Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[8/1, 12:23 PM] 'Yar Ƙwadago🌚: *'YAR ZAMAN ƊAKI*


©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️

https://chat.whatsapp.com/HFVRd4aXG6A8v3OngGn29A

1&2

Manyan motoci ne a jere sun yi jerin gwano kala-kala, idan ka ƙare musu kallo kusan kalolin motar launi biyu ne akwai launi farare da baƙaƙe. Abokan ango ne tsaitsaye kusan kowanne yana jiran ƴan matan da ya sauke don mayar da su gida, kallo ɗaya za ka yi musu ka fahimci suna cikin farincikin taya abokinsu murnar aure.

Gidan babba ne amma plat ne cike yake da kayan more rayuwa, ya sha ƙyalƙyali da hasken ƙan lantarki. Kana ƙare wa gidan kallo za ka fahimci dukiya ta samu makwanci a wurin, duba da irin ɗimbin dukiyar da aka narka a ciki.

"To Zarah kin ga dai kin samu gida irin wanda kowacce ƴa mace take fata, ki yi biyayya ga mijinki ku zauna lafiya, shi zaman aure ɗan haƙuri ne yi na yi bari na bari..." Wata Dattijuwa da take kusa da Amarya Zarah ta riƙa yi mata nasihar zaman aure, ƴan matan da ke tsaitsaye sai kalle-kalle suke yi kowacce tana ayyana ina ma gidanta ne. Matan auren cikin su mafi yawa suna raya Allah ya hore wa mazajensu suma daƙara musu kamarsa, wasu daga cikin iyaye kuma na fatan suma Allah ya bawa nasu ƴaƴa irin wannan gida.

Zarah bata furta komai ba kasancewar kanta na cikin mayafi, har mutanen da suke cikin gidan suka watse sakamakon abokan Ango sai zabga horn suke yi. Ɗakin Zarah ya rage daga ita sai ƙawayenta uku, a hankali ta zame mayafinta tana ƙare wa ɗakin kallo. Amma kana ƙare wa fuskarta kallo za ka fahimci akwai ɓacin rai a tattare da ita, Lubna da ke gefe ta ce: "Zarah ya dai na ga har yanzu ba ki da walwala ko dai akan maganar nan ne?"

Dogon tsaki Zarah ta yi ta furta, "Lubna an yi min adalci kenan? Ace daren farkona wai za a kawo min wata ƴar zaman ɗaki?" Aisha ta taɓe baki tana faɗin, "Ni fa ban ga abin damuwa ba, kuna ɗakinku tana nata. Kuma mutumin nan yana tsananin ƙaunarki, ki dangwali arziki ki bar arziki a mazauninsa." Sadiya ta yi gajeren tsaki tana cewa, "Wallahi Zarah abin haushi gare ki, bakya cin uwar yarinya idan ta ji wuya da ƙafarta za ta gudu.Ki zauna wata ƙanƙanuwar yarinya ta ɓata miki farincikinki, ki zo ki yi biyu babu."

Nan take ƙawayen Zarah suka ci gaba da bata shawarwari na kyau da na banza, lokaci ɗaya ta ware tana farinciki don ta fahimci abin da suke ɗorata a kai.

Ba a jima ba Ango ya ƙaraso shi da abokansa, fito wa ya yi daga motar abokinsa Sani. Bayan motar ya buɗe Walida na zaune tana ƴan kalle-kalle, tana ganin ya buɗe mata ta yi masa murmushi. Hannunta ya kama ya ce, "Fito mun zo gida." Wani Abokinsa Yunusa da ke gefe ya ce,

"Mutumina ba ka so cin amarci ba, haka kawai ranar aurenka ka ɗauko yarinya yoo ko ƴar cikinka ce ai ka kaita ajiya." Khalid ango ya yi dariya ya ce, "Ku dai kuka sani kanku ake ji." Cikin raha abokansa suka raka shi, aka yi barkwancin da aka saba tsakanin Angwaye da Amare, daga ƙarshe aka yi sayen baki ƙawayen amarya da abokan ango suka watse.

Zarah ban da yaƙe babu abin da take yi don kar ta nunawa Khalid bata so zuwan Walida ba, Khalida ya ɗauko manyan ledoji biyu duka cike suke da kaji. Gefe ɗaya katan-katan ɗin lemuka ne sai manyan yegot da kayan ƙwalam da maƙwalashe. Khalid da kansa ya ɗauki Walida ya kaita ɗakinta haɗe da ajiye mata ƙaramar ledarta da ya saya mata kazarta guda ɗaya a ciki, sai lemon jarka da alawoyi. A madadin Khalida ya fita sai ya zauna a gefen gadon, shi kaɗai ya yi jim kamar mai nazari sannan ya furta, "Wannan wacce irin rayuwa ce haka ni ban haifa ba, ba dangin iya ba na baba amma na ƙare da dakon wahala."

Walida da ke gefe ta zuba masa ido ta ce, "Uncle magana kake yi?" Khalid ya wayance da dariyar yaƙe ya ce, "A'a Walida. Cewa na yi Walida ƴar Uncle, yanzu dai ga namanki ko sai da safe za ki ci?" Walida ta leƙa ledar tana juyar da kanta gefe tana shinshine-shinshine ta ce, "Amma dai wannan kazar ba gashin inji ba ce?" Khalid ya zuba mata ido wani takaici ya kama shi, a ɗiƙile ya furta, "Idan bakya ci ki bari sai da safe kya ci."

Khalid na gama maganar ya nufi bakin ƙofa tun bai ƙarasa ba Walida yanƙare baki ta fashe da kuka. Riƙe ƙugu Khalid ya yi a ƙagauce ya dawo murya a shaƙe ya ce, "Me ye kuma?"

Ledar kazarta ta nuna masa tana maƙale hannu ta ce, "Kazar nan ce take cizo na a hannu, kuma ni ka zo ka kwanta a nan." Da mamaki Khalid ya furta, "Kaza kuma? Gasasshiyar kazar ce take cizonki..." Khalid bai rufe baki ba ya ji ledar kazar ta bada ƙaraas alamun taunar ƙashi, da sauri Khalid ya sake buɗe wa sai dai ga mamakinsa yana buɗe ledar ya ga sai taunannun ƙashi, wasu ma an yi dugu-dugu da shi. Cinyoyin kazar ne kawai aka cinye tsokokin ba tare da an tauye ƙashin ba.

Yana shirin yin magana ya ji Walida ta saki ƙatuwar gyatsa sannan ta ce, "Uncle zan sha ruwa." Khalid ya ƙwalalo ido waje ya ce, "Ina kazar cikin ledar?" Walida ta ce, "To ai sai na sha ruwa zan ci." Khalid ya sake bankaɗe ledar ya ce, "Ba yanzu na nuna buɗe kazar har kika ce ba gashin inji ba ce?" Walida ta sake sakin gatsa haɗe da ɗaukan tsinken sakace tana kwakwule haƙoranta.

MEYE HARSASHENKU AKAN WALIDA? 😂

LITTAFIN KYAUTA NE AMMA BAN YI ALƘAWARIN YIN TYPING MAI TSAYI BA SABODA LITTAFIN KUƊIN DA NAKE YI, ZAN YI ƘOƘARIN YIN POSTING KULLIN INSHA ALLAH.🥰

Ummou Aslam Bint Adam🌚
[8/2, 11:52 AM] 'Yar Ƙwadago🌚: *'YAR ZAMAN ƊAKI*


©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️

https://chat.whatsapp.com/HFVRd4aXG6A8v3OngGn29A

3&4


Khalid zuru ya yi yana kallon Walida da take sakace tana lumshe ido, sai da ta gama sakace ta ɗago daga kishinɗe ta ce, "Uncle ƙishirwa nake ji." Ba tare da ya kalli wurin da yake tsammanin anan ruwa da yegot ɗin suke ba, ya miƙa hannu har lokacin idonsa na kan Walida, yana taɓa robar yegot ɗaya ya ji ba faɗi garam alamar an shanye abin da yake ciki. Wannan karon sai da cikinsa ya kaɗa amma don kar ya nuna mata ya ɗan tsorata ya hau borin kunya da cewar, "Wai me yake faruwa ne? Kaji tun ba a je ko'ina ba sun ƙare shi ma yegot ɗin an shanye shi duka, wallahi duk uban da yake aikata min haka daidai nake da zamaninsa."

Amarya Zarah tana can zaune tana jiran dawowar Khalid ango, ƙamshin kazar ne ya gama cika mata hanci ban da haɗiyar yawu babu abin da take yi. Jin shirun Khalid ya yi yawa ya sa ta fara jin haushi saboda tana tuna Walida wani takaici yake mamaye birnin zuciyarta, a hankali ta miƙe ta isa bakin ledar kazar. Ta faki ido tana kallon hanyar shigo wa amma jin shirun da ta ji ya sa ta kai hannu da niyyar buɗe ledar, lokaci ɗaya ta ji kamar an ce. "Wayyo ni Amarya Kaza." A ɗan zabure Zarah ta ja da baya tana waige-waige don yadda ta ji kazar na magana raɗau a kunnenta, da sauri ta nufi sashen da ta ga Khalid ya bi.

Tana zuwa ta samu Khalid tsugunne a gaban Walida yana cewa, "Walida ki yi bacci kin ga Auntynki na can tana jirana." Walida ta kwaɓe baki ta ce, "A'a ni dai ka kwana a nan." Ganin yanda Khalid yake lallaɓa Walida ya tunzura zuciyar Zarah, tun daga bakin ƙofa ta saki uban ashar tana faɗin:

"Khalid me kake yi haka? Wai ni ce Amaryar ko yarinyar nan? Tun da ka shigo gidan nan ka taho wurin yarinyar nan ni ina can ina zaman jiranka, wallahi da na san wulaƙancin nan za a min da..." Tun bata ƙarasa ba Walida ta tashi zaune ta ce, "Don Allah ki yi haƙuri Aunty." A zafafe Zarah ta dakatar da ita da cewar, "Rufe min baki munafuka ƙanƙanuwarki da ke sai iyayi." Khalid ya miƙe jiki a sanyaye ya ce, "Don Allah ki yi haƙuri Zarah, ni fa ba wani abu ne ya tsayar da ni ba. Dubi ledar nan." Khalid ya yi maganar yana ɗago wa Zarah ledar kazar. Ganin taunannun ƙashi ya ƙara harzuƙata ta ce, "Eh to tun da kun cinye gani ƴar iska ai dole ka nuna min ƙashi amma gaskiya Khalid ka cuce ni da na san cin kashin da za ka min kenan da..." Khalid ya katse Zarah tare da zayyane mata abin da ya faru. Da farko ta so ƙaryatawa amma da ta tuna abin da ta ji sai tsoro ya sake kamata. Suna nan tsaye Walida ta ɗago ta ce, "Uncle ku je ni fa bacci nake ji."

Khalid ba ƙaramin daɗi ya ji ba, cikin shauƙi, so da ƙauna ta riƙo hannun Zarah suka wuce sashensu. Suna zuwa Khalid ya rungumo Zarah yana kashe mata ido ɗaya ya ce, "Habibity kin ga yadda kika yi kyau kuwa?" Kafin Zarah ta yi magana suka ji magana kamar raɗa an ce, "Duk kyawunta ta kai kaza." A firgice duk suka waiga, Khalid ya fara leƙe ta window ya ce, "Zarah amma dai babu wanda aka bari a ƴan kawo amarya ko?" A daƙile Zarah ta ce, "Sai ƴar zaman ɗaki waya sani ko laɓe take mana." Khalid ya wayance da cewar, "Haba dai Walida ba za ta yi haka ba. Yanzu dai miƙo min ledar kazar nan ki ga."

Zarah ta yi baya cikin zaro ido tana faɗin, "Wa ni? Ai idan ka ganni a lahira kaini aka yi. Jin kunnena na ji kazar nan ta yi magana, kai anya Khalid gidan nan ka sa an yi masa sauka kuwa?" Khalid ya ƙarasa ya ɗauko ledar kazar yana cewa, "Ban da almara ya za a yi Kaza ta yi magana kina son dai tsorata kanki ne." Yana gama maganar ya baje musu kazar suka zauna sai dai har lokacin Zarah bata gama sakin jikinta ba."

Katuwar cinyar kaza Khalid ya ɗauko ya gutsira sannan ya miƙa wa Zarah ya ce, "Buɗe baki My love." Zarah ta buɗe baki yana miƙa mata a baki sai ji ta yi zuwait an zuge tsokar sai ƙashi. Zarah da take baki a buɗe ta kalli Khalid, shi kuma sam bai lura da abin da ya faru ba. Wata tsokar naman ya sake ɗauko mata ya miƙa mata, a wannan karon Zarah ta cinye amma tana yin tauna ɗaya taji an ce. "Wayyooo cinyata ni kaza." Da sauri ta kalli Khalid ta ce, "Hubby ka ji me na ji kuwa." Khalid ya tura tsoka baki yana tauna ya ce, "Zarah don Allah ki kwantar da hankalinki, na fa gidanki ne karki tsorata kanki." Babu yadda ta iya haka ta ja bakinta ta yi shiru don ta ga Khalid bai yarda da abin da ta faɗa ba, yana sake bata kazar ta nuna masa ta ƙoshi. Sai lemo ta sha kaɗan amma har lokacin zuciyarta wasu-wasi take.

Bayan sun kammala Khalid ya tuna da wani magani da abokansa suka bashi, da sauri ya tashi cikin dabara ya nufi kitchen acen ya buɗe jarkar ya shanye gabaɗaya. Ita ma Zarah yana fita ta zuge jakarta ta ɗauko wani tsumi da aka bata ta shanye, tana jin motsinsa ta wurga jarkar ƙarƙashin gado. Khalid na zuwa ya cire kaya ya ɗaura towel yana faɗin, "Dear bari na watsa ruwa sai mu ɗaura alwala mu yi sallah." A kunyace Zarah ta amsa tana sunne kai ƙasa ita a dole kunya take ji, tana nan zaune Khalid ya faɗa banɗaki.

Shigar Khalid ba wuya ta fara jin kyarkyara a kofar ɗaki kamar kaza za ta saki ƙwai, a hankali ta tashi ta leƙa ta window ga mamakinta sai gani ta yi gasasshiyar kaza na rawa babu kai a jikinta. Ajiyar zuciya ta sauke zuciyarta na lugude ta ji an furta, "Mu kashe mu binne mu sha amarci da angona."

Khalid da ke toilet ɗin cikin ɗaki bayan ya sakale towel yana shirin kwara ruwa a jikinsa kamar almara ya ji an ce. "Sannu mijin kaza." Da sauri ya waiga yana dube-dube nan take ya ji ƙamshin gasasshiyar kaza ta game hancinsa, yana shirin janyo towel don ya fita ya ji an shafo bayansa. Da gudu ya fisgi towel ya hau kiciniyar ɗaurawa, hannunsa har rawa yake zai buɗe ƙofa ya ji an sake cewa, "Mijin Kaza yau fa ranar farinciki ce." Wani tunani ne ya faɗo wa Khalid ya ga idan ya yi ƙarfin halin magana koma waye zai tsorata shi za su dawo daidai. Tsayawa ya yi a wurin ya ce, "A gidan uwar wa na zama mijin kaza ga matata can Zarah a ɗaki." Yana rufe baki ya ji an ce, "Gashi har magani ka sha min don mu sha soyayya, ka ga daga yau zuwa ƴan kwanaki zan fara sakar maka ƙwai zo ka ji angona." Kafin ya yi wani yunƙuri ya ji an fusgi towel ɗin ya ji alamar yatsun kaza na tsikarinsa a jiki.


NA BARKU HAKA DA MIJIN KAZA😂 SU SHA AMARCI LAFIYA.

Ummou Aslam Bint Adam.🌚
[8/3, 12:51 PM] 'Yar Ƙwadago🌚: *'YAR ZAMAN ƊAKI*


©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️

https://chat.whatsapp.com/Bkw4WZsTlH5I8pEbP946SA

5&6

Khalid bai za ci lamarin haka yake ba don haka ya kai duka da gwiwar hannunsa, a daidai wurin da yake jin alamar ana kartarsa da yatsun kaji. Yana kai dukan ya ji siririyar muryar ta sake cewa, "Haba mijin kaza kar ka bari mu yi haka da kai." Hantar cikin Khalid ba ƙaramin kaɗawa ta yi ba, da farko ya ɗauka idan ya kutuntuma wa mai maganar ashar za su dawo daidai. Yana tsaka da tunanin ya ji an dafa kafaɗarsa ana cewa, "Mijina na baya ma gardama ya so ya yi min, kaima karka min haka mijina, don idan ka min gardama gunduleka zan yi." Khalid ko saurara bai gama yi ba ya zuba uwar ƙara yana ƙoƙarin jan ƙofa amma ta ƙi buɗuwa. Ganin ba shi da mafita ya sa ya fara ƙwala wa Zarah kira, don yadda ya ji ana shafar ƙeyarsa abin ba ƙaramin tsorata shi ya yi ba.

Zarah ba ƙaramin tsorata ta yi ba don haka ta koma can ƙuryar gado ta duƙunƙune kanta a ciki, tana nan zaune ta ji ƙarar dirar abu a kan gado. A hankali ta zaro kanta don ganin abin da ya faɗo saboda ilahirin jikinta rawa yake yi, ta gama tsorata har ta ayyana gari na wayewa za ta koma gidansu idan ya so sai dai Khalid ya nemar mata wani gidan. Zarah na ɗago kai ta ci karo da ƙatuwar soyayyar cinyar kaza tana murginawa tana faɗin, "Sai ni ƙanin kaza wato zakara, yayata za ta tasha amarci da mijinta Khalid ni ma ga tawa amaryar tana jirana, amma ni dai ki gafarce ni ɗan ƙunan baƙin wake ne amaren mata nake bi ina kaiwa farmaki." Zarah ta waro ido waje don ko a mafarki bata taɓa tozali da abin da ta gani ba, tana nan zaune ta ji Khalid ya ƙwala ihu yana kiran sunanta.

Zarah na jin haka ta fasa ihu cikin tashin hankali tana cewa, "Khalid don Allah ka fito ka ga kaza tana magana wallahi gidan nan aljanu sun yi yawa a ciki." Zarah na rufe baki ta ji cinyar kazar gabanta ta buga tsalle ta ce, "Ki daina mayar da mace don ni ba Kaza ba ce, yanzu haka haƙƙina na zo karɓa yau mu ɓarje amarci." Cinyar na gama magana ta fara fisgo zanin Zarah nan take Zarah ta fara jan zaninta suka fara kiciniya da cinyar kaza.

Khalid na jin abin da Zarah ta ce ya sake waigawa ya fisgo towel ɗin yana faɗin, "Wallahi ni ma ina cikin wani hali Zarah ki kawo min ɗauki." Daga bayansa ya ga an ɗauke towel ɗin an yi saman toilet ɗin da shi aka ce, "Wallahi ka bani haɗin kai ko na kira ƙannena zakaru su sheme min kai na haike maka yanzu." Khalid na jin haka ya rushe da kuka kamar ƙaramin yaro har da majina ya ce, "Don Allah ku yi haƙuri ku sake ni wallahi ni ba mijin Kaza bane."

Shiru ya ji ba a amsa masa ba don haka ya yi tsammanin ko an rabu da shi ne, ƙofar ya ci gaba da fisga yana bugawa da ƙarfi kamar almara sai ji ya yi ƙofa ta buɗe. Da sauri ya fice daga banɗakin a lokacin ya samu cinyar kaza na ta kiciniya shiga zanin Zarah. Daga wurin da yake a tsaye ya yi kukan kura ya faɗa kan gadon da niyyar ya janye matarsa daga kaidin cinyar kazar, sai ji ya yi an ɗauke shi an buga da ƙasa sannan ya ji an ce, "Ka tashi kasa kayanka ka tafi wani ɗakin ba wannan ba, kuma karka sake ka tafi ɗakin da babu ɗan'adam a ciki. Idan so samu ne ka je ɗakin Walida ko ta zo ta same ka."

Khalid duk irin buguwar da ya yi bai sa ya karaya ya ce, "Wai uban waye yake son shiga tsakanin ma'aurata a daren amarcinsu? Babu inda za ni kowanne matsoraci ne ya fito mu yi gaba da gaba." Khalid tun bai rufa baki ba sai ji ya yi an yi saman fanka da shi, ƙafafuwansa na jikin fanka kansa yana ƙasa yana reto. Tsoro azaba da wuya ta sa ya sako fitsari daga sama ba tare da ya sani ba, Zarah na ganin an tasamma halaka mijinta ta sa kuka tana faɗin:

"Don Allah ku ƙyale shi karku kashe min mijina." Zarah bata rufe baki ba sai ji ta yi an turo ƙofar ɗakinsu an shigo, Khalid yana daga saman fanka idanunsa suka hango masa wata ƙatuwar kaza, tsayi da girman kazar za su iya yin girman yaro mai shekara huɗu. Cikinsa ne ya fara kaɗawa cikin rawar murya ya ce, "Wayyo Zarah Kazaaaaaa."

Zarah na shirin yin magana Kazar da take tafe tiƙis tiƙis ta karɓe zancen da cewar, "Haba Mijin kaza zuwa na yi da kaina ba aike ba, na tafi da kai mu ɓarje amarci ko na biyo ka sama Angona." Khalid ya fara saka hannuwa yana kare jikinsa ya ce, "Don Allah ki koma ni wallahi ba mijinki ba ne." Khalid tun bai rufe baki ba Kaza ta hau saman madubin Zarah tana tafe tana wata irin girgiza za ta ɗafe saman fanka, Zarah na daga zaune Cinyar kazar ta ce mata:

"Zarah ki bani haɗin kai ko na yi kidinafin ɗinki."

Khalid na ganin Kaza ta tunkaro shi gadan-gadan ya sake ƙwallah ƙara yana faɗin, "Zarah kazaaaaaaa, wayyo za ta min fyaɗe." Zarah ita ma ta kanta take yi don haka ta ce, "Khalid Zakara zai yi kidinafin ɗina." Kaza na hawa saman fanka ta yi tsallake ma maƙale hannun Khalid yana cewa, "Angonaaaaaa."

NI MA SAI NA CE NA BARKU LAFIYA KU TAFI CETO KAR KAZA TA HAIKE WA ANGO, NA YI NAN BYEEEEEEEEE😂😂😂


Ummou Aslam Bint Adam🌚
[8/4, 9:01 PM] 'Yar Ƙwadago🌚: *'YAR ZAMAN ƊAKI*


©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️

7&8


Khalid na jin yanda Kaza ta cafki hannunsa ya ware murya cikin tashin hankali ya ce, "Wayyooooo Allah Kaza za ta haike min." Kazar ta ra gwaɗar da kai tana girgiza tozonta ta ce, "Angona yau fa ranar farinciki ne ka taimaki kanka ka ba ni haɗin kai." Tana gama maganar ta miƙa bakinta wurin saitin fuskar Khalid ta ce, "Matso na sumbace ka masoyi." Khalida ta juyar fa kai gefe yana tofar da yawu. Kazar ta tashu sama firrr kamar tsuntsuwa tana kaɗa fukafukanta, bata dira a ko'ina ba sai kan tafin ƙafar Khalid da suke can saman fanka. Khalid na jin Kaza a daidai ƙafarsa ya fashe da wani matsanancin kuka tare da faɗin, "Wayyo za ta mayar da ni Zakara, wayyo Zarah Kaza za ta mayar da ni zakara."
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment