Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > aihausabooks@gmail.com

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels

WhatsApp Number: 08138873799


Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************

FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪


®

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


💌 SAK'ON NA MASOYA NE🤗

Ina mai neman afuwa kan jinkiri da aka samu na cigaban wanga littafi, Sidiya mai yawan hidama ce, da fatan za a cigaba da mata uzuri. Ina Godiya da kulawar ku. Sidiya ce ke mu ku fata na alkhairi🤝




WAIWAYE



Daga cikin Masallaci aka fara abinda ya had’a jama’a a wannan masarauta, wato d’aurin aure, in da aka umarci waliyin Ango da Amarya su matso kusa. Waziri ne ya fito daga 6angaran Sa’ayrasa, Fabarusa kuma Sarki Abdulrahaman ne ya nuna kan sa a matsayin waliyi.

Daga waje Khalil ne ke ta yiwa Yarima Barde hira, amma shi ina hankalinsa na ga Gimbiya K'amariyya, Allah Allah ya ke a shafa fatiha ya tafi garera don jin soyayyar ta ya ke har ransa, bare kuma yau gabar da ke tsakanin Masarautasu za ta kau, za su yi soyayyarsu a zahirance ba tare da wani shakku ba. Jin an shafa fatiha Yarima Barde ya tashi ya na mai fad’in.
‘’Alhamdulillah tunda an amra sai ku tashi mu tafi ko?’’

Har Khalil da Jafar sun tashi, tuni su ka tsaya cak jin marok’a na fad’in

‘’An d’aura auren *Yarima Abubakar BARDE* tare da *Gimbiya Fatima* akan sadaki (50000 CFA)"
Yarima Barde da sam bai lura da abinda su ka ji ba tsabagen hankalinsa ba ya wajan, a hasale ya kai kallonsa ga abokannasa ya na mai fad’in
‘’Me ku ke jira ne? Mu tafi, Allah Allah na ke na gana da Gimbiyata.’’
Su kuwa marok’a ba su fasa shela ba. Khalil ne yayi k’arfin hali ya ce
‘’Da ma kai ne Barde?’’
Cikin rashin fahimta Barde ya ce
‘’Ni ne wa?’’
‘’Angon da aka amrawa amren.’’
Jafar ya bashi amsa a tak’aice. Kai Yarima Barde ya girgiza cike da murmushin irin ban son rainin hankali fa. Khalil ya ce
‘’Saurara ka ji Barde’’
Nan kuwa muryar wani marok’i da ya zo giftawa ta dafda su ya doki kunnan Barde, fad’i ya ke
‘’An amra auren Yarima Abubakar Barde da Gimbiya Fatima....’’
Nan ya ya tsaya cak tamkar wanda aka zarewa rai, su kansu abokannasa sun girgiza kwaran gaske.

Daga cikin masallaci, ana gama d'aurin auren, inda kowa ya ke mamakin sauyin al’amura da aka samu, musammam jama’ar Sa'ayrasa, shi kuwa Aisar tunanin hanyar fita daga cikin jama’a yake, domin zuwa neman Bintu ba tare da Junaidu ya ankare ba. Bayin Sa'ayrasa ne d’auke da farantin goro da alawa, su ke bin kusirwa kusirwa in da suke mik’a farin tin jama’a na d'iba san ran su.
Bawan da ya zo kusurwar da su Aisar su ke, Aisar ya fara mik’awa, in da ya girgiza masa kai alamar ba ya buk'ata, har bawan zai wuce, nan idanun Aisar su ka sauka bisa yatsun bawan, me zai gani? Zobensa da ya bawa Bintu ne cikin yatsun na shi, bai ankara ba sai ji yayi Aisar ya damk’o hannunshi, a tsorace bawa ya saki farantin hannun sa dan ko shakka babu ya san tawagar shugaban k’asa ne gabansa.Hakan ya dawo da hankalinsu Junaidu da sauran ‘yan tawagar garesu. Aisar na mai duban idanun bawan ya furta
‘’Ina ka sami wagga zo6en? Menene dangantakarka da mai zo6en? Ina Bintu d’iyar bayi?’’



Babban gida kuwa 6angaran Jakadiya, Bintu na zaune tare da su Jakadiya sai ga Gimbiya K’amariyya ta shigo, ta yi kyau kwarai cikin jajayen kaya, ta d’aura alkyabba ruwan zuma bisa kayan, ga bayi nan biye da ita. Ta zo kar6ar mabudin wajan aje baki na musammam domin kar6ar Yarima Barde.

Ta na zaune ta na jiran Jakadiya ta shiga ciki dan d’auko mata mabud'in, su ka ji an shigo 6angaren Jakadiya an gud’a. Tuni hanjin cikin Bintu ya kad’a don kuwa ta san ta faru ta k’are an yiwa mai dami d’aya sata, aure dai an aura. Tuni ta fashe da kukan da dama ya tsaya k’asan mak’ogaran ta.
Jakadiya ta fito d’auke da mabud’i, yayinda Ladiyo ta shigo jiki na rawa, sai tafa hannu ta ke cikin salati da sallallami. Jakadiya ce ta tambaya ko lafiya, yayin da hankalin kowa ya koma gareta.
Cike da ladabi Ladiyo ta durk’usa gaban Jakadiya ta na mai fad’in
‘’Yau na ga lafiyar Allah Maigari gauro talaka da mata hud’u.’’

Cikin k’aguwa Gimbiya K’amariyya ta ce
‘’Me ya faru ne Ladiyo?’’

‘’Wato Allah shi taimaki Gimbiya, ji da gani dai ba ya k’arewa sai randa kurman bebe ya makance, Sarki Abdulraman na Fabarusa cike ya ke da abin mamaki, wani lamari sai shi.....’’
‘’Yo to wani abin mamaki? Ya ce ya fasa ne?’’
Jakadiya ta tambaya cikin rashin fahimta. Kana Ladiyo ta ce

‘’Eh to ya fa fasa be kuma fasa ba, da ya tashi yin bazata, sai ya amrawa d'ansa Barde Bintu.....’’
Hakan yayi daidai da ihun da Gimbiya K’amariyya ta kurma ta na mai zubewa k’asa sumammiya. Nan da nan aka yi kanta. Bintu kuwa yanda maganar ya doki kunnenta ta tabbatar ta zama kurma, don kuwa ba ta jin hayaniyar da ake gabanta
‘’Ya amra ma d’an sa Barde Bintu....’’
Maganar da ke ihu jikin kunnenta kenan.











®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE! (2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣



Tuni waje ya kaure da salati da salallamin bayi, Jakadiya ce ta sa aka yi maza aka shigar da K’amariyya daga cikin d’aki gudun gulman da ta san tabbas sai ta yad’u daga bakin bayin da ke wajan. Bintu kuwa ta ma kasa gane komai, kukan ta kawai ta ke, aure dai an d’aura mata, ko ta na so ko ba ta so tafiya ne dole a tafi da ita. Gashi a rasa wanda za a d’aura mata sai saurayin Gimbiya K’amariyya, Yerima Barde na Fabarusa! Hannu biyu Bintu ta d’aura bisa kan ta ta na mai fad’in

‘’Wayyo ni Bintu alk’iyama ta ta zo’’

Daga cik’in uwar d’aka, bayan an kori duka bayin da ke b’angaran Jakadiya, Hajja Kilishi da Inna Salti wanda Jakadiya ta aika Ladiyo da Kyallu su sheda ma su abun da ke faruwa ne su ka shigo d’aya na bin bayan d’aya, biye da su Gimbiya Binta ce, wacce ita ma labari tuni ya je mata.
Jakadiya ta umarci bayin da su ka taka mata baya su yi jiran ta waje. Bayan an watsa ma Gimbiya K’amariyya ruwa, da rokan Allah ta farfad’o ta na mai bin su da kallo kamar lokacin ta fara ganin fuskokinsu. Kanta bisa kan cinyar Inna Salti, Jakadiya zaune gaban ta sai kuma Gimbiya Binta wacce ta dad’e da gigicewa da jin lamarin da ya faru, in ban da kuka babu abinda ta ke don gani ta ke duk laifin Bintu ne ko shakka babu ita da uwarta ne su ka sa musu hannu wannan balk'in ya fad’a kan ‘yar uwarta.

Ko da idanun Gimbiya K’amariyya ya sauka kan Gimbiya Binta, ita ma d’in ta fashe da kuka don sai a sannan ne ta dawo cikin hayyacinta sosai. Cike da damuwa Hajja Kilishi ke tambayar

‘’Menene ne? Gide menene ke faruwa? Tun dazu fa nake tambayar ki Binta amma amsa ta gagara daga gareki, yanzu kuma mun samu ta farfad’o maimakon a sami sauki ina, kun maishe da gida kamar wajan makoki! Shin ba kwa gudun abinda zai je ya dawo? Kun fa san gidan ga cike yake da baki da kyar na sami hitowa daga cikin jama’a, ko rufa mana asiri ku sheda mana abun da ke faruwa.’’

Cikin kuka muryarta dak’yar ya ke fita, Gimbiya K’amariyya ta amsawa Hajja Kilishi, ta na mai fad’in

‘’Na shiga uku Hajja, Inna Salti na shiga uku, na d’au wuk’a na dab’a ma kaina, Allah Ya nuna min ikonSa, Barde…..Yarima Barde na Fabarusa……’’

Kuka ya ci k’arfinta, ta kasa k’arasawa sai shasshek’a ta ke. Cikin rashin fahimta Inna Salti ta ce

‘’Barde? Me ya faru da Barde na Fabarusa?’’

‘’Ni kam ta dad’a sa kai na cikin duhu, jakadiya wagga yarinya ba gamo ta yi ba kuwa?’’

Cewar Hajja Kilishi cike da damuwa.

‘’Yarima Barde da Didi masoya ne, shi ne dalilin ta na k’in amincewa ta auri sarkin Fabarusa wanda yake mahaifi a gareshi.’’

Gimbiya Binta ce ta amsa ma su.

‘’Kayya! Kai wagga lamari da me yayi kama! Kun ga irin ta ko? Gashi dai an cuci d’iyar mutane kin kuma cuci kanki K’amariyya, anyi gudun gara an tadda zago! Jakadiya dai ga irinta nan dai kin gani don kuwa wagga kulli ke da wagga d’iya ku ka kulla.’’

Fad’in Inna Salti ta na mai nuna matuk’ar b’acin rai.

Jakadiya da tunda aka fara maganar ta sha jinin jikin ta, jikinta ya yi sanyi kamar wacca aka tsunduma cikin ruwan sanyi cewa ta yi

‘’Uhum Allah shi ja da ran ki, yo to ni me zance? Ni ina naga ta ce wa? ‘’

Cikin kuka don kuwa idanunta sun rufe K’amariyya ta furta

‘’Don Allah ku taimaka a warware wanga lamari, don Mai Sama, kwarankwatsa zan iya rasa rayuwata, dan Allah ayi maza a shedawa takawa kafin na rasa raina, Ammu ki taimaka min…..’’

Kai Hajja Kilishi ta jinjina kafin ta ce

‘’Gide Takawa zai saurari wanga azzance kuwa Jakadiya? Yanzun ga ya na can wajan liyafar d’aurin amren nan......’’

Kafin Jakadiya ta amsa Gimbiya Binta ta yi saurin taran numfashin ta ta hanyar fad’in

‘’Ku taimaka tun kafin a makara, dan kuwa ba Sidi ba ko ni ma ina tara muddin ba a warware wanga
amre ba, ya d’iyar bayi za ta amri mutum kamar Barde, dan Allah Jakadiya ki sama mana mafita tun kan na had’iyi zuciya na mutu dan kuwa ciwon da na ke ji ya ma fi na Didi’’


‘’Makara kam an riga an makara, saidai fa a jira bayan komai ya lafa a yiwa Takawa magana watakil shi bai zai rasa dabara ba.’’

Cewar Hajja Kilishi yayin da tashi tsaye jiki sanyaye, tak’ara da fadin.

‘’Kunsan mu na da baki, duk abinda za ku yi kada ku manta da martabar Takawa, ku kula ku kame kanku kada ku jawo mana abun da zai halaka yankin ga gaba d'aya’’

Ta na gama Magana ta juya abun ta ta fice, ta bar Inna Salti tare da Jakadiya cikin al’ajabi. Gimbiya Kamariyya gani ta ke sam Hajja Kilishi ba ta damu ba saboda ita dama ba ta ta6a haihuwa ba shi ya sa sam ba ta damu da lamarinsu ba. Ita kuwa Gimbiya Binta abinda ya tsaya mata a rai bai wuce na ta na murnar raba Bintu da masoyin a Aisar, sai gashi ta zama matar wanda har ta gama rayuwar ta a doran k’asa ba za ta sami kamar shi ba, abun takaici ta yiwa yar uwarta asarar masoyi, duk akan wanda sam be ma san ta nayi [truncated by WhatsApp]
®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


2⃣

Daga cikin masallacin Sa’ayrasa, ko da bawa ya tsinci kansa gaban Aisar, hannunsa damke cikin na sa yayinda yake jero masa tambayar da shi kansa bai ta6a jin ko da makamancin sunan ba a matsayinsa na bawan barga da kwananan ya dawo cikin sawun bayin da ke kula da lambu. Zufa ne ya shiga keto masa, cikin kame-kame da in’ina ya ce

‘’Eye? Na’am lillahi warasulihi wanga zoben tsintarsa na ka yi, idan kuwa na yi karya aratta kashe ni….’’

Maimaikon Aisar ya saki bawa sai dad’a damke hannu bawa yayi. Cikin neman d’auki bawa ya kai dubansa ga sauran yan tawagar na shugaban k’asa ya na mai neman d’oki. Hakan yasa Junaidu tausaya ma bawan duk da ko shakka babu ya san zoben hannun bawa mallakin d’an uwansa ne. Kana ya na mai shiga tsakanin bawa da Aisar ta hanyar ciro hannun Aisar daga cikin na bawa yayinda yayiwa bawa nuni da ya ciro zoben, nan da nan bawa ya ciro zoben, ya mik'awa Junaidu kai durkushe ya na mai fad’in

‘’Tuba na ke, aradun Allah tsinta na kai, ku min rai……’’

Nan bawa ya fashe da kuka, wanda hakan ba k’aramin dad’a kular da Aisar ya yi ba, ji yake kamar ya shek’eshi har sai ya matso gaskiya daga bakin bawan.

‘’Ka ga ba kuka za ka yi ba, babu abun da zai ma muddin ka fad’a masa gaskiya, shin in aka sami wanga zoben?’’

Cewar Junaidu ya na mai kok’arin saka idanunsa cikin na Bawa don gano inda bawa ya dosa. Shi kuwa bawa ya gama rikicewa sai rantse rantse kawai yake, fad’i yake

‘’Tsinta na ka yi, kwankwasi tsinta na ka yi a lambu, aradu tsinta na ka yi.’’

Jin an furta
‘’Ko shakka babu gaskiya ya ka fad’i, don na shedi wanga bawa mai gaskiya ne.’’

Gaba d’aya hankalinsu ya koma ga mai maganar. Sanye ya yake cikin bakar jamfa wanda aka masa ado da bakin zare, idan ka d’auke rawaninsa da yake fari komai na jikinsa bak'i ya sanya, kai kace wani taron bakin ciki ya halarta, ko da shike a nasa 6angaran hakan ta ke. Kallo d’aya Aisar ya masa ya d’auke kai ya na fad’in

'’A matsayinka na wa za mu k’ar6i shedanka?’’

‘’A matsayinsa na Yarima Nuhun Sa’ayrsa ranka shi dad’e.’’

Fad’in bawan da ke tafe da Yarima Nuhu kenan, ganin idan ba a yi dagaske ba yanda ran Yarima Nuhu ya ke a dak’ule komai mai afkuwa ne. Jin haka Junaidu ya bawa Yarima Nuhu hannu suka gaisa haka sauran yan tawagar amma ban da Aisar wanda idan ransa yayi dubu ya 6aci, don haka a kusa ya ke. Sanin hakan ne ya sa Junaidu yin saurin yiwa Yarima Nuhu bayani, ya na mai nuna ma sa zoben. Ganin zoben da kuma jin wanda Aisar ya ke tambaya Yerima Nuhu ya san ko shakka babu Bintunsa ta arziki a ke nema, zoben nan shine zoben da ya kar6a daga hannunta ya wulgar. Wato wannan shi ne Aisar d’in da yake soyayya da Bintunsa….

Bawan nan dai da ke tafe da Yarima Nuhu ne cike da ladabi ya furta

‘’A hakik’anin gaskiya wanga bawa ada bawan barga ne, be dad’e da dawowa sahun bayinmu masu kula da lambu ba, saboda haka ina mai tabbatar maka ba zai san wagga d’iyar bayi da ku ke magana akai ba, dan yanda alama ya nuna ko shakka babu ta na daga cikin bayin cikin babban gida tun da har aka iya tsintar zoben hannunta cikin lambu, haka nima da na ke bawan kofar gabas, ba mai yiyuwa ba ne na santa, domin kuwa ba mu da wata alak’a da zai had’amu da bayin cikin babban gida’’

‘’Shin ina za mu sami wagga d’iya?’’

Aisar ya tambaya ya na mai fatan samin mafita daga bakin bawa. Nan take bawa ya masa alk’awarin tayashi cigiyar Bintu nan ba da dad’ewa ba, sannan su ka sallami wannan bawa da zoben Bintu ke gareshi. Yarima Nuhu ya shaida mu su abinda ya kawo shi gare su, wato sheda ma su ana buk’atar su d’akin taro. Ya na gama shaida mu su yayi gaba dan kuwa yanzun da ya gane Aisar shi an samrayin da ya kwace zuciyar Bintu ya fi ma sa d’aci akan auren da aka d’aurawa Bintu a yau, dan wannan ya san ba mai d’orewa ba ne musammam idan aka yi la'akari da wanda aka d’aura mata.

Dakyar Junaidu ya lalla6i Aisar, sai da ya masa tuni da ba fa su kad’ai ba ne, akwai manya cikinsu, sun zo d’aurin aure ne bisa wakilcin shugaban k’asa ba wai hakan nan bak’akatan su ka zo ba, sannan ya samu ya d’an shawo kansa, ta hanyar masa alk’awarin bayan komai ya lafa Junaidu da kansa zai tsaya har sai sun samo Bintu kafin su juya gida, ko da kuwa hakan ya na nufin raba tafiya da tawagar ta su. Da wannan su ka yi tattaki zuwa d’akin taro ba tare da sun bari manya daga cikinsu sun fahimci abinda ke faruwa ba.


Yarima Barde kuwa da dabara Yarima Jafar da Khalil su ka ja shi mota, gaba d’aya ya zame mu su tamkar mutum mutumi, ya d’auke mu su wuta. Cikin mota sai da su ka d’au kusan rabin awa babu wanda ya iya furta komai.

Dogarin Masarautar Fabarusa ya zo ya buga musu kofa, nan ya zube ya na mai sheda mu su umarnin Sarki Abdulrahman na a ma su iso gareshi.

‘’Su na cikin masallacin ne?’’

Yarima Jafar ya tambaya, in da Dogari ya ba shi amsa da

‘’A'a, sun wuce ga d’akin taron masarauta tunda jimawa, Yarima kad’ai ake tsimayi ranka shi dad’e.’’

‘’Mu na nan tafe.’’

Cewar Khalil, yayinda Dogari ya tashi da sauri ya na fad’in

‘’A iso lafiya.’’

Yarima Jafar na duban Yarima Barde ya ce

‘’Ka bawa zuciyarka hakuri mu amsa kiran Mai Martaba’’

Ko kallonsa be yi ba bare ma ya nuna alamar ya san da shi ake, kamar an aje dutse. Ganin haka Khali ya ce da Yarima Jafar.

‘’Ka san halin Barde a sama ya ke, ina zaifi mu lalla6a mu je a dai ga fuskarshi, in ya so sai mu nemi izinin tafiya ta hanyar ba da uzirinmu ga Mai Martaba.’’


Da wannan shawara su ka fito daga motar, amma Yarima Barde fitowa ta ma sa wuya, sai da Yarima Jafar ya ma sa tuni akan wanda ya sa a yi kiransa sannan ya fito cike da k’asaita, dama shi idan ransa ya 6aci nan fa sarautar ta sa ke bunk’asa. Ko da dogarawan da ke tsimayinsu su ka ga fitowarsa tuni su ka rufa musu baya, zuwa d’akin taro, kai kace Sarki Abdulrahman na Fabarusa ne da kansa ke [truncated by WhatsApp]
®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪





GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


3⃣


Dakin taron ya cika fal da jama’a, tawagar Aisar da shigowar su ke nan, na su 6angaran na shugaban k’asa su ka zauna. Haka ma hakiman Sa’ayra da Fabarusa, Agadez, Diffa da sauran Hakiman yanki da sassa na jamhuriyar Nijar wajan su na musammam su ka zauna. Haka kuma yankin Sarakuna wanda Sarkin Sa’ayrasa mai gayya mai taro ya hakimce, kusa da shi kuma Sarkin Fabarusa ne zaune cikin aminci. Hakan ba k’aramin farantawa jama’a rai yayi ba, wai ashe dai akwai ranar k’arshen gaba tsakanin Sa’ayrasa da Fabarusa? Shin dama akwai rana irin ta yau da za a ga Sarakunan wanga yanki zaune cikin aminci?

Busa na alkgaita ke tashi daga waje, jama’ar Sa’ayrasa kwan su da kwarkwatar su sun yi dandazo cikin d’akin taro, murna gun su ba a cewa komai domin kuwa a yau yunwa zai kau a k’asar su. Ganin shigowar su Yarima Barde tuni dogarai su ka hau yiwa ango kirari. Shi kuwa Yarima Barde sam ba cikin hayyacin sa ya ke ba, amma in aka d’auke Yarima Jafar da Khalil wanda dama sun san halin da abokin na su ya ke ciki babu wanda zai kalle shi ya ce ya na cikin wani hali, sai dai ma ayi tsammanin tsabar sarauta da miskilanci ne yake d’ibar sa.

Sai kuma Mai martaba Sarki Abdulmalik na Fabarusa, wanda kallo d’aya ya yiwa d’an na sa Yarima Barde bayan ya kai gaisuwar sa ga Mai martaba Sarki Sule na Sa’ayrasa, ya gane halin da ya ke ciki, kasancewar wajan mahaifin na shi ya yo gadan kafiya, cijewa da kuma yin burus kamar be san abun da ke faruwa da shi ba, amma in aka tona cikin zuciyar su, Allah kad’ai ya san tafasar da ta ke. Murmushi Mahaifin na sa yayi, cikin ran sa kuwa yacewa ya yi



"d’an mu Abubakar, alkhairi ne mu ka kulla ma ka ba sharri ba, nan gaba za ka gode ma na kwaran gwaske’’

Ganin Yarima Barde durk'ushe gaban Sarki Sule, haka ma abokan na sa biyu, hannun su na dama dunkule suna mai jinjina ga Sarki Sule, fadawan Sa'ayrasa su ka amsa ma su da

"Jinjine dama lafiya alher, gaishe ka Yarima Badde, an gaishe ku samari"



Sarkin Sa’ayrasa kuwa cikin nuna ya amsa gaisuwar ta su shi ma ya dan daga na shi hannun daman a dunk'ule. Yarima Barde ya shiga ran sa saboda kamala da kwarji na sa, ji ya ke ina ma ina ma, ina sirikin na sa ne na gaske, da ya san haka Sarkin Fabarusa zai aikata, da ya bayar da d’iyar sa ko da kuwa ba a san ran ta ba ne.


Ko da Yarima Barde ya had’a ido da Mahaifin na sa, sai ya yi saurin saukar da na sa idanun. Duk wannan
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

1 Comments On BINTU DIYAR BAYI Part 2
avatar
aminu-1-2

2 months ago

Reply

Thank you Please cigaba

Please Login or Register in order to submit comment