An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels [11/27, 7:15 PM] Masoyiya💖💖💖💖: ☘️☘️NAZLAH☘️☘️ *DAGA ALƘALAMIN* SALMAJI / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ *WANNAN LITTAFIN TUN DAGA FARKINSA HAR KARSHENSHI SADAUKARWA NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF) WANNAN LITTAFIN WAKE NA RUBUTASHI , ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI, YA KUMA KARA RUFA MIKI ASIRI DUNIYA DA LAHEERA..........* *WANNAN LITTAFIN NA KUƊI NE #200 NE KUƊINSA KI DAURE HAJIYA KI BIYA NAKI, DOMIN SHAN KARATUNKI CIKIN KWANCIYAR HANKALI......* *🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟* {R.S.W.A} https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c *_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_* _(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_ *Alk’alaminmu ‘yancinmu* *BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*( DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN KAI, YAH RAB YARDA NA FARA LITTAFIN NAN LAFIYA KASA NA KARESHI LAFIYA, ALFARMAR ANNABI DA AL-QUR'ANI) 3-4. """""""""""""""""Ba sai kin kara fada min komai ba, ai dama bakyason laifinsa duk ranar da baƙin cikinsa ko muguntarsa suka kasheki zaki gane mugun halayarsa",,ta fada tana taimaka mata, shi kuwa jin hayaniya ta kara yawa a kansa yasa yace "Wai ha haka ne, ke meyasa jaka ce, duk yarda na fada miko magana bakyaji, ko kullum kinfi son nayi ta dukanki sai kace jaka, kina cikin wannan halin ma ba zaki tausayawa kanki ba Mutswwww" ya ƙarasa fada yana jaan tsaki......... Haushi kamar zai kashe Iya,, cikin fusata tace "Uwar kace Jaka, kai dama ashe har yanzu halinka bai chanja ba, ina ga bayan shaye-shayen da kakeyi har da ciwon hauka ya kamaka", ta fada tana ɗankara mishi dakuwa........... sosa kanshi ya yi, tare da cewa, "Au wai da Iya ce", banza tayi dashi, ganin ya yi zaune yasa tace "Malam ka bamu guri dan Allah", sumi-sumi ya wuce daga ɗakin yana wani haɗa hanya, yanayin tafiyarsi kawai zaka kalla kasan shi din Dan shaye-shaye ne ma bugawa a jarida................ mayar da hankali Iya tayi akan Maryama da take ta uban nishi, ruwan rubutun da tazo dashi ta fasa ledar tare da sanya mata a baki, sha ta fara yi cikin fita hayyaci, bayan ta gama sha , ta shafe mata tun daga saman cikinta har ƙasan mararta da ruwab rubutun, cikin ƙanƙanin lokaci Naƙuda ta tahau gadan-,gadan cikin mintuna da bazasu wuce 20 ba Allah ya sauketa lafiya, tana haihuwa ta matsa daga kusa da Yarinyar da take tsanyara kuka ta kwanta tana sauke numfashi, wani bacci mai mugun nauyi ne ya yi Awan gaba da ita............. Gyara Yarinyar da take tsala kuka Iya tayi tare da ajiyeta gefe, kayan jinin ta fita dasu, sai da ta daura ruwan zafi akan katon murhun da yake tsakar gidan kafin ta ci gaba da wanke kayan da aka ɓata, lokacin da ta gama wankewa ruwan zafin ya yi zafi sosai, ɗiba tayi tare da shiga dashi ciki, kyakyawar jaririyar da take kwance idanunta kyarrr tana kallon sama ta dauka, tare da yin bissimillah ta fara dan shafo ruwa da hannunta ta goga mata, wani jalar kuka mai firgitarwa ta tsanyara, wanda yasa ita kanta Iyar sai da taji tsoro............. ganin babu abin da ya sameta, yasa taci gaba da mata wankan, tana dan murmushi, gani Yaringar Sak Uwata ta biyo komai, sai dai har tafi Uwarta fari, dan ita wannan fara ce mai sirkin jaa-jaa kalar dai fatar turawa............. bayan ta gama mata komai, ta Ajiyeta domin zuwa ta dauko wani kwalli da ta daka domin ringawa Jaririyar Amfani dashi, tana ajiyeta ta sanya kuka, ficewa tayi da sauri domin zuwa ɗakkowa, tana fita Lawan na shigowa, direct dakin ya nufa, in da yake jin kukan Yarinyar yake kallo sai dai bai ga Yarinyar ba, hakan yasa ya yi kan Maryama da take kwance tana baccin wahala, ƙafarshi yasa ya fara shurin hannunta tare da cewa "Ke! ke!! ke!!! ke ki tashi ki dauke wannan Aljanar Yar taki ", ya fada yana zama, dakyar ta mike ta nufi inda takejin kukan yarinyar .............. laluɓawa ta farayi har ta samu inda take, raɓata jikinta tayi, tuni tayi tsiit kamar wadda akace wa Mamarta ce ta dauketa, ba'a dau lokaci ba Iya ta dawo da tandun kwallin sanya mata tayi, tare da mikawa Lawan ita tace "kar ɓeta ka riketa zamu shiga wanka", tana daurata kan hannun Lawan ta fasa kara da kuka sosai, kallon Iyar ya yi tare da cewa "Iya kuka take,kuma ni wlh banason kukan Yara", harara ta dalla mishi tare da cewa "Nima ai haka nasha wahalar kukanka dan haka ka ɗana", ta fada tana jaan hannun Maryam , tsakar gidansu dake kwal-kwal a shere suka fito, kama hannunta Iya tayi suka shiga bandakin da yake fes shima yasha shara............. Wankan Runhu Iya tawa Maryama , ai kuwa kafih su fito har ruwan nono ya sauka sosai, har tana ji yana dan zubar mata, har kuma suka fito daga wankan Yarinyar nata tsala ihu iya karfinta.................. da kanta ta taka ta nufi cikin ɗakin, Tabar Iya waje, tana shiga yace "Ungo wannan Yar mai masifar kuka", jikinta har rawa yake takarɓeta, ɗiwawunta ta fara neman inda zata ɗosana, zama tayi kusa dashi kaɗan dan ba duka tama zauna ba, tsawa ya daka mata tare da cewa "sauka! sauka salon ki zubamin ƙazanta a saman gado, to wallahi har ki yaye na haramta miki hawanshi", da sauri ta zauna ƙasa, Iya ce ta shigo, ɗakin hannunta dauke da kaskon wuta rushi ringis a cikinshi jaajir, akiyewa tayi tare da komawa ta ɗauko faranti, ajiyewa tayi tare da cewa "ke baki da hsnkali ne kike zama ƙasa, daga haihuwarki yau, salon kije ki janyo mana wata matsalar", ta fada tana kallonta, dan murmushi tayi tare da cewa "ba komai a ƙasan fa Iya", shiru Iya tayi dan tasan ba kowa zai hanata hawa gadon ba sai Lawan.......... "to taho Maryama kici Abin ci", matsawa tayi gurin Iyar tayi, bde mata kwanon tuwan dawo da miyar kuka tayi, miyar taji haɗi ga ƙanshin man shanu na tashi sosai,kallon Iya Lawan Ya yi tare da cewa "Iya ni ina nawa ?" sakin baki tayi tana kallonshi, sai kuma tace " ni nace kaje ka buga chacha da kuɗin da zaka ci abin ci dan haka sai ka nema", shiru ya yi yana kallon tuwon da ba ƙaramin bi dashi ya yi ga.......... Haleeem da ya shigo dakin ta jawo jikinta tare sa fara bashi abincin yana ci yana shafa kan baby gal din da yake luluɓe da gashi baki siɗik mai yawa sosai, ganin komai normal yasa Iya mikewa ta tafi gida, tana fita ya diro daga kan gadon, anshe tuwon ya yi, tare da komawa gefe ya ci gaba da ci, ba tare da tunaniin sun koshi ba ko basu koshi ba ............... ganin gari na walkiya yasa ta mike ta fara shiryawa cikin kodaɗɗun kayanta, wata tsohuwar rigar Haleeem ta dauka ta sanyawa babyn tare da luluɓeta, shimfiɗa ta shiga yi musu a ƙasan sumintin cikin ɗakin, kafin ta gama Haleeem ya yu bacci gyara mishi kwanciya tayi tare da kwanciya itama, tana kwanciya ruwan sama mai karfi ya tsuge, ruwan aka fara mai karfin kamar zai ɗaye rufin kwanukan mutane ya tafi da su.............. luluɓe Haleeem tayi da kyau, tare da daura baby'n akan kirjinta ta luluɓe sosai, kasantuwar kayan jikinta ba wani na kirki bane yasa sanyin da akeyi take busu mata, sanyi ne ya kamata kyarma ta soma yi, gashi ɗakin babu ko abun rufewa balle ta rude, labulen kuwa irin boka-bokan nan ne, ba wani na kirki ba , kyarma jikinta yakeyi, Addu'o'i ta fara yi, tana riƙe da yarinyar a kirjinta, an dade sosai ana ruwan kafin ya fara tsagaitawa............. . Har suka kawo wani gida mai kyau wanda yaso fin wanchan gidan da suka baro kyau, amma bai daga kanshi ba ya kalli ko hanya, a haka har suka ƙaraso gida, shima gidan sojoji ne suke tsare dashi, sai da suka dai-daita parking a tsakiyar gidan, ficewa duk sukayi motar suka bude mishi, kafin suka tsaya suna sarawa motar, ya jima kafin ya zuro kyawawan fararen ƙafafunshi waje,cikin izza da taƙama, ya fito tare da nufar wata ƙofar glass , yana tsayawa kofar ta bude, wani ƙayataccen palo mai kyau ne ya bayyana, shiga ya yi, da Sallama , wata hamshaƙiyar Mace ce da taci wani dan ubansu lass, mai kyau kallo daya zaka mishi kasan cewa ba ƙananan kuɗi aka kashe ba gurin sinyanshi................. Amsa Sallamar tayi, tana murmushi, mikewa tayi tare da cewa "Sannu da zuwa Auta ", murmushi ya yi, tare da tsugunnawa har ƙasa ya gaisheta, amsawa tayi tare da cewa "nasan bakayi break ba kaje kayi kafin mu tafi", girgiza kanshi ya yi, tare da cewa "Na koshi", kallon tuhuma ta mishi, ganin ya ɗukar da kanshi alamar bayason ta kara mishi wata magana, yasa ta mike tare da daukar mayafinta da jakarta dake kusa da ita tare da cewa "Haleesa ki fito mu tafi, muje", mikewa ya yi, yana gaba tana bayanshi, har suka ƙarasa gurin mota, shi da kanshi ya bude mata mota ta shiga kafin shima ya zagaya, bude mishi akayi ya shiga driver yaja motar Escort dinau na bayansu da gabansu........... tunda suka shiga motar babu wanda ya yi, magana dan shi lumshe idanunshi ma ya yi, yana saurarar karatun Al-qur'anin da yake tashi cikin motar, a haka suke tafiyar cikin kwanciyar hankali.............. kusan 3 hours suna tafiya kafin su karaso, wani gari mai suna Lambar Ƙunci, tafiya suka ci gaba dayi har suka karaso Shuwaki, shigarsu cikin garin yasa suka fara yin slow down da motar dan sun iso cikim garin da zasuzo, tafiyar five minutes ce ta ƙaraso dasu ƙofar wani gida mai matsakaicin kyau, shi ba na talakawa ba shi kuma bana masu kuɗi chan ba................ Wani dan tsoho ne ya tashi yana cewa, "iyeee wa nake gani haka kamar mutanan Katsina", ya fada yana washe bakinshi, yar dariya suka yi Hajiya ce tace,"aikam dai Mune Kawu ya gidan", murmushi ya yi tare da cewa "lafiya lau kuwa, wa nake gani kamar Soja marmari daga nesa ", murmushi Hamid ya yi, dan shi bai fiye dariya ba sai dai murmushi," ah'ah wannan marmari ne daga kusa ", dariya duka sukayi, kafin su wuce ciki................. Suna shiga cikim gidan akayo musu chaaaa, Yaran ne suka rungume Hajiya suna cewa "Ga Yayah Hauwa! ga Yayah Hauwa" dariya tayi tare da cewa "Eyyi Yara sun girma kalli yarda Amina da Maryam suka wani zanƙale sukayi girma, har sunfi Haleesa girma"ta fada tana shafa kansu, dariya duk sukayi, suna boye fuska, Hannu Haleesa wata Yarinya wadda ba zata wuce sa'annin Haleesar ba tayi, murmushi Haleesa tayi tare da cewa "Aminannure", harararta tayi tare da cewa, "kar fa ki manta ni Mamarki ce", dariya duka aka kwashe da ita tare da cewa, "Eyyi ai sai fa Mama", tura baki Amina tayi tare da cewa, "nan gaba mai sai kin tɗringa gaisheni Yarinya", ana dariya aka shimfaɗa musu taburma, zama sukayi sai da suka zauna kafin matan gidan su Ukku su haɗa baki gurin cewa "Wai Yau Mai gidan ne yazo, tab lallai yau akwai cefane kenan" suka fada suna dariya......... "Ni ne fa Yau nazo naga Matana"Hamid ya fada yana murmushi, fira suka shiga yi, Haleesa kuwa tana chan ta shige cikin su Amina da Maryam suna ta fira........... Basu jima da shiga cikin gidan ba, aka fara shigowa da kayayyakin abin ci lemuka kwalayen biscuits da dai sauransu, murna Yaran suka shiga yi suna tsalle, sun jima sosai, kafin Hajiyar tace "Zamuje gidan Bava Balki amma kafin mu tafi zamu dawo", har ƙofar gida haka suka rakasu, mota suka shiga suka wuce, basuyi wata tafiya sosai ba suka ƙaraso gidan Ya'u Tela, cikin farin ciki suma suka karɓesu Baba Balki Kanwar Baban Hajiya sai Tsokanar Haleesa da Hamid takeyi,Mijinta da kishiyarta kuwa sai nan nan sukeyi dasu, suma haka aka dire musu kayan arziki sosai kafin su ce zasu tafi , Kallon Hajiya Baaba Balki tayi tare da cewa "Ni kam Hauwa'u yaushe zakije gurin su Rafan Habu ?" murmushi tayi tare da cewa "ai ban ma jima da zuwa ba sai bikin Yarinyar Yayah Hadiza zan koma", "to shi kenan ki gaishesu in kinje", jinjina kanta kawai tayi............ mikewa sukayi zasu fita, suna fita suka haɗu da wani katon mutum mai jiki sosai , sai dai ya manyata sosai, yana kan mashin gabanshi rungume da bangajin tsire, cike da murna ya tsaya dan yasan yau kakarshi ta yanke saƙa, gaisawa suka shiga yi , cike da jin kunya Hajiya tace "yanzu dama zamuje gidan ai yan gidan nanan ko ?", ta fada tana kallonshi, "E muje Kudidi nan kuwa, " "to shi kenan muje" Sallama sukayi da Baba balki tare da bin bayanshi zuwa gidan................ Yana gaba da Mashin dinshi suna biye dashi a baya, har suka karasa gidanshi da yake bakin titi, fitowa sukayi suka shiga cikin gidan, Kudidi ce ta fito cikin farin ciki tare da cewa "Yau Kishiyata Haleesa ce a gidan , lallai Yau muna da Babbar Baƙuwa ya baki fadamin zuwanki ba, na share miki ɗakin zaure", dariya Haleesa tayi tare da cewa "Waaaa ai ni mijinku yamin tsufa dal nakeso", ta fada tana wani yaryara hannu, irim na wasan jika da Kakanninta............... "Hakan zakiyi maleji Amaryarmu", taɓe baki tayi tare da cewa "Ah'ah kuyi ta kaya ke sa Hassu amma ni ina zan kai muku mijinku", dariya duk sukayi, dan Yarinya ce karama amma ta iya zaro zance................ "In da kowa yake kawai nan zaki kaishi", "uhmmm ayi ta kaya", dariya Kudidi tayi tare da cewa "ahhhhh to kaji fa Amaryar taka", murmushi ya yi, tare da cewa "kyaleta kawai tunda batayi, " Hamid ne yace "aiko da taci tsire, yarda take da mugun son nama karma mai kure", duk dariya akayi ita kuwa sai tura bakinta takeyi, sun dan jima gidan ma, sai da suka mishi sha tara ta arziki, kafin su fito, sako suka bada akai gidan Baba Mati suka wuce dan lokaci ya kure sosai ba zaiyiyu su biya tachan ba kafin su wuce.................... ************ Gidansu Jamseey Sadiyya ta nufa, hannayenta rike da basket, da Sallama ta shiga dan matsakaicin gidan nasu da bana masu kuɗi bane, ba kuma za'a kirashi na talakawa ba, dan gidan yana da dan kyau, fitowa Jamseey tayi daga wani daki da yasha labulaye masu kyau, murmushi tawa Sadiyyar tare da cewa "Sannu da zuwa Aminiya", " Yawwa Sannu Ƙawa", ta fada tana mata murmushi itama............ "ki shiga ki zauna bari na gaisar da Mommy nazo", ta fada tana wucewa, shiga tayi dakin tare da fadawa kan bed din da yasha gyara sosai kamar ba ɗakin budurwa ba, ɗakin Mamarta Jamseey ta shiga, zama tayi kusa da Mamar tata, kallonta tayi tare da cewa "Jamseey Baby yane ko Wannan Shashashar Kawar taki tazo", dariya tayi tare da cewa, "ai kema kinsan ajene, tunda sassafe zaki ganta", dariya Mommyn tayi tare da cewa, "ki ci gaba da daurata a layi tunda ita bata da wayau, ni yanzu abinda nakeso da ke, kiyi yarda zakiyi ki samu mijin nata a hannunki, so nake ta gane bata da wayau, dan sai kin shiga cikin gidan nan kin koya mata hankali tunda ita bata da wayau, yanzu tashi kije ki karɓomib abin da tazo dashi", ta fada tana naɗe ƙafafunta, dariya tayi tare da cewa "haka nakeso Maamana", ta fada tana mikewa ficewa tayi, tare da komawa ɗakin da ta baro Sadiyya a ciki, sai da ta kai wa Mommynta Abin cin kafin ta dawo su dasa sabuwar fira......... Bayan rana ta ɗaga Sadiyyar ta fito ta tayata aikin gida , sai da ta tayata yin aiyukan duka kafin ta koma ɗakin taci gaba da zaman Asara, tanayi tana chart, zama Jamseey tayi kusa da Sadiyya tare da cewa "Aminiya data nakeson ki turamin tawa ta kare", ta fada tana wani kwanciya kusa da ita, "okay bari na tura miki", ta fada tana fiddo wayarta, 5G ta tura mata, kallonta tayi tare da cewa "gaskiya wannan bazai isheni ba, inason na turawa Hayeem dan dazun ya kirani ya cemin bashi da data", "kai Ƙawata kina bautawa Saurayin nan naki da yawa ", haɗe rai Jamseeey tayi tare da cewa, "kin ga in ba zaki turamin ba karki cimin fuska", ta fada fuskarta na nuna zalar fushi.......... "Ke wasa nake miki bari na kara miki sai ki tura mishi", ta fada tana kara tura mata wata datar, "Eyyyy ta shigo bari na tura mishi", ta fada ko alamar godiya babu akan fuskarta, dariya Sadiyya tayi tare da cewa "to Uwayen Kauna ayi kauna lafiya ........... ~DAGA TASKAR SALMAJI / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️~ [11/27, 7:24 PM] Masoyiya💖💖💖💖: ☘️☘️NAZLAH☘️☘️ *DAGA ALƘALAMIN* SALMAJI / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ *WANNAN LITTAFIN TUN DAGA FARKO HAR KARSHE SADAUKARWA NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF), WANNAN LITTAFIN WAKE NA RUBUTASHI, ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI , ALLAH YA RUFA ASIRI DUNIYA DA LAHEERA* *WANNAN LITTAFIN NA KUƊI NE, #200 NE KUDINSA KI DAURE HAJIYA KI BIYA DAN SHAN KARATUNKI CIKIN KWANCIYAR HANKALI,KUMA YANZU NE ZAN KARA GANIN MASOYAN YAR LELE 🧚‍♀️🧚‍♀️, WANDA SUKE CEWA SU MASOYANA NE, TO KU NUNA NIN KAUNA TA HANYAR SIYAN WANNAN LITTAFIN NAWA, KAR KU MANTA #200 NE KAWAI* 1499884120 UMMASALMA SANI ACCESS BANK *🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟* {R.S.W.A} https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c *_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_* _(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_ *Alk’alaminmu ‘yancinmu* *BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* ( DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN KAI, YAH RAB YARDA NA FARA LITTAFIN NAN LAFIYA ALLAH KASA NA GAMA LAFIYA, ALBARKACIN ANNABI DA AL-QUR'ANI) 5-6. """"""""""""""""""Ta fada tana gyara Kwanciyarta", Shiru Jamseey tayi bata ce da ita komai ba, a taƙaice dai ranar a gidansu Sadiyya ta yini, gashi ko abin ci basu bata ba itama kuma bata damu ba, sai dai aiki wannan Yaron siyan Maƙulashe ta aiki wannam haka ta ri gayi har rana ta faɗi, kallonta Jamseey tayi tare da cewa "Aminiya tashi nu tafi gidanki", kamar raƙumi da akala haka ta bita zarai-zarai har gidan nata, palon tsaf-tsaf mai aiki ta gyara ko ina tar, bedroom dinta sula wuce, anan naga zalar ƙazanta komai a harmutse babu gyara, zama sukayi kan bed din, jona wayarta tayi a charge tare da mikewa, gurin da take ajiye tsintsiya ta nufa, zata dauka ta tattare ɗakin.............. Kallonta Jamseey tayi tare da cewa "mai zakiyi da tsintsiya haka ?" , kai tsaye ta bata amsa da " tattare ɗakin zanyi naga ya yi kura da yawa", cikin zuciyarta tace anzo gurin, kallonta tayi tare da cewa "shara kuma yanzu ɗakin nan mai ya yi haka ?", yatsina fuska tayi tare da cewa "sai naga kamar ya yi datti" zare ido Jamseey tayi tare da cewa, "anya kuwa baki makance ba ina dattin ni banga wani datti ba sai dai idan idanunki ne suke nuna miki, to nan mai ɓa zaki share, ko da yake share", ta fada tana kallonta................ "Ah'ah barshi kawai dama ɗakin ne naga kamar Ya yi kura shi yasa amma barshi kawai dan ni kaina nauyin jikina nakeji ", ta fada tana fadawa kan bed din, wani kill smile Jamseey ta saki tare da cewa "da kuwa kon hutawa kanki," ta fada tana latsa wayarta............ chan kuma ta ɗago tare da cewa, "Aminiya Yunwa nakeji", kallonta tayi tare da cewa, "to kije kitchen ki girka abinda kikeso mana",,ta fada tana mayar da hankalinta kan wayar hannunta da ta gama bawa amanar kanta............... Mikewa tayi ta nufi hanyar barin bedroom din, tana fita kitchen ta nufa, tana zuwa ta bude store kayayyakin abin ci ta fiba, sai da ta ɗibi komai kafin ta bude kofar baya ta cikin kitchen din ta zura kayan waje, Indomie shidda ta ɓare ta zuba a cikin tukunyar da take tausa, cikin minutes kaɗan ta gama ta juyo cikin tray tsayawa nayi ina kallonta ganin ta fito dashi ta ajiye a tsakiyar palo ta wani dai-daita zama.................. fitowa Sadiyya tayi, zama tayo lan kujera duk da taga uwar Indomien da kwan da Jamseey ta dafa amma bata ko daga kai ba, ci ta farayi, sai da tayi naƙ kafin ta juye sauran a leda ta ce, "ni fa zan tafi muyi chart dan naga haɗari na haduwa, "okay to shi kenan Ƙawa bari na rakaki ko bakin get ne", girgiza kanta tayi tare da cewa , "ah 'ah ba sai kin rakani ba kiyi zamanki", jin hakan yasa ta koma ta zauna, ficewa Jamseeyn tayi da sauri,,sai da ta zagaya ta dauki abin da ta fitar kafin ta wuce gida abinta................ tana fita da wasu yan mintuna, sai ga jiniyar motarsu Hamid mikewa Sadiyya tayi daga in da take, yana bude kofar ta nufi in da yake, mamaki ne ya cikashi na ganinta da kaya da ya fita ya barta dasu,sanan palon kacha-kacha da alama bata gyara komai, fadawa jikinshi tayi tare da cewa "Welcome back My Solder", wani ƙarin rana ne ya daki hancinshi, numfashinshi ne ya tsaya chak na tsawon lokaci kafin ya ci gaba da aiki, da sauri ya matsa da ita daga jikinshi ya wuce sama............... da sauri ta dauki wayarta, ganin Jamseey ta turo mata sako yasa ta bude voice note din sai da ta gama saurara ta mayar mata da amsa kafin tace, "ban fada miki ba My Solder ya dawo yanzu, mai kike ganin ya kamata nayi", dariyar kyeta Jamseey ta saki, kafin ta fara cewa, "to yanzu abun da zakiyi, kice kiyi wanka ki shirya, sai kije bedroom dinshi" mikewa tayi ta shiga bedroom dinta, wankan tayi ta shirya tare da cewa, "to na gama gani zanje bedroom din nashi", ta fada tama tura kofar shiga, ko da ta shiga baya ciki,hakan yasa ta zauna kan bed tare da cewa "gani nazo ma baya cikin bedroom din da alama wanka yake", murmushi ta kara saki tare da cewa, "to in ya fito ki tarɓeshi da salo, ki kwantar dashi ki mishi tausa, sannan ki ringa shafashi sai ya hau network ki gudu dan banason ki bashi sai kin wainashi, yarda zai fi rikeki da daraja" dariya Sadiyya tayi tare da cewa "gaskiya ne Ƙawata nagode da shawararki",,tana gama voice note din Hamid na fitowa daga wankan da ya shiga................ da sauri ta mike ta taroshi, mamaki ne ya kamashi sai dai da yake shiɗin Namijim duniya ne bai yarda ta gane mamakinshi ba ko kaɗan,tsane mishi ruwan jikinshi ta shiga yi, bayan ta gama ta shafa mishi lotion vest da boxer ta bashi ya sanya, kallonshi tayi tare da cewa "nasan ka gaji kwanta na maka tausa", ta fada tana kashe mishi ido, ba musu ya kwanta tare da ringinginawa, hannunta ta daura kan tattausar fatar jikinshi ta fara tausa mish a hankali, cikin minutes kadan yanayi ya chanja gaba daya ya fita a hayyacinshi, tana ganin haka ta,zame jikimta tare da ficewa da gudu, ta datse bedroom din ................ rasa yarda zaiyi ya yi, hakan yasa ya shiga bathroom ya sakarwa kanshi ruwan sanyi mai sanyi, hakan kuma ya yi dai-dai da saukar ruwan sama mai karfin gaske, wanda gaba daya ya kara dagula mishi lissafinshi................ ********** Asubar fari Jaririya ta fara tsanyara kuka, mai matuƙar sauti, da firgitarwa, sai kace wadda ake yankar naman jikinta haka take kukan da ihu , kukan da takeyi kuma shine ya yi sanadiyar tashin Lawan daga bacci,cikin ruwan masifa ya fara kiran "Maryama! Maryama!! Maryama Wallahi ki tashi ki dauki Yarinyar nan ku fita a ɗakin nan in ba haka ba,zanyi ball daku ke da ita,haba wannan wace iriyar masifa ce, kinzo kawai kin haifar wa mutane Yarinya mai masifar kuka, ki tashi ki dauketa nace ko", ya fada yana shurin hannunta, a firgice itama ta farka tare da daukar Babyn ta sanyata a jikinta tana rirrigawa.............. tsawa ya daka mata tare da cewa"tashi ki fice ki bat ɗakinan nan da yarinyar nan , kafin na ɓaɓɓalaku ke da ita", a hankali ta mike ta fita da Babyn a hannunta, gefe chan ta samu ta zauna, tare da fara feeding din Yarinyar, dan-danan kakejin Yarinya tayi shiru, sai da ta ƙoshi kafin ta kona cikin ɗakin jikinta na karkarwa kasantuwar har lokacin lemar da aka kwana da ita na ruwa bai tsane ba, kwantar da Yarinya tayu tare da kwanciya itama, bacci ne ya kara daukarta................... tun 7 Iya tazo ta daura musu ruwan wanka, wannan karon Maryama da kanta tayi wankan Babyn kawai Iya tawa wanka, Maryama na fitowa ta Umarci Haleeem maza yaje ya yi, baya ta gama shiryawa ta fito tare da fara tsaftace tsakar gidan da shara ta fara kafin ta haɗa yan kwanikan wanke-wankensu ta haɗu kunfa wankewa ta shiga yi, sai da ta gama fes ta kikkife, kafin ta fara kiciniyar haɗa wuta, Iya ce ta shigo, zare ido tayi tare da cewa ",duk wa ya yi wannan aikin haka ?", kafin Maryama tayi magana Haleem yace "Umma na ce Iya", zare idanu ta karayi tare da cewa......... "Maryama aiki har haka, tashi kije ki huta bari na haɗa wutar", ta fada tana ƙarasowa, girgiza kanta tayi tare da cewa "ah'ah Iya bari nayi ai tama kusa haɗuwa",ta fada tana mata murmushi, shiru Iya tayi har Maryama ta haɗa wuta, kallonta tayi tare da cewa "to akwai abun Sarrafawa ne ko kuwa", "akwai Iya", da sauri Haleeem yace "Ummu babu fa, kece kika ce karya babu kyau, wanda ya yi ana ƙonashi a wuta" ya fada yana rike baki, shiru Maryama tayi, kallonta Iya tayi tare da cewa "mai yasa ba zaki faɗamin ba", kamar ba,zatayi magana ba sai kuma tace, "nayi tunanin kafin na gama hura wutar zai kawo abinda za'a sarrafa ne", "kema kinsan indai Lawan ne bazai kawo ba, bada ban kar na mishi baki ya ƙara lalacewa ba , na sai na mishi," da sauri tace "kiyi hakuri Iya dan Allah kar ki misi baki, danbin kika mishi ba'asan yarda abun zai kara komawa ba, kiyi tayi misho addu'ah insha Allahu zai daina", ta fada,tana mayar da kwallar idanunta................. ficewa Iya tayi tana jinjina wa halayya irin ta Maryama , dan ita ko bata da abu bazata taɓa fada tace babu ba, kuna duj irin ƙuntatawar da Lawan yake mata bata fadawa kowa sai dai ta shanye, amma da yake shi din ba dan goyo da tari bane , ko gaban mutane sai ya duketa ko zagi, Iya kanta da take Mahaifiyar Lawan tana Alah tur da halayarshi, amma ita ba zata tama budar baki tace kaza ba, ko ya mata sai dai tayi Murmushi, kuma ko zaka kasheta ba zaata fadi sirrinsu ba ita da Mijinta............... hakan kuwa yasa take mugun shan wuya gurin Lawan din, garin kunu ta kawo musu, ƙadan ta ɗiba ta dama, zubawa Haleeem tayi, yana gama sha ya fice makaranta, zubawa Iya tayi tare da dibar dan kaɗan ta sha, tana gama sha Lawan ya shigo, ko sallama babu ya wuce ɗaki................ kunun ta dauka sauran wanda ya rage, ta shiga dashi ciki, ɗurkusawa tayi har ƙasa tare da cewa, "Mai gida ga kunu", mikewa ya yi, tare da daukar kofin, bude kunun ya yi, kallonta ya yi tare da cewa "Dan wannan kunun", dukar da kanta tayo ƙasa dan in yana guri ko ɗaga kanta bata iya yi............... a bakinshi ya kafa kofin, da sauri ya cire bakinshi tare da furzo na bakinshi akan fuskarta, da sauri ta dan daga kanta, masifa ya fara mata akan ta bashi kunu ba sugar, "dan iskanci sai ki bani kunu ba sugar, dan kawai salon rainin wayau, yar iskar banza to wallahi zaki gane kurenki", ya fada yana zare belt din jikinshi............... ganin haka yasa da sauri ta kwznce Yarinyar da take bayanta ta matsar da ita chan gefe, tsula mata belt din Lawan ya shiga yi, duk da da zafi amma ko uhummm bata de ba saboda biyyaya, kuka jaririya ta fashe dashi, tana ɗaga kafafunta........ kukan ta shiga yi sosai, tsagaitawz ya yi da dukanta tare da cewa "Dauke min wannan shegiyar Ɗiyar kafin na bugeta a gurin nan"da sauri ta dauki Yarinyar ta fice da ita, jikinta ya yi ruɗu-ruɗu , da shaidar belt, rirriga Yarinyar ta shigayi.............. Haka suka ci gaba da kasancewa har satin da ta haihu ya zagoyo, sai dai babu huɗuba, dan Lawan ki kallon Yarinyar bai taɓa yi ba balle har ya dauketa ya sanya mata wani Suna, ranar Iya na tambayar Haleeem ya fada mata, da sauri ta tafi da Yayah Lawan wanda suke Uba daya, karɓar Jaririyar tayi tare da cewa "yi mata Huɗuba", karbar Yar ya yi, Addu'ah ya mata tare da cewa "Wani suna za'a sanya mata?", da sauri Haleem da yake gefe yace " *Nazlah* Kawu ?", kallon Iya ya yi, jinjina mishi kai tayi, hakan yasa ya raɗa mata sunan............ har maraice Lawan bai kawo Ragon Haƙiƙa ba, hakan yasa Iya daukar dan Bunsurunta ta bada aka yankawa *Nazlah* , ba wani taro dan Lawan baya barinta fita ko nan da chan hakan yasa, babu wanda ya zo mata , sai Yan uwa.................. soye naman akayi aka ɗibar wa duk wanda ya kamata, sauran aka bawa Maryama, janta Iya tayi tare da cewa "Maryama kar ki sake ki bawa Lawan naman nan, in yazo ma kice ba'a yanka komai ba, tunda shi bashi da mutunci", jinjina kanta tayi.......... bayan fitar Iya sai gashi yazo, kallon Maryamar ya yu tare da cewa "Ke ina naman da aka soya" , daukoshi tayi gaba daya tare da ajiyewa a gabanshi kanta a ƙasa tsinta ya fara yi sai da ya gama kafin, kalleta cikin muryarshi yace "Ga sauran nan ki ajiyemin ko hanji daya kika ci ban yafe ba",,ya fada yana ficewa............... Naman da ya,zama haramiyarsu kenan ita da Haleem da ko yanka daya bai ci ba sai dai tayi ta bashi haƙuri, haka har kwanaki suka dan fara haurawa komai Iya take musu................. Sai dai kullum Lawan sai ya ta zagin Maryama har makwabta baji saboda kukan *Nazlah* dan gaba daya bata bacci da daddare sai kuka, hakan yasa gaba daya rayuwar Lawan yaji babu abun da ya tsana a duniya sama da *NAZLAH*........... hakan yasa Yarinya ta tashi cikin tsana da tsangwamar Mahaifi, bata da ƙatabus a fabanshi, tun tana Yar wata biyar, yake dukanta in tana kuka, a haka har Nazlah ta fara girma , tana da wata 10 gona cif ta fara tafiya, a lokacin kuma sai Allah ya daura mata kwaɗayi na masifa............ ba damar taga bakin mutum na motsi ta ringa mika mishi hannu kenan nata bakin shima yana motsi, tun suna dauka zata daina har Yarinya ta fara magana bata buɗi baki da konai ba sai "Yanman", hakan yasa Ummu bata fita da ita sai dai ta barta gurin Iya in zata fito......... wata rana, Lawan ya shigo da ledarshi cikin gida, tun da ya shigo idanun Nazlah nakan ledar nan har ya nemi guri ya zauna, mikewa tayi ta nufi gurin da yake dan nesa kaɗan ta zauna, indomie ya bude cikin ledar sai turiribtake da zafinta, ƙamshin Indomien ce ta daki hancin Nazlah wani mugun miyau ta haɗiye Kuttt tana kallon ledar, Lawan na lura da ita, daga ledar ya yi, sama da kallo ta kara bin ledae tana leqe tare da haɗiyar yawu............... mikewa tayi ya nufeshi, tsna zuwa gurinshi ta mika mishi hannu tare da cewa "Yanman",,ta fada tana kara mika mishi hannun,kallom tsana ya watsa mata tare da daukar garwashin wutar da take kusa dashi tare da daura mata a hannunwanta, ya rumtse mata hannunwan sosai yarda ba zata iya zubarwa ba.............. A zabar da ta ratsata ce tasa , ta saki kuka da azabar karfi , har cikin zuciyar Maryama sai dai tasan dama dole hakan zata faru tun da taga Lawan ya shigo da leda sai dai batayi zaton zai iya ƙonata ba............. sai da fatar hannunta fa fara salewa sosai kafin ya saki hannin izuwz lokacin kuwa kukanta ma baya fitowa da kyau........... ********* dakyar da siɗin goshi Hamid ya samu natsuwa, wanka ya yi tare da fitowa daga bathroom din, kwanciya ya yi ko abinci bai nema ba, haka ya kwanta coke da tunanuka sosai cikin ranshi.......... washe gari ma unguwa ya sake zuwa , kamar jiya Yau ma a gidansu Jamseey ta yini sosai, sai Yamma ta dawo, ko da ya dawon yau ba laifi kayan palon tsaf , nashi kuwa dama babu wani datti kuma kullum sai an gyara mishi............... Shawararta ta nema akan zai tafi da ita partcourt gurin aikinshi kasantuwarshi na Sojan ruwa (NAVY) sai da ta fadawa Jamseey kin amincewa tayi da tafiyar tata, hakan ya tace mishi ita ba zataje ba, jin hakan yasa ya ci gaba da shirin tafiyarshi.......... kwana biyu tsakani ya yi chanewarshi Part court, nima kuma sai na tsaya anan sai kuma mun kara haɗuwa a page din gaba........... *karfa ku manta Nazlah na kuɗi ne #200 ne kuɗinsa , ki biya ki karanta cikin jin dadi da annashuwa🥰* wannan shine account details din. 1499884120 Ummasalma Sani. Access bank. sai ki turamin da shaidar biyanki tanan.... 07033371851 ~DAGA TASKAR SALMAJI / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️~ [11/27, 7:24 PM] Masoyiya💖💖💖💖: ☘️☘️NAZLAH☘️☘️ *DAGA ALƘALAMIN* SALMAJI / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ *WANNAN LITTAFIN DAGA FARKONSHI HAR ƘARSHENSHI, SADAUKARWA NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF), WANNAN LITTAFIN WAKE NA RUBUTASHI, KIYI YARDA KIKESO DASHI, ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI, YA KUMA KARA RUFA MIKI ASIRI, DUNIYA DA LAHEERA* *🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟* {R.S.W.A} https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c *_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_* _(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_ *Alk’alaminmu ‘yancinmu* *BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* (DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN ƘAI,YAH RAB YARDA NA FARA LITTAFIN NAN LAFIYA, ALLAH KASA NA KARESHI LAFIYA, ALFARMAR ANNABI DA AL-QUR'ANI) *PAGE 1-2* Tafe nake cikin wata Unguwa mai suna Barhim Wanda Unguwar Qauters ce,hakan yasa Unguwar bata da wata hayani ko ina tsiiit kasantuwarta na Unguwar masu kuɗi, duk in da zaka jiyo sauti to sautin karene, cikin natsuwata nake tafiya, har na ƙaraso gurin wani katafaran gida mai kyau da fasali, hayani yaji, hakan yasa na karasa jikin gidan, tura kofar nayi, jin babu wani abunda ya tokare kofar alamar gidan ba kulle yake ba yasa na tura na shiga, kofar palon da na gani bude na tunkara gadan-gadan, hayaniya najiyo hakan yasa na dan kara tsawon tafiyata,......... . ina shiga naji ana burutun, da gudu duf-duf-duf, da sauri nabi inda nakejin sautin gudun,saman benen gidan na hau, kai tsaye dakin na nufa , cikin daga sauti naji tana cewa "Wallahi Hamid baka isa ka kusance ni ba, sai ka bani kuɗin da na fada maka, in ba haka ba kuwa sai dai kayi hakuri da buƙatar ka", ta fada tana tulla mishi harara................ Dara-daran idanunwanshi farare tas-tas masu kyan fasali da girma, ya kara buɗewa tare da cewa "yanzu ke Sadiyya dan zan anshi haƙƙina shine zaki ce sai na biyaki kuɗi, mai yasa ke kwata-kwata baki da tsoron Allah, Sadaki fa na biya aka Auramin ke bawai zaman Dadiro mukeyi da ke ba da zakice sai na biya kuɗi zan kusanceki," ya fada yana kara daura mata rinannun idanunshi akan fuskarta............. Jijjiga jikinta tayi, tare da cewa "Ai Wallahi bari na fada maka ka gama kusantata ba tare da ka biya kuɗi ba, kama daina yimin wani wa'azi domin tanan yake shiga yana fita tanan", ta fada tana nuna kunnuwanta............. Mararshi da take mishi Azababban ciwon ya dafe, tare da cewa "yanzu haka kika zaɓarwa kanki, tunda hakane, nawa kike bukata yanzun ?", ya fada idanunshi na tara hawaye ............... Wani murnushi ta saki tare da cewa, "Nairah Dubu dari biyar kachal nake bukata", ta fada tana wani ƙas-ƙas da Chewing-gum din da yake bakinta, wayarshi ya dauka, ya fara latsawa kallonshi ya yi tare da cewa "Na tura miki", yatsina fuska tayu tare da cewa "Ni banji Alert ba", ta fada tana tura dan kwalinta gaban goshinta................ "Ai kinsan bazance na tura miki ba Alhalin ban tura ba", ya fada ranshi na dan ɓaci, ƙas tayi tare da cewa "na sani ko karya zaka fara min", ta fada tana wani yatsina, a harzuƙe ya mike ya nufota, ganin ya nufota gadan-gadan yasa ta zura da gudu ta fita a bedroom din, wani bedroom na kusa da wannan ta shige tare da sanya key, dukan kofar ya farayi, muryarshi a dishe yake cewa "ki sani zaki kwana a cikin fushin Allah da Mala'ikunsa, kin hanani Haƙƙina sai da na baki kuɗi, na baki kuɗin kuma zaki gujeni, ki sani haƙƙina bazai barki ba, ki bude Sadiyya, ko kinfi son naje na fadawa halaka", ya fada yana kara dukan ƙofar......... Daga chan cikin ɗakin taɓe baki tayi tare da cewa "Sai fa kayi ta yi, dan Wallahi bazan bude ba, kuma kuɗi ma yanzu na fara ƙarɓa", ta fada tana daukar wayarta, latsawa ta fara yi, tana ji yana dukan kofar amma tayi burus dashi............... Sai da ya gaji da dukan Kofar , kafin ya koma bedroom din da ya fito, yana jaan ƙafafunshi, yana shiga mata kofa ya nufa, budewa ya yi, haɗaɗan bathroom ne ya bayyana, fadawa ciki ya yi, tare da sakarwa kanshi ruwan sanyi, dukan kashin ruwan ya ci gaba dayi, yana tsaye ko motsi baiyi ba, ya dade sosai a haka,kafin ya fito jikinshi na ɗigar da ruwa, bai damu da ya goge ruwan ba, ya fada kan gado, yana sauke wani numfashi mai zafin gaske, cike da ƙunar rai.................. Dayan Ɗakin kuwa, gyara kwanciyarta tayi, jin ya daina buga kofar yasa, tayi kiran waya minutes kaɗan aka dauka, shewa tayi tare da cewa "Ahaayeeeee Naanaye, "murmushi akayi daga chan kafin wata muryar daban ta dakin dodon kunnena, cikin dariya tace "Duniya taki Kawata bani nasha yau kuma da wace kikazo", ta fada cikin sigar Ƙawaye masu kai mutum ga halaka................. dariya tayi tare da cewa, "Ahhaf in da nake sonki kennan , ke da na kiraki kinsan da wata siga nazo miki da ita", "Uhmmm ai sai dai na fadawa wani halinki amma badai a fada min ba, yanzu dai bani nasha" ,,dariya ta kara saki tare da cewa "ai ban baki labari ba yanzun nan mutuminki ya turamin #5000k kuma na gudu na kyaleshi da abunshi, ai daga yanzu na gama yarda ya kusance ni sai ya bani cash, cash dib ma in naga dama ko ya bani na gudu", ta fada tana wani juya kwanciya daga in da take............... Dariya ta sheƙe da ita tare da cewa "Kai wannan abun yamin Suga, kici gaba da gasa mishi aya a hannu, bamce ki bashi ba sai kin gama lale dan Iska, ke ko dattin Aljihu bance ki barshi dashi ba",ta fada cikin maganar mata yan duniya,wanda suka san takan tsiya, dariya tayi tare da cewa "ai dadina dake kina da man kai, yo dama ta ina zan yarda ai ko zan yarda sai na tabbatar da ba samu rabona", haka suka ci gaba da surutansu wanda basu da kai balle gindi, sai shawarwarin banza take bata, ita kuwa sai dariya take tana kara hawa kan motar ƙaiƙai................. Cikin mugun yanayin nan ya kwana, yana murkususu, sai yanzu yake nadamar Auren Sadiyya da ya yi, gashi bata mishi komai,,ko bakutarshi in yazo da ita bata sauke mishi, gashi a rayuwarshi bashi da tsarin yin Aure-Aure balle saki............... *WASHE GARI* Tun Asuba bai koma bacci ba, dan yana dawowa daga Masallaci gurin motsa jiki ya nufa, motsa jikinshi ya fara yi, kusan 2 hours yana abu daya, kafin ya nufi cikin gidan tana share zufar da take yanko mishi, zaune ya tarar da ita a palo, ta chaɓa Ado cikin wani tsantsareran lass mai kyan gaske, ba wata babba bace dan ba zata wuce 19 to 20 years ba, ba laifi tana da dan kyanta dai-dai gargwado............... kallonshi nayi shima din dai ba zai wuce 27 to 28 ba sai dai yana da garin jiki sosai, dan in ba fada maka akayi ba bazaka taɓa dauka Asalin shekarunshi ba kennan, saboda yana da babban jiki, yana da tsawo sosai gashi da ƙiba sai dai ba irin ƙiba ba sosai dai-dai misali dan ba za'a kirashi mai ƙiba sosai ba sannan ba za'a kirashi ramamme ba, tsaka tsakiya ne, sai dai Allah ya zuba kyau ,dan kallo daya zaka mishi kasan cewa shi cikakken Bafulatani ne, dan fari ne tas yana da matsakaicin baki mai dauke da ƙananan lips masu dan kauri kaɗan , dogon hancinshi har baka, idanunshi dara-dara fsrare tar sai golden Eyes ball da yake da shi, gashin girarshi da na idanunshi gazar-gazar gwanin kyau , Fatabaraqallahu Ahsanun qalikin ,Masha Allah , na furta dan ya haɗu iya haduwa yakai karshe a gurin kyau.............. yana karasowa cikin palon tace "Good morning My Solder", ta fada tana dan mishi murmushi, wani kill smile ya saki tare da cewa "Morning how are you ?", "Alhamdulillah", jinjina kanshi ya yi tare da cewa "Good", yana fadar haka ya hayewarshi sama............... Tana mugun Mamaki da shi duk abinda zata mishi vaya yin fushi, ko ya yi ina saurin saukowa da wuri, wayarta ta dauka da sauri ta danna kira , ring biyu aka dauka , daga chan ɓangaten aka ce "Ya akayi ne Ƙawata", dariya tayi tare da cewa, da dauri ta dakatar da ita tare da cewa "Yanzu My Solder ya dawo daga motsa jiki", dariya tayi tare da cewa, "ya akayi kikasan haka zan fada ?",,dariya tayi tare da cewa "Sharw kawai yanzu ya akayi, mai kika girka na aiko na Ansa",,dariya tayi tare da cewa, "Wallahi Doya da kwai kawai ba soya, ganinan ma zuwa gidan baasai kin aiko ba", ta fada tana kike................ Mayafinta kawai taja , sai da ta shiga kitchen ta haɗo kan komai kafin ta fice , abunta dan ko tambayarshi batayi ba........... Yana shiga Wanka ya fads bathroom ya yi, yana fitowa yaji wayarshi na ringa, da sauri ya matsa gurin Wayar *Hajiya* ya gani rubuce akan screen din wayarshi, kashe kiran ya yi, tare da kira back, sai da ya ɗuƙar da kanshi Ƙasa kafin yace "Ina Kwana Hajiyata" murmushi tayi tare da cewa, "Alhamdulillahi Auta , wai nace kayi sauri kar dare ya mana a hanya, dan kasan bana son dare a hanya ko kaɗan", ta fada cikin so da kaunar Ɗan nata............... Jinjina kanshi ya yi tare da cewa "To insha Allahu Hajiyata ganinan a hanya", "To sai kazo", suna fadar hakan ya kashe wayar, cikim sauri-sauri ya shirya cikin Shadda mai kyau sai maiko take taji aikin surfani wanda kana kallonshi zakasan kuɗi ya yi kuka gurin aikin , takalminshi da Agogonshi Gucci sai bakar Zanna da ya kafa a kanshi,baƙin gashin kanshi da ya kwanto bayan wayanshi, ya yi kyau sosai, turaruka ya fara fesawa sai da ya yi wanka dasu kafin, ya fara takawa cikin takun isa ya fito daga bedroom din, dayan bedroom din ya leqa tun da ya ga wayam yasan ta fice, gefen bed ya karasa raper na 1k ya ajiye mata kan bed din tare da fice abinshi........ Rantsatsiyar Motarshi mai kyau da tsari ya nufa, sai yanzu ma ni naga Sojojin da suke shawagi a gidan da Alama ma sune masu gadin gidan, nayi mamaki sosai dan lokacin da na shigo jiya banga wannan tulin mutanan ba, suna ganinshi suka fara sara mishi, wasu ukku ne suka rugo da gudu suja bude mishi bayan mota, daya ne ya shiga cikin motar, sauran kuwa suka shiga cikin wasu motoci guda biyu suka mara mishi ba, tsula gudu suke kan hanyar , duk wanda ya gansu gefe yake dan yau manya ne akan hanyar da jiniyarsu suke tafiya............. ************** Wani daki na shiga da babu wani haske sosai cikin ɗaki, ina shiga na hangi Wata mata Durƙushi take akan guyayinta, tana jujjuya kai ga wata uwar zufa da take karyo mata, sai kace wadda ta haɗiyi kunama, murkususu take tana cije lips dinta, a hankali ta fara nishi mai sauti irin na wanda yake cikin fitar hayyaci, ta dade sosai tana cikin wannan halin, a hankali ta fara rarrafe har ta isa gadon bononta da yake cikin ɗakin.............. A hankali ta fara dan dukan gadon, tana nishi, a hankali ta fara furta "Mai gida! Mai gida!! Mai gida!!!", ta fada tana daura kanta jikin gadon bonon , wani wawan tsaki akaja kafin wata murya ta daki dodon kunnena, cikin faɗa yace "so nawa zan fada miki in ina bacci ki daina tashina mai yasa ke gaba daya, bakya da tunani ne, kamar Dabba haka kike Al-amuranki , Wai ya akayi ne ma," ya fada cikin fada-fada.............. Hawayen da suke maƙale a idanunta ne suka zubo, cikin rawar murya tace "Dan Allah kayi hakuri", tsaki ya kara jaa tare da cewa "to! da hakurin ya mutu Sadakar nawa kika bada Ke! Maryam Wallahi ki kiyaye ni, dan zanyi mugun saɓa miki Shashasha kawai", cije lips dinta tayi tare da cewa, "dan Allah ka taimakamin ina jin naƙuda ce nake", dariya ya sheƙe da ita tare da cewa "Au haba naƙudar ce, Uhmmmm lokacin da kikazo kikaji dadin ki wa ya hanaki , sai yanzu ne kike cewa kina wata naƙuda, to ki haife mutanen duniya ma mana ni ina ruwa, dan haka karki kara tashina ko kuma Wallahi ki gane kuranki ", ya fada yana juyawa............... rasa yarda zatayi tayi, ga wani azababban ciwon baya da na mara da ƙafafu da ya sauko mata gaba daya, a hankali take rarrafawa har ta isa bakin kofar ɗakinta da ko siminti bata samu arzikinshi ba, kanta ta leqa tare da cewa "Haleem! Haleem!! Haleem!!!", ta fada cikin rashin fitar murya............ Wani Yaro da bazai wuce Shekara 9 zuwa 11 ba ya fito daga wani ɗaki da gudu tare da cewa, "Ummu gani", rike hannunshi tayi tana sauke numfarfashi tace , "Haleeem jeka ka kiramin Iya yi sauri", ta fada tana dafe mararta, "Ummu baki da lafiya ne ?", ya fada cikin muryar tsoro, jnjina kanta tayi , tare da cewa "yi sauri kaje", ta fada tana sakin hannunshi.............. da gudu ya fita daga gidan, minutes kaɗan sai gashi sun shigo da wata Yar Tsohuwar mata sai dai ba tsohuwa bace chan ta dai manyanta, da sauri ta karasa gareta, tare da dafa kanta da tan jinginar a jikin ginin ɗakin tana hawaye ga wani kyarma da jikinta yakeyi, naman jikinta har wani rawa-rawa yake, cikin tausayawa tace "Maryama! Maryama Assha naƙudar ce, sannu tashi mu shiga ciki", ta fada tana riketa, dakyar ta yunƙura, da taimakon Iya suka shiga cikin ɗakin.................. tsakiyar dakin suka tsaya, kallon kan gadon da Lawan ke kwance tayi, cikin fada tace "Kai Amma Lawan anyi ɗan iskan Yaro ashe dama haka kake, yanzu matarka tana naƙuda amma kana nan kwance, amma kayi Asara wallahi, k......" dafata tayi tare da cewa "Iya bai sani bane, kuma...", ɗaga mata hannu tayi tare da cewa ".............. *Wannan littafin na kuɗi ne #200 ne kuɗinshi, ki daure ki biya kisha karatunki cikin kwanciyar hankali* ~DAGA TASKAR SALMAJI / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE~🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ [11/27, 10:42 PM] Sarauniyar Yaƙin Marubuta: ☘️☘️NAZLAH☘️☘️ *DAGA ALƘALAMIN* SARAUNIYAR YAƘIN MARUBUTA / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️. *WANNAN LITTAFIN GABA DAYA SADAUKARWA NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF)WANNAN LITFAFIN WAKE NA RUBUTASHI, KI YI YARDA KIKESO DASHI, ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI , YA KUMA KARA RUFA ASIRI , DUNIYA DA LAHEERA........* بسم الله الرحمن الرحيم 7-8. """""""""""""Yana tafiya Jamseey ta tattaro kayanta gaba daya ita da Ƙanwarta Jasmin suka dawo gidan, tunda suka dawo komai a gidan sukeyi, basa ko dan zuwa gidansu su zauna, sai dai su ɗibi abin ci su bada akai,basa mata aikin komai, kwana biyu kawai gida ya fita daga hayyacinshi, mai aikin da take zuwa tana gyara palon ma Jamseey ta hanata zuwa, Sadiyya kuwa kamar wadda aka Asirce bata iya yin komai, kullum tana tule, duk abi da suka ce mata shi takeyi, bata son ganin bacin ransu ko kaɗan biyayya take musi kamar uwarsu........... ********* Tsabar kukan, Ummu ko leqowa waje bata yi ba saboda kawar da kai ga Yaranta, haka Nazlah ta mike ta shiga ɗakin tana kuka, kan jikin Maryama ta zauna tana shasheƙar kuka , tare da nuna mata hannunta, hannun ta rike tana dubawa, bata san sanda hawaye ya zubo mata ba ganin hannun gaba daya ya tashi, sharw mata hawayen idanunta ta shigayi, ita kuma nata na zubowa, ganin Ummu na kuka yasa itama ta kara fashewa da kuka, dan duk da bata wuce shekara daya da rabi ba amma gaba daya batason ganin Mamarta na kuka.............. yakice Labulen dakin Lawan ya yi, tare da cewa "wane shege ne yakeson mayar min da gida filim mutuwa, kumin shiru ko na tattaka ku gaba dayanku", ya fada yana daka musu tsawa................ Shiru Ummu tayi, kanar ruwa ya cita, Nazlah kuwa kara fashewa tayi da kuka tana boyewa jikin Ummu dan gaba daya bata son ganin Lawan ko kaɗan dan kallon mugu take mishi, "dan Ubanki rufemin baki ko nazo na tattaka ki", ya fada yana shirin shigowa ɗakin ,da sauri Ummu ta sanya tafi hannunta ra rufe mata baki, (Allah Sarki Mahaifiya, bata son duk abunda zai faru ga Ɗanta, tana iya jure dawainiyar Yaro tun daga ciki har izuwa haihuwa da raino, kashinka futsarinka, da komai naka ita take gyarawa, ko dan ciwo kaɗan bataso kaji, balle ta kai ga wani yaci zalinka, sai dai kawai tayi kawaici ta kyale bawai dan bataji ciwo a ranta ba, kawai dan mutunci da zaman tare, Allah ka tsare mana Mahaifanmu ka shirya mana Mahaifanmu sannan kaji ƙansu, ka gafarta musu zunubansu, Alfarmar Annabi da Al-qur'ani , Ameeen). sakin labulen ya yi, tare da ficewa yana banbamin bala'i, ganin ya fice da sauri ta dauki, Nazlar ta daurata akan gado tare da fara bincikar in da zataga maganin wuta, tasha wuya sosai kafin ta nemo maganin, tana kuka, Nazlah na kuka haka ta ciccire mata fatar da ta tashi, ta barbada mata maganin, bayan ta gama, feeding dinta ta fara yi tana shafa,mata kai tare da busa mata iska a hannunta, bacci mai nauyu sosai ya dauketa, ganin bacci ya yi awon gaba da ita yasa ta sauke numfashi da karfi, tunanin rayuwa ta fara yi, batayi aune ba taji ana kiran Magrib.............. Sallah tayi, lokacin da zata gama Haleem ya dawo daga aikin kanikancin da aka sanyashi, cikin murna ya matsa gareta tare da cewa "Ummu kalli, Oga na ya bani wannan", ya fada yana nuna mata wata sabuwar naira Ashirin da ya fitar a Aljihunshi, murmushi tayi tare da cewa "Allah ya mata Albarka, kaima Allah ya maka Albarka dama Ƴar uwarka," ta fada tana shafa kanshi, "Ameeen Ummu", ya fada yana jingina da jikinta.............. idanunshi ne ya hasko mishi ƙunar hannun Nazlah , da sauri ya mike ya nufeta , yana cewa "Ummu mai ya samu Nazlah", ya fada cikin rudu, yana kara kallon hannun, tuni kwalla ta cika mishi idanu dan bayason ganin ciwo ko ya yake a jikin Mahaifiyarshi ko Ƙanwarshi dan yana tsananin Ƙaunarsu fiye da komai, shafa kanshi tayi tare da cewa "Ƙonewa tayi dazun", girgiza kanshi ya yi, tare da cewa "kuma duka hannunwan Ummu ?", ya fada ya kara kallon hannun, "bana son surutu tunda dai ta ƙone ai shi kenan", ta fada tana kawar da kanta daga kallonshi, shiru ya yi bai kara cewa komai ba............... Chan kuma yace "Ummu mai zamu ci da dare", shiru tayi sai kuma chan tace "ga goma chan dauka ka haɗa da kuɗin hannunka ka siyo muku garin kwaki na ashirin sugar ta goma sai kusha", ta fada tana nuna mishi kabet dinta , mikewa ya yi, yaje ya dauka ya fice, minutes kadan sai gashi ya dawo da duk abin da tace,karɓa tayi tare da jiƴa musu, kallonshi tayi tare da cewa "sha ka rage mata", suna cikin maganar ta bude idanunta da suka jaajir , idanunshi na kanta hakan yasa da sauri ya dauketa ya sanyata a jikinsa........... fita ya yi da ita ya wanke mata baki, tare dawo da ita, garin ya fara bata,yana bata yana sha, surutu ta fara bashi tana cewa "Abbu! Abbu!! Abbu!!!", "shine ya ji miki ciwon", da sauri ta gyaɗa kanta ,shiru ya yi, dan shi tunda yaga ƙunar zarginshi ya ta'allaƙa ga Mahaifinsu, ganin Ummu bata son zance yasa bai kara magana ba............ ko rabin garin basu yi ba, Lawan ya shigo baaaga-baaaga, kwace kofin garin ya yi, tare da zama ya fara shaa, Nazlah na ganinshi kamar taga mala'ikan mutuwa, haka ta ringa ƙanƙame Haleem , taƙi yarda ko ido su haɗa............. shafa kanta ya shigayi yana karanto mata Addu'ar neman tsari dan har wani firgita takeyi, Lawan na gama shan garin ya kwanta sai bacci, dama ya gama shaa ya bugu............. ~********~ Bayan shekara daya da rabi, a lokacin Nazlah na da shekara ukku chass, ta ƙara zama wata cute gal, tayi wayau sosai ga karatu a bakinta, hakan yasa Iya ta kaita Makarantar tayani gantali dake chan bayansu, ba wata shahararriyar makaranta ba ce, dan sai Yaro na da mugun ƙoƙari kafin ya iya gane abun da ake koyawa saboda cunkushewarsu da rashin Malaman koyarwa, sai dai duk da haka tana ganewa sosai dan bata zama sai layin gaba, sai dai ba halin nan an na kwaɗayi, dan in taga abu miyanta har zubowa yake, tana tanɗar baki, hakan yasa mutane da yawa suka tsaneta, dan da taga mutum na cin abu zata je ta sanyashi gaba tana kallo, ko ta mika mishi hannu............. Umma na iyakacin bakin ƙoƙarinta na ganin ta hanata, amma abun ya faskara Haleem ma ya yi iya bakin ƙoƙarinshi, amma abun yaƙi ci yaƙi cinyewa hakan yasa suka barta........... sai dai da taga Lawan ko mai tale take take komawa cikin hayyacinta, ana cikin haka aka sanyata wata Islamiyya chan gefen Unguwarsu, Islamiyya ce mai kyau, wadda Fisabillilah wani Bawan Allah ya ginata, domin Gajiyyayu da Marayu, hakan yasa aka kaita chan, Haleem na zuwa aikinshi Ummu ma tana zuwa wani gidan Masu kuɗi tana musu aikatau suna biyanta, sai dai ko kusa bata taɓa zuwa da Nazlah ba dan tasan duk ranar da ta kuskure taje da ita, to wallahi ranar ta tashi aiki, dan korarta zasuyi, dan Nazkah bata gani ta ƙyale ba kuma taga abu batayi kamar ta fada ba, hakan yasa suke iyakar ƙoƙarinsu na ganin sun siya mata abubuwan Makulashe duk san kar ta gani hannu Yara ta roƙa, sai dai ko akwai abu a hannunta da taga na wani sai ta mika mishi hannu, in taga Yaro ne in bai bata ba, ta kamashi ta duka, dan fada gareta sosai ko dage ya shafa matw lafiya a faɗa............. Kamar Kullun Yau ma an tasosu daga Makarantar Boko , tana tafe tana karanta A B C D, tana gyada kai da taɓa hannu, idanunta ne suka hararo mata Wata Yarinya da Alale a hannunta tana ci, kamar Walƙiya baga ta kwasa a guje, gaban Yarinyar ta tsaya, tare da cewa "Kandala", ta fada tana murmushi tare da haɗiyar miyau............. Harara ta dalla mata tare da cewa "lafiya zaki tsayamin aka", ta fada tana ci gaba da cin Alalenta, murmushi tayi tare da zama kusa da ita tana cewa "ai abun ba na fada bane, Ƙawata", ta fada tana dafa kafaɗarta, sauke hannunta tayi tare da cewa "wace ce Ƙawar taki?, yanzu ne kikasan da ni a matsayin Ƙawarki, yanzu da kika ga abun duniya ko, to wallahi ahirrr dinki, dan ko zaki mutu ba zakici Alalen nan ba", ta fada tana dauke kwanonta ta mayar gabanta, "ke Dalla ki ajiye muci nima anjima in na siyo abuna zan baki", ta fada tana mika hannunta cikin kwanon................. kwaɓe hannunta tayi tare da cewa "Cire kin hannunki a cikin abuna", ta fada tana mikewa, cikin jin haushi tace "to wallahi sai na ci ko zaki mutu dan ma in binki cikin lalama", ta fada tana dalla mata harara......... ta fada tana fige kwanon hannun Kandala, wawushewa tayi tare da turata baki duka, wani azababban Mari Kandala ta sakar mata, tare da riketa mata wuyan riga tace "Wallahi ko da wannan Uban naki dan caca kike yawo sai kin biyamin alalena", ta fada idanunta na tara hawaye............... Tsalle Nazlah tayu tare da ƙifa mata wani wawan mari tare da cewa "ke dan Ubanki har kin isa ki zagi Ubana, naga ai tare da ubanki suke cacan dan haka babu kin ga ba sauran gori", ta fada tana dukan kirjinta tare da kama wuyan rigarta............ fada ne sosai ya kaure a tsakaninsu, gashi unguwar babu yawan mutanen da suke zirga - zirga hakan yasa babu wanda ya rabasu, Hannu Nazlah ta daura akan Kandala, Jelar gashin dokin da aka sanyawa Kandala ta kama, tare da ja cisgowa gashin dokin ya yi , tare da gashinta gaba daya, jini ne ya fara zuba, ganin haka yasa da sauri Nazlah ta saketa tana zare ido, shafo kanta Kandala tayi ganin jini yasa ta zaro idanunta............... Sakin Nazlah tayi tare da dafe kaiiii, ganin ta saketa yasa ta falla da gudun tsiya ba inda ta tsaya sai gidan Iya dan tasan ta koma gida Ummu batanan kuma ko dafata za'ayi sai ayi a gama bata dawo ba, da gudu ta shiga gidan Iya, Iya da take bakin murhu tana ƙoƙarin hada wuta da sauri ta mike tana cewa "Kayya! Kayya!! me ne ne?", ta fada tana zare idanunta, sai da ta kai kofar dakin Iya kafih tace "Iya fada muka yi da Kandala har na cirw mata taura(jelar gashi) daya kuma wallahi ga jini na zuba " ta fada tana sakin futsari saboda tsoron da take ciki............... "Mtswwwww wace Kandala, ita abun da takeyi a cikin garin nan ai sai a daure Ubanta, kema ranar ba ta duke ki ba, dama ai rama cuta ga macuci ibada ne, ni da in kai karar Ɗa gwara a akawo min kararshi, " bata rufe haki ba Delu Uwar Kandala tayi Sallama, da gudu Nazlah ta banka karkashin Gadon Iya ta shige tare da rike bakinta tayi lakur............. Huci Delu ta fara yi tare da cewa "In wannan shegiyar Jikar taki take?",ta fada tana kallon Iya , cikin fada Iya tace "kul kar ki kara shegantamin Jika in ba haka ba zan nakaɗa miki tsinannan duka a cikin gidan nan", ta fada tana harararta, tula mata jelar gashin tayi tare da cewa "gashi nan ta cirewa Kandala jelar gashi kuma wallahi gidan mai gari zan kai, dan bazan yarda ba", ta fada tana dafe da kan kandala da take ta kwaɗa ihu............. yar dariya Iya tayi tare da cewa "kim dade baki kai gidan Sarki ba, ke in ana biya ta Ƴarki ai da yanzun an kasheta har laheera Ƴar da har ƙarƙashin gadon Uwar Yaro take binshi ta dukeshi, shine dan an taɓata zaki ringa wa mutane zancen banza, to kin dade baki kai kara ba, ni kuma daga nan har bangon duniya zanje domin kare jikata ", ta fada tana shigewa ɗaki, dan haushi ficewa Uwar Kandala tayi, bata ƙara cewa komai ba, dan tasan in bala`i take ji dashi Iya ta fita............... ************** Tun da ya dawo aiki yake fama da matsanancin ciwon mara da ya rasa yarda zaiyi, har wasu hawaye ke zubo mishi,yanzu haka kwance yake rike da mara yana juyu cikin fitar hayyaci, Wayarshi ce ta fara ring , dakyar ya iya gangarawa gefen da take ya dauka, dakyar ya iya cewa "Hello!", daga chan ɓangaren akace "hi Buddy ya kake?", jaan numfashi ya yi da azabar karfi tare da cewa " ba lafiya ba ", cikin dan damuwa Khalil yace "mai yake damunka", numfashi ya sauke tare sa cewa "matsanancin ciwon mara dakyar na iya dawowa daga aiki", dan tsaki yaja tare da cewa "har yaushe zaka yi ta fama , tunda matarka ta ƙi zama a tare da kai kawai kaima ka ɓalle bushashaeka ko haka zaka zauna kana cutar rayuwarka in zaka tsaya ka bude idanuka ka shiga duniya ka shiga, in ba haka ba ka mutu a banza wallahi, y............... *WANNAN LITTAFIN NA KUƊI NE, KI DAURE KI BIYA KUƊINKI HAJIYA, DOMIN BA ZANYI FREE PAGES DA YAWA BA, CMPLT DINSHI #400 NE, TURAWA PC #300, GROUP #200, SIYAN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA , DAGA ALƘALAMIN SALMAJI/SARAUNIYAR YAƘIN MARUBUTA / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE 🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️* 1499884120 UMMASALMA SANI. ACCESS BANK. *KU TURAMIM SA SHAIDAR BIYAN TA HANYAR YIN SCREEN SHOT KU TURAMIN TA NUMBER TA KAMAR HAKA...* 07033371851. ~DAGA ALƘALAMIN SARAUNIYAR YAƘIN MARUBUTA / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE~🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ [12/1, 9:33 AM] Sarauniyar Yaƙin Marubuta: ☘️☘️ *NAZLAH* ☘️☘️ *DAGA ALƘALAMIN* SALMAJI/ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ *WANAN LITTAFIN DAGA FARKONSHI HAR KARSHENSHI, SADAUKARWA NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF)WANNAM LITTAFIN WAKE NA RUBUTASHI, KIYI YARDA KIKESO DASHI , ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI, YA KUMA KARA RUFA ASIRI DUNIYA DA LAHEERA.* بسم الله الرحمن الرحيم 9-10 . """''''''''''''""""", yanzu dai ga wata zazzafar Beb nan ko na turota ?", ya fada yana shafa wata Yar matashiyar budurwa da taci bleaching ta ƙoshi............... jaan numfashi ya kara yi, ya dan jima sosai kafin yace "to", yana fadar haka ya kashe , kallonta ya yi tare da cewa "Mayyarshi to tashi kije, ina son ki rikita mishi lissafi, ina son ya manta mukaminshi, ke kisa har aikinshi ya manta dashi da salonki", ya fada yana dan dukan boom-boom dinta, wani fari tayi tare da jijjiga jiki tace, "haaaba K ai kaima kasa ni, sai na jiyar dashi dadin da ko matarshi da yake ƙirarin Ya Aura ba zata jiyar dashi ba, kai dai bari naje", ta fada tana sanya wani siririn gyale akanta da yasha wani uban attechement , tafiya ta fara yi tana juya mazaunanta ta cikin wani shaffafan wandon da yake jikinta, a haka ta fita daga gidan, ta nufi gidan Hamid da yake chan dan nesa da gidan kaɗan............... ko Sallama babu ta shiga cikin palon, bedroom dinshi ta tunƙara kai tsaye, tana tafiya tana tauna chewing-gum ƙas-ƙas-ƙas, takunta da kuma karar chewing-gum din da take ci ne yasa Hamid bude runannun idanunshi da sukayi jaaajir , murmushi ta mishi tare da fara takowa gabanshi, tana tafiya tana jijjiga kirjinta , da hips dinta, lumshe idanu ya yi yana jin yarda yanayinshi ke kara chanjawa.................. tana zuwa ta zauna kan cinyoyinshi, shafo fuskarshi tayi tare da cewa "hello Beb", ta fada tana yi mishi tafiyar tsutsa a kan fuskarshi zuwa ƙirjinshi, cikin bariki take mishi yawo da hannunta a jikinshi, tare da fara jujjuya jikinta kamar wadda bata ji dadin zaman ba, alhalin sarai da nufi take hakan, tuni Hamid dinshi da take da fushi ta wani mike, jin hakan yasa ta saki murmushi tare da sanya hannunta ta wani damketa, da azabar sauri ya bude idanunshi, da suka kara rinewa kai kace jini ne ya taru a ciki................... mayar da kanshi ya yi ya kara rufe idanunshi, hannayenta ta sanya ta fara kunce mishi belt din kayan sojojin da suke jikinshi wanda suka mishi mugun kyau kamar a saceshi, sai da ta gama tsaf kafin ta fara ƙoƙarin sanya mishi hannu a cikin boxer dinshi, da sauri ya riki hannunta, dan a duniya babu abin da ya tsana sama da wani yaga tsiraicinshi, jaanye mata hannunta ya yi, tare da cewa "yi duk abin da zakiyi ki samamun natsuwa amma banda bayyanar min da tsiraicina", ya fada ba tare da ya bude idanunshi ba, kamar ba shi ya yi maganar ba, jin hakan yasa ta rike H din sosai har sai da ya saki kara, cikin kwarewa da bariki ta fara romance nashi, sai dai shi ko hannunta bai taɓa ba har ya samu ƴar natsuwa............ mikewa ya yi, gaban wadrop ya nufa, kuɗi ya dauko tare da tulla mata a jiki ya shigewarshi Bathroom dauka tayi tana sakin wani kalar murmushi, kafin ta fice abunta, ko da ya fito bai tarar da ita ba................... shirinshi ya yi tsaf kafin ya fice abunshi, yana fita ya nufi office din Ogansu da ya kirashi yanzu ............... *Bayan sati biyu* haka yake fama da matsananciyar Sha'awa, mai fitar mishi da dukkan natsuwarshi, gar sai ya samu anyi romances nashi kafin yake samun sauƙi , gashi duk maganin da zai sha baya jin yana mishi amfani, dan har gurin Dr yaje ya rubuta mishi magani, sai dai a banza dan kamar ma kara inganci da kara ƙarfin sha'awar yake .............. Kwance yake , yana duba abu a laptop dinshi, wayarshi da take gefen bed ce ta dauki ruri, a hankali ya zare farin glass din idanunshi yana kallon wayar *HAJIYATA*, ya gani a rubuce, hakan yasa ya kashe kiran tare da calling nata back,da Sallama ta dauki wayar, Amsa mata ya yi, tarw da gaisheta, bayan sun gama gaisawa tace "Wai ni Aunta lafiya yau kusan 3 months kenan baka dawo gida ba,in ce dai babu wani abu da yake faruwa ko , dan duk na bi na damu", ta fada cikin damuwa................ dan Murmushi ya yi, tare da cewa "Hajiyata lafiya lau wallahi, Aiki ne ya dan rikeni amma cikin satin nan Insha Allahu zan zo, kar ki damu ", ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa, "shi kenan Auta sai kazo , Haleeesa na gaishe ka",,"ina Amsawa Hajiya ki gaisheta", suna gama fadar haka suka yi sallama tare da kashe wayar... kamar kullum Sadiyya da Jamseey na zaune suna yar firarsu, kowa na duba waya, kallon Sadiyya Jamseey tayi tare da cewa "Aminiya ina wannan Ƙawar tawa Beebo ?", ta fada tana kallonta... daga kai tayi tare da cewa "wadda tazo ranar", "yawwa ita" Jamseey ta fada tana mikewa "to mai ya faru da,ita ?", jim tayi tare da cewa "ita ce tace wai zata zo", "ayya ai kuwa tana da kirki to sai tazo", ta fada tana ci gaba da kallon wayarta. da Maraice guraren 4 ,suna zaune babu Sallah balle Sati suka ji Sallama da sauri Jamseeey ta mike tare da cewa "Oyoyo-oyoyo ashe dama kina hanya muke chat",,ta fada tana rungumeta dariya tayi tare da cewa",, ai kuwa ina hanya wallaho", gaisawa suka yi da Sadiyya, kafin su tashisu shige bedroom din Sadiyya ita kuwa tana palo tule sai kace jakka. har dare ya yi Beebo bata da niyyar tafiya, dan tana ma kwance male-male akan gadon Sadiyya tana waya da wani Saurayinta, wadda wayar kusan rabinta ta batsa ce sukeyi , sai dariya suke. sai da suka gama wayar kafin ta mike ta fito palo, tsayawa tayi tare da cewa "ni fa Wallahi Yunwa nake ji", ta fada tana kallon Jamseey, "Ayya Sorry Ƙawa yanzu mai kikeso a dafa miki ?", yatsina fuska tayi tare da cewa "wallahi ni Shawarma nakeson ci da Ice Cream", zare ido Jamseey tayi tana kallon Sadiyya ta ƙasan ido, murmushi tayi tare da cewa "Okay bari na dauko kuɗi sai kuje da mota na ku siyo",,ta fada tana mikewa, bedroom dinta ta shiga. kwashewa suka da dariya, Beebo ce ta kalli Jamseey tare da cewa "tab gaskiya kina morewa matar nan", wata arniyar dariya ta saki tare da cewa " ai wawuya ce ba zata hankalta ba sai ranar da na aure mijinta na mayar da ita yar aiki zata gane bata da wayau", ta fada suna tafawa. "aikam ni dai da kin gama min komai wannan gidan daula haka ai kika shiga kamar mu muka shiga, Allah dai ya kai damo ga harawa", taɓawa sukayi kafin su haɗa baki gurin cewa "ko baici ba yay ɓarna" , dai² nan ta fito hannunta rike da kuɗi. miƙa musi kuɗin tayi, karɓa Jamseey tayi tare da yatsina fuska, tace "wannan kuɗin fa ba zasu isa ba",dafe kai tayi tare da cewa "to jeki cikin hand bag din nan red ki ƙaro na dauka wannan ma zai isa", mikewa tayi tare da shigewa ciki, bata wani jima ba ta dawo hannunta dauke da kuɗin da zasu iya haura 50k, kallon Beebo tayi tare da cewa "Beeb tashi muje", mikewa tayi suka fita ba tare da ko ce mata sai sun dawo ba. ganin sun fita yasa ta kwanta kan kujera tare da ci gaba da kallon Film din Amaryar tiktok da take kallo a wayarta, bata damu da ta tashi tayi Sallah ba ko wanka balle ta shiga kitchen,haka taci gaba da zama kusan 3 hours kafin su shigo a gajiye, hannunsu rike da ledojin da ba zasu wuce ukku ba, gefenta suka zauna tare da sakin hucin gajiya, dariya tayi tare da cewa "Sannun ku da dawowa, kum kwaso gajiya ko", ta fada tana karmashe ƙafafunta, Beebo ce kawai ta amsa mata dan Jamseeey nachan tana waya. bayan sun gama cin Abin cinsu, Saurayin Beebo yazo lokacin around 11, da gudu ta miƙe wadrop din Sadiyya ta nufa, wata rantsatsiyar abayarta ta fiddo wadda ko ita bata taɓa sanyata ba, ta zura a jikinta, tare da murza powder da kwalli da dan jam baki, wani hill dim takalmin Sadiyya ta dauka, wanda shima bata taɓa sanyashi ba, ficewa tayi tana rolling gyalenta, tana fita palo sakin baki Sadiyya tayi tana kallonta ganinta sanye da kayanta, wanda ko ita bata taɓa sanyasu ba, sai dai bata ce komai ba sai ma kawar da kanta da tayi, "ni na fita zance, kar ku rufe gidan zan dawo", ta fada tana ficewa, tana fita taci karo da wata rantsatsiyar mota, mai makon ta nufi gefen mai zaman banza sai kawai ta bude side din driver. dagowa ya yi , yana kallonta, ihu ta buge tare da fadawa kanshi ta wani kankameshi, dan murmushi ya yi, tare da cewa "duk murnar gani na din ce, ?" gyada kanta tayi alamar "Eh", taɓe baki ya yi, tare da cewa "banga alama ba, in kina murna ai kinsan abun da zakimin domin na gane dagaske kina murnar zuwan nawa", ya fada yana shafa kanta ,yar dariya tayi tare da gyara zamanta akan cinyarshi, shi kuwa kallonta yake, kanshi ta tallafo tare da haɗe bakinsu ta fara kissing lips dinshi, tana shafashi, cikin wani shauƙi da yake taso mata. zip din da yake jikin abayar ya kama tare da yin ƙasa dashi, kirjinta ne ya bayyana wanda ko arzikin bra bai samu ba, haukacewa ya yi, da irin suffar jikinta shafa kirjinta ya fara yi yana sauke numfashi, itama numfashin take saukewa, tana jin yarda duk wata tsikar (gashin jiki) jikinta na tashi, baya ya yi, da kujerar ta kwanta tayi plate kwantar da ita ya yi tare da fara shafa mata duk wani lungu da saƙo na jikinta, mika ts fara yi, tasa ajiyar zuciya, hakan ne kuma ya tabbatar mishi da cewar tana amsar duk saƙon da yake aika mata, hannunta ya rike tare da daurawa akan p... dinshi, ita kuwa dama mai neman kuka ne sai kuma aka jefeshi da kanshin awaki, tuni ta rike tare da fara murzawa, tana fitar da wani emotional sound mai tada hankali. tuni ya ruɗe, ya ci gaba da shafata yana tsotse duk inda yaci karo dashi a jikinta, ita kuwa sai mika take, tana kara sakar mishi dukkan wata,ragama ko ince kofar jikinta, ganin ta gama kaiwa kwrshe, yasa ya zare mata pant, tare da cusa mata yatsunshi a jikinta kara ta saki mai kama da tajij dadi (Hasbunallah), a haka suka ci gaba da aikata masha'arsu, wanda shi yafi karfin tsoma jikinshi a nata sai dai ya sanya mata hannu, abun baƙin ciki ita kuwa sai wani ihu take tana kara ƙara mishi kaimi. kusan 20 minutes , kafin su saisaita kansu, sai dai suna like da juna, yar fira suka fara yi, tana kan kafarshi tana shafa sajenshi, shi kuwa yana shafa B...dinta, sai guraren 1am kafin suka gama firar 10k ya bata, godiya ta shiga mishi, kamar zata mishi sujjada, dakyar ya hanata godiya, ficewa tayibtana daga mishi hannu shima haka, har ya shige ciki. yar dariya ya yi, tare da cewa "na gano lagonki yarinya, ashe Yan matan yazu haka suka zama, in dai kana da Yan chanji babu abin da ba zasu maka ba, tab nikam ai na samu gurin rage zafi, sai dai bazan taɓa shigarta da jikina ba, dan kyankyaminta nake, sai dai nayi ta sama shegiya hannu, tunda ita uwar son abun duniya ce", ya fada yana kyakyacewa da dariya (Ƙalubale gareku Yan matan zamanin nan, wallahi duk namijin da kika yarda son kuɗinki ya kaiki, kika ko rike hannunshi bama wai hawa kan jikinshi ba, to bazai taɓa ganinki da mutunci ba, zai dauke ki banɗakin kasuwa kowa ya shiga ya fita, kuma wallahi ko aurenki ya yi, ba zaiga mutuncinki ba, sai dai kiyi ta haukanki, amma shi baya ganinki da mutunci kallon ballagaza yake miki, ke! na taƙaice miki labari da mugun wahala ma ya aureki, dan duk wanda wata mu'amulla ta iskanci ta haɗaki dashi, bazai yi burin Aurenki ba, Samarin yanzu da dama kallon Sha'awa sukewa Yan mata, ko ince Sha'awarsu take kawosu, har in kika yarda ya biya bukatarshi to zai barki dan dama sha'awa ta kawoshi ya biya Bukutarshi to mai kuma zaiyi dake, zai tafi ya yi ƙoƙarin samun wata mai tarbiyar ya aura ba ke ba,dan ya riga ya gane baki da tarbiya ke ballagazace kuma shaddar kasuwa, dan haka dan Allah a kula dakyau, banso na fayyace komai ba, amma duba da yarda matsaloli irin wannan da ya damu jama'a yasa dole na rubuta, duk marubucin da ya gani yamin afuwa niyyar gyara nayi, kar a daukeni marar Ɗa'a, dan da dama da san ransu suke aikata komai nikam ba da son raina ba). shigewa tayi ciki tana murna sosai, ko da ta shiga yarda ta barsu haka ta samesu, kallonsu tayi tare da cewa "wai ku bakwa da wani aiki ne sai latsa waya, abun ya yi yawa wallahi, duk lokacin da za'a shiga ko a fita a zaune za'a gan ku na lallatsa waya, gaskiya ya kamata ku chanja", ta fada tana shigewa ciki, duk dariya sukayi . shigewa tayi ciki, tana shiga ta faɗa kan bed tare da sakin yar kara tana mika, adana kuɗin tayi cikin hand bag dinta da take kusa da ita, kwanciya tayi tare da jawo wayarta, kunna data tayi tare da hawa, facebook dan ita tafi bawa chan din karfi, tana hawa taga *Maji dadin Matan Katsina* ya mata magana, da sauri ta shiga maganarshi ta duba, yar dariya tayi, tare da cewa "Iyeeeee woooo mu shegu kace an bude mana gidan hutu, shi kenan aiko zan fadawa Saurayina muzo mu dan shana, fatan dai akwai komai ma more rayuwa ?", ta fada tana yar dariya. kasantuwar Facebook dinta normal ne mai amfani da data yasa yana yin komai kamar WhatsApp dan har voice yake, jim kadan ya mayar mata da sakon voice note itama, kunnawa tayi wata magana mai zubin ta yan daudu ta dakin dodon kunena, da shewa ya fara kafin yace "ina ko jiranku ,ki haɗomin kan shege da shegiya , dan iska da Ƴar iska , karuwa da sauran duk yan iskan duk da kika sani, domin so nake na haɗesu tsaf na ci gaba da basu wuta",,ya fada yana dariya, mayar mishi da feedback tayi kafin bude sakon wani wai shi *Farfesa Muttaƙa* murmushi tayi tare da cewa "Farfesa nawa", bude saƙonshi tayi, "Beeb ina son ganin Abubuwana please ki daukar min videonsu ki turomin", ya fada shima a voice note, yar dariya tayi tare da cewa "a nawa to?", jim kaɗan sai ga feedback dinshi. "A nawa zaki turamin to , fadi sai na biya", "10k", ta fada cikin lokaci ƙadan yace "turo Account number dinki na tura miki", tura mishi tayi cikin abin da bai wuce 3minutes ba ya tura mata da 15k cash........... *AYYA YAN UWA KUYI HAKURI KWANA BIYU KUN JINI SHIRU, WALLAHI ABUBUWA NE SUKA MIN YAWA SOSAI....* *WANNAM LITTAFIN NA KUƊI NE, KI DAURE HAJIYA KI BIYA KUƊINKI DAN BA ZANYI FREE PAGES BA DA YAWA , COMPLT DINSHI #400, TURAWA TA PC #300, GROUP KUMA #200, SIYAN NA GARI MAI DA KUƊI GIDA,DAGA ALƘALAMIN SALMAJI / SARAUNIYAR YAƘIN MARUBUTA / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️* 1499884120. UMMASALMA SANI. ACCESS BANK. *KU TURAMIN SHAIDAR BIYAN TA HANYAR YIN SCREEN SHOT KU TURAMIN TA NUMBER TA KAMAR HAKA* 07033371851 ~DAGA ALƘALAMIN SARAUNIYAR YAƘIN MARUBUTA / ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚 ‍♀️🧚‍♀️~ [12/14, 1:16 PM] YAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♂️🧚‍♂️: ☘️☘️ *NAZLAH*☘️☘️ *DAGA AL[]ALAMIN* SALMAJI/[]AR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ *WANNAN LITTAFIN DAGA FARKONSHI HAR KARSHENSHI, SADAUKARWAR NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF) WANNAN LITTAFIN WAKE NA RUBUTASHI, KIYI YADDA KIKESO DASHI, ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI, YA KUMA K'ARA RUFA ASIRI DUNIYA DA LAHEERAH...* *🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟* {R.S.W.A} https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c *_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_* _(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_ *Alk’alaminmu ‘yancinmu* بسم الله الرحمن الرحيم page 11-12. 11-12. """""""""""Alert ne ya faɗo wayata, da sauri ta duba, tana gani ta saki ihun murna, har da tsalle, kasantuwar su Jamseey suna chan palo yasa basu ji ba, dandanan ta shiga yakice yar suturar da tayi saura a jikinta , manya²n breast dinta masu girma da daukar ido ta shiga haskawa da wayar tana mishi video , har HQ dinta ta shiga haskawa da wayar, daga karshe ajiye wayar tayi, ta kwanta tare da tallafo gaba daya breast dinta tana wani matsawa tana jijjigasu, daga karshe kwanciya tayi plate ta sanya hannu a HQ dinta ta shiga Murzawa tana cacakawa, tana lumshe ido tare da sakin nishi, tana wani lashe baki kamar wadda aka sanyawa zuma a baki. ban gama tsurewa da lamanta ba, sai da naga ta bude jakarta, wani abu mai kama da jikin maza ya faɗo daga ciki, komai da komai shape dinshi irin na jikin maza ne, sai dai shi wani irin kartakeke, ga girma ga tsawo, wanda na tabbatar babu namiji mai girman haka, baaƙƙiƙirin bashi da kyan gani dan gani daya zaka mishi tsikar jikinka duk ta tashi . lashe abun ta shiga yi da tongue dimta, tana wani turawa sai ya yi kamar zata sanyashi har chan sai kuma ta jaawoshi, haka ta ringa yi har na tsawon wasu mintoci, kafin ta cire, ta kuma kashe wayarta, kayanta ta mayar, tare da turawa *Farfesa Muttaƙa*. tana tura mishi cikin Azama ya bude, wani ihu Farfesa ya saki, tare da dafe jikinshi yana wani nishi, ajiye wayarshi ya yi, ya shiga wasa da jikinshi yana kallon videon sai yake ji kamar yana Saduwa da ita , haka ya ringa wasa da jikinshi yana lailayawa, har ya samu natsuwa. voice ya danna mata tare da cewa, "Ahhhhhhhh gaskiya kina kashe ni, da kayan dadin nan, washhhhh Beee , yaushe zaki zo gareni , I love you Bee", yana gama fadar haka ya tura mata. cikin Azama itama ta buɗe sakon, wata mika tayi najin saukar muryarshi da yarda yake jaa mata numfashi cikin kunnenta, tuni taji wani abu na ratsa ta, chart din batsa suka ci gaba dayi ita dashi, har zuwa 1am, a lokacin ne kuma Sadiyya ta shigo bedroom din tana hamma, fadawa kan ved din tayi, tayi rigingine, waƙa ta kunna, tana bi, ga bacci a idanunta , maimakon ta karanta Addu'ar bacci, in ma karatu ne ta sanya sai ta sanya waƙa, tana bin waƙar tana komai bacci mai nauyi ya dauketa. Washe gari, tun da wurwuri flight din Hamid ya sauka a garin Katsina , jirgin na sauka mutane suka fara saukowa, sai da kusan mutanan suka gama saukowa, kafin ya fara takowa jikin isa da taƙama da wata izza da yake ji da ita, tuni Rundunar Sojojin da suke gurin suka shiga Sara mishi suna ƙamewa, Sara musu shima ya yi, kafin ya wuce gurin motarshi. kafin ma ya karasa har Daya daga cikij Yaranshi ya bude mishi Motar, shiga ya yi, tare da kamewa a bayan motar, shiga duk suka yiyyi, tare da ficewa daga cikin Airport din, kai tsaye Goruba road , gidan Hajiya suka nufa dashi. tun shigowarsu cikin Unguwar, tasan da zuwanshi, dan jiniyarsu ma kaɗai ta isa ta sanar da ita, bayan hargowar mutanan Unguwa da sukeyi na murnan ganinshi, tana jin karar dirar motarshi cikin gidan ta mike ta nufi ƙofa, cikin farin ciki , kafin ta ƙarasa ya danna belt dib da yake jikin kofar. da Sassarfa ta karasa zuwa gurin ƙofar, tana budewa ya fada jikinta, tare da sauke numfashi mai nauyi, cikin siririyar muryarshi mai amsa amo yace "Miss you so much Maa", shafa kanshi tayi, tare da sakar mishi wami ni'imtaccen Murmushi wanda a fuskar Mahaifiya ne kawai ake samushi , ta sakar mishi , tare da cewa "ya hanya ?", kanshi ya daura akan kafadarshi, tare da cewa "Alhamdulillah", jaan hannunshi tayi suka fara takawa izuwa cikin palon gidan, zaunar dashi tayi akan kujera, tare da zama gefenshi tana kallon. cike da mamakin ramar da ya yi, tace "Muhammad", a hankali ya Amsa mata cikin sanyin murya, taɓa kashin wuyanshi tayi tare da cewa "me ne ne wannan, ciwo kayi ne", ta fada tana zazzaro idanu. Siririn Murmushi ya saki , tare da cewa "Qlau nake Maa, kawai yana yin aiki ne ba hutu", jinjina kanta tayi bawai dan ta yarda da cewa aiki ne ya sanyashi rame ba ,haka sai dai in wani abu, amma da yake bata son sanya wani abu tsakaninsu yasa tayi shiru. Shafa cikinshi da yake mishi kuka , ya yi tare da kallonta yana kwaɓe fuska, alama ta mishu da ido alamar me ne ne , cikin muryar Shagwaɓa da Sakalci yace "I'm feel hungry", fa fada yana yamutsa fuska. kama hannunshi tayi suka nufi dinning room , tare da cewa , "ai dama komai an gama kai ake jira, " ta fada tana jaa mishi kujara, zama ya yi, yana kallon coolers din da aka jajjera akan dining din, zama tayi kusa dashi, tare da bude wata babbar cooler , haɗɗaɗiyar fried rice ce ta bayyana, wadda kallo daya zaka mata kasan ta hadu saboda yarda take daukar ido da yarda tayi kyau, tasha kayan haɗi sosai. zuba mishi tayi kafin ta kara bude wata cooler farfesun kifi ne ya bayyana a ciki sai kamshin kayan kamshi yake, ya yi kyau shima, cikin dan bowl ta zuba mishi, tare da kara bude wata cooler tuƙƙaƙen tuwon Shinkafa ne , ya bayyana, zare ido ya yi , ganin zata zuba mishi. kwaɓe fuska ya yi, tare da cewa "ni da wa?", harararshi tayi, tare da cewa "kai da wanda ka gani a kusa" ta fada tana ƙoƙarin zuba mishi, da sauri ya rike hannunta tare da cewa,"wannan ma is okay ", ya fada yana sanya spoon s ciki, cikin natsuwa ya fara ci da Bissimillah dauke a bakinshi. tun da ya fara ci, baiyi magana ba, har ya tsame spoon din daga cikin Abincin tare da furta "Alhamdulillah", kallon shi tayi da mamaki ƙarara akan fuskarta, "mai kake nufi?", ta fada tana kallonshi. kwaɓe fuska ya yi, tare da cewa "Allah kuwa na ƙoshi", ya fada yana kwantar da kanshi akan kafadarta, "Baka cin Abinci shi yasa ka rame ka lalace haka, to ba zan lamunta ba, maza² dauka kaci kafin na ɓata maka rai", ta fada tana haɗe fuska, shiru ya yi, dan baisan kuma mai zai kara cewa ba, dan ya mugun ƙoshi. ganin ya yi shiru, yasa ta dauki Spoon, ta dibi abin cin ta fara bashi, bai mata musu ba ya bude baki, baifi 3 spoon ba ya fara kakarin amai, a dan tsorace ta jaan ye hannunta, daga kan spoon din, mikewa ya yi, da sauri ya nufi toilet din dake cikin dinning room din. kafin ya ƙarasa shiga, aman ya taho mishi, da sauri ya duƙa ƙasa, ya fara kwarara amai, a dan tsorace ta biyu bayanshi, duƙawa tayi kusa dashi, tana shafa bayanshi, tun yana aman cikin hayyacinshi, har ya fita a hayyacinshi, aman ma har ya koma babu komai cikinshi, sai kakari da wahala. dakyar aman ya tsaya, wanke mishi bakinshi, tayi ta kamashi suka fito palo, zaunar dashi tayi akan kujera, tare da zama, kanshi ya daura akan cinyarta ,yana sauke numfashi, ganin yarda yake yasa Nadama saukar mata, tasan tun yana Karami in har yaci Abin ci da yawa to karshenshi sai dai ya Amayar dashi, bacci ne ya dan daukeshi, baiyi ko 3 minutes yana baccin ba ya farka , a hankali ya fara bude idanunshu, har ya budesu tarrr akan fuskar Hajiya , da sauri tace "Sannu ya jikin naka", ta fada cikin tausayawa. murmushi ya yi, tare sa cewa "ni babu abun da yake damuna", ya fada yana mikewa zaune, hamdallah tayi, kalle² ya fara yi cikin palon, kafin ya kalleta yace "Hajiya ni banga Auta ba", ya fada yana kara jujjuyawa. Yar dariya tayi, tare da cewa "kaga ta tafi gidan Addarta ", da mamaki ya kalleta , tare da cewa "Wace Addar bayan duk basa Ƙasar", zare ido tayi, kafin tace "Aisha Man , ai sun dawo kusan two weeks da dawowarsu, "ta fada tana kallonshi, taɓe baki ya yi, tare da cewa "Lallai Yayah, ashe ta dawo shine bata fada min ba, ta kyauta ai", ya fada yana mikewa. kallonshi tayi, tare da cewa "ina zuwa haka?", dan tsayawa ya yi, tare da cewa "gida zanje Hajiya, zuwa Anjima zan dawo", ya fada yana yin gaba, fatan sauka lafiya ta mishi, kafin ya fice. Yana fita ya tarar da Yaranahi, zazzaune suna cin Abinci, suna ganinshi suka zabura suka mike gaba dayansu, suna sara mishi, kowa gurin mota ya nufa, murmushi ya musu, kafin yace "ku zauna ku gama cin Abin cin, in kun gama ku shiga da kayan ciki, ni zan tafi gida, in yaso in kuka gama kwa taho", ya fada yana wucewa. Abbas ne ya yi, saurin bude mishi mota ya shiga, shima shiga ya yi mazaunin driver, tare da kunna motar, tafiya ya fara yi, tun kafin ya karaso bakin get aka bude musu, yana zuwa ya fice, kan titi ya hau, kasantuwar Unguwar kusan gaba dayanta titi ne, dan Unguwar Sarakai ce , da manyan Yan siyasa, basu wata tafiya sosai ba suka ƙaraso Barhim . Tunda suka tun karo Unguwar zuwansu , ya isar da Yan Unguwar, hakan yasa kowa ya shiga taitayinshi, dan baya wasa da mutum, in ka mishi iskanci ko ka nemi yiwa wani to taka maka wuya zaiyi ba abun da yasha mishi kai, Suna karasowa getman din ya wangale musu get din gidan suka shige. sai da Abbas din ya dai-daita parkinga kafim ua fito, yana shaƙar daddar iskar da take kaɗawa, cikin izza ya fara takawa cikin gidan, bai ko damu da Sojojin da suke sara mishi ba, yana zuwa jikin kofar ta bude da kanta, ƙafarshi na taka shiga cikin palon yaci karo da Plate a ƙofar shigowa palon. da mugun Mamaki yake kallon cikin palon, ganin komai a hargitse, da alama ɓa tunda ya tafi babu abun da aka gyara cikin gidan, da Sallama ya shiga cikin palon, da sauri Sadiyya ta mike tana kallonshi, fuskarta ta bayyana tsantsar farin cikin ganinshi. gurinshi ta nufi tana washe baki, cikin muryarta mai dadi tace "barka da zuwa, saukar yaushe?", ta fada tana karɓar brief case din da yake hannunshi, sakat mata ya yi, ya shige ba tare da yace mata komai ba. ********* "Ke! Nazlah tashi kizo ki shirya, ki tafi Makaranta dan su Salamatu tun dazun naga sun wuce Amma ke baki da Niyyar mikewa ki tafi", tura baki Nazlah tayi, tare da cewa "to kema Umma mi Wallahi na gaji", ta fada tana , ci gaba da yanka kyallayen da suke gabanta. Haleem ne da ya shigo yanzu, ya daka mata tsawa, tare da cewa "Zaki tashi ko sai na tattakaki Sakarar Yarinya, " ya fada kamar zai duketa, da sauri ta mike tana diddira ƙafafunta ta shige ɗaki, ta kusa Minti goma da shiga amma bata fito ba, "zaki fito wai ko sai na shigo ɗakin", Haleem ya fada cikin muryarshi mai dadi da kuma Amo, a hankali ta bude labulen ɗakin ta fito tana share hawaye, fuskarta tayi jargwab da hawaye, gabanshi ta tsaya tana cuno dan karamin bakinta. kallo ya ƙare mata tare da cewa, "shige ji tafi, kuma Wallahi na fito na gsnki a hanya kina wasa ko kin tsaya sai na ɓallaki", ya fada yana dungure mata kai, kuka ta fasa tare da ficewa, tana kukan ita an tsaneta komai sai ace dole tayi, a haka ta kama hanyar zuwa Makarantar , babu nisa sosai daga gidansu zuwa Makarantar sai dai, sai an tsallaka titi, tana cikin tafiya ta haɗu da wani Yaro dan Unguwarsu mai suna Idi, ganin tana kuka yasa ya fara mata dariya. da sauri ta ɗago kanta tana kallonshi, cikin hasala da jin haushi, kan Yaron tayi da gudu, tana zuwa ta cukwikuyeshi , ta hadashi da bango, tare da fara gwara kanshi, tana zazzaga mishi ruwan masifa, yakushinta Yaron ya fara yi yana neman hanyar guduwa. damkarshi tayi, tare da kafa mishi cizo a wuyanshi, ta rike ta cije , taƙi saki, ihu Yaron ya saki, yana son ta sakeshi, amma ta gama duƙunƙuneshi, mutane ne suka fara taruwa, suna son rabasu, amma taƙi rabuwa dashi, taƙi sakin Yaron ga wuyanshi har ya fara jini , wani Mutum ne, yazo ya fisgeta daga jikin Yaron tare da dalla mata mari. Tsautsayi yasa Yatsan hannun mutumin ya fada cikin bakinta, wani wahalalan cizo, mai ratsa kwanya , wsnda yake bi ta cikin jijiyoyin jiki ta sakar mishi, wanda yasa mutumin, ba shiri ya saki ihun azaba, tana ganin idanun mutane sun fara yo kanta, ta saki hannun mutumin da gudu, kamar iska haka ta tsallake titi zuwa Islamiyarsu. Tana cikin gudun ta haɗu da wani tsoho Daga mata hannu ya yi, itama ta daga mishi, cikin kwala murya yace "ki kula ana Taro Makarantarku, kar ki bari a duke ki, ki gudu", ya fada yana juya baya. babu wanda ya lura da lokacin da ta shige ciki, ruɗewa Mutumin ya yi, yana cewa "Aljana! Wallahi Aljana ce kun gani ta ɓace ɓat", ya fada cikin ruɗu da tashin hankali, wani Matashi ne yace "Wallahi Alhaji ba Aljana bace, mutum ce, Allah dai ya shirya, dan fitinar Yarinyar nan tayi yawa", ya fada yana jinjina kanshi. itana shiga cikin Islamiyyar tasu ta tarar da Malam Arabi na dukan latti, tsuru² tayi da ita, ba abin ta koma waje ba tasan boom din da ta haɗa, gashi bata kaunar bulala ko kaɗan dan har in aka mata to ranar bata kwana lafiya, take dubura ta faɗo mata, ana dukan wata ta mike, tabi bayanta, kasantuwar suna da yawa wanda aka duƙa, ba lallai ne a iya ganeta ba, har ta gota Malamin wata Yarinya tace "Malam Arabi ga Nazlah chan ta ruga baka bigeta ba", da hanzarinshi ya juyo, tare da kwalala mata manya²n idanunshi masu kama dana Nufawa. "Ke! Uban wa yace ki tashi ban dukeki ba ki gudu?", ya fada yana zazzare mata idanunshi, cikin jin haushi tace "Malam Arabi ka daina zagar min Uba kaga dai babu abun da ya maka", ta fada tana dalla mishi harara dan arayuwar ta tsani zagi, "Ke! dan Ubanki ni kike cewa haka?, Nace Uban wa yace ki tashi ki tafi?", cikin dakiya da nuna rashin tsoro, ta kawar da kanta tare da cewa "Ubanka ne", ta fada tana karkaɗa kanta. Ware idanunshi ya yi, da mugun Mamaki, cikin Azama ya damki wuyan hijab dinta tare da cewa "Kutumar Uba, dan Ubanki ni kike zagi?, Ashe Yau zan ci Ubanki kuwa", ya fada yana zuba mata bulala a gadon bayanta. ihu mai karfi ta saki, tare da cewa, "ba kaine kace Uban wa ya sani guduwa ba, kuma ai Ubanka na haɗu dashi yace min in naga ana taron Makara na gudu, kuma dan na fada maka shine zaka duke ni", ta fada tana ƙoƙarin kwacewa, zuba mata bulalar ya kara yi a tsakiyar kanta, wadda ta zago har fuskarta, tuni shatin bulalar ya tsaga fuskarta ya yi, wani jaaa lokaci daya abunka da farar mace. jin yarda bulalar ta ratsa mata cikin jikinta, da kwanyarta har tana barazanar illata mata jinta da ganinta yasa ta faɗi kasa, yana ƙoƙarin riketa, ya mikar da ita, ta shige cikin rigarshi Yar shara,Makalewa tayi tana gunjin kuka, ƙoƙarin fiddota ya shiga yi, amma ta manne. gefen Mararshi ta samu, ta gasa mishi wani Lalataccen cizo, mai illata yan hanjin ciki, riƙe gurin tayu kam taƙi sakinshi, zufa ce ta fara karyo mishi, cikin jikinshi, ba abin ya yi, ihu ba ace Malam na kuka, gashi kuma ya kasa cirota daga cikin jikinshi, haka ta ringa bi tana mammana mishi cizo duk inda ta samu, yakushi kuwa, babu inda bata ya kusa ba, ƙoƙarin cire rigar ya fara yi, amma ta rike kam taki sakin rigar, taki kuma daina cizonshi. ganin Yana niyyar kashe kanshi, yasa ya saki ihu tare da cewa "Wayyo Jama'a ku kawo dauki, wannan shegiyar Ƴar zata kashe ni, wayyo Marata wayyo", ya fada yana ƙoƙarin guduwa, hardewa ya yi, ya fadi cikin filin makarantar. birgima ya fara, yana kokarin cireta, amma abu yaci tura, hakan yasa yaci gaba da zunduma ihu, tuni Malaman Makarantar sunzo sun zagayesu, dakyar da jibin goshi, suka samu suka fito da ita daga jikin Malam Arabi, ana fitar da ita ya fice daga makarantar da gudu, yana haki,bai tsaya ko ina ba sai da yaje gida, zubewa ya yi a tsakar gida yana haki, Matarshi ce ta kalleshi, tare da cewa "Lafiya Malam", girgiza kanshi ya fara yi, alamar ba lafiya, sai dai ya kasa yin magana. ruwa ta kawo mishi, dakyar ya sha, yana sha ya fara cewa "Wallahi ba Mutum bace! ba mutum bace!! nace miki Aljana ce", ya fada yana zazzare idanu tare da leƙen hanyar waje, ita kuwa ta kasa gane maganar da yake yi, sai binshi da kallon mamaki take, ganin sahun cizo na haƙora raɗo² akan fatar cikinshi, fa yakushi har kan kirji. sai lokacin ta lura da babu komai jikinshi sai gajeran wando, "Malam ina rigarka?", ta fada tana mishi kallon tuhuma, "na fada miki ba mutum bace", cikin tsawa tace "kai Malam yimin shiru, ashe halin da ka koma kenan, kwartanci ka fara, shine har da zuwamin ba riga, to ai na gani basai ka karamin wata magana ba, maci Amana kawai, kuma Wallahi naji dadi da aka maka haka, naso ma da sun gurguntar da kai, kaga kwartanci ya yi rana", ta fads tana mikewa daga gurin ta shige ɗaki abinta. ************ Bulali Malaman suka sanya aka cicciro musu, suka sanya Nazlah Office, zasu duketa, hankalinta in ya yi, dubu ya tashi da ganin irin bulalan da aka zagayeta dasu, Faɗuwa tayi a gurin , jikinta na wani kyarma, daga baya kuma ya saki bata ko motsi, daya daga cikin Malaman ne ga zabga mata bulala, akan ƙafafunta, tare da cewa "tashi Munafuƙa yau sai kin gane kurenki, na abubuwan da kike yi, dama dama muke jira, yau kuma gata ta samu, ba Aljannu ba, ko Uban Aljannu ne yau sai mun ci ubansu", ya fada yana yin ball da ƙafafunta. wani Uban ihu ta kwarara, tare da fara wani Yare wanda duk cikinsu, babu wanda ya iya gane mai take cewa, Malamin ne ya dagota tare da haɗata da bango, ya dago bulala zai zabga mata, wani Wulaƙantaccen kallo ta watsa mishi, tare da sanya hannunta dauki wata bulala da take kusa da ita, ta zabga mishi akan sankonshi , a ruɗe ya saki bulalar hannunshi, yana dafe kanshi da yaji kamar an sauke mishi shi, kafin ya yi wani yunkuri, ta kara zabga mishi a gadon bayanshi, gantsarewa ya yi, tare da sakin ihun azaba, ganin tana dukanshi, yasa gaba daya Malaman suka yo kanta, tama cikinsu tayi, tana dukanshi suka dukanta, abun ka da Jinnu , karfi ba daya ba, tuni ta haɗa musu jini da Majina, cewa take "Uban waye yace ku taɓa mana Goɗiya, yau sai kun gane baku da wayau, dama ku Bil Adam dinan baku da mutunci, bakusan kawaici ba, kuma baku da kunya, daga Yau ko wani ne yace ku kara taɓa ta zaku ga abin da zai faru da ku, marasu kunyan Wooofi kawai", wata murya da sam batayi kama da tata ba ta fada, tana zazzare musu idanu, karatu suka haɗa baki gurin yi mata. dariya ta sheƙe, da ita, tare da karasa musu karshen Ayar da suka dauko, haka suka dunga yi, tana dukansu suna karatu tana karasa musu, duk surar da suka dauko ita take karasa musu. da gudu, suka bude office din suka fice, ita kuwa Hamma ta buga tare da sulalewa a gurin Summamiya, Malamai kowa ya kama gabanshi, Ɗaliban ma ganin Gwagwarmayar da akeyi yasa kowa warewa, dan babu mai zama anan wannan badaqalar............ Ga duk mai so, zai iya min magana ta number na kamar haka👇 07033371851 ```DAGA TASKAR SALMAJI / ƳAR LELEN ROYAL/ SARAUNIYAR YAƘIN MARUBUTA``` [12/21, 12:10 PM] YAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♂️🧚‍♂️: ☘️☘️ *NAZLAH*☘️☘️ *DAGA AL[]ALAMIN* SALMAJI/[]AR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ *WANNAN LITTAFIN DAGA FARKONSHI HAR KARSHENSHI, SADAUKARWAR NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF) WANNAN LITTAFIN WAKE NA RUBUTASHI, KIYI YADDA KIKESO DASHI, ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI, YA KUMA K'ARA RUFA ASIRI DUNIYA DA LAHEERAH...* *🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟* {R.S.W.A} https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c *_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_* _(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_ *Alk’alaminmu ‘yancinmu* 13-14 """"""""""""""Babu wanda ya kula da Nazlah kowa ta kanshi ya yi, babu kuma wanda ya yi tunanin zuws gidansu ya faɗi halin da take ciki. Ummu tana ta jiranta, dan an kawo mata kashedinta har gida, hakan yasa take jiranta taji ba'asin Abun da ya faru, kafin ta dauki mataki a kanta, shiru² Nazlah bata dawo ba har gabanin Magrib, hakan yasa hankalinta ya tashi, ta kasa zaune ta ƙasa tsaye, tana cikin Safa da marwa, Yah Haleem ya shigo, kallonta ya yi tare da cewa "Ummu Lafiya kuwa?", ya fada yana kallonta, da sauri ta juyo gareshi tare da cewa "Nazlah ce bata dawo ba, tun ɗazun da ta fita Islamiyya, gashi Abbanku baya nan, kuma ya hanani fita in baya nan, ko zaka je ka duba min ita ?", ta fada tana kallonshi, "to Ummu bari naje na duba", ya fada yana juyawa. cikin sauri yake tafiya zuwa Makarantar tasu Nazlah dan duhu har ya fara rufawa, cikin sa'a ko da yaje makarantar a bude take, sai dai ba kowa a ciki, hankalinshi ya fara tashi, cikin daƙiya ya fara dudduba Ajujuwan Makarantar, sai dai ba kowa a ciki, kuma duk a bubude, cike da tsananin mamaki yake kallon Ofishin Malaman da yake a bude , kuma makarantar ba kowa, hankalinshi ne ya kaiga wani waren takalmi da ya gani yashe a ƙasa kusa da Ofishin, tafiya ya fara yi zuwa ofishin, da sauri ya shiga yana furta "Innalillahi Nazlah! Nazlah!! Nazlah!!!", ya fada yana jijjigata. A hankali ta fara bude idanunta, da suka mata nauyi, "Yah Haleem..! ta fada tana shigewa jikinshi", mikewa ya yi, da ita jikinshi ya nufi hanyar waje, da ita rungume a jikinshi, hanyar gida ya nufo da ita, yana cikin tafiya yaji an kwala mishi kira, da sauri ya juya yana kallon Iya da take nufoshi, da sauri ta ƙaraso gareshi tare da cewa "kaga Nazlan?", Nuna mata ita ya yi, tare da cewa "gata bacci na tarar da ita tana yi, babu kowa a makarantar sai ita daya", ya fada yana direta ƙasa, ganin yarda take ta mutsu² da son ya sauketa. Yana sauketa, ta Afka kan Iya tare da cewa, "Iya goyani bacci nake ji", ta fada tana riketa, da mamakina babu ko kunya Iya ta duƙa Nazlah ta haye bayanta, zaro ido Yah Haleem ya yi, tare da cewa "Iya dama har yanzu baki daina goyata ba,kar ta je ta karyaki fa", ya fada yana yunƙurin dauke Nazlah daga bayan Iya. kaɓe hannunshi Iya, tayi tare da cewa "mai yasha ruwanka da harkarmu, baka ji tace bacci take ji ba, " ta fada tana zare dan kwallinta, kyakyawan dogon gashinta mai kyau ne ya bayyana, wanda duk da tsufar da tayi amma yananan sumul sai dai furfurar da ba'a rasa ba akan tsoffafi. dakyar take takawa da Nazlah akan bayanta amma haka take tafiya, Yah Haleem ya yi, ya yi ta sauko da ita amma taƙi, sai ma kara kankameta da Nazlah tayi ta rumtse idanunta. ************* Da sauri ta bi bayanshi, tana shiga ta tarar dashi zaune gefen bed dinshi, ya buga uban tagumi, zama tayi kusa dashi, tare da cewa "lafiya kuwa My Solder?", ta fada tana dafa kafaɗarshi. dago idanunshi ya yi, ya watsasu cikin nata , Cikin faɗa ya ce"wai ke ba zaki chanja halinki ba, duk abun da ake fada miki va zakiji ba, bayan rashin kula da ni , hanzu kuma har wani sabon salo kika koya ba rashin tsafta, duba wai nan ɗakin Mijinki ne, amma kacha² ba gyara ba komai, yanzu wannan rayuwar da kika daukarwa kanki kina tunanin mai daurewa ce, ?" ya fada yana kallonta. cuno baki tayi gaba, tare da daura kanta akan kirjinshi, "to ba yanzu , zan tashi na gyara ba", ta fada tana mikewa, bathroom dinshi ta fara wankewa, wanka ya shiga, kafin ta fito har ta gyara mishi bedroom, kallon Bedroom din ya yi, jinjina kanshi ya yi, tare da cewa " tab da matsala kuwa", ya fada yana kara kallon bedroom din , dan kawai sunan ta gyara ne, amma babu abun da ta wani gyara, shara ce tayi , sharar ma bata yi ba, dan chan da datti chan share, chan datti haka sharar tayi. , kallon Bedroom din ya yi, jinjina kanshi ya yi, tare da cewa " tab da matsala kuwa", ya fada yana kara kallon bedroom din , dan kawai sunan ta gyara ne, amma babu abun da ta wani gyara, shara ce tayi , sharar ma bata yi ba, dan chan da datti chan share, chan datti haka sharar tayi. Da sauri tazo gareshi, ta rungumeshi tana shafa kirjinshi, wata uwar tsawa ya daka mata, tare da cewa "zaki matsa min anan ko sai na babbalaki", ya fada yana tureta a jikinshi , cikin tsoro ta matsa, dan tunda takw dashu bai taɓa mata fada ba, sai taga fuskarshi ta koma kamar ta kumurci, da sauri ta nufi hanyar ficewa "Stupid girl", ya fada yana jaan tsaki, dan yanzu yaji ta fita ranshi kwata² baya son ganinta. yana gama shiryawa, ya fice abinshi, driver yazo da sauri zai bude mishi mota, saurin dakatar dashi ya yi, tare da shigewa ya bata wuta, direct gidan Addarshi ya nufa, tun daga nesa yake burkaka horn kafin ya ƙaraso tuni get man din ya bude mishi get,shigewa ya yi ciki, ko dai²ta parking baiyi ba ya fice zuwa cikin gidan. Tura ƙofar shiga palon ya yi, yana saka ƙafarshi ciki yaji ance "Oyoyo Uncle! Oyoyo Uncle", wata Yarinya da ba zata wuce 3years ba ta faɗa yana rungumeshi, daga Yarinyar sama , dan murmushi ya saki tare da sakar mata kiss a forever dinta, yana cewa "Baby ina Mom naki?", ya fada yana dafa kanta. gyaran murya yaji anyi, da sauri ya kalli inda yaji anyi gyara muryar, ware idanunshi ya yi, yana binsu da kallo, nima bin inda yake kallon nayi da kallo, wasu Hamshaƙan mata huɗu na gani, zaune farare tar² kamar jini zaiyi tsartuwa a jikinsu, suna masifar kama dashi, ƙara ware idanunshi ya yi, tare da cewa "surprise", ya fada da murna fal ranshi, da sauri ya nufesu , rungumesu duka ya yi, yana jin yarda wani sanyi yaƙe ratsa zuciyarshi, duk kuma wani baƙin cikinshi na tafiya, kallonsu ya yi, suma shi suke kallo suna mishi dariya, dan duk ya ruɗe da ganinsu, ko dan sun dan jima basu haɗu duka ba, sannan babu wanda ya faɗamishi zai zo a cikinsu. washe bakinshi ya ƙarayi tare da cewa "wai ni shin meeting aka haɗa ne ko ya?", ya fada yana daura baby akan cinyarshi, dariya duk sukayi kafin Adda Nabila tace "meeting din mai fa Auta", cuno baki ya yi tare da cewa "Yo duka na ganku lafiya dai ko, kuma babu wani dan kira", ya fada yana kallon Haleesa ya kalla da take ta game da waya , ko kallonshi ma batayi ba. "kawai mun dawo ganin gida ne", Adda Nafisa ta fada tana ajiye mishi robar ruwa da cup a gabanshi, tare da tray din yankkakun kayan marmari, "aikam dai kum shammace ni, dan banyi tunanin zuwanku ba yanzu", ya fada yana kai cup din ruwan da Adda Zainab ta zuba mishi, Adda Zainab ce tace "dama ko baka zo ba muna da shirin muje gidanka gobe, sai kuna gaka kazo,"jinjina kanshi ya yi, kafin yace "Ke..! Auta lafiyarki kuwa", ya fada yana daka mata tsawa, da sauri ta zube ƙasa ta ce "Sannu da zuwa Auta ban lura bane game ta dauke min hankali, ina Anty Sadiyya?", ta fada cikin tsoro, dan tasan karamin aikinshi ne ya mangareta. banza ya mata yaci gaba da fira da Yan uwanshi, sai wajen 10 kafin ya wuce gida, a palo ya tarar da Sadiyya da Jamseey, da sauri Sadiyya ta mike, tana mishi sannu da zuwa, gudun kar ya yarfata sai ya amsa, amma a zahirin gaskiya har lokacin fushi yake da ita, cikin yanga da ƙissa da ƙisisina irin ta yan bariki, Jamseey tace "Barka da Zuwa Yallaɓai", ko kallonta baiyi ba ya shige ciki, bin bayanshi Sadiyya tayi, Jamseey kuwa, wani makirin Murmushi ta saki tare da ce wa "Ooooh Allah ka kai damo ga harawa ko baici ba yay ɓarna, kai yama ci", ta fada tana lumshe ido tare da lashe lips dinta. tare suka shiga cikin bedroom din, sai da suka shiga kafin yace "Wace waccan a palo?", ya fada cikin tuhuma, dan shi kallo daya yawa Jamseey ya gane goggiyar yar bariki ce, "Au Jamsy ai Ƙawata ce", ta fada cikin share zance, ganin tayi fatali da zancen yasa ya share shima, bathroom ta jufa, ruwan wanka ta haɗa mishi mai dan ragwamen zafi kafin ta fito, kallonshi tayi tare da cewa "ga ruwan wanka", tana fada ta fice , girgiza kanshi ya yi, kafin ya shige cikin bathroom. ```Washe gari``` Kamar yarda su Adda Zainab suka fada, hakan ce ta faru guraren 1pm sai gasu, su da Yaransu kusan su goma, har da Haleesa, da Sallama suka shiga cikin palon, shiru babu wanda ya amsa, ƙara sallamar sukayi still ba bu wanda ya amsa , ƙarasa shiga sukayi ciki , guri suka samu suka zazzauna,suna bin palon da kallo , farin tayis amma ya koma ruwan ƙasa saboda rashin tsafta, kallon Adda Nafisa tayi tare da cewa "Tooo! Ikon Allah wai ni kaɗai naga abun da na gani ko kuma kun gani?", ta fada tana tsaresu da idanu. Kallonta Adda Nabila tayi tare da cewa "nima na gani,amma dai ina jin ba lafiya ba, tunda kika ga gidan nan haka, killan ko bata jin dadi ne, Auta shiga ki gano ko tana nan ma", ta fada tana Kallon Haleesa, mikewa tayi da Ƴar Adda Zainab Ihsan ta nufi hanyar ɗakin Sadiyya, tun daga Ƙofar shiga ta jiyo shewar Sadiyya da Jamseey, da mamaki ta ƙarasa cikin bedroom din, zaune ta gansu suna fira kowa da waya a hannunshi,duk binta da kallo sukayi, dan kimtsa fuskarta tayi tare da cewa "Anty Sadiyya baki ji zuwan mu bane?", ta fada tana kallonta. dan taɓe baki tayi, Jamseey ce tace "Wace ce wannan?", buɗar bakin Sadiyya sai tace "Dangin Miji mana dangin tsiya", da sauri Haleesa ta kalleta,,tana maimaita dangin tsiya, dan murmushi tayi tare da cewa "Ayya lallai kam dangin tsiya mana, tunda anzo cikin Arziki anyi male² an manta da tsiyar da ta liƙewa tsoho a jiki, in kin gama shashancin sai ki fito palo ana son ganinki", ta fada tana jaan tsaki tare da ficewa. zare ido Sadiyya tayi tana nin bayan Haleesa da kallo, dan ita sam batayi tunanin Haleesa zata iya mayar mata da magana irin haka ba, "tab lallai sai kin dauki mataki akan wannan Yarinyar"Jamseey ta fada cikin zuga, kwafa Sadiyya tayi tare da cewa "barta dan buhun Ubanta,,zata gane kurenta ne", ta fada rana mikewa, kallonta Jamseey tayi tare da cewa "ina zaki?", ta fada tana rikr hannunta, dan janye hannun tayi tare da cewa,"zanje naga waye yazo", "kar kije dallah ki barsu, in sun gaji sun tafi", ta fada tana mata kallon ƙasan ido. zama tayi, tana cewa "to ai shi kena", ta fada tana daukar wayarta, Jamseey kuwa dariya tayi a ƙasan ranta tare da cewa "shashasha haka zanta miki rijiya kina fadawa, tunda ke baki da wayau", ta fada tana yar dariya a fili. rai ɓace Haleesa ta fito daga ɗakin ,zama tayi gefen Adda Zainab , kallonta tayo tare da ce wa "lafiya? ina Sadiyyar?", ta fada tana kallonta, taɓe baki tayi tare da cewa "tana zuwa", zama suka ci gaba dayi, suna Yar fira tsakaninsu, kusan 1hour suna gurin, kallonsu Adda Zainab tayi tare da cewa "ni dai bari na shiga na dubo Ƴar nan, shiru har yanzu bata fito ba", ta fada tana yin hanyar sashen Sadiyya. Dan murmushi ne ya suɓecewa Haleesa, dan tasan Adda Zainab bata daukar raini, dan ko Hameed din baya kawo mata wargi , tana tafe tana mamakin kiɗan da take ji yana tashi, daga cikin bedroom din Sadiyya, alamar tana nan kuma lafiya,dan da bata da lafiya da ba zata ji kiɗa ba, kuma tana da tabbacin Haleesa ta sanar da ita zuwansu. tura ƙofar bedroom din tayi, da masifa Sadiyya ta juyo, dan ta dauka Haleesa ce ta sauƙe mata kwandon bala'inta, ido biyu tayi da Adda Zainab, tuni masifa da bala'inta, suka koma ciki dan wani kwarji da ta gani akan fuskar Adda Zainab din yasa ta haɗiye duk abun da yake bakinta. dan murmushin da baikai ciki ba tayi tare da cewa "Sannu da zuwa Adda", kallo ta ƙare mata tare da cewa "Sadiyya..!", cikim kama kai ta ce "Na'am Adda!". "ba kiji zuwan mu bane?", ta fada tana ƙara tsareta da ido, shiru ta danyi kafin tace "ban ji ba", jinjina kanta tayi tare da cewa "Haleesa bata shigo ta fada miki ba?", dan sosa kai tayi tare da cewa "ta shigo amma na dauka wasa take ba da gaske ba", ta fada tana dan tura baki. "Sadiyya ya akayi kika koma haka?", ta fada tana haɗe ranta, shiru Sadiyya tayi bata ce komai ba, tsawa ta daka mata tare da cewa "kin zama Aura! kin zama ballagaza!! kin zama jakka, ki duba ki gani yanzu nan wai gurin kwanan bawa ne, shin wai da da kina gidanku haka kikeyi ne?, ko kuwa raini ne da iskanci yasa kike yin haka anan?, baki san komai na gidanki ba, ina da tabbacin ko girki dakyar in kin iya, tun da dai har kina zaune da ranki da lafiyarki, amma ba zaki iya kula da gidanki ba, ko sai an kawo wata kafin ki ringa hauka kina ƙururuwar , tare da cewa an cuceki, to wallahi ki zauna da hankalinki in ba haka ba uhmmmm", ta fada tana sakin wani kill smile irin na you will see. rai ɓace itama ta fito, kallonsu tayi tare da cewa "Muje", ta fada tana nufar ƙofa, "lafiya Adda?", Adda Nafisa ta fada tana kallonta, bata ko kulata ba ta fice, mikewa dukkansu sukayi suka fice babu wanda ya ƙara bi ta kan Sadiyya, Motocinsu suka shiga tare da ficewa a gidan. gidan Hajiya suka koma, a zaune suka tarar da ita tana jaan casbaha, zama sukayi gefenta tare da gaisheta, amsawa tayi, kafin su fara fira, Adda Zainab dai na zaune abun duniya ya Addabi ranta, jin tayi shiru yasa Hajiya kallonta tace "kina Lafiya kuwa Zainab?", firgigit ta juyo ta kalli Mahaifiyar tasu, rausayar da kanta tayi tare da cewa "Hajiya Aure nake tunanin in da zan nemar wa Autanki", ta fada tana gyara zama. duk kallonta sukayi cike da mamaki, "Aure kuma?", Hajiya ta fada tana ƙare mata kallo, da son gasgata abun da take fada, jinjina kanta tayi Alamar tabbas, "Hajiya duba da yarda Hameed yake gudanar da rayuwarshi da da yanzu ba daya ba, tun daga haka yaci ace kun gane yana cikin matsala, bashi da wani kwanciyar hankali, kullum sai zuƙewa yake, shi yasa nakeson ya ƙara aure", ta fada tana kimtse fuskarta, dan ma kar wanda ya kawo mata wargi cikin ƙannen nata. "to da kika je gidan kin fahimci wani abu ne?", dan murmushib taƙaici tayi tare da cewa, "ah'ah kawai", "to ke yanzu wa kike ganin za'a aura mishi a tunaninki?", Hajiya ta fada tana kallonta, shiru tayi tare da cewa "Yarinya Ƙarama wadda ba zata wuce 10 to 11 years ba, dan yanzu ba zai ƙara aurar Babbar mace ba, dan Aurensu da matsala", zare ido Haleesa tayi tare da cewa "Adda mai 10years ai ko sa'ata bata kai ba, wannan ai rainonta zaiyi", ta fada tana kallonta, wani kallo ta aika mata kafin tace "Eyyi na sani, kuma na yanke magana, dan haka bana bukatar wani ƙarin bayani", Shiru Hajiya tayi dan tasan Adda Zainab bata magana biyu, har in tayi magana to ta zauba kamar yankan wuƙa shi yasa babu mai mata musu in tayi magana tayi. "To Allah ya tabbatar da Alkhairi", dan murmushi tayi tare da cewa "Ameen!, sai dai ina son ko anyi Auren ya zamo na Sirri pls, bana son a fadawa Auta", Adda Nabila ce tace "me ne ne Fa'idar mishi Aure bai sani ga, ni a ganina gaskiya hakan bai yi ba, ya kamata ace da saninshi", duk sauran suka ce "Eh gaskiya Adda a fada mishi", karo na farko da ta bar maganarta tabi tasu, jinjina kanta tayi, ta ce "to shi kenan, za'ayi hakan", murmushi Hajiya tayi tare da sa musu Albarrka. suna zaune kira ya shigo wayarta, mika mata Haleesa tayi, karɓa tayi, tare da ƙarawa a kunnenta, "Masha Allah Malam Arabi , Allah ya sanya Alkhairi, insha Allah zamu halarta baki dayan mu", ta fada tana dan murmushi, sallama sukayi ta kashe wayar. kallonsu tayi tare da cewa "gobe akwai sauka da za'ayi da Walima a makarantar da muka buɗe chan Ƙofar Marusa, dukkan ku ku shirya tare zamu tafi", ta fada tana ci gaba da tasbihin ta , Amsa mata sukayi tare da ficewa kowa ya shige ɗakinshi. ****************** ```Washe gari``` Tun da sassafe Nazlah ta fita daga gidan Iya zuwa gidansu, da yake gaba da na Iya kaɗan, tafiya take cikin natsuwa tana karanta Arzikar din safe a hankali cikin ɗaɗɗar muryarta, a wannan lokacin in ka ganta zaka rantse da Allah babu ruwanta da duniya. "Nazilatu Masifatu!", taji an faɗa a bayanta, a fusace ta saki Azikar din da takeyi ta juyo bayanta, harara ta dalla mata tare da cewa "ke! Hasina ki fita a harkata ko naci kutuumar Ubanki tam", ta fada tana juyawa. 07033371851 ```Daga Taskar Yar lelen royal star```` [12/21, 12:10 PM] YAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♂️🧚‍♂️: ☘️☘️ *NAZLAH*☘️☘️ *DAGA AL[]ALAMIN* SALMAJI/[]AR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ *WANNAN LITTAFIN DAGA FARKONSHI HAR KARSHENSHI, SADAUKARWAR NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF) WANNAN LITTAFIN WAKE NA RUBUTASHI, KIYI YADDA KIKESO DASHI, ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI, YA KUMA K'ARA RUFA ASIRI DUNIYA DA LAHEERAH...* *🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟* {R.S.W.A} https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c *_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_* _(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_ *Alk’alaminmu ‘yancinmu* 15-16. """"""""""""""""""Jaawo Hijab dinta taji anyi, dunƙule hannunta tayi tana juyowa ta bugarwa Hasina baki, da sauri ta sakar mata hijab din, tana tarba gaba daya hannunwata a bakinta, ihu ta fasa lokacin da taga jini na fitowa daga cikin bakin, wani abu taji ya faɗo guda biyu, tana ciro hannun ta duba sai ta ga haƙoranta guda biyu a hannunta. cikin mugu²n ta shin hankali ta laluba, zaro idanunta tayi jin haƙora gaba babu su, kuma ta tabbatar da cewa sune suka fita, ihu ta kwada tare da cewa "Wayyo na shiga ukku ta ciremin Haƙora da sanyi safiya", ta fada tana daura hannayenta bibiyu aka. Wata muguwar dariya Nazlah ta kwashe da ita tare da cewa, "ai ba haka na so ba, so nayi gaba daya haƙoran su zube, Allah ne ya soki, amma gaba ki ƙara tara ta ki ga ikon Allah", ta fada tana ci gaba da tafiyarta. baki washe take tafiya, tana cikin tafiyar taji ta ci tuntuɓe, dan tsayawa tayi ta duƙa, kusan 2 minutes sai kuma ta mike ta ci gaba da tafiya fuska a haɗe kamar an aiko mata da sakon mutuwa haka ta ringa tafiya har ta ƙaraso gida, ba ko Sallama ta sanya kai cikin gidan, Ummu ta tarar zaune tana kiciniyar haɗa wuta, bata ko kalleta ba ta shige chan ciki ta samu guri ta zauna, tare da haɗa kai da guiwa ta fara gunjin kuka mai ban tsoro da tayar da hankali. a tsorace kuma cike da mamaki Ummu take kallonta, kamar daga sama Abba ya yakice labulan Dakin Umma ya fito da dorinarshi, yana cewa "wani sabon iskancin ne kika zo dashi yanzu da sassafen nan?, " ya fada yana ware bulalar, shiru tayi ta ci gaba da kukanta, da kana jinshi kasan ba nata bane, "Yau zaki ci ubanki, zan gyara miki zama, tunda baki san mutunci ba", ya fada yana daga bulalar zai zula mata. idanunta da suka rine suka koma jaaazir kamar jini ta watsa mishi, tare da ce wa"doke ni to", ta fada tana kallon cikin idanunshi abun da tunda take bata taɓa yi ba kenan, tun daga nan ya sha jinin jikinshi, "nace ka duke ni", ta fada cikin tsawa, sauke bulalar ya yi, tare da cewa "Allah ya soki kinyi magana yau da kinci ƙaniyarki", ya fada yana jura takalminshi, bai ko tsaya ba ya fice da sauri. Yah Haleem ne ya fito daga ɗaki, kallon inda take ya yi, kallo daya yay mata ya daka mata tsawa, ɗagowa tayi ta kalleshi, suna haɗa idanu tayo maza ta sauke idanunta ƙasa, "zo nan..!", ya fada tana ya fitota, ba musu ta mike izuwa gareshi, tana zuwa gareshi ta zube ƙasa , riƙe kanta ya yi, tare da cewa "mai ya kawoki yanzu da sassafe lau?", ya fada cikin sigar tambaya, cikin kuka tace "tabo mu akayi," ta fada tana kara dukar da kanta ƙasa, jinjina kanshi ya yi, tare da cewa "to kuyi haƙuri ku tafi", ya fada yana sakar mata kan. babu musu ta girgiza kanta alamar to, kafin ta yi mika a hankali da wata sanyayiyar hamma, sai kuma ta fara bin gidan da kallo, inda ta tashi ta koma batawa kowa magana ba, tana kuma zama sai ga Mamar Hasina da Hasina sum shigo Haƙora a hannu, sai zazzaga ruwan masifa suke. Haƙuri Ummu ta fars bawa Maman hasina ,amma kamar ana ƙarawa wuta fetur, sai kaucewa take zata kamo Nazlah, ita kuwa tana inda ta tashi fuska a turɓune in kasar da take gurin ta tanka itama ta tanka,gajiya Ummu tayi da bawa Maman Hasina Haƙuri tayi, ta ce "ga tanan yi mata duk abun da kike jim zaki mata tunda ba zakiyi haƙuri ba",,ta fada tana komawa gefe ta ci gaba da yunƙurin haɗa wutarta a murhu. Mamar hasina kuwakan Nazlah tayi gadan², kafin ta ƙarasa gareta taci tuntunɓe , kafin tayi wani yunƙuri, an yi sama² da ita an bata fettt a ƙasa, tare da fara mulmulata a gurin kai da ganin aikin ƙasan ba ƙaramin ɓata rai ba akayi a gurin, haka Mamar Hasina ta ringa mulmula tana ihu dakyar aka samu ta tsaya, sai da Ummu tayi ta bawa Nazlar haƙuri , Hasina kuwa tuni ta ari na kare, dan tun ɗaga Ummanta tayi waje, bata tsaya ba sai da ta kai gida tana haki, Nazlah kuwa bata ko taɓa Maman Hasina ba Hasalima tana zaune daga inda take ko kallon Maman hasina batayi ba da ta shigo.. dakyar Maman hasina ta mike tare da taimakon Ummu ta fita tana kuka tare da jaan ƙafa, sai da Maman Hasina ta fita kafin ta mike ta shige banɗaki wanka ta sheƙo da ruwan sanyi ta fito , ɗaki ta shiga ta shirya cikin sabbin kayan Makarantar Islamiyya da suka mugun karɓi jikinta suka mata kyau sosai, naɗe gashin kanta tayi,ta mishi kamar acuci maza, fitowa tayi daga ɗakin tana dai-daita sanyin hijab dinta. da tsananin Mamaki Ummu take kallon Nazlah dan ita a iya saninta basu chanja mata Uniform ba kuma bata ga ta shigo dasu ba, kallonta tayi tare da ce wa "Ke..! ina kika samu wannan kayan?", ta fada tana tsura mata idanu cikin wata murya da take nuni da cewa basu tafi ba tace "tambaya ko neman sani?", tunda Ummu taji haka sai ta jaa bakinta tayi shiru. miƙa mata dan gutun koko da ko rabin cup baiyi ba ta ce "Ungo", kallon cikin kofin tayi, dan murmushi tayi tare da ƙarma, matsaw tayi ta jaa kujera, kafa cup din tayi a bakinta , kusan 3 minutes ta sauke cup din tare da sakin sanyyayiyar gyatsa, ajiye cup din tayi, kallon cikin cup din Umma tayi tare da kallonta, jinjina kanta tayi cikin tarin mamaki ganin yarda ta bata kokon haka ta ajiyeshi gashi kuma wai har da gyatsa tayi, mikewa tayi sai da ta kusa ƙofar tace "mun taf..!", tana fadar haka ta fice , tana fita Ummu ta sauke numfashi tare da cewa "Allah gamu gareka..!", kafin ta dauki sauran kokon ta shige ɗaki dashi. A hankali take tafiya, cikin wata natsuwa da ta shigeta Yau din, haka har ta isa Islamiyyarsu da yan tsurarun mutane suka zo Yau din, dan kowa tsoro yake ji, da Bissimillah ta taka cikin Makarantar, batawa kowa magana ba har ta shiga cikin Ajinsu da babu kowa a jiki, layin gaba da shine layinta ita daya ta zauna. Cikin natsuwa tayi Bissimillah tare da fara rero karatuj Al-qur'ani mai girma cikin bawa ko wane harafi haƙƙinsa, bata bari ta shiga haƙƙin ko wane, haka ta ringa rerowa wanda da,kaki zakasan Allah ya mata baiwa bayan baiwar tata kuma akwai taimakon wasu mutaman daban. tana cikin Karatun Yan ajinsu suka fara shigowa, nayi mamaki na ganinsu, dan manya² ne yan Ajin nasu, dan wasu ko hasu haifeta ba, to sun girme mata nesa ba kusa ba, zama sukayi tare da fara labarinsu suna shewa da dariya, tsayar da karatun nata tayi tare da cewa "Amma nasan kunji da kunnanku karatu muke ko?", ta fada cikin sanyin murya, Hauwa'u ce tace "to sai me dan karatu kike, kinsan dai ba zaki hanamu labarin Saukarmu ba ko k...", idanunta ne suka fara ƙaƙƙafewa maganar da ta fara ta kasa karasawa, wata kumfa ta fara fitowa daga bakinta, da sauri duk yan ajin suka fice suna ihun neman taimako, ita,kuwa Oganninyar Zamanta ta gyara tare da ci gaba da karatunta, cikin suratul ```BAQARA``` dan har ta,kusa kaiwa karshen shafin karshe. Malam Abbakar da ya,kasance shine Malamin Ajin mai koyar dasu Al-qur'ani ne ya shigo cikin ajin, yana kallon yarda Hauwa'u ta kaƙƙafe yasa aikin Nazlah ne da yake sun mishi bayanin abun da ya faru, kuna shi yasan Nazlah na da mutanan Boye tun ba yanzu ba, duba da yarda yake musu karatu ta dauke a jikin biyawar farko gashi in zata bashi hadda har sai ta ƙaranta inda bai musu ba, wannan kwazon nata yasa aka daukota daga ajin da take aka dawo da ita wannan ajin dan tafi Ɗaliban ajin karatu da mayar da hankali, har mamaki take bawa Malamai gurin karatu dan har gyara take cinsu. " bana son haka, Saketa...!", ya fada yana zama kan kujera, dukar da kanta tayi dan tana tsananin jin kunyarshi da ganin mutuncinshi, cikib siririyar murya ta ce "in har bata dai na surutu ana karatu ba, wallahi ba zata ƙara magana ba har duniya ta naɗe", ta fads tana juya idanunta, sai ga Hauwa'u tana zazzzare ido an sakar mata maƙogwaro. dan murmushi ya yi , tare da fara amsar karatun da zasu gurin Sauka, bai karɓi na Nazlah ba dan yasan bashi da matsala da ita, sai dai sai kallonta yake, dan yajin labarin abun da ya faru jiya da Malamai, sai dai bai yi wani jimami ba sai Allah kara da ya musu dan Malam, basa da,kirki babu abun da suka ajiye sai cutar Yara. . baya sun gama Karatu aka tattauba yarda abubuwan sauka zasu kasance a gobe, kafin a tashesu su fice, direct gida ta nufa cikin farin cikin da ta rasa ko na me ne ne. tana zuwa ta faɗa jikin Ummu da take tunanib, yarda zatayo da su dan Yau basu da ko kwayar hatsi da zasu ci abin ci gashi tasan Nazlah da yunwa zata dawo firgigit ta dawo daga duniyar tunanin da ta tafi, kallonta tayi tare da cewa "har kin dawo..!?", gyads kanta tayi tare da cewa "Ummu Saukar mu fa gobe banga ana shirye² ba", ta fada tana kallon cikin gidan. Dan murmushi da bai kai ciki ba tayi tare da cewa , "muna nan muna yi", ta fada tana shafa kanta, shiru tayi bata ce komai ba, haka suka ci gaba da zama shiru, sun ɗan jima haka kafin Ummu tace "tashi kije gidan Iya kice ina gaisheta", mikewa tayi tana murna da tsalle ta fice, bin bayanta da kallo tayi tana jinjina irin wannan Yarinta ta Nazlah shekara 10 cikin ta sha daya amma bata daina sakalci ba, tana tsoron ranar da zata faɗi (period) batayi hankali ba. ba tayi 5mimutes da fita ba, ta shigo da kaya riƙi² a hannunta, har tana zubar da wasu da babbat kula, ajiyewa tayi a gaban Ummu tare da cewa "gashi...!", tana ajiyewa ta shige ɗaki, Ummu na magana amma bata tsaya ba, mikewa tayi ta bita ciki da niyyar tambayarta daga ina. tana shiga ta nemeta sama ko ƙasa babu ita babu labarinta, duddubawa ta shiga yi har ƙasan gadonta amma batanan, gabanta taji ya faɗi , dandanan wani tunani taji ya darsu a ranta, hakan yasa ta fice tare da zarar gyalenta ,tayi gaba zuwa gidan Iya. tana fita Abba ya shigo, ganin kaya zube a banza, sai ya kwashe ya fice, kai tsaye dandalin cacarsu ya nufa, yana zuwa ya tarar da wani ya sanya kuɗi duba biyar, kawai shima sai ya miƙa kayan, ya zauna aka fara bugawa dashi. ko da ta ƙarasa gidan Iya zama tayi suka fara firarsu, suna dariya tare da wani gwaranci da su kaɗai suke iya gane kanshi ,ko ince mutanansu ne kawai suke iya gane kanshi, dan mutanan kan Iya sune suka koma kan Nazlah saboda kaunar da take mata. cikin sauri Ummu ta tura kanta cikin gidan, ganinta zaune yasa ta ja burki tana sauke numfashi, cike da tsoro wace ce wacchan din?, ta tambayi kanta cikin ruɗu,shi ko mutanan Nazlar ne har suka chanja mata salo da haka?, kallonta Iya tayi tare da cewa "Ƙara so mana", girgiza kanta tayi, tare da ce wa "Iya bai san na fito ba", ta fada tana juyawa ta fice. Ummu tana zuwa ta tarar babu kaya , iya tashin hankali ta shiga, tasan dai ba mutanan suka zo suka dauki kayan ba , sai dai in Abba ne zai shigo ya dauka, bata ko zauna ba sai gashi ya shigo, bashi ga tsuntsu bashu ga tarko, dan ya zuba kayan am cinyeshi, shi kuma bai cin komai ba ,kasa ta zube tare da gaishe shi , amsawa ya yi a yatsine cikin fusata, dukar da kanta tayi tare da cewa "Dan Allah ko kaga kaya ɗazun akan taburma?" ta fada kanta na karayin ƙasa. wani banzan kallo ya watsa mata tare da ce wa "Eh na gani kuma na zuba su A caca, ko a kwai yarda za'ayi da ni," da bala'in sauri ta dago idanuta , sai dai bata iya cewa komai ba, bata san yarda zata fada mishi haɗarin kayan ba, bayan Sallah Isha Nazlah ta tattara komatsanta ta tafi gidansu. ``` Washe gari``` Tun Asuba Nazlah ta farka, tana ta yan tattare- tattarenta , bayan ta gama ta tashi Ummu dama Abba ba gidan ya kwana ba, bayan sunyi Sallah da Azkae din sade, tayi Karatun Al-qur'ani. bayan ta gama ta kalli Ummu tace "Ummu ina Kayan Abin ci a daura kar lokaci ya kure mana?", shiru Ummu tayi bata ce komai ba, ƙara tambayarta tayi, juyowa tayi ta kalleta kafin tace "Babanki ya daukesu, a harzuƙe ta kalli Umma sai kuma ta fice, bata jima ba, Ummu taji ƙarar ɓuruntunta , tana fitowa ta tarae tana kiciniyar daura tukunya ga kanyan Abincin na zube a gabanta. iya tashin hankali Ummu ta shiga, dan bata son Abubuwan ban su bude wa Nazlah ido, dama ta lafiyar kura balle kuma tayi hauka, tayata tayi suka daura, dandanan suka gama duk abun da ya dace, har wanka da sauransu. bayan Nazlah tayi wanka Ummu rasa kaya da zata bata ta sanya tayi, dan bata mata Ankon Saukar ba, haka yasa ta kasa shiga ɗakin da ba tasan mai zata ce mata ba, tana tsaye ta fito cikin shigar Atamfa super da ta mata kyau kwarai da gaske kalar green da farar hijab dinta da takalminta, tayi kyau sosai sai walwali take, dan ma wai babu kitso balle lalle, dan mutananta bata so ko kaɗan. Karo na farko da tayi Alfahari da mutanan Nazlah dan sun fitar da ita kunya, ko da ta shiga itama sabbin kaya ta gani ajiye, da ƙin sawa tayi, sai kuma wata zuciyar ta ce "Allah ne fa ya cida ki ki sa kawai" ,sawa tayi itama ta fito garau da ita, Yah Haleem ma cikin kyakyawar shiga ya shigo gidan da wasu Yara, su suka dauki Abincin suka tafi gurin Saukar. cike damkam suka tarar da gurin dan saukar bata mutum daya bace ta kusan mutum Ashirin ce, ga kuma gayyar manya mutane, dakyar suka samu hanyar shiga cikin taron, Nazlah sai wangale baki take tana magana ita daya, nikam nace ```tab wannan taron ai dole ma da Gayyarki ciki```… Guri suka samu suka zauna, ita kuwa gurin Ɗalibai Yan uwanta ta nufa, zama tayi kafin su gaggaisa, cikin Yar raha. ********* tun da sassafe Hajiya ta kira Hameed ta shaida mishi batun Saukar da za'ayi, haka yasa ya turo da kyautarshi ta Malamai da wuri, tare da manyan kyatutuka da ya shirya domin bayarwa ga Daliban sa sukayi saukar , Duka yan Uwanshi suma sai da suka sanya gudumuwarsu a ciki, dan dama makarantar kusan haɗin guiwa ne dasu, sai dai kuɗinshi sun fi yawa a ciki , dan shi yake biyan Malam duk wata. shi kuwa sai misalin 10am ya shigo cikin gidan da Sallamarshi sai baza kamshin turaren Giorgio Armani, yake cikin kwarjini da cikar haiba yake takawa zuwa cikin palon, inda suke zaune suna jiranshi, gaishesu ya yi Ƙanan suka gaisheshi, amsawa musu ya yi,yana zama kusa da Hajiya tare da daura kanshi a kafaɗarta, shafa kanshi tayi tare da cewa "Auta ka taushe hannu, kai kawai muke jira tun dazun", ta fada tana yunkurawa zata mike, kallon Adda Zainab ya yi, tare da ce wa "Adda ki ɗiba kin break fast mana",ya fada yana binsu da kallo. kallonsu suk Adda Zainab tayi, suma suka kalleta kafin ta ce "To ina matar gidan? da ta bar mijinta da yunwa..!", shiru ya yi alama baya son zancen hakan ya tilasta mata yin shiru itama, sai da ta diɓar mishi kafin su fice, mota huɗu sukayi Adda Zainab da Hameed daya, Hajiya da Adda Nabila da Adda Nafisa daya, sai Haleesa da Yaran su Adda daya, sai dayar kuma Sojojin Hameed ne a ciki . kai tsaye makaranta suka nufa , basu dau wani dogon lokaci ba suka ƙarasa dan tsakanin Unguwarsu Hajiya da Makarantar ba nisa sosai,suna shiga ciki aka basu hanya, suka shiga, ganinsu yasa gaba daya Malaman suka mike zuwa taryarsu, bayan gama gaishe-gaishe aka samu gurin da aka tanadar musu mai AC da Fanka, cikin rumfa, Nazlah tun da taji karar shigowar Motoci zuciyarta tayi wani mugun bugawa da karfi, hakan yasa ta dafe saitin. bayan gama bude taro da Addu'a wanda Nazlah tayi , da gabatar da baƙi da Malam Abbakar ya yi, sai aka danyi drama ta larabci wanda shima har da Nazlah wadda ita take jaan ragamar drama ,bayan ta gama aka fara karatun sauka, wanda Nazlah aka fara kira ,,cikin natsuwa ta hau kan munbari, fuskarta a bude tar ta,karayin wani fari, sauran kuwa duk da niƙaf ita kuwa bata sanyawa dan numfashinta daukewa yake in ta sanya, cikin ƙira'arta mai dadi ra fara karatu wanda duk wanda yake gurin hankalinshi da idanunshi na kanta ,amma banda Hameed da kanshi na ƙasa saurararta kawai yake, har ta gama ba'a cita gyaran ko wasali daya ba,balle akai ga fidda kalkala dan tasan inda haƙƙoƙinsu suke, kuma tana kiyayesu . bayan ta gana aka kikkira Abokan saukarta, suma sukayi, sai sai Yawan cinsu duk da akwai kura-kurai a cikin karatunsu, bayan sun gama aka basu kyauttuka, wanda Nazlah tafi kowa samun kyauta mai tsoka, bayan bada kyattutuka da bada shahada, aka kira Nazlah again domin gabatar da Nasiha ga mutane, cikin gajiyawa ta kara hawa munbarin, cikin wata murya mai dadi ta fara magana, muryar da ko baka kaunar Uwarka da Ubanka in ka jita sai ka kaunaci mai ita ta fara magana, wanda yasa Hameed ya dago idanunshi ya dubi inda ake maganar, sai da gabanshi ya faɗi, dan kamar ance su kalli juna su biyun, kusan 30 seconds idanunsu na cikin na juna kafin ta jaanye idanunta, shi kuwa bai iya daukewa ba dan zalar mamaki ya cika mishi zuciya ganin Yar Yarinyar da take raira wannan karatu da tafseer duk a lokaci daya gashi komai za'ayi sai an kirata. bayan ta gama Adda Zainab da karɓi Laundspeaker ta jaaddada godiya ga Iyayen Yaran da sukayi Sauka da bada kyauttutukanta, da jaddada Albarka a gesu, duk a cikim harshen larabci, sai da ta gama kaf kafin ta kira sunan Nazlah Lawal, a hankali Nazlah ta dago da gajiyyayun idanunta ta kalleta, alama ta mata da tazo, mukewa tayo tazo har gabanta kafin ta sunkutar da kanta kasa alamar girnamawa. Cheack din 2 millions ta damƙa mata a hannu, tare da kara sanya mata albarka, dan Yarinyar ta bala'in burgeta ta kuma shiga ranta, har ƙasa Nazlah ta duƙa tanawa Adda Zainab godiya........... 07033371851 ```DAGA TASKAR ƳAR LELEN ROTAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️``` [12/21, 12:11 PM] YAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♂️🧚‍♂️: ☘️☘️ *NAZLAH*☘️☘️ *DAGA AL[]ALAMIN* SALMAJI/[]AR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️ *WANNAN LITTAFIN DAGA FARKONSHI HAR KARSHENSHI, SADAUKARWAR NE GA YAYATAH (MARYAM YUSUF) WANNAN LITTAFIN WAKE NA RUBUTASHI, KIYI YADDA KIKESO DASHI, ALLAH YA RAYA MIKI ZURI'ARKI, YA KUMA K'ARA RUFA ASIRI DUNIYA DA LAHEERAH...* *🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟* {R.S.W.A} https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c *_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_* _(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_ *Alk’alaminmu ‘yancinmu* 17-18. """"""""""Shafa kanta tayi, tare da girguza kanta alamar ta daina mata godiya haka. sosai Nazlah tasha kyattutuka na ban mamaki, dan daga ko wane sashe kawo mata kyauta ake har mutananta sai da suka minmiko mata, su kansu su Adda Nabila Yarinyar ta burgesu, haka aka tashi kowa da mamakin Nazlah da burgeshi a cikin ranshi. Su Nazlah kuwa haka suka dauki niƙi-niƙin kayyayakin kyauttutu kansu , suka tafi gida, sai dai Abun Mamaki bayan sun shiga gida suna shiga Ɗaki suka ci karo da kyauttutuka na ban mamaki ajiye tulugu guda, da kallo Ummu take bin kayan kafin ta kalli Yah Haleem tace "Haleem abun nan ya fara tsorata ni da yawa, mutanan nan so suke su kashe ni da tsoro, ɗiɓe kayan nan ka fice dasu", ta fada tana zama kan Yangwananniyar Katifar da take gefe. Yah Haleem na kai hannu zai dauka, Nazlah ta rike hannunshi, ta re da cewa "Bandirawo dai na,,wannan kyauta ce ba'a mayar da hannun kyauta baya ,shaidan ne kawai yake mayar da kyauta in an mishi", ta fada kanta *ƘAASA*. Cikin Hasala Ummu tace "zaki bari a fita da su ko sai na saɓa miki?", ta fada cikin bada umarni, kallon Ummu tayi kafin tace "Ummu kar a fitar da kayan nan kyauta ce aka kawo mata, in kuma aka fitar dasu to duk abun da ya biyo baya ba ruwana , domin wannan ba daga ni bane daga Sarki ne", ta fada tana komawa gefe ta zauna, kallon Ummu Yah Haleem ya yi, itama ta kalleshi , sai kuma suka kalli Nazlah da ta duƙar da kanta ƙasa tana kallon Kyauttutukan da suka shigo da su. "A fita da su?", Yah Haleem ya fada yana kallon Ummu, girgiza kanta tayi, tare da cewa "ka barsu", kallon Ummun Nazlah tayi kafin ta mike ta fice daga ɗakin , tana fita tsakar gida ta cire dan kwalinta da hijab ta fada banɗaki,bayan Nazlah ta fita Ummu tace "Haleem ya za muuyi da kayan nan, kasan Mahaifinku da ya shigo zai tattarasu ya tafi da su chan ya salwantar dasu , mai shawara?", ta fada tana kallomshi. jinjina kanshi ya yi, tare da cewa "to ko mu kai gidan Iya sai a ajiye ?, kin ga ba zai bi kayan chan ba", ya fada yana kallon uwayen kayan da suka kusan cika dakin, dan ɗakin ba wani mai girma bane sosai, jijjiga kai tayi tare da cewa "hakan kawai za'a y.....!!", bata ƙarasa ba suka ji Nazlah ta kwala ƙara. da sauri jikimsu har mazari yake suka fito suna rige², turus Ummu tayi tana kallon Hijab da Dan kwallin Nazlah da yake yashe a gurin, Yah Haleem kuwa toiler din ya nufa dan daga ciki yake jiyo ihun ta. yana shiga ya tarar da ita ƙasa yashe tana burgima da ihu, dakyar ta iya cicciɓarta ya fito da ita sa boda wani nauyi da tayi, ɗakin Ummu ya shiga da ita, tare da shimfiɗeta a ƙasa, "mai haka!", Yah Haleem ya fada cikin ɓacin rai, ganin yarda ya haɗe ranshi ya yi kicin²,yasa Nazlah cewa "Murna muka zo..!" , ta fada tana ci gaba da burgima. tsawa ya daka mata tare da cewa " haka ake murnan?, kuma tun ɗazun mai yasa baku zo ba, lokacin da kowa yake taya murnar sai yanzu?, shin kunzo ne domin ku dagula mata lissafi ko kuwa kunzo ne domin ɓata mata ranar farin cikinta?", ya fada cikin ɓacin rai. girgiza kai tayi tare da ce wa"bamu da ikon zuwa a wannan lokacin domin Sarkin Musulamai ne a gurin, ba muzo dan dagula mata lissafi ba, hasali ma murna muka zo tayata akan wata murnan, amma zamu tafi ", ta fada tana daga kai zata yi Atishawa, saurin dakatar da ita ya yi , ta hanyar daka mata tsawa, da sauri ta natsu, cikin kaushin murya yace "mai yasa kuka fara bayyana kan ku tun yanzu?,ko kuna son nakasa mata rayuwa ne?", ya ƙarasa fada cikin rauni. shiru tayi kafin ta ce "lokacin bayyanar mu ne baiyi ba sai yanzu, da ya yi da tuntuni mum bayyana, ko da yake dama muna a laɓe gane mune kawai ba'ayi ba sai yanzu, kuma mu dan Allah kayi haƙuri kun tafu", tana kai wa nan tayi atishawa da karfi ba tare da ta bari ya ƙarayin wata magana ba. shimfiɗeta ya yi, tare da fitowa, ajiyar Zuciya Ummu ta sauke tare da raɓawa gefe daya ta zauna, abun duniya ya mata yawa, kallonta Yah Haleem ya yu, tare da ce wa "kar ki sanya damuwa a ranki, ni bari na fita, na samu mana abun da zamu ci",ya fada yana yin gaba, da fatan Alkhairi ta bishi , yana fita Abba ya shigo yana washe baki, kallonta ya yi, tare da ce wa "Ummun su sannu da hutawa", dagowa tayi baki bude tana kallonshi, zama ya yi a gefenta tare da ce wa "ina chan ina buga caca naji wani abun Alkhairi da ya sauka, ni ban ma san zatayi sauka ba, wai waya ma sanyata makarantar, ina kayan suke", dan tsananin takaici da mamaki kasa magana tayi, sai ta tyna lokacin da ta fada mishi za'a sanya Yarinyar Makaranta ya je ya kaita, sai cewa ya yi "na kai wa? wannan shegiya?, ni fa bana kaunarta, in ma kika kaita kukayi Amfani da sunana Ban yafe ba", har ƙasa ta zuƙunna rana rokonshi yaƙi, sai dai Haleem ya kaita aka yi mata register da sunansa, amma yanzu sai gashi wai yazo a bashi abun da ta samu. "bakya ji ina miki magana kika yi shiru?",,Abba ya daka mata tsawa, Iya da take shigowa tace "To Ubanka zata ce maka in baya yi shiru ba Wallahi Lawan ka kiyayeni , na ce ka fita a idona na rufe", ta fada tana shigowa cikin hasala, da ɓacin rai. "to wai Iya mai yasa kike so ki shiga tsakanina da Iyalina ne, ba fa na son haka", ya fada cikin daga murya shima, "Eyyi dama in baka yi haka ba ai baka cika da Mu'azu ba, to bari na fada,maka sisi ba zaka samu ba a cikin abun da Yarinyar nan ta samu, dan bakasan komai na,karatunta ba", ta fada tana shigewa ciki. kayan ta tattara cikin buhu ta dauka ta fice dasu waje , Yara ta dinga ɗiba tana ba mawa suna kai mata gida, har ta jide tsaf , Lawan kuwa yana zaune cike da baƙin ciki, dan wata caca zasu buga da wani Alhaji da ya sa 50k , shbe yazo ya kwashi abun da suka samo ya kai, dan ya zauna ayi c'ac'ar dashi. ```BAYAN KWANA BIYU``` Kullum Adda Zainab da Nazlah take kwana, take tashi da ita a cikin ranta, ga kuma abun Hameed kullum gani take yana ƙara ta'azzara. kamar kullum suna zaune cikin palo, suna fira, Haleesa ce tace "Wai ni kam Adda , ya batun nemawa Auta Mata yar 10years kin fasa ne ko ya?, gaba baki ƙara maganar ba!,"numfashi ta sauke kafin ta ce "bawai na fasa ba har yanzu ina kan bakana" , da sauri Adda Nabila tace ",Ni kam Adda mu gwada sa'ar mu akan Yarinyar nan mana", duk kallonta suka yi kafin Adda Nafisa tace "wace Yarinya..!?", dan murmushi tayi kafin tace "Hafizar nan mana Nazlah", tsalle Haleesa ta buga tare da ce wa "Wallahi kuwa nima tunani nake a kanta, dan Allah Adda",,ta fada tana dan yi fuskar tausayi. Jinjina kanta tayi, tare da cewa "nima ita nake tunani, amma bari na fadawa Hajiya in ta aminta da ita gobe ba sai muje ba", ta fada tana mikewa, duk bin bayanta sukayi, dan zuwa ɗakin mahaifiyarsu, zaune suka sameta tana karatun Al-qur'ani, zama sukayi a gefenta, suna saurarob Daddadar muryar Mahaifiyar tasu da ta ƙara dadi da tana karatun, sai da ta kai karshen page din da take, kafin ta tsaya tana kallonsu, ta cikin Eyesglass dinta, ganin yarda suka natsu yasa ta zare glass din , ta tattara gaba daya hankalinta garesu. Adda Zainab ce ta matsa tare da riƙeta, Alamar magana mai muhimmanci zata fada mata, dan murmushi tayi kafin tace "ina sauraronki daga gani akwai magana mai muhimmamci a bakin ki", ta fada tana kallon sauran, duk murmushi sukayi , gyaran murya tayi tare da cewa "Hajiya akan Maganar Auran Autanki, mu mun ga dacewa da natsuwar Yarinyar nan Nazlah, kuma munyi sha'awar zamanta a cikin Ahalinmu, shine muka zo mu fada miki", tun da Adda Zainab ta fara magana Hajiya ta zuba mata idanunta, sai da ta kai karshen bayaninta ta sauke numfashi tare da cewa "Uhmm Zainab, lallai kam nima sai da na ayyana hakan a cikin raina, sai dai wannan Yarinyar tawa Auta Ƙanƙanta, ba zata iya dauke buƙatunshi ba, za'a iya cutar da ita, ke kanki kinsan Auta yana da buƙatuwa sosai, bakya ganin za'a tauyeta ,"shiru ta dan yi, kafin tace "Hajiya ina ji a raina Yarinyar nan ba zata cutu ba har an ta aureshi, sannan ina da yaƙin cewa zai kula da ita, kuma dama ai Miji shi yake koyawa Matarshi komai, in ma ragwanci ko Jarumta, dan haka ina ganin babu wata matsala, domin Yarinyar nan tana da ilimin Addini, ina da yaƙinin ba zata taɓa kauce hanya ba, kuma zata,kula dashi, dan tasan haƙƙin miji akan matarshi, idan kin Amince gobe muje gidansu", ta fada tana kara damke hannunta. Numfashi ta sauke kafin tace "toshi kenan", fa fada tana ci gaba da karatunta, da murnarsu suka fito, bayan sun fito kuma Adda Zainab ta cewa Haleesa "An somin Wayar Hajiya na kira Malaminsu ", ta fada tana daukar wayarta. da sauri Haleesa ta mike, ta karɓo mata, kiran Malam Arabi tayi akan gove zasu zo, cikin rawar jiki ya amsa musu, dan yasan suka zo zai kwashi damje gidanshi, dan basa zuwa su tafi basu dan lafa mishi wani abu ba, su kuwa firar Nazlah suka ci gaba da yi. Washe gari guraren 4pm sukawa gidansu Nazlah Dirar mikiya da taimakon Malam Arabi da ya rakosu har gidan, bayan sun zo gidan ya tsaya a waje su kuma suka shiga ciki. da Sallama suka shiga , suna shiga suka tarar da Nazlah na shara, Ummu na gefe tana duba Azkar, Sallamar su ce tasa Nazlah dago kanta tana dubansu,washe baki tayi tare da cewa "Ah'ah sannun ku da zuwa, maraba lalle, ku shigo", ta fada tana nuna musu hanya. taburma ta shimfiɗa musu suka zauna, kafin ta gaishesucikin mutunci suka gaggaisa, Adda Zainab ce ta ce "Uhmm dama gaisuwa muka zo da rokon iri", cikin rashi fahimta Ummu tace "too gaisuwa da roƙon Iri kuma Hajiya?, ban gane mai kike nufi ba", ta fada tana gyara zamanta. dan gutun murmushi tayi tare da cewa, "Ƴa muke so ki bamu",shiru Ummu tayi tare da cewa "anya kuwa nan gidan?, dan nan gidan babu wata Babbar Ƴa mace sai Nazlah, sai dai ko gidan gaba va nan ba", Yar dariya tayi tare da cewa "ita din nake nufi", rike baki Ummu tayi tare da cewa. "to a gaskiya wannan ba magana ta bace, amma bari na aika a kira muku Iya sai kuyi magana da ita, ta fada tana kwalawa Nazlah da ta shige ɗaki da Ƴar Adda Zainab karama kira. Amsa mata tayi kafin ta fito, goye da Yarinyar a bayanta, dan murmushi Ummu tayi, dan tasan Nazlah da mugun son Yara, ga son ta daukesu, sai dai fa har in ta miƙawa Yaro hannu ya mata ƙuya tofa ba,zata ji kunya ba, gsban uwar ɗa zata makeshi, in kuwa yazo ta ringa lelenshi kenan tana goyashi, da bashi abubuwan wasa da na ciye-ciye hakan yasa Ummu tai hamdalah lokacin da Ƴar Adda Zainab ta miƙawa Nazlah hannu bayan ta miko mata. gaban Ummu ta zauna, tare da cewa "Ummu ga ni..!", kallonta tayi tare da ce wa "Iya zaki kira min, kice tazo Anyi Baƙi, suna son Magana da ita", kallon Ummu Adda Nabila tayi, kafin tace "to ki bari kawai sai muje chan din, kar a ƙatse mata wani aiki da take yi ", ta fada tana mikewa. murmushi Ummu ta mata, dan dama ta rasa yarda zata ce su tafi chan din ne yasa tace a kirata, da tasan yanzu gab Abba yaje da dawowa daga gurin Cacarshi, mikewa sukayi Nazlah ta sanya Yan takalmanta Sino suka fice daga gidan. tafiya suka fara yi zuwa gidan Iya, suna tafiya tana musu Yar fira da yake Nazlah ba dai labari ba, suna cikin tafiya suka haɗu da Hasina, harararta Nazlah tayi , kallonta Adda Zainab tayi tare da cewa "mai ta miki kika harareta ?", yar dariya tayi kafin tace "Bata jin Magana ne to ina dai-daita mata zama ne," ta fada dai-dai lokacin da suka shigo gidan Iya. Da Sallama Nazlah ta fara kutsa kai cikin gidan, Iya da take zaune tana cin gujiya ta amsa musu, tare da cewa "Ƴar Halak kinki Ambato tun safe sai yanzu?", lokacin da ta kai karshen maganarta ne kuma ta hango su Adda zainab. Washe baki tayu tare da cewa !Ah'ah Ashe da baƙi kuke tafe, Maraba lalle sannunku da zuwa", ta fada tana wangale musu taburmar da take zaune kai, zama sukayi suna gaisheta, da fara'a sosai a kan fuskarta ta amsa musu, Gujiyar gabanta ta mika musu tare da cewa "Bissimillan ku", Adda zainab ce tace "Aaaaaah Gujiya ai kam zamu ci, dan ni ha dade banci gujiya ba"ta fada tana daukar daya. kara mika kwanon gujiyar tayi sosai gabanta, tare da cewa "ku ci dan Allah, ai gujiya abar marmari ce, nima na fita naganta shine na siyo na dafa " ,ta fads tana washe baki dan sam bata da rowar abun ta. ci suka fara yi, Adda zainab ce ta kalleta tare da cewa "kar kuma mu cinyewa Yar tsohuwa abin ta", ta fada tana yar dariya, dan akwai ta da raha, "Ke..! Nazlatu dauki ki ƙaro musu ma cikin tukunya", ta fada tana kallonta, dauka tayi ta ƙaro , tare da dibo musu ita da Haleesa, kallonta tayi ta washe Yan ƙananan fararen haƙoranta masu kyau tace "Zo muci anan ki bar manya su ci nasu", ta fada tana ajiye musu. matsawa tayi suka fara ci a tare, Su Adda kuwa suna ci suna yiwa Iya fira ana dariya, a lokacin in ka gansu sai kayi zaton sunyi irin 20years dinnan a tare , sa boda dukkansu, suna da fara'a, ga saurin sabo. sai da suka gama ci tas, kafin nazlah ta jaa Haleesa da Yaran su Adda Nabila suka nufi ɗakin Iya, wasa suka fara yi Haleesa na biyesu duk da ta girme musu tana shan dariya. Gyara zama Adda Zainab tayi, kafin ta kwashe duk abin da ya kawosu ta fadawa Iya, shiru Iya tayi tana sauraronsu, har suka kai ƙarshe , numfashi ta sauke tare da cewa "Uhmmmm Banƙi ta taki ba, amma dai Nazlatu Yarinya ce sosai, dan wallahi wannan kayan shiririta ne cike da kanta", ta fada tana kallonsu. dan murmushi duk suka yi kafin tace "hakan nakeso domin nafi son wadda zai raina bawai ta raineshi ba , wadda zai dauka tun tana Yarinyarta ita de wadda ko mai za'a daurata akai ba zata ƙi ba kuma zata saba dashi ta tashi dashi, mu dai muna roƙo da ku bamu, sai dai in va muku ba kuma hankalinku bai kwanta da mu ba, kuma kuna jin bazaku iya haɗa zuri'a damu ba", ta fada tana dan kallon Iya. "Iyeeeee kaji yar butar uwa, mu suwa ye da zamu ƙi haɗa zuri'a daku, ai babu wanda ba zai iya haɗa zuri'a daku ba, tunda kun dage na baku sai dai har sai kun gaji da shiriritarta , Allah ya sawa tarayyar albarka, amma kuma ni ba zan munafurce ku ba, Baban Yarinyar nan bashi da hali mai kyau , dan nasan ko ban faɗa muku ba za'a tareku a fada muku, domin wannan Alaqar Aure ce nasan dole a samu yan baƙin ciki da zasu shiga su fita, in kuwa na fada muku na fita ko ba sabulu", kallon juna suka yi . Adda Nabila ce ta ce "to Iya zamu iya sanin Halin dan kar muji wai-wai a waje", dan murmushin takaici Iya tayi kafin tace "uhmmm halin yan zamani ya sawa kanshi, caca yake da shan sugari, sai dai na tabbata wata rana zai daina dan ba halinshi bane, daga bayan nan abun ya sameshi", ta fada tana kallonsu, da tsoron kar su fasa. "Laaaaah Iya ai wannan ba komai bane, kaddara ce muna mishi fatan Allah ya shiryeshi, kuma hakan ba zaisa mu fasa Aure ba", Adda Nafisa ta fada tana dan murmushi. jinjina kai Iya tayi kafin tace "to shi kenan mun gode da karamcinku garemu, yanzu yaushe kukeson Auren ya kai?, dan ina son na nuna muku na baku Ƴar kamar yarda kuka nuna kaunarku garemu", ta fada tana rike hannun Adda Zainab. "Iya in ba damuwa nan da sati daya, domin zai tafi da ita ne chan gurin aikinshi da yake Soja ne to baya zama gida sai in yazo hutu, kuma bamu buƙatar komai naku domin komai da akwai shi kama daga kan, kayan ɗaki, kayan kitchen da sauransu", Adda Zainab ta fada tana murmushi, jijina kai Iya tayi kai Iya tayi tare da ce wa "to shi kenan mun gode sosai", Fira suka ci gaba da yi, cikin raha tana tsokanarsu suna tsokanarta, har guraren magrib kafin su wuce gida, cike da jin dadin karamcin Iyayen Nazlah gare su. Bayan kwana biyu, suka ririɓo kayan sa biki suka kawo kama daga kan goro,biscuits , sweet , chew gum, da kuɗi na sa rana da sauransu, ranar da aka aiko ranar Abba ya sani, sai dai ya yi ko in kula da maganar da Ummu ta kara tuntuɓarshi ma sai cewa ya yi "ke..! ki ƙyale ni da maganar auren nan, ina ruwa na da wani auren ta, ku da kuka ruruɓo abun ku ku zakuyi, dan wallahi tsinke ba zan bayar ba", ys fada yana ficewarshi, haka Ummu ta zauna Cikin damuwa, da tunanin anya Abba zai chanja halinshi kuwa, tun da ta aureshi take fama dashi bata taɓa jin dadin aure ba a rayuwarta, kuma haka taƙe haƙuri da dauke kai, dan tasan abun da Iya ta mata A rayuwa har abada ba zata iya biyanta ba, shi yasa take yada kai bata taba daga kai ta kalleshi ba, in yana mata abu, kawai ta dauka ita ibada take, kuma mai ibada baya taɓa sarewa, domin Aljanna yake nema. Yah Haleem kuwa da aka fads mishi, sai da ya nuna ƙin amincewarshi dan Yasan Nazlah Yarinya ce sosai , sai dai da Iya ta fatattakeshi ta nuna mishi da Yarda ake Aure sai ya haƙura badan ya so ba, haka akayi ta shirye-shirye, Oganninyar kuwa ita bata wani sani ba tadai ga ana ta ɗura mata abubuwa masu zaƙi ana mata shirye - shirye, amms kwaɗayi da wauta yasa ita duk abun da aka bata ba tambaya take shanyewa sa boda duk masu zaƙi ne. maganin Infection kuwa shine akan gaba wanda ake bata(uhmmm Yan uwa, in har Yarki budurwa ce zatayi Aure, maganin Infection ya kamata ki fara bata, dan shine akan gaba, Maganin Mata babu abun da yake sai tatso ni'imarta ta tattaru guri daya, sannan yana kara dankarar da infection a jiki, in zaki siya maganin mata na dubu 5k to ki siya maganin Sanyi na 15k , domin yanzu ba babba ba Yaro, ba mai kuɗi na talaka, kowa yana fama da wannan ciwon sai dai na wani yafi na wani,infection babban matsala ne,domin yana hana jin dadin Auren, yana sakar da wasu ciwuwukan da dama, sai kiga anyi Aure wata daya, biyu, ukku, an fara samun matsala, Yarinya bata jin dadin aure, ko Mijin baya jin dadin Mu'amulla da matar, sai kiga kwana kaɗan da aure an fara kawo kiki ƙorafe-ƙorafe, shin mai yake kawo wannan matsalar ?, amsan infection, idan mai ba zaki mata maganinshi ba, to karki dura mata kayan mata, dan har gwara ki barta ba ki mata komai ba, dan zai kara yawan infection din a jikinta, sannan zai dakushe mata ni'imarta , kinga kuwa gwara a ki barta haka , Allah dai yasa mu dace, a kula maganin Sanyi shine gaba da na Mata). Ana sauran kwana biyu biki da daddare, Hameed yazo gidan Hajiya, bayan sun gama gaggaisawa Adda Zainab ta jaashi bedroom dinta, kallonshi tayi tare da cewa "Auta...!", kallonta ya yi,yana son yaji mai zata ce. gyara zamanta tayi da kyau tare da cewa "ni na maka katsalandan kuma ina fatan ba zaka bani kunya ba zaka rike zaɓina da hannu bibiyu?", kallonta ya yi cikin rashin fahimta, tare da cewa "katsallandan din mai Adda? ai babu wani katsalandan da zaki a cikin rayuwata, nasan komai zakiyi ba zaki taɓa yi dan ki cutar da ni ba",,murmushi tayi tare da cewa "to naji dadi da ka fahimci haka,kasan ba zan taɓa cutar da kai ba, " jinjina kanshi ya yi. "toh Aure na nema maka, kuma an bamu , jibi daurin aure, sai dai kayi hkr nayi lattin gaya maka", idanunshi ya tsura mata cikin fargaba yace "Adda Aure fa?, duka yaushe nayi wanchan da zaki ce kuma wani aure yanzu?, " wani kallo ta mishi tare da cewa. "ni na nemo kuma an bani ,bani da damuwa da yaushe kayi wanchan, kaje ka ci gaba da shirye-shirye ka dan bama buƙatar komai naka , in kuma ban isa da na zaɓa maka mata ba sai ka faɗa min", ta fada tana tsura mishi idanunta, masu matuƙar kaifi da kwarjini. girgiza kanshi ya yi, tare da cewa "ni bana da sha'awar aure yanzu, hasali ma ni yanzu tsoron mata nake, duba da abubuwan da naga Sadiyya nayi, sai nake ganin kamar duk daya suke", dafa kafadarshi tayi tare da cewa. "na tabbatar wannan ba zata maka abun da Sadiyya take yi ba , ya bawa da tarbiyarta da kamala tare da kwarjini yasa na nema maka ita, kuma kowa ya yi na'am da ita, sannan Yarinya ce danya shataf wadda kai zaka koya mata komai na rayuwa, ka zaka koya mata yarda zata yi kuma duk abun da ka koyar da ita tashi zata tashi", tura baki ya yi gaba tare da cewa "Yar raino zaku bani dai, wadda duk zan koyawa wannan ai sai yar 10 to 12,"ya fada yana kallonta. Yar dariya tayi tare da cewa "to ka kaddara ma mai kamar wannan shekarun ce Yarinyar, " bude baki ya yi yana kallonta kafin yace "Adda 10 to 12 years, to a tatsi mage ko a kashe?,k 07033371851 ```DAGA TASKAR ƳAR LELEN ROYAL STAR``` [12/21, 9:28 PM] YAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♂️🧚‍♂️: 19-20. """""""""""Harararshi tayi tare da cewa "duk ma yarda aka mata dai-dai ne, tunda tona min Asiri kake da niyyar yi", "uhmmmmm ba zaki gane bane Adda girman bukatata ta wuce na Yar 20years ma balle 15, kaya kawai zaku haɗani da shi", ya fada yana mikewa. "ngd kuma ba sai ka gwadamin ban isa da kai ba", ta fada tana haɗe fuskarta alamar tayi fushi, matsawa ya yi kusa da ita, tare da riƙe hannunta yace "Adda na Amince..!", yana fadar haka ya fice daga bedroom din, cike da murna ta fito itama, haɗa baki suka yi gurin cewa "Adda ya amince?", wani kallo ta musu irin na wasa tare da cewa "ko yake jira sai kun amince", ta fada tana zama, dariya duk sukayi dan susan dole ma ne ya amince. Washe gari gaba dayansu suka tafi Saloon , sai da suka je kafin Adda Zainab ta sa driver ya je ya taho da Nazlah , cikin minti kaɗan ya je gidan, kafin ya je ma Nazlah ta shirya dan sun kira Ummu ta Yar kwararraɓar wayarta sun sanar mata,cikin shiga mai kyau Nazlah ta fito sai kamshi take ,mota Driver ya bude mata, shiga tayi ta hakimce a baya, sai da ya rufe kafin ya koma mazaunin driver, ya kunna motae suka kama hanyar shagon saloon din. 15minutes ne ya sadasu da ƙawattacen shagon Saloon din da yake kan Hanyar Kano road , shago ne mai kyau da tsari , na masu kuɗi, bayan sun karasa ya bude mata motar ta fito, jagora ya mata har ciki, da Sallama ta shiga cikin shagon, duk juyowa sukayi da murmushi kan fuskarsu suka amsa mata, ƙarasawa tayi ta ɗuka har ƙasa ta gaishesu, Jaan ta Adda Zainab tayi jikinta ta rungumeta, tare da cewa "kina lafiya Ƙanwar Adda?", ta fada da murmushi kan fuskarta. jinjina kanta tayi alamar lafiya lau, rungumeta suka shiga yi daya bayan daya suna tambayarta lafiyar ta, Haleesa da take mata murmushi tace "Sannu Amaryar Auta..!", dan murmushin yaƙe ta mata dan sam bata fahimci kan maganar ta ta ba, karɓar Ƴar Adda Zainab tayi ta zauna kusa da Haleesa tare da fara ma wasa. Wata Yar siririyar Mata ce ta fito daga wata yar kofa tana cewa "Ayya kuyi hakuri na barku kuna jira na, yanzu me za'a fara muku kuma da wa za'a fara, "ta fada tana dan murmushi. Nuna Nazlah Adda Zainab tayi tare da ce wa "ita zaki fara mawa gyaran jiki zaki mata da gyaran kai, sai ki wanke mata ƙafa , " kallon Nazlah tayi tace "kina son kitso?", da sauri ta girgiza kai alamar bata so, "mai yasa ba za'a miki ba? , zai fi fito da ke", dan kwaɓe fuska tayi tare da cewa "kaina namin ciwo in aka min", ta fada tana matsawa kusa da Mai gyaran jikin. wankin ƙafa aka fara mata, duk da cewa ƙafarta tsaf take ga laushe da tsantsi, hakan yasa da aka wanken sai ta kara kyau da tsari, kumba ta gyara mata ƙafar tayi tarrr² har wani jaa² take kamar jini zai fito, wani ɗaki suka shiga anan aka mata dilka da halawa, komai binshi da ido Nazlah take, dan ita wannan abubuwan bata sansu ba, sai kallon jikinta take, tana mamakin wai ita ce ta koma haka, jikinta ya koma kalar na jarirai, sai shinning yake gwanin burgewa, bayan an gama turara mata jiki da turaren jiki mai kamshi da zama cikin jiki suka fito. duk tsura mata idanu sukayi suna kallon zallar kyau irin na Nazlah dan haskenta ya kara fitowa sosai , dan in kai mata kallo daya ba lallai je ka iya gano daga wace ƙasar ta fito ba, dan kwata² batayi kala da Yan nigeria ba, zaunar da ita tayi gurin da zata wanke mata kai, dan kwallin kanta da tunda tazo bata cire ba Matar ta kama ta fara warwarewa, kyakyawan gashin kanta ne ya fara warwarewa daga gammon da ta mishi. tana zare gammon gashin ya warware gaba dayanshi ya zubo akan bayanta, faɗowa Haleesa ta kusan yi sa boda tsananin mamakin irin yawan gashin kan Nazlah, duk da Ahalinsu na da gashi sosai Amma bata taɓa ganin mai yawan gashi da kyan gashi ba irin na Nazlah, matsawa tayi gurinta jikinta na rawa ta kama kasan gashin tace "Duk wannan naki ne..!?", gyaɗa kanta Nazlah tayi. su Adda Dariya suka fara wa Haleesa dan sosai take zuba santin sama nata ne gashin, duk kuwa da cewa suma sun cika sa matsanancin mamakin yarda Yarinyar ta tara abubuwa da yawa, na daukar hankali. gyaran gashin aka shiga yi mata, cikin kankanin lokaci aka gama, dan gashinta yana da taushi kamar na jarirai gashi da suɓi uwa-uba bashi da cunkushewar nan,a yaryare yake, duk kuwa da cewa yana da yawa amma bai cunkushe ba, bayan an gama Adda ta bada Ribbons guda huɗu aka daure mata kanta dasu. izuwa lokacin idanun Nazlah sunyi jaa, dan gaba daya hankalinta ya fara tashi da yarda ake jaan gashin kan nata , dan bata son abun da zai taɓa kan, dan ma tana jin kunyar su Adda ne ba zata iya musu, musu ba da tuni ta mike . lokacin kuma Yan taya mai shagon aiki suka zo, umarnin fara hakafarawa ta basu, hakan yasa suka farawa su Adda Zainab, Nazlah kuwa Abin ci Adda Zainab ta sa aka kawo mata , ta zauna chan bayansu suna ci ita da Yar Adda Zainab. ba a dau wani lokacin mai yawa ba, aka gama musu dan nasu bai dauki lokaci kamar na Nazlah ba dan wankin kai ne kawai da wankin ƙafa, bayan sun gama, suka tafi gidan su Nazlah gaba daya, lokacin Yan Uwan Iya duk sun hallara gidan ana ta hada ², ana gyaran kayan miya da sauran kayan Abinci. . Tara ta mutunci aka musu , aka kawo musu Abin ci da Lemu wanda Iya ce ta bada aka karɓo musu, bayan sun gaisa suka bawa Ummu haƙurin kayan lefe da ba'a kawo ba, sai taje chan zasu bata kayanta, murmushi Iya tayi tare da ce wa "Ba komai ai gwara ma da baku kawo ba kuka barshi chan, dan wahala za'a sha sai an kawo kuma a mayar", basu wani jima ba sosai suka tayi suna godiyar karamci irin na Yan gidan. Washe gari, Nazlah da rigama ta tashi,wanda hakan ya haddasa mata zazzaɓi , sai dai Iya ce ta dauketa zuwa gidanta, domin chan ne mai rangwamen hayaniya. Tun 10 mutane suka fara daddala, zuwa gurin daurin Auren duk kuwa da cewa ba wata Gayya sukayi sosai ba, dan Bangaren su Nazlah Yan uwa kawai suka gayyata, Chan gidan Ango ne suka yo gayyatar mutane, 12 bata ƙarasa ba Adda Zainab da Haleesa da Hameed duka zo gidan . lokacin da Hameed ya fito, ya yi mugun mamakin ganin Abokanshi a ƙodar gidan , dan shi kanshi jiya yaji zancen Auran, bai kuma fadawa kowa ba dan har Sadiyya bai faɗa mata ba, gurinshi duk suka tattaso suka zo, Khalil ne ya dan duku ƙafadarshi yace "Buddy ashe dama shirin shigewa kake daga ciki, amma ka bari ciwo zai kashe ka, amma wallahi ka shammace ni,kawai sai dai Invitation card naga yana yawo a media , na nemi wayarka kuma shiru ba'a samunka", dafe kanshi ya yi, tare da cewa "yi hkr pls kasan yana yin abun ne sai a hankali, dadin media din kenan ai, amma naji dadin ganin ka wallahi, na gode maka". Ammar ne ya dan duki kafadarshi daga baya yace "mu da baka ji dadin ganin mu ba, ba komawa zamu yi ba ai", juyawa ta yi, yana dariya suka rungumi juna, fira suka ci gaba dayi irin ta Abokai, Adda Zainab da Haleesa kuwa tuni suka shige ciki. Ko da suka shiga ciki ,cikin girmamawa ake gaishesu har ƙasa, har suka shiga Ɗakin Ummu da take cikin shiga mai kyau shar³ da ita sai murmushi take, nuna wa Adda Zainab kusa da ita tayi, zama tayo suka gaggaisa, fira suka shiga yi da dangin Iya, da yake duk fara'a garesu ga saurin sabo yasa, suke firarsu cikin jin dadi, da tattauna yarda zancen Auren yazo, Haleesa ce tace "Ummu ina Amaryar Auta,da Iya?, naga ban gansu ba", dan murmushi Ummu tayi tare da cewa "Suna gidan Iya ko asa a raka ki chan din ?". dan gutun murmushi tayi tare da ce wa "Laaaah Ummu nasan gidan bari na je", ta fada tana mikewa, Amsar Yar Adda Zainab tayi ta fice da ita zuwa gidan Iya. Da Misalin karfe 1pm na ranar Juma'ah , aka daura auren Hameed Abubakar da Nazlah Lawal akan sadaki naira dubu dari biyu, wanda Adda Zainab ce ta bada kuɗin sadakin, Daurin Auren sosai ya samu halarta mutane Manya da ƙanana, kowa ka gani fuska washe dan an wadata kowa da komai abin ci da lemuka har ba'a magana. bayan an gama daurin auren Hannu Yah Haleem ya mikawa Hameed cikin yar fara'a yace "ina taya ka murna, Allah ya sanya Alkhairi", dan murmushin da bai kai ciki ba Hameed ya yi, tare da ce wa "Na gode, uhmmm Haleem ko , Yayan Nazlah?", gyaɗa kanshi Yah Haleem ya yi, murmushi ya ƙara sakar mishi, kafin su zauna cikin Abokan Hameed din ,hannunshi kuma na rike da na Yah Haleem,sai da kowa ya watse Hameed ya rage daga Hameed sai Abokansa ,Adda Zainab ta fito daga cikin gidan, suna haɗa ido ya dan kauda kanshi. Yar dariya tayi tare da ce wa "Ango kasha kamshi..!", Yar harararta ya yi, tare da dauke kanshi, dan matsawa kusa da shi tayi, tare da cewa "Allah in baka saki fuskar nan ba sai na ɓata maka rai" ta fada cikin raɗa. kamar zai yi kuka haka yawa fuskarshi, dan wani kalar yanayi yake ji, shi dai ba zaice farin cikin Auren yake ji ba,kuma ba zai ce Yana jin baƙin ciki ba, kawai dai yana yi yake ji , shi ba sama ba shi ba ƙasa ba, gadai shinan. riƙe hannunshi tayi tare da cewa "Muje ciki ka gaiyar da mutane", ta fada tana fara takawa, bin bayanta suka yi duka da Abokanshi, sai baza kamshi suke, har ƙasa suka ɗuƙa suka gaisar da mutanan dake cikin gidan kafin su shiga ɗakin Ummu, itama har ƙasa suka gaisheta, Adda Zainab ce ta kalli Ummu tare da nuna mata Hameed tace "Wannan ne Hameed din", "Hameed wannan ita ce Ummun Nazlah", bai ɗago kanshi ba, sai dai zuciyarshi tayi wani mugun bugawa, Ummu kuwa dan murmushi tayi bata ce komai ba, yar dariya Adda Zainab tayi dan tasan kunyarshi Ummu take ji, sai dai ita ta tabbatar wata rana sai ta daina jin kunyarshi dan duk ranar da Ya fara son Nazlah sai ta bani da rashin kunyarshi , dan baya iya boye abun da yake so. mikewa sukayi zasu fice , Ummu ce tace "Zainab...!", juyowa Adda Zainab tayi ta dawo baya tace "Na'am Ummu..!", "a raka su gidan su Iya", ta fada tana dan kallonta, murmushi tayi tare da cewa "Yanzu kuwa ai ni zan rakasu ma",,ta fada tana ficewa. tana fitowa Khalil yace "Adda wai ina Amaryar ne?, naga ban ganta ba", ya fada yana dan murmushi, "kai kuwa Khalil mai kake ci na baka na zuba, yanzu zan raka ku gidan Kakarta tana chan ai" ta fada tana yin gaba, duk bin bayanta sukayi, anan suka bar motocinsu suka bi bayanta. Da sallama Adda ta kutsa kai cikin gidan , Iya da take tsakar gida ta Amsa mata, tare da cewa "Zainabu ce? shigo mana...!", ta fada tana kara buɗe taburmar da take kai, jin ance Zainab yasa Haleesa dan leqowa ganin Adda Zainab ce yasa ta fito. Gaisawa da Iya tayi kafin tace "Iya da Anguna muke tafe", yar harararta tayi kafin tace "shine kika barsu a waje, ke Haleesa jeki ki shigo dasu, bari na karo taburma", ta fada tana mikewa, Haleesa kuwa tayi waje, ison shigowa ta musu, kafin ta juyo . kafin su shigo Iya ta shimfiɗa musu Taburma, Adda Zainab kuwa ta shige cikin ɗaki Gurin Nazlah, zama sukayi kan taburmar tare da gaishe da Iya Amsa musu tayi da fara'a,kafin tace "ina Angon nawa yake?", ta fada tana kallonsu. Khalil ne ya nuna Hameed da hannu tare da cewa "gashi nan Mama", murmushi tayi tare da cewa " , kar ka yarda a baka nunar rana, a bar ni, dan wannan dan fari²n duk rana ce ta duketa, ni kuwa ka gani fess da ni , gani dakwau ," ta fada cikin yar tsokanar jika da kaka, Dan murmushi Hameed ya yi, tare da cewa "Haba Iya ai sabuwa ake so mai jini a jika", ya fada yana yar dariya. Bangaren Adda Zainab kuwa, tana shiga ta nufi Nazlah da take fitar da numfashi sama², sosai zazzaɓin ya yi zafi, matsawa tayi gareta ta sanya hannunta akan wuyanta, da sauri ta cire saboda wani mugun zafi da ya daki fatar hannunta, "Nazlah!", ta dan furta da ruɗu, idanunta da suka mata nauyi ta bude tana kallon Adda Zainab bata iya Amsa kiran da ta mata ba. ganin tana jin jiki sosai, yasa ta fito tare da cewa "Iya zazzaɓi ne sosai a jikinta, akwai magani a bata kafin a tafi da ita Asibiti",,ta fada cikin yar damuwa, shi kuwa gogan taɓe baki ya yi. "Maganin ya ƙare dama shi kenan ta ƙarasa shanyeshi ɗazun, ban san mai yasa wannan zazzaɓin nata ya ke yawan taƙura mataba kwana biyu ga,zafi ga naci ",ta fada cikin tausayawa Nazlah. Kallon Hameed Adda Zainab tayi tare da cewa "taso ka dauketa mu tafi hospital dan jikin ya yi zafi sosai har na fara jin tsoro", ta fada tana kallonshi, shi kuwa shiru ya yi kuma bai tashi daga in da yake zaune ba. "Wai ni kam ba da,Hameed nake magana bane?," ta fada cikin yar tsawa, mikewa yay, yana jin Adda ta fara shiga haƙƙinshi da yawa. bin bayanta ya yi suka shiga ɗakin, sai da suka shiga tsakiyar ɗakin kafin yace "ina take?", ya fada yana dan duddubawa , nuna mishi Nazlah da take kakkafewa tayi, ido ya fitar waje kafin yace "Innalillahi wa'inna ilaihi raju'un, wannan Ƴar Abar Adda mai yasa zakimin haka ne?, yanzu wannan ni ba abin kunya bane na nunata a matsayin mata, lallai da sakyal dan kuwa anyi bonono rufin ɗaki da Ɓarawo, dan wlh wannan ko bata mutu ba, zata sha wuya, kaji abu kamar mage, ji yarda,ta wani lafe tana futar da numfashi kamar,zata mutu k....... 07033371851 ```DAGA TASKAR ƳAR LELEN ROYAL STAR``` An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels