Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

TSOHON ALKAWARI 1
.
Nazir Adam Salih (Nas)
.
A ranar ashirin da takwas ga
watan Afrilu na shekarar
Milladiyya ta dubu biyu da guda
hudu wacce ta yi daidai da ranar
Laraba na tashi a rude,
kwakwalwata a cunkushe domin
sama ko kasa na nemi sabuwar
basirar da zan yi rubutu na rasa.
Tun misalin karfe goma nake
zaune na sa littafin a gaba ina
kallo har zuwa karfe goma sha
biyu na rana kwakwalwata ba ta
zo min da komai ba sai tunane-
tunane marasa amfani. Ina nan
dai zaune cikin akurkin dakina ni
kadai da biro a hannu sai
jujjuyashi nake yi kamar sigari
daga karshe dai na tabbata ta
kare min dan haka sai na ajiye
biron na mike tsaye gami da
mika kuma cikin damuwa.
"Me ke damuna ne?" Na tambayi
kaina ko da idanuna suka kai ga
shafin littafi na ga ko alif ban
rubuta ba sai na yiwa kaina
murmushi, maganar
makaranta littattafaina ta fado min sa'ar
da suke cewa wai ta qare min,
lokacin da na kasa fito musu da
cigaban
ALJANI YA TAKA WUTA
da kuma
BINDIGAR KWALI NA BIYU
lallai ga dukkan alamu suma da
gaskiyarsu tabbas ta kare min
tunda dai gashi na sa littafi a
gaba na kasa rubuta komai
tsawon sa'o'i biyu.
.
Na gama hakura, na fito kofar
gida kenan sai na hango wata
yarinya dauke da fanteka da
kwanuka a samanta abin
tsautsayi ta zo tsallaka kwata
kenan sai kafarta ta zame,
fantekar a cike take da danwake,
wannan shi ne ya yi sanadiyyar
barkowar wani zazzafan gumi a
kan goshina, zuciyata ta fara
harbawa, sakamakon abin da na
tuna, tabbas na san inda zan je
na samo labari. Na sake duban
dunkule-dunkulen dan wake
burjuk a kasa sai ta tuno min da TUBANI
ina tuno da tubani sai na tuno da dattijo
SIDI MAI JAKA A
cikin sauri na nufi gidan wata
kakata, na yi sa'a kuwa na
sameta a gida. Bayan mun gaisa
sai na ce da ita.
"Tubani nake son ki yi min." Ta
dubeni cikin dariya ta ce "Ka ci
gidanku ja'iri dan nema, kai a
zamaninku ana yin tubani ne? Sai
dai jefi-jefi." Na dubeta gami da
sa alamun nutsuwa a fuskata na
ce. "Dan Allah ki yi min wallahi da
gaske na ke yi, fada min duk
abubuwan da za a saya sai na
baki kudin..."
.
Bata sami damar suturta tubanin
nan ba sai bayan karfe biyu.
Bayan na gama sallar Azuhur sai
na ga ta bade tubanin da yaji
sosai, domin na riga na san Sidi
Mai Jaka zai yi matukar farin ciki
da hakan, na sa ta dada kwarara
masa mai, sannan aka zuba min
shi a cikin kwano.
Karfe biyu da kwata na isa gidan
Sidi Mai Jaka dake bakin kasuwa.
Abin da ya fi damuna shi ne tun
sa'ar da muka rabu da shi
shekara biyu da suka wuce ban
kara zuwa wurinsa ba.
.
Ina isa kofar gidan sai na leka
zauren cikin doki, gabana na ta
faduwa domin kada na yi zuwan
banza ko baya nan. Ga mamakina
Sidi Mai Jaka na nan zaune akan
kujerar katakonsa, carbi a
hannunsa, haka nan akwai lofe a
gefensa a ajiye bisa wani farin
buzu. Sidi Mai Jaka ya dago kai
muka yi ido biyu, ko dakika biyu
ba a yi ba ya shaida ni.
.
"A'aha, yaushe a gari inji ma ki
bako Nas, ashe daman kuna
duniya?" Na dubeshi da dariya.
"Baba Sidi kuma tsofaffi ba ku
bar duniya ba ballantana mu."
Sidi Mai jaka ya fashe da wata
shakakkiyar dariya.
Na dubi Sidi Mai jaka kallon tsaf,
kana idanuna suka yo nazarin
zauren. Ko kusa ko alama babu
wani canji a kamannin Sidi Mai
jaka ko kuma zauren gidan. Wani
abin dadin mamaki kuma shi ne,
tsohuwar rigar nan dake jikinsa
mai kamar rariya, ita ce dai har
yanzu bai sake wata ba, na yi
mamakin karfin hali irin na
wannan rigar, domin sa'ar da na
fara ganinta shekaru biyu da
suka wuce ban taba tsammanin
zata sake wata guda a duniya ba
ta fatattake ba. Har yanzu katon
farin tabaron nan nasa na nan
daraf akan hancinsa.
.
Jikinsa kuwa sa'ar da na dubeshi sai na
fara tunanin me yiwuwa tun
bayan rabuwata dashi a shekara
biyu wankansa bai fi sau uku ba,
me yiwuwa ma sai dai ko alwala.
Amma fa duk da wannan
al'amari na Sidi Mai jaka ina
matukar girmamashi. Shekaru
biyu da suka wuce, wannan
tsoho Sidi mai jaka dogo fari
yankwanannen tsoho, kansa fari
fat, da furfura, farin gemu da
fuska ma'abociyar fadin goshi ya
taba bani labarin wata malamar
asibiti TANI da wasu yan fashi.
.
Sidi mai jaka ya dubi kwanon
dake hannuna cikin farin ciki yace.
"Ko shakka ba na yi wannan
alkawarina ne na TUBANI ko?" Na
ajiye kwanon a gabansa lokaci
guda kuma na matsar da lofen
dake kan farin buzun na zauna
na dubeshi cikin murmushi.
"Tabbas ka canka tubaninka ne."
.
Fuskar Sidi Mai jaka ta washe,
cikin nutsuwa ya mika hannu ya
dauko wata butar roba, ya guntsi
ruwa a bakinsa ya kuskure
bakinsa ya fesar a jikin bango.
Kana ya janyo kwanon tubanin
nan ya bude ya fara kallonsa
cikin nutsuwa.
"Nas, ina me yi maka albishir da
cewa wannan kyauta ta tubani
da ka kawo mini tamkar wani
dan mukullin labari ne da na
dade ina son na baka to sai dai
kuma shekaru biyu kenan yau
rabonka da nan sai yau Allah a
kawoka."
"Haka ne." Na ce dashi, sannan
na dada gyara zama domin na
san sabon labari ya riga ya zo....
.TSOHON ALKAWARI--> 2
.
Shekaru biyu kenan yau rabonka
da nan sai yau Allah a kawoka."
"Haka ne." Na ce dashi, sannan
na dada gyara zama domin na
san sabon labari ya riga ya zo....
Sidi Mai jaka ya birkita manya-
manyan tubanin, sannan ya
dauki tsinke, ya tsiraki wani kato
ya tura a baki, nan da nan
idanunsa suka fara zubar da
hawaye saboda yaji.Ko wace ce
ta yi ma tubanin nan, ba karamin
kwarewa ta yi ba Nas." Sidi mai
jaka ya ce dani. Na gyada kai. Sidi
mai jaka ya cire farin tabaron
dake idanunsa ya sa hannun
rigarsa ya goge idanunsa sannan
ya dubeni ya ce."Nas kune samari
yanzu idan aka ce ka yi auren jari
za ka yi?" Na dubeshi cikin
mamaki na girgiza kai na ce."Ya
danganta da irin macen...koda
yake dai ni a gaskiya baya bani
sha'awa, ni na fi son auren da
muke kaunar juna don Allah." Sidi
mai jaka ya dubeni ya kyalkyale
da dariya ya ce.Abin da Anas
mijin Mabaruka gurguwa kenan
ya kasa fahimta." Na dubeshi a
karo na biyu "Wa yekuma Anas
mijin Mabaruka gurguwa?" Sidi
mai jaka ya tsikari katon tubani
ya jefa a bakinsa."Shi ne labarin
da nake son na baka Nas ban
saniba ko kana da sha'awar irin
wadannan labarai na irin
wadannan mata masu matukar
son kansu a duniya fiye da
kowa?" Na yi shiru na dan lokaci
ina juya, abin da ya ce cikin
zuciyata. A gaskiya ni a son
zuciyata na fi son a bani labarin
yan ta'adda irin wanda ya bani
shekaru biyu da suka wuce, to
amma da yake ni yanzu ta riga ta
kare min dole ne na saurari
komai domin bani da zabi. Wa ya
sani ma ko wannan ma ya fi
wancan labarin dadi."Zan so
kuwa na ji labarin wannan
gurguwa, wace ce ita'" Na
tambayeshi, Sidi mai jaka ya yi
dariya ce."Bi ni a hankali Nas
dadina da kai gaggawa sannu a
hankali zan fara saka ma
zararrukan labarin ina kulla maka
su kamar yanda gizo-gizo ke
sakar gidansa" Sidi mai jaka ya
dan yi shiru sannan ya ci
gaba."Ita wannan gurguwa mai
suna Mabaruka ba a taba samun
wata mace a zamanin ta mai
arzikinta ba, miloniya ce a fagen
kudi, to sai dai kuma wani ragin
jin dadi da ta samu shi ne
gurguwa aka haife ta" Sidi mai
jaka ya juyo ya dubeni."Nas,
domin ka fahimci zaren labarin
nan da kyau, dole ne na ajiyar
zaren labarin gurguwa
mabaruka, na koma na dauko ma
hoton Anas" Na dago kai a
kagauce na kalle shi."Ka ce kuma
da labarin gurguwa za ka ba ni."
Sidi Mai jaka ya gyara tabaronsa
kana ya tsikari tubani guda ya
jefa a bakin salatinsa."Dole ne
mu fara da zaren labarin Anas, in
kuwaba haka ba Nas, ba za ka
taba fahimtar labarin nan ba" Na
gyada kai cikin fahimta."Yauwa
Nas, ina son ka dauki zuciyarka
ka mayarda ita cikin wata
mashahuriyar otal." Na dubi Sidi
mai jaka cikin kaguwa na ce
dashi "Na mayar""Yauwa" Ya ce
dani sannan ya fara.****
"To Nas ga Anas nan a cikin
dakin karbar
baki na otal din yana zagayawa
cikin farin ciki da annashuwa
domin aljihunsa a cike yake da
albashinsa na wannan
watan"Sidi mai jaka ya yi yar
atishawa sannan ya ce."Kafin na
ci gaba bari na baka hoton Anas.
Ka ga Nas Anas dogo ne wankan
tarwada mai kyawun fuska na
ban mamaki. Domin an ce ba
mata kawai ba hatta maza idan
Anas ya zo wucewa sai sun
kalleshi sun yaba da halittar
Ubangiji. Wani karin abin
burgewa kuma gareshi shi ne
duk irinsuturar da ya sa sai ta
karbeshi cif-cif kamar daman da
ita aka haifeshi. Wannan da
kuma iya zancensa da tarairaya
shi ya sa dimbin mata suke
kaunar Anas kamar su hadiyeshi.
Wani abu da zai baka mamaki
Nas, shi ne Anan ba wai yan mata
bane kawai ke son sa, hatta
dattijan mata ma suna kaunarsa
sau da yawa masu budurwar
zuciya daga cikinsu kan yi
kokarin su kaiwa Anas cafka
musamman ma dattijan
zawarawa attajirai. Wani sa'in
Anas ya kan kula su ba don
komai ba kuwa sai don dan abin
hasafin da sukan bashi.Daya
daga cikin abin da Anas ya fi
kauna a rayuwarsa shi ne hira da
kyawawan mata, sau dayawa
Anas ya kan tsinewa talauci sau
daruruwa cikin zuciyarsa, domin
a cewarsa shi ne ya shiga
tsakaninsa da kyawawan mata
masu aji. Duk da yake dai
kyawunsa kan janyo ra'ayin
kyawawan mata, to amma Anas
bai taba gamsuwa ba domin shi
ya riga ya sani, akwai irin
kyawawan matan da kyawunsa
bai isa ya janyo su ba. Wannan
ita ta sa Anas ya yi kurda-kurda
ya sami aiki a Lagwada Hotel. Duk
da yake dai shi ba kowan kowa
bane a otal din domin aikinsa ya
fi karfi a rabon abinci, wani sa'in
kuma ya kan nunawa baki
dakunansu su ta hanyar daukar
dakon yan jakunkunansu, to
amma wannan bata dami Anas
ba domin shi burinsa ya cika. Dan
wannan ita ce hanya daya jal da
zai yi ta ganin kyawawan mata
iri-iri, yanda yake so duk kuwa
da cewa bashi da ko kwabo.
Babban abin farin cikin Anas shi
ne ya ga ana liyafa a otal din,
musamman ma ta bakin aure,
domin tana bashi damar gani
kyawawan mata wani sa'in ma
har yazanta da su. Anas yana
daya daga cikin irin samarin nan
marasa zuciyar nema, wadanda
harkullum kwanan duniya
burinsu su ci BULUS ba tare da
sun sha wahala ba. Dan haka......
.TSOHON ALKAWARI--> 3
.
Wadanda harkullum kwanan
duniya
burinsu su ci bulus ba tare da
sun sha wahala ba.
.
Dan haka Naira dubu takwas din da ake
biyan Anas a wata sun isa su
sashi farin ciki, tun da dai ba zai
iya kokarin samun abin da ya fi
haka ba.Anan, sai Sidi mai jaka ya
yi shiru ya dago kai ya dube
ni."Nas, ina fatan kana fahimtar
hoton Anas da nake ta kokarin
zana ma" Na gyada kai na ce."Ina
fahimta" Sidi mai jaka ya gyara
zama sannansai ya ce."Bari to in
koma da kai can baya kadan inda
nake cewa Anas yana zagaya wa
a otal din cikin farin ciki, lokaci-
lokaci ya kan shafi aljihunsa a
fakaice domin baya son mutane
su fahimci cewar dan albashin
Naira dubu takwas din aljihunsa
yake tabawa. Haka nan shi kuma
bashi da imanin da zai iya jurewa
daidai da minti gudabai taba
aljihunsa ba domin ji yake yi
kamar kudin za su zube.Anas ya
ci gaba da zagaya wa a dakin
karbar bakina otal din ya gaisa
da wancan ya yiwa wannan
wasa har dai ya kawo daidai kan
kanta inda Balaraba mai bada
dan mukullan dakuna ke zaune.
Anas ya matsa kusa da kantar ya
dora hannunsa sannan ya dubi
Balaraba da kyakkyawar fuskarsa
ya hasketa da murmushi fararen
hakoransa suka fito fili."Hajiya
Balaraba ya ya garin
ne?"Balaraba ta dubeshi da
murmushi sannan ta turo biron
dake hannunta cikin kunne ta
fara juya shi, tana kanne
ido."Lafiya lau Anas. Har ka tashi
ne?"Anas ya dubi agogo sannan
ya dube ta."Da saura dai
Balaraba." ya dan yi shiru sannan
sai ya ce."Balaraba ba ki ga
motsin Halima ba ne?" Balaraba
ta girgiza kai."Ban ganta ba,
rabona da ita tun jiya da yamma
kamar ya yanzu da ta zo neman
ka." Balaraba ta ci gaba da susa
da biron cikin kunnenta."Anas,
wai don Allah yaushe za ka daina
yaudarar yayan mutane ne?"
Anas ya dubeta da murmushi ya
ce."Sai kin shirya Balaraba."
Balaraba ta harareshi."Me kake
nufi da sai na shirya?"Anas ya
shafi kyakkyawar fuskarsa."In
har kin yarda za ki aure ni, me zai
sa na ci gaba da yaudara? Daman
ke ce ai ki ka ki da tuntuni kin
amince dani da tuni na yi aure na
huta." Balaraba ta kyalkyale da
dariya."Oh! Anas Allah ya rufa
asiri wallahi wadda bata san ka
ba ka cuce ta." Ta dan yi shiru ta
sunkuyarda kai.Balaraba
bazawara ce, sau uku tana aure
tana fitowa. Da yake tana da
sakamakon diflomarta a hannu
kuma basira ta bace mata
maimakon ta yizamanta a dakin
miji sai ta nemi aiki a otal, a
lokacin watanta takwas kenan da
fara aiki. Tun sa'ar da ta fara
dora idanu akan Anas ta ji duk
duniya babu wanda take kauna
sai shi. Balaraba kyakkyawa ce
daidai misali, to sai dai kuma
bata cikin irin tsarin matan da
Anas ke so, domin a cewar Anas
duk macen da ta fiye gajarta bata
cika kyakkyawa ba ko da kuwa
tana da kyawun fuska. Balaraba
ta so ta cusa kanta a wurin
Anas,to amma irin jeri-jerin
matan da kan zo neman Anas tun
daga cikin gari har otal din, shi
ya gargadi Balaraba ta hadiye
maitarta ta yi shiru. To sai gashi
kuma yanzu Anas da kansa yana
zolayarta da zancen soyayya. Duk
da yake Balaraba ta tabbata
karya yake sai da kalaman nasa
ya faranta mata rai."Balaraba."
Anas ya kira sunanta. Balaraba ta
juyo frgigit."Tunani n me ki ke
yi?" Balaraba ta dago kai ta
dubeshi na dan tsawon lokaci
sannan sai ta ce."Kana da labarin
kayatacciyar liyafar da za a yi yau
a otal din nan?" Anas ya dubeta
cikin mamaki."Tun jiya na sami
labari a wurin Sabi'u amma ni bai
ce dani ta hadu ba." Balaraba ta
dube shi."Ai kuwa tun..."
Kalamanta suka makale a fatar
bakinta ba ta karasa ba. Anas ya
dubeta cikin mamaki sai ya ga
bashi take kallo ba bayansa take
kallo. Can wajen kofar shigowa.
Anas ya yi mamaki domin duk
kusan lokaci guda jama'ar dake
cikin dakin tarbar bakin suna
surutai suka yi shiru na dan
lokaci. Anas ya juyo sosai domin
ya ga abin da ke faruwa. A daidai
lokacin ne to ya hangesu.Wasu
kyawawan mata ne suka shigo
kowaccen suta ci kwalliya ta gani
ta fada. Anas ya ji yawun bakinsa
ya kafe, sannan sai ya lura daya
daga cikin yan matan tana tura
kujerar guragu ta farinkarfe akan
kujerar a zaune sanye da kayan
alfarma masu tsadar gaske, wata
budurwa ce gurguwa, za ta yi
kimanin shekaru ashirin da
bakwai.Koda Anas ya ci gaba da
kallon gurguwar da yan matan
ke turawa, sai ya yi ajiyar
zuciya."Kai amma fa an yi asarar
kayan kwalliya." Balaraba ta
dubeshi da dan murmushi ta
ce."Me ya sa ka ce haka?" Anas ya
dan yi shiru sannan ya dada
waigawa a karo na biyu ya kalli
gurguwar, sannan ya juya ga
Balaraba."Kin san ni ban cika
shiri da munanan mata ba.Dube
ta fa gurguwa mummuna amma
kayan jikinta sun fi na kowa
tsada, ai dole in ce an yi asarar
kayan kwalliya." Balaraba ta fashe
da dariya."Kai dai Anas wallahi ba
ka da kaico, me ya sa kake son
muzanta munana? Suma fa Allah
ne ya haliccesu kamar yadda ya
halicceka kyakkyawa kuma idan
ya so yana iya sa wa ka aure ta......TSOHON ALKAWARI-4
.
Me ya sa kake son
muzanta munana? Suma fa Allah
ne ya haliccesu kamar yadda ya
halicceka kyakkyawa, kuma idan
ya so yana iya sa wa
KA AURE TA."
Anasya harare ta."Allah sawwake,
kin ga Balaraba ni fa bana son
mugun fata, tun da abin na ki
haka ne ma ni kin ga tafiya ta."
Anas ya juya cikin sauri ya nufi
cikin otal din a daidai lokacin ne
to ya hango Sabi'u cikin sauri ya
matsa gareshi."Sabi'u ka ga
wata mummuna da alamun
kudi." Sabi'u ya dubi Anas ido da
ido, akwai wani yanayi a irin
kallon da yake yi da ya sa Anas ya
jigwiwarsa ta yi sanyi."Ya ya na
ga kana yi min wani kallon uku
ahu?" Sabi'u dan lukuti, gajere
ma'aboin son sa kayan turawa
duk kuwa da cewa ba wani kyau
suke yi masa ba, ya gyara
tsayuwa sannan ya dubi Anas "Ka
san
inda kake wage bakinka, in kuwa
ba hakaba wata ran za ka kwana
a ciki. Shin ka san waccan
gurguwa ko wace ce kuwa?"
Anas ya girgiza kai ya
ce."Fahimtar dani." Sabi'u ya
gyara wandonsa wanda ke
kokarin sullubewa ya fado."Ni na
san ba ka santa ba shi yasa kake
kokarin muzantata. To bari in
fada ma, ka ga duk munin nan
nata, wallahi ba muni bane a
gurina, kuma ka ga dai gurguwa
ce to ni a gurina kafafunta sunfi
naka sau dubu amfani." Sabi'u ya
dan yi shiru sannan sai ya dago
hannunsa ya dan daki kirjin Anas
ya ce."Wannan gurguwa da kake
gani ita ce Mabaruka S. Faruk,
daya daga cikin matan da suka fi
kowacce arziki a matan Afirka."
Sabi'u ya ya balligoro ya jefa a
bakinsa sannan ya dubi
kyakkyawar fuskar Anas da
murmushi."Na san ka sha jin
labarinta, me yiyuwa a zahiri ma
baka taba ganinta ba, to yau gata
a otal din ka, bikin cika
shekarunta ashirin da takwas a
duniya za a yi. Mu kanmu nan
otal din ba karamar sa'a muka yi
ba, domin da liyafar a Landan za
a yi sai Mabaruka ta ce ba za ta
iya doguwar tafiya a cikin jirgi ba
domin wai juwa kedamunta
wannan shi ya sa su zuwa nan,
ina fatan ka fahimce ni? Dan
haka Anas ina son ka yishiru da
bakinka domin otal din nan ta yi
muguwar cin riba da liyafar nan
da za a yi, idan ka sake manaja ya
ji kalamanka akan Mabaruka, na
rantse ma har da gemun tsohona
ba za ka sake awa guda a gidan
nan ba za a sallame ka daga aiki."
Anas fuska na tsiyayar da gumi
ya dubi Sabi'u a tsorace. Ya mari
bakinsa da hannu"Shegen baki
yau ya kusan ya janyo min tsiya."
Sabi'u ya fashe da dariya ya
ce."Zo mu je mu fara shirye-
shiryen abubuwan da za su
bukata, ka san fa muke da
alhakin kula dasu." Sabi'u ya juya
cikin sauri Anas ya bi shi a baya
da sassarfa kamar doki. A
zuciyarsa yana tunani, Mabaruka!
Cab! Ai kuwa ya sha jin labarinta
ba tun yau ba. Wani abokinsa ya
taba cewa dashi. "Anas duk
matan kasar nan babu mai
arzikin Mabaruka gurguwa, kai
bar ma ta kasar nan duk Afirka
sai an tona. To amma a
tsammanin Anas da ya ji an ce
tafi kowacce mace kudi a Afirka
ya dauka zai ganta wata
kyakkyawa ajin farko, irin matan
nan masu shekia fuska kamar
madubi irin wadanda duk
tsananin duhun dare sai kaga
surar fuskarsu saboda tsabar
kyau. Abin da Anas ya gani ya
sashi kaduwa musamman ma
yanzu da aka ce dashi wannan
yankwananniyar matar mai
tababben hanci kamar begila ita
ce Mabaruka gurguwa uwar
kudi! Allah mai yadda ya so. Anas
ya ce cikin zuciyarsa.Tun karfe
biyar na yamma aka fara liyafar
farfajiyar otal din babu masaka
tsinke duk inda ka duba motoci
ne manya-manya masu bawo. Da
yawa daga cikin bakin basu sami
damar shigowa da motocinsu ba
saboda cunkuso.Anas da sauran
ma'aikatan dake bangaren girke-
girke suka yi ta rabon kayan
lashe-lashe da makulashe. Dakin
da ake liyafar tangamemen gaske
ne, wanda aka gina shi da
zummar ya dauki mutum dari
uku ba tare da wani ya shaki
numafshin dan uwansa ba, Anas
ya fara waige-waige yana
kokarin ya karewa Mabaruka
kallo.Ya ce gaba da zagaya wa
lokaci guda kuma cikin jama,a
yana yin abin da ya kamata sai
dai kuma akwai wani abu da ke
damun Anas sa'ar da ya kawo
kusa da inda su Mabaruka suke
zaune da manyan kawayenta.
Jikinsa na bashi cewa kamar
kallonsa ake yi a baya. Wannan
ita ta sa Anas juyawa a wayance
ya dubi bayansa. Gabansa ya fadi
ras! Sa'ar da suka hada idanu da
Mabaruka, ko shakka ba ya yi shi
take kallo, haka nan har da
murmushi a fatar bakinta. Anas
ya ji bugun zuciyarsa ya karu
lokacin da yaga kamar mabaruka
ta daga hannu ta yafato shi. Anas
ya shiga cikin rudani domin yana
fargabar kada ya je wurin kuma
ya kasance ba shi take kira
ba.Anas ya waiga bayansa domin
ya ga koda wani take sannan ya
sake juyowa, sai ya ga ta sake
yafuto shi da hannunta. Cikin
rawar jiki ya nufi inda take zaune
tare da sauran kyawawan
matannan. Anas ya ji duk gwiwarsa ta yi rauni kamar ba za
ta iya daukarsa ba domin
kyawun matan da suka kura
masa idanu ya yi yawa, ko kusa
ko alama basu yi kama da irin
yan matan da yake mu'amala da
su a baya ba.Anas ya ratsa a
hankali ta tsakanin kyawawan
tebura ya karasa gaban
Mabaruka. Yana zuwa saiya
rankwafa a gabanta ya ce."Gani
ranki ya dade ko bani ki ke kira
ba?" Mabaruka ta dubeshi da
mummunar fuskarta ta saki wani
abu da take tsammanin wai
tattausan murmushi ne."Kai nake
kira mana" Ta dan yi shiru,
sannan ta ci gaba."Daman so
nake na fada ma don Allah ku yi
sauri ku gama shirye-shiryen
mana, ka ga kamata ya yi ace tun
da wurwuri kun gama komai
kafin mu zo" Anas bai iya dago
kai ya kallisauran yan matan da
ke bayanta ba, to amma
yatabbata duk kallonsa suke."To
ranki ya dade" Anas ya amsa. Ya
yi kamar yamike tsaye ya koma
kan aikinsa to amma sai ya ga
alamun bata gama bayaninta ba.
Mabaruka tadubeshi ido da ido,
kana sai ta yi kasa-kasa da
muryarta ta ce dashi."Ka bar aikin
haka nan ka tafi ka gyara jikinka
sosai, ka jirani a waje idan an
tashi ina son ganinka.
"Kasa-kasa da murya, Ehemm..
Anas ya dubeta cikin mamaki,
lokaci guda kuma ya godewa
hayaniyar al'ummar dake wurin
liyafar domin ya tabbata hatta
kyawawan matan dake jere a
bayanta ma ba su ji abin da ta ce
dashi ba ballantana sauran
jama'a. Shi kansa yasan ba dan
yana kallon motsin fatar bakinta
ba da ba zai taba fahimtar abin
da ta ce ba. To amma duk da
haka yana shakkar abin da ta ce
dashi. Dan haka sai ya ya dubeta
a rude ya ce. "Ban fahimce ki ba
ranki ya dade?" Mabaruka ta yi
masa murmushi ta maimaita.
"Ka je ka sake kayan dake jikinka
ka kuma jirani a waje, idan an
tashi zan turo a yi min kiranka
ina son magana da kai."
Kusan awa daya da rabi ya shafe
zaune karkashin wata
dukurkusar bishiya mai kama da
ta dabino dake farfajiyar otal din
yana jiran tsammani zuciyarsa
cike da tambayoyi sama da guda
dari.
Amma manya-manyan
tambayoyin da suka fi damun
zuciyarsa sune; shin mene ne
dalilin ganawa dashi? Shin laifi ya
yi mata? To ai kuwa har
murmushi take yi masa sa'ar da
take bayanin. To mene ne dalilin
da zai sa ta ce ya sake kayan
dake jikinsa? Babu mamaki ji ta
yi kamar jikina yana wari. Anas
ya ce da kansa. Duk da yake dai
sa'ar da ya baro wurin liyafar sai
da ya yi ta shinshina jikinsa
domin ya ji ko wari yake yi, to
amma har zuwa wannan lokacin
da yake sake kayan dake jikin
nasa Anas bai gamsu ba, lokaci-
lokaci sai ya sunsuna hannun
rigarsa kana ya duba agogon.
Sa'a daya da rabi kenan yana
zaune a gurin yana jira. Tab!
Anas ya yamutse fuska cikin
damuwa. A karo na farko a
rayuwarsa ta harkar mata sai ya
ji ya fadi babu nauyi domin a
tarihinsa wata mace bata taba
sashi ya yi jiranta daidai da na
mintuna biyar ba, sai dai ita ta
jirashi. Amma sai gashi yau
tarihin ya sauya, wai Anas da
kansa ne yake zaman jiran wata
nannadaddiyar gurguwa
mummuna mai dogon hanci da
fadi kamar nakiya, lallai duniya
juyi-juyi! Wannan tunani shi ya sa
Anas ya saki wani tattausan
murmushi a cikin duhun daren
da ya fara shigowa sannan ya
dada jingina bayansa a jikin
bishiyar da yake zaune, ya share
gumi daga goshinsa a zuciyarsa
ya ce.
"Kada ka damu Anas, a da can
kyawawan mata sun yi jiranka, a
yanzu kuwa kai ne kake jiran
mummuna da kudi, ko ba komai
dai ba talaka kake jira ba. Abin ya
kan baiwa Anas mamaki, wata
sa'ar ma har dariya idan ya tuna
da cewa wai daya daga cikin
matan da ta fi kowace kudi a
Afirka yake jira! Anas na nan a
zaune yana ta sake-sake bai ji
zuwanta ba sai muryarta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment