Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[03/08, 11:42] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️

*TASWIRAR KADDARA*

♠️♠️♠️♠️♠️


Written by
Mrs A.M🥰

Page 1

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM



Ina zaune a matsakai cin tsakar gidan mu ina duba littafina kasancewar Jamb din da zan rubuta wannan shekarar gashi lokaci yana ta kurewa saura sati biyu mu zama jamb din.

Hankali na ya kasu kashi biyu, daya yana kan English din dana ke rubutawa daya kuma yana ga tunanin inda *MIMI* ta shiga, tun da akai la'asar ta fita ban kara ganin taba, kwafa nai ina tunanin yadda zan hukunta ta tunda tasan cewa bana son tana fita da yamma haka ita kadai.

Wata yarinya mai kimanin shekaru 4 fara kar kamar balarabiya sbd tsabar kyaun da Allah yai mata ta shigo gidan tana sanye da riga yar kanti har kasa duk da rigar tadan kode amma kal take a wanke sai alamun kasa kasa daka kasan rigar da alama yarinyar tayi wasa a kasa ne.

Tunda ta shigo na kafe ta da ido ina tasbihi a raina, kullum na kalli Mimi sai nayi tasbihi ga Ubangiji sbd tsabar kyaun ta, fara ce tass mai dauke da zagayayyiyar fuska tana da manyan idanu sosai tubarkalla sai dogon hanci wanda ya dace da zagayayyiyar fuskar ta sai kuma karamin bakinta jajir dashi, maida kallona kan gashin ta nai dake tufke amma jelar har kusan duwawun ta take sbd tsayin gashin ta.

Lumshe idona nai jin wani hawaye yana kokarin zubo min, muryar ta mai cike da shagwaba naji a kusa dani tana fadin *"MAA* kiyi hakuri baxan sake ba Hidiya ce tace inzo muyi wasa a garden din gidan su."

Kallon ta nake kawai ina bin kumatun ta da kallo yadda dimple dinta na gefen kumatun ta na dama yake lotsawa sosai, hakan ba karamin kyau yake karama ta ba.

Hade rai nai cikin dan fada fada da saurin maganar da nake da shi nace "ban hana ki fita ba amma wato kin fara raina ni koh Mimi shine har zaki fita BA tare da na sani ba"

Rau rau tai da idonta daya fara tara hawaye ta kama kunnuwan ta da hannayen ta tace "Maa kiyi hakuri bazan sake bafa kar kiyi fushi dani"

Daga bayan mu Umma da ta fito daga daki tayi dariya tace "zo kinji kawata kema kinsan Maa dinki baxa ta iya fushi dake ba"

Makale kafada tai tace "toh Umma ai bata ce ta hakura ba"

Janyo ta jikina nai cikin tsananin kaunar ta nace "na hakura babyta amma kar ki sake fita ba tare da kin fada min ba kinji koh"

Daga kai tai tana kuma kwantar da kanta a jikina sai shagwaba take zuba min ina biye mata, girgiza kai Umma tai kawai tana dauke kwallar dake neman sakko mata a fuska.

Muna zaune a tsakar gidan Umma da Mimi na kan tabarma ni kuma ina daga kitchen Aysha ta shigo cikin uniform din islamiyya.

Fitowa nai hannuna rike da ludayi nace "kinyi saurin dawowa yau Aysha ina su Kamal din"

Zama tai akan tabarma tana ajiye jakar hannun ta cikin gajiya tace "suna hanya Ya *BATUL* ai baxan iya jiran suba wallahi duk ba gaji fah kinji kafa ta"

Dariya nai nace shiyasa nace "sannun ku ai kun kusa sauka ki dinga hutawa kema"

Kallon Mimi tai tace "shine kika ki zuwa islamiyya yau koh ai Malamar ku tace sai ta zane ki gobe"

Murguda karamin bakin ta tai tace "ai bani da lafia kaina yake ciwo shine Maa tace nai zama na gobe sai naje"

Na bude baki zanyi magana knn su Kamal suka shigo, kallonsu nake da dukkan alamu ba lafia ba don yadda Kamal yake ta hura hanci yana goge gumi.

Kallon Khalil nai don nasan yadda kamal yake ko na tambaye sa baxai iya min magana ba, cikin saurin magana ta nace "mai aka masa naga sai huci yake ko fada sukai ne"

Goge goshin sa Khalil yai cikin nutsuwa kasancewar sa komai a nutse yake yace "Ya BATUL Manniru din gidan Kawu Nasiru ne sukai fada dashi, wai kawai don Malamar su Mimi tace bata ganta ba a gaishe mata da ita shine da muka fito ya tare mu yana fadin baiga amfanin saka Mimi a makaranta ba tunda *SHEGIA CE* ita Shi kuma khalid ya mare sa shine suka fara fada da kyar aka rabasu" ya karashe hawaye na zubo masa.

Tunda ya ambaci shegia naji kirjina na min wani irin zafi cikin masifar dake taso min na shiga dakin mu, hijab na dauko na fito dashi a hannu na ina kokarin sawa.

Umma da tai shiru kanta a kasa ta dago ta kalle ni tace "meye haka Batul ina zaki je"

Girgiza kai kawai nake don tsabar bala'in dake cina bana Jin ma zan iya magana in da abinda na tsana a duniya shine a dangan ta min Mimi da shegia tabbas nasan gaskia ake fada amma raina baci yake a duk lokacin da aka kirata da haka kuma ko waye ya fada mata sai na gaya masa maganar da nasan zai dade yana jin takaicin ta.

Da kyar na hadiyi wani yawu nace "zanje gidan su ne in jawa uwani kunne akan yaranta wallahi Umma duk lokacin da suka kara shegan tamin yarinya sai nasa an karya musu kafafu don uban babansu."

"Mai kuma babana yai haka ake zagin sa Batul".

Juyawa nai ina kallon babanmu daya shigo hannun sa rike da leda wanda wannan dabi'ar sa ce kullum zai dawo daga kasuwa sai ya siyo wani abu komai kankantar sa ya shigo da shi.

Turo karamin bakina nai gaba ciki ciki nace "Manniru neh ya cewa Mimi shegia shine zanje na jawa uwani kunne akan su kar nasa su cilla su karya min kafar su ace ban fada musu ba"

Zaunar dani baba yai akan dakalin kofar dakin mu yace "don sun ce haka sai ki biye musu, kinsan dama abinda suke so knn suyi magana wani ya biye musu su tada fitina ki rabu dasu wata rana ko ance su fadi haka baxa su fada ba Batul"

Nidai Shiru nai kawai ina girgiza kaina tunda Baba yace na rabu da su na kyale su Amma wallahi sai nasa cilla ya zane min yaron nan in da hali na ko yar karamar targade ne ya masa a kafafun.

Ina zaune a wajen Aysha ta shiga kitchen don karasa girkin da ban gama ba, su Khalil kuma sun chanja kaya sun fita, Mai da kallona nai gurin su Baba da yake wa Mimi Wasa sai dariya take tana jan gemun sa. Kafe ta nai da ido ina Jin tsoron zuwan ranar da zata tambaye ni *WAYE MAHAIFIN TA* mai zan ce Mata ban san saba ban taba ganin fuskar sa ba banma san ya yanayin sa yake ba abu daya ne nake da shi mallakin mahaifin ta shi kuma bansan ta yadda zai kaini ga mahaifin nata ba.

Lumshe idona nai tsanar ko waye baban ta yana taso min tabbas da zan ido hudu da shi da ina da dama saina caka masa wuka a kirji......




*************

Zaune suke a lafiyayyan palourn gidan daya kasance mallakin mai gidan ko wanne dare anan iyalan gidan suke taruwa suke zama tare suke cin abincin dare.

Mami ce ta shigo palourn cikin shigar ta da kowa yasan ta da shi wato lifaya mai tsadar gaske red colour wacce ta haska farar fatar ta kana kallon ta zaka san cewa ita din shuwa arab ce, zata kai shekaru 45 Amma jikin ta bai nuna ba sbd tana da jiki nai kyau.

A hankali take tafiya hannun ta rike da kaskon turaren wuta data saka, sai da ta fara ajiye kaskon a kan table din gefen manyan kujerun Palourn sannan ta juya ta kalli Abie da tunda ta shigo ya kafe ta ido yana sakar mata murmushi mai cike da ma'ana, itama mayar masa da martanin murmushin tai tana masa wani kallo na kasan ido kafin ta isa kan kujerar da suke zaune shida Mama ta zauna itama.

Gaisar da Abie tai cikin nutsuwa kafin ta juya taiwa mama sallama, ciki ciki ta amsa ta daga kanta sai hura hanci take, itama bata damu ba ta maida kallon ta kan TV tana kallon news.

*JUNAID* ne ya fara shigowa cikin nutsuwa sanye da jallabiya as usual hannun sa dauke da carbi yana ja a hankali, kara sowa yai kusa da Abie ya tsugunna ya gaishe su, cikin so Abie ya amsa yana shafa kwantaccen sumar sa.

Mami ma murmushi take kafin tace "ina ka baro Samira din yauma baka zo da ita bakoh?"

Sosa goshin sa yai yana sunkuyar da kansa don baya iya hada ido da iyayen sa yace "Mami tana gidan su ne ynxu in zan wuce zan biya na dauke ta"

Gyada kai tai tace "Allah yai muku albarka ya warware muku dukkan matsalolin ku"

Ameen ya amsa yana komawa gefen ya zauna a kasa yana jan charbin sa cikin nutsuwa.

Baiyi minti goma da shigowa ba Yusuf ya shigo bayansa Sagir ne sai auta Mufeeda, Suma sai da suka gaishe da Abie dasu Mami sannan suka koma kusa da Junaid suna masa magana kasa kasa.

Hade rai Mama tai ta sani kusancin yaran ta da su Junaid tayi yadda zata yi ta raba su Amma abin yaci tura ta zage su ta zuga su amma a banza sudai kome zata yi baza su daina kula Yan uwan suba, kusan kullum ma a part din Mami suke wuni wannan abin yafi komai bata Mata rai.

Kallon su Abie yai kafin ya girgiza kansa yace ina *AZLAN* Junaid ne ya amsa Shi da fadin "Abie yana nan zuwa da zan fito ya shiga wanka neh"

Gyada kai kawai Abie yai yana maida kallon sa TV, ba'a dau lokaci mai tsayi ba suka fara jiyo fito yana doso palourn gaba dayan su suka zubawa kofar shigowa palourn ido duk da kuwa sun san waye zai shigo din.

Cikin takun jarumta ya shigo palourn yana sanye da three quarter brown colour sai armless riga light brown wacce ya bude botir din gaban rigar guda uku hakan ya bayyana kirjin sa, kafar sa sanye da wani takalmi mai kama da silifas, kamar su daya da Junaid don kana ganin su zaka gane Yan biyu neh sai dai Shi yafi Junaid haske kuma ya fisa kyau da kirar jiki mai kyau, cikin takun jarumta ya karaso tsakiyar palourn bayan ya cire takalmin sa.

Binsa da kallo Mami tai tana girgiza kai ganin askin kansa ita ynxu ma data sanin ce masa yaje yai aski take, da kansa sumar ce kawai ya tara sosai duk da sumar tasa a kwance take kamar ta larabawa amma tace yaje ya rage ta gashi ynxu yaje an kwashe gefe data an bar masa gefe daya. Mai da idonta kan damtsen hannun sa na dama tai dake dauke da katon tattoo na zaki a jiki, sai gefen wuyansa na hagu kuma da aka masa tattoo na miciji inda aka biyi da jelar micijin har wajen kirjin sa, girgiza kai tai a ranta tace "Allah ya shirya min kai Azlan"

Daga tsayen da yaje ya dan rankwafo yana tura hannun sa a cikin aljihun sa cikin muryar sa Mai kaushi da kame wa yace "Evening Abie" ba tare daya jira amsar Saba ya juya gun Mami yace "Evening Mami", Mai da kallon sa kan Mama yai ya zuba mata manyan idon sa da suka sha kwalli yace "Eve Hajia"

Hadiye wani yawu tai a duniya tana tsoron Azlan duk iskancin da zata yi a bayan idon sa take yinsa amma tana matukar tsoron sa, cikin inda inda tace "lafia"

Yamutsa fuska yai yana duba apple watch din dake daure a hannun sa na hagu ganin pass 8 yasa shi kallon Abie yace "zan iya ware wa Abie"

Girgiza masa kai yai takaici kamar zai kashe sa yace "na fada ma wallahi yau baxa ka fita a gate dinnan ba na gaji da halin Ka in Ka fita shashancin Ka baxa ka dawo ba sa tsakar dare"

Girar sa ta hagu ya daga yana shafa gemun sa yace "ta gate nedai Ka haramta min ware koh"

Daga kai Abie yai cikin tabbatar wa, juyawa yai ya kalli su Junaid da suka zuba masa ido gaba dayan su, yana juyowa duk suka juya suka maida kallon su kan TV sai Junaid ne kawai ya tsare sa da ido yana masa magiyar ya saurara yaji abinda Abie zaice.

Tabe bakin sa yai ya kalli Mami yace "kina bina da addua fah Mami kar wata ta danne miki ni tayi min fyade ta raba ni da budurwarcin dana ke ajiye wa"

Sunkuyar da kai su Mufeeda sukai yayinda Abie ya zuba masa ido kawai yana mamakin inda Azlan ya dakko rashin kunya sam bashi da kunya ga kwarjini da Ubangiji yai masa ko shi daya ke mahaifin sa kwarjini yake masa sosai, ita dai Mami addu'ar daya ce tai masa take yi a zuciyar ta tana kuma roka masa shirya.

Juyawa yai yana tafiya cikin jarumta, sai da yakai bakin kofar palourn ya juyo ya kalli Abie yace......






Ya kukaji salon book din🥰

Littafi ne mai cike ta sarkakiya ku biyo ni don na warware muka duk wata sarkakiyar dake ciki.



Comments Nd share plz🥹



Mrs A.M🥰❤️
[03/08, 11:42] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️

*TASWIRAR KADDARA*

♠️♠️♠️♠️♠️


Written by
Mrs A.M🥰

Page 2

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM


Sai da yakai bakin kofar palourn sannan ya juyo ya Abie yace "baxan taka dokar kaba," daga haka yasa kai ya fita.

Da sauri Abie ya mike yabi bayansa sanin dayai masa tunda har ya shirya zai fita sai ya fitan kuma ba ta gate zai bi ba, bin bayansa Junaid yai shima da sauri yana girgiza kansa.

Azlan yana fita daga palourn bayan gidan yaje ya dakko ladder ta karfe cikin zafin nama, ya rike ta da hannu daya kamar ba abin nauyi ya dakko ba, ware ta yai ya saita a jikin bangon gidan yadda zai mai daidai, su dai masu gadi suna zaune sai satar Kallonsa suke ba halin su bari ya gane suna Kallonsa.

Cikin sassarfa ya shiga takawa hana hawa sai da ya Kai karshen sa yadda zai dira daga gidan sannan ya juyo ya kalli Abie da Junaid, shafa gemun sa yai kafin ya saki wani murmushin gefen baki daya bayyana dimple dinsa guda daya na bangaren dama, juyawa yai ya dira daga gidan.

Sai da Abie ya dafa kirjin sa yana addu'ar Allah yasa bai ji ciwo ba, maganar da Azlan yake da karfi ne yasa Abie sauke ajiyar zuciya.

Shi kuwa yana dira mikewa yai ya karkade jikin sa sannan ya kalli dogon ginin daya diro, shafa gemun sa yai yana lasar lips dinsa iPhone 13 pro max dinsa ya zaro a aljihun sa, wata number yai dialing bata dade tana ringing ba aka dauka.

A kausashe yace zo mu hade ina kofar gidan mu, daga haka ya kashe wayar, bai dade sosai a wajen ba wata lafiyayyar mota ta shigo layin, a daidai kusa da shi ta tsaya bai wani tsaya jiran komai ba ya bude gurin mai zaman banxa ya shiga suka figi motar a guje suka bar layin.

Abie kuwa girgiza kai yai kawai suka koma palourn, Mami ce ta kalle sa fuskar ta cike da damuwa tace "ya fita koh Abie"

Zama Abie yai yana ajiyar zuciya yace "don na ce masa baxai fita ta gate ba shine ya haura katanga ya dira"

Lumshe idon ta kawai tai tana binsa da addu'a duk da ya kasance mara Jin magana amma shidin mafi soyuwa a gare tane baya Wasa da duk abinda ya shafe ta kuma baya mata karya.

Mama kuwa ajiyar zuciya ta sauke cikin Jin dadi sbd dama ita duk ranar da yazo suka zauna da shi takura mata yake, ta rasa mai yasa yaron ya raina ta tunda take dashi bai taba ce mata Mama ba sai dai Hajia da Yaya ma yake ce Mata saida Abie da Mami suka dinga masa fada sannan ya fara ce Mata Hajia.

Haka suka ci abinci kafin su gama aka shiga hira, sai wajen 10 sannan Junaid ya mike kallon Abie yai yace "Abie bara na tafi zan biya na dauki Samira a gidan su"

Murmushi Abie yai cikin kauna yace "Allah ya tsare ya cigaba da kare mana ku Allah ya warware muku dukkan matsalolin ku"

Fuskar sa cike da murmushi yace"Ameen"

Kallon Mami yai cikin nutsuwa yace "Mami sakon samiran tace min kin ce zaki bada sako in taho mata da shi"

Mike wa Mami tai cike da tausayin yaron nata ta ce "muje na baka dama dambun naman da nai ne nasan tana so sosai shine na zuba mata"

Tabe baki Mama tai tana gwasine fuska itama ta kusa aurar da Yusuf dinta tayi sirikar.

Bayan sun shiga part din Mamin Mika masa leda Mai dan girma tai wacce take dauke da dambun naman a cikin, sai da ta kara masa nasiha sosai akan yadda da KADDARA sannan ya tafi.

Binsa tai da kallo cike da tausaya wa shekarar sa biyar da aure amma har ynxu matar sa ko bari batayi ba, duk inda suka je kuma matsalar daga gare sa ne amma matar tasa lafiyar ta Lau, da farko da aka gane matsalar daga gurin sane yaso rabuwa da samiran amma ta dage ita akan ta yadda da KADDARA zata zauna da shi ko da baxa ta taba haihuwa ba har karshen rayuwar su..



***********

Kallon cilla nai dake zugar sigarin sa cikin kwanciyar hankali, tsaki nai cikin fada fada nace "wallahi cilla in baxa ka rage shan sigarin nan ba zamu raba hanya haba"

Yar da sigarin yai a kasa ya murje ta sannan ya kalle ni yana murmushi yace "afuwan aminiya ta xan kiyaye Insha Allah tun safe ban sha ba fa."

Tsaki na kuma ja kafin nace "cilla so nake ka targada min Manniru dan gidan kawu nasir, yaron nan dan baya jin magana shine zai zagi Mimi"

Ashar ya saki yana jan kafar sa baya kafin yace "kika ce zagin shalele yai wallahi sai na karya sa don uwataii"

Gyada kai nai cikin takaici nace "ba sai ka karya saba kawai kasa amasa shegen duka yadda gobe ko wani ya gani zai zagi Mimi sai ya kwabe sa"

Murza kafa a kasa Cilla yai kafin yace "an gama aminiya ta kuma abokiyar shawara ta muje in taka miki ki karasa gida sbd yan jagaliya"

Jera wa mukai muna tafiya yana ban labarin yadda zai casa Manniru har muka karasa kofar gidan mu, sallama nai masa na shiga gidan, ba kowa a tsakar gidan hakan yasa na nufi palour don nasan suna zaune ynxu tunda an kawo wuta.

Da sallama na shiga palourn duk suka amsa min, Zama nai a gefen kafar baba ina cire hijab din jikina.

Kallona Umma tai tace "kin biya gurin cilla neh koh don nasan yadda kika dade din nan sai dai in kun hadu dashi"

Sosa keya ta nai nace "Umma a kofar gida muka hadu fa shine kawai muka gaisa"

Girgiza kai Umma tai tace "ni na rasa me yasa kike Kula wannan yaron wallahi sam baya ji tubarkalla"

Abba ne ya ce "A'a Umman Aysha ki bisa da addu'a kawai shima dana Allah ya shirye sa da dukkan zuri'ar musulmai baki daya"

"Ameen" muka hada baki gaba daya muka ce, mike wa nai ina fadin "sai da safe Baba gobe da school kuma ina son na fara shiga school din su Mimi"

Khalil ne yace "Ya Batul zan raka ki in zaki kaita"

Harara na sakar masa sannan na juya na nufi dakin mu nida Aysha, akan katifar mu 6 by 6 na ga Mimi tana sanye da rigar baccin ta kanta sanye da hula, murmushi nai na karasa gurin wardrobe dinmu, kayan bacci nasa na hauro kan katifar addu'a na fara ma Mimi kafin nima nayi, janyo ta jikina nai na rungume ta hawaye masu dumi suna zubo min a fuska tabbas a duniya Mimi ce rauni na ita nake kallo nake tuna *TASWIRAR KADDARAR* data same mu shekaru 5 baya.

Lumshe idona nai ina ina tuna abubuwan da suka faru shekarun baya lokacin ina da shekara 14 gashi ynxu ina 18 amma abun kamar ynxu ya faru......



**********

Kallon Haidar Azlan yai yana tabe jajayen lips dinsa yace "in baxa ka kaini club dinba sauke ni in karasa ai ina da kafa"

Girgiza kai Haidar yai yace "Azlan kayi ma kanka fada Kai ynxu ya dace ma ace kullum kana hanyar zuwa club gurin Yan mata"

Shafa gemun sa yai yadan lashi jajayen lips dinsa kafin yace ina ruwan Ka Mata ai abin nishadi neh kuma don naje AI ba budurcina zan basu baaaa.......








Comments Nd share plz🥹




Mrs A.M🥰❤️

[04/08, 20:17] Deejarh🤍: ♠️♠️♠️♠️♠️

*TASWIRAR KADDARA*

♠️♠️♠️♠️♠️


Written by
Mrs A.M🥰

Page 3

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Assalamu alaikum Fans ina muku albishir din mai da Book din Taswirar kaddara free Book, Allah y bar kauna🥰

Tsaki Haidar yai yace wallahi gaba dayan Ka dan iska ne, ynxu kai sbd takadari ne baka da aiki sai maganar budurci daga anyi magana sai kace kana tattala budurcin Ka.

Dage gira daya Azlan yai kawai yana tsotsar lips dinsa hayaniyar ta ishe sa shiyasa kawai yaja bakinsa yana tsotsa, kallon sa Haidar yai ganin yana tsotsar lips dinsa hakan ya nuna masa cewa baxai sake magana ba kuma yan miskilan cin sun hawo knn, shima Jan bakin sa yai yai shiru ya maida hankalin sa kan titi.

Tafiya mai dan nisa sukai kafin Haidar yai parking motar juya wa yai ya kalli Azlan daya kwantar da kansa a jikin kujerar motar yana gyada kai a hankali, bai yi magana ba sai bude motar yai kawai ya sauka ya tafi don tarar Keke napeo ya mai da shi gida.

Sai da Haidar ya fita tukun ya bude idonsa a hankali yana lasar lips dinsa, fitowa yai ya shiga gurin driver
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment