Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bata damar yi mishi magana ko hak'uri ne ta bashi.
Tana son ta fita ta duba 'ya'yanta tana tsoron kada ta fita ya kulle k'ofarshi, don tasa a ranta dole anan zata kwana.
Shine ma ya mik'e ya fita, dakunan yaran yasasu yin fitsari, sannan ya dawo falo yayi zamanshi.
Shiru Mama na zuba idon dawowarshi.
Sai can wajen d'aya 1:00am sannan ya tashi ya koma d'akin.
To Kwanan ranar dai haka sukayi shi babu d'adi dai...
B'angaren Hafsah kuwa kuka take yi gurshek`e..
Abubuwa ne da yawa suka had'ar mata, na farko nadamar zama silar samun sab'anin iyayenta, domin tasan da wayonta bata tab'a ganin hakan ba gabanta, sannan bataji dad'i Abba ya kamata da laifi irin wannan ba.
Na biyu kuma jimamin k'wace wayar ta da Abban yayi.
Sai kuma babban wato tunkarar yusuf da maganar abba.
Tunani dai shiya cinye rabin darenta.


♥♥♥♥ ♥♥♥♥

Kwance yake akan gadonshi daga shi sai singlet da gajeren wando. Ya kwanta rub da ciki.
Wani tunanin shima yake yi daban.
Yana jin dad'in yadda yarinyar take sonshi sosai, shima kuma yasan yana sonta, amma matsalar yarinyar 'Local ce'
Yusuf kenan ke tariyo (tunanin) irin rayuwar da sukeyi shi da Hafsah. Abin na bashi mamaki wani lokacin kuma yana jin takaicin hakan.
Kamanninta ya shigo tunowa.
Kyakykyawa ce, shi dai ta mishi kyau! yana son komai nata, amma me yasa bata mishi soyayya irin wacce yake so?
Ta iya kalamai masu sanyaya zuciya (sweet words) ta iya kwalliya, ita d'in kalar manyan yara ce.
"Her smile kills me!
Ya fad'a a hankali.
Yusuf yana son ya samo musu mafita ne akan k'in yarda dashi da Hafsah keyi.
A ganinshi "zama cikin mutane d'aya masu yare d'aya, al,ada d'aya, addini d'aya shiya sa ta rashin wayewa. A ganin shi Hafsa nayin rayuwar _kifi acikin rijiya ne._
Matsalalolin ya kasa kashi-kashi da niyyar samo musu mafita.
Na farko shine 'Rashin yarda dashi da Hafsah keyi, wanda ya danganta shi da 'rashin wayewa'..
Yasani cewa fushinsa na rikitata, saboda haka ya d'auki aniyar nuna mata fushinshi a duk sanda tayi mishi hakan, tare da yi mata barazanar rabuwa da ita, har lokacin da zata bada kai...
Yayi murmushi samun nasara don yasan Hafsah bata da jarumtar jure fushinshi.
Na biyu kuma Rashin wayewarta da zama waje d'aya, mafitarsu a wajensa shine d'aukarta su dinga fita yawon shak'atawa lokaci zuwa lokaci.
Sai kuma sauran banbance banbance dake tsakaninsu wanda zai mayar da hankali wajen sace zuciyarta, hakan zai sakata zama daidai da ra,ayinshi.
*TSOKACI*
Sau da dama zama baya yiyuwa idan ra,ayi ko kuma hali bai zo d'aya ba, sai dai idan d'aya ya rinjayi d'ayan bisa ga bin ra,ayinshi.

Akwai banbance - banbance da yawa tsakanin yusuf da kuma Hafsah. Wanda silar su shine samun dace da iyayen kirki da kuma tarbiyya, sai kuma aka sami akasin haka daga b'angaren 'Yusuf'
Haka fahimtar da suka yiwa soyayya ma da akwai banbanci.
A wajen Hafsah ta d'auki soyaya ne irin ta saurayi da budurwa a matsayin : 'Musayar kalaman soyyaya a tsakanin masoya sai kuma kyautatawa da kuma sadaukarwa ga juna da kuma fatan zama a Inuwa d'aya wato 'Aure'
A wajen Yusuf kuwa yana ganin soyayya Itace farantawa juna da kuma zama d'aya babu banbanci.
'Duk da addini da al,ada sun nuna banbancin inda aka saka wani geji 'iyaka' tsanin Mace da Namiji a wajen mu,amala.'
To shi Yusuf bai ga wannan ba gurinshi ma idan dai 'True Love' ake yi babu zancen wani addini ko kuma al,ada kawai a zauna a bi ra,ayin zuciyoyi.
Domin a wajen shi 'Sacrifice' wato sadaukarwar da Hafsah ke ik'irarin tana masa ba ita bace, tunda ita ganin ta bashi 'Dukkan yarda' shine ta sadaukar mishi komai.
Shi kuma yana ganin idan gaske ne sadaukarwar tata ya dace ya gani a aikace ba ik'irarin da kalmomin baki ba. Shi yasa yake tantama bisa son da take mishi.
Rashin dacen Yusuf da iyayen kirki yasashi fad'awa cikin wannan hali da kuma gurb'ataccen tunani.
Wato tun yana yaro d'an kimamin shekara goma sha biyu, ya tashi cikin wata 'wahalalliyar rayuwa', wanda shi yasanta kuma zai kirata da wahala.
Wato iyayenshi kanyi wasu abubu
agabanshi wanda sun d'auke shi shi yaro ne. Ba ruwan su, kasancewarshi a kusa da su baya hanasu yin wani abu daya shafi mu,amalar aurensu.. Sannan yana zuwa gidan abokanshi 'Turawa' yana ganin yadda suke yi.
Tunanin shi ya kulle da son gano hakan menene? Amma saboda k'arancin shekaru ya kasa ganowa, sai lokacin daya kai munzalin wasu shekaru 15 -16, kuma akayi rashin dacen yana da yanayin buk'atar hakan sosai. Alokacin ne kuma ya bazama nema wa kanshi mafita.
Yusuf nada k'awaye mata a makaranta wanda suke mu,amala tare, kasancewarsu turawa sai ra,ayinsu ya dace da na juna.
Sukanyi mu,amalarsu kamar babu banbancin 'Jinsi' a tsakaninsu.
Yusuf a lokacin nada budurwa 'Jessica' wacce suke soyayyarsu ta yarinta.
Mummy shi ta b'ata bude Diary nashi wata rana.
Yayi rubutu a cikin abin gwanin takaici, wanda ita hakan ya burgeta.

*'My Love Jessica and I'*
Our first time kiss was at school garden..
Rubutu ne sosai yadda abin ya faru, tsaf mummynshi ta karanta, amma ta share abin tayi murmushi.
Wai d'anta ashe ya girma haka?? 😡😒
Da irin wad'annan abubuwa ne kuke ganin rayuwar Yusuf da Hafsah zata tafi a Inuwa d'aya bayan kuma gefe ga Abba na shirin kafawa ya tsare??🤔
Anya ba ko dole wani daga cikin su yayi watsi da nashi ra,ayin ya bi na d'an uwanshi ba?
Idan hakane wa kuke ganin zai sauke nashi ra,ayin zuciyar YUSUF KO KUMA HAFSAH??🤔🤔
Muna Jiran ra,ayinku.
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to :Unique In Your Love Heart Members.
*AUNTY KHADIJAH (MK MAKEOVER💄💋)..GODIYA NKE,👏🏼 _KUMA MUNA BOOKING IDAN BIKIN HAFSAH DA YUSUF😅 YA ZO,_ KE ZAKI MATA KWALLIYA.*

Zamu hadu a page dinki na instagram #MK makeover.

*And also*
*D'AYA AUNTYN.*
*(AUNTY FATIMAH, MAMAN LITTLE MAMIE).. ALLAH Y A RAYA WANNAN BABY YA KUMA BATA GASHI IRIN NA FILLO KAMAR NAKI..*👍🏻👏🏼👏🏼



📄 *20*



*Washe gari* da asuba, abban ne da kanshi ya shigo ya tashe ta, kamar babu abinda ya faru..
A al,adarshi 'knocking' dama yake mata sai kuma ya tabbatar ta tashi ta bud'e kofa, sannan zai wuce masallaci.
Gabanta ya fad'i lokacin da taji shi yana kiranta, amma kuma hankalinta ya kwanta da taji yanayin kiran, dama baya d'aga muryarshi da asuba..
"Yaya,..Yaya, ki tashi kiyi sallah."
Ahankali ta mik'e ta bud'e kofar.
Tun da yaga ta bud'e ya juya.
Tayi hamdala a zuciyarta bata son had'a ido da abban nata.
Akan darduma ta zauna bayan ta idar da sallah ta, tunano ta ina zata fara tun karar Yusuf da maganar abbah ta ke.
Gashi ya k'wace wayar bare ta kira shi. Ta mik'e ta bud'e wata jaka ta dakko zoben da Yusuf ya bata, ta dawo ta zauna.
'Tun ranar da aka koma makaranta ta karb'a a wajen Mama tace mata, zata mayarwa da Basma, shine ta boy'e shi.'
Ta kur'a wa zoben ido, tana tunano wanda ya mallaka mata shi, ahankali kwallah ta cika idanunta.
Allah ka taimakeni.. Allah kasa kada Abba ya rabani da farin ciki nah!!
'Idan na rabu da Yusuf na rasa komai.
Ta janyo Diary d'inta da yake akan 'Bed side drawer' (gefen Gado)
*'Together forever'*
_Our love is built up with scriface and devotion.._
_I will not let it be possible..!!_
_And.._
_I promise you to be
_with you forever no matter what difficult and challenges I'm_ _gonna face.._
" _I love you my_ _Yusuf!_

Ta rufe Diaryn ta ajye, sannan ta mik'e ta nufi kitchen wajen Mama, tasan ita ma babu dad'i ta kwana.
Maman tana kitchen d'in kuwa.
Tayi sallama tare da cewa,
"Mama,Gudmorning"Maman ta kalleta
"An tashi lpia"
"Lpia lau."
"Bari in fere miki dankalin."
"Ok kiyi sauri to, kinga kada ku makara a school."
"Ta k'ara kallonta.
Idan kin gama kije ki bawa abbanku hak'uri."
"To Mama"
Tana gamawa ta mik'e ta nufi d'akin Abban, gabanta na fad'uwa.
A tsaye ta tarar dashi a falon shi ya rataya jakarshi yana shirin fita.
Tayi saurin durk'usawa har k'asa.
"Abba barka da safiya"
Ta fad'a kanta sunkuye.
"Barka, dai kun tashi lafiya?
Ya fad'a babu yabo babu fallasa.
"Lpia lau.
"To madallah"
ya fad'a yana shirin cigaba da tafiya.
Ahankali tace "Abba, don Allah kayi hak'uri kaji"
Ya d'anyi murmushi.
"Hmm, yaya kenan kinyi laifi ne?.. Ba kina ganin abinda kika yi dai dai ba ne koh?
Cikin raunin murya tace.
"Wallahi Abba ba haka bane, don Allah kayi hak'uri."
Ya juyo, ahankali ya kalleta sosai, sannan ya dawo ya zauna.
"To Me yasa kikayi haka?
"Babu komai"
" Um, dama na nunawa mama fa wayar"
"Tambayar ki nayi me yasa kikayi haka?
"Um babu komai"
" To a ina kika sanshi?
Anan ta d'an fad'a mishi yadda suka had'u da Yusuf d'in.
Da yadda ya bata waya.
Amma bata fad'a mishi sun tab'a had'uwa a wani waje ba, sai ma ta nuna ranar da suka had'u gidan Hajiyah shine ganinta na biyu ita da shi.
Abban ya d'anyi shiru sannan, fara mata magana cikin nasiha, don ya fahimci ita take buk'ata.
"Hafsah ke har yanzu yarinya ce, baki san me duniya take ciki ba.
Ba wai ina hanaki yin wasu abubuwa bane da nufin k'untata miki..Kin manta ni mahaifinki ne?.. Ki daina tunanin zanyi wani abu da niyyar takura miki kinji?
Ta gyad'a kai kawai.
"Ya cigaba.
"Idan kina son abu ki dinga tambayata ko menene shi, kinji yaya? Da kin fad'a min kina son waya da tuni na sai miki..
"Ina son kiyi karatune kinji.. Ko kin fi son in miki aure yanzu?
Tayi saurin girgiza kai.
"To, ki maida hankali kan karatunki kawai, in sha Allah zaki sami mijin da zakiyi alfahari da shi.
Ya mik'a mata wayarshi.
"Ungo saka min number shi.
Hannunta na rawa ta karb'a. Ita dai tana tsoron kada Abba, ya kira Yusuf.
Ta rubuta, ta mik'a mishi.
"Yauwa, yaya."
"Allah yai miki albarka.
Ahankali ta amsa da "Amin"
Ya mik'e.
"Maza ta shi kije kiyi shirin makaranta,nima yau da wuri zan fita.
"Abba a dawo lafiya"
Allah yasa.
Ya fad'a yana fita daga cikin falon.
Daya zo fita ta babban palour, yaran nata hayaniyar shirin Makaranta.

Suna ganinshi suka hau gaidashi. Abba "Gud morning".. "Abba ina kwana?
Ya amsa cikin fara,a yana shafa kansu
Mama ta fito da d'an sauri, daga kitchen.
"Barka da asuba"
"Barka dai."
"Am fita zakayi ne?
"Eh sauri nakeyi"
Bataji dad'in hakan da yayi mata ba, amma sai ta hadi'ye har da yi mishi murmushi.
"Adawo lafiya, Allah ya tsare."
"Amin.
"Sai na dawo.
"Ok bye"
Ta koma kitchen.
Yaran ma suka fara, "Bye bye abba Adawo lafiya.
Shima bai ji dad'in hakan ba, amma kuma so yake ya nuna mata laifinta. Don ya fahimci hafsah bata da laifi tunda da saninta take komai, kuma akwai k'uruciya atattare da ita.
Hafsah bataji dad'i ba Basma bata zo makaranta ba, taso ta kira Yusuf, ta fad'a mishi yayi shirin amsa kiran Abba. Kuma tana son neman shawarar Basma akan al,amarin.
Da yamma bayan abba ya dawo gida.
Mama ta ta tare shi. Babu laifi ya d'an saki jiki har yaci abinci.
Da daddare ne ta sameshi, yana d'akinshi yana wani aiki a computer.
Ta zauna kusa da shi.
"Abban Hafsah don Allah ka saurareni akan maganar nan.
Ya d'an tsaya da abinda ya ke ya kalleta.
Ina jinki.
Ta Kyautata muryarta.
Dama fa wallahi bada wani manufa na bata wayar nan ba, and wallahi na rantse bansan yarinyar nan tana zance ba."
Ya ajye Laptop d'in a gefe.
"Me kike son fad'amin, baki san tana zance ba, ya zanyi in yarda dake?
Bayan ke ta nunawa wayar?
"Eh ta nunamin"

_(kaji uwa😇👍🏼) love u mama nah_😘 #karima.
"So, sai na k'wace na kuma ce kada ta sake kulashi, yanzu lokacin yin karatu ne.
"Me yasa baki sanar mini ba.??
Kayi hak'uri bana son ina kawo maka damuwa ne, kuma lokacin ka dawo ne daga tafiyar dakayi, bana son ka damu kanka bayan kuma ga stress na office, then na zaci "I can handle it"
Amma ayi hak'uri.
"Hum! Yai ajiyar zuciya sanan ya d'anyi murmushi.
Mata kenan!! wato saboda ba,ason damuwata, sai akasa fad'amin matsalar da zata jawo babbar damuwa. #zancen zuci.


Afili kuwa ce mata yai. "Okey, ya akayi kuma kika bata wayar?
"Um, gani nayi ba babba bace wayar, kuma kada ta zaci ko ina zarginta ne, shine yasa na bata."
Ya d'an dara (dariya) kad'an. "Hmm Mrs habeeb kenan.
Sannan ya tausasa murya.
"Iya hangenki kenan, mata kuna da raina abu. Yanzu baki ga bata wayar da kikayi ya sa ta sami hanyar contacting d'in shi ba?
"Allah ya rufamin asiri iya gidan Hajiya appointment din nasu ya tsaya."
Ya fad'a yana 'yar dariya.
Baki san wani abu ba Ameenah, yanzu Hafsah gani take bata wayar nan da kikayi, kin bata damar contacting d'in yaron ne.
"Tayi shiru, yace
Baki gane hakan bane Koh??
Tayi d'an murmushin jin kunya, ita ina tunanin ta yakai nan.!
Sai kawai tace,
"Wai kana nufin sai Hafsah ta iya zuwa wani waje da saurayi??
"Hm, kina mamaki koh?
Ta gyad'a kai.
"Bana zaton zata iya yin haka"
"Hm, ki bar yaran yanzu Amina!
Ya saita muryarshi ta dawo 'Serious'
"Ni dai ina rok'onki da kuma baki umarnin, don Allah kada ki sake b'oyemin lamari makamancin wannan, domin idan matsala ta afku na rantse sai kinfi kowa shiga damuwa."
"In sha Allah zan kiyaye, ka k'ara hak'uri da ni"
"Idan kika yi hakan kin gama min komai."
Ya d'ora.
"Ina tsoron sha,anin samarin yanzu ne, akwai abinda nasani wanda ke baki sanshi ba, ki d'auka kula da kuma hak'k'ina ne dole in saukeshi, in sha Allah babu matsalar da zata gagareni kinji?
Ya k'arashe maganar da d'an murmushi.
Tayi ajiyar zuciya
"In sha Allah baza,a sake ba."
"Nagode sosai zaujaty!!, wasu abubuwan bazaki fahimta ba sai nan gaba. Yanzu kiramin Hafsan kiga wani abu."
Tace "To" sannan ta mik'e ta fita.
Tare da Hafsan suka dawo, ta zauna kusa da Mama.
Abban ya kalleta cikin sakin fuska yace,
"Hafsah kin fad'a mishi ina neman shi?
Ta girgiza kai ahankali.
Ya d'an had'e rai.
"To Meyasa?
"Abba babu waya,.. Kuma..
Sai tayi shiru.
"Hmm kuma me?
Da ya ake kike had'uwa da shi wato don ba naki ba ne kiran koh"?
Kwallah ta taru a idonta.
"Allah abba ba haka bane bansan inda zan ganshi ba."
"Hmm, kije gidansu mana."
Ya fad'a fuskarshi babu wasa.
Kwallah ta fara bin kuncinta tana zarya.
'Menene abba ya ke nufi kenan??
Kada dai har ya fara zarginta da zuwa gidan su Yusuf.
Sai yanzu ta yi nadamar k'in sanarwa ko da mamace tsakaninta da Yusuf, tasan zata fahimce ta.
Gashi yanzu hakan ya zame mata matsala cikin tarayyar su.
"Bazakiyi magana bane.?
Cikin kuka tace Allah Abba bansan gidansu ba."
Au,? Duk dad'ewar taku baki san gidansu ba.?
"To wacce unguwa yake?
Ta girgiza kai.
Sai yanzu ta tuna basu tab'a maganar inda gidansu yake ba.
Abba wallahi bansani ba.
"Alright."
Ya fad'a yana mik'a mata wayar shi, daya danna kiran Yusuf.
"Ungo yi mishi magana ta nan."
Mama dai idone nata kawai.

Ta karb'a tasa a kunnenta, sam bata san me zata ce mishi ba ma.
"Hello" taji ance daga d'aya b'angaren.
Ta d'an daburce.
Um am, hell.. "Salamu alaykum"
"Wa Alaykumussalam."
"Am Hafsah ce"
Oh! My sweet baby, mene ya sami wayanki ne, kin barni ina missing naki."
"Hmm, ta fad'a.
Sai wani rarraba ido take tana kallon abba da Mama.
"My baby inaso zanzo wajenki kawai ni dai yau"
Ta Kalli Abba wanda ya tsare gida.
Babu damar tace mishi kada ya zo, don bata son abba ya fahimci hirar da suke.
"Um, dama abbanmu nason ganinka"
"You say what?
Tayi shiru.
"Talk to me mana, Baby, mesa abbanki keson ganina?
Bata da mafita illa ta katse wayar, don haka tace "Okey, nagode, sai anjima."
A tare abba da Mama suka tambayeta "Meyace miki"??
Cikin in, ina tace,
"A wai yace in sha Allah zanzo."
Abba ya kalleta sosai.
'Ita Mama tuni ta yarda da zancen.
"Hum, shikenan tashi kije to"
Inji Abba.
Ta mik'e
"sai da safe.
Tana fita Abba ya kalli Mama,
"Bafa zuwa zaiyi ba!
Mama ta kalle shi da son neman k'arin bayani.
Ya tari numfashinta.
"Ki zuba ido ke dai"
A can B'angaren Basma kuwa..
Tana kwance kan gadonta shiru, wani tunani take. Ko na meye oho!
Wayarta da ke gefenta tayi k'ara.
Taja tsaki tare da mik'a hannu ta jawo wayar.
Ta ware ido lokacin da taga sunan mai kiran nata, akan 'Screen' wayar.
"H. Hamid'slove"
Tayi murmushi har da yin gyaran murya.
"Hello"
"Basmah gud evening"
"Hw are you"
"Am fine,
"Ok, please akwai magana da zamuyi dake, if you have time.
"Ok, no problem go ahead"
"Thank you.
"Am friend enki ne fa, she has a problem, bata saki jinkinta dani. I mean she always wants to make a difference between us, she always want to create a distance between us."
Basma tayi murmushi.
"Hmm, please be patient with her, I told you many times that Hafsah bata son kana mata abinda kake mata b'cause bata saba,ba..And yanayin naku ba d'aya ba.
"Nooo, I already know this, but why not if she loves me! ?
Basma tayi dariya.
Haha, no she loves you but she don't take care of you, as you want. And she will never do!!
Gaskiya na fad'a maka.
"Oh my gosh''.. Meyasa kka ce haka."? "Hmm k manta neh am her friend I know her more than you.."
Aransa yaji cewa gaskia ta fada.
"Kinaji nah,
Yanzu ma wani another problem enne, kinga fa yanxu munyi waya da ita, and she's telling me that daddy nata nason ganina!"
Cikin nuna mamaki sosai tace.
"To me yasa kun sami misunderstanding ne?
"No,
"Wllhi I don't know why yake son ganina."
"Hmm may be he wants to know Something about you, kasan ya hana ta kula samari, then itama naga bata son kana mata irin wannan abubuwan, so may be zaice ko kafito ne ayi muku aure"!!
Whatt??..are you telling me??..Hmm, impossible, I know I love her, but aure not yet gaskiya, barin fad'a miki bazan iya zuwa wajen abbanta ba"
Basma tayi wata irin dariya.
"Why not. kafito kawai musha biki!
"Hmm am telling you as her friend, please ki nuna mata she have to change her attitude, cause am tired da abinda take min, kuma I don't think zan k'ara zuwa wajenta, sai dai tana meeting ena somewhere na gaji fa"!!
Basma ta kisma wasu abubuwa wanda nima ban san su ba. (Sanin gaibu sai Allah)
Amma afili naji tayi dariya sannan tace,
"Alright" wannan shine solutions" Amma Advicebly kada kaje gidansu couse nasan halin abbansu!!
Anya Basma!! 🤔🤔
Thank you alot bye bye.. I zanje club at 12:00am
"Ok, hope to meet you there one-day!!"
"Kina zuwa ne?
"Yeah,
"Hafsah fa?
"Hmm, kana da son jan zance, ya za,ayi kaga wannan a club??
"Oh shut!!
Basma ta Shek'e da wata dariya.
"Bye bye"
"Ok, thank you u are important in my life."
"Hmm, kada ka damu"
Kawai tace.
Amma azuci cewa tayi.
"Sai ma na sami wata damar..
Ta ajye wayar tare dayin wani d'an ihu,
Sannan tace,
"Saura k'iris"
🤔🤔🤔
To me take nufi??




.
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔


Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*



📄 *21*


*Yau* da Hafsah taje makaranta, ta samu damar keb'ewa da Basma. Itace ta nemi su tattauna, 'don yau sai wai Basman ta nuna kamar bata santa ba. Itama Hafsan, sai ta d'an share, tasan ta da shariya wani lokacin. Sanan kuma fad'an Abba akan karatu ya shige ta, tunda ta daina yarda suyi hira da Basma, in dai ba 'break' aka fito ba.
Sannan kuma ga jarrabawar k'arshe dake tunkaro su.
Ita taje sit d'in su basman, basman na yin kwantan note d'in da bata zo jiya ba.
"Basma please ina da magana, akwai matsala ne fa"
"Hmm, H. Hamid kenan 'Queen of love"
ta kuma kallonta sannan tace, cikin rashin kulawa da zancen Hafsan,
"Kinga ina yin note ne, so ki bari sai anjima"
"Okay, but please hurry up it's urgent need wallahi"
"Hah, baki da dama!
Haka Basman kawai tace.
Hafsah ta mik'e,
"Bari nayi break kafin sannan kin gama."
"Okey" Inji Hafsah.
Ta tafi tana mamakin Basma. A saninta da ita note baya hanata hira, zata iya ajyeshi suyi hirar su, ko kuma tanayi suna hira.
"So ko itama mamanta ta mata fad'a ne?? Tayi tambayar azuciyarta.
Bayan ta dawo Basman tace bata gama ba, sai kawai ta rabu da ita.
Wasa-wasa har sati ya zagayo, kullum da uzurin da Basma zata kawowa Hafsah. Yanzu damuwar Hafsan ma d'aya ce, wato Yusuf, ta daina jinshi gabad'aya, tun ranar da ta fad'a mishi Abba na nemanshi, gabad'aya kewarshi ta dameta, har wata 'yar rama tayi.
Yau Monday kuma baifi sati biyu a musu hutu ba, sannan, cikin hutun ne zasu fara jarabawar 'WAEC'
Yau Hafsah tasawa ranta sai tayi waya da Yusuf d'inta don haka ta, je wajen Basma,
"Please B. Yunus, aramin wayarki wallahi I miss my dear very much, kinga abbanmu ya k'wacemin waya then, mun dad'e bamu had'u ba"
"Hmm, H. Hamid, yau banzo da wayaba fa"
"Oh my God!, yazanyi ne?
Mik'ewa tayi da sauri ta nufi d'aya raw d'in.
Wajen Aysha Tahir taje, tasan itama tana zuwa da waya lokaci zuwa lokaci.
"Pls Aisha help me ina son aron wayarki"
"Ok babu matsala, ta bud'e jakarta ta d'akko wayar.
"Ungo,
Hafsah ta karb'a. "Thank you, nagode sosai"
Aysha tayi murmushi ita bata da matsala, kuma jininsu ya had'u da Hafsah.
Can bayan ajinsu Hafsah ta zagaya. Guri ne mai shuke- shuke, tasan kuma ba,a fiya shiga ba don baya b'ullewa.
Fito da wayar ta sa numbobin Yusuf. Har wani rawar kai takeji yau zata ji muryar Yusuf d'inta.
Lokacin daya d'aga kiran ta kashe murya,
"Hello my dear"
Shima yaji farin ciki jin muryar Hafsah, yana sonta shima.
Ya d'an shagwab'e muryarshi.
"My Baby, kin yada ni, baki sona koh?
Cikin muryar jan hankali. Don yau sai taji ta rage jin nauyinshi, saboda kewarshi da ta dad'e cikinta.
Haba my baby, ina missing naka, wallahi baka ga yanda na damu ba, duk fa na rame, ko dai ka daina sona ne?
"Hmm, u always say that bayan kin koreni"
"Oh God, wane ni korar ka, haba baby please ka daina fada kaji"
"Gaskene fa, yanzu yaushe, rabon da mu had'u."
Sai yanzu ya tuna mata.
"Baby kak'i amsa kiran Abba fa, kullum sai ya min fad'a kuma ya tambayeni ina kake"
Please baby ki share, i can't, barin iya zuwa ba"
"To Meyasa?
"Abbanki zai min maganar auren koh?
"Noo dear, it's not wallahi kaga kawai yana son yasanka ne, aini Abba, bazai min aure ba a early shekaruna.
Yai ajiyar zuciya, "Gud, but ki share kawai in mun had'u sai na nemi ranar da zanzo."
"Thank yooouu"
"Yaushe ne zamu had'u to?
Yai k'asa da muryarshi sosai I missed you over, and I need you in ma side"
"Uumm, ta d'anyi shiru bata son ya mata magana da irin muryar, sai taji gaba-daya ya sanyaya mata jiki.
"Please Baby nah!
Ya fad'a cikin marainiyar murya.
"Oh, Kafad'amin lokacin da zaka zo wajen Abba."
Nace idan mun had'u, I will tell you, in kuma kink'i so I swear to God bazan zo ba."
"Oh, rufamin asiri dear, abba ya matsa min fa"
What do you mean by 'Ya matsa miki'??
You, I don't understand Hausa well,"
Hahh, tayi dariya sosai, sannan tace, "oh, ma British boy I love you,"
So I mean yana damuna akan maganar."
Yayi 'yar dariya, "Okeyy"
"Coming Friday, muna biki so, I think mu had'u can."
"No, u know fa banason taron jama,ah.
Idan kazo zan fito daga 'Hall' sai mu had'u.
"Gud idea ma baby I want you!
"Hmm,
Where is your friend, "Basmah"
'Tana class'
Okay please extend my greetings,"
Hafsah taji wani iri azuciyarta.
Kafin tace wani abu ya cigaba,
"She care about us,"
"Hmm, inji Hafsah, don abin ya isheta"
Yace ,
"Me zaki bani ne my Baby, please don't reject my request"
"What do you want?
"Please blow me some kisses!"
"Tad'anyi dif.
Bata son b'ata mishi rai a wannan lokacin. Muryarshi ta katse ta,
Ya d'an chanja murya,
"Why you always want to hurt me?
'Tayi shiru okay,
"Hmm, Okay, thank you..
Gabanta ya fad'i tayi saurin cewa.
"Am sorry my dear, I don't mean that, am sorry"
"Hm, kina ja min class fa"
"No,ba haka bane.
"I'm just trying to do..
Hmm, you are trying koh, sai kace zaki yi shooting da bindiga koh,?
Tayi dariya, kad'an tayi k'asa da muryarta kamar rad'a.
"Please forget it my baby, enjoy this "Muaan"😘
(😳 Hafsahh??🤔)

Shiko wani shauk'i yashiga, that's my baby girl I love you,"
Please need more"
"Tayi dariya am sorry,
"Bye,
"Thank you see you on Friday."
"Am gonna miss you baby nah!
"Bye!'
Ta lumshe ido, ta gaza cire, wayar daga kunnenta.
Ahankali ta k'ara furta "I love you my Yusuf!!
Ta janye wayar tana shirin b'oye wa ta hango english teacher na nufo wajen,
"Hey, what are you doing here?
"Am..nothing sir.
"Ke Banyarda ba,
Fito min da hannunki" Ya fad'a cikin tsawa.
Bata da mafita Illa ta fito da wayar ya kar'ba yana cewa "Stupid Girl"
Jiki a sanyaye ta dawo cikin aji, d'an farin cikin da Yusuf, ya sata duk ya gushe.
Ta nemi guri kusa da Aysha ta zauna.
Ta dafa hannunta.
Aysha ta kalleta kin gama wayar ne, ko fad'a kukayi"
Hawaye ya zubo mata kan kuncinta.
"Teacher Gajere ne ya k'wace wayar!!
Basma dake can baya ta riga ayshan magana,
"Tab' kema dai H. Hamid, doluwa ce sometime, kuma sai ki ka bashi.?
Hafsah dai tayi shiru, ita tsoron ta ma Abbanta, ya zatayi idan aka kirashi? Kenan anyi ta kamata da laifuka kenan?
Me Abba, zai d'auketa?.. In na lillahi wa innah ilaihiraji,un"
Muryar Aysha ne ya katseta tana cewa,
Wai ke H. Hamid meye na yin wani kuka? Kefa kin fiya abu, wallahi.
Ta sunkuyo ta rad'a mata a kunne,
"Please kiyi shiru, kin san fa, Basma 'yar rainin sense ce, sai ta rainaki yanzu ma fa sai wani murmushi naga tanayi"
Hafsah ta d'ago gami da

Please Login or Register in order to submit comment