Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

This Document is compiled by
Shuraihu Usman - 08140419490
YEAR of compilation - 2023;
Published to Taskarnovels.com.ng

SHARRI KARE NE 1

HIKAYAR ABUƘIR MARINI DA ABUSIR WANZAMI

(Daga Littafin Dare Dubu Da Ɗaya)

Waziri Aku

Abuƙir da Abusir maƙwabtan juna ne a cikin kasuwar birnin Iskandariya, shagunansu na kallon juna. Abuƙir marini ne, yayin da Abusir ya kasance wanzami.

Kamar yadda sana'o'insu suka banbanta haka ma halayensu suka sha bamban tamkar wuta da saɓi. Abuƙir dai duk inda mutumin banza ya kai to ya wuce nan. Mutum ne maƙaryaci, mai saɓa alkawari, mara amana, mayaudari, ga kwaɗayi kamar kura, rowa kamar na goye. Rashin kunya a wurinsa kuwa ko ɗan bashirwa na shafa masa lafiya.

Duk sa'adda wani ya kawo masa tufafi domin ya rina masa, Abuƙir zai fara neman kuɗi a wurin mutumin, wai zai sayi kayan aiki. Idan aka ba shi kuɗin sai kuma ya ɗauki tufafin ya sayar, ya shiga kasuwa ya samu tozon raƙumi da shinkafa ya saya, ya kai gida a yi masa dabge, sauran canji kuma ya sayi goro da sigari yana busawa abinsa.

Idan mai kaya ya dawo karɓar kayansa, sai ya kalallame shi da baki, ya ba shi haƙuri, sa'anna ya ce, "ka dawo gobe war haka, insha Allahu za ka samu kayanka."

Idan mai kaya ya sake dawowa, sai kuma ya kawo masa wani uzurin yana cewa, "ka sani jiya fa har na ɗauko kayanka zan fara aiki, sai aka aiko mini na yi baƙi a gida. Na rufe shago na tafi, to ban sake buɗe shagon ba sai yanzun nan. Ka yi haƙuri ka dawo gobe war haka, za ka samu kayanka."

Haka mutumin zai haƙura ya tafi. Washe gari idan ya dawo sai Abuƙir kuma ya ce, "Wallahi jiya har na haɗa kayan aiki sai aka aiko mini matata ba ta da lafiya, tilas na rufe shagon na nufi gida, ban kuwa sake buɗe shagon ba sai yau. Ka yi haƙuri, ba makawa gobe ka samu kayanka."

Idan mai kaya ya sake dawowa sai kuma ya samu wata ƙaryar ya gwabza masa. Haka zai yi ta yi wa mutum je-ka-ka-dawo har ya gaji ya daina zuwa. Idan kuma mutumin ya yi gajin haƙuri ya ce a ɗauko masa kayansa haka nan, sai Abuƙir ya langaɓe kai, kamar tsuntsun da ruwa ya yi wa duka, ya iya kissa kamar tsohuwar karuwa, sai ya ce wa mutumin, "bawan Allah, bari dai na faɗa maka gaskiya, ka san an ce ranar wanka ba a ɓoyon cibi. Tun ranar da ka kawo mini kayanka na rine su tsaf, rini kuwa ɗan ubansu, na shanya su a gaban shagona domin su bushe, na shiga kasuwa in sayo wasu kayan aiki, ko da na dawo sai na tarar da wani mara imani ya sace kayan. Ina jin kunyar in faɗa maka wannan batu, shi ya sa nake ta yi maka 'yan kusurwoyi."

Idan mutumin mai tausayi ne sai ya ce, "ayya! Ai ba komai, ƙaddara ce. Allah ya tsare gaba." Sai ya juya ya tafi. Da zarar Abuƙir ya ga ya ba da baya, sai ya riƙa yi masa gwalo. Idan kuwa mutumin mai zafin rai ne, sai ya zazzage shi, ya ce sakacinsa ne ya jawo. Idan ya ga wani abu mai amfani a cikin shagon, sai ya ɗauke ya tafi da shi, wai ko ya rage asara. Saboda haka shagon nasa ya koma fanko, ban da ruɓaɓɓun tukwanen ƙasa babu wani abin kirki a ciki.

Sannu a hankali duk mutane suka gane halin Abuƙir, aka daina kawo masa rini. Idan ya buɗe shagonsa tun da safe, sai rana ta koma ga Ubangiji babu wanda ya leƙa shagon, balle a kai masa aiki. Idan ka ga mutum a ƙofar shagonsa to baƙo ne ko irin ƙauyawan da kan shigo birni waɗanda ba su san halinsa ba.

To kullum idan ya buɗe shagonsa sai ya tafi shagon Abusir ya zauna tare da shi suna hira, yana kuma hangen shagonsa. Da ya hango wani ya tsaya a bakin shagon da kaya a hannu, sai ya zabura ya tafi wurinsa, idan na rini ne sai ya karɓa, ya kuma karɓe kuɗin aikin, ya ce masa ya dawo gobe. Da mutumin ya tafi, shi kuma sai ya shiga kasuwa ya sayar da kayan, ya sayi nama da kayan abinci ya kai gida. Su sha shagalinsu shi da matarsa.

Amma idan ya hangi wanda ya ba shi aiki ne tsaye a bakin shagon, sai ya ƙi fitowa daga shagon Abusir, har sai mutumin ya gaji da tsayuwa ya tafi. Ran nan dai ya karɓi kayan wani mai zuciya kusa, da mutumin ya gaji da zirga-zirga, ya kuma leƙa shagon bai ga kayansa ba, bai kuma ga wani abin amfani da zai ɗauka ba, sai ya kai ƙara wurin Alƙali. Alƙali ya aiko da masinja domin a tafi da Abuƙir. Da aka zo ba a same shi ba, sai masinjan ya samu kwaɗo ya datse shagon, ya ce wa mutane a gaya wa Abuƙir, idan ya dawo, ya je wajen Alƙali ya karɓo mabuɗi. Ya juya ya tafi.

Ashe duk abin nan, Abuƙir na cikin shagon Abusir yana hange. Da Abusir ya ga an rufe shagon Marini sai ya ce masa, "kai kuwa me yasa kake wasa da sana'arka haka? Duk sadda aka kawo maka rini ba a kwashewa lafiya. Ka je ka kai wa mutumin nan kayansa ka karɓo makullin shagonka."

Abuƙir ya ce, "wallahi an sace su."

Abusir ya ce, "haba, sai ka ce kai kaɗai ɓarayi suka raina a kasuwar nan. Duk wanda ya kawo maka rini sai ka ce an sace kayansa. Kai dai faɗa mini gaskiya."

Marini ya duƙar da kai, kamar wani mummuni, yana susar ƙeya ya ce, "abokina bari dai in faɗa maka gaskiya, sayar da kayan nake yi, ni kuwa sai na ce musu an sace."

Wanzami ya ce, "amma dai ba ka kyauta ba, wannan babban zunubi ne kake aikawata, Allah kuwa na fushi da masu saɓo."

Marini ya ce, "ban aikata haka ba sai don lalura. Kasuwancina ya durƙushe ba na samun aiki yanzu, balle na samu abin ɓatarwa. Talauci ya yi mini katutu, na rasa yadda zan yi da raina."

Wanzami ya ce, "ba kai kaɗai ba, ni kaina kullum da kyar nake samun na cefane a shagon nan. Ga shi dai na iya aski amma sai mutane su tsallake shagona su tafi wani shagon, wai don nawa shagon babu kayan alatu a ciki, sai ka ce kayan alatun ke yi musu aski. Ni da nake talaka, ina na ga kuɗin da zan ƙawata shago kamar na 'yan birni?"

Marini ya ce, "abin da na ga ya fi, idan ka yarda, mu bar garin nan, mu shiga duniya mu ga abin da Allah zai ba mu ta hanyar sana'o'in nan namu. Duniyar nan ta Assamadu dai da faɗi da yalwa, bai kamata mu tsaya wurin da za mu takura ba, motsi ai ya fi laɓewa." Marini ya yi ta jan hankalin Wanzami har ya ciwo kansa, ya yarda za su shiga duniya su nemi arziki daga falalar Ubangiji.

Za mu ci gaba.

Bukar Mada
02/10/2022SHARRI KARE NE 2

HIKAYAR ABUƘIR MARINI DA ABUSIR WANZAMI

(Daga Littafin Dare Dubu Da Ɗaya)

Waziri Aku

Da Abuƙir ya ga ya shawo kan Abusir, har ya yarda za su shiga duniya neman arziki tare, sai ya yi farin ciki, gayar farin ciki. Ya ce wa Wanzami, "ya makwabcina, yanzu kam mun zama 'yan'uwa, babu wani bambanci a tsakaninmu. Sai mu yi wa juna alkawari cewa, idan muka bar garin nan, ran da duk ɗaya daga cikinmu bai samu aikin yi ba, to wanda ya samu aiki zai ciyar da shi. Sa'annan mu samu ƙaton asusu mu riƙa ɗan tsinkular abin da muka samu na kuɗi muna jefawa a ciki, ka san an ce ajiya maganin wata rana, ran da duk Allah ya maido mu gida lafiya, sai mu fashe shi, mu ga abin da Allah zai ba mu."

Abusir ya yi na'am da wannan shawara. Suka ɗauki alkawari. Suka kuma yi addu'a tare da fatar tsinuwar Allah ga duk wanda ya saɓa wannan alkawari, suka shafa Fatiha. Suka shirya barin garin washegari.

Da gari ya waye suka ƙulle 'yan kayansu, Abusir ya rufe shago ya danƙa wa masu shagon mabuɗinsu, shi kuwa Abuƙir bai ko kula da nasa shagon ba, ya bar mabuɗi ga Alƙali. Suka samu wani jirgin 'yan kasuwa da za su fatauci suka shiga, babu ɗayansu da yake da wani guzurin kirki. Jirgi ya miƙa cikin teku, suka ba Iskandariya baya, tun suna hangen gine-ginen birni har suka daina ganin ko ɓirɓishinsu.

Daga nan sai Abusir ya ce wa Abuƙir, "abokina, ka ga akwai tafiya mai nisa a gabanmu, ba na tsammani ɗan guzurin nan namu zai ishe mu. Bari na zagaya cikin jirgin nan da kayan aikina ko Allah ya sa na samu wanda zan yi wa aski ko ƙaho ya ba mu abinci."

Abuƙir ya ce, "wannan daidai ne ɗan uwana." Ya gyara shimfiɗa ya mimmiƙe abinsa.

Wanzami ya ɗauki zabirarsa, ya saɓa wani tsumman mayafi a kafaɗa, wanda yake yi wa mutane aski da shi, ya shiga cikin jirgi yana zagayawa. Jirgin nan kuwa na ɗauke da 'yan kasuwa ɗari da ashirin, inda kuma Allah ya tarfa wa garinsa nono, sai ya kasance babu wani wanzami a cikin jirgin sai shi kaɗai. Yana cikin zagayawa sai wani mutum ya sa baki ya kira shi, "kai wanzami, zo ka yi mini aski."

Abusir ya tsaya ya yi masa aski. Mutumin ya kawo rabin dirhami ya ba shi, sai ya ƙi karɓa ya ce, "abokina, da dai za ka ba ni abinci da ɗan ruwa da na so. Wanna kuɗi ba shi da wani amfani gare ni yanzu. Tare nake da ɗan uwana, kuma ba mu da isasshen guzuri."

Mutumin ya kawo gurasa da yankan burodi ɗaya, ya kuma cika masa wani ɗan gora da ruwa ya ba shi. Wanzami ya ɗauki abinci ya kai wa Marini ya ce, "ci wannan, bari na koma in ga abin da zan kuma samowa." Marini ya karɓe abinci ya cinye, ya sha ruwa. Ya gyara shimfiɗa ya yi kwanciyarsa.

Wanzami ya sake kutsawa cikin jirgi. Duk inda ya jefa ƙafa sai a kira shi domin ya yi aski. Aka yi ta ba shi abinci iri-iri, kamar su gurasa, ƙosai, burodi, dabino, soyayyen nama, ƙyafaffen kifi, madara, cukwi da sauransu. Da aka ga dai ya iya aski, sai aka soma yi masa layi, ga shi kuma babu wani wanzami a jirgin.

Aka ce kowa ya samu rana to ya kamata ya shanya garinsa kafin ta gushe, don haka sai ya riƙa yanka ladar abin da za a biya shi, maimakon a ba shi abinci kurum, sai ya riƙa haɗawa da kuɗi. Idan aka ba shi abinci, sai kuma a haɗa masa da rabin dirhami ko dirhami ɗaya. Don haka ko kafin rana ta faɗi, ya tara kaɓukkan abinci, ya kuma samu dirhami talatin ya ƙulle a mayani.

A cikin waɗanda ya yi wa askin nan har da madugun jirgin, watau shugaban matuƙa jirgi. Yayin da yake yi masa aski ne madugun ya tambaye shi, me ya sa ake biyansa da abinci?

Wanzami ya kwashe labarinsa da na abokin tafiyarsa ya faɗa masa. Da Madugu ya ji haka sai ya ce, "af, don wannan kada ku tayar da hankalinku. In don abinci ne, to kullum da yamma ku zo tantina mu ci tare har Allah ya sauke mu lafiya. Muna da isasshen abinci ni da ma'aikatana."

Yayin da ya dawo inda Marini, sai ya tarar da shi yana ta sharɓar barci. Ya tashe shi. Da Abuƙir ya buɗe ido ya ga garar da Wanzami ya kinkimo a cikin kwando, sai ya wangame baki cikin mamaki, ya tambaye shi, "ina ka samo wannan abinci haka?"

Abusir ya amsa masa, "wannan yana daga falalar Ubangiji mai girma."

Abuƙir ya jajjanye hannuwan riga zai far ma abinci da ci, Abusir ya ce masa, "ya ɗan uwana, mu adana wannan saboda amfanin gaba. Ka tashi yanzu maza mu tafi tantin Madugu mu ci abinci, domin na faɗa masa matsalarmu, ya kuma yi alkawarin ciyar da mu har ranar da muka sauka."

Abuƙir ya ce, "wallahi ɗan uwana ba ni da lafiya, masassarar teku ta kama ni, da zarar na miƙe tsaye sai jiri ya ɗebe ni, in ji kamar zan yi amai. Bar mani wannan abincin na ɗan taɓa kaɗan na adana mana saura, kai kuwa ka tafi wurin Madugu ku ci tare."

Abusir ya ce, "babu laifi ga haka." Ya miƙa masa abinci.

Marini ya sassauta ɗaurin ɗamarar da ta tanke cikinsa, ya gyara zama. Ya jawo kwandon abinci gabansa ya fara wurga loma, kamar ana wurga dutse a cikin rami, yana haɗiyewa kamar giwar da ta yi kwana da kwanaki ba ta haɗiyi komai ba. Kafin lomar ta faɗa har ya yanko wata yana shirin jefawa baka, yana kallon abincin sai ka ce maye na kallon mara lafiya. Wazami dai ya ƙura wa ikon Allah ido.

Za mu ci gaba.

Bukar Mada
05/10/2022SHARRI KARE NE 3

HIKAYAR ABUƘIR MARINI DA ABUSIR WANZAMI

(Daga Littafin Dare Dubu Da Ɗaya)

Waziri Aku

Marini ya sassauta ɗaurin ɗamarar da ta tanke cikinsa, ya gyara zama. Ya jawo kwandon abinci gabansa ya fara wurga loma, kamar ana wurga dutse a cikin rami, yana haɗiyewa kamar giwar da ta yi kwana da kwanaki ba ta haɗiyi komai ba. Kafin lomar ta faɗa har ya yanko wata yana shirin jefawa baka, yana kallon abincin sai ka ce maye na kallon mara lafiya. Wazami dai ya ƙura wa ikon Allah ido.

Suna cikin haka sai ga wani mutum ya zo daga tantin Madugu ya ce wa Abusir, "Maigida ya ce ka zo kai da ɗan uwanka ku ci abinci."

Abusir ya dubi Marini ya ce, "ko za ka lallaɓa mu tafi?"

Marini ya ce, "ba na iya tafiya."

Wanzami ya miƙe ya bi mutumin har tantin Madugu. Da zuwa ya iske an shirya farantai na abinci iri iri. Madugu ya tambaye shi, "ina ɗan uwan naka?"

Abusir ya ce, "ba ya iya zuwa, yana fama da masassarar teku."

Madugu ya yi dariya ya ce, "babu komai, da ma duk wanda bai saba shiga jirgi ba, sai ya yi fama da wannan zazzaɓi, amma zai wartsake ba da jimawa ba." Ya samu ƙwarya ya jera farantan abinci a ciki, wanda mutum goma za su iya ci su ƙoshi, ya miƙa wa Wanzami ya ce, "ɗauki wannan ka kai masa, ka kuma yi hanzari ka koma domin mu ci namu."

Abusir ya karɓi abinci ya koma wajen Marini, ya same shi yana ta rizgar abinci, sai haƙoransa ke ƙara, ƙararas ƙararas, idan yana tauna abincin kamar karen da ke ragargazar ƙashi. Yana hannu baka hannu akushi kamar wanda aka ce za a kwace abincin daga hannunsa.

Abusir ya ce, "ba na gaya maka kada ka ci wannan abincin ba, za mu samu wanda ya fi shi daɗi a wajen Madugu? Dubi wanda aka ce in kawo maka." Ya miƙa masa ƙwarya.

Marini ya karɓa ya duba, da ya ga lafiyayyen abinci sabo, yana tiriri, sai ya ture busasshen burodi da gurasa gefe guda, ya faɗa wannan da ci kamar mayuwancin zakin da ya fito daga surƙuƙi ya samu wata 'yar dabba ya taushe, ko mayunwacin shahon da ya dirar wa ɗan tsako. Kai, kamar dai mutumin da ya kusa mutuwa don yunwa, aka kawo masa farfesun nama.

Abusir dai ya tafi ya bar shi nan, yana ta dinarsa shi kaɗai, ya nufi inda Madugu ke jiransa. Suka ci suka sha tare har suka tumbatsa. Ya yi masa godiya, ya dawo inda abokin tafiyarsa. Ya same shi duk ya cinye abincin nan da ya kawo masa, ya jefar da ƙwarya gefe guda mawofanciya. Ya kishingiɗa yana sakatar haƙori, yana nishi don ƙoshi sai ka ce bokalo. Ya ɗauki ƙwarya ya mayar wa Madugu, ya kuma yi masa godiya, ya dawo inda Abuƙir suka kwanta har gari ya waye.

Kashegari Wanzami ya ɗauki zabirarsa ya kewaya cikin jirgi, ya ci gaba da yi wa mutane aski, abin da ya samu duka na abinci ya kawo wa abokin tafiyarsa, shi kuwa ya amshe ya kimsa wa cikinsa, yana daga kan shimfidarsa, ba ya zuwa ko'ina. Idan ka ga ya tashi, to zai je ne ya yi abin nan da wani bai isa ya yi wa wani shi ba. Idan kuma yamma ta yi, sai Abusir ya kawo masa ƙwarya cike da abinci daga tantin Madugu. Haka suka kasance a cikin wannan jirgi tsawon kwana ashirin, har suka isa gaɓar wani babban birni daga cikin birane.

Jirgi ya tsaya, ya sauke wasu daga cikin 'yan kasuwa. Marini da Wanzami suka sauka tare da su, suka yi sallama da Madugu, jirgi ya yi gaba. Suka sauka gidan baƙi, Abusir ya biya musu kuɗin ɗaki daga ɗan abin da ya samu a cikin jirgi. Ya tafi kasuwa ya sayo musu kayan abinci da nama, ya kuma sayo murhu da tallen dahuwa da akussa da kuma cokullan cin abinci. Da zuwa ya ɗora sanwar abinci.

Shi kuwa Abuƙir tun da suka shiga ɗakin, sai ya bi lafiyar gado, sai barci. Bai farka ba sai da Abusir ya gama shirya abinci da nama, ya tayar da shi domin su ci. Suka ci suka ƙoshi. Abuƙir ya dubi Abusir ya ce, "ɗan uwana kada fa ka zarge ni, har yanzu jiri nake gani." Ya sake haye gado ya yi kwanciyarsa, ba a jima ba ya fara minshari.

Haka suka kasance tsawon kwanaki arba'in, kullum Wanzami zai shiga gari ya yi sana'arsa, ya sayo kayan abinci da nama, ya dawo masauki ya girka musu, ya shirya abinci cikin akussa sa'annan ya tayar da Marini da ke barci domin su ci. Idan suka fara cin abincin kuwa, sai Marini ya yi loma uku Wanzami bai yi ɗaya ba. Idan suka gama cin abincin, sai ya koma barc abinsa. Aka sake yin wasu kwanaki arba'in, Marini bai ko fita daga gidan baƙi ba, balle ya ce zai shiga gari. Ya yi ƙiba ɓulɓul kamar turkakken maraƙi.

Duk sa'adda Wanzami ya ce masa, "ɗan uwana, ya kamata ka ƙoƙarta ka shiga gari ka miƙe ƙafa ka kuma kashe kwarkwatar ido, da ɗai ban ga birni mai kyawun gine-gine kamar wannan ba, ban ga kuma mutanen da suturarsu ke ba ni mamaki ba kamar na mutanen wannan birni."

Sai Marini ya haye gado ya ce, "abokina kada ka ga laifina, wallahi jiri nake gani."

To, da yake Abusir mutum ne mai haƙuri kamar ƙasa, ga sauƙin hali kamar ruwa, sai ya ƙyale shi, bai taɓa sauya masa fuska ba, balle ya nuna gajiyawarsa. Aka ce jiki ba ice ba ne, yana da jini! A kwana na arba'in da ɗaya sai zazzaɓi ya rufe Wanzami har ya kasa fita wajen aiki. Don haka sai ya samu wani saurayi cikin masu kula da gidan baƙin ya ba shi kuɗi domin ya riƙa sayo musu abinci. Saurayi ya yi kwana huɗu yana sayo abinci yana kawo musu.

A cikin waɗannan kwanaki rashin lafiyar Wanzami ta yi tsanani ƙwarai, har ya fita daga cikin hayyacinsa. Ashe kuma kuɗin da aka ba saurayi na sayen abinci sun ƙare. To, da Marini ya ga saurayi ya daina kawo musu abinci kamar yadda ya saba, ga kuma yunwa ta fara dafa shi, sai ya tashi daga kan gado, ya tafi inda Wanzami yake kwance magashiyyan, ya birkice shi, ya ƙwaƙule 'yan kuɗin da ke jikinsa duka, ya tarar da sulallan azurfa alfen. Ya fice daga ɗakin ya rufe ƙofa, kamar babu kowa a ciki. Ya sulale daga gidan baƙin ba tare da kowa ya gan shi ba.

Za mu ci gaba.

A yi SHARE domin wasu ma su amfana.

Bukar Mada
08/10/2022SHARRI KARE NE 4

Waziri Aku

HIKAYAR ABUƘIR MARINI DA ABUSIR WANZAMI

(Daga Littafin Dare Dubu Da Ɗaya)

To, da Marini ya ga saurayi ya daina kawo musu abinci kamar yadda ya saba, ga kuma yunwa ta fara dafa shi, sai ya tashi daga kan gado, ya tafi inda Wanzami yake kwance magashiyyan, ya birkice shi, ya ƙwaƙule 'yan kuɗin da ke jikinsa duka, ya tarar da sulallan azurfa alfen. Ya fice daga ɗakin ya rufe ƙofa, kamar babu kowa a ciki. Ya sulale daga gidan baƙin ba tare da kowa ya gan shi ba.

Da fitarsa bai zame ko'ina ba sai gaban mai abinci. Ya tsaya ya cika tumbinsa tukuna, domin an ce da ruwan ciki akan ja na rijiya, sa'annan ya nufi kasuwa ya sayi tufafi masu tsada, ya ƙunshe ga takarda. Ya nemi gidan wanka kusa bai samu ba, sai ya gangara wata ƙorama da ya ga mafi yawancin mutane na zuwa don yin wanka.

Ya tulɓa wanka, ya sanya sabbin tufafinsa, ya shiga gari yana hura hanci kamar wani tajiri. Ya riƙa zagayawa cikin garin rariya-rariya yana kashe kwarkwatar ido. Ya tarar ashe dai garin nan gari ne mai tsari da kuma kyawon gine-gine, tun da yake bai taɓa ganin gari mai kyawu kamarsa ba. Nan take kuma ya lura da abu ɗaya da ya ba shi mamaki, mutanen garin duka ba su da wasu launin suturu da suka wuce fari da shuɗi.

Yana cikin tafiya sai ya iso ga wani shago da ya ga an shanya tufafi a gabansa, launin tufafin kuwa duka shuɗi ne. Ashe shagon nan marina ce, dami ya tsinke gindin kaba. Ya tafi ga majirayin shagon ya zaro farin adiko ya miƙa masa ya ce, "rina mini wannan ƙyalle yanzu ka karɓi kuɗinka."

Marini ya karɓi ƙyalle ya jujjuya shi ga hannunsa, sa'annan ya ce wa Abuƙir, "dirhami ashirin za ka biya."

Abuƙir ya dafe baki cikin mamaki ya ce, "wannan ɗan ƙyallen? To, a ƙasarmu dirhami biyu ake rina kamarsa."

Marini ya jefa masa ƙyallensa ya ce, "tafi da shi ƙasarku mana a rina maka. Idan ba dirhami ashirin ba, ba na rina shi."

Abuƙir ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment