Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar Gidan tsohuwa_πŸ˜…)



Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)




*AM BACK AGAIN BY THE GRECE OF ALLAH*



_Alherin da ke ciki Allah yasadani dashi, shairin dake ciki Allah ya tsareni dashi_
_Muje zuwa masoya ana bugun tare🀝🏻_ *UMMU SAFWAN CE*






*1*









Cikin sand'a tashigo cikin zauren gidansu, tana wasar b'uya, ita da k'awayenta

Lab'ewa tayi tasha jinin jinkinta kamar wacce tayi k'arya, tana tafiya a hankali yanda baxaka iyajin sautin takun k'afartaba."

Gafda zata shiga cikin gidan ne
Saiji tayi taci karo da wani abun,a gabanta."
turus tayi,
Taja ta tsaya gefe d'aya tana turo baki kasan cewar zauren gidan duhu ke gareshi,

Ta d'auka *Kaka* ne, kaka Kwaishi da fitinar tsuha,
Tashiga gunguni tana magana k'asa k'asa, " kai wannan tsohun kacika rigima yazaka taka min k'afa, idan kuma akace da kai ka kusan mutuwa, ka d'ora hannu a kai kace kai ba yanzun zaka mutuba."

Shuru taji anyi Bataji antanka mata ba."

Dogon tsaki taja harda d'an murgud'a baki taci gaba da tafiya
zata shiga cikin gidan kenan taji ta kuma taka k'afar mutum a karo na biyu."

Jikinta ya soma rawa fitsari ya fara d'iga a wandonta, saka makon marin da taji an kwad'a mata a fuska."

Wata irin k'ara tasaki ta fad'i k'asa tana birgima, "Wayyo idona na shiga uku tsohuwa kizo ki ceceni."

Mahmud dake tsaye cike da takaicinta, yace "Ke wace irin yarinya ce,wadda bata kallon gabanta, tunda kika shigo soron gidan nan naketa k'ok'arin naga na kauce mki amma duk da hakan saida kika taka min k'afa."
Oh kin d'auka *kaka* ne da kike fad'awa magana yanda kikaga dama?"
to bashi bane ni kika tak'ewa k'afa, wawuya kawai marar hankali wadda bata kallon gabanta bare bayanta,
Ni maganin rashin kunyarki zanyi kafin na bar gidan nan."

Tsohuwa dake sallah,
Sallamewarta kenan taji sautin kukan Dije a zaure."

Da sauri ta mik'e tsaye tafito daga d'akin tana fad'in "deejama wani mugunne ya dakeki?"

Ai kuwa deejama najin muryar tsuhuwa ta kuma bud'e baki had'ida sanya hannu d'aya ta dafe b idonta d'aya, "wayyo idona nashiga uku tsuhuwa idona ya tsiyaye."

Mahmud tsaye yayi ya tsura mata ido yana kallon ikon Allah, k'azafi takeso tayi mashi yanaji yana gani."

Ta mik'e tsaye dafe da ido sai kuwa takeyi tana tsalle tana fad'uwa, sai da tazo dafdashi ta kuma taka masa k'afa da k'arfi
ta xuba a guje tanufi wurin tsohuwa dake tsaye a k'ofar d'aki tana ruwan masifa."

Tanufi wurin tsohuwa tana fad'in "wayyo idona tsohuwa ki taimakeni yaya muhmud ya tsiyayar min da ido d'aya."

"Tsohuwa tace "burinka ya cika mamuda ka tsiyaye mata ido d'aya saika zuba ruwa k'asa kasha,
Ni wlh bnsan irin k'iyayyar da kakeyiwa deejama ba,
kwata kwata baka k'aunar ka bud"e ido ka ganta tana walwala a gida ko a waje."

Tunda burinka ya cika ka makantar da ita, saikazo ka kwashe kayanka ka koma gidanku. Mungode da ziyarar Allah amfana."

Muhmud da zaifita, jin k'azafinda dijana tayi masa yasashi dawowa ya fasa fitar.

Yace "Allah tsohuwa ki daina biyewa wannan yarinya, kwata kwata batajin magana kuma batada kunya. Tun da nazo garin nan kullum sai ankawo maki k'arar dijama, amma kullum sai d'aure mata kikeyi bata laifi."

"Saboda kana jin zafinta shiyasa ka tsiyayar mata da ido d'aya?"
Tafad'i hakan had'ida kamo dijama dake gefenta tsaye kamar ta shige mata a ciki dafe da ido d'aya."

Ta janye hannun deejama daga kan idon nata tana fad'in naga idon naki dije, idan ta kama mutafi asibity sai na kira ubanshi duk inda yake yazo ya d'aukemu ya kaimu asibitin."

Ganin babu abunda idon nata yayi, tsohuwa ta kuma kallon muhmud dake tsaye gefe d'aya yana kallon ikon Allah.

"To burinka bai cikaba baka makantar da itaba."

tarik'a hannunta "mutafi deejamar tsohuwa kisha hura ki nemi wuri ki kwanta kirabu da wancan Azzalumin."

Kallon mahmud deejama tayi ta fakaici idon tsohuwa tayi masa gwalo had'ida murgud'a mashi baki."

Nuni yayi mata da hannu a lamar zanrik'eki."

Bai d'aga daga inda yakeba. Sai sallama yaji anayi,
wata mata ce tashigo da yaronta janye a hannunta wanda bai wuce shekara goma ba da bokitin markad'e a hannunta duk ya b'aci da k'asa alamar b'ari yayi."

Tana fad'in "ina tsohuwa take?"
Fito fito dan yau na rantse da Allah bazanyi asaraba. Kullum na aiki yarona wurin markad'e sai dijama ta tareshi a hanya tayi mashi dukan tsiya sannan daga k'arshe ta zubar min da markad'e to yau hak'urina ya k'are Dan bazanyi asaraba sai anbiyani ehe "

Mahmud yadubi matar yace "d'aga murya kwarai yanda zasujiki suna ciki yanzun suka shiga."

Tsohuwa tafito deejama ta biyo bayanta,
Tsohuwa tace Abu mai waina mekike fad'i?"
Me kuma deejama tayi?"

Abu mai waina tarik'e k'ugu, ta maimaita mata b'arnar da deejama tayi mata."

Tsuhuwa itama ta hau masifa tana fad'in Sam ba Deejama ta aikata hakan ba."

"Na lura a garin nan babu wanda aka sanyawa ido irin deejama, yarinyar da na aika tasayomin sikari. Tayaya zatabi ta k'ofar gidanku?"

to Wani irin sokon yaro ne gareki da har zai saki baki,
Deejama tayi masa duka kuma har ta zubar mashi da markad'e." dan Allah Abu mai waina kifita a gidan nan tun cikin muna mu biyu, dan babu wani ranko da zan maki ehe."

Ai kuwa Abu mai waina tashiga ruwan bala'i,
"Ayi maka asara kuma baxa'a baka hak'uriba, to yau duk yanda za'ayi sai dai ayi amma sai anbiyani markad'ena."

Mahmud da yaji fad'an ba mai k'arewa bane, ransa ya b'aci yaciro d'ari biyar ya mik'awa Abu mai waina had'ida bata hak'uri."

Baki ta bud'e ta fara dariya takarb'i kud'in tana godiya,
Sai ta koma yin magana cikin lalama da taushin murya, "aisu yaran ne basajin magana, amma ya kamata a k'ara jawa deejama kunne saboda kaf a cikin k'auyen nan ta hana yara walwala idan ta fito kowa tsoronta yakeji."
Babu Wanda ya kuma tanka mata, sai Deejama da tace "kedai ki wuce kiba mutane wuri, tunda anbiyaki kud'in markad'anki, karki damemu da suruto."

Ta dubi Sale yaron Abu mai waina, ta harareshi tace "kai kuma sale duk na rik'aka saina karye maka k'afa d'aya."

Abu mai waina najin hakan kuma tasan halin dijama zata iya, zata fara wata sabuwar masifar mahmud ya bata hak'uri. SnnTa tafi,

a hasale yanufi wurin dijama zai daketa tsohuwa ta turata d'aki tana fad'in wlh karka daketa. Meye ruwanka, to muddun ka daketa saina sab'a maka a gidan nan."

Mahmud ya dawo baya, yana hararar dijama yana fad'in zan rik'akine saina d'ebi d'arina biyar a jikinki. Dan bazan biya mki kud'i a banzaba."

Yanajin tsohuwa ta fara ruwan masifa ya fito ya baro masu gidan."

Bayan sallar isha'i kamar yanda suka saba kowace yarinya zataci ado tanufi dandali,
Haka dijama tayi kwalliya tasanya atamfa riga daban Zane da d'ankwali daban, tazane fuskarta da kwalliya kasan cewar dijama kyakkyawace kuma bafulatana ce, domin ba sosai hausarta ke fitowaba."
An d'aure k'ugu da gyale."

Da gudu tafito gidansu tana rera wak'a, k'awayenta najin sautin wak'arta kowa ya fito daga gidansu suka tareta
Suna fad'in ga 'yar gidan tsohuwa nan ta fito, aikuwa da murna suka tareta suka jera suka nufi dandali."

Dijama ce gaba k'awayenta suwaiba da lantana da ladidi, da luba a bayanta suntake mata baya domin itace boos duk Wanda yaja magana ita ke tare mashi."

Gefe d'aya suka samu suka zauna a kusa da wani mai kifi,
Mai kifin yana ganinsu , Sai da ya kuma dallara fitila ya duba da kyau ya tabbatar da sune,
Ya sauke wani numfashi a ransa yace "Ashe yau zanyi kwantai bazan samu cinikiba. Saboda wad'an nan hatsibiban yaran."

'Dijama ta turo ido had'ida turo baki cikin tsiwa ta dubi mai kifi tace "lafiya meya faru kake haske mana ido da fitila?"

Mai kifi da saida gabanshi ya fad'i dajin maganar dijama, dan ba k'aramin aikinta bane ta bad'e basa kifi da k'asa taja masa asara kuma ba yanda zaiyi. Ya k'ak'aro dariyar dole yace "yi hak'uri 'yar gidan tsohuwa ai bansan kece ba."

Ya d'auko leda yasanya mata kifi. Yace 'yar gidan tsohuwa ga wannan kici,
Ta dubeshi ta ya mutse fuska tace "ya'u kabar kifinka kawai yau bana ra'ayin cin kifin."

Abokananta suna su, amma saboda tsoron da suke mata yasa ko wacce ta had'iya yawunta."

Ya'u mai kifi yana ganin haka yatashi tsam ya d'auki tiren kifinshi ya bar wurin ya canza wurin zama yayi nesa da su sosai."

Dijama bata lura dashiba, hankalinta yatafi wurin kallon wani saurayi da budurwa dasuke hira da alama saurayin bak'one zuwa yayi."

Dariya tayi ta girgiza kai irin yanda ta hangosu saurayin sai wani kakkab'ar jiki yakeyi da hankicif, yana wani ya mutsa fuska wai shi d'an gaye."

Gaba d'aya ta nunawa k'awayenta shi, suka tuntsire da dariya,
Dijama tace "yawwa lantana jeki d'aukomin macijin robar nan naki Wanda yayanki yaje binni ya sawo maki."

Lantana ta zuba da gudu taje gida ta d'auko ta kawowa dijama."

Tace yawwa kuzo kuji abunda zamuyiwa wancan gayen."

Suka had'a kai wuri d'aya abu na basu umurni suna girgiza kai alamar sun fahimta
[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_πŸ˜…)



Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)






*2*







Dijama ta nuna masu inda zasuje su lab'e,
Sai data tabbatar da sun b'oye, sannan
A hankali ta lallab'a tanufi wurin saurayin da budurwar wad'anda suka samu wuri a gefen dakali suka zauna, suna hira suna dariya,

basu lura da itaba sunyi nisa wurin hirarsu ta masoya, ta lallab'a taje bayansu ta d'ora masu macijin robar Wanda aka sanyawa batur sai wutsil wutsil yakeyi kamar macijin gaske,
ta lallab'o ta baro wurin tayo wurin k'awayenta su lantana da suke lab'e wuri d'aya suna lekenta suna dariya."

Itama b'oyewar tayi tashiga lek'awa domin ganin yanda d'an gaye zaiyi."

Ganin basu lura da macijin a bayansu ba,
yasata fitowa tanufi wurinsu tayi kamar wucewa zatayi, sai da tazo daf dasu ta kurma ihu tana nuna bayansu "wayyo Allah maciji a bayanku."

Yahaya gaye yana waigawa yaci karo da maciji a bayanshi,
ai baisan lokacin da ya b'urka tusaba ya kurma ihu ya zubar da talkamin k'afarshi Ya zuba a guje yana fad'in wayyo Allah maciji jama'a Ku kawo min agaji."

Ladiyo dayake tasan halin dijama bataji tsoroba illah ta mik'e a hasale tanufesu,
Suna ganinta tayo kansu suka zuba a guje suna dariya harda rik'e ciki, suna fad'in wasa mukeyi
macijin roba ne."

Yahaya gaye da saida yayi nisa sosai da wurin sannan ya tsaya yana zarar ido yana maida numfashi sama sama, a can yajiyo sautin dariyarsu dijama suna fad'in wasa mukeyi macijin roba ne."
A hasale shima ya nufesu, cike dajin haushin muzantashi da sukayi a gaban budurwanshi, bugu da k'ari ga gudun da yayi harda tusa yasaki."

Aikuwa ya tunkarosu gadan gadan, dijama na ganin haka ta d'aga murya da k'arfi tace "kowa yayi ta kansa."
Suka zuba da gudu ko wannensu yanemi hanyar tsira."

Juyawar da zatayi ta gudu, taji tayi karo da mutum a dai dai lokacin da yahaya gaye yanufota, aikuwa ta mak'alk'ale mutumin wanda batasan kowaye shiba,
D'aga idon da zatayi sai taga Ashe yaya Mahmud ne."

Mari ya kwad'a mata, ya rik'a hannunta ya mik'awa yahaya gaye yace "gata kaci ubanta,
Domin ko mu kanmu mungaji da ita, mungaji da hali irin nata, kayi mata dukan tsiya ninace."

Yahaya gaye babu abunda yakeyi sai ruwan masifa,
Ladiyo ta matso kusa da ita ta xungure mata kai tace "kinci darajar yayanki da yau sai na lahira yafiki jin dad'i,
Dijama da sai zarar ido takeyi tana kallon fuskar yahaya gaye tanaso tayi dariya amma ba hali."

Mahmud yaja hannunta yana rankwashinta a kai yana mata fad'a, sai da sukazo k'ofar gida ta kwace hannunta da k'arfi tashige gida tana fad'in Allah ya isa mugu kawai."

Da Sauri yabita cikin gidan yana Neman ya rik'ata, aikuwa ta fad'a d'akin tsohuwa da gudu,
tsohuwa na ganinta tayi saurin tashi zaune tace "babu Wanda zaibiyoki sai mamuda domin nasan shi kad'ai ke k'ok'arin yaganki bakya motsi, hakan yayi dai dai da zuwanshi k'ofar d'akin yana huci, tsohuwa tace "karka kuskura ka shigo min d'aki
kaji na fad'a maka."

Yaja yayi tsaye a k'ofar d'aki yana huci,
Saida dijama ta kalli fuskarshi ta tuntsire da dariya harda rik'e ciki, dariya takeyi sosai, sai ta kuma kallonshi ta kuma tuntsirewa da dariya,
Ya kuma hasala, tana ganin ya hasala sosai tace "yaya kasan ko menakeyiwa dariya?"

Ya wurga mata harara had'ida girgiza kai."

Tace "ba komai yake bani dariya ba sai yahaya gaye, yanda yasaki tusa ya zuba a guje."

Shima kanshi gudun da yaga yahaya gaye nayi sai da yabashi dariya kasan Cewar duk abunda sukeyi a kan idonshi,
Dariya taso sub'uce mashi yayi saurin barin wurin, yanufi d'akinshi, yana fad'in idan kingama dariyar saiki kawo min abincina ina jiranki."

Yitayi kamar bata jishiba, tashiga bawa tsohuwa labari suna dariya."

Tsohuwa tace "tashi kije ki d'auki abincin yayanki ki kaimasa yana can yana jiranki."

Ta turo baki tace "ni tsohuwa bazanjeba saboda duka na zaiyi."

Tsohuwa tace "baxai dokeki ba aina riga nayi mashi magana, nace karya dakeki kuma kinsan mamuda yanada jin maganar mutane, Wurin nan yana burgeni."

Sannan ta tashi tana turo bki tanufi kicin ta d'auki abincin shi tanufi d'akinshi,
Kai tsaye tashiga d'akin batare da tayi sallama ba,
ta tarar dashi zaune a kan katifarshi dagashi sai best da gajeran wando, jikinshi ko ta ina gashi gashine yayi kwance akan kyakkyawar fatar jikinkinshi fara fes.

hankalinta ya tashi jikinta yasoma rawa aduniya bata tab'a ganin namiji a hakanba,
Tsawa ya doka mata wadda tasanyata tadawo natsuwarta yace "ubnwaye yabaki izinin kishigo min d'aki batare da kinyi sallama ba?"
Maxa kikoma kiyi sallama sannan ki kuma shigowa."

Da Sauri ta juya ta koma jikinta na rawa."

Yana ganin fitarta yayi saurin mik'ewa tsaye ya d'auko jallabiyarshi ya sanya."

Sallama tayi sannan ya amsa mata had'ida bata umurnin shigowa, sannan ta shigo,

Kallon yabita dashi yana harararta domin cike yake da jin haushinta, yanuna mata wni tebur yace "wuce ki ajiye a can."
Kizo inaso zanyi magana dake, kuma kika kuskura kika gudu ko kika yimin ihu saina k'arye maki hannu d'aya idan na rik'aki."

Sum sum ta wuce ta ajiye harda wani sunkuyar dakai kamar ta Allah, tazo kusa dashi ta durk'usa had'ida sunkuyar da kanta k'asa."

Ya Matso daf da ita ya kama kunnenta ya murd'a sosai saida tasaki fitsari saboda azaba,
Yace "maimaita abunda kikace d'azun.
Ni kikeyiwa Allah ya isa baki yafeba?"

Rantse rantse tashigayi ita batayi Allah ya isaba"don Allah kayi hakuri karka ciremin kunne, banyi maka Allah ya isaba."

"Idan kika kuskura aka kuma sake kawo k'ararki a gidan nan saina farfasa maki baki kinyarda."
Tayi saurin d'aga kanta alamar "eh." Idanta na zubar da hawaye."

Ganin fitsarin dake d'iga a zanenta yasa yayi saurin sakinta yaja da baya da sauri ya d'auko bulala yanufota yace "koki goge fitsarin nan ko yanzun na lahira yafiki jin dad'i."

Da Sauri ta mik'e tsaye, saiga takarda ta fad'o a zanenta, ya doka mata tsawa yace "ke zonan takardar meye?"

zaro ido tayi waje takai durk'ushe tana matsar hawaye tana fad'in dan Allah yaya kayi hak"uri bazan sakeba."

Tsawa ya Doka mata yace "ba kuka nace kiyi ba tambayarki nayi."

Cikin rawar murya tace "Anty bushira ce antyn suwaiba k'awata tace nakawo maka."

Ya wurga mata harara yace "bud'e karanta abunda ke ciki,
Da sauri ta bud'e takardar tashiga karanta masa, jin kalaman soyayya ne alamar tana sonshi, yayi saurin doka mata tsawa yace "rufe min bakinki kiyi min shuru,
Bari nafaracin k'aniyarki ke 'yar aiken kamun naje ga Wanda ta aikoki."
Ke fitsararriya marar kunya ke ake aikowa da takarda kikawo min?"
Tashi ki kama kunnanki."

Tana hawaye tana fad'in "Dan Allah yaya kayi hak'uri bazan sakeba."

Yasin sai kin kama kunnenki, yayo kanta da bulala a hannunshi,
Tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye takama kunnenta sai kuka takeyi tana bashi hak'uri."

Abincinsa ya jawo ya fara ci, yana kammalawa ya haye katifarshi yajawo jarida ya Shiga karantawa, ganin ta wahala sosai ya dubeta yace "tashi kiwuce kiba mutane wuri."

Tayi kuka idanunta sunyi jajir har sunfara kumbura, ya dubeta yace "ko gobe idan wata ta kuma aikoki da takarda da sunan kikawo min kika karb'a abunda zanyi mki sai yafi wannan, sannan idan kika kuma yimun Allah ya isa saina karye mki k'afa d'aya da hannu d'aya."
Wuce kibani wuri kinyi tsaye kin kafeni da ido kina kallona saikace Aljanah."

Sum sum tafita tana kuka, a bakin k'ofar d'akinshi ta tsaya tace anfad'a d'in "Allah ya isa ban yafeba,
Lokacin da kake zuwa k'ofar gidansu zance na sani ne?" Dan kawai ta aikoni da takarda saika sanyani kamun kunne saboda mugunta,
to banyafeba wuta balbal kuma sai dai idan Kaine Aljanin baniba."

Ganinshi tayi ya nufota ta zuba a guje tayi cikin gida, karo taci da Kaka zaune a tsakar gida, yanajinta a zaure tana Allah ya isa, dama yana da takaicinta ya sanya sandar hannunshi yashiga zungurarta da ita, yana fad'in mamuda kikeyiwa Allah ya isa marar kunya.'

Kuka takeyi sosai Wanda yasa tsohuwa tayi saurin fitowa daga d'aki ta ceceta
Tana fad'in yanzun malam saboda Allah akan mamuda kake zungurar dijama da sanda, ai dole jidama tayi masa Allah ya isa saboda baya raga mata, baya tausayinta ko kad'an."

Ta rik'a hannun dijama tace tashi mutafi ko gobe mamuda ya kuma zaluntarki kice masa baki yafeba."
[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_πŸ˜…)



Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)






*3*






Shiri takeyi zataje makarantar boko. Kasan cewar Wannan shine zangonta na k'arshe da zata k'are pramary school."

Ta kammala shirinta cikin riga da wando blue
ta sanya hijabinta fari, ta d'auko jakarta ta goya a bayanta,
ta dubi tsohuwa dake zaune gefe d'aya tana kallonta."

tace "ni dai tsohuwa nagama shiryawa zantafi."

Tsohuwa tace "to "dijamar tsohuwa Allah ya tsaremin ke kidawo lafiya,
Karki tsaya ko ina, kuma karki kula kowa a kan hanya kiyi tafiyarki dan karkiyi latti."

Tace "to tsohuwa, had'ida fitowa tasanya takalminta ta fita."

Saida ta kai k'ofar gida,
Sannan kuma ta juyo ta dawo a guje saka makon fitsarin da ya matseta,

Da sauri ta sunkuya ta d'auki buta a guje ta fad'a ban d'aki."

Wa zata gani yaya Mahmud ne,
ya juya bayansa yana wanka,
ihu ta kurma. Tana fad'in wayyo Allah k'ato ba wando,
Tafito a guje cikin tashin hankali da tsoro, had'ida sakin butar hannunta tazuba aguje."

Mahmud dajin ihunta yasanyashi Sanin shigowarta band'akin,
ransa yayi matuk'ar b'aci
Yashiga tunanin lallai wannan yarinyar bakad'an ta rainashiba tunda har take iya iskoshi band'aki." Tana kiranshi da k'ato ba wando."

Gudu take falfalawa kamar filfilwa,
bata zame a ko inaba sai makarantarsu,
Da shigarta makarantar ta cikin,
Taci karo da yara yan mkrtar tsugunne alamar latti sukayi,

Da gudu ta wucesu Batabi ta kansuba tayi shigewarta Aji."

Malam sani, mai hukunci yana ganinta ya rufa mata baya yana masifa,
kai tsaye ajinsu ya nufa,
ya tarar da ita zaune a kan kujerarta,

Kujerar da ba Wanda ya isa ya zauna akanta sai ita,
koda kuwa ranar da bataxo makaranta bane,
idan taji lbrin wani Wanda tsotsayi yasa shi ya zauna a kanta to sai tayi mashi shegen dukan tsiya."

Malam sani yashigo ajin a hasale, yadubeta
yace "ke dijama fito nan waje,
Wato kinyi latti saboda rashin kunya irin taki kika wani wuce mutane kika wuto aji,
Sai kace kinfi kowa to kisani hukuncinki ya k'aru dana sauran d'alibai."

Bata kulashiba sai ma tayi kamar bada ita yakeyiba,
Tsawa ya doka mata "ke dijama wai bada ke nake maganaba,?"

sai a lokacin ta dubeshi had'ida turo baki tana gunguni."

Cike da jin haushinta ya nufeta da bulala a hannunshi, bai tsaya b'ata lokaciba yashiga zuga mata bulalar."

Ihu ta kurma ta doka wani irin tsalle tashige mashi a babban Riga,
kasan Cewar malam sani ma'abucin sanya babban rigane.
Kokawa yashiga yi da ita yana k'ok'arin ya yakwace kansa daga gareta,
amma ina, idan yayi nan gefen ta dawo masa nan gefen, sai ihu takeyi kamar Wanda ake cirewa ido."

Malam sani ya jigata sosai zufa sai karye masa take, duk zufa ta wanke masa fuska,
ga dijama cikin babban rigarshi yakasa cireta, sai jujuwashi takeyi kamar zai fad'i k'asa."

Yashiga fad'in 'fito dijama nafasa dukan naki, kije kiyi zamanki,
amma ina ta cimuimuyeshi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On YAR GIDAN TSOHOWA
avatar
zainab-2-9-9

7 months ago

Reply

Thanks

avatar
zainab-2-9-9

7 months ago

Reply

Thanks

avatar
zainab-2-9-9

7 months ago

Reply

Thanks

Please Login or Register in order to submit comment