Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

JIKI MAGAYI-01

Copyright ©

Tafidan Zaria 1995

An fara bugawa 1955
An sake bugawa 1971
An sake bugawa 1973
An sake bugawa 1976
An sake bugawa 1978
Ansake bugawa 1980
An sake bugawa 1999 (Sabuntawa)

ISBN: 978-169-109-3
Published by
The Northern Nigerian Publishing Company Ltd., P. O. Box 412 Zaria.

Acikin Birnin Galma, akwai wani mai arziki, sunansa Malam SHEHU, Yana da jakunkunan kudi, da tufafi, da hajjoji, da kekunan dinki, da na hawa, da barori, da shanu a garkuna, da dawaki uku masu kyau suna harbin iska a barga tasa. Kullum da la'asar ya kan tafi barga ya zauna, barorinsa da mutanen gari masu son kwabonsa su zo su kewaye shi, ana! ta nishadi, fadi banza, fadi wofi.

Sabo da tajirancinsa ba inda sunansa bai kai ba, yana aikar yaransa fatauci ko ina, wadansu a jirgi, wadansu a mota, wasu su labta wa jakuna ko takarkarai ko rakuma hajjoji da goro, su shiga cikin kasa suna ciniki. Shi ma da kansa da wuya ya san iyakar dukiyarsa.

Shekararsa ashirin da yin aure, amma bai taba haihuwa ba. Ya yi aure da yawa, kullum gidansa ba a rasa matan aure hudu. Ya Batar da dukiya ba iyaka wajen malamai da bokaye da"yan bori garin neman maganin haihuwa, amma cikin matansa babu wadda ta taba ko batan wata. Ko yaushe idan ya tuna da wannan babbar hasara ta rashin ɗa sai ransa ya dugunzuma, ya dami dukkan mutanen gidansa da fade-fade, wani lokaci ma ba mai ganinsa a waje tun safe har wajen la'asar, yana can cikin dakinsa yana rokon Allah ya biya bukatarsa Ko yaushe addu'arsa daya ce, "Ya Ubangiji ka jikaina ka ba ni Ɗa
KO DA WANE IRI

Ana nan wata rana ya yi mafarki, ya ga wata godiya a gidan Malam Audu an kai ta kasuwa. Wani mutum kuwa yana sonta Kwarai da gaske har ya yi ciniki. Sai shi kuma da ya gan ta ya so ta kwarai kamar me, ya kara kudi aka sallama masa, ya biya, aka kawo masa gida ya daure. Wancan kuwa ya hakura tilas. Godiya tana gidansa har ta haifa masa dan dukushi kyakkyawa wanda kowa ya gani yana sha'awarsa. Da ya yi girma ya isa hawa, ran nan sai ya ce a yi masa sirdi. Aka yi, ya hau ya tafi kilisa. Daga can doki ya haukace ya ka da shi ya tsere, ya bar shi cikin ciwo kwarai.
Da haka ya farka daga barci, duk jikinsa na rawa, ya yi ta wasuwasin wannan abu cikin ransa har gari ya waye. Da assalatun fari ya aika aka kira masa wani malamin kasa. Da ya zo ya ce yana so ya ba shi labari. Malamin ya share kasa ya buga, ya ce, "Na ga maganar aure da kuwa haihuwa tsakani, na ga wani ya kwace gabanka, amma idan ka maida hankali za ka ture shi. Kuma na ga wahala cikin auren nan, in ka yi wata rana za ka yi danasani. In ka bi shawarata kada ka saka yatsa cikin wannan al'amari, ka bar shi yadda Annabi ya bar duniya. Saura Allah shi ya sani".

Bayan da ya tashi Malam Shaihu ya zauna yana birabini a ransa a kan mafarkinsa da abin da malamin ya gaya masa. Sai ya fado masa a rai Malam Audu yana da 'ya, sunanta Zainabu. Ya ce lalle ita ce aka nuna masa a mafarki, in kuwa haka ne in ya aure ta ya sami abin da ya ke bukata. Sai kuma ya tuna da sauran abin da ke cikin mafarkin, da shawarar da malamin ya yi masa. Amma don tsananin son ɗa ya maida duk wannan ba'a bakin kome ba idan dai bukatarsa ta biya. Ya ce watakila ma ba gaskiya ba ce, maganar matsubbata ce, sanin gaibu sai Allah. Da haka ya kwantar da ransa, ya gama shawara.

Daga nan sai ya aika aka yi kiran Malam Audu. Da ya zo suka shiga waje daya, ya ce masa, "Abin da ya sa na yi kiranka, na ga wani abu ne a wurinka wanda na ke so, ban sani ba ko watakila zan samu." Sa'annan ya buda masa.

Sai Malam Audu ya ce masa, "Wannan magana tana da wuya, domin kuwa ita Zainabu, tun suna kanana akwai wani yaro sunansa ABUBAKAR, tare suka taso, tana sonsa, shi ma kuma yana sonta, har kuwa kowa ya sani ita zai aura. Mutane da yawa da samari ba wanda bai zaburo yana sonta ba, amma ta ce sai shi. Shi kuwa Abubakar duk duniyan nan ba ya son kowa sai ita. Ka sani kuma yaro ne mai zafin zuciya kwarai, idan har bai auri Zainabu ba babu wanda ya san abin da zai yi. Ni ma da kaina ba na sha ba."

Malam Shaihu ya ce masa, "Idan ka ba ni izni in aika a kirawo ta domin in yi magana da ita, dukan abin da muka in sanar da kai."

Malam Audu ya ce, "Wannan fa ai ba maganata ba ce, sai wadda ka yi. Domin kuwa ina tsammani ko ka aika ba za ta zo ba, balle ku yi magana. Saura ni ba ni da ta cewa cikin wannan sha'ani."

Da ya koma gida ya shaida wa uwar yarinya ga maganar da suka yi da Malam Shaihu a kan Zainabu. Uwar ta ce, "Haba malam, wannan magana ma yaya za a yi ta? Idan muka yi haka ai a maida mu shashashai. Kada a ko fara yin ta ma

Da la'asar ta yi attajirin ya aika a kira Zainabu, Da aka shaida mata Malam Shaihu yana kira ta ce a koma a fada masa ba za ta zo ba. Aka koma aka fada masa. Sai ya sake aikowa a shaida mata jawabi daya kadai ya ke so ta zo su yi, shine jawabin aure.

Ta sake aikawa a fada masa ita ta rigaya ta yi miji, ba ta kowa da niyyar sake wani. Da aka zo aka fada masa ransa ya baci, ya yi fushi, ya ce, "Ashe akwai sauran mace a cikin wannan sarari wadda zan aika mata ina kira, sa'an nan ta kekashe kasa ta ce ba ta zo ba ?" Sai yaronsa da ya aika ya ce masa, "Haba, maigida, kai ka so. Ina kamarka mai kiran dubu daga wata kasa su amsa, sa'an nan ka bata kanka a wurin irin wadannan yara, ko da ya ke tana da kyau dai, ai bai kamata irinka a ci masa zarafi ba."

Ana cikin haka, sai kwaram wani cikin yaran Malam Shaihu ya tafi ya fada wa Abubakar, Malam Shaihu ya aika an kirawo uban yarinyar da ya ke tashi, ya kuma aika a kirawo ta, amma ta ki zuwa. Nan da nan sai ran Abubakar ya baci da jin wannan magana, ya rasa abin da ya ke ciki, ya yi ta doki yamma ta yi ya tafi wurin Zainabu.

Da yin yamma sai ya tafi gidansu, ya aiki kanenta ya fada mata, ta fito, suka tafi wurin da suka saba zama suna zance. Suka shiga cikin zancen duniya sai Abubakar ya ce mata, "Matar masu arziki!"

Ta ce, "Wace irin magana ce wannan da ka ke yi yau? Dama na gan ka yau duk harhar ka ke ji." Ya ce, "Abin da ya sa na fadi haka, domin na ji ance Malam
Shaihu mai arzikin garimmu ya aiko ki tafi." Ta ce masa, "Shi wanda ya ba, ka labarin bai faɗa maka jawabin da na aika a mayar masa ha?"

Mata, Halinku Na Da Wuya
"Ya fada mini, amma duk da haka raina ya tashi kwarai da gaske, domin kuwa na sani ku mata halinku na da wuya. Kin ji an ce da doki, da kogi, da mace, ba a ba su amana.
"Har ni ma watau ba ka yarda da ni ba mata ai duk halinsu daya ne." "To, sai ka ba ni dalilin da ka ce haka,"
Ya ce, "Abin da ya sa na ce miki haka, domin doki in kana sonsa, babu irin wahalar da ba ka yi masa, amma wata rana sai ya harbe ka. Kogi kuma sai kaje yanzu hanya ba ruwa, amma sa'ad da ka nufl komowa sai ka iske ruwa ya kawo, ba dama. Mace kuma an ce alkawarinta na kwana arba'in ne, idan ya wuce haka in ta sami wanda take so, komai son da ta ke yi maka ta bar ka. Malam Shahu attajiri ne, in baki so shi don kome ba za ki so shi don dukiyar tasa Sai ta yi murmushi ta ce, "Haba, Abubakar, ai da zai Yiwu kudinsa a ke takawa daga nan har mafitar rana, babu abin da zai sa in aure shi" Ya ce, "Kayya! Idan ka ga kare yana Sunsunar takalmi dauka zai yi. Amma duk abin da kika yi shi kenan." Suka yi sallama ya tafi gida, ya kwana yana ɓacin rai.

Da attajirin ya sami labarin abin da suka yi da Abubakar sai ya ce. "Bari in nuna wa yaron nan kowa ya ja da ni ya fadi." Sai ya aika aka kirawo masa wani mutum sunansa Malam SAMBO, wanda dukan mutanen garin suna tsoronsa, har da sarki. Da ya zo ya watsa masa kudi masu yawa, ya fada masa abin da ke tsakaninsa da Abubakar.

Malam Sambo ya ce, "Wannan magana mai sauki ce, wani ma ya yi rawa balle dam makada! Idan ma ka bukaci yaron nan ya mutu ne, ai Allah ya ba mu ikon da za mu yi wannan taimako."

Malam Shaihu ya ce. "Mutuwa dai ba ni so, abin da za ka yi ka juye zuciyar yarinyan nan da ta iyayenta daga gare shi."

Malaminsa ya ce masa, "To, shi ke nan, idan na koma gida yanzu ka aiko yaronka, zan ba ka wani taimako. Idan yamma ta yi ka yi abin da na aiko maka da shi, ka aika, idan ba ta zo ba ka aske mini gemu. Kuma zan aiko maka da wani magani ka san yadda ka yi ka kwaba shi cikin kudi kabata, idan dai ta karba har ta kai hancinta ta shafa, lalle magana ta kare, ko iyayenta suna so, ko ba su so, dole ne ka aure ta" Malam Shaihu ya yi farin ciki, ya kawo kudi masu yawa ya ba shi.

Da maraice ya yi ya aika aka karbo masą maganin, daya ya kwaba game da juda, dayan kuwa ya yi turare da shi. Sa'an nan ya aika a kirawo Zainabu. Da yaron ya tafi ya iske su suna zance da Abubakar Ya yi sallama, Abubakar ya amsa ya ce, "Me ka ke nema?"

Yaro ya ce, "Malam Shaihu ne ya aiko ni wurin Zainabu yana son ganinta." Sai Abubakar ya ce, "Koma, ka gaya masa ba ta zuwa."

Har yaron ya yi nisa, sai ta zabura ta tsunka a guje ta kirawo shi a gaban Abubakar. Ta ce ya fadawa maigidansa tana zuwa, amma waccan magana da ya aiko da fari lalle ba ta tsakaninsu. Daga nan Abubakar ya ce mata, "To, ai ga shi nan ko da jiya ban fada miki ba. "

Ta ce masa, "Haba, Abubakar, ai wannan ba kome ba ne. Gani ba ci ba ne, tafiyarta kuwa ba ita ce aurensa ba. Na rantse maka da gaskiyar zamani ba ni auren kowa nan duniya idan ba kai ba. Watau fadin ina zuwa ai domin ransa ya yi masa dadi ne kawai, kada ya ce na wulakanta shi sau biyu, domin kuwa ka san halin ku maza, idan aka yi muku gantsi a kan sha wuya wata rana."

Ya ce, "Shikenan, duk abin da kika yi daidai ne." Suka yi
sallama, ta yi masa rakiya,

Da komowarta gida sai ta yi wanka, ta yi shiri. Ta ce wa uwarta za ta tafi wurin Abubakar, yanzu tana komowa. Da fitarta ba ta zame ko ina ba, sai gidan Malam Shaihu, ta iske zaure tinjin ana ta hira. Sai ta wuce ciki ta jira shi a soro na uku. Jim kadan sai Malam Shaihu ya shuri takalminsa ya shiga gida, duk wuri ya gume da kanshin turare. Da jinsa yana zuwa, sai ta rufe kai.

Da shigowarsa sai ya ce, "Zainabu, kin zo? Don me na aika sau biyu a yi kiranki kika ki zuwa zan ci namanki ne?"

Ta ce masa, "Ai dama ce ban samu ba." Suka yi gaisuwa. Sa'an nan ya ce mata, "Abin da ya sa na
yi kiranki, na ji labarinki ne. Na kuwa ji akwai wani wanda ki ke sonsa, amma na sani ba a yi masa baiko da ke ba, ko an yi masa kuwa ni ina so, sai na ga abin da ya kore ni."

"Me zai kore ka, kai ba mutum ba ne? Mutum na kin
mutum ne ?"

"To, ina son ki da aure."

"Ni ma ina sonka, saura ba da aure ba," "Don me ba da aure ba ?"

Har Yanzu Ina Kaunarsa "Domin kuwa tun ina yarinya babu wanda na ke so tamkar Abubakar, har yanzu kuwa ina kaunarsa. Duk garin nan dai dai ne wanda bai neme ni ba, amma duk sun ga ba dama sun watsar. Kuma bari in gaya maka gaskiya, ka ga dai na sani kai
mai arziki ne, Abubakar kuwa talaka ne dan uwana, in na aure ka babu yunwa balle kishin ruwa. Saura da abu daya, na ji kai mutum ne mai zara, da yau za ka ga wadda ta fi ni kyau sai ka ce ita ka ke so. Kuma ka cika aure aure da yawa, duk wadda ka aura kuwa idan kuka yi 'yan shekaru ka ga ba ta haifu ba sai ka sake ta da cin zarafi, ga shi kuma, kana da matanka hudu, dukansu babu wadda ba ta girme ni ba. Ni ba zan iya kishi da su ba, ka sani kuwa ba a yin mata biyar balle ka ce za ka aure ni. Ya ce mata, "Wannan ba magana ba ce, tun da ya ke na ce ina souki da aure, idan kina sona ki amsa mini, ni nasan yadda zan yi. Ba a saki ?"

Ta ce, "Oho, tun da ya ke sakin wata za ka yi ka aure ni," ni kuma wata rana haka za ka sake ni, idan ka ga wata wadda ta fi ni kyau ka auro ta."

Kina Sona?

"Ba haka ba ne, Zainabu. Abu daya na ke so a gare ki, idan dai kin amsa kina sona, shi ke nan." "Babu dama!"

"Na ba ki damar kwana bakwai, dukan abin da kika shawarta ki komo ki shaida mini, domin in san abin da na ke ciki."

"Wace shawara zan yi? Ai shawarata ke nan."

"A'a, ke dai ki yi shawara."

Suka yi sallama. Za ta fita ya ce ta dakata masa. Ya shiga gida ya debo kudi da goro ya kawo mata

Ta ce, "A'a, wallahi ba ni karbar kome naka. Idan na karba aka gani a gida za a doke ni, kuma duk wanda ya ji tun yanzu na fara karbar abu daga hannunka, sai ya tabbatar mana da halimmu na mata." Ya ce, "Kwashe. Kin sani ko ba don wannan magana ba ni mai ba ki abin da ya fi wannan ne."

Na San Haka

Ta ce, "Na san da haka, amma yau muke dakai da baka ba ni ba?"

Yayi yayi ta karba, ta ki. Ta yi wuf za ta tashi sai ya kame zanenta, yace, "To, idan ba za ki karbi wadannan ba ga wani dan abu kankane ki yi maganin rana, domin kuwa bai kyauta tsakanina da ke ki zo gaishe ni ki fita hannu wofi ba, watau ba ki darajanta ni kenan ba." Ya sa hannu a aljihu ya dauko turaren nan da ya cude da magani ya ba ta. Ta karfa da kyar, ta tafi.

Da ta shiga gida ta dauki turaren ta ba uwarta, ta ce, "Ga shi Abubakar ne ya ba ni. Karbi ki ajiye mini." Dazata bata ta lakuta kadan ta yi bille da shi.

Da gari ya waye Malam Shaihu ya aika aka kirawo masa Malam Sambo, ya fada masa dukan abin da suka yi da Zainabu. Sai Malam Sambo ya ce, "Tun da ya ke ka ba ta turaren shikenan, kada ka sake neman ganinta, su da kansu sa aiko a neme ka"

Malam Shaihu ya yi masa godiya, ya sake kawo kudi ya bashi

Da yamma Abubakar ya tafi gidan su Zainabu da kansa, ya sa aka kira ta. Ya tambaye ta, "Gaskiya ne kuwa jiya bayan rabuwarmu kin tafi gidan Malam Shehu ?"

Ta ce, La

Ya ce, "Yanzu na sani tsakanina da ke rufarufa ne. Ina so ki fada mini a sarari idan ba ki sona.

Ta ce, "Ai ka sani budurwa haja ce, kowa ya gani yana so, kowa kuwa da irin tayinsa, amma mai saye daya ne. Ko da ba a yi mini baiko da kai ba, kaidai kana tashina." Sai ya tashi da fushi ya tafi abinsa.

Da ya koma gida ya fada wa uwa tasa abin da ya ke tsakanin- sa da Zainabu. Uwar ta ce, "Ai ni ko da na sani ba za ka auri Zainabu ba, domin kuwa tana da masoya masu arziki, ka sani kuwa kome na duniyan nan ba duka a ke yi domin Allah ba, sai don dukiya. Hakura, ka nemi daidai da kai."

Ya ce mata, "Haba, iya idan dai ni dan mutum biyu ne, sai na rama. Zan shiga duniya, da ko wane hali na sani Allah zai taimake ni. Amma kada ki damu. Ga Audu nan da kanwata da kakarmu, sun ishe ki zaman duniya, ni kuwa idan da rai watarana za ki ga na komo. Da ta ji haka ranta ya baci Kwarai da gaske, ta rasa abin da za ta ce masa, domin ta sani idan hankalin Abubakar ya tashi ba mai ikon tausa shi.JIKI MAGAYI-02

Daga nan uwar ta ce, "Ai ka sani abin duniya ba a yinsa da karfi, sai da rarrashi da ban magana. Abin da na ke so da kai ka yi hakuri a rarrashe ta, watakila ta koma cikin hankalinta Amma yanzu idan ka ce za ka yi mata na karfi, ka san halin yaran zamani watakila wannan ya zama shi ne dalilin da zamu rasa ta dungurungum babu rai babu girma." Sa'an nan ya kwance ta
Yammar fari sai gidan Malam Shaihu. Ta ce masa, "Tunda ya ke Abubakar ya yi zafin zuciyar tasa ina so ka fito zancen neman aure."

Da gari ya waye, Malam Shaihu ya aika wurin Malam Audu a fada masa yana nan yana aikowa a kan maganar da suka yi Malam Audu ya aiko a fada masa ba shi ba dai, sai ko abayan ransa a daura musu, Aka yi jayayya kwanaki da yawa. Sa'an nan yan'uwa suka taru suka yi wa Malam Audu. Ya amsa tilas, ba da sonsa ba ko kadan. Malam Shaihu ya fito zancen neman aure, aka yi masa baiwa ya biya wadansu ramuwa wadanda yarinya ta ci. A ran nan aka sa ranar biki. Dukan mutanen gari suna ta yi da Malam Shaihu don rashin dattakun da ya yi.

Randa za a daura aure ya saki matar tasa daya. Da yamma aka kawo amarya. Kashegari aka yi kasaitaccen biki wanda ko sarkin Galma ba zai yi irinsa ba. Abokansa daga ko ina suka zo . Babu irin abin da ba a yi ba, kowa sai cewa ya ke yi, "Tubarkalla, lalle mai arziki yana biki!" Sai facaka da kudi a ke yi, aka kwana uku ana wasa. Sa'an nan aka yi budar kai aka kawo gara. Mutane kuwa suka watse.

SAURAYI YA SHIGA DUNIYA

ABUBAKAR ya fita gida, bai san inda za shi ba, yana ta yawo har ya zo wani gari wanda a ke ce masa ZAUNA-DA-SHIRINKA . Garin kuwa na wadanda suka yi ko sata, ko wani abin kunya ne, suka gudo daga garinsu suka zo suka kafa tasu tunga, basa yin kome sai masha'a. Duk garin daga 'yan bori sai kasaitattun Barayi, sai matsibbata, da karuwai mata, Abubakar ya iso garin sai ya rika jin yizga tana tashi, da wake- wake. Sai ya zauna a gindin wata itaciya, yana hutun gajiya, har barci yakwashe shi.
Sai wani mutum ya zo ya gan shi yana kwance, ya tashe shi ya ce masa, "Samari, daga ina ka fito?" Sai ya farka daga barci, suka yi gaisuwa, ya tambaye shi ko
garin nan da wani shahararren malami. Mutumin ya ce masa, "Ba ka ji sunan garin nan ba?"

Ya ce, "Na ji." Ya ce, "To, ka ga wane malamin kirki zai zauna cikin wannan gari? Mu nan bama sha'anin komai da malamai sai tsafi da bori
Sai yace toh dakyau nuna mini gidan BABBAN MATSAFINKU.

Sai ya tafi da shi gidan wani waishi
TAUSAYIN KA-DA-SAUKI Da aka kai shi gidan bashi nan, ya tafi garin wata al'ada kwanansa uku, amma ana tsammanin da yamma zai komo. Ya zauna yana jiransa, bai komo ba sai da tsakad dare. Da ya shiga gida ya kintsa, sai wani daga cikin yaransa ya shiga, ya fada masa ya yi bako, tun da hantsi. Daga can sai ya fito, ya sa aka yi kiran Abubakar, suka kadaice. Da dai Abubakar ya gan shi sai jikinsa ya dauki rawa saboda kwarjinin dake gare shi. Suka gaisa, ya tambaye shi abin da ya kawo shi. Abubakar ya ce, "Maganata da yawa, sai Allah ya kai mu gobe na warware maka zarena da abawata."

Da gari ya waye, Abubakar ya tafi ya gaida Tausayinka-da-sauki. Bayan da suka gama gaisuwa ya ce masa, "Abin da ya kawo ni gare ka, bacin rai ne. Ni ke da wata yarinya wadda na ke so, ita kuma tana sona gaba da komai, tun muna yara har muka yi girma, ina nan ina tashinta za mu yi aure. Ina cikin shawara ke nan zan sa uwata ta tafi a yi mini baiko, sai wani attajiri a garimniu ana
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment