Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ο»Ώ[8:50pm, 30/03/2016] πŸ’“Princess✍🏼: ☘🍁☘ZAFIN SO☘🍁☘
🍁 🍁
☘🍁☘
🍁
1
Na
Amrah
πŸ”† GHWπŸ”†
Da
Haneefa Usman
NWA

GARGADI:
Bamu yarda wani/wata suyi copy and paste na wannan labarin ba, duk wanda ya aikata hakan mun barshi da Allah mai kowa mai komai.

KALAMAN GODIYA:
Duk kan yabo da godiya sun tabbata ga Allah madaukakin sarki, ka qara tsira da aminci ga manzon tsira annabin mu Muhammad (SAW) tare da alayensa, godiya ga duk kan masoyan mu maza da mata aduk inda kuke, duk da wannan shine farkon rubuta novel din mu nida Hanee, muna fatan ku kasance tare damu a wannan labarin, karku bari a baku labari.

☘🍁☘SHIMFIDA🍁☘🍁
Wannan labarin ya qunshi labarin wata yarinya matashiya wadda ta tashi a cikin gatan iyaye, sai dai kuma kash! Tayi amfani da wannan damar data samu ta hanyar wulaqantar da duk wanda yake qasa da Ita, wanda a sanadiyyar hakan ne zata samu dana sani daga qarshe.

'Yan uwan mu musulmai! Ku sani kar kuga Allah ya baka lafiya, dama, lokaci da kuma dukiya, kayi amfani dasu ta hanyar nuna rashin godiya da ya baka su, ku sani! Akwai dubban mutane da suke neman lafiya, dama, lokaci da dukiya amma basu samu ba, tou dan me kai/ ke kun samu wannan damar sai ku lalata su? Muna roqon Allah daya qara shirya mana zukatan mu, ya bamu ikon amfani da lafiya, da dama da Allah ya bamu.

COMING SOON................✍🏼

Haneefah and Amrah
☘🍁☘
🍁
[7:26pm, 2/04/2016] πŸ’“Princess✍🏼: ☘🍁☘ZAFIN SO☘🍁☘
🍁 🍁
☘🍁☘
🍁


Na Amrah πŸ”†GHWπŸ”†
Da Haneefah NWA
page1⃣-2⃣
☘🍁☘
🍁

Tafiya muke nida Hanee ko waige bama yi, da abn yayI nisa ma har gudu muka koma yi duk dan muga mun tarar da wannan hamshaqiyar yarinyar, bamu muka tsaya ba sai bakun wani qayataccen gida wanda da ka ganshi gasan na wani mai muqami ne, a daidai vakin gate yarinyar ta tsaya da motarta qirar range rover ash colour, horn tayi amma shiru ba'a bud'e gate ba, sai bayan kamar minti biyu ta qara wani horn d'in amma shiru gate man bai bud'e gate d'in ba. A fusace ta fito daga mota ko jakarta bata d'auka ba ta bar motar bud'e ta shiga gidan. Koda shigarta ta samu gate man d'in kwance yana rawar sanyi alamar baida lafiya, bata ko duba yanayinshi ba ta d'aga hannunta ta wanke shi da mari, dafe kumatunshi yayi wani zazzafan hawaye na saukar mishi, kafin ya ankara ta qara d'auke shi da wani marin, sai a lokacin tace "kai uban waye da zanyi maka horn har sau biyu amma ka kasa bud'e min gate? Bayan kuma kasan bisa ga d'abi'ata horn daya kawai nakeyi ko sallah kake dole kabarta kazo ka bud'en gate in shigo gida, mtswww wawan banza!".
Fita tayi bata koma takan motar ta dake waje ba, tayi tafiya mai nisa kafin ta isa inda farfajiyar gidansu take, shiga tayi kai tsaye babu ko sallamah. Ta samu momy kishingide ana mata matsar qafa, fad'awa tayi jikinta tana mayar da numfashi, a firgice momy ta miqe zaune tana fad'in "na shiga uku, auta me ya faru dake na ganki kamar ba'a hayyacinki ba?". Kyakkyawar budurwar tace "momy wai waye ta kawo mana wancan wawan a gidan nan?", momy tace "wa kenan?", a shagwa'be tace "gate man d'in can mana". Momy tace "ai! Wai baba faruku? Dady da kanshi ya kawo shi wai yana tausayinshi ne, me ya miki ne auta ta?", "momy wai har sau uku ina horn amma yaqi bud'en gate, motar ma tana can na bari a waje har da key d'in yana jiki ban cire ba tsabar takaici", miqewa tsaye momy tayi tace "auta! Baki da hankali ne? Baki gudun a sace ta ne? Kin san fa jiya aka kawo ta, waccan d'ayar ma ajiyeta kikayi fa aka sace miki a gidan biki". Kamar tana jira momy ta gama maganar aikuwa ta fashe da kuka tana fad'in "momy! Yau nice kike yiwa fad'a har da nuna min yatsa? Momy tunda nake baki ta'ba yi min haka ba, a dalilin wancan wawan tsohon gate man d'in? Tou barin je inda yake, wlh sai yabar gidan nan, ko uban wa ya tsaya mashi".

Haneefa Usman
Princess Amrah😘
☘🍁☘
🍁
[6:58pm, 7/04/2016] πŸ’“Princess✍🏼: ☘🍁☘ZAFIN SO☘🍁☘
🍁 🍁
☘🍁☘
🍁

Na AmrahπŸ”†GHWπŸ”†
Da Haneefah NWA
Page3⃣to4⃣
☘🍁☘
🍁

Fita tayi ko dan kwali babu a kanta, bata ko nemi takalmi ba ta kama hanyar d'akin me gadi, ta same shi still yana rawar sanyi wadda tafi yanda tabarshi d'azu. Bara jira komai ba ta fad'a d'akinshi, finciko shi tayi ta jefar waje, ta duba bakin katifar shi taga wata qaramar Ghana most go, dauko ta tayi ta jefa mashi a daidai isowar momy wurin, fitowa tayi daga dakin tace "a dalilinka momy na tayi man fad'a harda nuna ni da yatsa tayi, wlh yau sai kabar gidan nan, tsohon banza zaka nemi takurawa rayuwata, sai ka koma qauye aci gaba da cin tuwon dawa ai, mtsww" taja tsaki tare da barin wurin.
Abn haushi wai momy ta kasa ce mata komai, har tayi nisa da qyar tsohon nan me gadi yace "SAFNA!!! Ni kika wulaqanta haka? Ni kike kira da tsohon banza? Ko da yake banga laifinki ba, laifina ne da na qasqantar da kaina nake bauta a gidanku, hmmm!! Neman halak kenan, insha Allahu yanda na nema gareku kina wulaqanta ni bayan kuma nayi jika dake, ina roqon Allah ya kawo ranar da kema zaki nema a wuri na...." ya qarasa maganar cikin kuka da ban tausayi.

Da sauri ta dawo wurinshi ta sake wanke shi da mari tace "ba amin ba tsohon NAJADU!! Allah ya fika, kuma ni bazan ta'ba nema a wurinka ba, babana yana da kud'in da ko bayan ranshi zanci har in kyautar wa mabarata irinka" ta tofar da yawu qasa tace "tir! Da MUMMUNAN FURUCINKA".
Barin wurin tayi da gudu saboda qunar da zuciyarta ke mata. Momy bata ce komai ba sai bin bayan 'yarta da tayi tabar me gadi nata goge hawaye. Bayan kamar minti biyu yaja Ghana most go d'inshi ya fita. A hankali yake tafiya dan yana tsananin jin zazza'bi.



Da qyar ya samu yaje tasha ya hau motar qauyensu BAGARUWA, d'an chanjinshi ya biya kud'in mota ya isa. Ya samu Nawwaf na zaune qofar gida ya buga tagumi, koda yaga babanshi tuni ya tashi ya nufI wurinshi ya kar'bi jakar suka qarasa ciki yana mashi sannu da zuwa.

Haneefah Usman
Princess Amrah😘
☘🍁☘
🍁
[6:58pm, 7/04/2016] πŸ’“Princess✍🏼: ☘🍁☘ZAFIN SO☘🍁☘
🍁 🍁
☘🍁☘
🍁


Page5⃣to6⃣
Na Amrah
☘🍁☘
🍁


Da shigar shi gida bai jira komai ba ya kwanta kan wata tabarma dake shimfide a bakin qofar d'aki, NAWWAF dai sai bin babanshi yake da kallo ganinshi da yayi sukuku, "Abba sannu da zuwa", ya ansa da "yauwa NAWWAF, ina umman taka?",,,,," tana daga ciki ina jin, Ummah!", "ga ni nan, zuwa fa, aahhh lale marhaba da mutan birni, sannu da hanya" ummah ta fada tare da fitowa daga daki.

Wasu irin zafafan hawaye suka fara ambaliya a fuskar Abbah, duk hankalunsu ya tashi ganin abbah na kuka, a rude NAWWAF yace "abba wai me ya faru ne? Tunda kazo naga kana da damuwa a zuciyarka, ka fada mn matsalarka wlh na dauki alqawari indai ina da maganinta".
Ummah tace "malan meke faruwa da kai, kuka fa kakeyi, tunda nake dakai ban taba ji ko ganin kayi kuka ba, amma da mamaki sai gashi yau kana yi har idonka yayi jaa".

Sun d'auki tsawon lokaci shiru basu samu ansa daga Abbah ba, jin bashi da niyar basu ansa ne yasa Ummah tayi qarfin halin cewa "ka watsa ruwa malan ka kwaso rana sai kaci abinci". Baice mata komai ba ya miqe jikinshi na rawa ya nufi toilet. Da gamawarshi ya fito, abinci kawai yaci ya kwanta bacci yayi gaba dashi.

NAWWAF duk abn duniya yabi ya dame shi, sai zaman tagumi yake har abba ya farka yaga Ummah zaune kusa dashi tana hawaye, ga NAWWAF ma zaune a gefen Ummah, ganin su cikin wannan halin yasa shi cewa "kuyi haquri, bana son na fada maku abnda zai saku bacin rai ne shi yasa naqi fada maku, amma tunda kuna son ji yanzu zan fada",,,,,,,,,,nan ya hau basu labarin duk abnda ya faru tun farko har qarshe.

Zumbur NAWWAF ya miqe tsaye yace "Abbah ka bar naje Katsina na samu jakar yarinyar nan, wlh sai naci mutuncin ta kamar yanda taci naka mutuncin, kawai qaramar yarinya ta kiraka da tsohon banza, munafuki, Subhanallah! Abbah yau yau din nan zan tafi". Bai jira komai ba ya tafi dakinshi da nufin canza dressing.
Tsawa daya abbah ya mashi dole ya tsaya, abba yace "na saka ne? Wau kai NAWWAF yaushe zaka rage wannan ZAFIN zuciyar taka ne? Ya kamata fa kasan ka girma, kuma nace kabarta da duniya, duniya zata bida ta, ai laifi na ne da naje gidansu da aiki, kaga inda ace banje ba ai da bazata ci min mutunci ba, amma yanxu da nabar gidan ba shikenan ba? Sai kuma tayiwa wani ai".

Ummah tace "hakane malan, tou amma yanxu idan ka dawo gida ka zauna ya zamuyi da abincin da zamuci? Shi NAWWAF bai iya ko wace sana'a ba, shidai karatun boko kawai ya tasa a gaba, ni fa yanxu kusan shekarar shi biyu kenan da gama degree dinshi, har service ya gama amma babu wani aikinyi kullun sai zaman qofar gida yake, sai matacciyar zuciya kawai".
NAWWAF da hawaye ya wankeea fuska yace "Ummah indai hakane zan nemi kudi insha Allahu, neman kudi kuma ta tsaftatacciyar hanya, zan nemi halal insha Allahu ko ta hanya mafi wahala ne".

Dedicated to Rerbee'art sk msh❀

Princess Amrah😘
[7:07pm, 11/04/2016] πŸ’“Princess✍🏼: [5:48pm, 11/04/2016] πŸ’“AmrahπŸ’“βœπŸΌ:

☘🍁☘ZAFIN SO☘🍁☘
🍁 🍁

☘🍁☘
🍁


Page 9⃣toπŸ”Ÿ
Na Amrah
☘🍁☘
🍁

Koda sukaje kuwa sun samu Mal. Shazali anyi layi a gidanshi kowa da abnda ya kawo shi, Hamza yace "sai kabi bayan wannan na qarshen",
Nawwaf yace "yanzu wannan uban layin duk sai na bishi?",
Hamza yace "qwarai kuwa sai ka bishi, da haka kowa ya fara har aka kaiga na farko, yanxu za'azo kanka ai tunda naga duk masu bada balance ne",
Nawwaf yace "tou".


Layin yaita bi har akazo kanshi, mal. Shazalin da kanshi ya bashi kurar amma fa yasha gargadi kafin a bashi, da alqawarin zai ringa kai balance kullun yabar wurin cikin farin ciki da zumud'I, harda jarkokin aka bashi yaja suka kama hanyar gidan hayar da hamza yakeda daki a ciki.


TUSHEN LABARI.
Alhaji Marwan d'ane ga malan Sani mai gilashi, ya taso cikin tsananin talaucin iyaye, tun yana dan shekara biyar aka sakashi makarantar primary, daqyar da wahala suke samun kudin breakfast ma dan su kansu wanda zasuci wahala yake basu, mal. Sani kuwa baida wata sana'a kullun yana zaune a gida, baki daya xuciyarshi ta mutu, baya da wani burin tashi ya nemi na kanshi, Rabi itace matarshi, mata mai kokarin neman na kanta, kullun naseeharta daya ce wadda bata wuce mal. Sani ya nemi halak ba, amma sam baya daukar maganarta, wani lokaci ma sai yace wai gori take mashi dan taga itace ke ciyar dasu, har kuka takeyi idan ya fada mata haka.

Bayan shekara biyu a lokacin Marwan yana da shekaru bakwai a duniya kwatsam Rabi ta samu juna biyu, tayi godiya ga Allah amma sam abn bayyi mata dadi ba, saboda abincin da zasuci ma wahala yake masu, tun suna su uku kenan ina ga sun qara yawa, mal. Sani yaji dadi sosai data sanar dashi tana dauke da juna biyu,
Bayan kamar kwana uku da sanar dashi da tayi tace "mal. Kaga dai yanxu ina da ciki wata uku ya kamata ka fara qoqarin neman na kanka tun kafin lokacin yayi kuma aita daddafe daddafe a rasa yanda za'ayi",
Mal. Sani yace "sata kike so nayi ko yaya? Ko kuma ke zaki bani jarin?",
A zuciye Rabi tace "nifa malan ba haka nake nufi ba, me zaisa nace kayi sata? Amma kuma ai akwai hanyoyin neman kudi da dama wanda akeyi, kai kenan kullun kwanxe a gida, ni kwance kaima kwance babu mai tada wani",
Yace "kyayi kya gama Rabi, ni banda Inda zanje idan kin matsu ki fita kiyi dako", yaja tsaki ya shiga dakinshi.

Dedicated to Rerbee'art sk mshβ™₯

Princess Amrah
☘🍁☘
🍁
[6:08pm, 11/04/2016] πŸ’“AmrahπŸ’“βœπŸΌ:

☘🍁☘ZAFIN SO☘🍁☘
🍁 🍁

☘🍁☘
🍁

1⃣1⃣to1⃣2⃣
Na Amrah
☘🍁☘
🍁

Haka Rabi taita jan cikinta cikin rashin kulawa har yakai wata bakwai, alokacin ne ta yanke shawarar tsaida duk wani aiki da takeyi kamar; dakau, wanki da guga na kudi da sauransu. Bayan cikinta ya cika wata tara Ta samu da qyar da wahala ta tattar dubu sha daya harda tsohuwar ajiya, taba mal. Sani tace "mal. Ga wannan, a siyo ko qaramar tunkiyace wadda za'ayi yanka, idan kudin sun samu chanji sai a yo mana cefane. Ni kuma akwai dubu biyu hannu na sai in siyo kayan jinjiri dasu",
Mal. Sani da murmushi yace "yauwa uwar gida, wlh kina burgeni, zuciyar maza ne dake", bata bashi amsar komai ba da qyar ta shiga makotansu gurin A'I me kayan koli, irin kayan nan masu hangan roba ta siya wasu na mata wasu na maza ta hada kala takwas dasu sannan ta koma gida.
Ta samu mal. Sani bayanan a tunanin ta ya tafi siyo tunkiya dan ta fada mashi ta fara jin naquda. Bayan kamar minti arba'in mal. Sani yazo yana kuka,
"Me ya faru ne malan?"
Yana goge hawayen yace "dama na siyo tunkiyar ne na hadu da wasu mugaye a hanya suka qwace suka min duka a hanya", ido bude Rabi tace "tunkiyar? INNA LILLAHI WA INNAA ILAIHI RAJI'UUN" ji kake tiiiiii ta fadi qasa, hankalinshi bai ko wurin yaci gaba da "kuma fa uwar gida da sauqi aka samu tunkiyar, naira dubu tara aka bar min ita, baki ga girmanta ba qatuwa da ita",
Jin shiru ba amsa ne yasa shi cire hannunshi daga Ido da yake murzar qwallan qarya, ganin jini nata malala daga jikin Rabi yasa shi fasa ihu a daidai shigowar Marwan,
"Abba me ya samu mamana? Jifa jini na fita, mama ki tashi dan Allah", kuka yake sosai abn tausayi yace "abba kaine ka duki mama ko?",
Mal. Sani yace "wlh ban duketa ba Marwan",
"Ka duke ta mana Abbah! Ga jini na fita, ai idan ba'a duki mutun ba jini baya fita",
Bai kuma bashi ansa ba ya samu ya ciccibi Rabi ya saka a baro ya kama hannun marwan da hannu daya, dayan kuma yana tura baron.

Dedicated to Rerbee'art sk mshβ™₯

Princess Amrah
☘🍁☘
🍁
[6:30pm, 11/04/2016] πŸ’“AmrahπŸ’“βœπŸΌ:

☘🍁☘ZAFIN SO☘🍁☘
🍁 🍁

☘🍁☘
🍁

1⃣3⃣to1⃣4⃣
Na Amrah
☘🍁☘
🍁

Basu zarce ko ina ba sai qaramar asibitin dake cikin qaramar hukumar Kaita, da hanzari aka kar6eta domin ceto rayuwarta, sun dauki kimanin awa biyar akanta,
Wata nurs ce ta fito tace "wa keda Rabi'atu Sani?",
Da sauri mal. Sani yace "ni nazo da Ita, ina fatan
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment