Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

*∆ A SANADIN SOYAYYAR MINTI ∆*
_na ɓata rayuwata😭_

Na
*Jameey yar'mutan kankia ce❣️*

*MANAZARTA WRITERS ASSOC📚🖊️*
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
_________________


*Gajeran labari*
*Labarin gaskiya (true life story)*


https://chat.whatsapp.com/BS0N4RFqbe6LFqlXZZ9vxD

*my real fan's kusan dai cewa na tafi hutu, ba zaku sake jina ba sai wani lokaci wanda nida ku bansan lokacin ba har sai Allah ya nuna mana zamu sanshi, sai gashi wata baiwar Allah tayi man magana akan nayi hakuri na rubuta labarinta dan masu irin halinta sunji su daina, idan ma akawai masu niyar farawa suma su daina idan sukaji abunda ya faru a kanta bisa da biye ma zuciya da tayi har ta aikata SOYAYYAR MINTI WATO A TURANCE ROMANTIC LOVE, da naso nace ba zani ansa ba, yanda ta nuna man damuwa da kuma nuna man amfanin labarin da taimakon da zaiyi shiyasa na ansa nace zanyi amman zanyi shi a GAJERAN LABARI duk da ita ba a short ta bani shi ba, ta bani shi a long story nice nayi summarize din shi na maida shi short saboda karda munayi mu koma school na ajiye shi ba tare da mun gama ba wannan kenan*


*Abunda nike so daku shine kuyi comment sosai hakan zai bani kwarin giwwar baku shi cikin sati insha Allah*


_Godiya ta musamman zuwa ga_
*Zauren Yar'mutan kankia fan's group*
*Real jameey novel fans 1&2*
*Sansanin Yar'mutan kankia*
*Zee-abu hausa novel*
*Ban raina allura ba fan's*
*zauren manazarta fans*
_Da dai sauransu duk ina maka godiya ta gareku_


*oyoyoyo! Ina maki murnar dawowa duniyar yanar gizo social media kenan, kawata aminiyata wato FJ marubuciyar BAGIJJA, Allah yasa kin dawo sa'a kuma a cigaba da suburbudo mana zafafan novel mana shan karatu❣️*


*Wanann page din naki ne Real eeshow marubuciyar BAN RAINA ALLURA BA! ITAMA KARFE CE kiyi yanda kike so dashi🤗*



Page 1⏩2


Wata macece wanda bata wuce shekara 50 ba zaune a madaidacin parlourn gidansu ba abunda taje sai aikin kuka dan abun duniya ya taro yayi mata yawa, wata yarinya ce ta fito daga cikin wani daki ta zauna kasa kusa da kafar matar itama kukan take, dan ta rasa mai zata ce ma mahaifiyar tata kallonta tayi sanann tace.


"Mama Dan Allah kiyi hakuri ki yafeman wallahi ba zan sake ba, nayi maki wannan alkwarin, wallahi sherin she... Tas! Mama ta wanke ta mari tana nuna ta da yatsa cikin fushi ta fara cewa. "Allah ya tsine maki albarki insha Allah ba zaki gama da duniya lahira ba Khadija, tunda har kika sa na zubda hawaye saboda dake kika jaman zagi a cikin unguwa, Allah ya i... Da sauri Khadija ta rike kafafun Maman tata, tana girgiza mata kai tana hawaye masu ciwo dan kukan ma ya gagareta dan tana cikin tashin hankali ba kadan ba, yanda Maman tata take tsine mata tana mata fatan masifa ta fada mata bayan kuma itace uwa gareta mahaifiya, cikin tashin hankali tace. "Mama dan Allah ki barni haka karda abun yayi man yawa kin tsine man sannan kuma zakiyi man Allah ya isa, nasan ko baki ce man Allah ya isa ba ni tawa rayuwar tazo karshe tunda har ta dalilina kika zubda hawaye, Dan Allah Mama ki yafeman wallahi ba zan sake ba, kiyiman Uzuri Ma... Katse ta Mama ta sake yi ta hana Khadija magana, wurga mata hararar tsana tayi sannan tace. "Wallahi Khadija na tsaneki bani sonki a yanzun bani kaunar ganinki, ke har wani uzuri zan maki Khadija? Bayan cikin shegene a jikinkinki duk tarbiyar da ba baki, abu daya nike so ki sani bani bake har abada, karki sake kirana da sunan Mama ta na yafeki daga cikin ƴa'ƴana, ki kirani da suna HAFSAT dan yanzun ni ba mahaifiyar ki bace, Allah ya tseni maki albarka."


Allah Sarki kuka na sake rushewa dashi dan duniya tayi man kunci bansan ya zanyi da rayuwa ta ba, sannan kuma na tsorata da yanayin da mahaifiya ta take ciki, tashi nayi na koma dakina na cigaba da kukana, wanda tunda jiya mukaje asibiti likita ya sheda mana ina dauki da karamin ciki dan wata wata nake aikin kuka, ba kukan komai nike ba Ila kukan dana sani da biye ma son zuciyata, yunwa naji ta taso man Kuma bani sha'awar cin komai sai dan'wanke da manja da yaji wanda yaji tabarnuwa da kayan kamshi na yaji, tashi nayi na fito parlour tadda Mama nayi zaune tana share hawaye matsawa nayi kusa da ita nace. "Mama yunwa nike ji Kuma dan'wake nike son nace." Ji nayi Mama ta wanke ni da mari cikin zafin rai tace. "Wallahi baki da kwanon abinci a gidan nan, kije wanda wanda yayi maki cikin ki gaya mashi abunda kike son ci, sannan Kuma karki sake kirana da sunan mama na gaya maki tsinanniya lalataiciya dake."

Kasa motsi nayi, ba abunda nike sai hawaye dan ni yanzun na kasa kuka ma, ji nike daman nike kukan da Mama take da naji saukin abunda nike ji a raina, hakuri na sake bata sannan na tashi na koma dakina inajin yanda yunwa take azabzabata na rasa yanda zanyi gashi bani son cin komai idan ba dan'wake ba, haka na wuni a daki a ranar banda sake fitowa waje ba, balle har Mama ta ganni ta sake tsineman, tun karfe 1 nike zaune inajin yunwa har karfe hudun marece yayi, tunowa nayi inada wasu kudi da Nura ya bani tunin dadewa, cikin sauri na tashi na dauko kudin na zura hijab dina dan zuwa nema ma ciki abunda zan sama shi, ina fitowa na tadda Mama da Yaya Aisha sun hada kai suna kuka, Yaya Aisha Yayata ce wanda muke uwa daya uba daya, da yake nice Auta a gidanmu yanda na gansu ne hankali ya tashi dan nasan kukan da suke tsaye nayi ina kallonsu nima a zubda hawaye, kallona sukayi lokaci guda suna man wani irin kallo wannan kallo ba komai bane illa kallon tsana dan Ina ganin tsantsan tsana a cikin kwayar idonsu, ta sowa Yaya Aisha tayi ta nufoni gadan gadan ni Kuma ina ja da baya haka muka kamayi har muka kai karshen bango, kulle idona nayi dan nasan ba dadi zatayi man ba, kamani tayi ta fara wanka man mari tana zagina, nan suka rufeni da bugu ita da Mama, tun ina yi basu hakuri har nazo da na kasa sai dai ido, tun ina gane idan nike har ta kai da bani gane mai akeyi, haka suka kama buguna suka barni kwance sheɗashaɗa cikin jini rai hannu ga Allah, ba su damu da wani hali nike ciki ba, tun la'asar sukayi man haka suka yashar dani suka cigaba da hidimar gabansu, Yayane ya shigo Jamilu shine yana da matarshi kuma shine babba a gidanmu, yana shigowa ya taddani cikin wanann halin kallon Mama yayi sannan yace.


"Mama mai yasamu Auta na ganta kwance cikin jini kuma hankalinku kwance harda ke Aisha."?

Cikin fushi yayi tambayar dan yasan abunda ke faruwa dani likitin da yaga mana ina da ciki shi ya kirashi waya ya gaya mashi halin da ake ciki da yake abokinshi ne, kallon shi Mama tayi sannan tace. "Jamilu Khadija cikin shege tayi gaya maka ne banyi ba, dan na fiddata daga cikin jerin ƴa'ƴana, baku ba Khadija kuma kabarta ta mutu, idan taso nima akashe ba damuwa ta bane."


Kallonta yayi ya fara cewa. "Haba Mama ya kamata ki yarda da kaddara mai kyau da marar kyau shine cikon imani, kisani wannan cikin yana cikin zanar kaddarar Auta dole sai tayi wannan cikin wallahi kaddararta ne, banyi tunanin ganin haka daga gareki ba Mama, kuma ke Ai... Wanke shi Mama tayi da mari tana cewa. "Har ni zaka gaya man kaddara Jamilu, inace nice na haifeka va kaine ka haifi kanka ba, tun kafin ka zama mutun nasan zanar kaddara, balle kace man wata kaddara wallahi Jamilu badan nakai zuciya nesa ba kaima da na tsine maka wallahi mutun banza, ka fita ido na kulle daman ace da ka haifi namiji kwara mace dan ita mace itace tasan kishin uwarta daman ace ciwon ƴ'a mace na ƴ'a mace ne."

Tunda Mama ta mari Yaya Jamilu bai sake cewa komai ba, sai ma zuwa da yayi zai dauke ni ya kaine asibiti domin cito da rayuwata cikin fushi Mama tace. "Mudun ka dauketa sai na tsine maka albarka Jamilu."

Share
Comment
And
Vote


*A SANADIN SOYAYYAR MINTI*
_na ɓata rayuwata😭_

Na
*Jameey yar'mutan kankia ce❣️*

*MANAZARTA WRITERS ASSOC📚🖊️*
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
_________________


https://chat.whatsapp.com/BS0N4RFqbe6LFqlXZZ9vxD
Idan kinsan baki comment karki shigo pls

*wannan page din nakune A SANADIN SOYAYYAR MINTI FAN'S da ZEE-ABU HAUSA NOVEL DA BAN RAINA ALLURA BA FANS kuyi yanda kuke so dashi dan naji dadin comment dinku sosai inason ku cigaba da yi man haka, yana kwaraman kwarin giwwar yi maku typing sosai da sosai, ina maku son fissabillilah🤗❣️*


Page 3⏩4


"Wallahi mudun ka kuskura ka taɓa Khadija to sai na tsine maka albarka, mutumin banza wanda baya kishin uwarshi."

Cikin kuka Yaya Jamilu ya matsa kusa da Mama yana cewa. "Dan Allah Mama ki man rai kar ki biye ma kizo daga baya kina da na sani karki manta Autarki ce ba kwance cikin wannan halin, kuma hannunka baya ruɓewa ka yanke ka yada."


Shiru Mama tayi ta share hawaye, tsaki tayi ta bar mashi parlourn dan mudun ta tsaya cikin parlourn tsab zata tsine ma Jamilu, haka itama Aisha tabi bayan Mama, kallona Yaya Jamilu yayi sannan ya ida isowa wajena ya daukeni cikin sauri ya fita dani ya sani cikin motor dinshi sannan muka dauki hanyar asibiti, sosai yake ba motarshi wuta ikon Allah ne kawai ya kaimu dan gudu yake ba na wasa ba, muna zuwa ya ruga ya kira nurse suka turo bisa keken mararsa lafiya, haka aka turani rai hannu ga Allah, direct emergency room aka wuce dani, tsayawa Yaya Jamilu yayi baki emergency din yanata safa da marwa.

Niko tunda aka shiga dani likito suka dufuha kaina dan cito raina da abunda ke cikin cikina dan jini nike zubdawa bana wasa ba, sun kusa awa uku suna abu guda sannan suka samu suka tsada jinin, allurai sukayi man sannan suka kaine dakin hutu, fitowa likitan yayi yace ma Yaya Jamilu. "Alhaji Jamilu ina son ganinka a office dina." cikin damuwa Yaya Jamilu yace mashi. "Allah yayi mata cikawa ko."!? Kallon shi kawai likita yayi sannan yace."komai dai mainene meet me in my office." gwaɗa mashi kai kawai Yaya yayi sannan suka tafi office dinshi, duba da yanayin da yake ciki yasa likita ya bashi ruwa mai sanyi yasha sannan ya fara magana yana cewa. "Alhaji sai dai ayi hakuri, dan muso mu cito cikin da ke jikinta, amman Allah ya kaddara sai ya zube sakamon faduwar datayi har cikin ya bugu, sannan magana ta biyu sai anyi mata wankin ciki kuma mahaifarta bata kwari bai zama dole ta sake daukar wani cikin ba inba wani ikon Allah ba, hakuri zakayi haka Allah ya kaddara sannan zaka sa hannu domin zuwa gobe idan Allah ya kaimu ayi mata wanke cikin idan Allah ya kaimu."

Cikin tashin hankali Yaya yace. "Innalillahi wa'inna'alaihijirun, abokina kaidai kasan komai Auta bata taba aure ba, kaddara ce ta hau kanta wanda ba mai tsalake kaddara idan Allah ya kawota, ba wani abu da za'ayi mata wanda ba sai anyi mata wannan wankin ba, dan da matsala ace za'ayi ma budurwa wanki ciki ka duba dan Allah."


Kallon shi Doctor yayi cikin tausayi dan yasan abokinshi yana cikin damuwa balle yasan yanda suke son autar tasu, cewa yayi. "Wallahi Abokina babu wata hanya idan ba wannan ba, da ace anyi hakuri an raini cikin ta haifeshi da lafiya lau, dan kaddara ce kuwa, wannan yana cikin kudin kaddarar Khadija, amman garin ya hakan ta faru har Mama ta bari ta faɗi har haka."? Cikin takaici da bakin ciki Yaya Jamilu yace. "Ai daman abunda Mama take so kenan, cikin nan ya zube, taddawa nayi ita da Aisha sun mata dan'banzar duka, dakyal na samu ta barni na kawota asibiti, amman ka bani lokaci naje na gaya ma Mama halin da ake ciki komai kenan sai ka jini."

Kasa cewa komai Dr Dikko yayi, dan baiyi tsanmanin jin haka daga wajen Mama ba, cewa yayi. "To shikenan ka dawo lafiya, sannan ka dawo da wanda zata kulla da ita mutun daya, kasan dokar asibitin nan ba'a kwana amman tunda gidane mutun daya zai kwana, fatanmu Allah ya bata lafiya."

"Amin ya Allah." cewar Yaya Jamilu sannan ya fita, sai da ya fara biyawa gidanshi ya gayama matarshi halin da ake ciki sannan yace ta shirya ma Dija babbar diyarshi wanda muke sa'a daya da ita yace ta tafi dan kula dani shi kuma zaije gida suyi magana da Mama, haka aka aiko man da Dija shi kuma ya wuce gida wajen Mama.

Koda ya shiga sallama yayi ya tadda parlourn ba kowa wuce wa yayi ciki na ya tadda yaiyaina mata guda hudu duk sunzo dan an gaya masu abunda ke faruwa, sai hakuri suke ba Mama dan Yaya Aisha tunda taga halin da Yaya Jamilu ya fidda ni tayi da nasanin bugana da tayi, dan kuwa Mama bataji komai ba Yaya Fatima ce tace. "Mama ya kamata ki sama ranki hakuri, mu dauki kaddara wanann abu jarartace ya kama mun zamo masu cikon imani, ke kuma Aisha kin bani mamaki wallahi bai kama ki biye ma Mama ku bigi Auta ba, ya kamata ace kin ba Mama hakuri ba ki tayata wannan mumanan aika aika ba." cikin jimami Yaya Amina tace. "Ni ko wani hali Auta take ciki amman dan Allah Mama kiyi hakuri." ita dai Yaya Khausar bata ce komai ba, dan abun duniya yayi mata yawa so take taji muna wani asibiti domin taga lafiya ta, shigowar Yaya yasa duk suka miƙe suna tambayar shi halin da nike ciki, samun waje yayi ya zauna ya nemo jarumta ya sama kanshi, sannan ya gaya masu halin da ake, ai take suka fara koke koke, dan Yaya Aisha tafi su dan kuka take tana nadamar buguna da tayi abun Mamaki ba abunda Mama tace inba kallonsu da take ba, hawaye ne kawai suke zuba bisa idonta, kallonta Yaya sannna yace. "Mama baki ce komai ba kinji halin da ake ciki Auta tana buƙatar taimako."

Tashi Mama tayi zata bar dakin, Yaya Fatima ta riko ta tana cewa. "Mama dan Allah ya kamata ki yafema Khadija, ki anshi kaddarar da tazo mana tana bukatar taimako."


Zaunawa Mama tayi sannan tace. "Bintu mai zance? Aje ayi Allah yasa a gama lafiya." Tana gama fadin haka ta tashi ai take Mama ta wanke jiki ta fadi kasa tana amain jini, da gudu sukayi kanta suna kiran suna ta.


Daukarta Yaya yayi suka wuce asibiti, gado aka bata sannan aka sama mata drip dan temper dinta ce ta hau sannan Yaya ya cike takadar da za'ayi man aiki, sai wajen mangrid Mama ta farko haka ta matsa aka sallamaita ni kuma aka barni da Dija, duk da nima na farko amman ba sosai nike yin magana ba.


Washe gari da safe Doctor ya shigo ya duba jikina, hana bani komai yayi yace 10am za'a shiga dani ayi man wankin ciki, sanann ya tafi wajen 9 na safe Yaiyane duk sunzo sun cika asibitin suna duba lafiya, goma nayi aka zo tafiya dani za'a yi man aiki haka na bar yan'uwana suna kuka, dan bansan wani hali nike ba nidai naga suna kuka.




Wajen Mama kuwa tunda ta koma gida take kuka, dan tanajin ciwon abunda ya faru dani sosai, dan ma anbar mata Yaya Amina a gida ita ta kama kwantar mata da hankali tana gaya mata maganganu masu dadi wanda zai sa taji sanyi a zuciyar ta.


Kallon Yaya Amina tayi sannan tace. "Amina bakisan abunda nike ji ba shiyasa, amman na yafema Khadija Allah yasa ta dauki darasin duniya, daman ita duniya haka take tafi bagaruwa jifa, na yafe mata Allah yasa iyakar kaddararta kenan kinga ta biye ma san zuciya ta lalata rayuwar ta a banza."

Haka aka kirasu waya aka gaya mata anshiga dani dan yi man aiki, tayi man fatan fitowa lafiya.


*Allah Sarki, rayuwar Khadija da ban tausayi sosai wallahi nan bakuji komai ba😭, nima lokacin da take gaya man nayi kuka har na godema Allah, fatan dai Allah ya kara tsaremana imanin mu Amin, ya karemu da aikata aikin da na sani*



Share
Comment
And
Vote




*A SANADIN SOYAYYAR MINTI*
_na ɓata rayuwata😭_

Na
*Jameey yar'mutan kankia ce❣️*

*MANAZARTA WRITERS ASSOC📚🖊️*
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
_________________
https://chat.whatsapp.com/BS0N4RFqbe6LFqlXZZ9vxD


*Wannan page din nakane Yayana na kaina Muhammad Kareem MK, Allah ya kara daukaka da lafiya Amin*

*Gaisuwa ban girma gareki Maryam Majitapha lawal My Maryam ina maki fatan alkhairy ta wajena*

_Haba my real fans, ya ban ganin ruwan vote and comment a wattpad😢, pls show me ur love a wattpad mana😍_

*Wattpad JameelarhSadiq*

Page 5⏩6

Kallon Mama Yaya Amina tayi sanann ta dafa ta tace. "Mama dan Allah ki kwantar da hankalin ki insha Allah za'a shiga lafiya kuma a fito da Auta lafiya." Kallonta Mama tayi sannan tace. "Amina ba wannan ke tada man hankali ba, yanzun ace Auta za'ayi ma wankin ciki? Karki manta Yarinya ce fa, bata wace shekara sha takwas ba, ina lisafi wata mai kamawa take cika shekara ta sha tara, amman har za'ayi mata wanki ciki, idan za'ayi mata aure mai za'a cema wanda zata aura? Ce mashi zamuyi tayi cikin shegen? Ko kuma muce mashi har wankin ciki an taɓa yi mata Amina."?

Numfasawa Yaya Amina tayi sannan tace. "Hakane Mama amman nasan na Allah basu kyarewa mudai muyi mata fatan samun miji na gari wanda zai rike ta amana ba tare da yayi mata gori ba watan watarana."

Dariya Mama tayi sannan tace. "Ai ba wanda zai iya aurenta Amina, dan haka tana samun sauki wallahi zan aura mata Alhaji Salahu, fatan dai Allah yasa a dace."

Cikin ruɗewa Yaya Amina tace. "Haba Mama ya kikeso ki bada gudumuwa wajen lalacewar rayuwar Auta, a rasa wanda za'a daura ma Auta sai Alhaji Salahu koni ya haifeni balle Auta, kuma matan shi uku dan ma ta hudu ta rasu, har ƙawa nike da ita a gidan fa."


Wurga mata harara Mama tayi sannan tace. "Wallahi ba wanda ya isa ya hanani aura ma Khadija Salahu , idan ba shi ba wa zai aureta? Yarinyar da ta zubdar da mutuncinta a waje ai Alhaji Salahu rufa mata asiri zaiyi ya aureta."

Cikin kuka Yaya Amina tace. "Dan Auta tayi ciki shine yasa zakiyi mata haka? Maiyasa kika kasa yarda da kaddara ne Mama? Mama kinsan kaddara tana cikin cikon imani amman ke kin ki yarda da hakan, yanzun baki gudun tace zata gudu tabar maki gidan? Dan nayi imani ga Allah Auta ba zata yarda da auren wannan mutun min ba, Mama karki ce nayi maki rashin kunya a matsayinki ba mahaifiya ta, amman ko nice kika ce na auri shi wallahi ba zan aureshi balle Auta da take budurwar wannan zamanin, kum... Tas Mama ta wanke Yaya Amina da mari tana cewa. "Dan ubanki har kin isa ki hanani abunda nayi niya? Ko kin fini son Khadija ne? Ai nasa nice na dauki cikinta nayi rainonshi har na tsawan wata tara da kwana tara sannan na haifeta ko? Kuma na bata nonona tasha, ai gata nike nema mata da zaki kama challenge dina dan nace zan aura mata Salahu, yanzun ma zani nayi mashi maganar ta tana gama jini za'ayi bikinsu ko kuna so ko baku so, dan nasan bakinku daya da yan'uwanki to ku sani ba wanda ya isa ya hanani wallahi."


Mama na gama fadin haka ta dauki hijab dinta ta tafi gidan Alhaji Salahu dan yin magana dashi, haka ta bar Yaya Amina zaune tana kuka ganin kukan baiyi mata maganin komai ta shiga kitchen ta dafa abinci tasa a cooler sannan ta fito ta shiga motarta ta wuce asibiti , lokacin da ta shigo hospital din aka fito dani angama yi man wankin cikin.


Fitowa tayi da abincin ta nufo wajen su, duk da suma sun danyi kuka amman ba sosai ba dan Yaya Jamilu hakuri ya basu sosai ya kuma kwantar masu da hankali shiyasa sukayi shiru kallo daya Yaya Jamilu yayi mata ya ganne akwai matsala dan tasha kuka sosai, kunsan ace babban uba daman Babana ya rasu ne tun ina cikin ciki bansan Babana ba, shine dai Ubanmu mu dukanmu daman duk matane shi kadaine babba, baice komai ba tana ijiye abincin yace tazo yana son ganinta a waje, aiko suka fito suka samu waje su dukansu akabar Dija ta cigaba da kula dani.

Office din Doctor Dikko suka je suka zauna sannan Yaya Jamilu yace. "Amina gaya man maike faruwa ya jikin Mama ko jikin tane har yanzun."!? Cikin tsoro yayi mata maganar dan daman hankalinshi ba kwance yake ba yana tunanin halin da Mama take ciki.


Share hawayenta Yaya Amina tayi sannan tace. "Yaya wallahi Mama tana son ta ɓata rayuwar Auta duk da ta kasance uwa a gareta, wallahi bansan yaushe Mama ta chanza hali ba Yaya." Ta karasa maganar cikin kuka, kallonta Yaya Fatima tayi sannan tace. "Amina kiyi mana bayani mu fahimta kin yi mana magana a dabarbarce bamu gane ina maganarki ta dosa ba."

Shidai Yaya kasa cewa komai yayi yana jiran yaji abunda Yaya Amina zatace, balle Yaya Aisha take kuka har yanzun dan ta kasa yafema kanta akan abunda sukayi man ita da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment