Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

HIRA DA MATATTU























Jamila Umar Tanko:

JUT

Haqqin mallaka:Jamila Umar tanko
Copyright: Jamila umar tanko


Wannan littafi mai suna HIRa DA MATATTU na 2 na kudi ne.

300 ne kacal Zaa biya
0112240731
Gt bank
Jamila umar tanko

Idan an biya a turo shaidar biya ta wannan lambar:
08061225337

Na gode


HIRA DA MATATTU .....1 (True life story)

Haqqin Mallaka: Jamila Umar Tanko
Copyright: Jamila Umar Tanko


Saudaukarwa:
Na sadaukar da wannan littafin ga matan da suka yi jahadi wajen biyayyar aure ko su na raye ko sun rasu. Allah Ya duba yaransu ya raya su akan sunna.


Gargadi:
Baa yarda wani/wata ta juya labarin ban zuwa wata Shiga ba fim ko rubutu ba tare da izinin Marubuciyar ba. Sannan ban yarda a karanta shi a you tube channel, ba tare da izinina ba.








[2/28, 5:26 PM] Jamila Umar Tanko: 1

Sharifah ta ci gaba da cewa "duk wanda ya san ni a duniya toh ya san ni tare da Shariqah dan kamar 'yan tagwaye mu ke. Mun shaqu sosai kamar yadda uwa take shakuwa da 'ya'yanta.
Bayan son Allah (S.W.A) da ManzonSa (S.A.W) daman wannan baa hada su da kowa, sannan iyaye su daban ne. Duk duniya babu abinda na fi so irin yadda na ke son Shariqah, haka itama.
Ita karamar kanwata ce ba ita take bi na ba ma, Bello ke bi na ita kuma take bin sa.
Na riga ta yin aure da dadewa, amma a kullum tana gidana, idan ma bata zo ba ni zan je gida saboda ita, kasancewar mijina ba zaunin gari ba ne, yayi min lamuni idan baya nan zan iya tafiya gida in kwana. Kusan kullum tare muke kwana shinfidarmu daya, mu na raba dare mu na hira.
Baiwar Allah ta fi ni hakuri da hangen nesa, ko da zan zazzage ta sai ta fada min gaskiya.Babu mai goyon bayana a duniya irin ta, komai girman matsalata tana tare da ni kuma ita kadai nake fadawa komai nawa.
Ko kwalliya na yi idan Shariqah ba ta ce na yi kyau ba toh ba na yarda akan na yi kyau din.
Na haifi 'yata Hamidah, na rantse da Allah bayan wahalar daukar ciki watanni tara da nakuda da shayarwa zuwa kwana arba'in ban san wahalar raino ba. Shariqah ce komai na game da kula da jaririya, duk wata kazantar jariri da zaryar zuwa asibiti ita ce.
A lokacin ina tafiya jami'a wani lokaci ma ina gida a kwance ita ke faman rainon Hamidah. Har fada ake yi da ni ina cewa idan ba za ta yi ba a bar 'yar a wajen.Mutane su cika da mamaki. Ta yaya uwar da ta haifi 'yarta zata ce haka? Saboda na san ai ba za ta iya barin 'yar ba ne shiyasa nake cika baki.
Watanni takwas kadai Halidah ta yi ta na shan nono, na yaye ta, na damqawa Shariqah suka kaura gidansu gaba daya.
Hamidah ta tashi a tunaninta Shariqah ce mahaifiyarta, ta sanni amma ta dauka ziyara kawai nake kawo musu a matsayina na 'yar uwarsu.
Hamidah ta sha laulayi na jinya kala-kala haka Shariqah ta ke wuni a layin asibiti tana jinyar ta.
Samari da dama 'yan gayu sun sha ganinta a hanya su na so, daga sun matso suka ganta da 'ya har tana kiranta mummy sai su yi kwana a zatonsu matar aure ce.
Qawayenta har tsiya suke yi mata cewa sai an yi kwalliya zaa fita unguwa kawai sai ta dauko musu 'ya tana bata musu tsari. ita kuwa sai ta ce idan zaa so ta dole a so ta da 'yarta.
Ko tafiye-tafiye su ka yi qasashen waje da yake makarantar kudi ta yi kuma dukka qawayenta 'ya'yan masu hali ne ta kan fada musu ita bata son su siyo mata komai su siyowa 'yarta Hamidah. Ko ba ta fada ba ma sun san abinda zasu yi ya faranta mata rai shine su yiwa Hamdah sayayya.
Daman gashi kamarmu daya ni da Shariqah dan haka Hamidah ta yi kama da ni sai ta yi kama da Shariqah.
Aure ne kadai ya raba Shariqah da Hamidah. Na tabbatar da ta auri miji mai fahimta da daman da ita za ta tafi amma bata yi wannan sa'ar ba. Aka bar Hamidah a wajen mahaifiyarmu.
Mahaifin Hamidah ba mutumin da ya san darajar gidansa ba ne, haka ba mai kula da haqqin iyalansa ba ne, shiyasa ma ya bar 'yarsa ake riqonta dan bai sauke nauyin da Allah Ya dora masa ba.
Hakan ya fiye min alkhairi saboda idan na dauko ta na kawo ta gidana ma akan Hamidah kullum sai mun yi fada.
Mutum ne da baya son zaman lafiya ko kadan, Idan ya na so ya bani haushi ko ya takale ni da fada toh sai ya hau azabtar da ita dan haka ne ma ta taso da tsoronsa kuma bata son ganinsa ma ko kadan.
Bai sauke haqqina da Allah Ya dora masa na ciyarwa, sutura, asibiti, muhalli ba, dan haka bai hana ni fita neman kudina kowacce kasa ba. Dan mutuwar zuciya ma nawa yake so ya ci saboda zuciyarsa ta mutu.
Mahaifiyata na tsaye tsayin daka akan matsalolina da na 'yata dan haka da jarina da na ta nake juyawa.
Hakkinmu da ya tauye shine ya jawo masa koma baya, baya ganin daidai a dukka aiyukan da yake yi. Kullum ana korarsa daga aiki ya na wahalar neman wani aikin. Wannan kuma na bar shi da Allah, na ci gaba da kula da kaina da 'yata da taimakon Allah da taimakon mahaifiyata.
Mu ka bar Hamidah a Karkashin kulawar mahaifiyata amma kuma a koda yaushe tana zuwa gidan Shariqah kasacewar gari daya ne kuma tazarar unguwannin babu nisa.
Allah Ya bawa Shariqah haihuwa a jejjjere ba tsayawa. Allah Ya jarrabe ta da auren miji mai tsanani da kishiya da 'ya'yan kishiya mararsa kirki. Babban abinda ya kara kawo tangarda su na zaune su dukka a cakude a gida daya, bata jin dadin zama da su ko kadan.
Shariqah mace ce mai hakuri, komai sai ta rufe bata fadar damuwawarta. Hamidah ce kadai ta san komai ita ce abokiyar shawararta amma sai ta ce ma ta kada ta fada min. Saboda sun san ina da zafi wasu lokutan bana son rainin hankali.
Mahaifiyarmu mace ce mai son yara kuma a tsaye take akan matsalolin yaranta.Ko bayan rasuwar mahaifinmu ba mu ce wayyo Allah ba, saboda ba mu rasa komai ba. Mace ce mai kamar maza ta yi nata ta yi na wasu ma.
Wahalar da Shariqah take sha a gidan miji bai nuna ba saboda ga ta a kusa da mahaifiyarta mai sonta mai taimakonta da dukiyarta da nuna ma ta so da kauna da bata shawarwari akan ta yi hakuri rayuwar aure ibada ce.
Sai bayan da mu ka rasa Mamarmu sannan maraici dukka ya bayyana a jikin Shariqah.
Bayan masifaffen kulle wanda ko islamiyya baa zuwa a gidansa, daman biki ko suna da gaisuwar mutuwa, dangi dukka sun sallama ta baya bari ta je a cikin Kano ma balle a wani gari.
Dukka kayan dakinta masu kyau masu tsada na kasar waje, sai da suka kwankwatse, baya gyara balle ya canja musu kuma ke matar gidan da kudinki ba ki isa ki kawo masu gyara su shigo masa gida su gyara miki ba. Har da mugunta 'yayan waccan matar suke zuwa su lalata mata komai dan ita bata magana.
Ta rame, ta yi baqi-qirin ta fita daga hayyacinta. Wataran kudin Pampers guda daya jal sai ta gagare ta balle na cerelec da zata bawa yaranta bata da shi, kuma shi babu wadannan a cikin lissafinsa.
Yaranta sun tashi babu kuzari da yawa ma tana goyonsu sai da suka kamu da ciwon tamowa wato na rashin balance diet. Yara kanana sai dai su ci mai da yaji.
Suturun da ta saba sakawa babu irinsu sai dai masu arha taron yuyuyu, man shafawa da sabulun da ta saba yin amfani da su a gidansu dukka babu. Kuma ya na da halin da zai yi fiye da hakan amma baya yi."

*** *** ***
Sharifah ta yi shiru ta yi tagumi dan tsananin takaici ta kasa kuka amma radadin da zuciyarta ke yi ya nuna a cikin idanuwanta. Sun yi jajawur, ranta a bace.
Samha ta dafa hannunta tana jinjinawa alamar tana ba ta hakuri.
Sharifah ta yi ajiyar zuciya ta ce "maganganun su na da yawa akan mutumin nan Adamu, ga shi sun haifi yara da yawa tare. Alfarmar yaran nan ta sa ba zan iya fadar rabin azabar da ya bawa Sharifah ba. Ko rabin-rabin abubuwan da suka faru ba zan iya fada ba. Wasu ma har yanzu ban sansu ba, an boye min baa so a fada min. Wasu kuwa ta kunshe a ranta ta tafi da kayanta ba zata iya fadawa kowa ba."
Samha ta gyada kai ta ce "na fahimce ki kawata ki ci gaba da labarinki ki fada mana wanda zai iya faduwa. Na jinjinawa mata masu jahadin zaman aure irin su Shariqah. Aljanna na nan na jiran mata irinsu da su ka rayu cikin ukuba su ka yi biyayyar aure. Kamar Rabi'atul Badawiyya(RA) matan aljanna."
Aliyu sai kabbara yake ya na jan gemu an tabo babin ustazai, ji yake dama ya hadu da wannan mijin na Shariqah ya yi masa nasiha.
Anas kuwa babu abinda yake yi sai gyada kai yana tunano irin bautar da yake yiwa matarsa Binta, da irin 'yancin da ya bata na sakewa ta yi abinda take so, ta je inda take so amma bata gode masa daga ita har iyayenta.Ta na ta bin zugar qawaye da dangi. Ya ji dama Shariqar ya aura ta yi masa wannan biyayyar shi kuwa ya jiye mata dadi. Dan ya so Shariqah a rayuwarsa, ya so ya aure ta Allah bai kaddara ba. Kwatsam kawai ya ga katin daurin aurenta ba dan tana son mijin ba sai dan kadararrar aure da ta haihuwa. Wanda babu mahalukin da ya isa ya hana kaddarar bawa ta faru da shi. Wannan haka yake komai mukaddari ne kuma rubutacce ne.


*** *** ***
Sharifah ta ci gaba da cewa "Ko Shariqah tayi yunkurin fita daga gidan idan abin yayi ma ta yawa, mijin yana tsoratar da ita da cewa idan ta fita ma ina za ta je? Tunda bata da sauran gata iyayenta gaba daya sun rasu, danginta babu hadin kai, babu mai kula da ita. Kuma idan zata fita bata isa ta tafi da yaransa ba har da na goye, duk kotun da zasu je sai ya kwace su.
Wannan rashin fahimtar ita take saka mata da yawa ci gaba da zama a ukuba a gidan mijin da yake gallaza musu har su rasa rayuwarsu.
Ta kai ta kawo gidanta da suturarta da ta yaranta babu tsari gaba daya ba irin rayuwar da ta taso ba ce, ta fada wata rayuwar da ba ajinta ba ne, ba ta saba gani ba.
Shariqah kyakykywar mace ta koma abar tausayi, baqiqirin ta rame babu maganar gayu ma.
Aure bautar Allah babu wanda ya damu da ita a dangi, wasu lokutan ne ma idan na ganta na kan hau fada ina cewa akwai abinda take boyewa zan sami mijin in yi masa magana. Sai ta hana dan ya dora su akan kishiyarki na jin haushi dan na yi miki abu kaza dan haka ko marinsu yayi kokari suke su fito su na yaqe su na dariya kada kishiya ta gane an yi fada.
Ya same su ya dinga cin karansa babu babbaka babu wanda yake yi masa magana. Bayan rashin wadatasu da kudi ga tsananin kulle, su ba zasu fita ba kuma baya so a zo.
Takai ta kawo yana korar baqinsu, Idan bakuwa zata kwana sai dai a boye takalmana ta. Kishiyar na lallabawa ta fada masa akwai bakuwa a gidan Shariqah. Sai da tsakar dare misalin karfe goma sha biyu sai yayi sumame ya shiga ya ritsa su...."


*** *** ***
Sharifah ta yi shiru ta kasa ci gaba da magana saboda tsantsar radadin da take ji a cikin zuciyarta tamkar fami labarin yake yi ma ta, akan katon gyambon da yake fafare a cikin zuciyarta."
Samha ta dafa kafadarta ta girgiza ta, ta ce "ki zubo da hawayen zai sa ki ji sanyi. Saboda Idanuwanki sun yi jajawur, zuciyarki ta na bugawa da sauri."
Sharifah ta girgiza kai ta ce "haba Samha tun yaushe na wuce babin yin kuka akan bil'adama. Na yi rantsuwa da Ubangijin da Ya busa min numfashi ba zan sake yin kuka ba, sai dai in kai su kara wajen Allah wanda Shine gatana kuma gatan Shariqah, in roqe Shi ya nuna min hanyar da zan bulle wajen daukar mataki da fansa.
Na shiga bala'an da ya fi karfin kuka, mutane sun ba ni mamaki kuma sun ci amanata wanda a baya ban taba sanin haka mutum yake ba sai yanzu."
Samha ta fara tausayawa Sharifah tun bata gama jin labarinta ba. Ta tabbata Sharifah ta shiga bala'in da a dole ma kamanninta suka canja, ta rame ta yi baqiqirin tayi kuraje.
Sharifah ta ci gaba da cewa "mijin Shariqah ya binciko bakuwar Shariqah, ya hada su su dukka ya ci musu mutunci. Shariqah na kuka bakuwar tana kuka ya ce ya yi rantsuwa ba zata kwana a gidansa ba. A cikin daren ya kore ta daga gidan, kuma 'yar uwarmu ce daga wani gari me nisa ta zo Kano yin sari. Ba ta san yadda zata bi ta je unguwar wasu 'yan uwan na mu ba. Yarinya budurwa ya kora a cikin dare dan qarfe goma sha biyu ta gota.
Akwai karamar kanwar mu wacce muke uba daya mai suna Dinar, watarana ta zo hutu daga makaranta kwana itama aka ce sai dai a boye ta, har ta gama yin kwanakin da zata yi ba zai san tana ciki ba dan idan ya sani zai iya korar ta itama.
Ba ta san shi ba sai dai ta dinga leqensa ta windo, tunda bata nan aka yi aurensu kuma bata zuwa gidan.
Yaran Shariqah basu san danginta ba saboda baa kai su ziyara, toh uwar ma bata je ba balle yaranta. Dan haka basu san kowa ba sai wadanda suke iya daurewa da wulakancinsa su je gidanta.
Asibiti ne kadai ya yarda ta je shima sai ya hada da tsine-tsine idan ta kuskure ta biya wani gidan. Wato ya san ta tara barka da gaishe-gaishen mutuwa bila adadin dan bakar mugunta shine baya so ta je ta sauke nauyi.
Tunda ya fatattaki kawayenta da 'yan uwa ai zai fi samun damar da zai ci karansa babu babba akanta wannan ce manufarsa.
Ta koma baiwarsa ba matarsa ba, ko generator zaa kunna sai idan yana gidan idan zai fita sai ya kashe, sai ya dawo zai kunna. Idan yayi tafiya kuwa idan zai yi wata guda ke matar gida ba ki isa ki kunna ba, ko da kina da kudin siyan man fetur.
Daman ita uwar gidan 'yar wahala ce bata fito daga gidan dadi ba, ita Shariqah ce duk bata saba da wannan qangin ba. Akwai ranar da ta zuba mai a inji ta kunna. Ta kashe lafiya kalau amma dan annamimanci sai uwar gidan ta aiko danta ya yanke igiyar saboda idan ya dawo ya gan shi a lalace sai ace Shariqah ce ta kunna. Haka kuwa aka yi, ya zo ya tambaya aka gada masa Shariqah ce ta kunna, ya ci ma ta mutunci tas.
Sunan kishiyar Talatuwa ita da 'yayanta suka dinga hada mata tughu kala-kala, a gaban Hamidah ake yin wasu abubuwan sai Shariqah ta ce kada Hamidah ta fada min .
Abin ya kai har qawayenta da suka yi makaranta tare suka ga halin da take ciki ya kazanta. Hatta kujerunta na falo sun lalace idan baqo ya zauna akai sai ya zurmuka ciki sai an zakulo shi. Su ka hada meeting cewa anya kuwa na san halin da Shariqah take ciki kuwa? Amma aka yi shiru aka zuba masa ido? Su ka yi niyyar su zo su same ni. Daga baya me suka gani dai suka fasa zuwa dan su na ganin zaa ce sun shiga abinda da ba ruwansu tunda tana da dangi babu wanda ya taba yi masa magana, su yaya zaa yi su tsoma bakinsu?
Wataran ledar pure water da za ta siya su sha ta gagare ta, bata da shi komai bai wadace taba.
Idan ma asiri ya yi ya rufe mana baki toh asirinsa ya ci dan babu wanda ya iya yi masa magana.
Ta yi hakurin jiran kudin hayar gidanta na gado dan ta gyara kujerunta amma da kudin suka zo sai ya karbe. Ya ce shi zai samo mai gyaran. Ta san halinsa ba zai taba bari maza su shigo su kwashi kujerun ba, har gara ta lallabashi shi din ya gyara sai ta bashi kudin.
Mutumin nan ya karbe dukka kuma ya qi kawo masu gyaran. Mafarin da ta kamu da ciwon zuciya kenan."
[2/28, 5:50 PM] Jamila Umar Tanko: 2
Ban san ma ta je asibiti an ce tana da ciwon zuciya ba, sai daga baya take fada min a waya. Dan a lokacin ba na zama a Kano, ina zama a Rivers ni da mijina.
A lokacin Hamidah ta dawo wajena tunda babu inda za ta zauna kasancewar Mamarmu ta rasu.
Na ji hankalina ya tashi matuqa na shiga damuwa ba 'yar kadan ba gami da tunanin me ya jawo ma ta kamuwa da ciwon zuciya da kananan shekarunta? Amma ban yi mamaki ba domin kowa ya dube ta ya san bata jin dadin gidan mijin..Sai a lokacin ne Hamidah ta ke fada min wasu daga cikin matsalolin da Shariqah take ciki. Da irin cin kashin da mijin da kishiya da 'yayan miji ke yi ma ta. Su yi ma ta rashin kunya kuma su daki 'ya'yanta."
Sharifah ta juya ta dubi Hamidah wacce ke sharbar kuka ta ce " ki tashi ki shiga daki tunda ke zuciyarki ba ta iya jurewa idan ana labarin Shariqah."
Hamidah ta ja kannenta suka shiga daki, masu wayon dai jikinsu ya yi sanyi sun ji an ambaci mahaifiyarsu, yayin da kananan suke wasansu basu kawo a ka ba ma. Allah sarki, Allah ba Ya barin wani dan wani ya ji dadi.

*** *** ***
Maman Samha ce take ta kiransu a waya hankalinta a tashe yake, ta kira lambobi kowannensu bai amsa ba. Ta shiga gagarumar damuwa dsn ta na zaton fatalwar ce ta tafi da su.
Sai yanzu wayar Samha ta shiga girgiza, ta dauko da sauri ta duba taga 7 missed calls din Mama.
Ta dubi Anas da Aliyu a gigice ta ce "Mama ce fa take ta kira ashe. Waye ya ce ma ta mun fita ne?"
Anas ya tabbatar ma ta da cewa shine ya fadawa Samira, ko da ta Allah kan kasance aksnsu asan inda suka tafi . Kowannesu ya zaro wayarsa daga aljihu ya duba
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2

Please Login or Register in order to submit comment