Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

💘SHIN SO DAYA NE?💝

*MALLAKAR:HAFSAT AL-MUSTAPHA*

*WATPADD:HAFNANCY*

*Gaisuwar ban girma gareku my wadpaddians & Hafnan's novella group,thanks for showing me true love,I also love you all so very much... 💗💗💗💕*


*KASHI NA BIYU:RIKICIN KARSHE*

🌼BABI NA DAYA🌼

Page 1-3

Ban kai ga isa kofar fita ba,sae kawai naji kaina ya harba,atake naji kamar ana buga min ganga akan,dakatawa nayi tare da rik'e kan da hannaye bibbiyu.

"Muido lafiyarki kuwa? " haka naji Anty Hajaar ta fada.Ni kuwa ko tankata banyi ba sabida wani irin jiri da naji yana nemar kwasheni ya kifar akasa.

Gani nayi tsayuwar na nemar gagarata don haka sena koma da baya na zauna da k'arfi agefen gado.

"Amaryar Nakowa lafiya kike kuwa?" Hakan naji k'awayena sun fad'a tare da tasowa suka zagayeni,wasu ta saman gado ayayin da wasu kuma ke tsaye agabana suna meh jiran nayi musu bayanin abinda ke damuna.

Ash ce ta shigo dakin tana fadin"Oya Fateenah,'yan mata duk ku taso aje ayi ho....... "

Ganin da tayi an zagayeni,sae sannu ake min ya saka ta cillar da mayafinta tare da rugowa da gudu,ture wasu friends dinmu tayi wanda hakan ya bata damar samun kusanci dani.

"Fateenah wats wrong? Lafiya naga kin dafe kai da hannuwa bibbiyu?"

Ash kuwa tsoro ne ya cika xuciyarta fal. Azuciyarta tace"Oh! Yah Allah kar dai ace Fadima ta samu labarin wanda aka daura mata aure dashi shiyasa ta shiga cikin wannan halin?"

Ita Ash tana waje sanda su angwaye suka shigo,sae taci karo da Mahmood wanda kuma aka nuna mata cewar ai shine angon Fadimar.Atake anan taji cikinta ya duri ruwa,ji tayi tana matuqar buqatar toilet awannan lokacin don yadda taji kamar tana shirin sakin gudawa ajikinta.Ai kuwa da azama tayi toilet din.

Koda ta fito,sake komawa tayi,alokacin suka ci k'aro da Suhaima wacce itama kiranta akai da ta fito suyi hotuna da angwaye,itama tana ganinsa wai amatsayin angon yar'uwartata,murza idanuwanta tayi da kyau don ta kara tabbatarwa da lallai ko shi dinne.

Ai kuwa shi dinne dai ba wai kamanni ba,da azama ta koma ciki don labartawa yayartata shine suka ci karo da Ash din.

Ash tace"Ke kuwa kanwa meya faru ne naga kina rafka wannan uban saurin har bakya kallon gabanki kike tafiya?"

Arud'e tace"Hmmm! Anty Ash kin san wa kuwa nagani amatsayin angon Yaya Fadima? Wallahi wannan wan saurayinta Mubarak dinnan na Kano ne.... Kin tunashi ai? Wannan Engr.Mahmood ne yake da suna ko....?"

Ash tace"Wallahi nima na ganshi,ganinsa ya saka nayi toilet don wata gudawa naji ta taho min alokaci guda don fargaba..... "

"Amma taya hakan ta faru? Dama yana sonta ne? Kuma taya akai har ya samu ya shawo kan mahaifiyarsa ya aureta bayan tun ganin farko da tayi mana bata qaunarmu musamman ita yaya Fadimar?mafi daurewar kan wannan al'amari ina shi Mubarak din yake ne da duk hakan ta faru??"

Suhaima ce take fadin wannna maganar ahankali cike da kuma tashin hankali.Ita kuwa Ash cewa tayi"Wannan tambayoyin duk abakin shi uban gayyar zamu samu amsoshinmu..... Kuma.... "

"Wae Suhaima kuskus din meh kukeyi ne tsaye anan baza kizo ayi hotunar ba kun shanye mutane can tsaye arana suna jira? "

Anty Hajaar ce ta katse musu hirarsu alokacin da take kokarin xuwa ta kira Fadimar itama ta fito ayi da ita.

Da sauri Ash ta janyo hannun Suhaima suka rab'a ta gefen Anty Hajaar suka fice waje.Suna fita suka hada idanuwa da Engr.Mahmood,sakar musu pretty smile yayi.

Su kuwa kallon junansu sukayi,Ash ta rad'awa Suhaima magana akunne.Murmushi tayi sannan tayi wajensu don daukar hotuna.ce mata tayi kada ta kuskura ta nuna masa surprise face ko kuma tayi gangancin tambayarsa taya akai ya samu auran Fadima?

Ita kuwa Ash komawa tayi dakin Fadima,Allah-Allah kawai take tayi Fadimar tayi creating wani scene wa Anty Hajaar kamar yadda tayi kwanakin baya,don idan tayi hakan ai babu yadda za'ayi ta fito tayi hotunan.Tasan tabbas Fadima nayin ido hudu da Mahmood amatsayin mijinta,xata iya zauncewa kuma ita bazata so ace Fatin ta nunawa duniya cewar bata san mijin da aka aura mata ba.Shiyasa take ta addu'ar Allah yasa kafin ta isa dakin ta tarar kawai Fadimar ta riga tayi creating wani scene.Ai kuwa dadi ne ya kusan kasheta ganin yanayin da Fadimar ta shiga duk da cewar ba hakan taso ba.Ta fison koda Fadimar xatayi wani tashin hankalin toh ta bari sae bayan an kaita gidan Mahmood din amma ba wai tayi anan idan ta ganshi ba.

(Back to the scene).

Dakyar na budi baki nace"Ash wani azababben ciwon kai ne naji ya saukar min yanzun nan..... "

"Subhanallah.... " ta fada tare da kai hannu tana taba wuyana.

Zaro idanuwa muka ga tayi tana fadin"Fateenah wallahi jikinki har ya dau zafi,zazzabi ke shirin rufeki..... "

Anty Hajaar ce tayi saurin taran numfashinta wacce take tsaye tun dazu take kallon ikon Allah,cewa tayi"Iskancin banza da wofi.... don kawai nazo kiranki ayi hotuna dake shine xaki kirkiro wata k'aryar banza can....? "

Ash ta kada baki tace"Haba Anty wannan wacce irin magana ce kike yi haka? Kema zo ki taba jikin nata kafin ki karyata zancen.... "

"Yi min shiru anan! mara kunyar banza da wofi ai daga ke har ita jirgi daya ce ta kwasoku ta rashin kirki da mutumci..... "

Karkata akalar zancen nata tayi xuwa gareni"Ke kuwa Fadima ni abin naki ya dena bani mamaki sae tsoro donni de ban taba ganin amarya irinki ba,ranar da aka kawo gaisuwarki some mana kikai,yau kuma daga cewa ki fito ayi hotuna kin kirkiro xancen rashin lafiya,ko dae auran ne kawai bakyaso ayi miki ita gaba daya? "

"Anty Hajaar don Allah ni ki tafi kawai kada ki k'ara mata wani ciwon akan nada..... " acewar Ash wacce ta soma fusata da xancen Anty Hajaar.

"Eh! tatacciyar mara kunya ai dama wucewa xanyi yanzun nan kuwa,kuma ke Fadima bari mah kiji na gaya miki,gwara mah ki bar wannan k'aryar rashin lafiyar don ko kina shure-shuren mutuwa ne anjima zamu kaiki dakin mijinki,kuma ai ke kikace kina sonsa don haka ya zamar miki dole ki zauna dashi don an riga an dauraku kuma anjima kadan xamuyi miki rakiya xuwa gidansa..... " (lol kai Anty Hajaar din nan 'yar gari ce).

Fuuu! ta juya ta fice kamar kububuwa.Sae ayanzu hawayen da suka makale acikin ramin idanuwana suka samu damar gangarowa.Sam Anty Hajaar bata dauko halin Umma ba,Umma sam bata da wani hayaniya kamar Anty Hajaar,komanta da sanyi take yinsa,maganarta mah cike da salo da karairaye murya,sab'anin Anty Hajaar maganarta da fada take yinsa,shiyasa sam bata cika shiri da mutane.

Kawayena sae sannu suke ta min.Haka aka gama hotuna banje anyi dani ba.wasa-wasa sae da zazzabin nan ya kwantar dani,har allurai biyu sae da madam Iyabo ta min (da yake ita din nurse ce). Jama'a kuwa sae cewa suke wai amarya na zazzabin bankwana da iyayenta ne.

Ash ta gargadi Suhaima da kada ta kuskura ta gayawa Fadima cewar Engr.Mahmood ai shine mijinta,ta bari idan aka kaita ta sani kuma tasan dole zata haqura ta xauna.

Ni kuwa sae ji nake ana 'amaryar Mahmood Nakowa' azuciyata nace"Nakowa shine sunan mijin nawa? "

(Dayake su Mahmood basa amfani da sunan Nakowa shiyasa bata sansu da sunan ba.... Kai Engr. akwai brain,shi ya bada wannan sunan awajen daurin aure don kada Fadima tayi saurin d'agowa don ta siyasa ya tambayi Mubarak ya gaya masa cewar be taba fada mata family name dinsu ba...)

Shi kuwa Mahmood picture daya ya dauka sannan suka fice da tawagarsa don be ga amfanin tsayawa daukar hotuna ba bayan babu sahibar tasa aciki.Shi kansa was juz like Ash,yayi murna ba kadan ba da addu'arsa ta karbu,Fadima bata fito ba balle ayi tashin hankali,dama can Anty Hajaar ce da iyayinta tace ya tsaya ta kira Fadimar suyi hotuna.

***
Wuraren karfe hudu da rabi aka bugo musu waya cewar ga 'yan daukar amarya nan tafe na ita Fadimar.

"Fadima lallab'a ki shirya tunda jikin naki da dan sauki,ki hanzarta don an bugo wai 'yan daukar amarya na kan hanya....... "

Da sauri na tari numfashin mama Jamila wacce k'anwace ga Abbanmu"Mama ina za'a kaini? "

Mama tace"Can kano za'a kaiki don nan danginsa suke,idan yaso daga baya shi mijin naki da kansa zai maido dake nan Zaria gidan da zaki zauna...... "

Wani kuka ne ya kufce min jin cewar kano mah za'a kaini garinsu Mubeen dina,nace"Gaskia ni dai mama babu kanon da zaku kaini,ni dai kawai awuce dani gidana kawai..... "

Bud'e baki tayi tace"Ikon Allah! yau ni Jamila gani ga mara kunyar amarya,Muido ina kika tab'a jin anyi haka?kul! kada mah ki bari wani yaji don dariya zasu miki suce kuma baki da kunya,an san kina mararin zuwa dakin mijinki amma ki bari asoma mik'aki ga danginsa kafin ki koma dakinki kamar yadda akeyi ah al'adance.... "

Wani haushi ne ya rufeni ganin ita sam Mama bata fahimci abinda nake nufi ba,ita azatonta kawai zumud'in tafiya gidan miji nake.

"Ki tabbata kafin na dawo kin shirya kanki,maza kawayenta ku tashi ku taimaka mata ta shirya kanta.... "

Had'iye wani muyau meh daci nayi,kana nace"Mama banda lafiya fa,haka kuke son ku kaini?"

Afusace tace"Kya warke acan,idan kuma mutuwar ta tashi xuwa kya cika adakin mijinki kinga kuwa asirinki arufe tunda kina da aure akanki,sannan ga wata daraja,rahama da kuma haske da gawarki zata samu,kuma mutane zasu fi ganinki da mutumci da kima ah idanuwansu,uwa-uba mijinki meh masifar sonki nasan ze daga miki tafin kafarsa ki samu aljannarki...... "

"Mama pls ki bari banso,ya isa haka jeki xan shirya.... " na fada tare da rushewa da wata sabuwar kuka.Mama cikin jindadi ta wuce abinta don ganin maganganun nata sunyi tasiri ak'wanyar Fadimar.Kawayena kuwa sae dariya suke ta min.Ash ta taimaka ta shiryani cikin wani tsadaddan light brown swiss lace wanda akayi masa kwalliya da flowers navy blue.

Fati mamza wacce dawowarta kenan daga gun wani biki anan Zariar,itace ta cigaba da shiryani,ta min daurin dankwali meh shegen kyau,sannan ta yafa min tsadadden mayafina navy blue meh kwalliya ajikinsa na kyalkyali da flowers.Mayafin daga saman kai ta yafa min ita.takalmana flat ce brown colour kalar kayan.

Ta feffesheni da turare,aka fito dani xuwa bangaren Abba inda anan ne za'a mana fada da nasiha.Gida ya rud'e da rangad'e rangad'en guda.Koda na shiga falon na tarar har Suhaima ta rigani isa,zaune take akasa kusa da kafafuwan Umma,ta kifa kai asaman cinyar Ummar tana rera kuka ahankali ayayin da Umma ke dan bubbuga bayanta alamun rarrashi.Can gefensu Abba ne zaune sae karkada kafafuwa yake yana meh fesar da iskan bakinsa.

Ganin shigowar Fadima da Kuma kukan da itama take rerawa ya saka Umma saurin mik'ewa don bazata juri tsayawa yin bankwana da 'ya'yan nata ba.

Hanyar fita ta nufa alokacin da taga Fadimar ta sami gu ta zauna akasa akusa da Abba.

"Haba! Kareemah dawo ki sallami 'ya'yanki mana,ki dawo kiyi musu fatar alheri acikin sabuwar rayuwar da zasu shiga..... "

Sabon kuka dukanmu muka rushe dashi har Umman,dakyar ta dawo ta nemi gu ta zauna.Abba ya shiga lallashinmu da Kuma ban baki,dakyar muka haqura mukayi shiru don sauraren nasiharsa agaremu.

Abba yayi gyaran murya sannan ya soma jawabinsa"Alhamdulillah! Alhamdulillah! godiya ta tabbata ga mahallicin sammai da kassai,mahaliccin dabbobi,aljan,mutum da duka komai meh rai ko mara rai.Na godewa Allah da ayau ya bani damar sauke nauyin daya rataya bisa wuyana amatsayina na mahaifinku na ganin na aurar daku ga nagartattun mazaje na gari,Fadima hakika nasan ko kadan ban kyauta miki ba dana hana miki auren zab'inki,amma ina son ki san cewar ko kadan banyi kuskure ba,don idan baki manta ba,ah addinance wajibi ne iyaye su zabarwa 'ya'yayensu abokanan rayuwa na gari,don haka karki ka laifina don na aurar dake ga wanda ba zabinki ba,Wallahi Fadima ina meh tabbatar miki da cewar watarana keda kanki zaki zo kice Abba nagode da zab'inka,ashe zab'inka alheri ne agareni.........."

Haka de Abba yayi ta mana fada da nasiha kan mu riki aurenmu da kyau Kuma mu baiwa auren muhimmanci sosae,mu bi mazajenmu sau da kafa sannan kuma mu k'yautatawa danginsa.Haka mah Umma itama tayi mana fad'a sosae.Ashe wai wasu acikin danginmu wayenda suka sanni tare da Leedar sunyi ta mamakin yadda akai ya koma mijin Suhaima,Abba de ce musu yayi haka Allah ya tsara tun fil'azal cewar Suhaimar itace matarsa amma ko kadan be labarta masu komai na game da shashancinmu ba.

Su goggonnina,mamannina da wasu kawunnina duk se da suka shigo suka mana fada da nasiha meh ratsa xuciya.Ni da Suhaima babu abinda muke illa kuka.Daga k'arshe akayi waje damu don har 'yan daukar amarya hadda na Suhaima sun iso.Sae da akayi da gaske kafin arabamu da su Abba da kannena.

Abba yace baya son tarkacen mutane da nufin kai amarya,sam an bar yayin nan.Mama Jamila,Anty Hajaar,Mama Sadiya cousin dinsu babanmu,sae kuma kawayena biyu,Ash da zuwairah kadai akace zasu bini.

Ita kuwa Suhaima mutane har Kusan goma ne wai zasu bita tunda nan cikin Zariar za'a kaita kuma ayau din zasu komo,kuma duka kawayenta suma zasu bita.Nayi kuka sosae,sae nake ganin kamar an nuna min rashin gata ne.

Ni da Kawayena muka shiga mota daya,ayayin da dayar motar kuma su mamanni ne aciki. Sae gud'a ake tayi har motocinmu suka bar kofar gidan.....




A/N
Hey Fadima sa'ad Mainasara welcome to Nakowa's family!!!

Ina kuke tunanin za'a kai Fadima? Family house ko kuwa gidan Baba Mu'azzam za'a sauketa? Ku biyo.

Sorry guys! chapters na kashi biyu zasu dunga zuwar muku a little bit scanty don novel din ya Kusan zuwa karshe & I want the chapters too be a little bit much..... Yeeeepeeee shout out to Hafnan! Her first novel is about rounding up!!! 💗💗

©QUEEN CE©


*💘SHIN SO DAYA NE? 💝*

*MALLAKAR:HAFSAT AL-MUSTAPHA*

*WATPADD:HAFNANCY💞*

*KASHI NA BIYU:RIKICIN KARSHE*

🌼BABI NA BIYU🌼

*💧💧💧KAI AMARE💧💧💧*
💧💧 💧💧
💧 💧

*page 3-6*

Har muka isa kanon ban mah san mun iso ba sabida tun shigata motar,cigaba nayi da sana'ar kukana,Ash kuwa sae aikin rarrashina take don ni da ita kawai muke xaune agidan baya,ita kuwa Zuwairah gidan gaba ta xauna wacce jefi-jefi suke d'an taba hira da meh tuki wanda na lura kamar yana cikin abokan ango.Shi din mah yayi rarrashin duniyar nan amma naki nayi shiru,can yace arabu dani kila so nake shi angon nawa yazo ya rarrashi abarsa da kansa,abin ya baiwa su Ash dariya,ni kuwa haushi maganar tasa taban kamar na tashi na kifa masa lafiyayyun mari.

Mubarak ne ya fad'o min arai,yanzu shikenan mun rabu kenan? Yanzu baza'a taba k'irana da matar mubeen ba kamar yadda nake ta burin hakan sae matar Mahmood Nakowa?abin mamaki mah wai dangin mijin nawa ah kanon suke,kada watarana fa mu had'e dashi.... Wani b'angaren xuciyata kuma yace"xancen banza keda mah ah Zaria zaki zauna? Sannan meye naki na wani damuwa akan mutumin da baya qaunarki,mutumin da kuma sam be damu da rayuwarki ba?

"Toh! amaryar Nakowa mun iso,sae ki had'iye kukan naki ya isa hakanan kinga gidan surukai xamu shiga kada suga kina koke-koke su aza ko surukar tasu ba jaruma bace...... "

Ash ce ta katse min gajeriyar tunanina alokacin data bud'e min kofa da k'yau wai na fito,sae asannan na ankara da cewar har mun iso ban sani ba.

Sannu ahankali na sako kafafuwana waje tare da dire su akasa,wani daddad'ar ni'imtaccen iskar yammacin nan ne ya soma min barka da xuwa.fitowar tawa tayi daidai da wayar da wannan meh tukin keyi wanda ayanzu nasan sunansa don naji Zuwairah ta ambaci sunan wai *'KHALEED'*.

Cewa yayi"Kai dan iskan ango kana ina? gashi fah mun iso amma anki bamu amaryar..... "

Saurarawa naji yayi,can yace"Na taba maka irin wannan wasar ne? Ka yadda dani anki bamu ita wai sae kaje da kanka.... "

Ya sake saurarawa,can ya d'an d'ara yace"Kai wasa nake maka mallam karka min hauka,ga amaryarka nan mun kawo maka ita,tasha kuka kuma har yanxu tana kan yi ne sae kazo ka lallashi abarka........ "

"Ayyyirihiiiiiiii,lale marhaba da zuwan amarya.... " rangad'e rangad'en gudar dangin mijina ne ya hana min jin k'arshen maganar Khaleed da mijina.Ni kuwa jin sun nufoni ya saka na k'ara jan mayafina gaba don kada suga fuskata.

Wata 'yar matashiyar budurwace naga ta rungumeni tana fadin"Oyoyo!amaryarmu sannu da xuwa...... "

Mama Jamila ce ta rad'a min magana akunne,cewa tayi"Ki shiga da kafar damarki tare da bismillah,haka kuma xakiyi idan aka maidaki can gidanki.... "

Daga mata kai nayi alamar naji jawabin nata,daga haka naji wasu mata su wurin uku suma sun rungumeni kamar zasu kada ni akasa suna min sannu da xuwa har muka shige gidan.

Wani daki aka saukemu aciki wanda muka ji wani daddad'ar kamshin turaren wuta ya mana maraba da xuwa,gaskia ba laifi suma kanawa akwai son kamshi.Maganar gaskia ba k'aramin karramamu akai ba,nima sae naji na d'an saki jikina amma har xuwa wannan lokacin ban yaye mayafin kaina ba,ina nan lullub'e aciki kamar wata munafuka,lokaci xuwa lokaci nake dago kai na d'an saci kallon mutane.

Cikin k'ank'anin lokaci muka ga an cika mana gaba da kayan ciye-ciye da shaye-shaye.Mama Sadiya ne suka dan taba amma babu yadda basuyi dani ba amma naki ci.Ce musu nayi ak'oshe nake.Ak'arshe dai ruwa kawai na d'an sha.

Mama Jamila ce tace"Yarinya idan zaki mah saki jiki toh tun wuri ki saki don anan zamu barki,gobe idan Allah ya kaimu komawa gida abinmu xamuyi..."

Juyawa tayi ga Mama Sadiya tace"Sadiya hanzarta ki gama cin abincin ki min rakiya xuwa gidan wata k'awata dake nan jambulo,bazamu jima ba..... "

"Toh Addah... "acewar Mama Sadiya don Mama Jamila na gaba da ita.

Ni kuwa wani sabbin hawaye naji sun ziraro min saman k'unci,tayaya xan soma rayuwa agidan wasu bayan na sab'a da namu?taya mah xan soma had'a shimfid'a daya da wani k'aton gardi amatsayin mijina?

Yaye min mayafi naji anyi ana fad'in"Ai kya bari muga fuskartaki muga ko kin fini kyau koh? "

Ji nayi an fashe da dariya,ni kuwa gabana ne naji ya yanke ya fad'i,dakyar na iya d'ago kai ina duban wacce ta yaye min mayafina,ido hudu nayi da wata tsohuwa wacce kana ganinta kasan ta dad'e ana cin sallar idi da ita.Sae dai ba'a wani gane tsufanta don jikinta meh k'yau ne.

Tace"Masha Allah!.. Ashe dai megidan nawa balarabiya ya zab'o mana shiyasa yake ta rawar kafa da dokin auranta..... "

Aka sake fashewa da dariya akaro na biyu,ni kuwa d'an murmushin leb'en baki ne kawai ya sub'uce min,atake anan na gane cewar wannan tsohuwar kakarsu ce.

Tace"Amarya share hawayenki,don ni dake xamuyi zaman lafiya idan da hakan kika zo,idan kuwa da akasinta kika zo,toh nima nan uwargida ashirye nake...... "

wasu 'yan mata ne naji sunce"sae kakus! Kakaaa rigima.... " aka fashe da dariya.

Haka dai tayi ta mana barkwanci da wasannin wanda atake anan naji kawai tsohuwar ta shiga raina.Su Mama Jamila kuwa suna gama ciye-ciyensu suka sa kai suka fice xuwa unguwar da suka ce xasu,muka rage daga ni,Ash,Zuwairah sae kuma Anty Hajaar wacce ga dukkan alamu jininta ya hadu dana Kaka rigima,don sae hira suke ta xubawa.

Ba'a wani jima ba muka ji an soma k'iraye-kirayen sallar magrib,daya bayan daya muke shiga bandaki muna dauro alwala.

***
Itama Suhaima anata b'angaren an musu tarban mutunci,sosae aka karramasu.Reedah itace wacce ta soma rungumota,ta rad'a mata magana akunne"Oyoyo sahibata,barka da xuwa,yau Allah ya cika muku burinku ta mallakar junanku,Suhaima dear welcome home as matar yayanah...... "


DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment