Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

HADA DOCUMENTS DAGA
ESHAAT SMILER HOM OF HAUSA AND ENGLISH DOCUMNTS WHASTAPP 08066360176 FOR MORE







*MIJIN 'KWAILA* ����‍♀

sabon salo daga labarin *zahra adam ishaq*


"-chapter one-"

Ahankali yake tafiya da motar sakamakon yanda ya iske saitin bakin makarantar yaran yacika yakuma batse da dandazon yaran da'aka riga aka taso daga makaranta,ya d'anja gajeren tsoki lokaci guda yana kallon tsadadden agogon dake hannunshi ya taka burki kamar yanda sauran masu ababen hawa y'an uwanshi sukaja nasu burkin sakamakon dakatar dasu da yellow piper yayi.
Ranshi 'kwarai yana a dagulene koda yake ba abin mamaki bane ganin fuskar tashi babu walwala kusan dukkan na tare dashi sunsan dahakan duk da yake mutum mayen barkwanci lokaci kankane yakoma kamar wani horror abin tsoro ga kowa saboda yanda yakecin magani kullum idanunshi suna manne da farin gilashi saboda yanda ya matsama idanun nashi da kuka wanda har yazuwa yau d'innan yakasa dena kukan,
Baya zato ko tunanin zaidena kukan rasa jigon rayuwarshi dayayi a cikin watanni shidda dasuka gabata.
Yazuwa wannan lokacin yazama abin tausayi ga kowa to ai dolene dukkan mai imani ya tausayama d'an sangirin saurayin maicike fal da 'kuruciya akan fuskarshi da dukkan sassa na jikinshi,
Rashi yayi babba rashin dayake ganin bazai ta'ba samun tamka ko madadin taba.ZAHRA ADAM ISHAQ cikakkiyar budurwar dasuka sha'ku tun yarinta shine yaci kashinta da fitsarinta ya goyata a gadon bayanshi yamata soyayya dabai ta'ba yima wani mahalu'ki a duniya irintaba rana guda ciwon mara yayi fatali da rayuwar zahara yazuwa barzahu,
Adai dai lokacin da yarage saura kwana uku rak!
Daurin aurensu,
Yashiga rud'u mara misaltuwa dayawa yawa anzata ya haukace,amma dayake allah gafurune kuma rahimu saiya tashi kafad'unshi yakuma saka mashi dangana duk da ikirarinshi na dena kallon kowacce y'a mace da gashi tunda yarasa zahra.
Y'amma dayawa sunsha kawo kansu gareshi wasu iyayensu zasu kawo talla wasu text zasumai amma haryau baiga mai maye gurbin zahra ba,
Yashafi gefen fuskarshi daya tuna aneesa wacce tanace mashi kamar chewing gum saboda so,
D'iyar 'kawar mummy ce,
Ya girgiza kai batare daya ankare ba.
Kamar ance dashi ya kalli gefen damarshi ya hangota cikin dandazon yara sa'anninta kamar sauran yara akwai uniform bulu da farin hijabi jikinta sai y'ar jakar makaranta saqale a hammatarta,
Wata mummunar fad'uwar gaba ta riskeshi lokaci guda ya cire gilashin fuskarshi yasake murza idanu gabanshi na bugun goma goma,
Dai dai lokacin data tsallako gefen dayake yara sun ragu sosai,
Tana tafe tana tsokanr yaran dake gefe da ita.
Caraf idanunta suka sar'ke cikin na ishaq wanda tuni anbasu hannu amma tsabar kallonta baimasan anbasu hannunba.
Tarin ababen hawa dasuke bayanshi suka addabeshi da horn hakan yasakashi waigawa da sauri, lokacin wani har yayi mashi overtaken yana fad'in "amma kai wawane,idan kallon mata kazoyi toka bamu hanya mu wucewa zamuyi "
Ishaq bai tankaba yagyara parking mota zuciyarshi kamar zata tsage saboda tashin hankali.
Ganin ita yaketa kallo yasata cewa da 'kawayenta"ummilolo kukalli d'an 'kauye yanata kallona kutsaya kuga yanda zanmashi gobe bazai sake kallonaba,ummana tace mai kallon mutane mayene."
Saita lalla'ba kamar zata wuceshi sai dai tana zuwa saitinshi inda ya sauke glassa d'in motar ta tofa yawu, cikin sa'a kuwa ya sauka akan fuskarshi.
Sauran students y'an uwanta suka saki baki suna kallonta duk sun kasa tafiya,
Yayinda su ummilolo suka hau tsalke suna kyalkyala dariya.
Itama dariyar take don asukwane tabar wajen da gudu,
Tana zuwa tami'kama su ummilolo hannu suka tafa, kafin tacigaba dayima ishaq gwalo tanasaka hannayenta saitin kunnuwanta almar eho...ya numshe idanu yana tunano zahranshi a irin wannan lokacin tayi makamancin hakan gareshi, lallai batada maraba da zahra, hannu yasaka ya lakace miyon,ya sumbata zahra daban take, komai nata so yakeyi.
Bai ankareba ya hango zahra can kusa dawani matashi irin masu tallar agwaluma d'innan,
Ta mararaice fuska tace dame agwaluma "kai don Allah bani d'aya?
Me agwaluma cikin mamaki ya kalleta yace"kibada kud'i sai abaki agwaluma yammata."
Sudai su ummilolo sun 'kunshe baki sunason dariya suna tsoron bala'in zahra don sunsan akwai daru.
Ta murgud'a wa mai agwaluma baki,"nace kabani d'aya kawai."
Me agwaluma ya fusata yace"tunda ubanki yabani jari meze hana inbaki d'aya."
Tazaro idanu"la la la..kazagi ubana?
Me agwaluma yayi tsaki,
Aikafin ya ankare tuni ta duma wawa uku ta sura ta fece aguje da fad'in "pdp!!!"
Sauran yara dasuke tsaye sukace "wawaaaa!!!"
Tuni sun duma hannaye suna dumbuzar agwaluma,
Ganin yara sun kwashe agwaluma yasaka me agwaluma binta aguje bayan ya jefar da tiren dayazama empty.
Shegen gudu gareta ko barewa ta shafa mata lafiya,
Sauran yara sukad'au ihu "sai zahra !!sai zahra!!!!
Gaban ishaq dake kallon duk abinda yafaru yabuga da karfi.
Ya maimaita sunan ZAHRA???


��������

Aunty y'ar charas��
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN KWAILA* ����‍♀


chapter 2.





Gudu take kamar wacce zata tashi sama,
Ahaka tasha kwanar layinsu da yawa y'an unguwar sunsan halinta don haka suna ganinta suka fara dariya,
Wasu nafad'in "mai hali baya fasa halinsa zahra."
Saida ta kutsa d'an sirdad'en lungunsu kana ta dakata da gudun tana luliya agwalumar abango dafad'in"luliya-luliya danya awakin baba da dad'i."
Sai dai batayi auneba ta hango mai agwaluma a three thirty ya kutso lungun,
Hakan yasakata idasa fad'awa gidan kamar wacce aka cilla da kibiya .
Umma dake tsaye bakin band'aki da buta a hannu, zahra batamasan ta angije ummanba,ta danna d'akinta gami da gar'kama sakata.
Umma tabita da idanu,
Yayinda anty hafsat dake tsaye gefe tabita da tambayar lafiya zah....
Bata 'karasaba sukaga me agwaluma ya fad'o gidan,
Baikobi takansuba yarufama zahra baya zuwa d'akin datake ciki.
Anty hafsa cikin mamaki ta tareshi dafad'in"lafiya malam bakada hankali zaka fad'o cikin gidan matan aure bako sallama.?"
Yayimata kallon banza ranshi yana zafi kafin yace"aiba sallama ta kawoniba,wlh sai anbiyani kud'ina kokuma in karya yarinyarcen,
Yanuna d'akin da zahra take ciki.
Yayinda take lekowa ta window tana mashi gwalo,
Yakuma 'kufula,
Anty hafsat itama hararshi takeyi tana nuna mashi kofa"get out"
Ya kalleta da jan idanunshi"bansan wannan yaren ba."
Anty hafsa itama akwai masifa don haka tamike dafad'a,
"nizakama rashin kunya,wato kashigo gari ka waye haryanzu jahilcin kauye bai sakekaba,idan laifi akamaka kai ataka basirar da wannan cin maganin dakakeyi zaka kwatarma kanka y'ancine,?
Tajuya a fusace ganin yanda yake harararta,yana mata qunquni.
"bari inkira police idan yaso idan kaje bayan kanta zakayi bayanin abinda yashigo dakai gidan matan aure."
Umma tariketa tana fad'in"me yayi zafi hafsat,bansanki da hakaba,
Kifara tambayar abinda zahra tayimashi don bana raba d'aya biyu itace ta tsokanoshi.."
Umma tasake kwantar da murya tana tambayar me agwaluma abinda yafaru,
Idanunshi taf da hawaye, yake bama umma ba'asin yanda komai ya farun.
Umma tagyad'a kai tana fad'in"nasan za'a rina ai,
Nidai zahra bazan maki bakiba sai dai ince allah ya shiryeki,abinda kikeyi amma nagaji nagaji da halinki bari babanki yadawo a tattara amaidake can kauye inyaso kici gaba da halinki a can am.a nikam nagaji."
Tajuya afusace tanufi d'akin da zahra tuni ta danna mashi sakata.
Anty hafsa tazuge jakarta tafiddo da dubu d'aya tamikama mai agwalumar tana hararashi dafad'in"next time kasan yanda zakayi magana da nasama dakai ".
Shima hararta yayi,
Sai dai bai tankaba.
Anty hafsa tadafa kafad'ar umma wadda tazauna zugwui da damuwar da zahra ke sakata akoda yaushe,
Tace"umma pls banason ganin damuwarnan taki,kina sane da lalular dakike fama da ita,
Umma kamata yayi kinama zahra addu'a bawai yawan damuwaba."
Umma tasauke numfashi"toyaya zanyi kinasaje da halin yarinyar nan,khatta da sunan da yaran unguwa suke kiranta dashi wai *zahra'u mala'ikar yara inkin mutu ba ruwan Allah walakiri ya jibgi kayanshi*."
Umma taci gaba"sam idan kinga nasamu naji sa'ida to kuwa zahra tatafi makaranta toyanzu hatta da makarantar abin yaci tura iya shege kullum sabon salo take fiddowa,jiya Monday tafara zuwa makaranta js 1,take amma wai baifi wata biyu da shigartaba yara bakwai ta fasama kai da dutse,dacirema wata yarinya ha'kori,
Principal ta bugeta shine tatara yara bayan antashi makaranta sukayima motar principal ature,da 'kasa har suka fasamata glass din mota.shine fa akazo hargida dakorarta sukayi dakyar babanku yasamu ya mayar da ita suka amsheta ,amna saida yabiya kudin duka asarar dasukayimata kinga ayau har ta dakko wata maganar.
[9/20, 1:16 PM] mum meenat: Anty hafsa ta sauke ajiyar zuciya,
"nidai umma sainake ganin kamar lamarin zahra fa akwai sa hannu wannan abin datakeyi bafa normal abu bane,gaskiya is abnormal ne umma yakamata mutashi tsaye,yarinya saikace ana kad'ata da ruwan hanji sam zahra bata d'auko halayyarmuba."
Umma tace "kema kya fad'a ai,nida ace ba'a gida na haifi zahraba tozan iya rantsewa da Allah anyiman musayar tane batawa bace ba.gata sam bata d'auko kamanni dakuba,hakanan bata dauko halayyarkuba.
Ku shidda na gaifa allah ya dauki ran maza biyun dasuke cikinku sai kumata guda hud'u da allah yabarmun,duk na aurar daku ku ukku akan matakin karatun zamani dana addini dai dai gwargwado bamu tauyekuba,gakunan duka cikin rufin asiri amma zahra sam tazamo zakka acikinku,itabaga karatuba baga natsuwar ba,itakenan kamar tunkiya duk inda ta gifta sai ance kayya."
Umma ta'kare maganarta kamar zata fashe da kuka.
Da'kyar anty hafsa ta shawo kan umma,ta lalla'bi zahra ta bud'e dakin tanufi kitchen tadauko abincinta wanda tuni ya sandare saboda hucewa,
Tazauna kamar wata saliha tanacin abincin anty hafsa namata fad'a akan rashin jinta.
Itadai bata tankaba,
Har lokacin sallar la'asar yayi tatashi tayi wanka akaja wata kwasheshiyar jagira wadda tasamu matsugunni a gefen kunne,
Tad'auko janbaki jajawur ta dafsa bayan ta zagaye bakin nata da tarin ba'kin kwalli.
Tajuya da fuska tanama madubi murmushi tana tsuke d'an matsakaicin bakinta aganinta ba nabiyunta wajen kyau.
Duk da tana cikin 'kunci baihanata ganin kyawon nata ba
Sai dai aranta kullum tanajin haushin meyasa anty hafsa da anty salma kai harma da anty lubna duka suke farare tas,
Amma ita saitayo duhun fata,
Taja tsoki ita d'aya dafad'in"nadaisan dama ummanmu ba sona takeyiba shiyasa ta haifoni ba'ka.
Tasaka uniform na islamiyya check blue dasuka d'au guga sukayi luf dasu,
Tafito har lokacin umma bata dena fushi da itaba,
Takalli umman cikin kukawa tace"umma natafi,"
Umma tace"adawo lafiya sauran yauma akawomun 'kararki kinyi fad'a dawani mutum zaki bani labari."
Ta turo baki gaba,batare da tatankaba,
Umma tayi tsaki dafadin"shashasha kawai shekaru shabiyu amma fitinarki tafi ta masu shekaru ashirin."
Itadai gaba tayi abinta kamar yanda tasaba,
Tafito lungunsu tana gunaguni,charaf idanunta suka sauka akan na ishaq wanda ya sar'ke hannayenshi a kan kirjinshi yakafe kofar lungun nasu da idanu,
Duk da rashin tsoro irinna zahra saida gabanta yafad'i,amma dayake tsiwa gareta saita murgud'a mashi baki dafad'in''kurwa
ta kur namana d'aci,me d'a yaci d'anshi mara d'a yaci 'ko'kon tsuliyarshi."
Ishaq duk da baya jiyo abinda take fad'i shidai komai takecewa ahakan burgeshi tayi,
Yanason d'an murgudennan nata,
Ya numshe idanu daya tuno da zahra gaf da bikinsu yakafeta da idanu tayimashi murgud'e dafad'in "kallonfa,
Alokacin murmushi yasaki yanace da ita"nanda wata biyu saina tsotse bakin murgud'enanna naki."
Alokacin dariya tasaki dacewa"kai yaya ishaq,bakajin kunyata nifa kanwarkace".
Ya runtse idanu,kamar zai fashe da kuka afili yafurta "i really luv yhu zahra,inason koda mace mai sunankine bare kuma mai kammani dake."
Post everyday nsha Allah
September 20, 2017 at 7:31pm ·

��������

by
Anty yar charas ����
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN 'KWAILA*����‍♀

*to you maman Aliyu this page is for you*��



Chapter 3.


'karfe hudu na yamma dai dai lokacin da matashin ya cinna hancin motar tashi yazuwa cikin tanqamemen get d'in gidan,tare da matsa horn wanda yasaka megadin tashi da sassarfa yaxuwa bud'e katon get din.
Kamar almara ko mafarki haka baba yusha'u yake kallon fuskar ubangidan nashi dake cike da zallah nishad'i,
Yasake murza idanuwa aranshi yana ayyana'shin anma oga kyautar d'an mutum ne da kayanshi kome,?
Ganin yakasa aiwatar da aikinshi yasaka ishaq sake matsa horn da 'karfin gaske wanda yasaka baba yusha'u tale get din yana washe hakora dafad'in"barka ubangidana barka dazuwa isyaku na zahra baban zahra kaga angon zahra'u...
Isha'q ya numshe sexy idanunshi lokaci guda yanajin wani yanayi yana tsalga ainahin 'kasan zuciyarshi,
Ya'isada shigoda hancin motar lokacin daya saka hannu a aljihun jeans dinshi ya dumbuzo kud'in da bazai tantance adadinsuba ya dam'kasu ga baba yusha'u wanda tuni ya warcesu yana sake jinjinama isha'q d'in.
Yafito daga motar bayan ajiyeta a mahalinta,yana cilla key's din motarshi sama yana cafewa a tattare dashi akwai zallah nishad'in daya kwashe watanni shidda gam batare dayayi makamancin hakan ba.
Yakutsa kai acikin 'katon falon dayakai ma'kura wajen tsaruwa,dagani babu tambaya yasamu tagomashin dukiyarda tsayawa 'kididdigeta 'bata likacine.
Da sallama yashiga cikin falon idanunshi suka sauka akan 'katon kyakyawan hoton zahra wanda tayishi alokacin datake saukowa daga cikin jirgi,ajikinta akwai ba'kar suit saitayi roling white gyale akan wuyanta harzuwa kanta.
Fuskarta akwai full make'up don ita gwanar kwalliyace abinda yake karama isha'q kaunarta don yanason mace y'ar gayu.
Tasaki silent smile dake 'kayata fuskarta mai matsakaicin kyau.
Duk da ganin doctor ruqayya (wato mahaifiyarshi)
Baihanashi 'karasawa ga hotonba yasaka yatsanshi guda ya xagaye gefen kumatunta dake murmushin,lokaci guda idanunshi suka canja kala,
Yajuya kamar zaifashe da kuka,muddin zaidinga kallon hoton zahra bazai ta'ba kallon wata d'iya mace da gashiba,
Face zahra mai kamanni da zahransa.
Yadad'e tsaye jikin hoton yanason tabbatarma kanshi banbancin dake tsakanin waccen zahra 'karamar dakuma real zahramshi,amma yakasa gane koda abu d'aya dazai iya tabbatar mashi cewa bafa zahranshi ce takoma 'kan'kanuwaba.
Doctor ruqayya tatako a hankali zuwa kusa da d'an nata tadafa bayanshi cikin sanyin jiki da'alamar tausayawa kamar yanda tasaba.
Sa'banin da ayau fuskarshi fayau take babu tarin damuwarnan dake 'boye kyawon fuskar tashi.
Kama hannayenta yayi duka guda biyun idanunshi cikinnata duk da nata idanun suna manne da siririn farin glass din (medical).
Saida ya 'kawata fuskarshi da murmushi sannan yace"mummyna nasamu zahra..zahra tadawo gareni mummy awannan karon bazatayi nesa daniba,d'iyarki tadawo gareki mum....!
da hannu ta dakatar dashi"isha'q wai sai yaushene zakasan wanda yamutu baya dawowane,ayaushene zakasan cewar allah daya d'auki zahra yafimu 'kaunarta.saiyaushene zaka dena takura tunaninka da lafiyarka akan wadda babu ita a doron duniyane?
Zahra ta mutu, a gaban idanuna aka wanke gawar zahra.zahra d'iyar 'kanwatace nice na reneta tundaga ranar da mahaifiyarta ta haifeta batakoga fuskartaba takwanta tamutu,naso zahra na tausayama zahra nasani bayagani kaine mutum na biyu dayasha d'awainiya da zahra amma kasani zahra ba rayayya baceba.
Mutayata da addu'ar gafara dabeman dacewa don zahra mutumce guda harda 'kari
Ama yamuka iya'allah yafimu 'kaunar zahra ya amsheta a daidai lokacin damukafi bu'katarta,saimu bita da add'ua kaikuma kasaka dangana wa ranka ka rungumi 'kaddara matsayinka na musulmi nagari."
Bai katsetaba har saida ya tabbatar da takai aya,sannan yaaja hannayenta yaxuwa d'aya daga cikin kujerun falon yazauna yana fuskantarta,bayan yagama saita dukkan natsuwarshi gareta don ta yarda dashi takuma gane baizo da wasaba a wannan karon."mum wlh kiyarda dazancena mum,naga zahra ganin idanuna,zahra dai mum tana cikin students mum, a tattare da ita akwai yarinta nasani bawai ainahin zahrata baceba.amma inada tabbacin wannan itace zahran da zahrana take gayamun akoda yaushe,itace wacce zahra kefad'amun cewar _isha'q zaka samu zahra madadina koda bayan raina,zakasamu xahran da zata d'auke maka kewata.naro'keka da kobayan babu raina kajirayi xahra,kasota kamar yanda kake sona koma fiye da hakan._ _inamai tabbatarmaka itace alkairi a gareka._
Yaci gaba dafad'in"mum dani dake daduk wani ahali na gidannan yasan dahakan,mum kinatsu kituna maganganun zahra don allah kada kice wai bana cikin hayyacina."
Doctor ru'kayya tami'ke cike da tsantsar tashin hankali,tana zagaye katon falon hannunta goye a bayanta akan fuskarta akwai zallah damuwa dakuma rud'ani.
Sai dai kuma batasan tayaya zata'iya 'karyata isha'q a 'irina wannan lokacin dayazo mata da magana sahihiyaba.
A dukkan nazarinta dakuma hasashe irinnata tanada tabbacin isha'q yana cikin natsuwarshi ne.
Tasauke numfashi,itakam a dukkan tarihi ko'a mafarki kai a film's ko fili bata ta'ba ganin soyayya zahirinta irinta isha'q da zahraba,
Idan zahra tayi ciwo isha'q ko baya 'kasar shima saiyace bayada lafiya,
Kuma dsame inda zahra tafad'a yana mata ciwo.
Kai tasha jaraba soyayyar tasu tana ganin ko plane ne suka had'a mata amma inaaa,saitaga zahirin 'kaunane kawai dakuma had'uwar jini.
Sam bazata iya wancakali da bu'katar isha'q a wannan lokacin dayake neman taimako daga garetaba.
Tataka a sannu ta'isa gareshi tadafa kafad'arshi"bazan kiraka da wanda baya cikin hayyacinshi ba isha'q,nasani soyayya ba 'karya bace ba.
Koma dai menene kaci gaba da bibiyar yarinyar,nikuma zansamu lokaci kakaini har gidansu inganta da idanuwa don tabbatar da gaskiyar zancenka,kafinnan kasamama zuciyarka salama.zahra adam ta isha'q ce."
Yawani d'ane bayanta yana fad'in"tnx so much my luvly mother."
Ta murmusa kawai,gami da kama hannayenshi yazuwa dining don bin abinci.
**************
Zugar su zahra da'aka taso makaranta,kai dagani babu tambaya kasan yau akwai masifa,itada 'kawayenta duka zasu tseremata a shekaru amma tafisu yanayin girma,saboda jikinta irin ga'ba-ga'ba dinnan yake.
Su shidda reras duka suna fadanci wa zahra wadda keta ruwan bala'i ta d'aura kallabi saman hijabi taci d'ammara da dardumar dasuke xaunawa kanta a makaranta.
Bakinta har kumfa yake tana bamasu ummilolo labarin yanda zasuci uwar dije ali,wacce tasaka malam yayimata bulala biyu d'azu a aji.
Taraba yaran gida uku tace"ke ummilolo kune da hinda zaku shiga gidan saikuce a sammaku ruwa zakusha,daganan saikuce ina dije 'kawarmu tazo ta rakamu tana zuwa mukuma zamu la'be zaure mu'kunshe mata baki,mujawota aje lungun bata kashi.
Wlh saita gane batada wayo."
Sauran yaran sukace"eeeefaa haka za'ayi kuwa."
Sukatafi d'uuuu kamar garken tumakai,
Kafin sukai gidansu dije yamma tayi sosai,
Can wani kango suka hango almajiri yana kashi,
Zahrace tafara hangoshi taja dabaya da sauri,tace da sauran 'kawayennata"kutsaya kai ga al'majiri yana kashi,asamu d'an dutse a jefe takashin kashin."
Suka la'be suna lekenshi,can ummilolo ta dau dutse sauko a qeyyar almajiri,suna fad'in amma ka'iya kanannad'a maciji."
Kowando baigama sakawaba yabiyosu a guje,dayake ko barewa nan tagansu ta barsu almajiri ko 'kurarsu baiganiba.
Basuyi burkiba saizauren su dije,
Saida suka huta sannan suka gyara kamar natsattsu,ummilolo ce tashiga da sallama,innar dije na alwalar mangarib ta'amsa da kallon rashin sani akan fuskarta.
Ummilolo ta gaisheta ta amsa,sanna tace"don allah a sammun ruwa zansha".
Matar mai fara'a ta debomata ruwa a randa mai sanyi,ummilolo baki kawai ta d'ofana, ta mikamata kwanan dafadin "angode"
Matar tace"yauwa".
Tana juya baya ummilolo tayimata gwalo,
Sannan tace"ina dije yau banganta a makarantaba."
Matar tajuyo da fara'a tace"aiko na aiketa siyen manja aitadad'e da dawowa.kema naga kinmakara ko aikenki mamanki tayine.?"
Ummilolo tayimata gatsine dafad'in "uhm".
Matar tace "to ayimaza akai lada gida ko.?"
Ummilolo tajuya dasauri,tafita donyima ogarsu zahra albishir amma saita hango zahra ta nad'e 'kafar wando tacire hijab ta'ajiye gefe guda.
Tana turza 'kafafu a'kasa
Sauran yaran sunja masu layi 'atsakaninta da dije,
Dagudu ummilolo ta 'karaso ta bugi 'kirjin dije,sannan ta bugi na zahra tace"wanda yaji zafi ya rama."
Aikafin kace miye,zahra ta kaima dije duka"ninaji zafi."
Dije da tuni jikinta yad'au rawa tace"nidai bafad'a nazoyiba uwata ta aikeni,kuma inajin maganar uwata."
Zahra ta fidda manyan idanunta dafad'in"lalalala towaye bejin maganar tasa uwar?"
Dije da ido yacika da hawaye tace"kigane".
Zahra takaimata duka,
Nanfa fad'a yasar'ke,zahra 'karfi kamar doki nan danan tadunga sunkuta dije da 'kasa,
Yara sunamasu wa'kar "bamu rabawa sai dai mu'kara zugawa bugi cikin."
Zahra ko harwani 'kara za'kewa takeyi tana nusar ruwan cikin dije.
Isha'q daya dawo daga gidan abokinshi sadiq suna takowa a'kafa saboda hanyar batada kyau yayi parking motarshi acan farkon unguwar.
Yaci gaba dabama sadi'q labarin "abokina kai idan kaganta sam batada maraba da zahrata,"
Sadi'q yace"gaskiya abokina kakamu sosai wlh."
Isha'q yasaki dariyar 'kasaita dacewa"kawai kamanninta da zahrane yasaka naji wani mayen sonta,kai bayaga zahra banta'ba 'kaunar wata d'iya mace kanartaba."
Sadiq ya kwashe da dariya"gaskiya abokina koda banga girl dinnanba nasan mai zafice,don nasan bakayi da 'kwaila."
Isha'q ya murmusa...
Maganarshi ta ma'kale cik,
Sakamakon hango zahra dayayi da bataliyar yara suna dambe,zahra har 'kara over acting takeyi.
Sadi'q dake duban yaran yace"kai yarinyarcan badai masifa ba,allah tsine ranar da zata fito takoma ga allah batare da anrabata fad'a da yaraba.
Yarinya saikace shed'aniya,
Wannan zanga wandanzai kwasheta yakwashi bala'i.
Isha'q yaji 'kirjinshi yabuga dam.
muje zuwa guy's
September 21, 2017 at 12:05pm ·





������������
*Anty 'yar charas*��
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN KWAILA* ����‍♀





Chapter 4.


Isha'q yaji 'kirjinshi yabada dam,
Amma dayake jarumine saiya fuske gami da janye hannun sadi'q dafad'in "kayi abinda yadameka malam",
Sadi'q yasake kyal'kyalewa da dariya yana fad'in"allah yarinyar ce so funny"
Isha'q yaja tsoki bai tankashi ba,
Sai gab da isha'i zahra tanufo gida,'kirjinta yana bugun uku-uku aranta tana addu'ar "Allah yasaka umma bata tsakar gida,
Talala'bo tana sand'a lokacin datashigo gidan takalma a hannu bayan tafara zuro kanta taga gidan babu kowa.
Tafara tafiya sad'af-sad'af danufin fad'awa d'akinta sai dai batayi auneba taji umma tacafketa caraf ,
Ta waigo fuskarta da alamun tsoro,
Kafin tayi wata magana umma takifa mata mari.
Da tambayar "daga gidan ubanwa kike?"
Zahra idanu suka raina fata,
Tafara ro'kon umma"wayyo ummana kiyi ha'kuri bazan sakeba."
Umma tace"rufemun baki shashashar banza,bazan 'kara d'inkiba datana tasiri dayanzu namance dawata aba wai ita damuwa.meyasa kikeson sakamun hawan jinine zahra,abinda duka y'an uwanki basuyiba."
Umma ta'kare maganar kamar zatayi hawaye.
Zahra dai kuka take tana"allah umma nadena."
Umma bata bartaba saida tayimata ligi-ligi tasaketa,tafara haramar alwalar isha'i.
Zahra ta 'kyalla idanu taga umma tashige d'aki,
Hakan yabata damar sake ficewa gidan da saurin gaske,
Bazata mance kirarin dasukeyima kansuba wai *abuga asaki bata maganin d'an iska sai dai ta'kara taurin fata*.
Azauren su ummilolo tala'be,tana 'kwalama ummilolon kiran,
Hajara kishiyar innar ummilolo tafito tana masifa don tasan zahrace"kewai wacce irin ballagazar yarinyace,halan kekam uwarki bata kwa'ba maki.duka yaushe kuka shigo gidan amma dayake bakida tarbiyya harkin sake fitowa,to oya maza fice anan ummi babu inda zataje."
Shegiyar yarinyar yarinya mai kama da d'inya,ke ba'ka halinki ba'ki.
Zahra ta murgud'a baki dacewa "badai niba."
Inna hajara tace"sai ubanwa"
Zahra cikin rashin tsoro tace "ubanki"
Aiko inna hajara tayo kanta zahra tajuya da niyyar rugawa amma tuni inna hajara ta cafketa.
Mari biyu 'kwarara tayi mata, taci gaba dafad'in"duka iskancin dakikeyi 'kyaleki akayi.wlh kinshigo gonata ubanki zakici."
Zahra dayake ruwa ruwace tuni ta 'barke da kuka tayi waje aguje,
Takuwa koma 'kofar gida ta tara duwatsu tadinga yima gidansu ummilolo ruwan duwatsu,
Duk da haka bakinta bai sassauta da zagin datake d'urama hajaraba.
A tsotsayi d'an hajara yafito zashi kicin d'aukar abinci dutsen ya sauka akanshi jini sosai ya tsinke ganin hakan yasaka hajara kama hannunshi suka nufi gidansu zahra tanata masifa.
Zahra daganan zugar yaranta sukaja,suka la'be lungu ilai kuwa saiga inna hajara tadawo da abbalo ansaka mashi bandage,
Zahra da sauran 'kawayenta sukayi masu ature da 'kasa har cikin bakin hajara da idanuwanta.
Zahra data du'ka tana 'kyalkyala dariya tace"kuma wlh kisake dukana saina kama wannan d'an naki a islamiyya saina fasamai baki."
Inna hajara tace"tsinanniya kije zaki samu dai daike."
Zahra dake wani gantsarewa tace"tsinanniya tana bayan uwarta tanashan nono,"
Sauran yaran suka kwashe da dariya.
'karshe dai inna hajara ganin zasu kunyatata gaban mutane yasakata sulalewa tayi gida,acan tad'ora sabon bala'i tana sauke kwandon zagi akan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment