ne,da ka kalleta zaka fahimci ta manyanta sosae sai dae yanayin hutu yasa ba lalle ka iya kiyasta ainihin shekarunta ba,tana da haske don ba baka bace,ba kaman kuma da jikin ke samun hutu sosai, Tsaye mutumin yayi a bakin kofar shigowa ya dafa bango da hannunsa d'aya yana kallon matar da murmushi a fuskarsa. Sarai taji shigowar shi amman ta share taki d'agowa ta kalle sa idanunta na kan jaridar hannunta. Dan gyaran murya yayi,still tak'i dagowa ta kalle sa hakan yasa ya dan d'aga kafadarsa cikin ransa yace"Mun saba aii..." cikin parlon ya shiga ya tunkari inda take zaune yasa hannu ya dauke Telephone din dake gefenta ya maidashi adan sak'on da table dinshi yake, Zaunawa yayi gefenta ya d'an kwantar da kanshi a saman kafad'arta yace "Sweetheart fuskan shanun na miye ne? "What happen?" Ya kara tambaya,banza tayi dashi hakan yasa ya juya yana kallon fuskarta hannu yasa yana gyara mata bakin da ta turo alamun fushi,ya cigaba da magana, "Haba Beb fushin na miye ne..? kin wani turo baki,baki gan yanda kika yi muni ba,Smile plss..." ya fad'a har lokacin hannun shi na a gemun ta yana dan jan shi.Hannu tasa ta buge hannun shi kafin tace"Wato don kaga na damu da kai shiyasa nazama abun wulakanta wa ko? "Oh no Sweethrt ya zaki ce haka..,Am not hoping to see that day,dani zan wulakanta ki,ai ko wani nagan zai wulakanta man ke sai inda karfi na ya k'are" ya k'arasa maganar yana kara kwantar da kansa a kafad'an ta. "To amman miya sa na kira ka kace man kana zuwa harda wani cewa right away,Amman shiru ka k'i zuwa tsawon lokaci,akarshe na sake kira kak'i yin picking" tayi maganar tana dan harararsa. D'agowa yayi daga kan kafad'arta ya rik'e hannunta guda yace "Lokacin da kika kira I just came back and I was so tired shiyasa na bari in dan rage kayan jikina in watsa ruwa don insamu karfi" ya kai maganar da d'an murmushi, "To miyasa na sake kira baka dauka ba?" har lokacin bata saki fuska ba, "I was about to come here,lokacin da kiran ya shiga shiyasa naga no need in daukan"ya karasa maganar yana wani lumshe ido, "Yanxu dama duk saboda wannan ne kike ta faman daure fuska,to Am sorr.....bai karasa ba ta katse shi da cewa "bashi kadai bane" "To,what else? Ya tambaya. Gyara zama ta d'an yi shima ya gyara zama yana kallonta alamar ita yake jira tayi magana..."yanzu tsakani da Allah kana kyauta ma kanka,ace kullum sai nayi fama da kai kafin kazo kaci abinci,sam baka son cin Abinci..."katse ta yayi da cewa "Ni kuma,duk abincin da nike ci" Yana maganar da d'an murmushi a fuskarsa "karya kake baka wani cin abinci yadda ya kamata" ta fada tana harararsa,da mamaki yake kallonta with his eyes wide open yace "Yanzu ni da girmana kike cewa karya nike" d'an ta6e baki yayi yace "nidai nasan ina ci kawai dai rigimar kice,ko kuma so kike in rinka yin cin da ya fita Musulunci,Me I don't know" ya dan buga hannunsa guda kan kujera, "baka wani ci,d'an wanda kake cin ma ai sai kaga dama,kullum ka dawo aiki sai ka shige part din ka kadau uban lokaci wai kana wanka sai kaga dama kazo ka tsakuri abinci ka kuma fucewa,wani lokacin ma I have to called u,just like now dai" Yar ajiyar zuciya yayi kafin yace "Nidai nasan ina cin Abinci da banci ai bama za'a ganni haka ba,ji fa uban naman dake hannu na" yayi maganar hadi da d'aga hannunsa sama yana daria, ta6e baki tayi tace"Naman daga k'arfe ko,wllh kabi a hankali inba haka ba wataran k'arfen zai d'aga ka,ace mutum ya wuni yana zurga zurga baka nan baka can amman wai sai an matsa maka kaci abinci, da daddare ma ba wani na kirki kake ci ba da anyi magana kace wani Light food kake bukata". "Fata kike man karfen ya daga ni kenan"ya tambaya,"Ni ba fata nike ba kadama Allah ya nuna man ranar kawai dai ina so ka rik'a cin abinci sosae don kana bukatar hakan,ka daina yaudarar kanka da wannan murd'ewar don bogi ce,kullum kana dawowa direct ka wuto nan ka cika cikinka sai kaje kayi ta bauta ma jiki uwa wata mace,ni wllh ma na dade banji ko ganin mace da take ma jiki wahala irin ka ba abun naka yayi yawa", "Haka dai kika ce ni bana ganinsa a wahala duk abunda ya dace mutum yayi don tsaftar kansa nike nothing's too much" Yaci gaba, "Toh why not a rik'a kaiman abincin can part dina kinga in nagama wahalar jikin kaman yadda kikace sai inci ko? "Kaji dad'in kin cin kenan,a gaban nawa ma ba ci kake sosae ba, balle ba idona". Dariya yake sosae yace "sai kinsa man ido kenan,sai kace wani karamin yaro,You know what,in kingan nadawo na dade ban nemi abinci ba bana jin yunwa ne,kinsan bai yiwuwa in dauki wannan hours din wurin aiki ba tare da naci komai ba" Yamutsa fuska tayi tace "Abinci! Kai dinne zaka ci abinci a waje,wanda ma aka yi cikin gidan sai kaga dama zaka ci balle wanda aka yi a waje,nasan dai kasha wannan bak'in lemun d'an gado sai ko snacks kilan,suma in kagadama kenan"jingina bayansa yayi da kujerar yace"Yanzu dai zaki sa akawo man abincin ko kuwa,don am running out of time fa,ya fada yana duba Wrist watch dinsa,yaci gaba"In kuma inyi tafiya ta to" yayi maganar da sigar tsokana, "Ka tafi mana,cikin wani ba naka ba". "Uhm ai kam da baki bar ni nayi exercise dina ba yadda ya kamata kiran wayarki kadai ya isa ya hana ni yin komae" Yayi maganar yana yar daria."Allahu,yanzu ni har nazama abun tsokana ko,don kawai kaga na damu da kai,don nasan inka cutu tamkar ni na cutu ne shiyasa amman in sha Allahu na daina takura maka,continue doing as u like"ta karasa maganar tana kokarin tashi,da sauri ya jawota jikinshi sai faman daria yake yace "Just kidding u beb" ture sa ta fara yi tana ce mashi "Ni ka kyale ni abun da ke ranka game dani ne ka fada ai" Daria yake sosae don sun saba sai ta tak'alo magana karshe kuma tayi fushi kan abunda bai kai ya kawo ba, Mutsu mutsu ta shiga yi tana son kwace kanta sai dai ya rike ta gam ba yadda za'ai ta iya kwacewa,a kusa da kunnanta ya kai bakinsa yace"Haba Hajiyan Senator nine fa na wajenki,your heartbeat" "Naji sake ni to" yace"sai kince kin hakura my sweethrt, "na hakura amman zan dau mataki a kanka..." wane irin mataki kuma? Tace "to ka sake ni sai in fada ma" sakin ta yayi tace "Matakin share ka zan d'auka ba ruwana da kai duk abunda kaga ya dace da kai kayi tunda ni gani kake ina takura ma" ta karasa maganar tana turo baki. "Oh ya Allah,ba kince kin hakura ba miye kuma na repeating same magana,ba kyau fa ruk'o kinsani,kuma ni na gaya maki wasa nike,ina jin dadin yadda kike so na kina nuna mun kauna nima kuma ina kaunarki and am telling u this deep from my hrt" Ya k'arasa yana nuna mata bangaren zuciyarsa,Murmushin jin dad'i tayi don ba karya yayi ba tana matuk'ar jin shi a ranta, Shima wani hadaddan murmushi yake yace" That's my beb" da sauri tace "kaga ka daina ceman beb din nan tsofai tsofai dani kayi tace man wani beb kamar wata tsohuwar yar dunia ta k'arasa maganar tana ta daria,"No ba wani yar dunia,ni ke beb dina ce,pls kisa akawo man Abincin" "toh" tace ta fara kiran mai aikin ta,"Saude,saude...,"daga ciki Sauden ta fara amsawa ta fito parlorn ta kofar Kitchen dake a gefen dining area tana kokarin k'arasowa inda suke Hajiyan tace "Je ki kawo masa abinci,"toh sauden ta amsa ta kalli inda yake ya kwantar da kansa a jikin kujerar da suke zauna,tace "Ina wuni...." lpy" ya amsa ba tare da ya d'ago ba, Yan mintuna ta d'auka ta dawo dauke da Tray saman shi wata irin Warmer ce mai kyau a gefen warmer din Bowl ne an d'aura Plates kalar bowl din, samansu kuma Cokulla ne da Serving spoon da gani na kulan ne duk anyi Wrapping dinsu,dining table din ta nufa...."Bring it here"ya dakatar da ita daga daurawa saman table din ta nufo inda suke saida ta fara daura tray din saman kujera one seater ta kinkimo sofa table din da kyar hajia na fadin"bi sannu dae kar ki bige kafa," To" tace lokacin ta karaso da table din gaban shi ta maido tray din saman shi ta fara Serving din shi,wata hadaddiyar fried rice ce tasha Vegetables don ba abunda babu na kayan hadinta sai kamshi ke tashi ta warware papern jikin serving spoon din ta fara zuba mashi,ta kusa zuba rabin plate din yace "Is okey.." wani kallo hajiya tayi mashi kana tace da Sauden k'ara masa,"To sauden tace, ta k'ara zuba one spoon tana kokarin karawa..."Ya isa! Yace da dan hanzari waigawa yayi ya kalli hajiar yace "In ta cika man karshe barinshi zanyi ne" ta6e baki hajia tayi tace "kai dai ka sani" d'an murmushi yayi ya juya ga abincin lokacin saude ta rufe warmer din ta bud'e bowl din wanda yake dauke da pepper chicken kamshin sa ba'a magana ta debo wata katuwar cinya ta daura masa a gefe tana kokarin kara masa ya dan d'aga mata hannu alamar ya isa,hajia dai na kallon shi ya d'ago suka had'a ido "Uhm" tace ta juya mashi k'eya, d'ayan plate din da ta rufo wanda ta zuba mashi abinci ta rufe bowl din da shi ta warware cokullan wanda Spoon ne da Fork ta sa mashi cikin abincin,mik'ewa tayi tace "Wane lemu zan kawo" yad'an daga hannu yace"Just water" Hajia tace" Ai mu bamu da lemun da ya saba sha" tayi maganar tana ta6e baki" Zan d'auka in zan fita" yace lokacin kuma ya fara cin abincin sa, "Coleslow din ya kare ne?" Hajia ta tambaya,Saude tace "A'a yanzu zan kawo masa da ruwan" "Just bring the water" yace,hajia tace "kawo masa ruwan kawai,"Toh" Saude tace ta juya don daukko ruwan,Bottled water ne da Acrylic cup ta kawo masa d'ora su tayi gefen tray din ta d'ago,"Thanks" yace,da alama halinsa ne duk akai masa abu yace thanks,"A ci lpy" Saude tace ta juya ciki, Cikin natsuwa yake cin abincin,hajia ce ta fara magana"Wai yanzu har ka fita d'aga karfen? Yar daria yayi yace "Nifa ba daga karfe kawai nike ba duk wani abu na motsa jiki wanda naga ina ra'ayi ina yi,wani lokacin ma ball nike bugawa," "Ball? ai nayi zaton ka daina ta tuntuni" yace "Eh na daina football amman inayin Basket ko Volleyball Har Badminton ma in ina ra'ayi" ya karasa maganar lokacin ya kai abinci bakinsa, Ajiyar zuciya tayi,tad'an tur6une fuska tace, "To kad'an huta yau mana tunda yamma tayi sosae" ta fada tana kallonsa,sai da ya cinye abincin dake a bakinsa yace "So kike in kasa bacci yau,kinsan fa I'm addicted to it" shiru tadan yi kafin taci gaba, "Turawan nan duk sun lalata ka,da duk baka wadannan abubuwan inaga kwallon kafa ce kawae ka ke yi itama kace wai ka bari" Murmushi yayi yace "Sun dai gyara ni,Exercise ai is very² important.....har lafia ma mutum yafi in yana yi,yanxu kinga zan iya d'aukanki a hannuwana bama goyo ba inta yawo dake ko'ina batare dana gaji ba,Wani irin kallo tayi masa tace "Tunda ga jaririya ba" yar dariya yayi taci gaba, "To mi zai hana ka rika yi nan cikin gida tunda akwai wadataccan fili dama kuma naga ai akwae kayan motsa jikin a can G.R.A ko? Kaga kasamu lokacin kanka," yace" No!a Gymnasium yafi dadi cikin sauran players anan dawa zan rika yi,ko ke? dan ta6e baki tayi kafin taci gaba, "Amman dai bada wancan gingimemen mashin din zaka fita ba ko? Ya fahimci bike dinsa take nufi,"Saboda me kika tambaya"yayi maganar yana dan yagar cinyar kazar da ya d'aukko da fork,tace "hakanan nidai bani son mashin din wllh,baida wani Amfani," dariya ya d'an yi yace "Da baida amfani ayi shi sweethrt...." "to ai nidae had'arin shi kawae na sani, Shifa ya kusa kashe dan gidan tsohon shugaban k'asa da kyar ya rayu,an ma ce sai da akasa masa k'arafa a cikin kai fa" Tana maganar fuskarta dauke da damuwa, taci gaba "ga yaron nan dan gidan Honorable Dalhatu Mande wanda ya mutu can kwanaki shima fa bike dinne ya kadashi kwanya waje haka aka tattaro shi nasan duk da lokacin baka k'asar bazaka rasa jin labarin ba a social media ko? Gyara zama yayi ya aje sauran naman yace "Ai nama san shi munyi junior secondary tare duk da dai mu muna a gaban su,nasan lokacin da ya fad'i da bike din....." da sauri Hajia ta rik'e ha6a tana salati "Yanzu duk da haka shine ka zuba uban kudi naira na gugan naira,har naira million biyar ka jajibo mana masifa!" Shi dai kallon ta kawae yake "To gaskia ni bana son mashin din nan wllh don aduk lokacin da ka fita dashi hankali na mugun tashi yake har sai naga kadawo nike samun natsuwa to wllh asan yadda za'ai dashi gaskia,hakanan mutum ya zuba mak'udan kudi ya siyo ajalinshi ina dalili" ta k'arasa maganar tana watsa hannuwa. "Yanzu ya kike son ayi dashi? da sauri tace"A sayar dashi kawae don bana ce aba wani ba tunda ba mashin din arziki bane inma kai baka da abunda zakai da kudin ni kaban ina da abunda zanyi dasu" Ajiyar zuciya yayi kafin yace " ke mi zaki yi da kudi? da sauri tace"Yo in zuba a Organization din mu mana kudi na yawa ne a wannan wurin ai kullum buk'atar su ake ba kaman yanzu da mutane ke fama kaga kaima ka samu lada kuma an kawo karshen wancan dirkeken mashin din maras Amfani. D'an ta6e baki yayi yace"In dai kina bukatar kudi ne ki gaya man na baki,Amman maganar saida bike din can bata taso ba,kinsani bana siyan abu in kuma saida,In har na mallaki abu to fa sai dai na bayar badai saidawa ba" ya karasa hadi da d'an girgiza kai,yaci gaba, "kuma ma ni inason abuna that was why I bought it all the way from US" yayi maganar on serious note,Hajiya tace "Nima ba don had'arin shi ba bazance ka sayar ba,kawai dai ina gudun wani mummunan abu ya faru da kai ne ba fata nike ba" Maida jikinta tayi ta jingina da kujerar,fuskarta har lokacin da damuwa, Tissue ya yago daga saman table din da telephone yake ya fara goge hannu,kallonshi hajiya tayi sai kuma takai dubanta cikin Plate din abincin da ya ci,ya cinye saidai yabar d'an saura kaman yadda dai yan gayu ke yi,naman dai ne yaci rabi yabar saura. "Yanxu cinyar kazar ma bazaka iya cinyewa ba? "Na k'oshi ne" ya bata amsa "To da ka barta waye zai ci sauranka" "Ke mana" ya bata amsa a takaice. ta6e baki tayi,tadan d'ago daga jikin kujerar "Ni kam bazan ci ba kai zaka ci......."bata samu damar karasa maganar ba saboda sauran naman daya dauka ya tura mata a baki ya rike kanta da hannu daya sai kace ya rike karamar yarinya,bugun hannunshi ta fara yi tana kiran"HAISAM! HAISAM!,mi kake yi hakane" baki cunkushe da nama take maganar,bai kyale taba har saida ya tura mata ita duka ya mik'e yana daria "Ba gashi ansamu wanda ya cinye saura na d'in ba" baki cunkushe da nama tana taunawa take harararsa,duk'awa yayi a gabanta ya kama dukkan hannuwanta sai kace wasu Saurayi da Budurwa,koda yake a hak'ikanin gaskia suma cikakkun masoyan juna ne suna kaunar junansu sosai,suna sa junansu yin abu,haka suna hana junansu,ya fara magana cikin nutsuwa"Nasan don kin damu da ni ne that was why kike zullumin kada bike nima ya kasheni..."dan murmushi yayi kafin yaci gaba "Itafa mutuwar nan d'aya ce sweethrt sabubbanta kuma da yawa,so don ina hawa bike ba yana nufin dole shine zai kashe ni ba ko ya lahanta ni kaman yadda yayi ma wasu,Kowa akwai silar Ajalinsa wasu ma hakanan suna a kwance ko a zaune suke mutuwa,kamar dai yadda kike zaune din nan sai kiga na hau bike din naje na dawo lapia ke kuma kin mutu a zaunen...." da sauri ta tsaya da taunar naman da take tana mashi wani kallo,Daria yake sosai ganin yadda ta yi, lokacin ya mike ya nufi dining area gaban Handbasin ya tara hannuwansa yana wankewa kafin ya bude k'atowar Deep Freezer din dake jikin bangon kitchen ya d'aukko Canned Coke ya rufe,"I know why u look all worried,saboda wancan tsohon ne" ya fad'a yana nuna k'aton hoton wani mutum da Coke din hannunsa dake a gidan saman da Plasma t.v take,sanye yake da kakin Sojoji babban mutum ne sosai kayan sun kar6i jikinsa yana da kyau ba laifi ga dogon hanci,kalar fatar shi kuwa za'a iya kiranshi da wankan tarwada wato shi ba bak'i ba,ba kuma fari ba,daga kasan hoton anyi rubutu kaman haka,GEN. ADAMU ZAKEE,daga k'asan rubutun kuma shekarun daya dauka a raye ne zuwa shekarar daya mutu,kallon hoton hajia take da wani irin yanayi kafin ta juyo da kallonta kan Haisam wanda yake kokarin fita,d'an murmushi tayi sam ba walwala a tare da ita tace,"Take good care of ur self for me,pls banda tuk'in gangancii". "Don't worry beb zan dawo lapia,ba yanxu zan mutu ba...tare ma zamu mutun amman sai nayi aure,nayi ya'ya harda jikoki kaman ke,da nayi Achieving all my goals,then sai mu mutun" Ya karasa maganar yanata faman daria adaidai lokacin kuma ya kai bakin kofan fita...da dan d'aga murya hajiyan tace kace sai nazama leda kenan" Daria sukai su duka,a lokacin kuma ya fice,ita kuma hajia ta maida dubanta kan hoton sojan mutumin nan tana girgiza kai, A yanayin Haisam bazaka ta6a tunanin za'ai wannan dogon hiran dashi ba don kallo daya zakai mashi ka yanke cewa irin miskilan mazan nan ne, masu ji da kai,kuma hakan ne don ba kowa yake sake mawa ba yayi fira haka,sai mutanen da ya shak'u dasu sosae suma d'in sai yana jin yin firan,Amman tsakaninsa da hajiyansa wannan ko yaushe yana da lokacinta kaman yadda itama hakan yake a wurinta. *💖ASANADIN MAKWABTAKA💖* *BY OUMMU IMAM📲* *Free Page7️⃣* Da d'an hanzari ya nufi Part dinsa bayan ya fito daga part din hajiar,hango T.k yayi cikin Parking spot yana ta faman goge motar daya dawo da ita,hakan yasa ya juya shima ya nufi Parking space din ya d'aga ma T.k hannu alamar yazo,da sauri T.k ya daura dan towel d'in saman motar ya nufo sa tun kafin ya k'araso wurin shi ya d'an daga murya yace "My bag" hadi da yi masa alama da hannunsa wato ya d'aukko masa jaka. Juyawa T.k yayi da dan gudu gudu ya nufi part d'insa,shikuma ya shiga cikin Parking space din yana kokarin fiddo da Bike din,daidai lokacin da ya fito dashi cikin harabar T.k ya dawo d'auke da jakar,wata katuwar jakar goyo ce sandar racket ta leko ta cikin jakar ya rataya hannunta daya a bayansa,saukko da jakar yayi yana kok'arin mika masa ya tsaida shi,alama yayi masa da hannu ya bud'a jakar hakan yasa T.k ya aje jakar kasa sannan ya bud'e. Umarni yayi mashi da ya fiddo masa takalman ciki,T.k yasa hannu ya fiddo da wasu kambos masu kyau ya mika masa kana ya zuge zip d'in jakar, D'an jujjuya su yayi da alama basu yake son sawa ba,sai kuma ya juya hannunsa ya duba agogo,ganin lokaci yaja yasa ya duk'a don yasa takalman cire na kafarsa yayi sannan yasa kambas din,ya mike lokacin da ya gama daura igiyoyin takalmin ya haye saman Bike din ya zauna sosae,shi kam T.k sai faman kallon mashin d'in yake ko kyaftawa bai yi, Hannu Haisam ya mik'a ya ciro helmet (hular kwano) daga saman kan bike din yana kokarin sawa a kansa,juyawa yayi ya kalli T.k wanda ke tsaye k'ikam da jaka a hannu ya k'ura masa idanu. Yace"Yadae T.k,ko zaka d'ana ne? da sauri T.k yace "Ah yalla6ai wannan ai sai ku,yafi karfina" yayi maganar yana daria,d'an murmushi Haisam yayi yace"Saboda me yafi karfin ka baka iya mashin ba? Da sauri T.k yace "Na iya yalla6ai irin dai namu wanda aka saba hawa,banda wannan ni tsoronsa ma nike wllh ko goge sa nike sai inta ganin kaman zai fad'o ya danne ni, shiyasa duk in ina goge shi ban yarda na duk'a k'asa" ya karasa maganar yana ta faman daria,shima Haisam din yar daria yayi,ya mik'a masa hannu lokacin da ya gama sa hular alamar ya bashi jakar,da sauri T.k ya mik'a masa,ya amsa ya goya ta a bayansa sosae,d'an juyowa yayi ta cikin hular yace, "Ka shirya soon zaka d'ana don bai yiwuwa kana masa wahala amman baka ta6a hawa ba" yayi maganar da sigar tsokana hakan kuma na nuni da yana shiri da T.k din har suke magana haka, Zaro ido T.k yayi sosae yace "Nidai yalla6ai wallahi na yafe" ya d'an daga hannunsa, shikam Haisam daria yake ta cikin hulan ganin yadda T.k ya zaro ido yana mamakin yadda kowa ke tsoron bike din wanda shi kam sarrafa sa yake tamkar ya hau keke,don sun saba yin gasar tsere dashi a U.S,A daidai lokacin ya kunna bike d'in yana murza shi, kararsa ta karad'e cikin gidan ji kake wani "BHUUMMM²...." da sauri T.k yaja baya,yayin da d'aya daga cikin Officers din bakin gate ya mik'e da sauri ya kama gate din yana sliding din sa,dayan kuma yace"Bari mutum ya matsa kar a d'ebi kwanyarsa yanzun nan" gaba d'aya suka sa daria,A daidai nan kuma Haisam ya taho da gudu,da sauri Officer din daya bude Gate yayi tsalle sai gashi a gefe guda,gaba d'aya ya basu daria sosae harda Haisam din wanda ya fice. Hajiya dake zaune a Parlour tana jin k'arar Bike din tasa hannu ta rufe kunnuwanta har saida ya fice kana ta bud'e,girgiza kai tayi a fili tace "Allah Ya Tsare". ________________________________ Fitowa daga cikin dakin Fatuu tayi,kofar d'akin gwaggo ta nufa sarai fa taji abunda gwaggon tace tayi amman saboda jan magana taje kofar d'akin tana cewa "gwaggo gani" daga cikin d'akin gwaggon tace "baki ji mi nace kije kiyi bane? "Eh" taba gwaggon amsa, "Kije cikin kitchen nace garin tuwo na nan cikin roba kiyi sauri ki tankad'e" Juyawa tayi ta nufi kicin d'in wanda ke a gaban dakinta tana ta faman zum6ura baki tana k'unkuni da gani bata son yin tankad'an. Daukko garin tayi ta fito kofar kicin din ta aje robar da karfi duk don jan magana,ta koma ta daukko tray din silver da rariya shima ta sake shi k'asan yayi k'ara sosae,daga cikin daki gwaggo tace"A'ah Fatuu lafian ki kuwa? Cikin turo baki tace"fad'uwa yayi" gwaggo tace "Yi maza ki gama to", Zaunawa tayi k'asa dirshan ta fara yin tankad'an fuska daure,fitowa gwaggo tayi don ta fara had'a wutar yin tuwon a bakin k'ofa ta tsaya cak tana karema Fatuu kallo wadda duk tayi dama dama da gari har a kumatun ta,gashi duk ta zuzzubar a k'asa,karasowa inda take gwaggo tayi tace "Yanzu don Allah garin ne kika yima haka,kuma miya kai gari har a fuska?Shiru Fatun tayi sai faman d'aure fuska take,"ba da ke nike bane? Sannan tace"Ni fa bamma san ya zuba ba" "To mi akai miki kike ta faman d'aure fuska,hala tankad'en ne baki son yi? "A'ah" tace sannan taci gaba da magana tana turo baki "kema ce gwaggo wllh....sai kuma tayi shiru, "Nima ce mi? Gwaggo ta tambaya tana kallon ta da mamakin jin tace itace to ita mi tayi kuma. "Sai kiyi ta faman yi mana tuwo,sai kin kashe mu dashi" hannu gwaggo tasa ta rike baki alamar mamaki tace"Ni din ce zan kashe ku da tuwo,har da yaushe yaushe nake yin tuwon da zai kashe ku, Amman wllh fatuu baki da godiar Allah sam,ko yau da rana ba shinkafa da wake nayi maku ba?" "To ai baki yin shinkafar ne muci ta har dare sai ki tayin tuwo da daren,kuma wani lokacin ma har da safe sai kice wai shi za'a ci" tayi maganar tana ta turo baki. "To bazan yi shinkafar har daren ba tunda bake ke nemo man kudin shinkafar ba,iya fitina kawai da asara kika iya siyo man,inma baya ga sharrinki ba sai ina nan da yamman nike samun yin tuwon ba,Kuma in bama samun wuri ba acan k'auyen naku ba tuwon kuke ci ba rana da dare wani lokacin har a d'umama da safen gwarama ni,in anci da safe ana had'awa da wani abun,ko ke ai sai kin gadama kike ci da safen ko" tana ta magana har ta shiga cikin kicin ta fito da murhu ta nufi can bangaren d'akinta wani dan fili ne anyi rabin katanga ba'a ida ba akwae keji da yan kaji a ciki ta aje murhun ta fara d'aukko itace daga gefen cage din tana sawa acikin murhun, "Wallahi mu bama yin tuwo rana da dare,wannan ai sai su Yaaya dasu Altine,mu fa kinsan yan gayu ne a gidan,don mu har shayi da biredi muke sha,kuma ana mana shinkafa da miya har da naman zabbi ehe" Ta karasa maganar tana murgud'a baki don tasan gwaggon ba ganinta take ba, Daga inda gwaggo take tana kok'arin daura tukunya saman murhu tace "Ai sai ki tattara ki koma can din kici gaba da shan shayi da shinkafar tunda ni nan kashe ki zan da tuwo" da d'an fada fada tayi maganar,itakam fatuu sai ta kyalkyace da daria tace "Ai ko na tafi sai kinje kin dawo dani,don nasan baki iya zama ba tare dani ba" Girgiza kai kawai gwaggo tayi,don tasan inta biye mata haka zatai ta mata surutan banza da wofi "In kin gama kije ki wanke man tsakin kuma ki sauri", "To" fatun tace tana kokarin mik'ewa,don taga kaman ran gwaggon ya 6aci ta kuma sani sarai mi zai iya biyo baya,Wanke tsakin take yi a wurin da ake wanke wanke ta fara magana"Gwaggo fushi kika yi? ta6e baki tayi tace"Uhm,inyi fushi dake ince nayi fushi da wa,ai da mai cikakken hankali ake fushi...."da sauri Fatuu tace "Wayyo gwaggo ni d'in ce banda cikakken hankali,wllh inada hankali na" ta k'arasa maganar tana ta turo baki, Wai nikam ina Amadu ya shige ne,tun d'azun banji d'uriyarsa ba ko da na lek'a nemanki naga kes dinsa a rufe" fatuu tace"Nima dana fita a rufe yake kuma har na dawo yana rufen", "To ko ina ya shige,Allah yasa l..." gwaggo bata k'arasa maganar ba suka ji ana bud'e d'akin da ke cikin zaure,da sauri fatuu tace"To gama shi nan ya dawo,"KAWU AMADU,KAWU AMADU..." ta fara kwala masa kira,Wani matashin saurayi ne mai d'an tsawo fari kaman gwaggon sai dai yanayin rashin hutu yasa farin nasa yin kala kala,Shigowa yayi yana amsa kiran da fatu ke masa shima da karfi "Na'aaamm" yace "wannan kira haka Hajia fatuu..."da sauri tace "Maman ka keta neman ka bani ba" tayi maganar tana nuna masa gwaggo wadda ta fito daga inda take yin girkin tuwon tana girgiza kai jin maganar da fatuu tayi,kallon sa tayi da murmushi tace"Ina ka shige ne wai Amadu? Yace "Wllh naje wani wuri ne daga nan na biya kasuwa don akwae abubuwan da suka k'are ana ta nema,lafia dai ko?" ya tambaya,"Eh lafia lau,dama maggi nike so namu na nan ya kare," yace"To" ita kuwa fatuu cewa tayi"Kashh dama baka dawo ba" da sauri suka juya su duka suna kallonta da mamaki ya tambaye ta"Saboda me? tace "Inda baka dawo ba har aka gama tuwon dole abar ni ai inyi kwad'o da mai da yaji tunda ba magin miya" ta k'arasa maganar tana gyad'a kai,Gwaggo ce tace"kar ka biye mata,kaje ka bud'e shagon,tun dazun take shashancin da ta saba,tuwon ne bata so,kuma sai nayi,sai dai mutum kar yaci,ta juya ta koma wurin girkin. Amadu ya kad'a kai zai fita a hanya yake fad'in"Lallai yarinya tuwo ai saiti ne,sai da shi mutum zai ji shi gam gam,adaidai nan ya fice,ta6e baki Fatuu tayi kasa kasa tace"dama ai bakin ku d'aya uwa da d'a,kun daukko ni zaku kashe ni" Gwaggo ce ta katseta"Wai nikam har yau tsakin bai wanku bane? "Ya wankuuu" fatuu ta fad'i da karfi,"To ki kawo man mana da ruwan, kije ki kar6o magin kuma" tace "to, Magin taje ta amso sai da ta rabo shi da biscuit wai yunwa take ji kafin ta kawo magin tace "Gwaggo wai miyasa baki yin tuwon a kan d'an gas dinmu,kinfi son kiyi ta wahalar hura icce ne? "Gas d'in ne yayi kasa,kuma dai ni nafi son yin tuwo kan murhu yafi dahuwa" gwaggo ta bata amsa,"To ki kawo ni inyi miyar asaman gas din" fatuu ta fad'a, "Niba in baki yin miyar ba,k'arshe kije kiyi ma mutane shirme" "Wallahi bazanyi ba" Fatuu ta fad'a,gwaggon tace"aifa dayake ke kike son yi dole ki fad'i hakan,da hakanan ne nace kiyi man abu sai kin gama 6ata man rai sannan, Taci gaba"sau nawa na baki kikai man ba daidai ba,kawae don inason ki iya girkin ne nike sake baki,don kar inyi maki aure baki iya ba..."Wata irin juyowa Fatuu tayi tana ma gwaggo dake talga tuwo wani irin kallo tace"Aure! Wa za'ai ma auren? "ke mana,nan da d'an lokaci kadan mi za'a jira" gwaggo ta bata amsa,da sauri tace"Wallahi ba wanda zai man aure har sai nazama Doctor ehee" Gwaggo ta juyo tana kallonta tace"Likitoci ai nutsattsu ne,a hakan ne zaki zama wata doctor,kece kullum rigima da yaran unguwa ga rashin nutsuwa wurin wauta kuwa kece lamba ta d'aya" "Amman dai ai inada kokari a Makaranta,kuma Malaminmu yace in kana da kokari komae kake son zama zaka zama," gwaggo tace"to nidai ina gaya maki muddin kina son ki zama likita sai kin daina rashin jin magana ki natsu don nidai duk likitocin da nike gani masu natsuwa ne,kije ki daukko kayan miyan in nuna maki wanda zaki jajjagan in kinga dama",Juyawa tayi ta nufi kicin da k'arfi tace"To Kakus zan natsu,amman duk wanda ya raina min wayo bazan yarda ba eheee"daga haka ta shige cikin kitchen din. *💖ASANADIN MAKWABTAKA💖* *BY OUMMU IMAM📱* *Paid Book* *Free Page8️⃣* Officer Civil D,ne ya dawo saman benci ya zauna bayan ya rufe gate d'in har lokacin suna dariyar abunda ya faru lokacin da Haisam ya fice,ya kalli Abokin aikin nasa yace "kasan mi? Officer P yace "A'a" Officer CD yace "Wallahi tunda nike ban ta6a ganin mutumin da ke burgeni sosai ba irin mutumin can Haisam,"Mike burgeka a tattare dashi ne? ya tambaya, "gaba d'aya lifestyle din shi,kai wallahi ba don ance mutum tara ne bai cika goma ba da nace shi din ya cika goma cib,ga kyau,ga ilimi,uwa uba kuma ga kud'i,ga iya daukar wanka malam ko a mata sai anyi dogon bincike za'a samu kamarsa he's a very handsome and classy guy, da kuwa za'a bada kyautar wanda yafi kowa tsafta a Nigeria to wllh ba wanda ya dace sai shi,Daria Officer P,ke yi sosae ganin yadda Abokin nasa ya dage sai faman bayani yake,yace "Kai dai shi ka sani ne shiyasa kake ganin hakan, duk da dai duk abunda ka fad'a game dashi ba k'arya kayi ba gaskia,Amman ni kasan mi ma ya burgeni da shi sosae? Da sauri d'ayan yace "Sai ka fad'a..." yaci gaba "Rashin girman kansa,a fuska idan ka ganshi lokaci guda zaka yanke mashi hukuncin yana da girman kai,sai kayi mu'amala dashi zaka fahimci yana da saukin kai,ji fa ranar nan yadda yazo ya zauna nan muna yin fira har d'an sa baki ya rink'a yi,duk da ba wani dad'ewa yayi ba wallahi nayi mugun mamakin hakan don ban ta6a zaton hakan b,su kam dai sunji dad'i wllh,itama hajia badai kirki ba, Officer CD, yace"Wallahi kam ai wasu mutanen are very lucky,kaga kaman su suka tsarawa kansu rayuwa"cikin tsananin daria d'ayan yace "kai baka cikin su ne? "Uhm inda ina cikinsu ai baka ganni nan kullum tsugunna bakin gate ba,in za'a shiga in bud'e,in aka fito in rufe....d'ayan yace "A dai rik'a gode ma Allah,don shi gwanin hikima ne daga haka sai kaga ka kai inda baka ta6a mafarkin kaiwa ba,duk rayuwar da ya za6a ma bawa ita ta dace dashi,in ka kasance mai gode masa sai ya kara inganta maka...da sauri Officer CD ya katse shi da cewa "Wannan gaskia ne,Alhamdulillahi ala kulli halin,ya cigaba"yauwa nikam inata son intambaye ka..."Officer P yace "game da me fa?" yace "wai mike tsakaninka da Saude ne? Wani irin kallo yayi masa yace"Wace Saude? d'an harararsa yayi yace "ni zaka ma duniyanci kace baka san wace Saude nike magana akai ba" daria Officer P yayi yace "Oh wai ko Saude ta nan gidan kake nufi,to ni mike tsakanina da ita banda alakar wurin Aiki daya da muka hada" ya k'arasa maganar yanata daria,Officer CD yace"don kun had'a wurin Aiki d'aya shiyasa take baka kulawa ta musamman kenan" daria sosae yake yace "ni banga wata kulawa ta musamman da take bani ba kawae dai Sharri zaka man,in don Abinci da take kawowa wannan ai mu duka take kawo mawa,kuma da izinin masu gidan" ta6e baki yayi yace "Uhm kaji nayi maganar Abinci,kuma ko a Abincin ma ai akwae ayar tambaya don ba iya Abinci take kawo ma ba duk wani kayan kwalam da makwalashe da akaci aciki sai ta kawo maka,rannan fa ina ji tana tambayarka wae mi kake so a dafa,ni mamaki ma yasa na kasa yima magana a lokacin" daria sosae Officer P yake yace "nidai ba abunda ke tsakanina da ita,ka rufa man Asiri kada Matata taji kasa a hanamun kwanciyar hankali" ta6e baki yayi yace "in tayi wari maji ai" Yace "ba abunda zai yi wari bare har kaji. Daukar takalman da Haisam ya cire T.k yayi ya koma cikin parking space din ya k'arasa goge motar,sannan ya nufi part d'in sa don kai takalmin ya kuma gyara masa dakin,a ka'ida dama indai Haisam din ya shiga part din bayan ya fita sai an shiga an gyara masa,kuma t.k ne mai gyarawa.Yana shiga ya aje takalman a gefen kofa ya nufi saman kujera L-shape ya zauna ya d'aura kafa daya kan daya ya wani sha murr,can ya kece da dariya a fili yace "yasin dole ake ganin masu kudi kaman suna da girman kai,yo mutum na kwana yana tashi cikin wannan daular ai dole aga yana fad'in rai koda shi ba haka bane a wurinshi....haka t.k yayi ta sokana dama ya saba duk yazo gyaran sai yagama shiririta kafin yayi abunda ya kawo shi,don yana da tabbacin ba CCTV a cikin parlon sai a waje. Mikewa yayi yana fadin"to mima zan gyara anan,ba abunda parlon yayi" Bedroom ya nufa nan ma dai tsaf yake,kwalaben turaren da Haisam yayi amfani dasu ya maida ya jera su,ya dau Bathrobe din daya aje gefen gado ya maida ita cikin laundry ya shanya,ya shiga cikin toilet din wanda yake Had'addan gaske ne mai matsakaicin girma,irin toilet din daya amsa sunan Toilet din yan gayu,komae na cikinsa fari ne tun daga kan,bathtub,toiletseat,washbasin,shower curtains,bathroom cabinet,soap dispenser,hatta tiles d'in dake a k'asa da kuma bangon toilet din fari ne kal sai yan abubuwa k'alilan ne Silver kaman su Mixer tap,detachable shelves,abun saka tissue wato Toilet roll holder,da Towel rack wanda ke dauke da fararen towels k'arami da babba rataye a saman shi,sai salk'i kewayen yake yi yana daukan ido,tamkar ba'a amfani dashi,tsaye t.k yayi yana tunanin to mima zai ma toilet din? d'igo-digon ruwan da Haisam yayi wanka ne kawae a k'asa shima ba wani mai yawa ba don akwae bath mat a gaban bathtub din wadda ke absorbing ruwa in an fito daga cikin kwamin, itama fara ce sol,ka'ida ya fito daga kwamin wankan sai ya fara taka ta kafin ya taka tiles d'in kasan don bayan tsane ruwa tana preventing zamewa. Detachable shelves t.k ya nufa wadda ke like a sama d'auke da toilet cleaning items,ya ciro safar roba yasa kafin ya daukko liquid cleaner da scrub sponge komawa yayi gaban bathtub ya d'iddiga liquid cleaner din ya wanke,bayan ya gama ya maida robar cleaner din ya daukko disinfectant spray ya fesa a saman tiles din kasa yasa mop ya goge fess,ya ciro karamin towel dake sagale a jikin rack ya goge bathtub din da ya wanke,ya dawo ba ko digon ruwa jikinsa,ya juya ya bud'e seat shima dai fess yake ba wani dirty illa ruwan cikinsa da kalarsu take blue kaman ruwan swimming pool hakan kuma ya faru ne sakamakon cleaner tablet da t.k ya saka ciki lokacin daya gyara part din da safe,hakan na nufin ba'ai amfani da seat din bama,flushing yayi har saida ruwan suka koma fari kal sannan ya rufe,ya yago wipe daga cikin wipe dispenser dake manne a gefen seat din ya goge jikin seat din dan damshin jikin wipe din yasa nan da nan seat din ya rinka wani irin sheki gwanin burgewa,ya jefa wipe din da safar hannunsa a cikin farin wastebin dake a bayan kofan toilet din,har zai fita sai kuma ya hango cabinet a bude,komawa yayi ya duba ciki ko akwae abunda ke bukatan gyara,su toothpaste brushes,sabulai,da turarurrukan wanka ne shake a cikinta,ganin komae a jere lpy lau yasa ya rufe ta ya juya ya fice hannunsa rike Mop da yai amfani ya maido ta cikin laundry ya aje. Washing machine ya nufa ya bude,ba wasu kaya aciki sai underwears din da Haisam ya cire dazun,juyawa yayi ya duba cikin cabinet din laundryn ko akwae wasu kayan daudan pajamas kala daya ne da Haisam ya cire da safe,ya daukko su ya saka cikin machine din,a ranshi yace "bari da safe in ya cire wasu sai in hada in wanke"ya rufe,dan karamin farin towel mai laushin gaske ya dauka ya koma bedroom din ya goge furniture din ciki wadanda dama suke ta kyalli,bayan ya gama ya fita parlour desk kawae ya goge sai ya dan tattara bakin kofan shigowa ya dau takalman daya aje na Haisam da floor wiper da dan towel din da yayi Amfani ya maida kowanne wurin da ake aje shi,ya dawo parlon hannunshi rike da Air freshner ya feshe parlon wanda dama yake ta sakin k'amshi mai sanyin dadi,maida freshner d'in yayi ya dawo cikin parlon sai da ya bud'e fridge ya dau lemo Fanta ya bud'e yana sha daga haka ya fice bayan ya jawo kopan ta rufe. T.k,yaron gidan Hajia ne,tun yana d'an karami,Almajiranci aka kawo sa daga wani kauye dake a k'aramar hukumar birnin magaji jahar Zamfara,ta sanadiyar wani dan garinsu Isiyaku wanda ada shine ke Aiki a gidan,to sukan je tare da t.k yana kama masa suna yin shara,da goge gogen motoci sai Aike in Hajia na bukatan wani abu,daga baya isiyaku ya sanarma Hajia cewa zai koma gida don zasu tafi da yayansa neman kudi lagos,Hajia ta bashi shawaran ya tsaya zata sa shi a makaranta yafi tafiya neman kudin nan,amman yaki tsayawa don ba son karatun yake ba,to a lokacin ne t.k ya ce ma Hajia shi ya rika zuwa yana yi mata Aikin? Hajia na Murmushi tace "d'an malam ai harabar gidan nan tayi maka girma baka iya share ta...da sauri t.k yace "da kwarankwatsa zan iya,a gonar babanmu kunya goma nake nomewa kuma wani lokacin har in kara" Hajia taita yin daria jin zancen shi tace "ya sunanka? Yace"Tukur Halliru,ta amince ya cigaba da yin Aikin amman tana shakkun in zai iya don lokacin baifi shekara 11 ba. Aikuwa t.k yaba hajia mamaki don sosae yake yin aikin ba wani kuskure,gashi akwae ladabi,daya ci ya koshi to fa ba zama Aiki kawae ko ba'ace yayi abu ba yaga ya dace yi yake,a lokacin hankalinsa da karfinsa sun girmi shekarunsa,nan da nan ya shiga ran Hajia tasa shi makaranta ya fara daga primary 4 don ya fad'a mata a garinsu ya fara karatun kafin aka kawo sa karatun Allo,sosae t.k yake fahimtar karatu don lokacin ya dawo gaba daya gidan Hajia da zama tasa shi a wata makarantar Allo dake nan cikin unguwa amman kafin ta aikata hakan sai da taje da kanta har makarantarsu ta sanar da Malaminsu niyyarta ta bukaci ya bata number din baban t.k,aka kuma ci sa'a baban nada waya lokacin ta kira babanshi sosae ta fahimtar dashi tace in yana son karin bayani game da ita ya tambayi Isiyaku,ta ba t.k wayan ya k'ara yimasa bayanin Isiyakun da take nufi,Sosae baban t.k yaji dadi don kafin ta kira sa malaminsu t.k din ya kirasa yayi masa bayanin abun Arzikin data kaima makarantarsu,na kayan abinci,omo da sabulai,da takalma silifas,harda kudi masu yawa tace a rarrabawa Almajirai. Cike da zumud'i malam halliru ke sanarma matansa guda ukku abun Arzikin daya samu t.k,mahaifiyar t.k wadda itace ta karshe cikin matan tayi tsananin farinciki yayin da sauran kuma bakin ciki ne ya turnike zuciyoyinsu,dama sun takura ma mahaifiyar t.k don suna ganin mijin yafi ji da ita,don uban gidansa ya bashi auran ta,kullum suyi tayi mata gori suna cemata yar sadaka,ladan noma,ita dae bata biye su don hakuri ne da ita. Malam halliru yaso barin t.k yayi karatun boko don wani malaminsu t.k d'in lokacin har gida yazo ya roki uban daya bar yaron yayi karatu mai zurfi don yana da kokari,amman sauran matan suka tada balae wai sam basu yarda ba yadda aka tura yaransu sukaje suka yi karatun Allo,to dole shima t.k din yaje,ba yadda bai ba ya fahimtar dasu hakan k'aruwarsu ce gaba daya,amman firr suka ki amincewa don bakin ciki,ba k'aramin tashin hankali ya fuskanta ba,ba yadda ya iya haka ya turasa,mahaifiyarsa Hasiya nata kuka,don ta so yayi karatun,dayake Allah hakimun ne sai gashi tafiyar tasa ta zame masu Alkhairi,rabo kuma ya rantse,Malam halliru ba k'aramin girgiza yayi ba lokacin daya kaima t.k ziyara,ganin cikin daular da d'an nashi yake,bada niyyar kwana yaje ba,amman hajia ta matsa ya kwana,da zai tafi ta hada masa sha tara ta Arziki harda Atamfofi ya kaima matansa. Zaune malam halliru yayi a tsakan gida yana basu labarin irin Arzikin da t.k yake ciki,ya sanar masu mahaifiyar sanata ce yake wurinta kuma matar tsohon ministan tsaro Gen.Adamu zakee,kaman yadda t.k ya fad'a masa,murna wurin Hasiya kam ba'a magana,sai ma da t.k din yazo da Sallah,har gida aka rinka zuwa ganin tukur dan gidan sanata,haka mutanen gari ke fada. Private school hajiya tasa shi yayi secondary,bayan ya gama kuma ya tafi Polytechnic dake nan katsina inda yanzu ya shiga ND2 yana karantar SLT,ba faman da Hajia bata yi dashi ba akan aikin da yake ba kaman wankinta da ya hana kaiwar da ake dry cleaning shike wanke mata su fess ya goge a cewarsa baiga abun wahala ba abunda da injin ake yin wankin,Manyan abubuwa irinsu barguna,labulaye da carpet kawae ake kaiwa wurin wanki. Lokacin da Haisam ya dawo hajiya tace ma tk ya samo wanda zai rink'a gyara masa part dinsa acikin abokansa yan makarantar allon su dake kawo masa ziyara akai akai,nan ma cewa yayi shi duk zaiyi ai ba wani aiki ne mai wahala ba,kuma dama yana bala'en son Haisam,ba k'aramin burgesa yake ba,shiyasa in yana gyara masa part din nasa cike da himma yake aikin,ba algus don dama shi tun yana k'arami aikinsa ba ha'inci,shiyasa in ya dage shi zaiyi abu sai hajia ta kyalesa don tasan zai iya din,kuma ba'a ganin ba daidai ba wani lokacin takan tsokane shi tace "na manta jikan nawa fa kakkarfa ne don tun yana karami kunya goma yake nomewa" sukan yi dariya atare, Shikam t.k duk yana yin hakanne don hud'ubar da mahaifiyarsa ke masa duk in yaje ganin gida,takan ce ba abunda zamu iya saka masu dashi,haka zakaga ana zuwa gaida t.k in yaje tamkar shine Senator din,iyaye har tura yaransu yanmata suke wae ko zai taya,basu san t.k ya wuce ajinsu ba sai yar birni,in ya tashi dawowa haka mahaifiyarsa zata bashi,su kuka,kubewa,daudawa,barkono da sauran su ya kawo ma hajiyar,mahaifinsa da har hatsi yake bashi ya kawo,Hajiar ta hana tace iya su kayan miyan ya isa ta gode. Wannan kenan game da Tukur Halliru Birnin magaji,wanda tuni yazama dan gida a gidan Hajiyar sanata don har Senator Ali Adamu zakee yasan da zamansa. A next page zamu fara nitsawa cikin labarin In shaa Allah,aci gaba da share pls. Thanks as u do so🤝🥰 *💖ASANADIN MAKWABTAKA💖* *BY OUMMU IMAM📱* *Paid Book* *Free Page9️⃣&🔟* Washe gari juma'a,daga cikin d'aki gwaggo ke magana"Wai fatuu bazaki fito ki tafi ba sai kin makara,kuma a buge ki kizo kina cewa malami kaza ya tsaneki ko" fitowa fatuu tayi sanye da uniform din makaranta hannun ta d'aya dauke da jaka School Bag dayan kuma takalma ne Sandals na roba,a k'arkashin hammatarta ta sak'a jakar ta duk'a tana kokarin sa sandals din saidai igiyan tak'i sawuwa sai faman kici kici take yi dashi a fili tace"Wannan shegen takalmin ni wallahi na gaji dashi" haushi taji ta buga shi da k'arfi a k'asa tace banzan takalmi yaki sanyuwa. Duk maganganun da take a kunnan gwaggo,fitowa tayi ta tsaya a bakin k'ofa hannunta d'aya dafe jikin bango tana kallon Fatun sai kiciniya take. "To taya zai sanyu kin kasa natsuwa kisa shi sosae,ji bi yadda kika wani takure kin cusa jaka a hammata,d'agowa tayi tace"to yaya zanyi" fuska a tur6une da alama takalmin ya k'ule ta, "Ki aje jakar mana a gefe,ki zauna sosai kisa" Aje jakar tayi ta dan zauna a bakin k'ofa kamar yadda gwaggon tace,aikuwa sai gashi takalmin ya sanyu ba wani 6ata lokaci,da sauri fatuu ta d'ago ta kalli gwaggo tana daria tace "Kinga d'an banza ya sanyu kuwa" gwaggo ta dan ta6e baki"Uhm ba wani d'an banza,dama ba ki yadda ya kamata ya sanyun bane,ace komi mutum zai yi bazai sa natsuwa ba, Mik'ewa fatuu tayi tana kokarin goya yar jakar goyon a bayanta tace"zan tafi" gwaggo tace"To adawo lpy,Allah ya tsare" wani irin kallo fatuu tayi mata tace adawo lafia kuma? Gwaggo tace"Eh mana ko baki son Addu'ar ne?, "A'a ina so mana amman ai banji bayani ba" tayi maganar tana yi ma gwaggo alamar kud'i da hannuwanta,gwaggo tace"wai don Allah ba ranar da zaki ce yau dai gwaggo kibar kudin ki ne? Da sauri fatuu tace "iyeee,to kuma dami zan hau mota kuma inyi break,in baki bani ba? Gwaggo tace "to acici baki da magana dama sai ta abinci,a duk satin duniya sai kin cinye mani naira d'ari biyar wani satin ma sai sun fi haka tunda sai ki dawo kice man baki samu bus ba kin ranci kudi kinyi ciko kin hau Napep ko mashin", Fatuu da ke tsaye ta k'agara gwaggo ta sallameta ko ta tafi tace"Don Allah gwaggo kiban,taya karatun zai yiwu da yunwa to ko mota dai ai sai an zuba mata mai take aiki ko" yar daria gwaggo tayi, fatun tace "yau baki zuwa aikin ne? "Zanje,amman sai da rana", Fatuu tace"kenan zan dawo in iske ki? Gwaggo tace "Anya kuwa kinsan yau juma'a,da wuri zan tafi,wurin k'arfe d'aya haka", "to ammn dai zaki yi mana abinci ko ba sai na dawo ba inyi"tayi maganar da sigar shagwa6a" gwaggo ta rike baki tace"Ah kajita ko da yaushe-da yaushe nike tafiya in bar mata wani yin abinci,ai sai dai in ina aikin safe ne kuma shima kusan tare muke dawowa,kamar wadda ta iya wani abincin arziki", Fatuu tace "ai dai ina yi kuma ki ci har kice yayi dad'i" daria gwaggo take tace"Mai karya.....fatu tace"d'an Aljanna,tana daria,"gwaggo kiban don Allah" mik'o mata naira d'ari tayi wadda ke cikin hannun da ta dafa bango dashi,da sauri fatuu ta amsa tace"daman kudin na a hannun ki,amman sai kinja man rai,juyawa tayi ta fara tafia,sannan tace "Kar ki damu kakus,zan biya ki duka kud'aden da kika kashe man in nazama Doctor" har lokacin gwaggo daria take ta girgiza kai tace"nadai fad'a maki ai natsattsu ne ke zama likitoci,in baki natsu ba,ba wata Doctorn da zaki zama" da d'an karfi tace"Insha Allahu zan zama harna rik'a yima ki Allura ma,na tafi" ta karasa fada yayin da ta kusa isa zaure. Gwaggo tace" To Allah ya tsare adawo lafia ban.......,Fatuu dake cikin zaure ta k'arasa abunda gwaggon zata fadi da karfi"BANDA RIGIMA DON ALLAH FATUU" daga haka ta fice daga gidan,girgiza kai gwaggo tayi tana ta daria tace" Shiryayya,a haka ko nace d'in wani lokacin kafin ta shigo gidan an kawo man k'ararta,Allah dai ya shirya"daga haka ta koma cikin d'aki. Tafiya fatuu take ta raba hanya biyu,sam ba natsuwa a tafiyar,hanyar shiru dayake safiya ce sai yara jefi jefi yan tafiya makaranta kamar dai ita,sai wani cilla k'afa take kamar zata tashi wai ita nan sauri take,Horn d'in da akai da k'arfi ne a bayanta yasa tayi saurin komawa gefe,sannan ta juyo tana kallon motar da ta taho,Peugeot ce 406,Maroon color,cikin ranta tace"dama mai motar nan ya rage man han....bata k'arasa ba sakamakon mutumin data ga ya wuce fuuu a cikin motar bai ko kalleta ba,da sauri fatuu ta zaro ido had'i da rike ha6arta tace"Kai! Wancan ai mutumin nan ne na jiya mai kama da Aljani,ba dai a layin nan yake ba? ta karasa maganar da sigar tunani harda d'an waigawa baya,tace"Uhm inma nan din yake,shi dai ya sani" taci gaba da tafiya har tazo wata kwana d'an nesa da gidansu,tana karya kwanar ta tsaya da alamun mamaki a fili tace"lallai ma wannan haulatun,har yanzu bata fito ba,tana nufin in bita har cikin gida kenan" kwafa tayi sannan taci gaba da tafia,ad'an gaba kadan daidai wani gida inda yaro ya fito dauke da d'an bokitin plastic ta tsaya tace ma yaron "Kai haulatu na nan ciki" yaron yace "Eh naganta tazo ta karbi koko a rumfar da Innarsu ke saidawa" ya wuce,ita kuma fatuu ta kad'a kai ta shige cikin gidan wanda gaba daya k'asan gidan kasa ce,sai daga can gaban dakuna ne akai ma k'asan shafen siminti shima duk ya farfashe,a gefe guda wata mata ce cikin wata yar baranda da yara tsaitsaye tana zuba masu koko,matsawa fatuu tayi bakin barandar tace "Innarsu Haulatu ina kwana" da washe baki ta amsa"lafia lau fatee yan makaranta,haulatun na ciki" kad'a kai fatu tayi ciki,tana hawa saman simintin wata yarinya ta lek'o tana daria,wankan tarwad'a ce tana da kyau ba laifi,hannunta d'aya rike da hijabin Uniform dinta dayan kuma kofi ne tana shan koko,tsayawa fatuu tayi tana harararta,fuska daure tace"Ashe ma baki shirya ba don wulakanci kika sa inata sauri" haulatun wadda keta faman daria tace"wallahi markad'e innarmu ta aikan kuma sai na iske layi,amman ai na shirya hijab kawai zansa da Sandals",da yar tsawa fatuu tace "Da Allah to kisa mu tafi,salon sai mun makara wannan banzan displine d'in ya bugi mutane, daman ya tsane ni" ta k'arasa tana murgud'a baki, Haulatu tace"bafa kyau zagin malami fat...." ta katseta"naji,wayace ya tsane ni"fatuu ta haulatu tace"bafa tsanarki yayi ba,kece kike ja ai yana dukan ki,ni kinga yana duka na?" ta kai maganar tana kurbar koko,"dalla ki fito mutafi ko inyi tafiya ta wallahi,daman ke ai baki ganin laifin kowa sai nawa"da alamar ranta ya 6aci, Haulat tace"Haba kawata daga fad'ar gaskia...." "to ki rik'e gaskiyar banso" inji fatuu,mik'o ma fatuu kofin kokon haulat tayi tace ida shanye wa",harararta Fatuu tayi da sauri tace "Wa!Ni zan sha wani koko,kokon ma sauran ki,Allah ya kiyaye,ta tofar da miyau gefe" girgiza kai haulat tayi da d'an murmushi ta idasa fitowa,aje kofin tayi a k'asa ta sanya hijab din da Sandals din dake aje bakin kofar d'akin,ta d'auki jakar ta,ta leda irin ta biki tace"Mu tafi" atare suka nufi hanyar fita,haulat ta shiga rumfar da innarta take,ta ajiye kofin data sha koko tace ma Innar "zan tafi" kud'i innar ta miko mata naira sittin tace"A dawo lpy" Allah yasa" haulat tace ta nufi hanyar k'ofar gida,don ita fatuu tuni ta fuce. A kan hanyarsu ta zuwa bakin titi inda zasu hau Bus fatuu sai faman masifa take ma haulat tana cewa ai in suka rasa Bus itace a matsala don tasan bata da isassun kud'in da zata hau Napep ko mashin,baiwar Allah haulatun ita dai tayi shiru tana sauraranta da alama tana da hakuri,gashi da gani ta girmi fatun ko a yanayin jiki tafi fatuu tsawo a sanyaye tace"Insha Allahu ma zamu samu,in kuma ba'a samun ba sai in dawo ba wani abu,in Allah ya kaimu Monday naje"daga haka ba wanda ya kara cewa wani abu. Suna isowa bakin hanyar kuwa sai ga Bus din da yar fara'a haulat tace "Alhamdulillah",juyowa fatuu tayi tai mata wani kallo fuska a d'aure. Haulatu kawar fatuu ce,tun lokacin da tazo garin,lokacin da gwaggo tasa ta a makaranta har gida taje ta had'a su suyi kawance,don tasan halin haulat yarinya ce mai hakuri da natsuwa,ita kadai ce zata iya jure halin fatun a yaran unguwar,gwaggo ta roki haulat da ta d'auki fatuu a matsayin kanwarta ta rik'a nuna mata abubuwa masu kyau,ta kuma rika hanata maras kyau,gwaggo bata 6oye ma haulat komai ba game da halin fatuu, a gabanta kuma tayi ma fatu fad'a sosai akan ta zauna lpy da haulat ta rik'a jin maganarta,intaji sun yi fad'a tasan itace ta ja,kuma sai ta sa6a mata,Innarsu haulat ta tabbatar ma gwaggo cewa haulat bata da matsala karta damu,dama kuma ana ganin mutuncin Gwaggo a unguwar,Ita kuwa haulat tunda taga fatu taji tayi mata,jininta ya had'u da ita,tace ma gwaggo zata kula da ita insha Allahu,A haka kawancen su ya k'ullu,duk da ance wai sai hali yazo d'aya ake abota,to nan dai halin sam bai zo daya ba,dama kuma sai ansamu bambanci abota ke lasting,misali,daya mai wayo daya mara wayo ko daya mara hakuri daya kuma mai hakuri kaman su kenan,Amman duk da hakurin Haulat wani lokacin sai fatu ta k'ule ta har tayi fushi,sai kuma ta dawo taita bata hakuri har sai taga ta hakura,dama ko gwaggonta haka take mata. K'arfe sha biyu da rabi na rana daidai aka tashe su kasantuwar ranar juma'a ce,Haulatu ce tsaye tana ta faman kwala ma Fatuu kira "fatuu ki taho mu tafi kar acika bus d'in kinsan yau Juma'a fa gaba daya ake tashi harda seniors" ita kuwa fatun tana can sai faman bin students take da gudu tana bugun su,wai na bankwana daga yau sai Monday,girgiza kai Haulat take tayi don ta gaji da tsayuwar,sai da ta gama buge bugen ta taho da d'an gudu sai faman nishi take tana daria, jakarta a hannu d'aya, Dafa kafad'ar Haulat tayi da dayan hannun tace muje k'awalliya,juyawa kawai haulat tayi bata ce mata komae ba suka tafi. Abunda haulat ke gudu shi ya faru don kuwa School Bus d'in ta cika dam sai dai su tsaya a tsaye ko su zauna a k'asa,Haulat ta kalli Fatu tace"Kinga abun da kika ja mana ko,da ana tashi muka taho ai da mun samu seat kika tsaya shiririta,yanzu ai sai mu zauna a k'asan" ta k'arasa maganar da dan 6acin rai,fatuu tace"tabb nikam bazan zauna a k'asa ba duk a tattake ni,ga k'asan ma duk k'asar sandals din mutane,"To ya zamuyi,nidai ban iya tsayuwa gaskia da anzo tudu ko wurin yin kwana mutum yayi ta bugewa" inji Haulat, "ki tsaya kika ga ni,sai na samu seat d'in zama" fatuu tayi maganar yayin da take kutsawa cikin Bus d'in,hango wata yar senior section tayi wadda unguwar su d'aya don tare suke hawa Bus a bakin titi,su biyu ne a zaune,a daidai wurin su ta tsaya tace "D'an matsa man in zauna, "Kamarya? Yarinyar ta tambaya,fatuu tace "Ai ku biyu ne kuma har mutum ukku ana zama ko" tayi maganar tana turo baki,"To in mu biyu ne mu tsaranki ne? Fatuu tace "Yo ina ruwan mota da wani tsara ai dai duk makaranta d'aya muke ko" da sauri yarinyar ta nunata da yatsa tace"Ke karki yi man rashin kunya yanzun nan in mari wannan kumatun naki,dama naji ance baki da kunya to ni in kika yiman zane ki zanyi wallahi" da alama itama yarinyar masifaffa ce, cikin harzuka fatuu tace "Ki zane wa,ai ni wallahi nafi k'arfin ki zane ni sai dai mu zane juna,don ba fina k'arfi kikai ba ehee" ta murgud'a mata baki,da sauri yarinyar ta yunk'uro zata mari Fatuu,ita kuma fatun tayi saurin kaucewa....Sauran Students din cikin motar ne suka had'a baki wurin cewa"Kwandasta ana fad'a" da sauri Haulat ta nufi inda fatuu take bata san mike faruwa ba,amman tana jin ance ana fad'a tasan da Fatuu ne,shima kwandastan ya nufo ciki yana fadin"suwa ke mana fad'an? "gasu nan" students suka ce, daidai inda suke ya tsaya yarinyar ta rik'e wuyan hijabin Fatuu itama fatun haka sunyi cirko cirko,cikin daka tsawa Kwandastan yace"ku saki juna!! Kowa ya saki kowa,yaci gaba"miya had'a ku" da sauri yarinyar tace"Wannan yar rainin wayon ce,wai sai mun matsa mata ta zauna,kuma na gaya mata ba wuri amman zata yima mutane rashin kunya sai kace wani ya hanata tazo da wuri..." ta k'arasa maganar tana ta huci ita kuwa Fatuu ta cika famm kaman zata fashe sai hararar yarinyar take,kwandastan ya juya wurin ta yace "Ah kece baki da gaskia,tunda an riga ki sai ki hakura ki zauna a k'asa ko ki tsaya ki rike karfe,In kuma baki iyawa sai ki hakura ki fita kawai,Amman kar wanda ya kara yimana fad'a,in ba haka ba zan kori mutun ne" ya juya ya nufi gaban motar yana jaddada masu abunda yace. Haulat ce ta kama hannun fatuu wadda ta cika fam,tana yima yarinyar wani irin kallo,"Zo mu zauna a k'asan kawai fatuu don Allah ki kyale ta kar a kore mu kin...."da karfi Fatuu ta fuzge hannunta,ita kuwa yarinyar sai faman cika take tana batsewa tana wani yamutsa fuska. Wata student ce yar junior section acan dayan 6angaren motar tace"Fatuu zo ki zauna ga wuri na matsa maki" k'wafa fatun tayi ta duk'a ta dauki jakarta wadda ta yarda lokacin da zata rike hijabin yarinyar da suke fada,ta nufi inda aka matsa mata ta zauna,ita kuwa haulat baiwar Allah wuri ta samu a k'asa ta zauna sam bata iya tsayuwar. Adaidai kan kwanar da aka saba aje yan unguwar Bus din ta tsaya students d'in unguwar suka fara fitowa harda su Fatuu,sannan yarinyar da sukai fad'an itama ta fito tana ta suratai da kawayenta yan senior guda biyu"Yan section d'insu ke tsoronta shiyasa take masu iskanci,ni in yarinya tace zata yi man wallahi maganinta zanyi yadda gobe ko ance taja wani fad'a bazata yi ba,hakanan azo garin mu ana cin arzikin mu kuma ace za'a rik'a yimana iya shegeee" wata cikin kawayen tace"Wai daman ba yar nan garin bace? "Eh yar jahar Adamawa ce,da gani ma acan d'in yar k'auye ce irin yan rugar nan,kinsan dan k'auye daya samu wuri sai iya shege iri iri" k'awayen suka tuntsire da daria,d'aya tace"kai Murja" wadda aka kira da murja tace "Allah kuwa,duk tabi ta Addabi mutane,duk da ba a layin gidansu nike ba,a layin bayansu muke inajin labarin iskancinta,shiyasa a cikin Bus din nan naso in saita mata hankali da kwandastan nan bai zo ba,tasan ni ban tsoronta" duk maganganun da suke a kunnan Fatuu don a bayansu suke kuma da karfi yarinyar ke maganar don Fatun taji, A farkon kwanar gidansu kawayen nata yake,Murja tace "bari in biyo ku inyi fitsari" suka shige tare,tsayawa fatuu tayi wadda kiris ya rage ta fashe don fushi tana kallon gidan da suka shiga,Haulat tayi saurin cewa"Don Allah,mu tafi Fatuu,karki biye mata" tana kokarin janta" k'in tafiya fatun tayi ta cije a wurin haulat taci gaba "In kika tsaya yin fad'a yanzun nan kinsan za'aje a fad'i ma gwaggo gara ki rabu da ita kawai" A hankali Fatun ta juya suka fara tafiya amman ba haka taso b..,can ta tuna ai gwaggon ma ta tafi aiki tunda ta tabbatar mata bazata dawo ta iske ta ba,da sauri Fatuu ta mika ma haulat jakarta tace"Ki tafi man da ita gidan ku,da safe sai kitaho man da ita Islamiyya", "Ina zaki kuma?" haulat ta tambaya fatun tace"Na manta ne gwaggo ta aike ni..." Haulat tace "to mutafi tare man....da sauri Fatu tace"A'a kije kawai ni kad'ai zanje" Haulat ta girgiza kai tace "ba wani aiken ki da akai fad'an dai zaki tsaya ko...?da tsiwa Fatuu tace "Eh d'in fadan zan tsaya ina ruwanki" haulat tace"Don Allah fatuu kiyi hakuri mana" "Inyi hakuri? Kinajin yadda take gaya man maganganun banza zaki wani ce inyi hakuri, to wallahi bazan yi ba" Haulat tace "haba fatuu,Allah fa yana tare da masu hakuri..." "To ni banda hakurinn ehe" Fatuu tace,hannu haulat tasa ta rufe baki, jin abunda Fatun tace. Ganin haka yasa fatuu ci gaba da magana"Ai ba haramun bane in anyi ma mutum abu yaji bai iya yafewa ya rama,ke komai akai sai kice ma mutum yayi wai hakuri shikenan so kike a raina ni,inzama sakarya kamar ki ko" cikin sanyin murya Haulat tace"Ni babu wanda ya raina ni,kinga wani na tsokanata ne? Kuma yin hakuri ba sakarci bane,wani lokacin rashin hakuri ba abunda yake ja ma mutum sai dana sani mara Amfani,gara ma kayi hakurin tunda Allah da kansa yace yana tare da masu hakuri,in kayi hakurin sai kiga ya saka maka ta inda bakai zato ba"daga haka ta mik'a ma Fatu hannu,ta bata jakar,ita kuma ta juya don tasan ba lalle ta iya hanata yin fad'an ba, cikin d'aga murya Fatuu tace "In ma k'ara ta zaki ki kai to gwaggon bata nan tana wajen Aiki" girgiza kai kawai Haulat tayi batare da tace mata komai ba bare ma ta juyo. Wani gida dake kallon jikin gidan da Murja ta shiga nan Fatuu ta shiga ta 6oye a bayan k'aure tana lek'o waje ta tsagar jikin kofar jira kawai take taga fitowarta,Aikuwa bata fi minti biyar ba sai ga murja ta fito tana yarfe hannunta da alama ruwa ne a hannun,da sauri fatuu ta cire hijabinta ta d'aure ta tamau a k'ugu ta k'ara gyara d'aurin kallabinta,sai da ta bari murjar ta wuce kofar gidan data 6uyan ta fito cikin sand'a tamkar mage na shirin kama k'adangare da gudu ta shak'o murja ta baya cikin sa'a ta kada ita k'asa ta fara bugu dama Fatuu badai karfi ba gashi takai mata hari ta baya sai faman bugunta take,tana fad'in "kafin kiyi magani na ni zanyi naki" cikin wahala murja tace "Don Allah kiyi hak.....bugu Fatuu takai mata a baki nan take bakin ya fashe tace "hak'urin uwarki zanyi,badai ni kike ce ma yar kauye ba, aikam zaki ga yar k'auye, Lokaci guda yara suka kewaye su suna kallon fada,yawanci duk d'alibai ne masu dawowa daga makaranta had'i da Almajirai ba wanda yayi yunk'urin raba su don yaran sun san halin Fatuu. Wata mota ce 406 maroon ta shigo cikin lungun,ba kowa bane cikinta face Haisam,a hankali motar ke shigowa har yazo gab da yaran,dole ya tsayar da motar ba tare da ya kashe ta ba,don ba hanyar da zai wuce yara duk sun rufe hanyar,shiru yayi yana tunanin lafia,don bai hangen su fatuu dake fad'an,Horn ya latsa amman sam hankalin yaran na akan fad'an basu ma ji ba bare su bashi hanya,Wani magidanci ne ke k'okarin fito da wani tsohon mashin daga zauren wani gida acan gaban inda ake fad'an,adaidai lokacin da ya fito waje yace"Bismillahi,mun fito da sunan ka ya Allah,ka matso mana da rabon mu na alkhairi kusa Albarkacin wannan rana,bud'e tankin mashin d'in yayi ya d'an girgiza yace "tabb ashe ma ba man,Allah gamu gareka yan canjin da suka rage man su kenan na bada cikin gidan a samu a harhad'a,yanzu kuma anfito za'a neman gashi ba isashshen mai ma a mashin d'in ,kai rayuwar nan tayi tsanani Allah ka dafa mana",daga haka ya maida murfin tankin yana rufewa, A daidai nan kuma Haisam ya k'ara yin Horn mai karar gaske nan da nan yaran suka shiga darewa ya rage sauran su fatuu dake ta faman tumurmusa a k'asa,da sauri mutumin nan ya juyo jin Horn d'in,sai a lokacin ya lura da meke faruwa a hanyar da sauri ya jingine mashin d'in ya nufi wurin masu fad'an da dan gudu gudu don ya samawa mai motan hanya,k'okarin rabasu ya shiga yi saidai sam fatuu tak'i ta rabu da yarinyar,duk abunda ke faruwa kan idon Haisam,yana kallon yadda mutumin keta kokarin 6am6are fatuu daga jikin d'ayar yarinyar amman ya kasa,saboda ta kafe,tak'i ta saki yarinyar,nan take ran Haisam ya 6aci,bud'e motar yayi,da karfi ya maida kofar ya rufe har lokacin motar na akunne,ya tunkari inda suke fad'an,yau ba suit ne a jikinsa ba,riga ce longsleeve shirt maroon color sai wando jeans bak'i ma6allan rigar ma bak'ake ne,takalmansa kuwa daga saman su maroon din fata ce,shimfid'ar takalmin zuwa kasan shi kuma baki ne,sumar sa tasha gyara sai salk'i take ba k'aramin kyau yayi ba, yauma dai da alama Too match din yayi da motarsa wadda take maroon. Yana isa wurin yasa hannu guda ya fizgo Fatuu ya turata gefe guda sai gata a k'asa wanwar,sauran yara suka sa dariya ganin yadda ta wani wuntsila,juyawa yayi ya kalleta,da dogon dan yatsansa ya nunata yace"You Again..!" da ganin yadda yayi maganar ya ganeta ne,da sauri Fatun ta mik'e tana mashi wani irin kallo ta turo baki cike da tsiwa tace "To ina ruwank....bata k'arasa ba ya wanka mata mari ji kake tasss,da tsananin firgici Fatuu ta dafe inda ya mare tan sai faman zare ido take........, *💖ASANADIN MAKWABTAKA💖* *BY OUMMU IMAM📲* *Paid Book* *Free Page1️⃣1️⃣* Su kam yara mi zasuyi in ba daria ba suna fad'in yau anyi maganin masifaffa,hakan ba karamin fusata fatuu yayi ba,Tsawa Haisam ya daka masu yace"kowa ya bar nan!" nan da nan kuwa suka kama gabansu banda Fatuu wadda har lokacin tana dafe da kuncinta sai faman hura hanci take tana mashi wani irin kallo mai kama da harara, cikin yar tsawa yace mata"C'mon leave this place kafin in k'ara maki wani" ya nuna mata hanya da yatsansa,daga jin yadda yake magana zaka fahimci ba mai hayaniya bane,A hankali ta fara tafiya tana yi tana waiwayensa har Lokacin kuma bata cire hannunta daga kan kumatun da aka maran ba,da alama taji zafin marin. Juyowa Haisam yayi cike da takaici bayan Fatuu tasha kwana,kallon murja yayi wadda jini ke ta zuba daga hancinta da bakinta tasa hannu ta dafe hancin,jinin har ya 6ata mata brown hijab din ta,ya ma kasa cewa komae sai mutumin nan ne keta faman girgiza kai yace "kai jama'a yanzu ina Amfanin haka,kuna ya'ya mata kunzo tsakiyan hanya kuna fad'a ji yadda aka raunata ki,ina amfanin haka,cikin sheshshekar kuka murja tace "Wallahi ba abunda nayi mata,ni bama bangare d'aya muke ba a makaranta kawai don tace in....bata k'arasa bayanin ba Haisam ya katseta ta hanyar yima mutumin magana don a tunaninsa komai yarinyar zata fad'a game da Fatun gaskia ne, "Don Allah ko za'a samu chemist nan kusa?" ya tambaya fuskarsa sam ba walwala,da sauri mutumin yace"Eh akwae,sai dai yana ad'an can gaba in an fita bakin titi" duba agogon hannunsa yayi kafin ya kalli yarinyar "Muje" yace mata fuska ad'aure, juyawa tayi zata nufi inda motarshi take,da sauri mutumin yace "Yalla6ai in sauri kake ka kawo sai in kaita" d'an dakatawa Haisam yayi yana duban girman mutumin,d'an murmushi mutumin yayi don ya fahimci kallon da yake masa yace "kar kaji komai yalla6ai zan kaita,tunda ga mashin d'ina can ajiye,dama hanyar zan bi,kaga ba sai kasha wahalan komawa ba", Sigh yayi"Ok,nawa ne kake ganin zai isa a duba ta? ya tambaya, Mutumin yace "ai ina ganin dressing ne zasu yi mata,k'ilan su had'a mata da maganin kashe rad'ad'i duka dai nasan bai wuce naira d'ari biyar haka,da Alama mutumin yana da kyan hali duk da halin rashin da yake ciki bai fad'i fin abunda yake tunanin za'a kashe ba,hannu Haisam yasa cikin aljihun jeans dinsa ya ciro wallet maroon mai kyau,kudi ya k'irgo dubu biyu yau ma sabbi fil dasu,ya mika ma mutumin gently yace"Ayi abunda ya dace" da sauri mutumin yasa hannu ya kar6a yana fad'in"to,to.." yana shirin juyawa Haisam ya sake mik'a masa wasu dubu biyun,da d'an zare ido mutumin yake kallon kud'in yace"Yalla6ai su kuma mi za'ai dasu? Cikin girmamawa yake maganar duk da kuwa ya girme masa nesa ba kusa ba,amman girman ya koma kan Haisam tunda shi mai kud'i ne,Allah kai mana Arziki mai Amfani,Amin, "kasa fuel" haisam yace daga haka kuma ya juya,godiya mutumin ya shiga yi yana fad'in"Allah yasa kagama da duniya lafia,Allah ya jikan magabata,Allah yasa kafi haka,ya Albarkaci iyali...." ko a ina iyalin suke. Hannu kawae haisam ya d'aga masa bayan ya nufi inda motarsa take,acikin zuciyarsa kuwa yanata amsa Addu'oin da mutumin yake masa, bud'e motar yayi ya shiga dama a kunne take a hankali ya fara tafiya mutumin nata d'aga masa hannu,horn yayi mashi lokacin da zai wuce shi, juyawa mutumin yayi ya nufi wurin mashin d'in don ya saukko dashi bisa hanya don yana da tabbacin zai kaisu bakin hanyar,sai faman washe baki yake yana godema Allah yanzu yanzu ya gama rok'on Allah da ya matso masa da rabon sa na Alkhairi kusa sai gashi ya samesa a kofar gida Allah kenan,ita kuwa Murja mutumin taso ya kaita don Yan kwanakin nan suna yawan ganinsa ita da kawayenta da safe in zai tafi Aiki,su kuma zasu makaranta,suyi ta santin kyawunshi har Addu'a suke Allah yasa watarana ya rage masu hanya,yau dai ga dama ta samu sai kuma rashin rabo ya gifta. Juya kan motar yayi lokacin da yazo karshen lungun ya hau mik'akkiyar hanyar da zata kaisa har gida,Wata irin k'ara ce ta ziyarci kunnuwansa,A hankali ya d'aga idanuwansa ya kalli Rear view mirror din motar don daga bayansa yaji k'arar,lokaci guda yanayin fuskarsa ya canza zuwa tsananin mamakin abunda idanuwansa ke gani a bayan motar,nan take kuma ya tsaida motar ya bud'e kofar ya fito cikin tsananin mamaki,bayan motar ya nufa ya tsaya yana kallon Glass din bayan wanda yai tartsatsa duk ya tsatstsage wani wurin ma ya 6ule alamun wani abu aka jefo ma glass din,juyawa yayi ya kalli d'an can gefe dashi gaban wani gida,Fatuu ce atsaye ta rik'e kugu ta turo baki tana huci har lokacin hijabinta na d'aure a k'ugunta, kallonta yake ba ko kyaftawa ya had'e girar sama data k'asa,ganin irin kallon da yake mata ne yasata juyawa ta ruga da gudu cikin lungun dake opposite da wanda Haisam din ya fito. Wani bak'in matashin saurayi ne da tunda ya taho daga d'an nesa yaga lokacin da fatun ta jefi bayan motar da dutsi ya karaso wurin,sam ba natsuwa tattare dashi gashin kansa duk yayi cibir cibir yana sanye da kod'addun kaya t-shirt da wando 3-qurter wanda duk ya farfashe,ya d'an sa6ulo ana hangen boxer din ciki la66ansa sun yi baki sosae alamun dai yana shaye shaye,tafa hannuwa ya shiga yi yana salati ganin yadda glass din yayi"La'ilaha illallahu,Muhammadu d'an Abdullahi,tayi tsiyar da ta saba,wannan yarinya anyi yar Akuya wallahi" yayi maganar yana wani ciccije baki irin yadda yan shaye shaye keyi,shidai Haisam still yayi yana ta kallon ikon Allah,matashin ya cigaba"Wallahi Oga haka take bata jin magana ko kad'an eeh duk tabi ta hayyaci mutane tamkar Aljana haka take,toh wallahi Oga ko ni duk iskanci na bazan yi kwatankwacin wannan aika-aikar ba don nasan mizai je ya dawo eehh" ganin yadda Haisam d'in ke masa wani kallo yasa yace "koda yake Oga ba wani iskanci ma nike ba fa,kawai ina nufin yar k'iriniyar mu ta samari" yana maganar yana wani janta, "Amma Oga sam bai kamata ka kyale yarinyar nan ba,inba haka ba zata ci gaba da wannan Akuyancin ne ya kamata kadau k'wakkawaran mataki" nodding kai Haisam yayi alamar to,kawae ya juya don ya gaji da saurararshi, cigaba da magana matashin yayi yana bin bayan Haisam d'in lokacin har ya kama k'ofar motar zai bud'e "Oga in maka kwatancen gidansu ne?" juyowa haisam yayi hannunshi d'aya rike da kofar ya bisa da ido sai da yadau yan seconds yace"Ina jinka" da sauri matashin ya fara magana harda gyara tsayuwa za'ai zuga"Yauwa Oga idan ka mik'e wannan hanyar da zaka bi,ka shiga ciki ina kasan gidan Hajiyar Sanata? Kai Haisam ya d'aga masa alamar "Ehh" ya cigaba"Yauwa to kafin ka kai gidanta ai kasan akwai wata yar kwana da ta raba gidanta da sauran gidajen 6arin tunda ita gidanta kaga tangameme ne yad'an shigo ciki kuma katangar gidanta akwai tsawo....,kowa ya tambaye shi wannan bayanin oho,ya cigaba "to ai gidansu ita waccan Aljanar yarinyar na nan daga shi sai wani sai ita kwanar akwae ma d'an kiyos a gaban gidan,In ma baka gane ba Oga da ka tambayi gidan DIJE ATTENDER,za'a nuna ma da yake awurin kakarta take kuma ita kakar aiki take a asibiti irin masu.....bai k'arasa ba Haisam ya dakatar dashi ta hanyar d'aga masa hannu yace "na gane" yana k'okarin juyawa matashin yace "ko nazo na raka ka ne Oga?" "No Thanks" Haisam yace lokacin kuma ya shige cikin motar,da sauri matashin ya rufe masa kofar yana fad'in "Allah ya tsare Maigida,Sauka lapia maigida" yana d'aga masa hannu kai da gani kud'i yake son ya bashi,shi kam Haisam jan motar yayi yai gaba abunsa don ya fahimci d'an shaye shaye ne, Rik'e kugu saurayin yayi a fili yace"Hakanan a banza na wahalar da kaina ma ashe wurin yi masa kwatance,ko yar asi bazai ban ba,mtsww.." yaja tsaki,kafin ya cigaba"ni har nasa ran zan samu na kayan harka,wasu mutanen dai sun cika mak'o wllh" daga haka ya juya saida ya harbi k'asa irin yaji haushin nan kana yai gaba yana ta wuwwurga k'afa shiga niga,Allah ya shirya. Ko ta kan kwatancan da akai masa bai bi ba,straight gida ya nufa yana karya kwana Officer ya tashi don bud'e masa gate Haisam ya dakatar dashi ta hanyar yi masa horn,juyowa yayi ya nufo wurin motar a hankali ya d'an sauke glass d'in yace ma Officer d'in "I will park it here" daga haka ya maida glass din ya rufe sai daya dan d'auki mintuna kafin ya bud'e kofan ya fito hannunsa d'auke da laptop da charger dinta,Officer yace "You're Welcome Sir" "thanks" Haisam yace kafin ya shige ta k'aramar kofa direct part d'insa ya nufa. Yana shiga palor ya cire takalmansa a gefe saman desk ya nufa ya aje laptop da charger din,ya wuce saman kujera L-shape ya zauna ya jinginar da bayansa had'i da d'age kansa yana facing sama da gani abunda ya faru yake tunani,don makamancin hakan had never happened to him,hasali shi yara ma tsoron sa suke ba abunda ke hadashi da su,shiyasa da yaga fatuu zata yi masa rashin kunya ya mare ta don tun a jiya ya fahimci bata da kunya,shi da har manya ma shakkarsa suke sai gashi yau Fatuu ta aikata masa wannan d'anyen aiki. *💖ASANADIN MAKWABTAKA💖* BY OUMMU IMAM *Free Page 12 &13 D'agowa yayi after some minutes yasa hannu gefensa ya d'auki wayarsa wadda ya aje lokacin da zai zauna Contacts ya shiga yayi searching wani suna Iro Mechanic yai dialing kira,bugu biyu aka d'aga speaker ya kunna ya aje wayar a hannun kujeran ya koma ya jingina daga d'ayan bangaren aka fara magana"Assalamu Alaikum" kafin Haisam ya amsa aka cigaba da magana "Allah ya taimaki babban Engineer" amsawa Haisam yayi da fad'in"Malam Iro ya aiki" on the other hand aka amsa "lafia lau wallahi ranka ya dad'e,barka da juma'a" haisam ya amsa"Barka dai,mota ce zaka zo ka d'auka tana nan na parker ta a waje", Iro yace"toh yalla6ai badai matsala ta samu ba ko? d'an murmushin gefe yayi yace "Malam Iro ku da an nemeku ai kasan matsala ce ko" Iron yace"Hakane yalla6ai,to Allah yasa ba babban matsala bace," hannu haisam yasa ya dan shafi fuskan shi kafin yace"Eh,Widescreen din baya ne yayi damage,so it needs to be changed" Salati Iro ya saka yace"yalla6ai garin yaya,wacce ciki ta samu matsalan? Haisam daya fara k'osawa da maganar amsar k'arshen kawai ya bashi "406,in ka lissafa komae let me know" yana niyyar latse kiran da sauri Iro yace "to yalla6ai sai a sanar ma da Jami'an nan zanzo d'auka tunda kace tana a waje duk da sun san mutum sai....." Haisam ya katse shi da fadin"zan fad'a masu" daga haka ya katse wayan. Mik'ewa yayi walking slowly ya nufi gaban desk ya dauki telephone yai dialing numbers sannan ya kara a kunne daga can bangaren daya kira aka d'auka"Security" shine abunda aka ce,shi kuma yace"Somebody will come and take the car I parked out there" daga can bangaren akace "His name sir?" "Iro Mechanic" Haisam ya fad'a daga haka kuma ya kife kan Telephone d'in ya nufi bedroom d'insa,da alama bautar jikin zashi yi inji dai hajia. Bai dade sosai ba ya fito, sanye da wani lallausan farin Voile ana hangen farar vest d'in ciki sai dai ba sosae ba anyi mashi dinkin Senator style,irin style d'innan wanda rigar ke tsayawa a rabin cinya sai dogon hannu wanda ake matse k'asanshi da link yasa links d'in silver da ratsin bak'i,kafafunsa na sanye da takalma plain half cover bak'ak'e masu kyaun gaske kai da gani kasan zasu yi tsada ga wata Hadaddiyar agogo silver,sai hula da ya sa itama bak'a sai dai bata rufe duka kan ba ana ganin gashin kansa daga gefe gefe haka ma na k'eyarsa ya turo,tana da d'an karamin kulu a tsakiyar ta,irin hular nan ce da ake cema Igbo cap amman da ganin jikin wannan mai tsada ce. Part d'in hajia ya nufa tana zaune saman kujera one seater jikinta sanye da jalbab fara sol ga glasses mak'ale a idanuwanta ta d'an duk'a tana karatun Qur'ani wanda ke a saman table,da sallama ya shiga a kujerar kusa da ita ya zauna yad'an kwantar da kanshi yana sauraren k'ira'ar ta a cikin suratul kahf,bai jima da shiga ba ta kammala,d'aga hannuwa tayi tana Addu'a lokaci guda suka shafa ita da Haisam wanda ya d'ago yana kallon ta da murmushi a fuskarsa bud'e baki tayi zatayi magana... ya rigata da cewa "Na karanta a Office" gaba d'aya sukai daria tace "wato har kasan abunda zan tambaya kenan" yace "yeah" d'an ta6e baki tayi tace "ai kwadayin falalar nike maka shiyasa nike tambayar ko ka karantan" "I knew" yace, hajiya taci gaba"To ya wurin aikin,Amman kad'an jima baka dawo ba don har nayi tunanin ko acan zakai sallan juma'ar" shiru yayi ya koma ya d'an jingina yana tuna abunda Fatuu tayi mashi,hajiya ta lura da yadda yanayinsa ya canja da sauri tace"lafia dai ko?? d'agowa yayi ya kalleta yace "Yes,kawai motan ce ta samu matsala", "Wace irin matsala kuma" Hajia ta tambaya da yar damuwa a fuskarta,shiru Haisam yayi baima san mizai ce mata ba,don shi kunya ma yake ji yace wai wata yarinya ta jefar masa mota har ta fasa glass,kuma yasan in har ya fad'i mata abunda ya faru tabbas bazata bari ba sai taje gidan su yarinyar ko ta aika a taho mata da iyayen yarinyar ma don Hajia tana da kirki amman akwae fad'a ba kamar kuma kan abunda ya shafi d'an lelenta Haisam tabbas bazata bari ba,duk da bawai don a biya ba,so bai ma son abun yazama wani big issue,don shi a tunaninsa yarinyar is Abnormal don abubuwan nata sun wuce hankali "Kayi shiru" hajia ta katse shi,d'agowa yayi da d'an murmushi yace"bafa wata babban matsala bace kawai it was faulty lokacin da zan dawo,amman nasamu na k'araso tana waje and I called Iro zai zo ya tafi da ita" sauke numfashi mai karfi hajia tayi don tayi tunanin ko had'ari yayi duk da ta ganshi lafia lau,tace"K'arfen nasara ba tabbas,duka yaushe Iron yazo yayi masu service da ka dawo" d'an ta6e baki Haisam yayi yace "ko kuma ba'a so na ara ba" wani irin kallo hajia tayi masa tace "Eh din,ai kaima kana da taka bama daya ba,karka k'ara daukar man tawa" gaba d'aya sukai daria a daidai lokacin kuma aka fara hud'ubar hausa bayan angama ta larabci a Masallacin gidan,da sauri Hajia ta mik'e tana fad'in kai yau dai mun taushe hannu wallahi,na dawo a gajiye bacci yai awon gaba dani....."ba kince yau ba zaki Aiki ba?" Haisam ya tambaya,"Eh wani abu ne ya taso dole naje, amman ba wani dad'ewa nayi ba don ko tafiya ban bar T.k yayi ba 11:30 muka dawo" ta k'arasa maganar lokacin har yayi gaba ita kuma ta fara kwala ma saude kira"Saude,Saude" fitowa Sauden tayi tana amsawa jikin ta sanye da dogowar hijab brown,hajia tace"Yauwa to mutafi" Saude ta juya tana gaida Haisam wanda ke k'okarin fucewa ya amsa ba tare daya juyo ba suma suka rufa masa baya. Jin an tada sallar juma'a yasa Fatuu lek'owa daga inda ta 6uya,wani gini ne wanda ba'a ida ba,cikin sauri take tafiya tana yi tana waiwayen bayanta kaman zata tashi sama har Lokacin hijabinta na d'aure a k'ugu ga kanta da yayi wani tum da gani kan a tsefe yake duk tayi bud'u bud'u saboda tumurmusar da suka yi a k'asa ita da murja,ta cikin lungun dake tsakanin gidan hajia da nasu ta 6ullo,tsayawa tayi bakin lungun tana lek'en kofar gidansu wanda yake wayam ba kowa shagon kawu Amadu ma a rufe yake don shima yaje makaranta kuma bai dawo ba dama gashi yau juma'a daga can kasuwa yake wucewa ko lokacin da su Fatuu ke yin fad'a sai da wasu yara suka zo kawo sheda suka tarar gidan a rufe. Ganin ba kowa yasata fitowa daga cikin lungun da sauri ta shige gidan farko wanda daga shi sai nasu har tana yin tuntu6e wurin shiga,a cikin zauren gidan taci karo da wani yaro ya fito da sauri da sallaya a hannunsa,tace "kai Umar je ka amso man makulli" yaron yace "kije ki kar6a man nifa sauri nike masallaci zani kuma har an fara...." tsawa ta daka mashi tace" dalla je ka amso man ba yanzu aka fara sallar ba ta d'aure fuska tana harararsa" juyawa yaron yayi rai 6ace yaje ya amso mata makullin don yasan mi zai biyo baya in bai amso ba, Da sauri ta bud'e gidansu ta shige ta maida kofar ta rufe had'i da sa sakata. Ita kuwa Murja bayan Mutumin ya kaita Chemist,aka duba ta ba wani rauni mai yawa bane ha6o ne tayi a hanci saboda bugun hancin da Fatuu tayi sai le6enta na k'asa daya fashe aka yi mata dressing sannan aka bata magani pain reliever,duka ko d'ari biyar dinma ba'a kashe ba,bayan sun fito daga Chemist din Mutumin ya bata naira dubu yace gashi itama ta rik'e,sannan yayi mata nasiha sosai kan rashin dacewar suna ya'ya mata su rink'a yin fad'a haka, ya kuma roketa da tayi hakuri kar tace zata d'auki fansa,kuma ko taje gida kar ta fad'i don ita fitina a kwance take Allah kuma ya La'anci mai tado ta,Murja ta tabbatar mashi da tayi hakuri bazata k'ara yin fad'a da ita ba,Ya k'ara mata naira d'ari yace ta hau mashin ya k'arasa da ita shi kuma ya tura nashi ya tafi yasha mai,bayan ya tafi ta kama hanya k'asa bata hau mashin d'in ba tana ta farin ciki ta samu Naira dubu harda d'ari daya a fili tace"Ko ba komae na rage zafi,wannan mahaukaciyar yarinyar wama zai k'ara fad'a da ita". Bayan angama Sallah Hajiya suka fito daga 6angaren da mata ke yin sallah nan da nan mutane suka kewayeta ana ta kwasar gaisuwa,har d'an rankwafawa wasu keyi in zasu gaidatan,Saude na tsaye a gefe,Haisam ne ya k'araso wurin, ganin yadda hajiyan keta gaisawa da mutane yaji bazai iya jiranta ba ya wuce,Part d'inta ya koma ya kishingid'a saman 3-seater bayan ya cire hular kansa dama duk ta damesa don in yasa dinki irin wannan bai cika sa hula ba,yau ma don yana friday inma baisa ba,hajiya zata matsa masa ne dole sai ya sa, Sai bayan wani dan lokaci su Hajiyan suka shigo,tana shigowa Parlon ta fara kokarin cire jalbabar jikinta tana fad'in "Alhamdulillah,Allah ka nuna mana wata juma'ar cikin k'oshin lpy" Saude ta ce "Amin" ta mik'a ma Saude jalbabar, jikinta na sanye da doguwar riga cotton mai gajeren hannu gaban rigan anmashi wata irin sak'a mai kyau har zuwa k'asa kanta daure da kallabin rigar,ta idasa shigewa cikin parlorn ta zauna kujerar dake kallon wadda Haisam yake kwance yasa pillow a bayansa ya d'an d'ago yana kallon T.V tace "Shine ka k'i jira na mu dawo tare kaman yadda muka tafi a tare" tayi maganar tana cire glass din fuskarta ta aje a saman hannun kujera,d'an murmushi yayi ba tare da ya juyo ba yace"Ina zan iya tsayawa ki gama da wannan mutanen da sukai circling d'inki sai kace kece Senator din" ya karasa maganar da sigar tsokana,daria sosae hajia tayi tace ai ni nafi Senatorn tunda ni na haife sa..." Saude ce ta k'araso ta cire hijab d'in jikinta sanye da riga da zani na atampa tsaf tsaf da ita ta d'an dafa kujera tace"Hajia na gama jera Abincin" hajiya tace "to sannu" daga haka Sauden ta juya,Hajia ta kalli Haisam tace "Oya Food is ready,tashi muje" sai lokacin ya kalleta yace "kije zanzo" harararsa tayi tace "Zaka tashi ko kuwa" hannu ya mik'o mata,tace"mi kenan? Yace "ki dauke ni tunda dole sai tare zamu" kama hannun tayi tana k'okarin kado shi k'asa da iya karfinta,ganin haka yasa haisam janyo hannun da karfi sai gata ta fad'o saman shi gaba d'aya suka sa daria a tare suka mik'e yana fad'in "tsohuwa ba k'arfi". Dining area d'in suka nufa a tare suka zauna bayan kowannansu ya wanke hannunsa a Handbasin d'in da ke gefe,Saude dake tsaye bakin k'ofan kitchen tana dariyar yadda Haisam yaja hajiyar dama kuma sun saba,ta k'araso don yin serving d'insu,wasu Luxury warmers ne guda ukku kai da gani kasan zasu yi kudi ba sai an fad'a ba,Milk color ne,yayin da handle d'insu da kasan su da saman marfin inda za'a juya a bud'e akayi masu wani irin design mai kyau golden,K'atuwar ta fara bud'ewa wadda cikinta ke d'auke da tuwan shinkafa da kuma sakwara kowanne a gefe guda sunyi fari tas an nad'e su da faran leda gwanin burgewa, Plate ta janyo zata fara zuba ma hajia ta dakatar da ita da fad'in "Zuba mashi" "to" Saude ta amsa,wani plate din ta ciro ta warware tuwo guda ta d'aura,ta d'aukko sakwara zata bud'e Haisam yace"Wannan ya isa..." Hajia dake kallonshi tace "Pounded yam ce fa,kuma nasan kana sonta" Shiru yad'an yi yana tunanin anya zai iya cinye su,gashi yana d'an son abinci swallow,ganin haka yasa hajia cewa saka mashi "To" Saude tace,ta saka masa sakwarar sannan ta bud'e warmer ta biyu wadda ke d'auke da had'addiyar miyar Egusi wadda taji ganda da kifi tarwad'a tayi kauri kitif ta d'aukko plate mai gida biyu ta zuba miyar a gidan farko sannan ta bude warmer ta ukku wadda ke dauke da Liver pate wato miyar hanta wadda itace ta sakwarar duk da za'a iya ci da ta agushin ma,ta zuba mashi a dayan 6arin plate din ta turo plate d'in gaban shi tace "gashi" Alamu yayi mata da taba shi cokali da hanzari ta ciro cokalin had'i da fork don in zai d'auko nama ta saka masa a plate d'in tuwon,ta janyo wani Glass jug mai kyau cikinsa d'auke da Kunun Aya fari k'al mai kauri tana k'okarin zuba masa a glass cup ya dakatar da ita da fad'in "Let me finish" hajia tace ni zubo man,tayi maganar bakinta cike da Abinci don tuni tayi serving kanta bata jira Sauden ba,"to,saude tace ta cika mata cup da kunun ayar ta tura a gabanta,juyawa saude tayi ta nufi freezer wani d'an babban Acryclic bowl ta fiddo mai marfi d'auke da fruit salad ta aje masu ta koma ta daukko bottled water shima ta kawo masu tace"Aci lpy" hajia ce ta amsa da"Allah yasa" har Saude ta juya zata tafi hajia ta tsaida ta da fad'in "Kin dai zuba naki ko,nasan ki da duminiya" murmushi Saude tayi tace "na zuba hajia, "to kin zuba nasu Officer?" Saude tace"Eh yanzu zan kai masu" d'aga kai hajia tayi sai kuma ta cigaba"Wai ni ina T.k ne ko a masallaci fa ban ganshi ba,ban kuma ga yazo ya d'auki Abinci ba...kafin Saude tace wani abu T.k d'in ya shigo da sallama sanye da dogayen kayan yadi ya nufi dining d'in ya tsaya daga gefe yana gaida hajia,tace "Ina ka shige ne wai tunda muka dawo ban k'ara saka a ido na ba ko a masallaci ma ban ganka ba" T.k yace "nad'an lek'a makaranta ne acan nayi sallah", "Au dama zaka makarantar baka gaya mun ba muka fita?" d'an murmushi T.k yayi yace "Ai dama duka lectures biyu gare ni yau,kuma Lecturer d'in safen yace bazai samu zuwa ba,ta biyun ce naje" cikin girmamawa yake maganar,hajia tace "Amman duk da haka dai ka makara gaskia,sai fa 11:30 muka dawo,kuma har kayi wanka sannan ka tafi, wace lecture kasamu,ka je dai yawo kawai" ta tura ganda a bakinta, T.k yace "dama dai attendance nike son inje insamu kuma na samu nayi" tace"duk da haka daga yau in kasan zaka makaranta na bukaci mu fita ka gaya man sai insa Officer ya kaini,amman banso kana wasa da karatu sam" T.k yace "In sha Allah" sannan ya maida kallon shi kan Haisam wanda duk maganganun da suke ko kallon su baiyi ba,yace "Yaya Haisam barka da juma'a" hannu haisam d'in ya d'aga masa saboda akwae abinci a bakinsa daga haka ya wuce kitchen don amsar Abincinsa. Ajiyar zuciya Haisam yayi wanda ya kusa cinye abincin saura tuwo d'an kadan a cikin plate din,ya yago tissue acikin kwalinta dake saman table din yana k'okarin goge bakinsa, d'an tura kujerar yayi baya yad'an kwantar da kansa Hajia ta d'ago tana kallonsa tace "Sai kace wanda yake wani uban aiki,to wannan guntun da ka rage fa? ai dai ba wani ya matsa maka cin biyun ba kai ka ga zaka iya don haka sai ka idasa cinyewa" d'an ta6e baki yayi yace "dama nasan sai kin tanka..."da sauri hajia tace "eh d'in,inma bayaga abun ka wannan guntun ai shine Albarkar" d'agowa yayi ya kalleta da d'an murmushi yace "kika sani ko yau ma wani zan samu ya idasa man shi...."da sauri Hajia ta d'aukko wuk'ar yanka bread daga cikin cutlery set din dake saman table din tace "Bismillah" daria sosae haisam yake yi yace "Wannan abun fa da kika rik'e? tace "na kare kai ne" gaba d'aya suka sa daria,Hajia tace "don Allah idasa mana",dan lumshe ido yayi yace "Owk tunda kince Allah,amman fa na koshi in cikina ya fashe you will see the consequences" yayi maganar yana jaddada mata da spoon d'in da ya d'auka,tace "Eh naji" ta jawo Jug din kunun ayar ta cika mashi cup ta tura gaban shi. Mik'ewa yayi bayan ya idasa cinyewa ya d'au cup d'in kunun ayar ya nufi cikin parlon hajia na fadin "Fruit salad d'in fa? Hannun da ba komai ya d'ago mata ba tare da ya juyo ba yace "bansan ina zan sa shi ba" ya idasa shiga cikin parlon ya kishingid'a saman kujera 2 seater yana d'an kurbar kunun ayar yana kallon T.V,bayan wani dan lokaci itama hajia ta mik'e bayan ta zuba fruit salad din acikin d'an bowl tasa cokali ta nufo cikin parlon tana kwala ma Saude kira,da hanzari sauden ta fito tace "gani hajia" hajia ta juya tace mata"Je ki clearing dining din mungama" "to" Saude tace ta nufi Dining area din ta kwashe duk abubuwan da sukayi amfani ta kai Kitchen banda Warmers d'in Abincin don gidan hajia bai rabuwa da bak'i manyan mutane,ba kamar yau da yake Friday ta tabbatar wasu zasu zo a buk'aci ta basu Abincin,tasa towel ta goge wurin yayi fess kaman ba'a zauna anci Abinci ba. *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* *Mallakin* ⬇️ *ZAINAB LALUH*🌹 *(Oummu imam)* *Littafin A Sanadin Makwabtaka 300 ne,ga mai bukatar ci gaba da karanta shi bayan angama Free Pages sai ya tuntube ni ta wadannan numbers din 09016265659 ko 09013804524,pls just whatsapp banda phone call,Thanks🤝* *Free page1️⃣4️⃣&1️⃣5️⃣* Saman kujerar dake opposite da wadda Haisam ke kishingid'e hajia ta zauna tana shan fruit salad d'in da ta d'ebo tana yi tana kallon American film din da Haisam d'in ke kallo, "Dad called me when I was in office" Haisam yace ba tare da ya kalli Hajiyar ba,d'an ta6e baki tayi tace"Ai nima dai ya kira ni tunda safe,yayi man barka da juma'a" yar daria Haisam yayi yace "Jealous Old Woman" itama dariyar tayi tace "ai don kasan yafi ji dani" gyad'a kai yayi yace "I knew,shiyasa ma koda ya kira ni maganar ki yayi man" da sauri Hajiya tace "Maganata kuma? Kai ya d'aga alamar Ehh,tace "to wace magana ce da ni bai man ba da ya kirani sai kai zai yi mawa,ko dai gulmata ku ka yi?" ta dakata da shan fruit salad d'in tana kallon shi alamar shi take jira ya bata amsa, sai lokacin ya juyo da kanshi yana facing d'inta yace "gulma kuma,No kema kinsan baza muyi hakan ba" ya d'an dakata,sai kuma yaci gaba "Ya tambayi yaushe zan kai mashi ke ne" wani irin kallo tayi mashi tace "Ka kaini kuma,da can da nike zuwa lokacin baka k'asar kai ke kaini? Yar daria yayi yace "to ai yaga kin dade baki je bane shi kuma yana son ganin ki" d'an ta6e baki tayi tace "to tunda yana son ganina sai yazo ya ganni,haka itama waccan ta lagos d'in last week ta kira ni tana ce man wai don Allah inje ta na son ta ganni na...." Haisam ya katse ta "Aikine yayi masu yawa they're always busy" hajia tace "To ni ban aikin ne?" murmushi yayi yace "Kina yi amman ai ba kaman su ba,ke You are less busy kuma Aikin naki is voluntary ke kika sa kanki...."katse shi tayi da cewa "Ai dai duk aiki aiki ne" tayi maganar a harzuk'e daria yake yace"ni daman ai baki ji nace aikin ki ba aiki bane Celebrity" da d'an murmushi tace "Ni ce celebrityn? Yace " Yeah,anata son ganinki kina wulakanci" yayi maganar cikin wasa,dariya Hajiya tayi tace "Miye abun wulak'anci don nace duk mai son ganina yazo inda nike" dan ta6e baki yayi yace "I think suna son kije kid'an kwana biyu ne" tace "Ai ina zuwan ko,kawai ni haye-hayen jirgin ne ba so nike ba wllh" ta k'arasa maganar fuskarta dauke da damuwa,ta aje bowl din saman sofa table kusa da cup din kunun ayar da Haisam ya sha ya rage kad'an,Sannan ta maida Kallonta kan hoton Sojan mutumin nan ko kyaftawa ba tayi. Ganin yadda ta k'ura ma hoton ido yasa Haisam d'an juyar da kanshi shima ya kalli hoton,girgiza kai ya d'an yi ya juyo da duban sa kan Hajiyar yace "Ba lalle silar ajalin ya zama d'aya ba Sweethrt" "I know" hajiya tace,ta kauda kanta gefe har lokacin da damuwa a fuskarta, "In bakya son hawan jirgin ne ki fad'a ma Dad sai asamo k'wararran Driver da zai rink'a kai ki", Uhmm tace batare da ta waigo ba,ya cigaba"Ita kuma lagos d'in in zakije sai ki rink'a hawa luxurious Bus...." da sauri ta juyo tace"Waye zaije lagos a Bus?" Yace "Ke mana tunda bakya son hawa jirgin ko" yayi maganar yana dariya,itama Hajia dariyar tayi tace "tabb inje lagos a mota,aikam in na isa saidai k'ilan a kwashe ni a Wheelbarrow" gaba d'aya suka sa dariya "Saboda me? ba bakya son hawa jirgin ba" tace "Eah amman hakan ba yana nufin zan daina hawa jirgin ba in koma hawa wata Bus can" gyad'a kai yayi ya maida duban shi kan TV, "Yanzu yaushe zance mashi zaki je? ya tambaya ba tare da ya kalleta ba,da sauri tace "Ina wai? yace "ABJ" ajiyar zuciya tayi tace "zanje amman fa ba yanzu ba,dana samu isasshen lokaci Lagos zani don har ta turo man da kudin jirgi,duk da ma wannan kud'in sunfi karfin kudin zuwa lagos ta dai turo man ne kawai", "Har nawa ta turo maki kud'in flight? Ya tambaya,tace "1 million" nodding kai yayi yace"kice bribe aka baki kawai,shiyasa zaki ce lagos zaki,to ki maida mata kud'inta ni zan baki 3m ki tafi Abujan..."da sauri hajiya tace "ban mayarwa,wato ka maida ni ma uwar son kud'i kenan" tayi maganar tana ta dariya,shima dariar yake yace "Aikam zanyi reporting d'inki ICPC,ince ga wata Mom din Senator kuma matar Former Minister of Defence ta kar6i cin hanci..." Hajia tace"Yi sauri kar k'uda ya riga ka"gaba daya suka kwashe da dariya. Hajiya ta ci gaba da magana "ni ina zan iya da jarabar Momynku ta lagos,yanzu abun ince mata bazan samu zuwa wurinta ba,kuma taji na tafi Abuja kaji masifa" Haisam yace "Ai ke ta biyo" da d'an zare ido tace"Masifar?" yace"Eah mana" ta6e baki tayi "tunda fa ka raina ni ai komai kace man" murmushi yayi yaci gaba da kallon American film din da ake, "Wai ni ya FANAN take kwana biyu bamuyi magana ba nasan dai hakanan bata k'in kirana sai dai ko yanayin karatun ne ya hana,ni kuma ban kira naji ya take ba" d'an lumshe idanu Haisam yayi kafin yace "baki damu da ita bane" hajia tace "Aikuwa ni na damu da ita tunda na damu da kai,tunda duk abu d'aya ne ko" murmushi kawai yayi batare da ya waiwayo ba, "Ina son yarinyar saboda akwai hankali ga sauk'in kai sam bata d'auki duniya da zafi ba,ba kamar yar'uwarta ba" haisam yace"wa kenan? tace "FARHA mana,kai wannan yarinya sam halinta ba irin na yar'uwarta bane,ta cika girman kai,ta d'au kanta wata tsiya,ni ina ganin acan dangin Babanta Turawa tayo gadon halinta" dariya haisam yake yace"ko kuma danginku ko..."da sauri Hajia tace "Haram,wallahi mu bamu da wannan halin kaima sai dai in ka k'i gaskiya ko akaina ai kaga misali ba ruwana sauk'in kaine dani ba kuma yabon kai ba atoh,yarinyar nan fa ko kirana bata iya yi ina matsayin kakarta sai dai in muna waya da uwar in na tambayi yasu Farha,shine fa in tana kusa tace man gata hajiya,in kuma bata nan ne inta dawo sai ta kira ni tace Hajia ga Farha d'in ku gaisa", Ajiyar zuciya Haisam yayi sai lokacin ya juyo yana kallon hajiyar,ta ci gaba "ko gidan fa naje yarinyar nan bata iya zama muyi fira,bare kuma tazo d'akina don ta gaida ni, ko da safe wani lokacin in mun hadu a dining don yin Breakfast sai ni ce zance Hajia farha antashi lafiya,sannan za kaga ta wani yamutsa baki tace "Good morning granny" hajia tayi maganar tana kwaikwayon yadda Farhan ke yi da baki,shi dai Haisam sai daria yake yace "Ni kuma kinga in muka had'u lafia muke gaisawa though dai bama wani magana ma sosae,tace "Yo kaida ita ai duk kanwar ja ce,kawai dai kai sai mutum ya zauna da kai zai fahimci saukin kanka amman kaima wani lokacin ai ba son magana kake ba,amman Farhaaa huu badai girman kai ba wllh" ta6e baki ya yi yaci gaba da kallon shi. "Ai wallahi Allah ya yabawa aya zakinta,da bai sa Farha ce ke da kyau da sura irin ta Fanan ba,Wai! da bansan a ya zata rik'a duban mutane ba a hakan ma ya aka cika,ita kuwa Fanan dayake Allah yasan kyakkyawar zuciya ce da ita sai ya had'a mata harda kyaun sura" juyowa yayi yana duban hajia yace "Kina nufin Farha bata da kyau? da sauri tace "ina taga wani kyau da wani hancinta kamar ansammata,idanuwan ma ba wasu masu girma ba,sai uban kumatu,sak uwarta ta biyo hasken ne kawai na uban sai d'an gashin kuma" haisam yace"You see,if to say wani ya fad'a maki baki da kyau da kinji haushi,amman yanzu da bakin ki kin fad'a". Hararar shi tayi "Ni d'in ce banda kyau?" yace "yeah,kince Farha bata da kyau...." da sauri ta katse shi "to ni uwarta ce,ko baka ji nace da mamarta take kama ba? "To miye marabar ki da Mommyn Lagos d'in?" Jimm hajia tayi tana tunani,dariya Haisam yayi yace" I know you won't deny cewa kuna kama dama,don sak fuskan Mommyn Lagos taki ce,she's your duplicate" ya k'arasa maganar yana ta daria ganin yadda Hajiya ta kasa magana,can tace "naji to,amman duk da haka nafi ta kyau" tayi maganar tana daria itama,girgiza kai Haisam yayi "yanzu kina nufin kinfi Farha kyau kenan? tace "Eah hasken fata ne kawai tafi ni sai d'an gashi kuma" nodding kai yayi "Lalle,nan gaba ma har Fanan d'in cewa zaki kinfi ta kyau da alama..." da sauri Hajia tace "nan fa d'aya ai ko giyar wake nasha bana ce nafi Fanan kyau ba yarinyar da har uban nata tafi shi kyau,inaga itama acan cikin danginshi turawa ta samo kyaun nata,kaga kenan ita Farha ta d'aukko hali maras kyau,Fanan kuma sai ta d'aukko kyawun sura" gaba daya suka kwashe da dariya,cikin fahimta suke firar tasu da gani kasan akwai kauna mai tsanani a tsakaninsu. Telephone ne ya fara ringing alamar ana kira,Haisam ya yunk'ura don ya d'auka hajia ta tsaida shi "Yi kwanciyarka bari na d'auka dama na gaji da zaman" ta nufi inda telephone d'in yake ta kara a kunne tace "Hello,Salamu Alaikum" daga d'ayan bangaren akace "W/salam Hajia you have visitors" tace"Okey,hold on" ta rik'e kan telephone din ta fara waige-waige alamar tana neman wani abu,haisam ya d'an kalleta"lafia? Ya tambaya,tace "Eah nayi bak'i ne ina son inga su waye,na rasa ina na aje ma wayan tawa" yace "I don't think tana parlon nan don tunda na shigo banga wayan ba" tace "Oh! namanta tana bedroom kuwa da zan kwanta na aje ta,bari Saude ta d'aukko ma....." Haisam ya katse ta "Let me change it to CCTV" ya k'arasa maganar yana k'okarin canza kallon da ya ke zuwa cctv,nan da nan sai ga vedios din 6angarorin gidan sun bayyana a kan TV d'in,kan vedion farko mai dauke da rubutun CAM01 daga k'asan rubutun ansa Gate ya shiga vedion wajen gate din gidan ya bayyana,wata mota ce a gaban gate d'in mutanen da suka zo kuma suna cikin motar hakan yasa hajia fad'in"to ni bamma gane su waye ba,sai mota kawai nike gani ko sai nasa glass...."Officer da yake jiran umarnin hajia jin abunda take fad'a ta cikin telephone d'in yasa shi lek'o da kanshi ta d'an karamin windon d'akin da suke zama irin na masu gadi wanda window d'in ta fito waje yayi ma wanda ke a mazaunin driver magana,mutumin ya leko da kanshi,hajiya ta k'ura ma mutumin ido tana k'okarin gano ko waye....can ta buga salati tace ma Officer dake jiran umarninta "Officer let them in" yace "Ok", Kallon Haisam tayi tace "Kawunku ne fa" ba tare da ya kalleta ba yace"Wane Uncle? tace"kawun ku Mani,na daura" "Ok" yace ya fara k'okarin mik'ewa hajia tace "Ina zaka kuma? Yace "Zan baku space ne", "to amman ai yakamata ka tsaya ku gaisa ko" komawa yai ya zauna ya ciro wayarshi daga cikin aljihun rigarsa yafara daddanawa. Wasu Dattawa ne su ukku suka shigo na farkon daya fara shigowa yafi sauran jiki da tsawo,bak'i ne yana sanye da manyan kaya farar shadda had'i da babban riga da hula,sai na bayansa shima shadda ce jikinsa saidai ta d'an ji jiki kuma kalar babban rigar daban ta yan cikin ma daban,sai na ukkun wanda shi yadi ne jikinsa riga da wando da hula kuma duk bai kai girman sauran ba. Hajiya na ganin mutumin na farko ya shigo ta mik'e fuskarta d'auke da fara'a da alama shine Kawu Manin,shima yana ganinta ya washe baki yana fadin"Hajjaju makkatun wa madinatun,Hajiyar Minister,Hajiyar Senator " cikin dariya Hajia tace "duk ni kadai" yace"Eh mana ai duk sunanki ne" ya karasa maganar yana k'okarin zama a kujerar dake kusa da ta ta,ta kalli wad'anda suka zo tare tace "Bismillah,ku zauna" suka amsa da "to" suka zauna,sannan suka fara gaidata cikin girmamawa,da fara'a ta amsa masu,ta maida duban ta kan Kawu Mani tana fad'in "kuyi hak'uri fa an barku waje kuna ta faman jira,su ba ruwansu ko da mutum yana zuwa indai ba akai akai ba sai suce sai sun tambayi izini zasu barshi ya shigo", Da sauri Kawu Mani yace "Ah ba komai wllh,ai hakan is part of their work,ba kamar yanzu da ake fama da matsalar Insecurity hakan shine daidai,don shi mugu zai iya zuwa da kowacce suffa ya cutar da mutum" Sauran suka jinjina kai sukace "gaskiya ne" Kawu Mani yaci gaba "Allah dai ya k'ara tsaremu da tsarewarsa,don Al'amarin sai dai Addu'a kawai itace zatai mana magani" Gaba d'aya suka amsa da "Amin" harda Hajia, Haisam ne ya d'ago da kansa ya kalli kawu Mani yace "ina yini Uncle" sannan ya juya ya gaida sauran cikin muryarsa mai cike da natsuwa,a tare harda kawun suka amsa mashi da "Lafiya lau", "Haisam ne d'an gidan Hajiya" kawun ya tambaya da fara'a "Eah" haisam yace a tak'aice, kawu yaci gaba da magana "Masha Allah,Haisam ya karatun? Kafin ya bashi amsa Hajiya tace"Ai ya gama,yanzu haka yaci gaba da aiki a nan garin yana nan AIRPORT" da mamaki yace "Wai yanzu har ya gama karatun? Kinsan kafin ya tafi nazo nan muka had'u lokacin kike ceman zai tafi yin Master's Degree a U.S" tace"Aikuwa dai gashi har angama" jinjina kai kawu yayi yace"Time really flies,Allah yasa mudace" hajia tace "Aikam lokaci fa na gudu,Amin ya Allah",sauran ma suka amsa da"Amin", Kallon Haisam yayi yace "Haisam yanzu sai Aure ko,nasan yanzu ai ka kai 30yrs ko?"yayi maganar yana yar daria,d'an guntun murmushi haisam yayi kafin yace wani abu wayarsa ta fara ringing ya mik'e yace masu"Excuse me.." daga haka ya fice, Hajiya dake ta fara'a tace "bai ida shekara talatin ba yanzu ya shiga 29yrs yanayin jikin ne sai ka ce yama wuce 30,dama kuma ga daga karfe yana yi,Auren kuma tukunna dai sai nan gaba in zai koma" Kawu yace "karatun zai k'ara komawa ne? tace"Eh zai koma U.S d'in amman ba karatu zashi yi ba duk dama yace zai kara karatun in ya koman,akwai wani babban Company ne daya danganci karatun da yayi na Computer Engineering suna k'era kwamfutoci da sauran abubuwan su na fasaha dai,shine suke son yin aiki dashi,duk da yanzu haka matsayin Agent d'insu yake anan k'asar,to kasan Uban nashi akwai kishin k'asa,da k'in yarda yayi,sai da Haisam d'in yayi mashi bayanin dalilin daya sa yake son yaje can yayi aiki dasu sannan fa ya aminci amman yace sai ya k'ara yima k'asar shi koda na shekara biyu ne,don gani yake suna iya rik'e shi...." a d'an harzuk'e Kawu Mani yace"Very thougthful of him,wallahi Senator yayi man daidai,don ma bansan dalilin daya sa Haisam d'in ke son zuwa ba,da nace dama gaba d'aya ya hana shi,haba! for how long zamuyi tayin shuka su suna girbe amfaninta,sam wallahi mutanen nan basu son cigaban mu,shiyasa da sunga mutumin mu mai hazak'a sai su bukaci yayi aiki dasu,su kuma mutanen mu sam basu kishin k'asar su,what they're after is the money,su dai kud'i kawai,basu tunanin suma su gina tasu k'asar,koda bazamu iya kamo su ba,mu ha6aka tamu kasar ta yadda zamu daina relying kansu,d'an abunda bai kai ya kawo ba ace sai anfita waje" ya d'an tsaya ya sauke numfashi,sannan ya juya kan mutanen da ya zo dasu ya ci gaba"Wallahi Alhaji Sa'idu karka so kaga yadda mutanen nan ke cin moriyar mutanenmu sai ma kaje asibitocin su zaka sha mamaki yawanci sai kaga manyan likitocin da suke masu aiki duk mutanenmu ne....." Hajiya ta katse shi da fad'in "tabbas,don akwai lokacin da muka kai marigayi Minister da yayi wani ciwo kasar Germany,wallahi likitan dake duba shi mutuminmu ne,kuma ma d'an nan Katsina don bayan mun dawo har zuwa yayi duba lafiyar tasa..."Kawu Mani yace "You see...shine maganan da nike,suna can wasu na amfanuwa dasu sun bar mu nan munata fama da rashin k'wararrun likitoci". Ya juya kan hajia"Wallahi hajjaju mostly likitocinmu yanzu ain't qualified,yan kad'an ne suka san aikin su,wai sai kaje asibiti ko ka kai wani naka,abun haushi kana ma likita bayanin matsalarka sai kiga ya fiddo waya yana googling...wai sai ya tura ma google duk abunda aka bashi shi zai jibga maka kuji fa don Allah wanda ada sam ba haka likitocinmu suke ba k'wazo ne dasu" gaba d'aya suka jinjina kai cike da takaici, Wanda kawu ya kira da Alhaji sa'idu ya fara magana "A haka kuma wasun nasu sai d'an karan wulakanci,haka zakai ta jin Labaru maras dad'i da suka faru a dalilin wulakanci da kuma sakacin da bai kamata ace ma'aikacin lafiya ne yayi hakan ba,wanda na tabbatar in a k'asar wajen suke yin aikin kwatankwacin hakan basu isa suyi ba,ba tare da an d'au kwakkwaran hukunci akai ba" gaba d'aya suka jinjina kai hadi da fad'in "Sosai kuwa", Na karshen ne wanda bai kai su girman jiki ba,shima ya fara magana"Wato Alhaji Mani duk matsalolin nan sun fara ne tun daga tushen fara karatun,yadda yakamata ace ana koyawan ba haka ake koyawar ba ayanzu karatun duk ya ta6ar6are shiyasa masu halin sai su d'auke yaransu su tura su kasar waje karatu,su kuma da sun ga mutum nada basira sai su rik'e shi suna biyan shi kud'i masu yawa,wanda yasan baza'a iya biyansa kwatankwacin su ba a k'asar shi dama kuma ba itace a gaban shi ba,taci gaba ko karta ci gaba shi ba ruwanshi,su kuma maras halin da basu da wani zabi da ya wuce dole su tsaya nan suyi karatun a wahale gashi yawancin malaman sun maida karatun kasuwanci,da abunda d'alibi yakamata ya kashe kudi da wanda bai kamatan ba duka kashe kudin yake,gaba d'aya yanzu karatun d'an talaka ya zama wahala yan kadan ne ke iya jurewa su gama,shiyasa in suka fara aikin sai kaga kaman suna ramuwar gayya ne,ba malaman asibitin ba,ba malaman makarantar ba da dai sauransu,kowa bai tunanin duk abunda yayi ma wani zai iya juyewa kan nasa...., "To Al'amarin kasar tamu dai sai Addu'a kawai amman muna bukatar mu canza halayenmu inba haka ba,haka zamuyi ta zama jiya iyau abubuwa duk suna ta ta6ar6arewa,kowa damuwarsa taya zai samu kudi ba ruwanshi da kasar ta gyaru ko akasin hakan kuma dai ko mun k'i ko mun so k'asarmu ce ba yadda zamu yi,in ta gyaru mu zamu ji dadi akasin hakan ma mune a ciki" lokaci guda su duka sukayi ajiyar zuciya, Hajiya tace"Allah ya bamu ikon gyarawa gaba d'ayanmu harda shuwagabannin mu,yasa mana tausayin junanmu,Amin" suma suka amsa da "Amin", taci gaba da magana "Shi Haisam ma ba kudi ne zasu kaishi ba,sam ba sune damuwarsa ba wllh,dama yana da burin gina katafaren Company wanda ya danganci technology d'in anan k'asar,to shiyasa yake son yaje yayi aiki dasu don ya k'ara samun Experiences,don bama shine Company na farko da suka yi mashi tayin aiki ba,ko lokacin da yayi Degree d'insa na farko a can k'asar Singapore,akwai wani Company daga k'asar China da suka so yayi aiki dasu Uban nasa ya hana yace ya dawo nan gida yayi aiki,to lokacin ya fara a matsayin Engineer mai zaman kansa daga baya ya fara aiki ak'arkashin Ministry of Communication Technology, Kawu Mani yace "haba ni daman nasan badai kud'i ne zasu sa Haisam din son yin aikin ba,ashema babban dalili ne,aikuwa gara yaje kinga sai ayi abunda ake cema ban gishiri inbaka manda" ya d'an dakata kafin yaci gaba"Ai sanata akwai kishin k'asa,wallahi nike gaya maki hajiya da Allah zaisa ya zama shugaban k'asa da munji dadi" dariya hajiyar tayi, ya juya wurinsu Alhaji Sa'idu yace "Allah daba k'aramin adalin shugaban k'asa za'ai ba mai kishin cigaban kasarsa,ga dai misali nan kan Iyalinshi" suka jinjina kai had'i da fadin "gaskiya ne" ita kam hajiya dariya kawai take tace "tau da kamar wuya dai ya fito takarar shugaban k'asa,don takarar Senator d'in ma da yaya ya fito sai da mutane suka taso shi gaba da kyar ya aminci,haka da tenure d'insu ta kare ma so yayi yaki ci gaba,a cewarshi yafi son ya cigaba da aikin shi da kuma kasuwancinsa". Kawu yace "Ai shugaban k'asan ma sai a matsa masa ya fito in Allah yasa da rabo sai kiga ya zama,ni ba don komai bama wallahi sai don fatan samun sauk'in matsalolin nan da suka yima k'asarmu katutu..." ajiyar zuciya Hajia tayi tace "Allah dai ya za6a mana dukkan abunda yafi zama alkhairi" gaba d'aya suka amsa da "Amin ya Allah". "Oh munata tattauna matsalolin da in shekara zamu yi ba lalle mu gama ba,an barku ko ruwa ba'a kawo maku ba" hajiya tace tana kallon su Alhaji Sa'idu da murmushi,suma murmushin suka yi,ta kalli Kawu mani tace "ga Abinci can saman table,dama bamu dad'e da saukkowa ba nida Haisam,don da ana gama sallan juma'a ku ka zo ma a tare zamu ci" Kawu yace"Wallahi nan naso muyi sallar juma'an,to bamu gama abunda muka je yi ba da wuri,dole acan dai mukayi" hajiya tace"Wani wuri kuka je ne? Yace "Eh,Ministry of Agriculture muka je" tace "Allah sarki,ya noman ana tayi ko? Yace "Eh,Alhamdulillah muna ta k'okartawa" "To Allah ya k'ara taimakawa,wasu yankunan ma naga noman ya gagaresu saboda matsalar rashin tsaron nan,gona ta ma da ke hannun baban tukur bara ai noman bai samu ba,Allah ya kawo masu d'auki da mu gaba daya" suka amsa da "Amin" "Jama'a ku tashi kuci abinci don Allah" ta fad'a tana kallon su Alhaji sa'idu,Kawu Mani ne yace "ai inaga Hajiya kaman a sakko mana dashi nan zai fi" tace to,ta fara kiran Saude,daga cikin corridorn da bedrooms suke Saude ta fito tana yafa kallabinta,hajiya ta bata umarnin ta kawo masu Abinci cikin parlor,ta juya ta fara kawo masu,kafin ta gama jerawa Kawu Mani ya juya yana tambayar hajiya"hajjaju ya wajen mutanen Lagos,hajiya Maryam da k'waran mijinta kwana biyu bamu gaisa ba? Daria hajiya tayi tace "suna nan lafiya lau",a lokacin Saude ta gama serving abincin saman lallausan Carpet d'in parlon bayan ta gaishe su tace masu"Bismillah" suka amsa da "to" had'i da yi mata godia,ta juya ta koma ciki Hajiya ma tace masu zata d'an shiga ciki kafin su gama. *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* *Mallakin* ⬇️ *ZAINAB LALUH*🌹 *(Oummu imam)* *Littafin A Sanadin Makwabtaka 300 ne,ga mai bukatar ci gaba da karanta shi bayan angama Free Pages sai ya tuntube ni ta wadannan numbers din 09016265659 ko 09013804524,pls just whatsapp banda phone call,Thanks🤝* *Free page1️⃣6️⃣&1️⃣7️⃣* Haisam na fitowa daga part d'in Hajiya ya nufi Part d'insa yana amsa wayan da aka kira shi,a daidai stairs din balcony ya gama wayan,tura kofa yayi ya shiga cikin parlon ya zauna kan kujera hadi da daukar Remote yayi powering tv On,ya d'an kishingida yaci gaba da kallon American film d'in da yake kallo a MBCMAX, bayan wani d'an lokaci ya dau wayarsa ya duba time,sake d'aukan remote yayi yai Offing tv sannan ya mik'e ya nufi bedroom. Sanye cikin Sportswear ya fito,red t-shirt da wandonta black daga gefen hagu na rigan na dauke da tambarin ADIDAS wanda akayi da bakar sak'a haka wandon ma adai dai gefen da akayi rubutun rigan shima akayi da jar sak'a daga k'asa yad'an matse,ba k'aramin kyau yayi cikin shigan kayan ba,kuma da ganin laushin kayan tabbas zasu yi kudi,saida ya tsaya yasa takalma a corridor kafin ya iso cikin parlon ya dau wayansa ya fice zuwa masallaci wanda liman ke ta kwalla kiran sallah, Tare da su Uncle Mani ya fito bayan angama sallan la'asar d'in ya nufi cikin parking space don fiddo da Bike d'insa bayan yayi ma T.k da ya fito daga masallaci bayan sun fito umarnin ya daukko masa jakarsa kaman jiya, Uncle Mani ya nufi part d'in Hajia don yi mata sallama su kuma su Alhaji Sa'idu suka tsaya gefen motar da suka zo da ita suna jiran ya dawo gaba daya hankalinsu na kan Haisam daya fiddo bike d'in cikin harabar ya haye yana kokarin sa helmet,adai dai lokacin da t.k ya kusa k'arasowa da jakar, Hajiya da Kawu Mani suka fito suka nufo parking space din,Kawu Mani dake ta kallon Haisam tunda suka fito ya fara magana"Yanzu Hajjaju shima Haisam na hawa irin mashin d'in nan? Hajia ta ta6e baki tace " Unn" adaidai lokacin da suka k'araso wurin su Alhaji Sa'idu ya kunna mashin d'in gaba daya suka toshe kunnuwansu da hannayensu da sauri,haisam ya d'an juyo ya d'aga ma Uncle Mani hannu alamar yana masa sallama bai jira ya maido masa ba yaja mashin din da gudu ya tunkari gate d'in da tuni an wangale masa shi. Uncle Mani ya sauke ajiyar zuciya bayan Haisam ya fice yace"I don't know what's wrong with our Youths,abu mai had'ari shi suke mayarwa abun adon su,and what really baffle me with them shine duk irin mummunan had'arin da mashin d'innan ke haddasawa hakan bai serving dinsu misali su daina hawan...Alhaji Sa'idu ya kar6e"Sam basu bi dashi yadda yadace ne,haka zaka ga suna ta falla uban gudu kai kace zasu kiyama..."Mutumin na karshe ya katse shi da cewa"Ai wasu kam kiyaman suke tafiya wllh sam basu la'akari da irin titinan mu ba kaman na waje bane,su yi ta tuk'in ganganci,gashi naji ance mashin d'in tsada ne dashi sosae..."Hajiya dake tsaye hannuwanta goye a bayanta ta amsa "tsada kam! Miliyan biyar ya zuba kafin ya mallaki wannan nasan..."gaba daya suka zaro ido a tare suka maimaita kudin da hajiyan ta fad'a,ita kam kai ta jinjina masu Uncle Mani yace "to Allah ya kyauta,Allah ya k'ara tsarewa,gaba d'aya suka amsa da Amin" daga haka ya kalli hajia da d'an murmushi yace "to hajjaju mu zamu wuce sai wani lokaci kuma in Allah yasa rayuwarmu ta kai" hajia tayi murmushi tace"To Allah yasa rayuwar tamu ta kai" ta fiddo hannayenta dake goye a bayanta ta mik'a ma Alhaji Sa'idu kud'i dake cikin hannunta na dama da fara'a tace"gashi ayi ma iyali tsaraba nagode da ziyara,Allah yabar zumunci" hannu biyu yasa ya kar6a harda d'an russunawa suna ta godiya shida dayan,Uncle Mani yace"To ni hajjaju ba'a sallame ni ba" dariya tayi tace banda kai ai sune bak'i na, kai na gida ne" shima dariyar yake ya bud'e mota yace"ba wani abu nasan tawa sallamar babba ce tafi karfin hannu k'ilan,zan turo Account details" daga haka ya shige Abokan tafiyarma suka shiga suna ta kara godiar rafar 50k da hajia ta basu cike da farinciki hannu ta d'aga masu bayan sun fita daga cikin parking space din tace"Agaida Iyali",daga haka ta juya ta koma ciki. Tunda ta shige gida take kunshe a daki,bayan tayi sallar Azahar bacci yayi awon gaba da ita,ko Uniform d'in bata cire ba,bugun kofar da ake tayi ne ya farkar da ita a tsorace ta fito daga d'akin tana tafiya cikin sand'a har Lokacin kuma ana ta buga kofar da k'arfi,tsayawa tayi cikin zauren tana tunanin waye ke buga kofan haka? kodai mai Motar ne ya kawo k'ara,ji tayi gabanta yayi mugun fad'uwa nan take tsoro ya kama ta tace a ranta "to ya akai yasan gidanmu bayan lokacin da na jefi motan ba kowa wurin..." wani bugu aka yima k'ofar wanda daji mai buga kofan ya k'ule yasa ta tunkari kofar da sauri ta d'an leka idonta d'aya ta ramin makulli nan take ta gane waye da sauri takai hannu sama ta cire sakatan sannan ta d'an ja baya,aikam da karfi aka bugo kofan don da bata matsa ba daba k'aramin buguwa zatai ba,rai a6ace yake kallonta Kawu Amadu ne hannunshi daya rungume da kwali d'ayan kuma katuwar leda ce,Fatuu dake ta faman zare ido tace "sannu da zuwa Kawu Amadu...."da sauri ya katseta da fad'in "sannu da zuwan uwarwa,don iskanci daman kina cikin gidan kika barni inata bugun k'ofa tsawon lokaci,to waima uban me kike a cikin gidan daba zaki zo ki budan ba? d'an turo baki tayi tace "ba komai,bacci ne ya d'auke ni fa" a harzuk'e yace"to miye na kulle kofa don zaki yi bacci" da sauri tace "ina gudun kar a shigo ayi sata ne ina baccin...." "k'arya kike" yace yana k'are mata kallo kafin yaci gaba "fad'a kika jawo ko? Da sauri ta girgiza kai alamar a'a,kwafa yayi yace "ai na dawo gidan inma rigima ki ka jawo zan gani,kuma uban miye na zama da Uniform har yanxu a jiki da alama ma ko wanka baki yi ba,bare kiyi sallah" ya k'arasa maganar yana kokarin aje kayan hannunsa a bakin kofa,d'agowa yayi ya daka mata tsawa"wuce kije ki wanka kafin na buge ki a wurin" juyawa tayi ta nufi cikin gida tana d'an k'unk'uni har ta nufi d'aki taji yace"bakiji mi nace kiyi bane? Da sauri tace "naji.." yace"to wuce ki dau bokiti ki d'ibi ruwa" ta wuce ta xuba ruwan ta shige band'aki,shima yana shiga wankan yayi a d'an band'akin cikin d'akin nasa ya shirya ya kwashi kayan da ya siyo ya nufi shago don jera su. Sai can bayan Issha gwaggo ta dawo,fatuu dai na k'unk'ume a d'aki cike da zullumin kar akawo k'ararta, koda ta fito tayi ma gwaggon sannu da zuwa dakin ta koma ita kam gwaggo a gajiye take hakan yasa ko ta kan Fatuu bata bi ba balle har ta fahimci wani abu,sai can dare gwaggo tayi bacci sannan ta fito taci abinci tayi sallah ta koma ta kwanta tare da yankewa ranta cewa baza'a kawo k'arar tata ba tunda har aka kai wannan lokacin. Washe gari asabar da safe Fatuu ce da Haulat zaune cikin ajin su na islamiyya,Haulat ta kalli Fatuu da murmushi tace"sannu hajiyar fad'a" wata yar dariyar iskanci fatuu tayi tace "waya ce maki nayi fada" d'an ta6e baki Haulat tayi tace "har gida akazo aka fad'a mana irin fadan da kuka yi, wai har kin fasa ma Murja baki da hanci" murmura idanu Fatuu tayi tace"Yessss,gobe ma ta k'ara gaya man banzan maganganu harta kirani da yar kauye" girgiza kai haulat tayi tace"ni wllh don kince Gwaggo bata nan amman a lokacin da sai na kai k'arar ki tunda ke dai baki da hakuri" harararta Fatuu tayi tace "aida da ta dawo kinzo kin kawo k'arartawa sarkin masu hakurin duniya" haulat tace "tunda ya rigada ya wuce miye na inzo,Amman ai naji ance wani mutum ne yayi maganinki da ki ka k'i barin fadan ya wanka maki mari" ta kai maganar tana tik'ar daria,wata yar iskar dariya Fatuu ta sake yi tace"hehehe ashe yai maganina,muka dai yi maganin juna don shima yayi asara ehe" haulat ta dakata da dariyar da take tace "what do you mean da ku kai maganin juna?wace irin asara kuma? Fatuu ta gyad'a kai da turancin ta na yar sakandire tace "what u hear" Still haulat tayi tana ta kallonta can tace "don Allah Fatuu fad'a man abunda kika yi masa" fatun na shirin yin magana Malaminsu ya shigo hakan yasata yin shiru daga nan kuma basu sake samun daman yin magana ba don yana fita wani ma ya shigo a haka har aka tashi,akan hanyar su ta komawa gida Haulat tace "d'azun na tambaye ki mi kika yiwa Mutumin baki gaya man ba" banza fatuu tayi mata,haulat ta sake cewa "kinji,mi kika yi masa ne" ba tare data kalleta ba tace"ke dalla bafa komai,wasa nike,ba abunda nayi masa kawai don kar kiyi tunanin yayi nasara akaina ne" haulat tace "kawai dai bazaki fadan bane Amman ko nayi rantsuwa ba zanyi kaffara ba tunda kika ce yayi asara da akwai abunda kika yi masa...." cikin tsiwa tace "ehh d'in nayi, tunda ba ki yarda ba abunda nayi masa ba" shiru haulat tayi amman ba don ta yardan ba,can tace "to ki kar6i jakar ki ko,kince in taho maki da ita kuma kin barni inata kayanta" juyowa Fatuu tayi ta figi jakar ba ko nagode tayi gaba abunta sai wurga kafa take da alama dai ta saba da yin tafiya haka,girgiza kai haulat tayi tace daga abun arziki,tabi bayanta har suka zo bakin lungun da suke rabuwa,haulat ta d'an daga murya tace "sai munhade Anjima hajia Fatuu ikon Allah" Fatuu ta juyo tayi mata kallon up and down ta k'ara gaba,Haulat dai dariya tayi a fili tace"Allah ya shirye ki" daga haka ta nufi hanyar gidansu, adai dai kofar shiga gida fatuu ta waiga tana kallon hanyar da haulat ta bi a fili tace "don ina sakarya Allah ya rufa man asiri in tona ma kaina,don na tabbata na fad'i mata sai ta fad'a ma gwaggo ko kuma tayi ta ma mutane nasihar banza ita ga mai hakuri yen-yen-yen" ta d'age baki daga haka ta shige gida. Haulat ce keta faman sauri da yamma zata islamiyya don ta makara sakamakon aikenta siyen gero da Innarsu tayi,tana k'okarin shiga lungun da zai kaita har islamiyyar taji daga gefenta ana magana "Ke,ke yar liman wait" da sauri ta juya tana kallon mai maganan,ya nufota yana wata irin tafiya irin ta nigas,da mamaki haulat ke kallonsa tana tunanin ita miye had'inta da Gaye da zai tsaida ta,yana k'arasowa yace"Ke dalla tambayanki zanyi kike ta faman zare ido uwa mujiya" ita dai haulat shiru tayi tana jiran jin abunda zai ce,ya ci gaba "dama tambayanki zanyi k'awarnan taki an kamata tana can cikin cell ne ko har anyi gaba da ita? cikin rashin fahimtar zancen shi haulat tace "wace kawar tawa kuma? Wata yar iskar daria yayi yace "kina da wata k'awa ne bayan Aljanar yarinyar nan mara jin magana, kullum ba tare nike ganinku ba" nan take ta gane Fatuu yake nufi don duk in suna tare suka had'u dashi Aljana yake cema fatun,da sauri haulat tace "to mitayi da za'a kai ta cell kuma? tayi maganar cike da fargaba tana ta zare ido, rik'e ha6a gaye yayi yace "wai kina nufin baki san aika-aikar da aljanar nan ta aikata ba...? da sauri haulat ta girgiza masa kai alamar a'a, jinjina kai yayi yace"tabb,to wllh ruwa ta 6allo ma kanta don ina tabbatar maki sai taje gidan yari..." da sauri haulat ta dafe k'irji tana salati tace"don Allah Gaye ka gaya man abunda tayi,ni sam wllh bansani ba" sai da ya gyara tsayuwa ya karkace baki yace "to bari kiji wani mutum ne jiya hakanan Aljanar nan ta jefar masa glass d'in bayan mota,gaba daya ta dagargaza glass din don wannan glass din yayi konden..." cikin tsananin tashin hankali haulat tasa hannuwanta duka biyu ta rufe bakinta ya ci gaba "atoh kima fad'a mata ta shirya don comfat (confirm) in ba'a biya shi ba har yakai k'ara na rantse da Assamadu sai taje fursun,yo motar fa ba k'aramar mota bace,to tsaya ma kiji,mai motar dan gidan Hajiyar Sanata ne kinsan kuwa ba'a k'aramar harka a gidan nan......" daga haka ya kad'a kai yayi gaba abunshi, kasa motsawa haulat tayi na tsawon lokaci da k'yar ta juya taci gaba da tafiya a hankali gabanta sai fad'uwa yake tamkar itace akace zata gidan yarin,cikin zuciyarta kam mamaki kawai take na abunda fatun ta aikata,ashe asarar da take nufin mutumin yayi kenan,"tabb lallai Fatuu bata da hankali!" ta fad'a a fili tana jinjina kai. A daidai bakin ajinsu ta tsaya tana tunanin shiga don tasan ta makara gashi akwae malami cikin ajin,can dai tayi shahada ta kutsa kai tare da yin yar sallama,d'an kallonta malamin yayi yaci gaba da bayanin da yake hakan yasa haulat yin saurin shigewa ta nufi wurin zamansu sai dai ga mamakinta Fatuu bata a wurin,tunani ta fara yi a ranta bayan ta zauna"to Fatuu bata zo bane? Kodai anje an kamata...wani irin bugu gabanta yayi da sauri ta d'ago da kanta a lokacin kuma ta hango fatun acan dayan bangaren,tunda haulat ta shigo ta wuce Fatuu ta ganta a ranta tace "da nice na makara da ya buge ni,ni da kowa ya tsana"ta saci kallon malamin ta d'an hararesa kafin ta juya inda haulat take nan take suka had'a ido don tunda ta hango fatuu take ta kallonta cike da al'ajabin abunda gaye yace zai sameta,murgude fatuu tayi mata ta juya,haulat ta girgiza kai cike da tausayinta,ta kuma fahimci dalilin da yasa fatun ta canja wurin zama don ta saba hakan da d'an abu ya hada su wanda bai kai ya kawo ba sai ta canja wurin zama sai tagadama ta dawo ko haulat taje ta bata hakuri sannan ta dawo,haulat ce kad'ai ke iya jure halin fatuu don ta karanci halayenta tsab shiyasa ma bata biye ta. Haulat ce keta sauri ta isko Fatuu don da aka tashi ta tsaya copying rubutun da malam yayi bata nan daga littafin wata kawarta da suke zama tare,ita kuwa Fatuu ana tashi tayi gaba abunta don guje ma haulat din take karta k'ara tambayarta game da asaran da tace Mutumin daya raba su fad'a yayi don tasan halinta wani lokacin nacin tambaya ne da ita kuma karshe inta gano tana iya zuwa ta fadi ma gwaggo "Fatuu!fatuu ki tsaya" haulat dake biye da ita a baya tace,ganin bata da niyyar tsayawa yasa haulat yin dan gudu tasha gabanta,cak fatuu ta tsaya fuska ad'aure tace "miye haka zaki wani shage gaba na" kasa magana haulat tayi don k'arfin halin fatun mugun mamaki yake bata ta aikata irin wannan babbar ta'asar amman hankalinta akwance,tsoki fatuu taja tana kokarin bin ta gefen haulat din,taji tace "To ai yanzu nasan abunda kike 6oyewa hajia" da sauri fatuu ta kalleta sama da k'asa tace "ni mi nike 6oyewa? Haulat ta jinjina kai cike da takaici tace "asarar da kika ce mutumin nan yayi na tambayeki wace asara ce kika k'i fad'a man to yanzu nasan komai,ke yanzu fatuu abunda kika yi kin kyauta?hakanan ki jefar ma mutum mota har ki lalata masa glass....."katse ta Fatuu tayi da fad'in "naje na fasa d'in,dama nasan ai sai kin bi diddigi don kin saba sa man ido,to na fasan kuma ko gobe ya k'ara shiga harkata har ya d'aga hannu ya mareni sai na kara ja masa asara don ni ba ai man na kyale ehe" daga haka ta kad'a kai tayi gaba,cikin d'aga murya haulat tace "to kinsan wanene kika fasa ma gilashin mota.....? a fusace ta juyo tace"ina ruwana da ko waye,Allah yasa d'an sarkin makkah ne" ta juya taci gaba da tafiya abunta don ita tayi tunanin tambayarta haulat d'in tayi,cike da takaici haulat tai tsaye tana kallon bayanta a fili tace "lallai Fatuu bata da hankali wllh bata san bala'en da ta jawo ma kanta bane,tama k'i ta tsaya ta saurare ni...." girgiza kai tayi ta fara tafiya tana ta sak'e sak'e a ranta "ko dai inje in sanarma gwaggo don tasan halin da ake aciki..." girgiza kai ta sake yi da sauri a fili tace "kai a'a,bai kamata ta fara jin wannan mummunan labarin daga baki na ba gaskia" can kuma tace "to wai ma ni ina ruwana da zan damu,ita wadda ta aikata laifin ma ko a jikinta,kawai dai ba dad'i ne kana tare da mutum wani mummunan abu ya same shi,to amman tunda ita taja ma kanta ai ita ta sani" ta watsa hannuwa,daina bin bayan fatun tayi,ta canza hanya,lokacin da fatuu zata sha kwana ta juya bata ga haulat d'in ba ta6e baki tayi a ranta tace gwara da nayi mata haka inba haka ba sai tace zata zo ta gaya ma gwaggo,a fili tace "inma tazo ta fadan sai in k'aryata ta tunda dai ba a gabanta akayi ba kuma bata da shaida" tayi k'wafa tace "ta sake ta gaya ma gwaggo wllh 6atawa zamu yi ba ruwana da ita" tayi maganar tana mummurgud'a baki,To hajia Fatuu ba dai yau kika fara fadin haka ba,kuma ko kun 6ata da kanku dai kuke shiryawa don keda haulat sai Allah. *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* *Mallakin* ⬇️ *ZAINAB LALUH*🌹 *(Oummu imam)* Free Page1️⃣8️⃣ Gwaggo ce ta fito daga cikin kitchen lokacin ba'a dade da gama sallar isha ba,hannunta d'auke da d'an kwanon silver madaidaici rufe da murfinsa asaman shi kuma bakar leda ce dauke da wani abu an kulle, tsayawa tayi ta fara kwala ma fatuu kira "Fatuu,fatuu,Worei mi lilma", leko kanta tayi ta jikin labule tace" ina zaki aike ni?" hajia zaki kaima tuwon nan nasanta da son tuwon dawa" da sauri ta fito jin za'a aiketa wurin Hajiyar Sanata,hannunta rik'e da k'aramin bak'in gyale ta fara k'okarin cire hijab d'in islamiyya dake jikinta tana fad'in "dama kwana biyu banje ba wllh...." Gwaggo tace"to miye na cire hijab d'in kuma,kibarta mana" turo baki tayi tace"ni nafi son in sa gyalen kinga na fi shan iska ma", gwaggo tace "A daren nan zaki sa wannan figaggen gyalen da iyakarsa kafad'a,to bar aiken ni bari in mik'a mata da kaina..." da sauri tace "a'a to yi hakuri nabar hijab din" tayi maganar tana d'aga hannu alamar ban hakuri, gwaggo ta mik'a mata kwanon tace "kiyi maza ki kai mata kidawo,sauran kuma ki tsaya shiririta sai tsakan dare ki dawo" dariya tayi ta amshi kwanon ta rungume tana fad'in yanzun nan zan dawo kakus, Gwaggo tace "to ki d'aura akai mana salon miyan ta zubo ta 6ata maki hijab din", fatuu tace "bazata zubo ba zan kula" abunda gwaggo bata lura ba fatun ta 6oye gyalen da ta hanata sawa a kasan hammata shiyasa tak'i daura kwanon aka don kar ya fad'o ta gani, A zaure ta aje kwanon k'asa ta cire hijab din ta sagale ta jikin windon d'akin kawu Amadu tasa gyalen kana ta nufi gidan Hajia. A daidai gate ta tsaya wurin Officer dake zaune shi kad'ai tace"Sannu da gadin gate Officer" ya d'ago ya kalleta yana daria,don maganar tata ta bashi dariya yace "Yauwa kema sannunki yar fillo" tace "kai kad'ai a zaune ina d'ayan Officern yake? Rausayar da kai yayi yace ya tafi yin wani uzuri ne" ta ta6e baki tace "ba wani uzuri wayo yayi maka yanzun haka zance ya tafi wurin Budurwarshi ya barka kai d'aya kana ta aikin tsaro,wllh kada ka yarda ya maida kai sakarai kaima ka rama atoh" jinjina kai yayi yana d'an murmushi jin abunda tace,sam baiji komae ba don yasan ta sam ba datsar k'umba gareta ba duk abunda yazo bakinta fad'i take yace"to yar fillo ya zanyi in rama d'in? turo baki tayi tace "nifa ka daina ceman yar fillo" kyalkyacewa da dariya yayi don dama yasan bata son sunan yace "to ke ba yar fillon bace? tace "to nidai banso ka kira ni da Fatuu na kawae" yace "to shikenan hajia fatuu na bari,sai a fad'i man yadda zan rink'a ramawa nima" tace "yo kaima budurwar zakayi sai ka rink'a tafiya tadi....." katseta yayi yace "to ni ina zan samu budurwa nida kullum ina nan zaune ina tsaron gate" tace "Yo yadda yayi shima ya samu zaka yi" ta juya tana k'okarin shiga gidan yace "to ko ke kizama budurwar tawa kawai ma...", A fusace ta juyo bayan ta tsaya ta bishi da wani kallo,shi kam sai daria yake,tace" God forbid! ni bazan zama budurwar kowa ba yanzu sai na zama likita,kuma lokacin ni nafi karfin mai gadin gate,tana gama fad'in hakan ta shige sai kuma ta sake lek'owa ta cikin gate din tace "in budurwa ka ke so kaje wurin kawata Haulatu don ita ban ji tana da burin zama koda malamar makaranta ba,kuma nasan zata so ka don sakarya ce" daga haka ta shige tana ta tik'ar daria,shima Officer dariyar yake yana girgiza kai. A corridor ta tsaya ta cire takalmanta sannan ta d'an lek'a cikin parlon a hankali ta hango hajia dake zaune saman 2-seater ta d'aura takardu saman sofa table tana rubuce rubuce idanuwanta sanye cikin gilashi,cikin d'aga murya Fatuu tace"Assalamu alaikum ga bak'uwa,ga bakuwa daga makkah" hajiya ta d'ago ta kalli entrance tana daria,fatuu ta k'ara maimaita abunda tace,Hajia ta girgiza kai tasan in ba amsa mata tayi ba,haka zatai tayi tace"Maraba da bakuwa mutan makkah shigo" shigowa fatun tayi tana ta kyalkyalar dariya itama hajiyar dariyar take tace "ja'ira", kusa da ita fatuu taje ta zauna tace"Hajiyar Sanata ina wuni" Hajia tace "lafia lou yar gidan hajiar sanata,kwana biyu baki zo kika gaida hajiyar taki ba, jiya juma'a inata zuba ido banga kinzo yiman barka da juma'a ba" Fatuu ta d'age kai ta kwanta jikin kujerar tace "Ai jiya ban je ko ina ba a d'aki na wuni kamar maijego" ta kai maganar tana ta daria,hajiya dake kallonta tace "hala rigima kika janyo?", "a'a" Fatuu tace tana kunshe daria, Hajia ta girgiza kai tace"habawa,nida nasan hali,hakanan ba ciwo ba mi zai sa ki wuni a d'aka,har yanzu dai kin k'i daina yin rigima da mutane ko Fatima? dago kanta tayi daga jikin kujerar ta d'an turo baki tace"wllh hajiya mutane ne ke tono na..." hajiya dake kallonta ta katseta"ke kuma ba hakuri ko" dariya kawai fatuu tayi,hajiya tace "gaya man abunda yasa kika wuni a daki" sosae gaban fatuu ya fadi a ranta tace "tabb wllh bazan fadi mata na fasa ma wani glass ba" a fili tace "wata yarinya ce muka yi fad'a na fasa mata hanci da baki" ta kai maganar tana nok'e kai,hajia dake kallonta ta girgiza kai tace "kai jama'a! Yanzu ina amfanin haka fatima,aita gaya maki magana baki ji,ke sam baki da hakuri to kuwa kwanan nan zamu 6ata wllh,6atawa kuma ta har abada kar ma kiyi tunanin zaki ban hakuri in hakura...."da sauri Fatuu ta saukko daga kan kujerar ta duk'a gabanta tace "Don Allah Hajiar Sanata kiyi hakuri wallahi tallahi ita taja ni kinji na rantse,daga nace ta matsa man wuri a Bus din makaranta in zauna bayan an tashi,ta fara gaya man maganganu nai shiru na kyaleta,hakan bai isa ba da muka sauka taci gaba har tana fad'a ma abokanta wai ni daga k'auye aka kawoni..." tayi narai narai da idanu kaman zata yi kuka, Ajiyar zuciya hajiya ta sauke tana ta kallon fatuu da har kwalla sun cika idanunta, tasan dama hakan sai ya faru don bata son taji tace zasu 6ata,tace"shikenan tashi ki zauna,amman don Allah Fatima ki rika hakuri kinji,yawan fad'an da kike da mutane shiyasa suke tsokanarki ai,ki koyi kauda kai akan abunda bai kai ya kawo ba kinji yar gidan Hajiya" ta k'arasa maganar ta sigar lallashi, Gyad'a kai Fatuu tayi ta koma kan kujera ta zauna tana murmushin jin dadi,hajiya ta kalli kanta da gyalen ya d'an zame tace "wai har yanzu baki je an kitse kan nan ba? ko rannan ba saida nayi maki magana akan kije ayi maki kitso bane?" Ta marairaice fuska tace "wllh Balarabar ce zafin hannu ne da ita hajia,in tayi man kitso kaman kan zai tuge gaba d'aya,ni shiyasa banson zuwa" hajiya tace"ba wani zafin hannu,nima ai tana man kitson ko,kawai dai baki son kitson ne,don ma Allah ya taimakeki gashin mai kyau ne ai da tuni ya lalace yadda baki kula dashi d'in nan,bari in Balarabar tazo yiman kitson ai nasa tayi maki shi a gabana kuwa", ta juya ta kalli kwanon da fatuu ta aje saman carpet da ta shigo tace"mina samu da daren nan haka" Fatuu ta d'ago tace "tuwon dawa ne,Gwaggo tace na kawo maki" fuskar hajiya d'auke da murmushi tace"Aikam nagode wllh,dama kwana biyu banci tuwon dawa ba,gashi Dije badai iya tuwo ba....." Fatuu tace"nikam dai ai ta kusa ta kashe ni da shi" Hajiya tayi daria tace "A ina ki ka ta6a ganin tuwo ya kashe mutum fatima?" Shiru tayi tana ta turo baki,hajia dake ta daria tace"to kinga tashi kidau kwanon miyan nan kije kitchen kisamu bowl mai kyau ki juyo man miyan sai ki daukko man plate in saka tuwon inci abuna yanzu yabi jiki kafin in kwanta,sai ki wanke kwanon ki zubo abinci na nan a kicin d'in kije kici tunda ni dai bazanso tuwon ya kashe ki ba" ta k'arasa maganar tana ta tik'ar daria, Mik'ewa fatuu tayi ta dau kwanon miyan da ledan tuwon ta nufi kitchen,Hajia tace"ki fara zubo man ruwa a roba in wanke hannuwa", juyo miyan tayi ta warware tuwon a plate ta kawo ma hajia,har ta juya zata koma kicin don zubo abincin ta waiwayo tace"Hajia ina Aunty Saude ne? Hajiya da har ta fara cin tuwon tace "tana a backyard taje ba su d'awisu abinci" fatuu tace "aikuwa bari inje bayan,dama kwana biyu ban gaisa da mutumina Aku ba...." hajia ta katse ta "A'a kar kije bayan nan,kije ki d'ibo abincin kizo ki tafi kinga dare yayi,na tabbata kika je wurin Aku kuma ai sai an biyo sawunki,ki bari gobe in Allah ya kaimu,ana tasowa islamiyyar safe sai kizo kusha fira dashi,yanzu je ki zubo abincin ki ciko kwanon" Fatuu ta gyad'a kai taje ta zubo abincin wanda dafa dukan couscous ne yaji uban kifi sai k'amshi ke tashi,ta dawo parlon ta aje kwanon akan carpet ta nufi kujerar dake kusa da telephone ta zauna lokacin Hajia har ta kusa cinye tuwon,Fatuu tasa hannu ta dau kan telephone din ta kara a kunnanta ta d'aura kafa d'aya kan daya tana murmura idanu,tace"Hajia" hajiya da ta tura tuwo a baki tace "Uwun" tace "wllh in nazama likita sai na sayi irin wannan telephone d'in kuma har a Office dina na wurin aiki zansa" hajia tace "to Allah ubangiji ya bada ikon zama likitan,amman a Office dinma gwamnati zata sa maki ba sai kinsha wahalan siya ba.....", Saude ce ta shigo cikin parlon ta kofar baya hannuwanta rik'e da wata roba mai d'an fadi,tana hango fatuu ta aje roban a bakin kofar kicin ta nufo cikin parlon da fara'arta tace "Ah Fatuu yar gidan hajia yaushe ki ka shigo" Fatuu tace "tun d'an dazun,ai naso inzo bayan hajiya ta hana" ta d'an saci kallon hajia tana turo baki,ita dai Saude Murmushi kawae take, Hajia ta girgiza kai ta kalli saude tace "to wai wurin Aku fa zata da daren nan" Saude ta jinjina kai tace"lallai kam gara ki bari sai gobe don in ki ka je yanzu har sai an biyo ki nasan" Hajia ta gyad'a kai alamar atoh, tace"Saude kije bedroom a bedside din hagu da kin jawo drawer d'in farko akwae kudi ki daukko yan ashirin guda biyar ki kawo man" Saude ta amsa da "to" ta juya don cika umarnin hajiyan. Hannunta ruk'e da kudin ta dawo dan russunawa tayi ta mika ma ta,hajia tace tsaya ina zuwa,ta juya kan fatuu da ta yi mitsi mitsi da idanu ta d'age baki tana kallo tace "to taso ki tafi kinga har tara saura,yau dai banda wani abun ci,amman gashi kije ki siya ko biscuit ne" Fatuu ta mik'e tana fadin"to ki bashshi mana" Hajia tace "a'a,ai yaba kyauta tukwuici,na yaba da tuwon naji dadin shi kwarae,kice mata nagode Allah yabar zumunci,ya kara zakin hannu" takai maganar tana murmushi, Saude ta mik'a mata kudin,ta duk'a ta dau kwanon tace "Sai da safe Hajia" ta juya kan Saude tace "zanzo gobe da safe in antaso islamiyya Aunty Saude", Saude da fara'a tace "to Allah ya kaimu" daga haka ta rungume kwanon a 6arin hannunta na dama ta nufi hanyar fita....... *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* *Mallakin* ⬇️ *ZAINAB LALUH*🌹 *(Oummu imam)* _GARGADI!_ _Wannan littafin ni na kirkire shi,komae kaji yayi daidai ko shige da rayuwar ka/ki ko wani/wata to arashi ne ba da nufi bane kuma ina mai bada hakuri,Don haka kasantuwar littafin nawa ne,ban yarda wani/wata su canza mun littafi ba ko daukar wani bangare daga cikinsa ba tare da izini na ba,Haka ban amince ba,ban yarda ba,ban lamunce ba a yada man shi ba a wata kafa ba misali,YouTube da makamantansu,ba tare da an tuntube ni ba,ni mai littafin don neman izini,Don haka a kiyaye! kuma idan ka ko kin san ba wani muhimmin abu bane Don Allah kar ayi man magana don bazan kula mutum ba,Don haka mu mutunta kanmu_🤝 *Free Page1️⃣9️⃣&2️⃣0️⃣* Fatuu na fitowa harabar gidan aka bud'e ma Haisam gate ya shigo,parking space ya shige ya parker bike din,ya fito jakar shi rataye a 6arin hannunshi na hagu,hannunshi na dama rike da Bottle water ya d'aga yana d'an sha a hankali ya nufi part dinsa, Fatuu kuwa tsaye tayi a tsakiyan harabar ta rike k'ugunta da d'ayan hannunta da ba komae,a fili tace "Kai! waye wannan kuma da ya shigo a saman waccan dirkeken babur d'in dana gani rannan a ajiye? Ko bak'o akayi bansani ba" yadda tayi maganar kamar irin gidan ubantan nan. Fatuu bata ta6a ganin haisam cikin gidan ba,don bai dade daya dawo ba weekend dinshi na biyu kenan,dama kuma tafi zuwa gidan ranakun da ba islamiyya Alhamis da juma'a saboda Working days ba lokaci da safe taje boko da yamma kuma islamiyya haka Weekends ma Safe da Yamma tana islamiyya sai dai ko da dare in an aikota kaman yanzu da aka aiko tan shima aiken akan kwana biyu ba'a aiko ta ba,Wani lokacin kuma tana cema gwaggon zata zo ta gaida Hajiar in dare bai yi ba sosae,kuma da tazo suka gaisa hajia zata ce ta tafi gida dare yayi.Ranar Alhamis da ta wuce tazo gidan da yamma kaman yadda tace ma Gwaggo bayan ta fito ne ta biyo Jamila suka yi fad'a har ta zubar mata da Awara a lokacin ne kuma ta fara ganin Haisam d'in. Ganin haisam na niyyar shigewa corridor yasa ta bi bayanshi da sauri tana fad'in "Aikuwa sai naga ko waye" daidai lokacin da ta iso bakin fence door d'in shiga part d'inshi,shi kuma yana taka matattakalar hawa balcony,jin kaman motsi a bayansa yasa shi dan juyowa,da sauri Fatuu ta koma gefe ta la6e,a hankali ta lek'o da kanta lokacin ya kama handle din kofa zai bud'e ya sake waiwayowa nan take ta gane fuskarsa don gaba daya hasken fitilu ya haske wurin kaman da rana,da sauri tasa tafin hannunta ta rufe bakinta ta juya da d'an gudu gudu tabar wurin,ko amsa saida safe da Officer ke mata bata yi ba,ta yanki hanyar gida tana yi tana waiwayen bayanta,har tana yin tuntu6e, tana zuwa daidai kiosk din kawu Amadu yace"Ke,daga ina ki ke? Cikin rawar murya tace "d..daga gidan h..hajiya tuwo na kai mata" Yace"miye a cikin kwanon nan" bata bashi amsa ba sai kawai ta bud'e masa kwanon,da yake akwae wuta nan take yaga abunda ke ciki yace "Ah nima kam zanci in kin shiga ki d'an zubo man a plate" tace "toh" daga haka ta shige gidan da sauri,har lokacin hijab d'in da ta d'aura jikin window na nan,tasa hannu ta ciro ta wuce ciki,a bakin kofar kicin ta aje kwanon ta shige d'aki, fad'awa tayi saman Gado ta takure wuri d'aya sai faman zare ido take cike da fargabar Mutumin nan da ta gani,a ranta kuwa sai maimaita abu d'aya take "dama a gidan hajiya yake...!" a fili tace "Innalillahi,to ko ya gaya ma hajia..!!! Can kuma tace "to amman da ya gaya mata ai da tayi man magana" ta rik'e ha6a alamar tunani, Ta ci gaba"to ai bai san ni ko wacece ba,kai kilan ma ya fad'a mata fa" ta shiga yarfa hannuwa tace"Aikuwa in hajia tasani ta kuma gane ni ce...." shiru tayi saboda wani bugu da kirjinta ke yi sai zaro ido take, Gwaggo ce ta fito daga d'aki hannunta rik'e da buta zata band'aki,daidai kitchen ta tsaya tana kallon kwanon da Fatuu ta aje a ranta tace "Ah wannan ba kwanon dana aiki fatuu dashi bane,yaushe ta shigo gidan? hannu tasa ta bud'e kwanon k'amshin couscous din ya bugi hancinta,tace"tabbas fatuu ta aje shi" d'agowa tayi ta kalli bakin kofar d'akin Fatun bata ga takalmanta ba don dasu ta shige d'akin hakan yasa tayi tunanin ficewa ta sake yi kenan,kwafa tayi a fili tace "zata dawo ta same ni,saita fad'an inda taje a daran nan" daga haka ta wuce band'akin. Shiru shiru gwaggo nata jira taji shigowar fatuu,har bayan wani lokaci bata ji ta shigo ba hakan yasa ta fito ta nufi kofar gida ta lek'a ta wawwaiga ko zata hange ta amman bata ganta ba, wani yaro ta hango tsaye a bakin shagon Amadu tace "Kai yiman kiran Amadu don Allah" tunkan yaron yayi magana Amadu yace mashi "naji", bayan ya sallami yaron ya bud'e kofan kiosk din ya fito ya nufi inda Gwaggo take tun kafin yace wani abu gwaggo tace mashi "Fatuu fa? Da mamaki ya maimaita sunan fatu yace "ba tana a cikin gidan ba? tace "a'a bata nan" shiru yayi yana tunani can yace "gaskia nadai ga sanda ta dawo daga gidan Hajiyar Sanata tace ke kika aiketa,harma naganta ta dawo da abinci nace ta d'an zubo man" Gwaggo tace "to ta kawo ma abincin? Yace "a'a,tunda ta shiga banga ta fito ba gaskia,kin duba d'akinta? Tace "ai ko takalmanta babu a kofar d'akin,shiyasa ma ban duba ciki ba,don nasan in tana nan zan gansu a bakin d'akin" Amadu yace"ki dae duba cikin kilan ta shiga dasu don dama kaman a firgice take ta shiga gidan", Gwaggo ta ta6e baki tace " wannan daman ai koda yaushe ma a firgice take,bari in duba d'akin to" har ta nufi ciki ta juyo tace"ka shigo ga abincin can a kofan kicin sai ka d'iba ka rage mata" yace "toh" daga haka ta nufi d'akin Fatuu,tsayawa gwaggo tayi cike da mamakin ganin fatuu kwance saman gado ta duk'unkune wuri guda,ta nufeta ta d'an leka fuskarta sai taga bacci take,gwaggo tace "bacci kuma.." hannu tasa ta d'an bubbuga k'afafunta aikuwa nan da nan ta farka firgigit sai zare ido take tana kallon gwaggon, Gwaggo ta mik'e tana k'are mata kallo tace"yaushe kika shigo gidan? Kuma lafiya kike yin bacci haka? Saukko da k'afafunta tayi k'asa tace "tun d'azun na shigo"tasa hannu tana goge idanunta, "amman ba ke kika zo da abincin da na gani a kofan kitchen ba" tace "ni nazo da shi,hajiya ta bani" Gwaggo tace to "bazaki ci bane kika aje kika zo kina bacci,kuma ma nasan ko salla baki yi ba" ita dai fatuu sai faman zare ido take hakan yasa gwaggo tace"wai mike damunki ne kike ta faman zaro idanu,da gani baki da gaskia,halan wata rigimar kika jawo,don nasan wannan baccin dama ba na Allah bane,da gani na rashin gaskiya ne" gaban fatuu ya fadi rass cike da tsoro take kallon gwaggon, tasan in har gwaggon taji abunda ta aikata kashinta ya bushe balle kuma taji mutumin dan gidan hajia ne tabb......,tsawa taji gwaggo ta daka mata "ba dake nike bane fatuu,mi ya faru ki ka zo kika kwanta haka? A daburce tace "da..dama kare ne ya biyo ni" sam bata san ta ambaci karen ba, Gwaggo ta harareta tace"kece ke tsoron wani kare,sau nawa kike zuwa kina tono karen,ina kwanan nan kika je kika kinkimo d'an karya ta biyo ki har kofar gida,shine zaki wani ce man kare ne ya biyo ki...." da sauri ta katse gwaggon ganin zata gano k'arya take tace "ai ba irin shi bane fa,wannan fa irin mai gashi buzu buzu ne mai kaman zaki" ta kai maganar tana ta zare idanu tana hadiyar yawu, gwaggon tace "to ke miya had'a ki da irin wannan karen, ina ki ka ganshi da zai biyo ki? tace "ina fitowa daga gidan hajia wani mutumi yazo zai wuce dashi shine yaji kamshin abincin hannuna yayo kaina shine na rugo" gwaggo ta girgiza kai don ta yarda da abunda fatun ta fad'a,tace "Allah ya kyauta to" da sauri fatuu tace "Amin,ganin ta yarda da k'aryar da ta gandara, Gwaggo ta juya tana fadin "ki fito kici abincin,kiyi sallah sai kiyi baccin da kyau..."daga haka ta fice,fatuu ta dafe kirjinta alamar tasha,ta mik'e tabi bayan Gwaggon. Amadu na gab da fita hannunshi rik'e da plate din daya d'ibi abinci yaji gwaggo ta fito daga dakin fatuu tana magana,ya juya yana tambayarta fatun na ciki? Gwaggo ta ta6e baki tace "tana nan,wai kare ne ya biyo ta shine ta tsorata,harda su baccin dole" dariya Amadu yayi yace "Ashe akwae karen da zai iya firgita ta haka"ya girgixa kai daga haka ya fice. Washegari Safiyar Lahadi,Fatuu na zaune a ajinsu na islamiyya,tana ta zuba ido taga zuwan Haulat don dama tana riganta zuwa saboda gidansu Fatun yafi kusa da Islamiyyar inta biya ma haulat d'in ta koma baya sosae,sai dai ko in haulat din ta fito da wuri su hade sai in an tashi ne suke tafia tare, Har aka kusa tashi shiru haulat bata shigo ba,hakan yasa fatuu ta fara damuwa a ranta kuwa tunani ta shiga yi tana fadin"To lafia haulat bata zo ba??,sai kace ba fushi fatun take da ita ba,duk tabi ta damu,har aka tashi islamiyyar Haulat bata zo ba,hakan yasa fatuu ta yanke shawarar zuwa gidansu ta gani ko lafia, Tafe ta ke ita kadai a hanya don sam bata da k'awar da take tare da ita inba haulat ba, duk wadda ta fara k'awance da ita ba'a daukan lokaci ake rabuwa ta tsiya tsiya, da fatuu taga mota ta taho sai ta rufe fuskarta wai don kar ace mutumin nan ne na gidan hajia,dama ko da safe da zata zo islamiyyar cikin dar dar ta fito daga gida,karshe ma da gudu ta shige lungun jikin gidan hajiyan duk don kada Haisam ya fito su yi kacibus,a ranta ta ke cewa"Yanzu shikenan sai dai in daina zuwa gidan Hajiar...."ta girgixa kai a fili tace"kam aikam bazan daina zuwa ba tunda ma naga hajiyan bata sani ba ai" "to kuma in ku ka had'e wata rana yace ma hajiyar kece ki ka fasa masa gilashin mota fa?? wani 6angare na zuciyarta yace, sosae gabanta ya fad'i ta kasa cewa komae, Daidai lokacin da ta karya kwanar da zata hau layin gidansu a lokacin kuma Gaye da Abokinshi suma suka shigo kwanar,kai da kagansu sai dai kace Allah ya shirya,tun daga kan askin kansu har zuwa shigar da suka yi,tsayawa yayi yana yin arba da Fatuu,ya rik'e baki da hannunshi guda yace "Kee! Wai har yanzu kina yawo a gari ba'a damk'e ki ba? Wani irin kallo Fatuu tayi mashi tace "A damk'e ni akaini ina? Gaye yace" inda ya cancanta akai ki wato gidan yarii...." Idanu waje Fatuu tace "kaji man gaye da Muguwar fata,yo minayi za'a kaini gidan yari??? Wata yar iskar dariya yayi "Oh baki ma san mi kika yi ba ko,to glass din mota da kika fasa ma wannan mutumin rannan.."sakin baki fatuu tayi tana kallonshi cike da mamakin yadda akai yasan hakan,ya ci gaba "nasan komae yarinya ki ke wani kallo na,don akan ido na kika jefi motar,Oh ke kin d'auka kin jefi banza ko" ya k'ara shek'ewa da dariya "to billahillazi baki ci bulus ba,ruwa kika 6allowa kanki,don kud'in wannan glass din ko wanda ku ka fito ciki d'aya kika fasa mawa na rantse da sarkin da yake busan numfashi bazai kyale ki ba,yo kin kuwa san nawa glass d'in nan yake? Fatuu dake tsaye kaman gunki zufa har ta fara tsatstsafo mata ta girgiza masa kai alamar a'a,gabanta sai fad'uwa yake,Yace "to wannan gilashin yayi naira miliyan d'aya,don ita kanta motar zata yi miliyan 10..." Fatuu ta zaro idanu waje gaba d'aya,sai Maimaita million d'ayan take a cikin ranta,a razane tace "Nawa ne Miliyan d'aya? Gaye da ke kallonta,da mamaki yace "yo ke dama hakanan kike zuwa makaranta kwalwar kifi ce dake,miliyan d'ayan ce baki sani ba? Da sauri tace"nasani, kawae yawan kudin ne a zahiri ban sani ba don ban ta6a ganinsu ba" Gaye ya gyara tsayuwa yace "to kinsan dubu d'ari?" "dubu d'ari..." ta maimaita tana dan tunani,can tace"Eh nasani,Baffa na ya ta6a saida shanuwa dubu dari da talatin kuma har kud'in ma na rike a hannuwana,daya hannu na rike dubu d'arin,dayan kuma dubu talatin d'in" da sauri yace"Yauwa toh,ita dubu d'arin irinta sau goma sune miliyan daya,kudin gilashin kenan,ai mu ma barshi a kudin shanuwar sau goma kawae..." Cikin tsananin tashin hankali Fatuu ta katse shi, "kace kuma dubu d'ari sau goma yanzu kuma kace duka kudin shanuwar...." Gaye ya katse ta"Oh kina nufin baza'a biya kudin gyara ba kenan,ai dole abashi harda na wanda zai yi aikin sa glass din ko Aljana" Idanu waje fatuu ke kallon gaye tama kasa yin kwakkwaran motsi ga zuciyarta dake bugawa ba k'akkautawa lokaci guda taji fitsari na niyyar zubo mata,kana kallonta zaka fahimci tsananin tashin hankalin da take ciki ba kad'an bane, zuciyarta kuwa tana bugawa tana maimata mata "kudin shanu gomaaa!!!" Kamar Gaye yasan abunda take fad'a a zuciyanta yace "kin dai san bazan maki karya ba,don ba inda bama fad'awa a Nigeria,har legas dai tasan da zamana,ba kalar motar da bansan kud'inta ba,ke har kudin jirgi na sani balle wata mota k'aramar Alhaki. Abokin gaye da tunda suka tsaya bai tanka ba kunnansa d'aya mak'ale da earpiece yana sauraron waka yana dan jujjuya kai,yasa hannu ya cire earpiece din yace"Baabah wai yane? mi tayi ne naji sama sama kana ta mata bayani harda uban lissafi?" Gaye yace "ruwa ta 6allo ma kanta baabah....,nan ya bashi labarin abunda fatun ta aikata, yace "na gidan da muka wuto yanzu ka ke tambayata gidan waye,nace ma gidan Uwar Sanata ne kuma Matar tsohon Ministan tsaro? Abokin ya gyad'a kai alamar"Ehh,gaye yace"to mutumin gidan ne ta yi ma wannan aika aikar,don ni farko ma bansan d'an gidan bane ina dai d'an ganinshi kwanan nan yana wucewa a Motoci kala kala,har wani gangamemen Bike yake hawa,ina jin wannan bike din yayi million goma shima ko ma fi, sai shekaranjiya tsoho yaja ni zuwa sallar juma'a a Masallacin gidan,na ganshi tare da Hajiyar sun zo suma,to nan nagane dan gidan ne ashe" Ya cigaba"Kasan masu kudin nan da shegen wayo,in suka gina tangamemen gida sai suyi dan Masallaci wai Allah ga naka,don kar a masu surutun basuyi ba,duk da dai su nasu babba ne" yana maganar yana watsa hannuwa sai kace mai yin debate, Abokin fuskarshi da mamaki yana jinjina kai yace "kai kace master ce ta rashin ji" Gaye yace"ehh mana,wannan da kake gani furofesa ce ba master ba,don inta 6allo wani aikin yasin ko ni jinjina mata nike,dubi dai abunda ta aikata yanzu ni yaushe zan fara haka,ban aje ba,ban ba wani ajiya ba,Iyaye kuwa sai dai ace lahaula saboda talauci" yana maganar yana wani janta, Abokin ya kwashe da daria yace kama aikatan ai kasan inda za'ai da kai,billahillaxi gidan yari straight inbaka biya ba,aje aita cin gabza.."Gaye ya tuntsire da dariya yana rik'e wando, Yace"Allah yai man tsari da cin gabza baabah,shiyasa nike taka tsantsan,nadai je cell inyi kwanaki in fito don wannan yama zama gida,don ina daraja tuwon gyatuma ta,baka sanin dadin shi sai an had'aka da gabza yasinn..." gaba d'aya suka tuntsire da wata yar iskar dariya,ita dai Fatuu sai kallon su take tamkar yau ta fara ganinsu,zufa kuwa tuni ta lullu6e fuskarta,sai had'iyar miyau mai d'aci take. Abokin gaye ya kalleta cikin nuna tausayi yace"Wayyo baiwar Allah na tausayi maki wllh,yanzu zaki bar tuwon gyatumarki ki koma cin gabza,duk wannan hasken fatar naki da kyawun fuskar ki sai ya disashe qur'an,in kuma kina da gashi to duk kwarkwata sai ta cinye shi,sai dai ko in kuna da kud'i sai ku biya shi abunshi kawae...." Gaye ya katse shi da sauri "yo ina suka ga wani kud'i duk kanwar ja ce yasin,itafa kakarta ke ruk'onta kuma in fada maka kakar attendar ce a asibiti irin masu share share da goge gogen nan,ina zata ga miliyan d'aya ai yasin ko nayi rantsuwa bazanyi kaffara ba,ko kwatan miliyan bata da" Abokin yace "Kace dai dole sai anje an had'e da gabzar dai...." da sauri Gaye yace "Comfat,don a ranar sai da ya tambayeni nayi masa kwatancen gidansu,shiyasa nayi mamaki dana ganta har yau ba'ai ramm da ita ba, amman nasan kilan sunje basu samu kowa a gidan ba,kuma kaga jiya da yau ba aiki,amman na tabbatar gobe Monday dole azo a damk'e ta", Ya juya kan Fatuu yace "To Aljana,sai ayafi juna,sai Allah kuma ya k'addara za'a sake ganawa,don can d'in ba sauki, wasu ma wuya ke kashe su, nidai na yafe maki" daga haka ya juya kan abokin nashi yana fad'in "hayya,Baabah mu ware ko.." suka yi gaba abunsu suna wata yar iskar tafia. Kasa motsawa Fatuu tayi daga inda take don k'afafunta ba k'aramin nauyi sukai mata ba,Kalaman gaye na k'arshe sun matuk'ar razana ta"Ashe mutumin har yasan gidansu...! Shine abunda ya kara tada mata hankali,kallonsu gaye tai tayi har suka 6ace ma ganinta, irin su Gaye sai su kashe mutum,don halin da Fatuu take ciki tsaff zuciyarta zata iya bugawa don tunda take bata ta6a janyo rigima irin wannan ba,iya ta 6arar ma yara abu gwaggo ta biya ko ta bugi mutum har ta raunata shi gwaggon ta biya kudin zuwa chemist ta tsaya,yau gashi ta janyo rigimar da tabbas tafi karfin gwaggon,duk'awa tayi a wurin don kafafunta rawa kawae suke,ga kwakwalwarta sai tariyo mata da maganganun gaye take,bugun zuciyarta na k'ara tsananta ga zufa da ta wanke mata fuska har wuyan Hijab dinta ya fara jik'ewa,da za'a auna jinin Fatuu a lokacin tabbas daba k'aramin hawa yayi ba. Tsawon mintuna Fatuu na duk'e a wurin kafin tayi k'arfin halin mik'ewa ta fara tafiya a hankali,da kyar ta ke taka k'afafunta da sukai mata wani irin nauyi,a ranta kuwa ba abunda take Maimatawa fa ce "Kud'in Shanu Gomaaa..!!!!" *Littafin A Sanadin Makwabtaka 300 ne,ga mai bukatar ci gaba da karanta shi bayan angama Free Pages sai ya tuntube ni ta wadannan numbers din 09016265659 ko 09013804524,pls just whatsapp message banda phone call,Thanks🤝* *💖ASANADIN MAKWABTAKA💖* *BY ZAINAB LALUH📲* ~(Oummu Imam)~ *Paid Book* *Free Page 21 Wani mutum ne ya shigo kwanar ta bayan Fatun yana zuwa saitin ta yace "Ke bake ki ka yada jaka bane? sam Fatuu bata lura da ba jakarta a hannunta ba,don bata cikin hayyacinta,d'agowa tayi ta kafe Mutumin da idanu tama kasa bashi amsa,ganin yanayinta,ga fararen idanunta sun rikid'e sunyi ja yasa Mutumin cewa"baki lafia ne? d'aga masa kai kawae Fatuu tayi alamar "eh,juyawa yayi ya d'aukko mata jakar ya dawo inda take tsaye yace "Muje" bata ce komae ba tabi bayanshi a hankali take tafiyar har suka fito suka hau hanya Mutumin yace"ina ne gidanku?" da yatsa Fatuu ta nuna mashi, "to zaki iya k'arasawa?ya tambayeta,Kai ta k'ara dagawa,ya mik'a mata jakar yace "Allah ya sawak'e,ni ta can zan bi ne, ki bi a hankali ki k'arasa kinji" nan ma kan ta d'aga,Mutumin ya juya ya tafi, Ikon Allah wai yau Fatuu ce ta kasa magana,lalle ba karamin tashin hankali kalaman gaye suka jefa ta ba, Lokacin da ta iso gida shagon Amadu a rufe yake,tana shiga zaure taga k'ofar dakinshi a bud'e,shigewa ciki kawai tayi, tana shiga ta wuce band'aki tayi fitsarin da tuni ya d'aure mata mara don har ya d'an zubo ma,tana fitowa ta shige ciki,a bakin k'ofar dakinta ta aje jakarta ta shige,bata bi takan gwaggo ba don tasan bata nan tunda safe ta sanar da ita cewa aikin rana take,amman zata fita da wuri don zasu je Walimar d'iyar abokiyar aikinsu da aka d'aura ma Aure jiya Asabar,daga can zasu wuce Aiki, Can k'arshen d'an gadonta ta haye ta had'e kafafuwanta ta tura kanta ciki,tayi zuru tana ta tuna maganganun Gaye, kwata kwata ta kasa yin tunanin Mafita,don tana ganin ba wata mafita tabbas abunda gaye yace sai ya faru,don kud'in gilashin da yawa ba zai yuwu Mutumin ya yafe ba, tunda gashi harma ya tambayi kwatancen gidansu,sai lokacin wasu kwalla masu zafi suka zubo mata don tun d'azun ta kasa ma yin kukan,wani irin d'aci take ji a bakinta, Ta dau tsawon lokaci a haka, ta kasa ko kwanciya don komae bai yi mata dad'i,tana a haka har aka kira sallar Azahar,tana ji ana yin sallar amman ta kasa saukkowa daga gadon ga yunwa tana ji amman bata jin ma zata iya cin abinci, Amadu ne ya shigo cikin gidan don d'ibar Abinci bayan ya dawo daga salla,ya hango jakar Fatu da takalmanta a bakin k'ofar daki a ranshi yace "Yanzun haka tana can tana baccin tsiya bata tashi tayi Sallah ba" ya nufi dakin Fatun ya d'age labulen,kafin yace wani abu Fatuu tayi zumbur ta d'ago,hawaye duk ya wanke mata fuska,ganin haka yasa Amadu shigowa cikin d'akin yana kallonta yace"Miya faru?" dakyar murya can ciki tace "ban lafia.." Amadu dake ta kallonta har ranshi ya yarda bata lapiyan don da ganin fuskarta ma,yace"mike damunki", Tace"zazzabi da ciwon kai" yace"kinsha magani" girgixa masa kai tayi alamar "a'a" "To ai ba kwanciya zaki yi kita wani kuka ba,ba kinsan inda Gwaggo ke aje magunguna ba sai ki d'auka kisha ko" har ya nufi k'ofa zai fita ya juyo yace "Kinci Abinci" tace "a'a" juyawa yayi ya fice,ba'a jima ba ya dawo,hannunshi rik'e da plate d'in abinci yace"saukko ki ci" aje mata yayi a k'asa ya sake fita,sai gashi ya sake dawowa da Cup d'in ruwa da magani Panadol,tsayawa yayi yana mata wani irin kallo ganin bata saukko ba yace "ba saukkowa nace kiyi bane,in ki ka ban haushi sai in kyale ki kiyi ta zama da ciwon..." A hankali ta saukko cikin zuciyarta tana fad'in"in kayi hakuri ma daga yau ba sake ganina za kai ba" aje mata ruwa da maganin yayi ya nufi k'ofa yana fad'in "kafin in sake dawowa ki tabbatar kin cinye shi kinsha maganin"daga haka ya fice, Tunda ya fita ta kafe abincin da idanu,ta zabga uban tagumi tana ta faman tunanin a ina za'a samu kudin shanu gomaaa a biya mutumin nan,ita dai bata so akaita gidan yarin nan,gashi Gaye yace wasu wahala ke kashesu acan....,Zuciyarta ce ta raya mata "ARD'O" dammm gaban Fatuu ya fad'i,lokaci guda kuma ta fashe da matsanancin kuka,a fili take fad'in "Shi kadai ne zai iya biyan wadannan kudin,amman nasan ko kashe ni za'ai a gabansa da kwarankwatsa ba zai biya ba...." a zuciyarta tace "to ko in fad'ama Kawu Amadu ne..."da sauri ta girgiza kai a fili ta sake cewa"kafin gwaggo ta dawo nasan ya karairaya ni, don dama shi ake sawa yana zaneni"haka dae Fatuu tayi ta tufka da warwara,k'arshe ta maida hankalinta kan Abincin wanda jallof din shinkafa da taliya ne,a hankali tasa hannu ta d'iba ta kai baki ta fara taunawa da kyar take hadiye abincin,tana yin loma ukku ta tsame hannunta,sam bata jin dad'in abincin,shima d'aci yake mata a baki,tayi zuru tana kallon shi don tana jin yunwa sosae,a ranta tace "dama tuwo Gwaggo tayi kilan in fi jin dad'in shi...."Wata zuciyar tace"A ina zaki k'ara ganin tuwon ma,dama kinci Abincin don daga yau shima ba sake ganinshi zaki ba sai dai ki rink'a ganin gabza" da sauri ta jawo Abincin ta shiga turawa a baki ba don dad'i ba. Bayan ta cinye Abincin tana cikin shan Maganin Amadu ya d'aga labulen ganin ta cinye yace" Yauwa,yanxu sai kitashi ki yi sallah inkin gama sai ki kwanta,insha Allahu zaki ji kin wartsake",a hankali tace "toh" ta mik'e don yin sallar, Bayan ta gama sallar ta d'aga hannuwa sai Addu'a take tana fadin,"Allah don Allah na rok'e ka kada kasa a kaini gidan yari,don Allah,don masoyinka Annabi Muhammadu kasa Mutumin ya manta da abunda ya faru kwata kwata,nayi maka Alkawari na daina rashin ji,zan zama kamar Haulatu....." haka tai ta rok'on Allah tana kuka har tagama ta tofe a hannuwanta ta shafa,A saman abun sallan ta kwanta ta takure jikinta tana ta ajiyar zuciya a haka bacci ya kwashe ta. Bayan an kira Sallar la'asar Amadu yazo ya tada ta yace"ki tashi ki watsa ruwa kiyi Sallah,naji ruwan bokitin wurin wanke wanke nada d'umi sai ki d'ibe shi" kai ta daga masa kawae,ya juya ya fice. Bayan ta gama sallar tayi zaune a wurin ta buga uban tagumi,ba laifi ta dan ji dad'in jikinta,tunani ta fara yi ko ta tafi islamiyya taje tagani in Haulat tazo ta fadi mata halin da take ciki...,d'an tsoki tayi a fili tace"koma na fad'a mata,ba abunda zata iya yi,karshe ma ta kama man nasihar banza,baccin lokaci ya rigada ya k'ure" can kuma wata zuciyar ta raya mata"ba gara kije ba,watakil dalilin zuwan Allah ya tausaya maki yasa a k'i zuwa kama ki,amman in kika zauna kina iya ganin anzo yanzu an tafi dake.." zumbur ta mik'e ta nufi yar wardrobe dinta ta ciro wasu kayan Islamiyyar tasa, tunda ta nufo zaure take jin tashin kida a waje,Amadu ne ya kunna wakar india a shagonshi,a hankali take tafiyar don yadda take jin jikinta kaman ta tashi daga ciwo sam ba karfi,lokacin da ta fito waje ta girgiza kanta tace "Shi sam baida matsala,waka ma yake ji" hannu tasa ta share dan siririn hawayen da ya zubo mata a ido daya,tace"in sha Allahu nima indai Allah ya ku6utar dani ba ruwana da kowa" Allah sarki Fatuu har kin bani tausayi,sai dae Allah yasa ba tuban mazuru kike ba. Amadu ya hangota zata wuce ya leko da kansa yace "zaki iya zuwa islamiyyar ne? tace "ehh naji nasamu sauki" yace "dan jira" miko mata biscuit pure bliss yayi da sweet guda biyu yace"Sai kin dawo,kibi a hankali" daga haka ya maida kanshi ciki yana ci gaba da bin wak'ar da yake saurare hadi da dan jujjuya kai,tafiya take tana ta kallon abunda Amadu ya bata tana mamaki wai yau ba tare da ta rok'e shi ba ya bata,ko ya zage ta kaman yadda yake mata inta tambaye shi,wani lokacin har rankwashinta yake kafin ya bata yace ita zata cinye masa jari,dan murmushin takaici tayi a fili tace "tabbas shima yaji a jikinshi ya kusa rabuwa dani" taci gaba da tafiya tana yi tana goge kwallan dake zubo mata da gefen hijab dinta. Tunda ta zauna a aji kanta na k'asa,Haulat sai kallonta take tana nazarin yanayinta gashi akwae malami balle ta tambayeta abunda ke damunta,sam ta kasa natsuwa ganin kwalla na zubo ma Fatun tana sa hijab tana gogewa,tana sauraron bayanin malam dake masu Ahalari tana kuma satar kallon Fatuu, "FATIMA MUHAMMAD ARDO" Malam ya kira sunan fatuu,sai dai sam bata ji shi ba, Haulat ta ta6o ta,lokacin yana k'ara kiran sunan,da sauri ta d'ago Manyan idanunta da su kayi ja ta kalle shi hadi da fad'in "labbaika...." tashi ki k'ara yi mana bayanin da nayi" Malam yace,tsuru tayi ta kafe sa da idanu,don bata san akan mi yayi bayanin ba,gaba daya ajin anyi tsit ana ta kallonta, Haulat ta d'an dukar da kanta murya can k'asa tana fadi mata bayanin da yayi,Fatuu ta saci kallonta sai dai sam bata san mi take cewa ba, A fusace malam yace"ke muke saurare!" Fatuu ta dukar da kanta jin kwalla zata zubo mata,hakan ya kara fusata Malam din yace "fita kiba mutane wuri,tunda ba karatun kika zo dauka ba" ba musu ta nufi hanyar waje har lokacin kanta na k'asa,Malam yaci gaba da magana"don iskanci yara k'anana daku sai kuje kuyi samari,in kuka yi fad'a kuzo kuyi ta tunane-tunanen banza,in baku son karatun kuje kuce Aure kuke so mana" Sauran yan ajin suka sa dariya suna sussunna kai kasa alamun kunya banda Haulat da sam bata ji dad'in maganar da yayi ba,don tasan ba abunda ke damun Fatuu ba kenan,tabb ita da koda wasa akace ana sonta yanzu ta fara masifa da zage zage tana fadin ita bazata yi saurayi ba sai ta zama likita",haulat ta fada a ranta,ita kam Fatuu kallon Malam din tayi da runannun idanuwanta suka hada ido yace"ko zaki zo ki buge ni ne?" batace komae ba ta juya ta fice.... *💖ASANADIN MAKWABTAKA💖* *BY ZAINAB LALUH📲* ~(Oummu Imam)~ *Paid Book* *Free Page22⃣* Fatuu na tsaye ta jingina da karfen barandar gaban ajinsu ta tafi duniyar tunani,Malam ya fito,tsaye ya yi a bayanta yana kallonta kafin yace "ke cewa nayi ki fito ki tsaya? Wato kinfi karfin ki rage tsawon ki ko? Juyowa tayi ta kafe shi da idanu batare da tace komae ba,hakan yasa ya k'ule cikin daka tsawa yace " ba dake nike bane! Sunkuyar da kanta tayi k'asa tace"baka ce in rage tsawo na ba ai,cewa kayi in fito waje kawae....." katseta yayi "da yake ke dak'ikiyace komai sai ance ki yi ko?" kallon k'asan ido tayi masa suka hada idanu,a fusace yace "kee! ni kike harara...." daga bayansa yaji ance"abunda yafi harara ma yi maka zatai indae wannan ce" a tare suka juya don ganin mai maganar,wani matashin malami ne ya tunkaro su yana sanye cikin farar shadda jamfa hannunsa na dama rungume da Qur'ani dayan kuma rike da zungureriyar dorina,shine displine a Islamiyyar,ya iso inda suke fuska tamke,wanccan malamin yace"Yauwa Malam Nazifi,gatanan kayi mata hukuncin da ya dace,ina bayani hankalinta na wani wuri,nace ta fito kuma tafi karfin ta rage tsawonta", jinjina kai Malam nazifin yayi daga haka d'ayan malamin ya juya ya tafi, Kallon Fatuu yayi fuska A d'aure yace "bani hannuwanki! ta d'an marairace fuska tace"Malam don Allah ka buge ni a jiki' dama malam nazifi yasan bata son bugu a hannu,hakan yasa ya k'ara tamke fuska yace"ina wasa dake? Girgixa masa kai tayi,ya d'aga bulalan ba tare da yace komae ba,a hankali Fatuu ta mika hannuwan suna dan rawa ta runtse idanunta ya fara bugunta tamkar da gayya,yana yi mata bulala biyar ta janye hannuwan tana dan yamutsa fuska don ba k'aramin zafin bugun take ji ba" yace"nace ki sauke hannuwan ne?" turo baki tayi tamkar zata fashe da kuka tace "don Allah malam kayi hakuri....."ya katse ta "kinsan kina tsoron bugun kike ma mutane iskanci,bulala goma zanyi maki amman wllh kika yi wasa zata koma ishirin", sanin da gaske yake yasa ta sake mik'a masa hannu daya tana yi tana canjawa har ya gama,ta juya tana yayyerfe hannu don sosae ya bugeta hannuwan duk sunyi jawur,malam nazifi ya dakatar da ita daga tafiya ta hanyar fad'in "ban sallame ki ba" ta juyo tana kallonshi cikin ido ta d'aure fuska,"kije Office dinmu ki cika mana bokitinmu na ruwa,sannan kije ki wanke gaba d'aya bandakin ku na mata,basai nace kiyi ba,inkin so kina iya kin yi" daga haka ya juya ya shige Class dinsu don shine Malaminsu na Al'Qurani da tajweed,da sauri Haulat ta koma gun zamansu don dama tana a la6e bakin kofa tana ganin duk abunda ke faruwa. Fatuu ta sauke ajiyar zuciya ta juya don zuwa yin purnishments din da Malam ya bata,a hankali ta ke sa hannu ta na goge kwallar dake zubo mata cikin ranta tana fad'in "Mugu kawae,dama yafi kowa tsanata a makarantar nan,daga yau ba sai ka sake gani na ba zaka bugan..."a fili tace"dama ban zo ba,tunda ba za'a kyale mutum da abunda ya isheshi ba,a daidai nan ta iso bakin staffroom din,Haulat nata faman zuba ido don ganin shigowar fatuu,lokaci bayan lokaci ta ke kai dubanta kan k'opar shigowa amman shiru gashi har an kusa tashi kuma har lokacin malam Naxifi na cikin class d'in saboda abu biyu yake masu,sai lokacin da aka tashi Mlm Nazifi ya fita,da sauri Haulat ta d'auki jakarta had'i da ta Fatuu ta fice da sauri baiwar Allah har tana yin tuntu6e wurin fita,hanyar kewayensu ta nufa don taji Aikin da aka sa fatun,bata k'arasa isa ba ta hangota a hanya tana tahowa,Haulat ta ja ta tsaya tana kallonta itama Fatun kallon haulat d'in take har ta iso wurinta,hannu kawae ta mik'a mata alamar ta bata jakarta haulat ta mik'a mata jakar a hankali fatuu tace "nagode" daga haka tayi gaba, haulat itama ta bi bayanta har suka fita daga cikin Islamiyyar suka mik'i hanya,haulat a ranta tana ta tunanin mike damun fatuu haka,don tunda tazo ta lura da yanayinta tana cikin damuwa ga bugu da kuma aikin da aka bata, A fili tace"ba abun mutum ya tambayeta ba tayi man wulakancin da ta saba,gara ma in kyaleta,da tana son in sani ai da ta sanar dani" can dae haulat ta kasa daurewa ta kira sunanta da yake ba tazara sosae a tsakaninsu don a hankali fatun ke tafiya ba kaman yadda ta saba wuwwurga kafa ba,bata juyo ba haulat ta sake cewa"Fatuu"a hankali ta juyo tace"minene"haulat ta k'arasa gabanta tace "mi yake damunki ne naga kaman kina cikin damuwa tunda kika zo" fatuu tayi yar ajiyar zuciya ta ta6e baki tace"Uhmm,in na gaya maki damuwar zaki man magani ne" d'an murmushi Haulat tayi tace"ai bansan mike damunki ba,balle in san ko zan iya yi maki maganin" girgiza kai Fatuu tayi cikin karewar murya tace "koma kinsani bazaki iya man magani ba,don haka ba sai kin ji ba" ta juya ta ci gaba da tafiya a hankali, Haulat tayi tsaye sototo tana mamakin abunda Fatuu tace ma ta,don tasan bata 6oye mata abu in yana damunta,koma ta 6oye zata dawo ta bayyana mata,a ranta tace" to mike damunta haka da bazata fadi man ba...?cikin d'an d'aga murya haulat tace "Amman ko da bani iya yi maki maganin ai kilan in baki shawarar da zata iya yi maki maganin ko" shiru bata ce mata komae ba kuma bata juyo ba,hakan yasa Haulat juyawa tabi d'ayan 6arin dake kallon wanda fatuu tabi ta fara tafiya,Fatuu nata juya maganar haulat aranta na shawarar da tace zata bata,tabbas Haulat na bata shawara kuma shawarar nayi mata aiki,ta tuna wani laifi da tayi kwanakin baya wanda ta tsorata sosae hakan yasa Haulat ta bata shawarar yadda zata yi ta ku6uta bayan tayi mata fad'a,aikuwa shawarar tayi mata Amfani don ta tabbatar lokacin ba don aiki da abunda haulat din ta fadi mata ba Kawu Amadu sai ya karyata....,da sauri ta juya "Haulat,haulat.." ta k'wala mata kira har sau biyu,sannan haulat taja ta tsaya ta juyo fuska a d'aure da alama tayi fushi ne,ganin haka yasa Fatuu ta nufeta ta tsaya gabanta tace"bari in fad'a maki to,amman shawarar zaki bani kar kice zaki man fada don aikin gama ya rigada ya gama, kuma ko baki man fada ba ma nayi dana sani bazan kara aikata irin hakan ba..."ta sunkuyar da kanta jin kwalla zasu zubo mata,ajiyar zuciya haulat ta sauke ta kai dubanta gaban wani gida dake agefensu,ta kamo hannun fatun tace"muje can to ki fadi man nan akan hanya muke" daga haka suka nufi jikin bangon gidan suka jingina, Haulat tace "ina jinki,mike damunki?" Fatuu dake ta matsar kwalla kamar jira take haulat ta tambaye tan ta rushe da kuka tace "Haulat na bani na lalace,gidan yari za'a kai ni,kuma kilan acan zan mutu ma.." zaro idanu haulat tayi gabanta ya fara faduwa,cikin rashin fahimtar zancen fatuu tace"waye zai kai ki gidan yari?" cikin kuka Fatuu ta zayyana mata duk yadda sukai da Gaye harda aikenta da akai gidan Hajia jiya da daddare harta ga Haisam d'in. Ajiyar zuciya mai karfi Haulat tayi tace "nasan maganar ma" da sauri ta kalleta tace"kinsan za'a kaini gidan yarin dama kuma baki fad'a man ba.." jinjina kae Haulat tayi tace"jiya da yamma nima na hadu da gayen kuma shine ya sanar dani abunda kika yi har da aka tashi nayi maki maganar, kuma naso in sanar dake Mutumin dan gidan Hajiyar Sanata ne amman kika k'i saurarata k'arshe ma sai cewa ki kae wai ko dan sarkin makka ne ke ina ruwanki...." cikin kuka Fatuu tace"ai ni nayi zaton tambayana kike ko nasan mutumin" taci gaba da rusa kuka,Haulat tace "ki daina kuka,ki kwantar da hankalinki..." a fusace Fatuu ta katseta tace"amari hakkilo?ya za kice wai na daina kuka,kuma taya zan kwantar da hankalina bacin nasan tabbas duk abunda gaye ya fad'a gaske ne.." Haulat ta juyar da kanta gefe ta dan gwalo ido cikin ranta tace"tabb lalle abu yayi abu,yau su Fatuu harda yin fullanci,ita da bata son yi,wani lokacin inta fama da ita tayi man ta k'i yi" Fatuu dai sai kuka take tana sambatu "ni wllh bansan haka motan keda tsada ba,da bazan ma fara fasa masa gilashi ba,ace kudin shanu gomaa har sau goma ne kudin motar,ba dole gilashin ma yayi tsada ba" Haulat ta jinjina kae ta kalleta tace "nawa yace motar take ne" da sauri fatuu tace"Miliyan goma faaa" haulat tace "bama tada tsada sosae...",a fusace fuska jage jage da hawaye fatuu tace" miliyan goman ne ba tsada,shiyasa nace baki da hankali,koda yake nasan baki taba sanin yawan miliyan a hannu bane shiyasa zaki ce haka,yo inama zaki gansu" girgiza kae haulat tayi sam bata ji komae ba don dama ta saba datsa mata magana,tace "dama ban ce ai na ta6a ganinsu ba ko,kawae dae nasan akwae motoci masu tsada sosae da yan gayu ke hawa,don na ta6a ji yaya Osman dinmu yace harta miliyan d'ari akwae" da sauri Fatuu ta dafe kai tana fitar da numfashi mai karfi a rude tace "kice Allah yaso ni da ba irinta na fasa ma gilashi ba,yasin nasan wannan sai dae a harbe ni kawae" ta k'ara fashewa da kuka,ita kam haulat dan juyar da kanta tayi tana murmushi don dariya maganar ta bata, Zamewa k'asa Fatuu tayi ta zauna dirshan taci gaba da kuka tana sambatu"mi woni ni fatuu,mi woni..,na bani na,in Gwaggo taji wannan maganar nasan sai tasa kawu Amadu ya kakkarya ni kafin awuce dani kuma gidan yari inje in rink'a cin gabza kwarkwata kuma ta gwaigwaye man gashi,tunda nasan ba yafe man zai yi ba,gaskiyar Gaye wllh nasan ko kawu Amadu nayi ma haka ba zai ta6a kyale ni ba sai ya dau mummunan mataki akaina,balle wannan da ba abunda na had'a dashi,nasan ko hajia taji bazata hanashi ya dau mataki a kaina ba,daman kullum tana man fadan in daina rashin ji,ko jiya ma saida tace zamu 6ata,yanzu kuma taji wannan asaran da na yiwa d'anta ta uban kudi haka,tabb ai nasan ma ba za tace ya yafe ba,to mima muka had'a da ita da zasu yafe,daga makwabtaka....,ga Hajiya dama ta iya masifaa....mi maye ni Fatuu,na mutu kawae" ta d'ora hannuwanta saman kai kafin ta dago tana kallon Haulat wadda tuni dama ita ta ke ta kallo cike da tausayi,tace"dama nasan ba wata shawara da zaki iya bani,wannan babban abu ne ba irin wanda ki ka saba ban shawara bane,nasan dole sai an kaini gidan yarin" ta kai maganar tana ta faman yin sheshsheka. A hankali Haulat ta durk'usa kusa da ita ta kalleta tace"duk da haka ina da shawarar da zan baki,kuma ina tunanin Insha Allahu zata yi aiki..." da sauri fatuu tace"kenan kina ganin in nayi amfani da ita ba za'a kaini gidan yarin ba?mutumin zai hakura?" d'an murmushi haulat tayi"tace ehh,in Allah ya yarda zai hakura nike tunani..." fatuu ta k'ara katseta da sauri"toh don Allah fada man abunda zan yi ko minene zanyi indai za'a kyale ni nidai" Haulat tace "saurin mi kike,zan fad'i maki amman sai kin yi mani Alkawarin in dae aka kyale ki bazaki kara aikata makamancin wannan abun da kika yi ba" wani irin kallo fatuu ta juyo tana mata mai kama da harara,can kuma ta dauke fuskarta ta kalli gefen haulat d'in tace "da yake kare mai bak'in baki ne ya cije ni zan k'ara aikata hakan,ko baki ji tun d'azun nace maki nayi dana sani kuma bazan k'ara ba" ta kai maganar tana turo baki,Haulat tace"nasan halinki ne kin iya tuban mazuru,sau nawa kike cewa baki k'ara yin abu kuma kizo ki karan" Cike da gatse Fatuu tace"to gwaggo kiyi hakuri...,don kawae kinga ina neman taimakonki zaki taman maganganu sai kace ni mahaukaciya ce zan sake,ni in zaki fada man abunda zan yi ki fada man lokaci na k'urewa" ta kai maganar tana dan turo baki tana kallon hanya, Karasa zaunawa a kasa Haulat tayi,ta juyo tana kallon fatuu tace"KI JE KI BASHI HAKURI........ *💖ASANADIN MAKWABTAKA💖* *BY ZAINAB LALUH📲* ~(Oummu Imam)~ *Paid Book* *Free Page23⃣* *Haisam* Zaune a cikin parloun sa yana operating laptop wadda take mai kyaun gaske jikinta sai shining yake yayin da bayanta ke dauke da tambarin Apple,jin ana k'okarin shigowa cikin parlon kai tsaye batare da anyi knocking ba yasa ya dan waiga ya kalli kopan, A hankali aka turo kopan ta bud'e,wani matashin mutum ne wanda bazai wuce tsaran Haisam din ba ko ya girme masa da kad'an ya shigo,jikinsa sanye da jeans da longsleeve shirt,kalar fatarsa kuwa za'a iya kiransa da wankan tarwad'a don ba bak'i bane,fuskansa na dauke da k'asumba mai gashi da dan yawa sai dai bai tara a saman kansa ba,gashin fuskan nasa yasha gyara sai kyalli yake da gani yana kashe masa kudi yadda ya kamata. Suna had'a ido da Haisam wanda ya jingina bayansa jikin kujeran da yake zaune ya washe baki yana daria hakan ya bayyana wushiryar dake a bakinsa,shikam haisam murmushi kawae yake yana kallon mutumin,a bakin kofan ya cire takalmansa kafin ya nufo cikin parlon yana fadin"Haisam Alee zakee,yaro dan Senator jikan Minister,na hajiyar sanata sai dubu ta taru,kowa yake son ganin 6acin ran hajia to ya ta6a ka,yaro mai tsananin farin jini,har makiyanka burgesu kake inma akwae su kenan,yadda farin ka yake na daban,haka aniyarka ma take ta daban,kaine uban duk wani mai tsafta.....a 6angaren aiki kuwa,you are the best computer engineer in the whole nation,kai kasan hardware kasan software,a bangaren Networking da robotics kau baka da tsara,ana mutane ruwa biyu kai d'in ruwa ukku ne,kaine hausa,kaine fulani,kaine larabawa.....", Tunda ya fara magana Haisam dake zaune tamkar wani saraki,hannunsa na dama rike da beard dinsa yasa index finger d'insa yana dan bubbuga bakinsa,yanata bin mutumin da ido,ganin baida niyyar tsayawa da kirarin nasa yasa shi cire yatsansa daga bakinsa Calmly yace"Abbasss...." jin kiran sunansa da haisam din yayi yasa Abbas din kyalkyalewa da dariya ya miko masa hannu suka tafa kafin kuma suka gaisa,ya nufi dayan side din kujeran da haisam din yake ya zauna yana fadin"to ya kaji praising din nawa,am i good at it?" dan ta6e baki Haisam yayi hadi da d'age gira"Not bad"yace, still Abbas d'in daria yake"kace inna maida shi sana'a zanci Abinci dashi kenan?"ya fada, Haisam wanda har lokacin fuskansa na dauke da murmushi yace"shi kuma lecturing d'in ka kaishi ina?" zama sosae Abbas yayi ya d'an kwantar da bayanshi jikin kujeran yace"baka ga yadda ya zama ba,duk yana neman komawa shiririta,that's why na fara neman wata sana'ar kaga sai yazama inada alternative in ba wanccan sai inci gaba da bin yaran masu kudi ire-irenka ina masu kirari,nasan ba karamin kudi zan rinka samu ba" Haisam da shima ya dan kwantar da kanshi cike da zolaya yace"wani ke shiriritar da aikin naku baku ba?nan gaba ma in aka biye maku kashe ilimin zaku yi gaba daya,yakamata tun wuri ai taking action akanku" Abbas dake ta daria yace"wani action kuma banda hanamu salary da ake" dage gira haisam yayi"I mean sacking...." da sauri Abbass ya d'ago da kanshi yace"amman kai mugu ne H,zakee,wato kai burinka kenan a kora mu ko" sai lokacin haisam yayi dariyar da hak'oransa suka bayyana, "in an kora mu sai akawo suwa su koyar? ko su ku za'a maido tunda an fada ma lecturing d'in wasa ne", "banyi tunanin zaka yi man wannan tambayar ba,seems like ka manta a wace kasa muke ko,kuma nima kasan dae zan iya ai,miye a ciki,all i need to do is Pgde,tunda ba education nayi ba,kai tsaya kaji ko banyi ba zan iya lecturing din,harma in fi wasu da suka dade a fannin" ya karasa maganar cike da tabbacin abunda ya fada. Abbas yace"aikuwa da kasa mata sun rinka tara c.o" "Why?" haisam ya tambaye shi. "Muddin kazama lecturer ai shikenan kuma zaka janye hankalin mata ya dawo kan ka,ba kamar yan matan jami'a da basu shakkar nuna ma malami suna sonsa komae tsaurinsa,basu damu da zai wulakanta su ba,na tabbatar hakance zata faru da kai,ai gaba d'aya nike gaya maka attention dinsu kanka zai dawo,instead of focusing on their studies,kaga ba karamar barna zakai ba kaima,don kasuwa zakayi sosae abokina" ya karasa yanata faman daria. Shi dae haisam still yayi yana kallon Abbas,tsaf ya fahimci dalilin da yasa abbas din cewa mata zasu maido attention dinsu akansa,don tunda ya taso yana k'arami ake fada masa yana da kyau na musamman har kuma yanxu da ya girma ba'a daina fada masa hakan ba,haka kuma da wuya a kalle shi ba tare da ansake waiwaya wa ba. Abbas smiling broadly ganin haisam din yayi shiru yace"ko ba daidai na fada ba,I lie? Sauke 6oyayyan ajiyar zuciya haisam yayi kafin yace"in tambayeka Abbas...?"abbas yace"I'm all ears zakee" haisam ya cigaba"have u ever talk completely without mentioning women?na rigada na fahimci is hardly a kare magana da kai baka ambaci mata ba,to ni wannan ba matsalana bane,nothing concern me wit dem,kaima da suke kula ka ai don kana kula su ne,ko bansan ka bane" Dariya sosae Abbas keyi harda buga kafa yace"to in ban rink'a ambaton mata ba,maza zan rinka ambato H,zakee,ai mata namu ne,muma kuma nasu ne" d'an ta6e baki haisam yayi yana girgiza kai kafin yace"to ya Abuja?" "sai da ka gama caccaka ta har kana man mummunar fata sannan zaka tambayeni,ashe kaima baka tausayin malamai bayin Allah", Dan ta6e baki haisam yayi"U know I was just funning u dude,ina tausayin malamai mana,especially primary and secondary skul teachers suna matukar kokari sosae,but their Salary structure is still poor,kawae al'amarin kasan namu ne sai Addu'a,may Almighty Allah give us responsible leaders" "Ameeen ya Allah" Abbas ya amsa. "Yaushe ka shigo gari ne?" gyara zama Abbas yayi yace"ban jima da dawowa ba" jinjina kai haisam yayi kafin ya kuma tambayarshi"yasu Nafeesat and my Boy Abdul? Abbas yace"suna nan lafia,ita feenah ma tayi tunanin zuwa kayi ka koma,nace mata kana a gari hajia ta sa an maido mata kai nan,har take cewa shine ko ka leka ku gaisa" dan murmushin gefe yayi"in sha Allah zan je,am not well settled har yanzu" kai Abbas ya daga yace" Allah ya yarda dama ai sai a hankali komae zai warware tunda wurin aiki ka canja" daga haka suka ci gaba da hira. *** *** *** **** Haulat tace"Ina ganin kije ki bashi hakuri tun kafin goben tayi....."cakk fatuu ta tsaya ko kyafta idanunta batayi kamar an dasa mata aya,haulat ta ci gaba"kinga idan ya hakura shikenan waya kawai zai kira yace ya janye inma yakai karar taki", juyowa fatuu tayi tana kallon haulat da alamun mamaki tace"tabb lalle kema haulat din nan wani lokacin kaman baki da tunani wllh,kina nufin in kai kaina ma kenan,kinga daga nan sai hajia tasan ni ce in dama ya gaya mata" "ba kince da aka aikeki gidan,kinga 6angarenshi daban ba?"haulat ta tambaya, Fatuu tace"Eh,amman in naje ya cafke ni ya kaima hajiyar yace ga wadda ta rotsa masa gilashin fa?" girgixa kai haulat tayi"duk da bansan shi ba,nasan da wuya ya aikata haka gaskia,akwae mutumin dana ta6a gani sau biyu kuma ina tunanin shine....."da sauri fatuu tace"wani fari ko?zaki ga kalar farinsa daban" Haulat tace"ni bazan iya ganewa ba don duk a mota nike ganinsa ya wuce kawae dae fari ne" "shine ma,don duk garin nan ba mai irin kalar farinsa.." da sauri haulat ta katseta"ke ya akai kika sani" tace"tabb yo nida na ganshi a kurkusa har sau biyu,ko kafin ya rabamu fad'a da murja har in fasa masa glass ai ran Alhamis ma da yamma sai da ya rabamu da jamila ina kokarin zubar mata da Awar...tsit fatuu tayi lokaci guda kamar ruwa ya cita,sai faman zare ido take. Girgiza kai haulat tayi tace"kin bari yama san halinki kenan,Allah yasa ya hakura" a hankali tace "Amin,ai bazan kara ba"ta6e baki kawae haulat tayi tace"kije ki bashi hakurin,kar kiji wani tsoron wai zai cafke ki yakaima hajia,na tabbatar bazai yi haka ba,don sufa yan gayu aji ne dasu,ba don haka ba yadda Gaye yace yasan gidanku ai da yaso hajiyar ta sa ni da tun ranar ya kaita har gidanku tasan kece amman yadda kika je kaimata abinci bata yi maki maganar ba kinga tabbas bata san kece ba,don haka kije kiyi duk yadda zaki ya hakura,ki nuna masa kinyi nadama kar kuma kice wai don gaye yace za'a kai ki gidan yari in ba'a biyasa ba ki ka je bashi hakurin,inta kama kita kuka ma,in bakije ba har gobe tayi indai har yakai k'arar taki to dole Hajia da gwaggo su sani koda ba'a kai ki gidan yarin ba,kuma kinga shikenan na tabbata hajia 6atawa zatai dake duk kuwa yadda take son ki,ga kawu Amadu hmmm...." Fatuu dai tayi zuru tana saurararta sai zare ido take gabanta na faduwa ta kalli haulat tace"amman kina ganin zai hakuran,ya yafe man haulat,kudin fa da yawa wllh ke baki san yawansu ba ne hmm"ta karasa maganar tana jinjina kai,haulat tace"In sha Allahu ina sa ran zai hakura,tunda na tabbatar yafi karfinsu,kuma ba ita kadaice motarsa ba,ko ni da nace maki na gansa sau biyu duk ba a mota kala daya nake ganinsa ba...."da sauri fatuu ta katseta "nima a mota daban daban nike ganinsa kuma kwalabo yake yi da kayan jikinsa da motar da ya hau" Haulat ta gyada kai"to kingani,kije dai ki bashi hakurin,kinsan wani duk zafin sa idan ka bashi hakuri akan laifin da kayi masa ka nuna kayi nadama bazaka kara ba,yana hakura" Fatuu tace"ni wllh gabana sai faduwa yake kar inje yasa akamani ko tuwon gwoggo na karshe ban ci ba..." wani irin kallon mamaki haulat tayi mata"ke da baki son tuwon kullum kina k'orafin za'a kashe ki da shi" tace"ai na daina,yanzu nagane ba shine mai kashe mutum ba,gabza ce,in kasamu tuwon kawae ka godema Allah kaci"tasa hannu tayi tagumi,ita dai haulat dan girgiza kai kawae tayi tana murmushi don tasan irin nadamar fatuu. Shiru sukayi nadan lokaci can fatuu ta kalli haulat tace"don Allah haulat to kizo ki rakani" da sauri tace"in raka ki ina? Fatuu tace"muje mu bashi hakurin....."girgiza kai haulat tayi da sauri"lokacin da kika yi masa 6arnar ai ba tare muke ba,hasali ma ba yadda banyi dake kiyi hakuri ba ki ka kiya,sai yanxu kice wai in raka ki,salon kija man balae" ta k'arashe maganar tana kallon gefen hanya. Fatuu tace"oh dama kinsan wani abu zai iya faruwa innaje shine kika tura ni don cuta? da sauri haulat ta juyo tana kallonta tace"kindai san ni bazan ta6a cutarki ba ai,kawai ina gudun babana ya ganni tunda kinga limamin masallacin gidanne,kuma kinsan ni ba wani zuwa gidan nike sosae ba sai in na raka ki wani lokacin,dama dai cikin azumi ne shine kullum sai naje kar6ar sadaka da yamma,wani lokacin kuma in raka ki da rana inje insha A.c ko don rage yunwar Azim..." cike da tsiwa fatuu ta katseta"dalla kin cika ni da wani bayani,kawai in zaki raka ni ki rakani,in kuma baki zuwa ki fada man in kama gaba na" Haulat tace "shikenan muje in raka ki amman iyakata wajen gate gaskia" wata irin harara fatuu ta wurga mata tace"to banso kisha zamanki,zanje ni kadai,kuma insha Allahu zai hakura,d'an bakin ciki sai dai ya mutu"daga haka ta mike ta kakka6e jikinta hadi da zura takalmanta ta juya zata tafi,itama haulat ta mike tana fadin"ai da ni yar bakin ciki ce da ban baki shawara ba ko,amman ba komae gobe ma rana ce,ko godiya bazaki man ba sai ma ki kira ni da yar bakin ciki" Juyowa fatuu tayi ta k'ara harararta tace"sai ki jira kiga shawarar taki in tayi aiki,kafin kiyi maganar wata godiya" Haulat tayi dan murmushi tace"insha Allahu ma zatayi kawata kuma kanwata,ba inda za'a kai ki muna tare mutu ka raba" wani kallo tayi mata tana turo baki daga haka ta juya fuu ta tafi. Cike da tsokana Haulat ta dan daga murya tace"kawata bazaki rakani ba,aike na akai in mun dawo sai muje in jira ki a bakin kofan ki shiga ki bashi hakurin" a fusace ta juyo ta kara watsa mata harara had'i da mummurgud'a baki daga haka tayi gaba abunta. Daria sosae haulat tayi ta juya tabi hanyar da tafara bi d'azun a ranta tana fadin"haka kurum kija man yanzu babanmu yaji wannan abun duk da badani aka aikata ba ai sai ya sa6a man wllh,taje dai ina mata fatan nasara,in ma fushi tayi ma shirya daga baya. Tafiya take sam hankalinta baya tare da ita,ta tafi duniyar tunanin shawarar da haulat ta bata,gani take anya kuwa zai hakura don a ganin da tayi mashi sau biyu tana ganin kaman ba zaiyi mutunci ba,ranar farko daya rabasu fada da jamila fuskarshi a murtuke take haka ranar da suka yi fada da murja daga magana bata ma idasa fadin abun da zata fadan ba ya gaura mata mari,tunanin hakan ne ke k'ara mata fargabar zuwa wurinshi,amman ba yadda zatayi dole taje kafin gobe tayi. Daidai shagon kawu Amadu ta tsaya tana jiran ya sallami wani yaro,kallonta yayi bayan yaron ya tafi,fatuu tace"sannu kawu" jinjina mata kai yayi ganinta sukuku yasa yace"har yanzu jikin?" girgiza masa kai tayi"da sauki sosae"ta fada a hankali,d'aura jakar islamiyyarta tayi saman kiosk din tace"kawu jakata zaka aje man,zan dan je gidan Hajia yanzu zan dawo"sanin ba kowa acikin gidansu yasa shi daga mata kai alamar toh,daga haka ta juya ta nufi gidan hajiyar sanata,kirjinta na bugawa damm damm tamkar ana mata luguden ta6are haka ta daure har ta karasa,ta karamar kopa dake a bude ta bi ta shige. _*Littafin A Sanadin Makwabtaka 300 ne,ga mai bukatar ci gaba da karanta shi bayan angama Free Pages sai ya tuntube ni ta wadannan numbers din 09016265659 ko 09013804524,pls just whatsapp message banda phone call,Thanks🤝* An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels