Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Compiled By Umar Dalha Funtua.

*_Typing📲_*



🤰🏻
*_CIKI DA GASKIYA........_*
_{🔪wuk'a bata hudashi🗡}_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*



*_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*
_~Home of experts and perfect writers~_


*_Sadaukarwa_*
_My sweet dady_
~(ALLAH ya gafarta maka)~
🤲🏻😭



*_part 2_*
(littafi na biyu📕)

*_Ina mai farin cikin sake had'uwa daku a CIKI DA GASKIYA.....kashi na biyu, ALLAH ya amfanar damu abinda ke cikinsa, kuskurena kuwa ku watsar dashi gefe, dannima mutumce kamar kowa ajiza, ALLAH ya mana jagora, yajikan mahaifanmu dadukkan musulmai baki d'aya._*
Ina godiya agareku sosai😘😘😘.


➡1⃣

Fadeela dake bayan Aysha tace, "gwaggo! Dama kece babu lafiya?, ina mama taganoki?.
Duk atare tajero tambayar.
Da k'yar Gwaggo bintu take fidda numfashi, da yak'en dole wa Fadeelah, Aysha kam takasa cewa komai, jitake tamkar takashe gwaggo bintu kawai kowa yahuta.
Wani mugun plashing yashigo wayarta, saikuma sak'o yashigo, samun kanta tayi da ciro wayar daga post d'in hannunta taduba.

_karki yarda kiyi wani abunda zai nuna gwaggonki tayi wani mugun Abu akanki, hakan tamkar wargaza aikinmune, ki kiyaye, so kisan yanda zaki nuna komai normal tsakaninki da ita saboda sister d'inki, karki 6atamin aiki._

Abinda aka rubuta kenan kuma an 6oye number, Aysha takuma maimaita sak'on a karo Na biyu, cikin mamaki tace wanene wannan?......
Muryar gwaggo bintu ta tsinkayo tana fad'in Aysha da gaske kece? Kece kika dawo garemu? Tayi maganar tana rushewa da kuka.
Da sauri Aysha taje ta rungumeta, ta fakaici idanun su fadeelah tafad'a ma gwaggo bintu magana a kunne, _gwaggo kada kiyarda ki nuna wata alamar dazata gane kin saka rayuwata agarari, wlhy inba hakaba sai an kasheki, kinuna murnar dawowata daga karatu, Dan ALLAH ya juya zalincinku agareni yazama alkairi nayi karatun._.
Su fadeelah dabasu San abinda ke faruwaba suka Shiga lallashinsu, fadeelah ta janye Aysha daga jikin gwaggo bintu tana bata hak'uri.
Bak'aramin mutuwa jikin gwaggo bintu yayiba, tabbas maganar Aysha ta shigeta, _(nace karan bana aishi ke maganin zomon bana gwaggo bintu😂)._
Aysha takoma kusada gwaggo bintu ta zauna, bishirah jitake tamkar cinye Aysha dan murna, suna rik'eda hannun juna, kai Aysha wlhy kin canja, ilimi dad'ine dashi, kamar bakeba wlhy😁.
Dariya Aysha tayi, wlhy nima duk kin canja mini bishirah, kinzama babbar budurwa, halan kinkusa aure ma?.
Hhh saura wata 2 ma.
Eyeee Ashe zamusha biki, ALLAH yasanya alkairi.
Ameen fadeelah ta amsa.
Sund'an dad'e a sibitin, amma gwaggo bintu takasa sakin jikinta, sai yanzu nadama da Dana Sani ke k'ara yawa a zuciyarta, taci amanar d'iyar zumunta, gashi wadda tasata aikata hakan y'arta ta azabtar da ita, tunda ta kwanta asibitinnan babu jinin hajia babba ko d'aya daya lek'o dubata, bare ita hajia babban, lallai tayi kuskuren dabatasan tushen gyarashiba, afakaice taketa share hawaye, Wanda Aysha Ce kawai talura dasu.
Aysha taja bishirah gefe suka zauna.
Bishirah nikam bayan barina gidannan miya farune?.
Humm abubuwa dayawa sun faru Aysha, ciki harda Auren da alhaji ya k'ara, tas bishirah takwashe komai tafad'ama Aysha, har zuwan gwaggo bintu Lagos da dawowarta, harda sanadin kwanciyarta a asibitin.
Aysha tace ALLAH ya kyauta.
Itama bata 6oyema bishirah komaiba, tabata labarin komai akan abinda yafaru da'ita, kuka sosai bishirah takeyi harda majina, tad'ora mata bayani akan amaryar alhaji mahaifiyartace.
Bishirah kinsan miyasa na baki labarin sirrina kuwa?.
A'a saikin fad'a Aysha.
Saboda ki taimakeni, kuma Dan ALLAH ki rik'emin sirrina, zan d'auki fansa akan hajia babba da sauran mutanen k'ungiyarsu, amma hakan bazai faruwa saina samu wasu sirrika atareda ita.
To Aysha wane taimaki kikson namikine?.
Kawo kunnenki.
Aysha tagama fad'ama bishirah abinda nikam banjiba🤷🏽‍♀.
Daga nan suka cigaba da tattaunawa akan al'amuran rayuwa dakuma yanda zasu 6ullowa komai kafin auren bishirah.
Hango fadeelah dake nufosune yasakasu mik'ewa suna dariya.
Aysha tace yi hak'uri yaya fadeela munbarki ke kad'ai, kinsan andad'e ba'a had'u baneba.
Batace komaiba sai juyawa tayi sukabi bayanta.
Koda suka koma basu dad'eba sukamusu sallama, Dan itama gwaggo bintu suna saran sallama yau da daddare.


_____________________________

K'arar dasukajine tasakasu farga da abinda ke faruwa, da sauri babban yaron Barau modibbo yalek'o, ganin jami'an tsaro yasakashi rikicewa, yunk'urawa yayi danufin guduwa amma sai hakan ya gagareshi, sakamakon harbinsa da Joseph yayi a k'afa.
Da sauri ya khaleel dake la6e kusadasu yafito shima, saukar harbi yaji a hannunsa Na haggu.
Da sauri yadafe wajen tareda kallon saitin da'akayo Harbin, barau modibbone, yakuma Harbin ya khaleel a ciki, amma bata shigaba, saboda rigar dake jikinsa mai kare shigar bullet.
Ganin haka barau modibbo yajuya da sauri zuwa wani d'aki.
Cikin sassarfa ya khaleel dawasu ma'aikata suka take masa baya, dukda d'an Karen azabar da hannunsa ke masa, ga jini tuni yafara jik'a yellow d'in rigarsa.
Neman duniya sunrasa inda barau modibbo yake, babu binciken dabasuyiba agidan, amma babu ko alamarsa.
Basusan ya silale tawata k'ofaba yabar gidan tabaya, dama antanaji k'ofarne saboda irin wannan ranar.
Saidaga baya ya khaleel yafarga da k'ofar, cikin cije le6ensa yatura Waldrop dake wajen gefe, cikin nazarin k'ofar yace, Taheer inaga yagudu ta Nan.....
Awahalce yake magana saboda jiri daya fara gani, sakamakon jinin dake zuba a hannunsa.
Suduka suka k'araso wajen da sauri, wasu fita sukayi, inda k'ofar ta kaisu harcan baya, alamar tashin motarsa suka gani, wannan ya tabbatar musu cewa yagudu.
Dawowa sukayi inda ya khaleel yake dafeda hannunsa, sai faman lumshe idanu yakeyi.
Da sauri Adams yak'araso wajensa, sunma manta boss yasamu harbi, youseef ne ya yago bedsheet d'in gadon da hanzari Adams yakar6a ya d'aure hannun ya khaleel Dan tsaida zubar jinin.
Basu wani 6ata lokaciba sukabar gidan da gawar wad'anda ya khaleel ya kashe, saikuma yaraonsa dasuka kama.
Dr Abraham sukakira, yace yana General hospital, suyi hak'uri su sameshi a can, Dan sun fad'a masa boss ne yasami harbi.
Da sari Adams ya amsa da to, Emmanuel muje general hospital.

motar Ramadan na niyyar fita daga Asibitin tasu ya khaleel tashigo, Ramadan yace ai wannan motar ya khaleel ce, yay maganar yana taka birki.
Wani irin fad'uwar gaba Aysha taji, tuna a yanayin daya fita d'azun, fitowa sukayi sudukansu. Ramadan yanufi motar da Sauri.
Da kansa yafito, saida kana ganinsa kasan babu lfy, Dan dak'yar yake d'aga ido ya kalli hanya, wannane ya haddasama tafiyarsa d'an rangaji.
Da sauri Ramadan yak'arasa ya rik'eshi yana fad'in ya khaleel lfy?.
Cikin jarunta irin tasa yace, shiga dani ciki, mubi ta baya. Banason su tada hankalinsu, harbine kawai.

Ta baya sukabi, Aysha da Fadeela suka nufi cikin asibitin hankalinsu a tashe.
Kai tsaye office d'in sa suka nufa, Bahama a ciki.
Babu dad'ewa Saiga Dr Abraham, tareda Adams suka shigo suma.
Duk fita sukayi, suka bashi damar aikinsa, ya khaleel nazaune akan kujera yajingina da bayansa idonsa a lumshe.
Cikin hanzari Dr Abraham yake gudanar da aikinsa.
Ya khaleel akwai jarunta, inbanda matse ido dad'an cije baki babu abinda yakeyi, har Dr Abraham yagama cire bullet d'in, sai zufa ya khaleel keyi saikace ana kwara masa ruwa, dukda kuma ac dake aiki a office d'in, duk wani abinda yadace anmasa, harda allurar barci, dak'yar Dr Abraham ya lalla6ashi ya kwanta a gadon dayake duba marasa lfy, amma da yadage akan gida zaije, Dr Abraham yace yayi hak'uri allurar da akayi masa ta sakesa first, saiya tafi.

Su Aysha Na waje sai safa da marwa sukeyi, ahaka baffah da Ramadan yakira yak'araso.
Cikin tashin hankali yake tambayarsu miya faruda Mu'azzam d'in?.
Adams ne yamasa bayanin harbine, baikai k'arshen zancenba Dr Abraham yafito.
Ya tabbatar musu ancire, kuma ya khaleel yana barci, zaid'an huta danya saka masa k'arin ruwane.
Damuwar tad'an ragu agaresu yanzu.
Amma banda Aysha, daketa share hawaye tun d'azun, idon baffah na kanta, duk abinda takeyi yana kallonta, ganin kukan datakeyi yak'i ya karene yasaka baffah matsawa kusada ita yana lallashinta, da nuna mata tamasa addu'a ba kukaba.

*_hours ago_*

Bayan awoyi kusan 5 ya khaleel ya farka, dama tuni ruwan ya k'are, saboda tashin hankalin da 'yan gida suka shiga yasakasu tafiya gida, lokacin anata sallar isha'i.
Su Aysha tuni baffah yasaka ya Ramadan ya maidasu gida dama.

Duk suna falo kowa jigum-jigim, hajia babba ce kawai babu da y'ay'anta, itama tana 6angarenta jigum, Dan labari yazo mata akan abinda yafaru da ya khaleel d'in.
Shigiwarsu tasaka kowa mik'ewa, kowa yayo Kansu, Dan dukkan mazan gidan suna asibitin, a babban falo yazauna sunata masa sannu.
Ganin yanda suke arud'e yasakashi sakin murmushi, yace kufa kwantar da hankalinku, ni Na warke.
Jiki a sanyaye suketa d'aga kai.
Anty Mamie takawo masa tea, kar6a yayi yana fad'in thanks you Mamie na.
Murmushi tamasa tana jinjina kai.
Ahankali yake sha idonsa Na kallon familien nasa, daduk suke zaune afalon, harsu hajia babba dasuka fito, saidai yanayinta yabama kowa mamaki yau, Dan babu masifa, saidai tanata kaffa-kaffa da ya khaleel d'in.
Ahankali yad'ago idonsa ya sauke akanta, tanacan raku6e bayan Umme amarya, daka ganta kasan a hargitse take.
Guntun murmushi yayi, aransa yace, trouble marker d'ina yau kuma miya maidata haka?.
Aysha dabatasan ita yake kallonba tad'ago ido danufin satar kallonsa, amma sai karaf suka had'a ido, da sauri ta janye nata tana d'an tura baki gaba.
Shima ya kauda kai gefe, ahankali yace anan da hali.
Hajia babba dake gefensa duk hankalinta atashe tace mikace?.
No momy bance komaiba, baradai naje nad'an watsa ruwa, Na rama sallolin dake kaina.
Ok.
Mik'ewa yayi sunata masa sannu.
Hajia babba tabi bayansa, dakanta tahad'a masa ruwan wankan, sai wani dama-dama takeyi dashi, danso take taji idan sun kama barau modibbo.
Abin Na momy mamaki yake bama ya khaleel, Dan bayaune karon farko da'aka ta6a harbinsa ba, amma momy bata masa irin wad'annan abubuwan, hasalima saidai Anty Mamie tamasa.
Baikawo komai aransaba yashiga wankan, itakuma tafita tabashi waje.



*bayan 2days*
Ya khaleel yaji sauk'i sosai, ga kulawa ta musamman dayake samu daga momy da Anty mamie, harma da mama dadukkan sauran 'yan uwansa.
Aysha bata ta6a zuwa gaidashiba a kwana biyunnan.
Daga wajen aikinsa kam lamarin ba'a cewa komai, manyansa dayawa sunzo, hakama wad'anda suke k'asa dashi.

Gwaggo bintu ma an sallamota jiya.
Mama da kanta tayima baffah bayanin dangan takarta da gwaggo bintu.
Baffah yasha mamaki, danbai ta6a zaton hakaba.
Yacema mama to yakamata gwaggo bintu takoma hannunta, baikamata tacigaba da zama mai aikiba, ya y'antata.
Mama taji dad'in haka sosai, Dan dama haka take so.
Wani sepia d'aki aka gyara mata a 6angaren mama.
🤣saidai abinda nalura dashi, gwaggo bintu bata murna da hakan, idan San samune ita kawai ta fece Kano abinta. Amma tana nuna hakan mama zata gane wani Abu, shiyyasa tayi gum da bakinta😂.

Hajia babba duk batasan hidimar da'akeba sai ayau.
Wannan lamari yatada hankalinta, da gaggawa ta aika aka kira mata gwaggo bintu kuwa.

Bintu! Wane labari nikeji agidanan? Kina nufin k! Y'ar uwar fad'ima ce? Idan hakane ina yarinyar damuka tura karatu?.
Ganin yanda tarikice sai abin yabama gwaggo bintu dariya, amma batayiba, mamaki takeyi dama akwai abinda zai tsorata hajia babba haka?.
Bintu dake nakefa, kikamin shiru.
Gwaggo bintu tanisa, tareda fad'in hajia ni k'anwar mijin fad'ima ce uban Aysha dakika kai karatu, amma ki kwantar da hankalinki batasan komaiba, har anzu azatonta d'iyarta tana makarantane, kuma ni bazan ta6a fad'a mata komaiba kinji.
Ajiyar zuciya hajia babba ta sauke, tadafa kafad'ar gwaggo bintu tana fad'in yauwa bintu ngd sosai, shiyyasa kike birgeni, ga wannan kud'in dubu100 ne, kiyi amfani dashi.
Sosai gwaggo bintu ta nuna murnarta, hajia babba ta sallameta tana zabga mata godia.
Fitowa tayi tana mai daria a zuciyarta, tace hajia laurah kenan, aii bazaki ta6a fitaba daga wannan tarkon, Shiga ukuma yanzu kika fara Shiga cikinta wlhy, masu iya magana kance *CIKI DA GASKIYA...* wuk'a bata hudashi aii🤷🏽‍♀ aii.

Nace na hajia babba kam babu *GASKIYAR NAN* nasan 6us!!!!! zamu hudashi🔪🤰🏻aradu😆😆😆🤣.


________________

Da daddare baffah yatara dukkan families d'in nasa, harda Ammah data dawo aranar saga Jigawa............✍





Komi baffah zai fad'a??🤔.
Kumuje zuwa my guys, inaji ajikina alkairine fa😁.
Bara nafara kwaso shoky💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻tun yanzun, kumafa kuyi aradu🤣



🤣🤣inda nace yau zanyi posting bazaku barni Na hutaba😂😂😂😜






😍😍😍😍😍❤❤❤❤❤💋💋💋💋💋
*_Typing📲_*



🤰🏻
*_CIKI DA GASKIYA........_*
_{🔪wuk'a bata hudashi🗡}_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*



*_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*
_~Home of experts and perfect writers~_


*_Sadaukarwa_*
_My sweet dady_
~(ALLAH ya gafarta maka)~
🤲🏻😭



*_part 2_*
(littafi na biyu📕)

_gaisuwa da fatan alkairi *Ayusha Ilyasu & Aysha Galadima*😍😍😍😍😘😘💋_


2⃣

Falon yayi shiru, kowa ya maida hankalinsa ga baffah, dukda ba wannan ne karon farko da aka ta6a irin wannan taronba agidan kuwa.
Amma a wannan karon sai taron yafirgita zuciyar wasu daga cikin al'ummar gidan, musamman ma hajia babba da gwaggo bintu, Dan taron harda su Aysha aciki, da ita kanta gwaggo bintun.
Bayan an bud'e taro da addu'oi Ammah tafara magana.
Nasan zakuyi mamakin wannan taro, to kudaina mamaki, nice nasaka babanku yayishi, maganar gsky taron yashafi wasunku, kuma ina fata yazama alkairi agaremu baki d'aya.
Ta maida kallonta ga baffah, tareda jinjina masa kai, alamar tabar wuk'a da nama a hannunsa.
Baffah yafara da sallama da nasiha, sannan yad'ora da fad'in wannan zama yashafi 6angarorine guda biyu zuwa uku.
Na farko shine bintu wadda kuke kira Maman yara tanada alak'a ga fad'ima, nasan kuma duk kunsan haka.
Duk suka amsa da eh.
To alhmdllh, daga yanzun tafita daga jerin masu aikin gidannan, itama tadawo cikinmu, zata cigaba da zama wajen fad'ima insha ALLAH.
Kowa ya nuna farincikinsa, Dan bazasu iya manta alkairin gwaggo bintu ba akan d'awauniyar yaran gidan, tundaga kan Amatullah taketa d'awainiya dasu, wannan yasaka taci suna Maman yara.
Ayanda nakula hajia babba ce kawai batayi na'am da batunba, amma batace uffanba.
Baffah yaciga da fad'in, akwai yarinyar Hama maisuna bishirah, zatayi aure nanda 2 month's idan ALLAH ya kaimu, to tunda bikinta yataho, itama mun dakatar da ita ta huta, ALLAH ya Sanya alkairi.
Nanma akace amin.
6angare na biyu kuma shine, za'a kawo sabbin masu aiki su hud'u insha ALLAH, dansu zama canji gasu bintu d'in.

Kashi Na uku kuma shine maganar auren Mu'azzam!......
Kowa Afalon saida yad'ago ya kalli baffah, musamman ya khaleel da k'irjinsa yay tsawar hadarin gabas Na tsakkiyar ogusta🤣.
Hajia babba ma ta kafe baffah da kallon kid'ima.
Ammah kam murmushi takeyi.
Aysha kuwa aii atare k'irjinsu yabuga itada ya khaleel😆.lol
Baffah yacigaba da maganarsa yana nazarin kowannensu, dariya taso kubce masa lokacin da idonsa ya sauka kan ya khaleel d'in, amma saiya danne ya kauda kai yana murmushi.
Zaman khaleel ya isheni hakanan, Dan haka Na yanke hukuncin masa aure da mace tagari, wadda Na yarda da ingancin tarbiyyarta, ban hanaka anangaba idan kasami wadda kakesoba ka k'ara.
Bawata baceba illah Aysha y'ar uwarka, yay maganar yana nuna Ayshar.
Mutum hud'une suka zabura alokaci d'aya.
Ya khaleel, Aysha, mama, hajia babba.😂
Ya khaleel yay k'arfin halin fad'in baffah wannan y'ar yarinyar?.
Kaci gidanku iro, dan k'aniyarka bakaine kata6a fad'amin kafison auren k'aramar yarinya ba? Shiyyasa ina dawowa jiya naga wannan y'ar albarka Na sanarma babanka matar aurenka tazo, haka kakeso muzuba maka ido muzama sakarkaru irinka?, ta maida kallonta ga sauran yaran, kutashi kujeku angama daku, inma da sauran bayani a nemoku daga baya.
Kowa mik'ewa yayi yabar wajen, saidai Aysha kuka takeyi Wanda batasan dalilinsaba, Na dad'ine kokuwa Na bak'in cikine?.🤷🏽‍♀

Tambayar dayakamata musani kenan masu karatu😂.


Daga Baffah sai matansa da ya khaleel da Ammah aka bari awajen.
Hajia babba tafara magana cikin 6acin rai.
Gaskiya Alhaji wannan had'in bazai yuwuba, kuma shima aisai atsaya aji za6insa, yanada wadda yakeso aiiko.
Baffah ya dubeta rai 6ace, to aii ban hanashi fad'ar za6in nasaba, shekaru nawa na6ata ina magana d'aya akan mu'azzam? Kinta6a tayani masa magana? Idan namiki maganar bacakike aure lokaci gareshiba?, to aii yanzu lokacin yazo.
Kai mu'azzam wacece za6in taka? Kata6a sanar dani kanada wadda kakesone nahanaka?.
Kan ya khaleel a k'asa yana sauke numfashi da k'yar, saboda damuwar dayake ciki, gawani Abu dayazo ya tokare masa mak'oshi saboda tashin hankalin had'ashi aure da waccan yarinyar da'ake shirinyi.
Ya girgiza kansa ahankali saboda tambayoyin da baffah yay masa.
Shiru yayi baice komaiba.
Wannan ya k'ara hasala hajia babba, tace Ibraheem kabud'e baki kayi magana Dan ubanka, Dan bazan ta6a amincewa jinina yara6uda jinin Fad'ima ba, bazai yuwuba kuwa.
Ya d'ago idanunsa jajur yazubasu kan hajia babba, please momy kiyi hak'uri, banida hujjar bijirema mahaifina, Dan yabani dama tuni, amma nayi sakaki da'ita.........
Rufemin baki mara kunyar banza, ka isa kafad'amin mahaifinka? Nima aii mahaifiyarkace, wahalar ma danaci akanka ko Quarter d'inta baiciba, Dan Ubanka bakai kacemin kanason *_Aleeya d'iyar Alhaji Mudansir Na goma ba?._*
Shine yanzu zaka canja magana anan? Kai sarkin biyayya? To magana d'aya nakeyi banyarda ka auri jinin fad'ima ba, inhar nice *Uwarka!.*
Da Sauri mama ta nuna hajia babba zatayi magana baffah ya girgiza mata kansa, alamar kartace komai.
Shiru tayi ta had'iye maganar ranta Na k'una.
Anty Mamie da umme amarya dai basuce komaiba, amma k'asan ran Anty Mamie tanata farinciki
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment