Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

This Document is compiled by
Shuraihu Usman - 08140419490
YEAR of compilation - 2023;
Published to Taskarnovels.com.ng

01. HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN
Allah shi ne Sarki mafi daukaka daga dukkan sarakuna. Shi ne mafi tsarki daga dukkan abubuwa. Tsira da aminci su tabbata ga Manzonsa kuma Annabinsa, Muhammadu dan Amina (SAW).
A wani shudadden zamani, a wani gari na cikin kasar Farisa, an yi wadan su mazaje guda biyu yan uwan juna. Babban sunansa Kasim karamin kuwa sunansa Ali Baba. Bayan rasuwar mahaifinsu, aka raba musu gadon yar dukiyar da ya bari, kowa ya kwashi rabonsa.
Kasim ya auri yar wani babban attajiri na garin, shi kuwa Ali Baba ya auri wata yarinya wacce iyayenta sun kasance talakawa ne. Ba a dade ba, sai surukin Kasim ya mutu, yarsa ta gaji dukkan dukiyarsa, domin ita kadai ce yar da ke gare shi. Ita kuma ta damka dukiyar nan a hannun mijinta Kasim. Nan take Kasim ya zama babban attajirin da babu kamar sa a duk fadin garin.
Shi kuwa Ali Baba sai ya kasance dan abin da ya gada na dukiya daga mahaifinsu ya kare. Ya zama talaka wanda bai mallaki komai ba sai jakai guda uku. Sai ya rika zuwa daji da jakansa yana saran itace yana lafto wa jakan nan yana kawowa cikin gari. Idan ya sayar, ya siyo abincin da za su ci, shi da matarsa.
Ana nan haka kullum, wata rana Ali Baba ya shiga daji domin yin sana'arsa kamar yadda ya saba. Bayan ya gama dora wa jakansa itace, yana haramar ya kora su ya tafi, sai ya hango 'kura ta toshe sararin samaniya daga nesa, ta tinkaro inda ya ke. Ya ga cewa idan ya ci gaba da tafiya mahayan nan za su cim masa, sai ya kora jakansa cikin rami, shi kuwa ya sami wata babbar itaciya mai duhuwa, wacce zai iya ganin abin da ya ke kasa ba tare da wanda ke kasa ya gan shi ba, ya haye.
Bai jima da hawa saman itaciyar nan ba, sai ya hango mutane akan dawaki a sukwane sun nufo inda ya ke. Suna zuwa wurin, sai duk suka ja suka tsaya. Kowane daga cikinsu ya sauka daga kan dokinsa, ya daure shi. Ali Baba ya dube su da kyau, ya ga cewa dukkansu samari ne majiya karfi, kowane yana rataye da takobi, yana dauke da kaya a kan dokinsa. Ya kirga su, ya ga cewa su arba'in ne cif.
Ashe mutanen nan barayi ne, masu tare fatake suna yi musu fashi, yanzu ma sun zo ne wurin da suke boye kayan da suke satowa. Ali Baba ya ga daya daga cikinsu, wanda yana zaton shi ne babbansu, ya tafi gindin wani dutse da ciyawa ta lullube shi, wanda idan ba yanzu ba Ali Baba bai taba lura da akwai dutse wurin ba. Ya tsaya gaban dutsen ya ce, "Fayau, bude dutsen Simsim." Dutse ya tsaga gida biyu, sai ga kofa ta bayyana. Barayin nan suka yi ta duruwa ciki da kayan da suka sato, bayan kowa ya shige, sai babban ya bi daga baya. Yana shigewa, sai dutsen ya koma ya rufe, tamkar babu dutse a wurin.
Ali Baba yana kan bishiya, yana kallon dukkan abin da ke faruwa. Bayan barayin nan sun shige cikin dutse, sai yayi kamar ya sauko ya kama doki daya ya hau, ya kora jakansa ya tsere, sai kuma ya tuna idan ya sauko kuma aka yi rashin sa'a da barayin nan suna fitowa daga dutsen nan, lalle za su kama shi. Saboda haka sai ya canza shawara, ya ci gaba da zama a kan bishiyar.
Can zuwa wani lokaci sai ya ga kofar dutsen nan ta bude, shugaban barayin ya fara fitowa ya tsaya a gaban kofar yana kidaya barayin nan a lokacin da suke fitowa, har ya kidaya talatin da tara, gami da shi arba'in ke nan. Da suka gama fitowa, sai Ali Baba ya ji ya ce, "Garam, rufe dutsen Simsim." dutse ya koma ya rufe. Suka hau dawakinsu suka juya ta hanyar da suka fito.
Da Ali Baba ya ga kurarsu ta bace, ya sauko daga kan itaciya, ya nufi inda ya boye jakansa da sauri domin ya kora su zuwa gida, sai wata zuciya ta ce masa, "Ka gwada fadin kalmomin nan ka ga ko dutsen nan zai bude." Ya tafi gaban dutsen ya tsaya dai dai inda ya ga shugaban barayin nan ya tsaya, ya ce, "Fayau, bude dutsen Simsim." Yana fadar haka kuwa sai kofa ta bude.
Ali Baba ya kutsa kai cikin dutsen nan. Yana shiga sai dutse ya koma ya rufe. Da farko yayi zaton zai ga duhu dindim a ciki, amma sai ya ga haske kamar an kunna fitilu. Ya duba haka, sai ya ga dukiya tsibi-tsibi. Tsibin zinariya daban, tsibin azurfa daban, na tagulla daban, gefe kuma ga kudi nan tsaba cunkus. Ali Baba yayi mamakin yadda wadan nan barayi suka tara dukiya mai yawa haka. Ya ce a ransa, lalle sun gaji dutsen nan ne tun daga kaka da kakanni, domin yawan su ba su isa su tara wannan dukiya ba koda kuwa sun yi shekara dari suna tara ta.
Ya tattaro wasu buhuhuwan zinariya, wadan da ya san jakansa za su iya dauka. Ya ce, "Fayau, bude dutsen Simsim." Dutse ya bude ya fito da buhuhuwan waje, sannan ya ce, "Garam, rufe dutsen Simsim." Dutse ya koma ya rufe. Ya jawo jakansa ya dora musu dukiyar nan sannan ya dora musu itace daga sama ya rufe yadda mutane ba za su gane ba. Ya kora su da sauri ya nufi gida yana murna.
Da ya isa gida, ya kora jakunan ciki ya kira matarasa suka sauke kayan. Koda ya zazzage, sai wurin ya haske, matar ta ga zinariya tana daukar ido. Ya shaida mata dukkan abin da ya faru. Ta yi godiya ga Allah, ta ce, "Dare daya Allah kan yi bature, hakika duk fadin garin nan yanzu babu wanda ya kai mu arziki. Bari na kidaya na gani"
Ali Baba ya yi dariya ya ce, "Mene ne na batan lokacinki wajen kidaya wannan zinariya? Sai ki yi kwanki ba ki gama gidaya ta ba. Abin da na ke so da ke shi ne, bakinki kanen kafarki, kada ki kuskura wani ya ji wannan labari. Zan je na haka rami mu binne wannan dukiya da Allah ya ba mu."
Matar ta ce, "Duk da haka dai ina so na san adadin wannan zinariya. Kafin ka gama haka rami bari na je nan makwabtanmu, gidan yayanka Kasim na aro karamin mudunsu na awon hatsi domin na ga ko mudu nawa wannan zinariya za ta yi."
Ya ce ba laifi amma ta tabbatar ba ta fadawa kowa abin da za ta auna da mudun ba. Ta fito ta shiga gidan Kasim, ta taras da matarsa. Bayan sun gaisa ta ce ta zo ne aron mudunsu na awon hatsi. Matar Kasim ta tambaye ta babba ko karami? Ta ce karamin ma zai yi. Ta shiga cikin daki domin ta dauko ma ta, ta ce a ranta, me wadan nan matsiyatan za su yi da mudu? Ina kuma suka sami hatsi mai yawa haka da har sai sun auna shi da mudu? Kuma wane irin hatsi ne wannan? Sai ta sami karo kadan ta manna shi a cikin kusurwar mudun wanda ta tabbata karon zai like kwaya daya ta hatsin da za a auna, ta haka za ta iya gano kalar hatsin da suka auna idan an maido mata da mudun. Ta kawo wa matar Ali Baba.
Bayan ta dawo gida, sai ta fara auna zinariyar nan mudu-mudu har ta gama kaf. Ta je ta sahida wa mijinta da yake hakar rami ko mudu nawa ta auna. Ta ce za ta je ta mayar musu da mudunsu. Ashe ba ta lura ba, kwayar zinariya daya ta manne da karon nan a can kasan mudun. Da matar Kasim ta karbi mudu, bayan matar Ali Baba ta tafi, sai ta duba cikin mudun. Wani irin mamaki ya rufe ta lokacin da ta ga kwayar zinariya a cikin mudun.
Nan take hassada ta daki kirjinta ta ce, ashe Ali Baba har yana da zinariyar da ta fi karfin a kidaya ta da hannu sai dai awo da mudu. Ina ya sami wannan dukiya? Ko ya fara sata ne? Bari mijina ya dawo in fada masa halin da kanensa yake ciki.
*** *** ***
ZA MU CI GABA JIBI INSHA ALLAHU02. HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN

Lokacin da Kasim ya dawo daga kasuwa tun bai huta ba, matarsa ta tare shi ta ce, "Maigida, na san da cewa ka dauki kanka a matsayin wanda ya fi kowa arziki a duk fadin garin nan, to amma abin da ba ka sani ba shi ne, yanzu akwai wanda ya dame ka ya shanye game da arziki cikin wannan gari namu. Domin yana da tarin zinariyar da ta fi karfin a kidaya ta da hannu sai dai a auna ta da mudu."

Kasim ya ce, "Wane ne wannan attajiri haka, amma dai bai dade da zuwa garin nan ba ko?"

Matar ta ce, "Ba kowa ba ne face dan uwanka Ali Baba." Ta kwashe dukkan labarin yadda matar Ali Baba ta zo aron mudu a wurinta, da kuma dabarar da ta yi har ta gano abin da aka auna da mudun.

Kasim ya kasance ba ya kula da taimakon dan uwansa Ali Baba duk da tarin dukiyarsa, ba ya ko yarda ya matso kusa gare shi, wai kada ya shafa masa talauci. Da ya ji wannan labari daga matarsa, sai ya cika da mamaki tare kuma da hassadar jin cewa wai har akwai wanda ya fi shi arziki a garinsu. Ya ce a cikin ransa, "Yanzu dare ya yi, amma gobe tunda safe zan je gidan dan uwana na ji inda ya sami wannan dukiya da rana tsaka. Lalle idan ya fara sata ne, zan tsegunta wa Sarki a daure shi." Ya kwanta amma ya kasa yin barci, yana ta kahon dandi har gari ya waye.

Da gari ya waye, tunda sassafe Kasim ya sallama wa Ali Baba. Bayan ya fito, ko gaisawa ba su yi ba, sai Kasim ya ce, "Ali Baba ka yi wa mutane badda sau, suna ganin ka a matsayin talaka wanda bai mallaki komai ba sai jakai guda uku da kake zuwa daji kana yiwo itacen siyarwa. Amma abin mamaki, jiya bayan na dawo daga shagona, matata ta ba ni wannan kwayar zinariyar ta ce mini a cikin mudun da ta ara muku ta makale. Wannan ya tabbatar mata da cewa ba hatsi kuka auna da mudun ba. Wannan ne dalilin da ya sa yanzu na yo maka sammako domin na ji inda ka sami wannan dukiya, idan kuwa ka ki fada mini zan je na shaida wa Sarki cewa kana daya daga cikin barayin nan da suka addabi mutanen wannan gari da kewayensa da sata, yanzu haka ma zinariya na nan kime a gidanka da kuka sato. Kuma na tabbata idan aka bincike gidanka kaf, za a gan ta."

Da Ali Baba ya ji wannan zance na dan uwansa, sai ya tabbatar da cewa matarsa ta fallasa musu sirrinsu ba tare da ta sani ba, don haka babu wani boye-boye illa ya fada wa dan uwansa gaskiyar abin da ya faru.

Ali Baba ya kwashe labrin abinda ya faru duka ya fada wa Kasim. Ya yi masa kwatancen dajin nan da kuma dai dai wurin da dutsen da barayin nan suke tara dukiyarsu ya ke. Ya kuma fada masa abin da ake cewa dutsen ya bude da kuma abin da ake cewa ya rufe.

Kasim na gama jin wannan labari, bai zame ko'ina ba sai kasuwa. Ya siyo jakai guda goma, kowane da mangalarsa, ya kawo gida ya daure.

Tun da asuba ya daura wa jakuna mangaloli, ya nufi dajin nan da Ali Baba ya yi masa kwatance. Can zuwa rana tsaka ya isa, ya bi kwatancen da aka yi masa har ya gano wurin da dutsen ya ke. Ya daure dabbobinsa a kusa da dutsen.

Ya tsaya gindin dutse ya ce, "Fayau, bude dutsen Simsim." Rufe bakinsa ke da wuya, sai ya ga kofa ta bude daga jikin dutsen. Mamaki ya rufe shi, nan da nan ya kwanto mangaloli daga jakunansa ya kutsa kai cikin dutsen, yana shiga dutsen ya rufe.

Kasim ya ga ashe dutsen wani katon daki ne mai cin dakuna sama da uku. Ya ga tarin dukiyar da ko a tunani bai taba zaton akwai irinta ba a fadin duniya. Komai bangarensa dabam, zinariya da azurfa da tagulla da tsabar kudi, ga su nan bila haddin. Ba tare da bata lokaci ba, ya fara cika mangalolinsa da ita yana tunanin abubuwan da zai yi idan ya kwashe ta duka ya kai gida.

Da ya gama cika mangalolinsa, ya ga kamar ma bai debi komai ba, domin babu alamun dukiyar nan ta ragu. Ya kiyasta cewa koda zai kwashe dukiyan nan duka, to sai ya yi wata uku ko fiye yana zuwa kullum yana dibar ta. Ya zo inda kofar dutsen ta ke ya ce, "Fayau, bude dutsen Cimcim." dutse ya ki budewa. Ya kara cewa, "Fayau, bude dutsen Jimjim." Dutse bai ko motsa ba.

Kasim yayi ta kiran kalmomi kamar su, Timtim, Kimkim, Zimzim, amma Allah da ikonsa har ya gaji ya kasa tuna kalmar "Simsim." Kamar ma da dai, bai taba jin kalmar ba. Daga nan sai murna ta koma ciki, domin ya tabbata idan barayin nan suka dawo suka same shi a ciki, lalle kashinsa ya bushe.

Sai duk dukiyar da ke cikin dutsen ta fita daga ransa, ya fara safa da marwa yana kokarin tuna kalmar da ake fada dutsen ya bude. Yayi duk iyakar kokarinsa amma ya kasa tuna kalmar. Da ya gaji sai ya sami wuri ya zauna yana tunanin makomarsa idan barayin nan suka same shi a cikin ma'ajiyarsu.

Bai san tsawon lokacin da ya kwashe a cikin dutsen ba. Can sai ya ji karar kofatan dawaki suna nufo wurin da dutsen ya ke. Tun yana jiyo su daga nesa, har suka zo daf da gindin dutsen. Daga nan sai ya ji duk sun sauka daga kan dawakansu. Ya duba cikin dutsen nan ko zai ga wani makami da zai kare kansa da shi, bai samu ba. Ya duba ko akwai wani wuri da zai iya boyewa, ya ga babu. Ya yanke shawarar ya tsaya daf da bakin kofa, idan dutsen ya bude sai ya yi wuf ya yi waje da gudu ya kama dokinsu daya ya sukwane shi, idan Allah ya taimake shi zai iya tserewa. Don haka sai ya tsaya daf da wurin da kofar za ta bude cikin shiri.

Su kuwa barayin nan da suka zo gindin dutse sai suka ga jakai guda goma a daure, suka duba ko'ina ba su ga mai su ba. Sai jikinsu ya ba su, domin ba su taba sa ran wani dan Adam zai iya zuwa cikin wannan daji ba, kuma har gindin dutsensu. Babbansu ya matsa gaban dutsen ya ce, "Fayau, bude dutsen Simsim." Nan take dutse ya bude.

*** *** ***

ZA MU CI GABA RANAR TALATA, DAI DAI WANNAN LOKACI, INSHA ALLAH.03. HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN

Kofa na budewa, sai Kasim ya fito waje da gudu, ya bangaje wasu daga cikin barayin nan. Kafin ya sake daga kafarsa wani daga cikin barayin nan ya raba shi gida biyu da takobinsa, gaya-wa-jini-na-wuce.

Barayin nan suka shiga cikin dutsen, suka ga mangalolin da Kasim ya cika da dukiyarsu. Kuma suka lura da cewa lalle ko bayan wannan dukiyar da Kasim ya dauka, akwai alamun an taba dibar dukiyar, ke nan ko Kasim din ne ya taba diba yanzu ya dawo ya kara, ko kuwa akwai wani bayan Kasim din wanda ya dibar musu dukiya.

Suka yi mamakin yadda Kasim ya san kalmomin da ake fada dutsen ya bude. Domin su gargadi duk wani mai zuwa yana dibar musu dukiya, sai suka raba gangar jikin Kasim gida hudu, suka manna kowanne sashe daya a bango daya na dutsen, watau kudu da arewa, gabas da yamma. Suka fita suka kora jakunansa zuwa inda suke tara dabbobin da suke satowa.

Da dare ya yi matar Kasim ba ta ga ya komo gida ba, sai hankalinta ya fara tashi. Ta dauki mayafinta ta ruga da gudu zuwa gidan Ali Baba. Ta same shi yana zaune yana hutawa.

Bayan sun gaisa, sai ta ce masa, "Ya kai dan uwan mijina, na san cewa kana da labarin mijina ya shiga daji da jakai, tunda assalatu, akan zai samo wani abu a can, wanda bai fada mini ko mene ne ba. Ga shi har dare ya yi bai komo ba. Shi ne na zo gare ka na ji ko ka san wurin da ya tafi? Ina jin tsoro, ya Allah ko wani mummunan abu ya faru da shi"

Ali Baba ya ce da ita, "Haka ne, dan uwana ya fada mini zai shiga daji, ai na dauka ya dawo, amma bari yanzu na shirya na tafi neman labarinsa. Ki koma gida zan sanar da ke abin da ake ciki idan na dawo."

Ali Baba ya tashi cikin daren nan ya daura wa jakansa uku mangaloli, ya kora su ya nufi cikin dajin da dutsen 'yan fashin nan ya ke. Can zuwa tsakiyar dare ya isa inda dutsen sihirin ya ke. Da isarsa gindin dutsen ya haska fitilarsa, sai ya ga jini faca-faca ko'ina a gindin dutsen. Tun daga nan sai ya sha jinin jikinsa. Ya ce, "Fayau bude dutsen simsim." Nan take kofa ta bude, ya shiga ciki.

Da shigarsa sai kofa ta rufe, ya haska fitilarsa, sai ya ga gawar dan uwansa Kasim, an datsa ta gida hudu, an manna kowane datse a bangon dutsen. Nan take ya yi sauri ya harhada su wuri daya. Sannan ya kuma dibar dukiyar da jakansa biyu za su iya dauka, ya fita daga cikin dutsen. Ya dora wa jakinsa daya gawar dan uwansa, sauran biyun kuma ya dora musu dukiyar da ya diba, ya samu kiraren itatuwa ya rurrufe mangalolin da su, yadda mutane ba za su gane abin da aka dauko ba. Ya kora su da sauri ya nufi gida.

Can zuwa da hantsi Ali Baba ya isa gida, ya shiga da jakansa biyu masu dauke da dukiyar cikin gida, ya fada wa matarsa ta sauke kayan ta boye su inda suka boye na farko. Ya kora jakin daya zuwa gidan matar dan uwansa.

Da ya isa gidan sai ya kwankwasa kofa. Bayan kwankwasawa ta biyu, sai ya ga Murjanatu ta bude kofar. Murjanatu ta kasance baiwa ce ga Kasim, Allah ya hore ma ta tsananin wayo da dabara, duk da ta kasance yarinya karama, mai kananan shekaru, amma hankalinta da tunaninta ya zarta na manyan mutane. Shi ya sa ma duk wata shawara da ita Kasim ya ke yi.

Ali Baba ya kora jakinsa cikin gidan, Murjanatu ta mayar da kofa ta rufe, ya umurce ta da ta kira masa matar dan uwansa. Bayan sun koma, ya sauke gawar Kasim ya shaida musu abin da ya faru da Kasim duka. Bayan sun gama yan koke-kokensu, sun share hawaye, sai ya ce musu, "Abin da na ke so da ku shi ne, ina so mutanen garin nan su tabbatar da cewa dan uwana ya mutu ne a gida, a kan gadonsa, sanadiyyar rashin lafiya, ba na so kowa ya san abin da ya faru da shi."

Abin da ya sa Ali Baba ya fadi haka kuwa shi ne, ya tabbata idan barayin nan suka koma maboyarsu ba su ga gawar Kasim ba, za su shiga binciken wanda ya zo ya dauke ta. To idan mutanen gari suka san gaskiyar labarin yadda Kasim ya mutu, da yadda aka rufe gawarsa guntu-guntu, labarin ba zai boyu ga barayin nan ba, kuma za su yi saurin gane Ali Baba su kashe shi. Amma idan mutanen gari suka san cewa Kasim ya mutu ne a kan gadonsa sanadiyyar rashin lafiya, kuma an yi jana'izarsa gaban mutane, shi ke nan babu wanda zai koma ta kan batun. Don haka babu yadda za a yi barayin su gane wanda ya dauke gawar.

Bayan Ali Baba ya tafi, sai matar Kasim ta ce da Murjanatu, "Na bar wannan a hannunki, ke kika san dabarar da za ki yi, ki kawar da hankalin mutane har su dauka cewa Kasim ya mutu ne sanadiyyar rashin lafiya a kan gadonsa."

Murjanatu ta ce, "Wannan abu ne mai sauki a wurina." Sai ta ruga da gudu zuwa shagon wani mai sayar da magunguna, hankalinta a tashe, ko takalmi babu a kafarta, ta ce da shi, "Don Allah yi sauri ka bani maganin zazzabi, ubangijina Kasim na can zazzabi mai zafi ya rufe shi, har ba ya iya gane masu zuwa wurinsa."

Mai magani ya dauko wani magni ya ba ta. Ta karba ta ba shi dirhami daya, ba ta ko tsaya karbar canji ba, ta nufi gida da sauri, ta na rike da magani a hannunta, tana tafe hawaye na fita daga idonta. Duk wanda ta hadu da shi a kan hanya, idan ya ga halin da take ciki, ga kuma magani a hannunta, sai ya tausaya mata, ya kuma gane abin da take ciki na jiyyar mara lafiya.

Ali Baba da matarsa suka dinga Safa da Marwa tsakanin gidansu da gidan Kasim, domin dai su baddalar da mutane a kan cewa wani abu na faruwa a gidan Kasim. Don haka lokacin da mutane suka ji kuka daga gidan Kasim tare kuma da labarin mutuwarsa cikin dare ba su yi mamakin hakan ba.

Tun da sassafe kafin Ali Baba ya gama shaida wa mutane labarin mutuwar dan uwansa Kasim, domin
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment