Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ο»ΏCompiled Umar Dalha Funtua.


πŸ’‘ *AUREN FARI*πŸ’‘


0⃣0⃣1⃣


*NA SADAUKAR DA LABARIN GA AUNTY RABI TAH ( HAJIA RABI BADAWI MAMAN IBRAHIM )*


Sauri takeyi kamar zata tashi sama, hannun ta rike da kwanon miyar manja, tun dazun aka aketa asibiti kai abinci amma don shiriri ta miyar ta baro gida shine ta dawo dauka.
Fakam fakam fakam tafiya takeyi ba ko jinkirtawa saboda tsoron kada Yaya Abba ya dawo masallaci a fada mishi yau kuma ga abinda tayi. Ji kakeyi rikichaaaa,!! Karam karam....... Ta antaya jikin mai tahowa da miyar da ita duk suka afka mishi yayi baya da karfi tare da riketa gamm bayansa ya bigi bango da karfi miyar ta karasa wanke mishi gaban farar gizna din sa, ya runtse ido da karfi lokacin da yajin miyar ya watsa mishi a ido yaji wani irin azaba ya ingije ta silbin miyar ya kwashe ta ta fadi duk ta nade miyar a hijabinta.
Ta mike a harzuke malam wannan wane irin wulakanci ne baka gani zaka jefani cikin miya in bata sabuwar hijab dita ta islamiya? Bayan asarar da ka janyo mun kai baka iya tafiya kana duban gaban ka?
Bala'i take zazzagawa yana kokarin goge yajin da ke idon sa. Sam bata lura da mutanen dake bin bayan sa ba, sai da wani ya finciko ta karfi zai kwada mata mari yayi saurin daga mishi hannu alamar ya kyaleta. Ta ja baya tare da rike kugu iyyyeee cewa zakayi tafe kake da masu tare ma fada to wallahi yau sai kun biyani miyata da hijabi na..... Sai lokacin ne ya kalleta idanun sa jawur ga bacin rai ga radadin yaji ya da ka mata tsawa ke gidan ku ba a koya miki tarbiyya ba? Wannan tsummar hijabin da banzar miyar manjar ki kike wa mutane rashin kunya akai? Kin San darajar kayan da kika bata? Ya zaro ido ya na nuna jikinsa.
Kai ka sani ni kasan miyar nawa aka kashe akayi ta? Ko kuwa kasan kudin wannan hijabin.....shut up!!! Ya daka mata tsawa tare da damko ta. Lokacin ne hankalin mutane ya dawo kan su. Wani yayi saurin dafa kafadar sa yallabai ba girman ka bane don Allah ka kar ka biye mata.
Ya hakade ta ya gitta zai wuce sai ta chafko hannun sa da karfi kamar wani zaki ya dubeta da karfi ya kalli siririn hannun ta sannan ya kalleta ita din dukan ta zai iya hadiyewa.
Wallahi duk mazuran ka sai ka biyani zaka bar wurin nan yama rasa me zai mata ya chafki hannun ya kudundune ta ya jefar suka wuce yabarta kwance tana ihu duk ta tara mutane kanta asibitin.
Abba da ya fito masallaci ya hango mutane taruru ya tukaro wurin yaga lafiya sai kawai yaga *umaimah* wani takaici ya turnuke shi ya figeta da karfi sukayi dakin jinyar, tunda tagan shi jikin ta ya fara kyarma. Suna shiga ya fara wanka mata mari biyu sannan ya tambayi ba asi, tana gama fada mishi kuwa yasa mata charger ya bata kashi sai da goggo ta karbeta.
Abincin sai dai aka siyo mai da yaji.
Umaimah marainiya ce, gaba da baya tana hannun wan babanta gidan banda gallaza mata babu abinda akeyi ko karatu sun hana a sanyata da tsiya sun kangarar da ita. Matar marikin nata ce aka kwantar duk da nisan da ke tsakanin su da asibitin kullum itace ke kai abincin safe, rana da kuma dare.
Kamar mahaukaciya haka ta fito kacha kacha ta nufi gida tana takaicin wulakancewar hijabin islamiyar data samu da kyar aka yi mata. Haka ta koma gida ta shiga wanke kayan da manjan ya kasa fita abinda ya kara harzukata tana addu'ar Allah ya kara hada ta wannan dan rainin wayon.
Sati daya, sati biyu....har an share kusan sati biyar basu kara haduwa ba gashi an sallamo goggo sai ta fita batun sa.
Umaima bata da kiwa ko Kadan shi yasa take cin gajiyar mutane da yawa cikin unguwar ana yawan kiranta gidaje mai shara, wanke wanke dan wankin yara haka dai idan ta gama abinci, sabulai mai da tsumma. Gidan su Sam babu Wanda ya damu domin sun dauki hakan kaskanci da bayar dakai wani lokacin ma sai suyi ta mata dariya tare da habaici. Ita kuwa tafi jin dadin bautar da takeyi wa mutanen gari suna godewa ba nan da kullum wulakncin safe da rana daban ba.
Duk satin nan bata zama gida tana gidan Alhaji yakuba tana taya su aikin biki, musamman gyaran daki domin sun yarda da ita matuka.Har yau ransa a 6ace yake, yarinya karama talaka kuchaka ta dizgashi, zuwansa asibitin biyu bai ganta ba inama lokacin ya kakkaryata lallai da ya huce bai zauna cikin bacin rai irin haka ba, ya ringa hasko ta cikin kuchakan kayanta da shegen yadin da take ikirari da sabuwar hijabi Wanda ko kyallen goge takalman sa yafishi daraja.
Ya buga tsaki ina jiye wayarinyar nan haduwar mu nan gaba....... Au wai baka shirya ba? Don Allah malam hanzarta kowa ya hallara kai kadai muke jira.
Ya kara hade rai ya mike okay ina zuwa.
Yauma cikin rantsattsiyar gizna yake fara tasha aiki na alfarma tafe yake yana kasaita ran nan nasa a 6ace. Yanda yake saukowa a benen yasa abokan duk bushewa da dariya baibi ta Kansu ba kawai yayi gaba abinsa. Mustapha ya yi nuni da baki ji yanda yake hura hanci kamar shine angon duk suka kara kwashewa da dariya.
Hajia ta kira umaima lokacin da ake ta faman tafiya party tace ke bazaki je bane? Murmushi tayi ta ce eh hajia. Dalili? Maza zo nan ta kama hannun ta tayi ciki da ita wata durowa ta bude kinga duk wadannan kayan Asma'u cewa tayi a bayar don haka ki zabi Wanda zaki zaka yanzu kije ayi dake idan kin dawo ko zuwa gobe sai ki zo ki kwashe sauran don ke na ajiye wa....ta zaro ido ni hajia.
Eh ke fa..
Maza shirya kada motocin su kare, wani paper lace ne milk dinkin riga da skirt ta dauka. Har zata fita taga hajiyar ta shigo da sauri ta miko mata takalma ungo wurin amarya na roko miki wannan kuma gyale ne sanya maza ki wuce.
Ko hoda bata shafa ba.
Tana zuwa ta fada mota. Ko da a ka sauke su. Fiddausi kanwar amarya na ganin ta tace yauwa umaima zo Ku shiga da kayan nan. Ta ce to ta shiga aiki. Dai dai lokacin da sukayi tsaya da mota kamar ance ya daga kai kawai ya hango ta rungume da lemuka.
Da sauri ya fito sai kuma ya yi turus daya tuna inda yazo.
Muje ko?
Ya rungume hannu a kirji tare da jingina da mota ya ce kuje ina zuwa ...duk suka kalleshi sai kawai yayi sauri ya fiddo waya yasa a kunne hakan yasa suka fahimci waya zaiyi. Suna wucewa ya mayar da ita aljihu, ta fito tana ta faman kakkabe kakkaben kaya yayi murmushi watau yau bata son abinda ka taba kayan jikin ta.
Sam bata lura dashi ba ta zo zata wuce sai kawai taji an fizgeta anyi bayan motoci, ta dago da karfi sai kawai ta ganshi. Ta fizge hannun ta tare da ingijeshi kana hauka ne zaka kama ni? Zai yi magana ta juya abinta kayan data fasa dauka kenan ta shiga ciki duk an zazzauna ta hango kujera can tsakiya ta isa ta janyo zata zauna ashe biye yake da ita kawai ya harbar da kujerar ji kakeyi *timmm* ya wuce abinsa duk aka juyo hankalin kowa ya dawo kanta ta wunkura da karfi zata isa gunsa fiddausi ta gani gaban ta. Sannu umaima ke nake nema zo muje ki taya my serving wani takaici ya turnuke ta ta bishi da kallo dai dai lokacin da ya hau gun anguna ya zauna ya juyo yana hararar ta.
Kunya duk ta baibaiye ta. Shine ya bude tΓ ro da addu'a ya bada tarihin ango don haka bata nan suna can suna shirya abinci.
Fiddausi tace kamata yayi mu fara kaiwa haka .
Umaimah tayi karaf Anty fiddausi kawo in faro daga sama wurin angwaye.
Yawwa Allah ya yi miki albarka umaimah dama kowa baison zuwa saman cen, ta dauki ture ta fara shiryawa. Zuwa na uku da zatayi ta debi cocktail juice da farfesun kayan ciki ta tafi tana isa kamar zata ajiye bisa yanda ta faro daga farko kawai sai ta antaya mishi duka ajiki har turen jikake rikichaaaa ...... Duk Wanda ke high table din tsaye ya mike hankali tashe........


*MAMAN ABDALLAH* CEπŸ˜ƒ
*KAUNA TA GA YABA KYAUTA MEMBERS*😘😘😘😘😘😘😘😘
[1/12, 9:11 AM] β€ͺ+234 809 454 8809‬: πŸ’‘ *AUREN FARI* πŸ’‘


0⃣0⃣2⃣

Kamar da gaske ta dan razana laaaaa ban gani ba taja baya zata gudu Ya chafko hannun ta, Asma'u ta daka mata tsawa haba umaimah baki gani ne? Tayi ta kicin kicin ta kwace hannunta amma ya ruke su tamau, ba komi ya fada yasa dayan hannun sa ya fizgen gyalen ta ya fara kwashe plates din dake bisa jikin sa sannan ya ya ci gaba da gogewa, duk illahirin jikin sa ya baci, yarinyar nan na janyo mun asara amma zan maganin ta a yau.
Biki ya tsaya chak! Yaga kowa ya mai da hankalin kansa abinda ya tsana kenan ransa ya kara baci. Ki kwashe kwanukan kikayi tsaye, ta kalli kanta ta yaya zata ratsa dubun mutane ba gyale? Wannan wulakanci dame ya yi kama? Ga kayan duk sun matse ta....ta daka mata tsawa ko ba kyaji? Ta duka tana kwashe kayan ya yi fit! Da kallabin ta kananan kalaban da ke kanta suka watso mata ko ina ta mike da sauri zata zazzaga mishi bala'i ya ce yafa gyalen don naga baya daukar miyar sosai gashi ba towel da zan goge kayan naki sun kama da bargo.
Ji tayi an fizgeta da karfi, tana juyawa taga fiddausi, haba umaimah kinsan waye kika batawa kaya? Zo muje ki karbo towel mota kikai mishi. Figai figai babu gyale ko kallabi nake binta zarai zarai idanuna sun kawo wani ruwan bala'i.
Anyi anyi ya tashi yaje ya sauyo kaya yakiya wai zai jira a gama. Ransa kuna kawai yakeyi amma ya kasa nuna wa duk da fuskar tasa kullum tamau.
Don Allah Anty fiddausi ko kallabinki ne bani in yafa kada in kuma ratsa mutane haka. Har zata yi musu sai kuma ta kwanto ta bata kowa head ya saka amma wani ikon Allah ita fiddausi ba ta sanya ba. Tun kafin ta hau saman ta hango kallabin da gyalen a kasan kafar sa yana goge sauran miyan da suka zuba. Tuni an ci gaba da sha'anin biki amma ganin ta hawo saman sai hankalin amarya ya dawo kanta, ta mika mishi towel din tare da banka mishi harara.
Baki iya goge masa wai yau meke damunki *UMAIMAH*?
Ya maimaita sunan cikin takaici a zuciyar sa *umaimah* ta duka ta fara gogewa shi kuma ya kara shan mur, dataga hankalin asma'un ya koma can sai ta fara dangwalo wata miyar dake ajiye ta na kara yaba mishi a inda bai samu miyar ba. Hada hannu. Ya kura mata ido yana wani irin mamaki wai yarinyar nan tasan waye shi? Yaci gaba da kallon ikon Allah tasha mur sai kwaso miya takeyi tana kwaba mishi sai tasanya towel din ta dalaye. Tana gamawa zata mike ya dankwafar da ita ta koma da karfi ta zukunne, ya kalli abokin sa yace idan bazaka sha wannan naman ba kaban, ya miko mishi bai ko kalleshi ba yaci gaba da kallon yan rawa, sai kokarin dagowa takeyi shi kuma ya danne kafadarta da hannu, ya dan waiga yaga kowa hankalin sa yana gun yan rawa ya sa hannu ya bude gaban rigar ta ya kwarara mata duka miyar cikin breast ware sannan ya sake ta tafadi ta baya dabas! Ya kawar da kai kamar baisan komai ba. Na kusa dashi ya kalleta easy! Tashi mana.
Ta mike a wahale miya na zurarowa cikin rigarta duk ta bata ta nama cike cikin brezia.
Kwalla suka shatato mata wannan wulakanci da me yayi kama? Ganin tana kuka yasa yaji wani sanyi a ransa hakika yanzu ya fahimci 6acin ranta. Ta fita farfajiyar tana faman zubda hawaye fiddausi ta tareta tare da daka tsawa haba umaima ji yanda kika batan kallabi, ta dubi kallabin Wanda ya zamo tamkar makwararin juyewar miyar. Zatayi magana ta fizge abinta tayi gaba.
Ta koma bayan hall din ta duke tana kuka, kukan takaici ba gyale ba kallabi. Tayi mai isarta, har duhu ya fara nan da nan taga mutane na fitowa alamar an gama ta kara lafewa jikin bango.
*zan jira a gama fitowa in koma in dauko gyalena da kallabi cikin miya in yafa hakanan amma bana iya ratsa mutanen can haka* ta fada cikin muryar kuka.
Wallahi ko waye ubansa a garin nan sai na rama wulakanci na ta buga tsoki.
Acikin hall abokan gewaye dashi suna faman ya taso amma ya kasa ko motsi. Baya iya ratsa dubun mutanen nan haka yanda aka sanshi a gari irin daraja da kimar sa.
Ya kara hade rai na fada muku kuje zan taho nayi waya za a kawo mun mota kuyi amfani da wacce mukazo ciki key na hannun.... Gashi nan daya ya fada. Ya tabe baki okay you can go zan taho, zasu kuma magana ya ce please Ku kyaleni wallahi kuna dada sani damuwa.
Dole suka fita, a rude amarya da ango suka iso zasuyi magana kenan ya yi murmushi karku damu bazan iya fita haka ba idan kowa ya gama tafiya zanje ya kalli Asma'u karki damu da abinda kanwar ki tayi mun......... Ba kanwata bace yallabai diyar makwabta ce amma tana shigowa gidan mu kama aiki........'yar aiki? Ya maimaita a rai.
......what ever ba komi kuje nayi waya za a zo a daukeni.
San in ko waye yasa sukayi gaba.
Umaimah kuwa lekowar da zatayi sai taga motar karshe ta fice yayin da wata ke shigowa ta zuro a guje sai taga sojoji biyu sun fito cikin wacce ta shigo din, tayi cikin hall din a rude, dai dai zai mike ya hangota ranshi ya bashi lallai gyalen ta biyo, ya kwashesu duk ya cusa aljihu duk da suke sharkaf da miya. Ganin shi bai wani daga mata hankalin ba domin ta gama rikicewa da dare gashi kowa ya watse, duddube duddube takeyi tana zare idanu shi kuwa yayi tsaye yaji ko zata tanka mishi sai kawai tayi hanyar fita ya zabura ya damko ta, kamar tana jira ta harzuka wai kai *maye* ne? To kurwata tafi karfin ka, meye hadina dakai yauni naga bala'i.... Ina kika ga bala'i wallahi yau sai nayi maganin ki ya figeta sukayi waje yana dube dube yana faman zare ido, kawai sai taga jelar gyalen a aljihunsa. Ta kalleshi taga lallai ya fara rasa hankalinshi don fushi, to me zai Mani? Ganin sojojin nan na tunkaro su yasa ta gantsara mishi cizo a yatsa kamar zata cire ya fasa kara *kaiiiiii* yana sakin ta tayi wajen *gate* din a dari da sittin.
Daya daga cikin sojojin ya yunkura zai kamota yayi saurin tsayar dashi.
Allah ya taimaketa tana fita ta samu adaidaita da kamar bazai dauketa ba tace party tazo bata gari suka biyota.
A kofar gidansu ya ajiyeta, ta karbi dari gurin sham'unu mai manja ta bashi, ta shige gida ana babban falo ana kallo ta sadada taje ta sauyo kayan.
Washe gari wunin biki taki lekawa hajia tayi aiken duniya sai ma tabar gidan.
Karfe bakwai na safiyar walima hajiyar ta aiko kanwarta ba halin kara wata dabarar saboda ta ce kafarta kafar umaimah. Ko kalaci batayi ba.
Tana shiga tasanya ta gyaran daki tana fada kin San idan bake kika gyara man dakin nan ba bana jin dadi amma hiratan jiya kika ki lekowa to yau ai kyasha aiki ko fidda dattin tayil dinan kadai ya isheki.
Ga kayan ki can na kulle miki amma ina gyalena dana ara miki? Gabanta ya fadi tayi dan kasake kafin tace, yana gida zan wanke ne, to ba komi tayi waje.
Ta shiga gyaran dakin tayi mishi fes cikin yan mintoci saboda bata da nawa, anata shirin walima ta ce umaimah maza shirya ku tafi walima,
A'a yau bana jin dadin jikina hajia kuma idan na tafi wazai gyara baranda? Ki bari su tafi sai in karasa gyara miki gidan.
Allah yayi miki albarka ya zaba miki miji na gari, ta washe baki amin hajiyar mu. Tayi waje da wasu kwanuka ta ce ina zanje mu kara haduwa da mugun nan? Inba rigima irin tau ba inani ina haye ma irin su?
Su hudu suka shigo tana ta faman hada kayan wanke wanke, kafar dattijuwar ta murguda tayi kichaaaaa zata fadi umaimah ta saki kwano tayo kanta ta tare sai ta fada jikin umaimah amma duk da hakan kana jin karar da kafar tayi kat!
Subhanallahi sannu mamah ta fada yayin da dattijuwar tace washhh!
Sai kawai cikin Matan nan wata ta ingije umaimah move... Ta tallabo matar.
Cikin fushi umaimah ta kalleta ta ce *move*? To anki ayi move din ta hankade ta ta tallabo matar duk suka zaburo kan umaimah, kada wacce ta matso, matar ta fadi a hankali. Sorry mama suka fada suna ja baya,
Au da taron dangi zasuyi mun? Ashe kuna sonta zaku barta ta fadi? Data kai kasa ai da kun ce *move* da hujja aikin banza.
Ta juya sannu mamah ita kuwa sai bin umaimah take da kallo bayan *Umar* ashe akwai Wanda zai iya fada kan lafiyar ta haka?
Kukayi kototo ku kamota mukaita daki ta daka musu tsawa.
Qalu innalillahi hajiya bilkisu lafiya? Sai bayan da suka ajiye ta saman kujerar sannan ta ce wallahi turjewa nayi. Tana faman runtse ido saboda azaba.
Umaimah tayi saurin zuwa gidan su cikin kayanta ta dauko kwankwalaton Robb tana shigowa hajiya ta ce yanzu nake Neman ki jekira sadi a kira mai kamu ya duba kafar, ta ce to bari in shafa mata Robb na dauko gida tukun saboda zogi.
Bata jira sun kuma magana ba ta tallabo kafar tana shafa Robb din a hankali mamaki ya cika hajiya bilkisu kallonta kawai takeyi, ita kuwa umaimah tana son gyara kafar data dago sai taga ita take kallo, hajiya na ajiye plate din nama umaimar ta zabura kamar wani abu, suna duban wurin ta mayar da kafar kowa yaji ta ce kas!!! Tare da karar da hajiya bilkisu ta saki. Sama akayi da umaimah ita dai taga anyi hanyar waje da ita.....


❀ *Maman Abdallah*❀



😘😘😘😘😘😘😘😘
[1/12, 9:11 AM] β€ͺ+234 809 454 8809‬: πŸ’‘ *AUREN FARI*πŸ’‘

0⃣0⃣3⃣

Tsawa ta daka musu, ina zaku kaita? Ga kafar ta gyaru ta jujjuyata, suka dire ta, hajiya ta ce ikon Allah umaimah ikon Allah karambanin naki hada gyara rauni?
Ta dawo sannu mama haka akeyi idan anyi tirjiya baban mu yana gyarawa...... Na sani tabbas na san haka.
Ta dalla musu harara kuje waje Ku jira, tsiraran mutanen da ke dakin suka ci gaba da yi mata sannu, umaimah ta duka tana kara shafa mata Robb.
Na gode nagode sannu na gode, bakin ta ya kasa dainawa har sai da ta kalleta tana yar dariya haba ai kece da sannu.
Tabar dakin ta tafi tana gyara kitchen. Wannan yarinya da hankali take hajiya suwaiba wallahi na yaba da kulawar ta sosai.
Hmmm umaimah kenan yarinya ce mai himma wallahi. 'Ya ce ko jika?
Ko daya marainiya ce iyayen duk sun rassu, tana nan makwabcin mu dan uwan mahaifin ta ya dauko riko, shine take shigowa tana dan kama mana aiki. Bata da kiwa ko kadan yarinyar nada dadin zama ga kazar kazar.
Allah sarki. Ta ce
Tana can baya tana hado kwanukan wanke wanke idan an wanke tana kaiwa kitchen dattijuwar da hajiya suka isko ta.
Umaimah hajiya ta kwala mata kira
Da sauri takaraso tana murmushi.
Ganin su biyu sai ta ce Aaaaaa kafa ta taku, ta karasa maganar tana yar dariya duk suka bushe da dariya hajiya ta ce to uwar iyeshege keda baki bar kowa ba.
Tafiya zatayi tace a kira ki rike mata kaya zuwa mota.
Tayi hanzarin warware hijabin da tayi damara dashi tace au to tare da karbar kayan.
Har get hajiya ta raka ta suka fita tare suna magana,
Ina ne gidan naku?
Umaimah ta daga kai kin hango jarkokin manja gasu can.... Ta daga ido inda baranda take?
Kwarai nan ne gidan mu.
Allah sarki.
Yaushe zaki zo Mani ziyara?
Umaimah ta zaro ido a ina?
Sai tayi yar dariya a gidana mana nima ki gyare man daki ki saman dan tsintsiyar kamshi. Ta kwashe da dariya kai wannan hajiya ce ta fada miki ko?
Tayi murmushi ai naji dadin yanda kika nunan kulawa yanzu idan za a barki gobe kizo don Allah uwani?
Umaimah nake ba uwani ba. Na sani sunan mahaifiyata gareki. Ashe diyata na taimaka duk suka kwashe da dariya.
Dai dai sun kawo inda motar, mutanen ta sunyi cirko cirko, lokacin umaimah ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment