Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

VISIT www.aihausanovels.com.ng For More Novel.

AIHAUSANOVELS is website consists of hausa novels note, the reason of launching this site is to Entetaint, Motivate and Educate our readers.



We provided hausa novels of many type, Such Adventure, love, romance, fiction, non-fiction, mystry, fantasy, action e.t.c from hausa Authors



We provided a new and old novels both softcopy and hardcopy from our Author with thier permission.



AIHAUSANOVELS shafin yanar gizo ne wanda yake ɗauke da littattafan hausa, dalilin bude wannan shafin shine domin Kayatar masu karatu da kuma ilimantar da su.



Mun samar da littattafan hausa na nau'uka daban-daban, kama daga littafin, soyayya, tatsuniya, almara, Hikayoyi, gyara kayanki (yadda mata zasu kula da kansu a gidan mijinsu) da dai sauransu, daga Marubutan hausa.


: *'YAN GUDUN HIJIRA*
_Labarin Sajida_
-----------------------------------------
_based on true life story_
🐾




🅾1⃣



Na



*ZAINUDDEEN ZAIN*
_DR. ZAIN_




dedicated to: _Marayun da suka rasa mahaifansu a sanadiyyar boko haram_




® *PEN WRITERS ASSOCIATION*




```QUOTE OF THE DAY```


_The price of success is hard work, dedication to the job at hand, and the determination that whether we win or lose, we have applied the best of ourselves to the task at hand._



*Shafin Masoya*


_ASEEYA ABUBAKAR IMAM_
_HAUWA AUWAL TSOHO_
_SAUDAT ABDULLAHI SAJ_
_HAFSAT IBRAHIM QUEEN HAFCY_
_NABEELA DIKKO_
_'YAR FATHER_
_AMEENA SANI MANI_
_FATIMA UMAR ABDULLAHI (MUMMY YUSUF)_
_FATIMA LAWAL UMAR ROGO_





```SHIMFIDA/TSOKACI```



Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ubangijin halittu, wanda bai Haifa ba kuma ba a haife shi ba, wanda yake da mulki cikakke kuma tabbatacce. Tsira tareda amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad (SAW) dangaban goshin Allah, wanda duk wanda ya kaucewa tafarkinsa ya bata. Tareda iyalan gidansa da sahabbansa hadi da duk wanda ya bi tafarkinsu ya zuwa ranar tsayuwa.



Godiya fiye da a kirga zuwa ga mahaifiyata, wacce ba zan taba buda littafi ba face na sankamamata godiya kan dawainiya da wahala da take yi a kaina, tabbas ba domin mahaifiyata ba, da maikaratu ba za ka san waye _ZAINUDDEEN ZAIN_ ba, ina rokon ubangiji da ya yafe mata kurakuranta, ya kuma sa aljanna ce makomarta. Ubangiji ka kareta daga sharrin duk wani mai sharri. Amin.



Masoyana, kuma naku daban ne, banida baki da zan iya furta godiya zuwa gare ku kan gwarin guiwa da nake samu daga wurinku, ina mika godiya kan addu’o’I da fatan alkhairi da kuke yi zuwa gare ni. Inaso kuma kusan cewa, ina yin ku sosai da sosai. Irin ana tarennan, kun dai gane.



Wannan labarin kirkirarre ne, duk da cewa jigon labarin ya faru da gaske, duk abubuwan da za su fito a labarin kirkira na yi. Labari ne na wata baiwar Allah da ta shiga gararin rayuwa, tun kuruciyarta har ta kai shekaru 31, an aurar da ita ne ga wani mutum da ke zaune a garin Maiduguri mai suna QASIMU, ita matar mai suna SAJIDA, haifaffiyar garin Kalgo ce da ke jihar Kebbi. Tun tana da shekaru 16 aka aurar da ita, duk da a lokacin tanada wanda take so sosai, a haka aka tankwarata, ita kuwa ta yi biyayya ga mahaifanta duk da rayuwarta ba ta so ba. Bayan aurensu da malam QASIMU, wulaknci kala-kala, sai ya dinga biyowa baya, duk abinda ta yi, ba ta burge shi, har dukan ta yake yi, a haka har suka haifi ‘ya’ya guda biyu: BILKISU ita ce babba inda take da shekaru 14 sai ‘yar karamar mai suna AMISHA inda take da shekaru 4, kafin AMISHA SAJIDA ta haifi da namiji, wanda rashin kulawa da take samu daga mijinta ya zama ajalinsa, wanda shi ne dalili da ya sa, a lokacin da ta haifi AMISHA, dole ta jajirce wurin ganin ta kula da ita yadda ya dace.



Dalilin Qasimu na wulakanta matarsa kuwa, shi ne, saboda shi ma da wacce yake so, amma a gida aka tilasta sa kan lallai sai ya aureta, shi ne yake wulakanta ta da zimmar ko zai rage radadi da raunin da aka yi wa zuciyarsa.


SAJIDA kuwa, ba ta sarye ba wurin kokarta janyo hankalin maigidanta zuwa gareta ba duk da ba ta son sa, amma ina, abin sai gaba yake yi, duk da sun ajiye ‘ya’ya kuma ga shi sun fara manyanta.




Kwatsam suna a haka, ‘yan Boko Haram za su kawo hari a garin nasu, wanda zai yi sanadiyyar bazamarsu cikin jeji da basusan ina za su nufa ba, za su hadu da masifu da dama a cikin jejin, haka za su koyi darussa su kuma hadu da mutane da dama.



Ya wannan abin zai faru, ina kuma za su tafi? Duka amsoshinku suna cikin wannan littafin mai suna; *’YAN GUDUN HIJIRA* _labarin Sajida_




***FARKO***




Lokacin damina ne, ga shi da misalin karfe biyar na maaraice, kuma da alama akwai alamun hadari duba da yadda giragizai ke shawagi a sararin samaniya, da kuma yadda suka lullube rana har ma za ka yi zaton dare ne ya shigo, iska mai sanyi wanda ke kadawa a hankali kadai ya isa ya saka mutum nutsuwa. Abin ka da gari mai yawan jama’a sosai, garin MAIDUGURI. Duka wannan yanayi mai dadi tareda kwantar da zuciya bai hana hawaye zuba ba daga idanun SAJIDA, zaune take cikin gida da ke dauke da daki kwaya daya wanda suke zama ita da mijinta QASIMU da ‘ya’yansu guda biyu BILKISU da AMISHA. Sai zabgar hawaye take har da shessheka a kukan nata, sai kokarin sharbar majina take daga hancinta, amma ina abin ya fi karfinta, tana tsakiyar ratsa kuka, ta jiyo kukan Amisha daga dan karamin dakinsu wanda ko kyaure ba ya da, ga labulen dakin ya yi datti kamar wanda aka dauko daga juji, jin kukan diyarta mai shekaru hudu a duniya, ya kara jefa ta cikin wani sabon kuka wanda har sauti ya fara bayyana, ta tsinci kanta cikin halin rashin iya motsawa balle ta je ta rarrashi diyar tata, wacce rabonta da ta saka abinci a cikinta tun garin kwaki da ta sha da safe. Cikin shesshekar kuka ta tada kanta sama, a ranta tana cewa, ya ubangiji kana ganin halin da muke ciki ni da ‘ya’yana, ka kawo mana dauki…tun bata kammala addu’ar ba sai ta ji shigowar BILKISU daga sallamar da ta yi kafin ta shigo. Fuskarta cike da hawaye ta tada kai ta kalli ‘yarta BILKISU da take kira da MAMANNE kasancewar sunan mahaifiyarta take da, “me ke faruwa naga kin dawo cikin damuwa, MAMANNE?” ta fada muryarta na rawa cike da alamun kuka ga kuma tausayi cikin muryar. “Sani mai shago ne ya ce ba zai sake bamu bashin garin kwakin ba, wai saboda ba ma biya, ya ce yana biyar mu bashin sama da shekara, kuma wai bai ga alamun za mu iya biyanshi ba, shi ba zai yarda mu kashe mashi shago a banza ba” ta fada sai ta karasa cikin kuka. Cike da tausayi ta janyo ta a jikinta ta rungume sai rusar kuka suke. Ita tunaninta daya ne, yanzu yarannan nata a haka za su kwana cikin yunwa da wahala.




Suna a haka, sai suka jiwo ana, sallama, jin bakuwar murya, sai suka yi sauri suka share hawayen da suka cika fuskokinsu, suka amsa sallama tareda yi wa mai sallamar iso, sai ga wata mata ta shigo, daga ganinta kasan irin matannan ne masu wadata, duk da ba za ka kira ta mai kudi kai tsaye ba, malama AISHA sunanta kamar yadda ta sanar da su bayan da ta gabatar da kanta.




“dama ina tsaye ne lokacin da ‘yarki ta zo neman bashi wurin mai shago, shi ne na biyota bayan naji abubuwa da ya fada a kanku, nasan tabbas kuna bukatar taimako, ga wannan” ta mika musu, awara tareda dankali da aka soya, sun sha yaji da albasa ga kabeji a ciki, ta kuma ce da su; “ku kwantar da hankalinku, duk abinda ubangiji ya yi, mai kyau ne, wata rana duk wannan talaucin zai gushe. Idan kin aminta, zan dauki diyarki aiki a gidana, sai ta dinga kawo maku abinci daga wurina, kuma na dinga biyant duk karshen wata”



Sai da ta yi ajiyar zuciya na tsawon lokaci, kana ta aminta, ba tareda ta ko yi tunanin shaidawa mijinta ba, domin tasan ba zai taba goyon bayan haka ba. Duk da ba zai taba taimaka musu ba ta ko wacce hanya.




“kinada aure ne?” inji malama Aisha ta fada a dai dai lokacin da ta kai idanunta tana kallon farfajiyar gidan da ya sha shara sosai, ga tsafta, amma gidan ba tsari ba kuma kulawa daga maigidan. “eh inada miji” “Allah ya sawwaka”



Nan ta shida mata cewa za ta zo da safe domin ta kai su su ga gidan, daga baya sai su saka ranar fara aiki, ta kawo kudi ta basu, ta ce ga wannan ku sayi kayan abinci, domin ai mutum ba ya zama da yunwa.




Ta yi mata rakiya har kofar gida, ta dawo ta kira AMISHA suka zauna suka saka awarar da dankalin cikin kwano, wanda har ya fara lamba, suka zauna su uku suna ci, su dukansu fuskokinsu cike da tausayi sai da aka fara kiran magariba, suka samu suka karasa ci, bayn sun wanke hannuwansu, AMISHA ta fara zabga musu surutu. Murmushi kawai SAJIDA ta yi ta ce “lallai AMISHA ba ki da kunya, wato dazu yunwa ce ta sa sai rusamin kuka kike yi, yanzu kuma za ki zo ki dameni da wannan surutu naki?” suka share da dariya, nan ta umarce su da su dauki butoci domin su yi salla lura da lokaci ya rigaya ya yi.




SAJIDA mace ce baka ga ta doguwa mai kakkauran jiki, tanada alamaun kirar karfi, ga ta da zuciya mai kamar maza, tanada kirki sosai ga addini kuma ga tausayi, nan da nan hawaye sun fito daga idanuwanta, ba kyakkyawa ba ce, haka ba zaka kira ta da mummuna ba, haifaffiyar garin KALGO ce da ke jihar KEBBI, aure ne ya kawota garin MAIDUGURI hannun QASIMU.



Da suka idar da sallah, ta kira Bilkisu ta aiketa da kudin da malama AISHA ta basu, domin ta siyo musu kayan abinci. Fitar BILKISU da kamar minti biyar sai ga hadari dauke da iska ya taso, kan titi sai guduwa mutane ke yi, wadanda ke cikin gida kuwa sai ta kansu suke yi, domin irin iskannan ne mai masifar karfi wanda har itace yake kayar wa.




Wanne hali BILKISU take ciki?
SAJIDA fa wanne yanyi za ta shiga?
Ina QASIMU da har yanzu bai dawo gida ba tun fitar sa da safe?



Duk amsoshin suna cikin shafi na gaba, labarin har yanzu bai fara ba.




DR. ZAIN
[2/3, 4:40 PM] Saudat A J: *'YAN GUDUN HIJIRA*
_Labarin Sajida_
-----------------------------------------
_based on true life story_
🐾


🅾2⃣



Na



*ZAINUDDEEN ZAIN*
_DR. ZAIN_




dedicated to: _Marayun da suka rasa mahaifansu a sanadiyyar boko haram_




® *PEN WRITERS ASSOCIATION*




```QUOTE OF THE DAY```




_A common mistake that people make when trying to design something completely foolproof is to underestimate the ingenuity of complete fools_




*Shafin Masoya*



_M. D. R. Arrigasiy_
_Fiddausi Sodangi_
_Ayush Iliyasu_
_Amra Auwal_
_Sayyada Maryam_
_Madara_
_Zeety_





***CI GABA***



Iska ake ta famar zabgawa mai dauke da masifar karfi tareda wani sanyi wanda ke saka mutum kakkarwa ba tareda ya nufa ba, haka kake jin iskan dauke da sauti mai firgitarwa, sai daukar bugun kwano yake daga kan dakuna yana yawo da su a sararin samniya da farfajiyar garin MAIDUGURi, itace kuwa haka suke faduwa kamar ma’askin dare ya hau kan mace mai gashi. Mutane kuwa sai kokarin ceton rayukansu suke yi ta hanyar neman hanyar wucewa gida, cikin gudu, garin gaba daya sai ya yi duhu, ko tafin hannunka ba ka iya gani, wutar PHCN kuwa tun kafin iskan ya kawo aka dade da daukewa, kasancewar masu hasashe sun tabbatar da yiwuwar iskan zai yi barna.



Hankalinta a tashe, ta rungume AMISHA sai zabgar kuka take yi, a ranta tana cewa wannan masifa har ina, yunwa da talauci ga shi sun janyo na yi asarar diyata, wayyo ni SAJIDA na shiga uku…kalaman ta take ta maimaitawa ke nan a zuciyarta, cen ta jiwo rufin dakinsu ya fara babbakewa, iska ya fara daukarsa, cen sai ji ta yi fuuu! Iska dauke da kasa na shigowa cikin dakin nasu ta sama, kasancewar rufin dakin iska ya dauke shi, ganin haka, ta kalli AMISHA da ke rungume a kirjinta, ta tada kanta ta kalli saman dakinsu, kawai ta sunkuyar da kai wani sabon kuka ya soma daga dan karamin bakinta, kasancewar wannan lokacin kukan ya kwaceta har sautinsa ya bayyana. Ba ta san lokacin da ta buda baki ba ta ce; “QASIMU! Wai kana ina ne, ya za ka tafi ka bar mu cikin wannan masifar? Oh! Ni ‘yasu, yanzu wanne hali BILKISU take ciki?” ta fada a daidai lokaci da take kokarin nemo malullubi da za ta rufe jikin AMISHA da shi, ganin yadda take kakkarwa ba ko tsayawa.




BILKISU kuwa, kasancewar inda aka aiketa ba nisa da gida, har ta rigaya ta siyo juyowa da za ta yi ne iskan ya taso, inda idanuwanta suka cika da kasa, ta rafka kuwwa, mutane da ke guduwa domin neman mafaka suka bangajeta ta fadi, ga ta a kasa ‘yan abubuwan da ta siyo sun watse sai lalube take kasncewar idanuwanta suna a cike da kasa, ga kuma matsanancin duhu da iska mai karfi bugu da kari ga sanyi, mafi muni kalar tufafin da ke jikinta, kan talauci wani hijabi ne da yanzu shekarunsa sha tara, na mahaifiyarta ne take sakawa, shi kadai suka mallaka, idan mahaifiyarta ta dawo daga lalurarta sai ita ma ta dauka ta fita, idan kuma fita ta kama su a tare, a haka take fita dole ba hijabi a jiki, har ‘yan unguwarsu na mata sharri, _mai hijabin da ya girmemata_ a jikinta kuwa zani ne, wanda ta yi daura gaba da shi, wannan ya bai wa sanyi damar ratsa jikinta yadda ya dace, musamman ma da hijabin ba kauri, saboda ya sha ruwa kuma ga huji wurare da dama a jikinsa.



Da laluben ta samu ta tattara wasu daga cikin kaya da aka aiketa ta siyo, ganin ta tattara sai ta nemi wata rumfa ta shiga ta tsaya, a lokacin tana gani idanuwanta sun fara budewa daga kasa da ta cika su. Iskan ya kwashi awanni hudu ana yin sa daga bisani aka sauko da ruwa masu matsanancin karfi, ganin iskan ya tsaya, kuma ga ruwa ana laftawa da har sun dauki awa daya da kusan rabi ana laftawa ba ko alamar tsaiko ko sassauci, Bilkisu ta ratsa ta cikin ruwan a guje ta nufi gida. Isar ta gida gaba daya jikinta a jike har kana ganin kwancin mamanta a kirjinta duk da daura gaba ne a kirjin nata kuma ga shi ko bra babu, cikin kakkarwar sanyi, ta yi tsaye, a lokaci daya ta sake kayan da mahaifiyarta ta aiketa ta siyo, ganin yadda mahaifiyarta da kanwarta ke shan kashin ruwa zaune cikin daki, kasancewar rufin dakin da iska ta dauke. “innalillaahi wa inna ilaihi raaji’un” ta fada a dai dai lokacin da take saka kuka tareda shekowa ta rungume mahaifiyarsu, wacce ita kuma ta rungume AMISHA da sunan hana ruwa su doketa



“inna, ku taso mu tafi” ta fada tana kokaarin jan hannun mahaifiyarta




“rufa muna asiri, so kike mahaifinki ya dawo bai tarar da mu ba mu jawo wa kanmu masifa? Kiyi hakuri, komai dan lokaci ne, wata rana wannan sai dai ki ba yaranki ko jikokinki labari”



“rayukanmu ne fa cikin hadari Inna, muna fa da damar hana faruwan haka, amma muna gani za mu jefa rayukanmu cikin hadari? Kalla fa kiga AMISHA karama ce sosai, so kike wani ciwo ya shige ta da har sai ta rsa ranta, nasan abinda kike nufi, kila ki ce wai za ki fita ba tareda izinin Baba ba, mutumin da bai kiyaye dokokin ubangiji da ke kansa ba, me ye laifi idan an saba masa? Kuma wannan abu ne da ya danganci rayuwa, addini ma ya aminta da ki fita kan hakan.”



“yimin shu, ki bari mu duka mu mutu, a nan din, ya fi mu fita mu mutu a wani wuri da ba dakin mijina ba”



Bilkisu ta koma gefe, sai kallon karamar kanwarta take yi cike da tausayi, hawaye kuwa dama sun saba da shawagi a lallausan kumaatunta.



Ta mayar da hankalinta ya zuwa mahaifiyarta, sai kallonta take irin kallon da ita kan ta ba ta san wanne iri ba ne, na tausayi ne, na haushi ne ko na kauna ne, oho, ita dai kawai ta kura mata idanu.



Haka ruwan suka ci gaba da sauka, har zuwa ukun dare, dama ba wasu tufafi suke da ba, ganin lakar da ya zagaye dakin nasu, haka ta rage tsayi kasancewar ruwa sun dketa duk ta side, ta rasa ina za ta ajiye ‘yarta wacce sai kakkarwa take kuma tuni jikinta ya fara zafi, ganin haka hankalinta ya tashi sosai, a kidime take yin komai, domin ta san idan ma rashin lafiya ne yarinyar take fama da shi, tau cikinta ta yi, domin Babanta ko sisinsa ba zai saka ba wurin nemamata lafiya.



Ganin mahaifiyarta a kidime, kuma lura da yadda hankalinta ya fi komawa kan ‘yarta karama, sai Bilkisu ta dakata daga tarkata kwanuka da take yi, ta matsa kusa da mahaifiyarta ta taba jikin AMISHA, ai kuwa sai da ta ja daga baya, ta ce; “umma! Kin ga abinda nake gaya maki ko, yanzu ina amfnin badi ba rai? Ga shi kin jawo wa Auta ciwo, kila ma pneumonia ce, tashi mu je asibiti”



“ke BILKISU, asibiti cikin darennan? Hala su ma’aikatan asibiti injimumuka ne da za’a tarar da su a wannaan lokacin, hudun dare fa ta kusa”



“ranar a Islamiyya, malaminmu ya gayamuna cewa, ma’aikatan asibiti sukan yi musanyar lokutan aiki, wasu kan yi da safe wasu da rana wasu kuma cen suke kwana suna aiki, kinsan sha’anin lafiya, ko da yaushe takan kama mutum ya nemi zuwa ganin likita, tunda ciwo ai ba sanarwa yake yi ba Inna, ki daure mu tafi, rayuwarta za ta iya shiga wani yanayi idan muka jinkirta.”



Nan ta yi ajiyar zuciya mai tsayi sosai, sai ta suri AMISHA wacce sai rawar sanyi take yi, ba ko mayafi a tare da ita ta fito cikin tsalelen dare karfe uku da mintuka, bayanta kuwa BILKISU ce da hijabi da zanen da ke a jikinta duka sun jike sun kame sosai a jikinta, har yanzu kukan SAJIDA take yi tana tafiya cikin sauri, hannunta daya a kan yarinyar dayan kuwa shi ne dauke da ita.



Suna zaune ne a unguwar Bulaburin sai suka nufi asibitin TH wato UNUVERSITY OF MAIDUGURI TEACHING HOSPITAL wacce wasu suke kir da TH wato teaching Hospital ko COSTIN kai tsaye. Haka suka ci gaba da tafiya, har suka karaso a gada ta GWANGE, ruwa sai wucewa suke yi ta karkashin gadar da karfi dauke kuma da sauti, suka wuce gadar suka karaso GWANGE suka wuce ta police station, abin mamaki duk da matsala da ake fama da ita na hare-haren BOKO HARAM, sam ba su hadu da jami’an tsaro ko daya ba, suka wuce suka karaso MARAZINE HOTEL da ke kusa da TH. Isowarsu TH suka tarar da kofar a bude inda mai gadi yake ciki abinsa yana ta sharar barci. A ranta tace oh! Wacce irin kasa ce wannan muke ciki? Suka shiga daga ciki, ga parking space bayan da suka wuce ta gefen hagu daga round about da ke cikin asibitin ganin sai ta rasa ina za su nufa, ganin labour ward, duk da ba karatu mai zurfi ta yi ba, tasan cewa layin masu haihuwa ne, hakan ya sa ta ci gaba da dubawa, har idanuwanta suka kyalla mata inda aka rubuta A&E wato accident and emergency a upstairs, hakan ya bata damar kara kaimi suka taka ta matattakalar suka isa, abin mamaki sai ta tarar da masu aiki a zaune sai faman fira suke, ga roaster a gabansu dayar ce rike da biro inda dayar ke dube –dube a cikin wayarta, dayar kuwa tana zaune tana saurar surutu, ta fahimcii hakan ne sandiyar su suna da wuta, kasancewar an tada gen.



Gaba daya suka mayar da hankali wurinta, “‘yaruwa lafiya?” dayar ta fadacikin damuwa. Kuka na kokarin kwace mata ta yi musu bayanin komai, cikin sauri, dayar da ke rike da biro, ta taso ta karbi ‘yar, jin yadda jikinta ya yi zafi, kuma ga kakkarwa da take yi, yasa ta yi sauri ta shiga da ita wani daki da ke da gado kwaya daya, ta kwantar da ita, bayan ta nemi pulse na ta ta kara bincikar me ke damunta sai ta fito ta sami mahaifiyarta, ta ce da ita; “haba ‘yaruwa ke wacce iri ce, za ki bari ‘yarki ta sha kashin ruwa haka? Ga shi yanzu saura kiris ta rasa rayuwarta, ga ki da alamun mai hankali, amma kina irin wannan, diya `fa rahama ne, kuma ansan uwaye musamman mata da kauna hadi da nuna kulawa gun diyansu”


“ki yi hakuri ranki ya dade, wasu lokuta abubuwa sukan faru, amma mu mutane ba ma da ikon hana faruwar haka, amma da ikon Allah haka, ba za ta sake faruwa ba”




“Allah ya sa; ina mahaifinta?”




Nan idanuwanta suka faar fiki-fiki, cikin rawar murya ta ce “ya yi tafiya ne, amma gobe zai dawo”



“zo” suka shiga ta mata wasu allurai guda biyu, sai ta rubuta mata wasu magunguna ta ce idan safiya ta waye sai ki siyo, a dinga bata, inda za ki sayo za su maki bayanin yadda za ayi amfani da shi, amma ki dinga kulawa don Allah”




Suka yi godiya, suka kwana nan asibiti, a rayuwar SAJIDA, ba ta taba kwana a wuri lafiyayye ba
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment