Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

MIJINA SIRRINA


[7/4, 5:13 AM]

El-hajj

_©HASKE
WRITERS ASSOCIATION (HWA)_
*​MIJINA SIRRINA​.....!*🌹
_(Labarin K'auna)_
**Based on a true life story**
_*NA​​*_
*_​​UMMI A'ISHA​​_*
_​Dedicated to Alh .I. Uba family​_
*_DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN
K'AI,Rabbishrahli sadri, wa yassirli amri, yafqahu
qauli.._*
_Shafin farko nakine pherty b~b.._
*​1​*
~~~ "Oyoyo yaya kabeer...,oyoyo yaya kabeer.."
Wannan shine ihun da yaran dake zaune cikin
tsakar gida suna wasa suketa faman yi daidai
lokacin da suka ga shigowar matashin saurayin
wanda ke sanye cikin farar shadda kansa babu
hula sai yar kyakkyawar suma da ya dan ajiye,
Fuskarshi dauke da murmushi ya rungume yaran
wadanda akalla zasu kai su kimanin guda hudu,
Daga inda take acikin kitchen ta sake lab'ewa
saboda bata son ya ganta duk da sanin cewar
dominta yazo gidan, sadadawa tayi ta buya a
bayan fridge gamida leka kanta ta window ta
yadda tasan bazai iya hangota ba,
Ganinshi tayi rike da hannun Amira da waleeda
kannenta sannan ga amir da husna atsaye sai
faman jajja masa riga suke suna tsalle,manyan
chocolate samfarin coconut chocolate ya debo
daga cikin aljihunsa ya mimmikawa yaran,
Sunkuyawa yayi wurin Amira saboda itace babba
tafi su husna wayo,
"Amira ina mama?"
"Tana falon abba?"
"Yaya NADIYA fa?"
"Tana kitchen mama tasata aiki.."
Murmushi yayi ya mike saboda yasan aduk inda
take taji shigowarsa shiyasa ta gudu ta buya,
Yana rikeda hannun su Amira ya bi hanyar da
zata sadashi da falon Abba,
Sai da ya tsaya yayi sallama mama ta amsa ta
bashi izini sannan yasaka kai ya shiga cikin
falon,
Mama yasamu zaune kusa da abba suna yin
hira gefe daya kuma kwanukan abincine da
abban yaci kasancewar bai jima da dawowa
daga wurin aiki ba,
Su walida da amira na biye dashi har cikin falon
sai da suka rakashi ciki sannan suka ruga da
gudu suka fita,wuri yasamu ya zauna kanshi a
kasa saboda kunya da kuma girmamawa,
Ganinsa yasa abba sakin fara,a tareda mikewa
daga kishingiden da yake ya gyara zamansa
yana murmushi,
"Kabeeru yanzu kake tafe? Barka da zuwa.."
Cikin jin kunya da sose sosen keya kabeer ya
daga ido ya kalli Abba,
"Ehh wallahi abba, shigowata kenan dama nazo
ne in gaisheku saboda kwana biyu ban samu
damar shigowa ba.."
Murmushi Abba yasake yi ya kalli kabeer din,
"Haba kabeer har yaushene rabonka da gidan,
nazaci ai jiyane kawai baka zoba amma ai
shekaran jiya ma kazo kodai ka manta ne?"
Maganar da abba ya fadice tasa mama tsoma
bakinta tana dan murmushi amma fuskarta babu
yabo babu fallasa,
"To ai Alhaji tunda yasaba zuwa kullum jiya
kuma baizo ba ai dole yaji kamar yafi sati daya
rabonsa damu"
Dariya abba yayi yakoma ya kishingida yana
kallon kabeer wanda ya gyara zama yafara
gaisar da mama,
Shiru falon ya danyi nawani lokaci saboda shi
kabeer nauyin mama da abba yakeji yanzu sam
baya iya sakewa yayi hira dasu yanzu kamar da,
Ganin yanata zaune shiru sai dai dan lokaci
zuwa lokaci abba yana sakoshi cikin zancen da
suke yi da mama yasashi mikewa,
"Abba bari naje waje.."
"To kabeer tafiya zakayi?" Abba yafada yana
gyara zamanshi,
"A'a ba tafiya zanyi ba waje zanje"
Fita yayi daga cikin falon cikeda kunya, yana fita
abba ya dubi mama yana fara,a,
"Nasan dama ba tafiya zaiyi ba wurin mutuniyar
tasa zaije.."
Shiru mama tayi batace komai ba saboda ita
kwata kwata bata son wannan maganar saboda
wani dalili wanda ta barwa zuciyarta ita daya
amma idan hali yayi zata bayyanar dashi ga
abban shima yaji, ganin taki zancen yasa abba
barin maganar ta hanyar shigo da wani zancen
daban domin ya fahimci duk lokacin da zaiyi
magana makamanciyar wannan wadda ta shafi
kabeer da nadiya mama bata bada goyon baya.
Yana fitowa daga falon abba cikin kitchen
yawuce, a bakin kofar kitchen din ya tsaya
saboda ganinta da yayi tsaye tana mopping
bayan ta kammala share cikin kitchen din,
Yarinyace yar budurwa wacce bazata wuce
shekaru goma sha biyar aduniya ba, tanada
hasken fata amma ba farace can ba, tana sanye
da atamfa kalar koriya dinkin riga da zani, daga
inda yake yana iya hango gashinta dake
nannade cikin dan kwalin dake daure akanta,
"Sannu da aiki.." Yafadi yana murmushi har
lokacin yana tsaye akofar kitchen din,
"Sannu da zuwa yaya kabeer" tafada ahankali
sannan maganar ma tayi tane cike da kunya,
"Yawwa sannu sarki aiki.."
Tunowa da tayi cewar bata gaidashi ba yasata
saurin dan rissinawa,
"Yaya kabeer ina wuni?"
"Bazan amsa ba har sai kin jiyo kin kalleni ido
da ido.."
Murmushi yasaki bayan ya furta mata hakan
saboda yasan ba karamin aiki ya hadata dashi
ba domin kunyarshi da takeji bazai taba barinta
ta iya hada ido dashi ba...
_*Ummi Shatu*_
[7/4, 5:13 AM] Humaira Khaleel: _©HWA_
*MIJINA SIRRINA.....!*🌹
_(Labarin k'auna)_
**Based on a true life story**
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to Alh .I. Uba family_
_Fatan alkhairi ga k'awata maryam qaumi,
kina raina akoda yaushe yan matan shaddad.._
_*2*_
aishaummi.blogspot.com
~~~Jin abinda ya fada ya sata sake sinne kanta
kasa tana kallon tiles din dake malale a kitchen
din,
"Bazaki gaida ni ba kenan in tafi ko?" Kabeer ya
fada har lokacin fuskarshi tana dauke da
murmushi,
"To ba na gaisheka ba kaki amsawa" nadiya
tabashi amsa tana mai sake juya masa baya
dan kar yaga fuskarta,
"Nadiya kenan wai wannan kunyar yaushe zaki
dainata ne? Kullum idan nazo sai ki gudu ki
buya alhalin nikuma saboda ke nake son zuwa
gidan nan, duk ranar da ban gankiba idanuwana
radadi da zugi suke yimin, kuma nazo sai ki
hanawa idanuwa tozali da kyakkyawar fuskarki?
Uhm nadiya? Dan jiyo mana.."
Badan taso ba ta dan jiyo dakyar tana kallon
kasa,
"Kinga kyankyaso nan a bayanki.."
Tun kafin ya karasa maganar ta dako tsalle
tabar wurin sai gata a bakin kofar kitchen din
kusa dashi, dariya ya fara yimata domin dama
yasan tana mutukar jin tsoron kyankyaso
shiyasa lokuta da dama yake tsoratata dashi,
Ganin yanata dariya yasata gane cewar ba
dagaske yake ba,
Fuska ta bata, "yaya kabeer ashe dama
tsokanata kake?"
Dariya ya sakeyi ya daga mata gira,
"Wasane matar yaya kabeer.."
Hannuwa tasa ta rufe fuskarta cikeda kunya
domin kowa adangi da haka yake kiranta tun
tana yar jaririya har ta girma, kowa matar
kabeer yake cemata,
"Yau ina ka bar hular taka ka taho haka?"
Sai da ya dan matsa kusa da ita sannan
ahankali yace,
"Wai duk zumudin zuwa ganinki ne yasani
manto wayata da hulata adaki har sai da nazo
nnpc sannan na ankara.."
Dariya itama tafara yi masa, yayinda shikuma
ya tsaya yana kallon yanda kumatunta ke
lobawa, hakan ba karamin burgeshi yakeyi ba,
"Kici gaba da dariyar bana son ki daina"
Tsagaitawa tayi daga dariyar da takeyi,
"Yaya kabeer na kawo kayi min assignment din
biology? Skeleton teacher dinmu yace mu zana
nikuma ban iya drawing ba"
Makale kafada yayi,"nima ban iya drawing ba.."
"Please yaya KB"
Jin abinda tace yasashi kallonta tareda sakin
wani tattausan murmushi,
"Dauko nayi miki"
"Yawwa yaya kabeer thanks.."
Rabawa tayi ta gefenshi ta wuce fuskarta dauke
da murmushi, juyawa yayi ya bita da kallo,
yanzu SS 2 take a secondary school alla alla
yake ta kammala domin so yake ya zama
mijinta sirrinta,
Yana nan a tsaye har ta fito hannunta rikeda
pencil, cleaner da note book dinta sai kuma
modern biology, tsayawa tayi ta bayanshi tana
kallonshi domin a zahirin gaskiya yayi mutukar
tsaruwa sam bashida makusa ko kadan.
Babu zato ya jiyo nan tayi gaggawar dauke
idonta daga gareshi,
"Yaya KB gashi.." Tafada cikeda jin kunyarsa
domin tasan yagane kallonsa ta tsaya yi,
Hannu ya mika ya karbi books din hannunta
sannan ya sakar mata wani murmushi, ahankali
ya furta,
"Ki ware idanuwanki ki kalleni son ranki kidaina
kunya saboda nidin nakine...."
Fuskarta ta rufe da hannayenta ta juya ta nufi
cikin kitchen tana cewa "kai yaya kabeer.."
Murmushi yayi kawai ya nemi wuri ya zauna kan
wani dan dakali dake zagaye da wasu flowers
wanda yake opposite da kitchen din,
Zana mata skeleton din yafara yi yayinda ita
kuma ta kafeshi da ido tana daga cikin kitchen
din bayan ta kammala mopping din da take yi,
Kallonshi ta tsaya take tayi ko kiftawa
batayi,dago kanshi yayi da niyyar yi mata
magana nan ya kamata tana aikin kallonshi,
Saurin kawar da kanta tayi ta juya zata koma
cikin kitchen nan yayi gaggawar dakatar da ita,
"Nadiya zo nan.."
Tana rufe da fuskarta ta karasa gabanshi ta
tsugunna,
"Meye kike satar kallona?? Ba nace miki idan
kina son kallona kawai ki kalleni kanki tsaye
batare da kunya ba..?"
"Nifa ba kai nake kalloba yaya kabeer" tafada
muryarta na rawa dan jin kunyarsa,
"To naji, idan nazana miki skeleton din ai basai
nayi miki labelling ba ko?"
Kai ta daga masa batare da tayi magana ba,
Murmushi yayi yaci gaba da zanen, "to bani
labari inji.."
"Yaya kabeer nikuma wanne labari na iya bare in
baka?"
"Ko na makarantarku ma idan kika bani ina so.."
"Ai makarantarmu babu wani labari acikinta"
"Kedai kawai bakya son ki fada min labarin
makarantarku..."
Kafin ta bashi amsa mama ta zo daf dasu zata
shiga kitchen domin dora tuwon dare, batare da
mama tayi magana ba tasaka kai ta shige cikin
kitchen,
Ganin mama yasa hirar tasu takare sai aikin
murmushi da suke aikawa junansu,
Littattafanta ya mika mata ya tashi tsaye yana
yimata wani murmushi wanda ita kadai ce ta
fahimci sakon da yake son isar mata,
Kitchen yabi mama yayi mata sallama ya wuce
batare da yayiwa nadiya magana ba amma
kuma yana ta kokarin aika mata da sakon
bankwana ta cikin idanuwansa sai dai ita ta
kasa kallonshi, tana tsaye tana satar kallonsa
har ya fice daga gidan,wucewa tayi ta nufi
dakinsu itada su amira,
Akan gadonsu ta zube tana mai tuno yaya
kabeer acikin zuciyarta duk da cewar har yanzu
bai bude baki ya furta mata kalmar so ba amma
tasan soyayya suke yi a boye ita dashi batare
da sun bayyanawa junansu sirrin dake cikin
zuciyoyinsu ba.
*_Ummi Shatu_*
[7/5, 3:35 PM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA
SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*HASKE WRITERS ASSO.*
**True life story**
*3*
aishaummi.blogspot.com
~~~Note book dinta ta bude tafara kallon zanen
skeleton din da yaya kabeer yayi mata, gefe
daya kuma kamshin turarenshi ne yake tashi
daga cikin littafin,
Bin zanen kawai take yi da kallo tana murmushi
wanda ita kanta bata san ko na menene ba
amma kuma zuciyarta tafi aminta da cewar
kawai na tsantsar farin cikine,
"I love you yaya kabeer.."
Tafadi ahankali tareda lumshe idonta,waleeda ce
ta shigo cikin dakin da gudu,
"Yaya nadiya kizo inji abba.."
Ajiye littafin tayi ta dauki hijabinta ta fita
saboda al'adar abbansu ce haka duk lokacin da
ya dawo daga office ko kasuwa to tattara
yaranshi yake yi a falonsa suyi hira masu wasa
suyi wasansu yana zaune yana kallonsu masu
karatu kuma suyi har lokacin sallar magrib yayi
a lokacin ne kowa zai dauro alwala yajasu jam'i,
haka sallar isha ma, wannan dalilin ne yasa su
nadiya basa fita ko ina idan ba makarantar
islamiyya ko boko ba sannan hakan ya haifar da
shakuwa mai karfi a tsakaninsu dashi,
Ahankali ta tura kofar falon abbansu ta shiga,
kishingide ta sameshi yana kallon labaran
yamma a tashar AIT, can gefe daya kuma Amira
ce da amir suke rubuce rubuce ajikin littafinsu
na makaranta da alama home work suke yi, sai
husna da walida daketa aikin mammatsa game
wanda duk karar game din ta cika cikin falon,
"Sannu da hutawa abba.." Nadiya tafada tana
kokarin zama kusa da abban nasu,
"Yawwa nadiya, kabirun har ya tafi ne?"
"Ehh abba ya tafi yanzu bai jima da tafiya ba.."
Shiru abban yayi ya maida hankalinsa ga kallon
labaran da yake yi, ita kuma nadiya wurinsu
Amira taje tasa ido tana ganin yanda suke yin
home work din har mama ta shigo ta iskesu.
K'arfe 9 nadare bayan su nadiya sun kammala
cin abincin dare mama tace suje su kwanta
domin har waleeda da husna sunyi bacci su
amir ne kawai idonsu biyu,
D'aukar husna nadiya tayi zuwa dakinsu ta
kwantar da ita akan katifarsu sannan ta sake
zuwa ta dauki waleeda taje ta kwantar da ita su
Amira suna biye da ita, gyarawa amir wurin
kwanciyarsa tayi ya kwanta sannan itada Amira
suka haye gadon dake cikin dakin suka kwanta,
Wayar mama dake ajiye a karkashin pillow dinta
ta zaro ta yiwa yaya kabeer plashing, kusan
kullum haka suke raba dare suna hira a wayar
mama amma ita maman sam bata taba sani ba
ita dai kawai tasan nadiya bata taba barin
wayarta ta huta mutukar tana gida sai dai idan
makaranta ta tafi to lokacin ne wayarta zata
samu lafiya.
Ko minti biyu da yi masa plashing din bata yiba
ya kirata,da murmushi akan fuskarta ta daga
wayar,
"Yaya kabeer kaje gida lafiya?"
"Lafiya lau nadiya, yasu mama?"
"Suna nan lafiya"
"Ya kunya?"
Dariya tasa saboda jin abinda ya fada,
"Yaya kabeer kenan kaima ai ya kamata ka rinka
jin kunyata.."
"Saboda me?.. "
"Saboda na cancanci hakan.."
Murmushi ya saki kafin ya bata amsa,
"See you, idan a wayane kibi ki isheni da surutu
amma idan nazo sai kiyi shiru ki kasa magana
kamar wanda zan kamaki"
Itama dariyar tayi, "to ba kaine ba"
"Nine me?"
"Kaine idan naganka sai naji nakasa yin
maganar.."
Dariya ya sake yi, "nadiya kenan.."
"Meya faru yaya kabeeru?"
Murmushi yayi saboda jin ta kirashi da kabeeru,
"Kin ganki ko? Bakinki ya iya fadin kabeeru sake
fada naji"
"Yaya KB.."
Dariya suka yi dukkaninsu musamman ma shi
kabeer din wanda yake cike da nishadi cikin
wannan dare,
"Yaushe zaka zo? Zaka zo gobe?"
"Yaushe kike son kara ganina? Duk lokacin da
kike son sake ganina zanzo.."
"Koda kuwa yanzu ne?" Ta tambayeshi tana
murmushi,
"Yes even now i shall come if you wish..."
"To ina jiranka idan har dagaske kake zaka zo
din"
"Dagaske kike kina son ganina yanzun..?"
"Kaji yaya kabeer da dawasa nake? Dagaske
nake mana"
K'arar bude kofa ta jiyo hakan yasata saurin
dakatar dashi,
"Ina zaka zo da tsohon daren nan?"
"Sabon dare dai ba tsohon dareba,wurinki zanzo
ki ganni"
"To yi zamanka na hakura da wasa nake yi.."
"Inama kiyi dagaske kigani idan zanzo ko bazan
zoba"
"Yaya kabeer kenan ai nasan zaka zo"
Murmushi yayi, "to yaushe zan kawo miki
budurwata ne ku gaisa?"
Jin abinda yafada yasata mikewa da sauri bayan
zuciyarta ta harba, nan taji wani shiru ya ziyarci
cikin kunnenta duhu ya mamaye ganinta yayinda
bacin rai ya lullube zuciyarta gaba daya.
*_Ummi Shatu_[7/8, 6:42 AM] Humaira Khaleel:
*MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin k'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
® *HASKE WRITERS ASSO.*
*_4_*
aishaummi.blogspot.com
~~~Hannu tasa ta danne zuciyarta gudun kada
ta faso ta fito waje,
"Nadiya... Yanaji kinyi shiru ko bazaki gaisa da
budurwar tawaba?"
Ajiyar zuciya ta ajiye ahankali, dakyar ta iya
sassaita tunaninta tayi magana ahankali,
"Yaya kabeer me zai hana ingaisa da ita idan
har ka kawo min ita?"
Dan murmushi yayi mai kayatarwa kamar yana
gabanta tana kallonshi,
"Ina fata dai har zuciyarki kika fada ma'ana da
zuciya daya.."
"Yaya kabeer kenan.."
"Nadiya kenan, nadiya yanmata"
Murmushin dole tayi kafin tayi magana,
"Yaya kabeer nafara jin bacci gashi kaga gobe
zanje school"
"Nadiya nifa da wasa nake yimiki banida wata
budurwa so karki dauka dagaske ne.."
Duk da cewar taji dadin maganarshi amma sai
ta basar,
"Kaji yaya kabeer da wani zance, to idanma
dagaske ne ni ba abin in tayaka murna bane??
Sanyayyen murmushi ya saki,
"Hakane to balle ma ba dagaske bane da
wasane"
Itama murmushin jin dadi da farin ciki tayi,
"Shikenan tunda kaji tsoro ka sauya magana.."
Yar dariya yayi wadda har tana iya jiyo sautinta,
"Nayarda naji tsoron..."
Juyi nadiya tayi taja bargo ta dan rufe rabin
jikinta,
"Yaya kabeer zan barka haka yanzu saboda
kasan gobe zan je makaranta"
"To ya nadiya babu komai, Allah ya kaimu goben
sai kin jini" yafada cikeda tsokana,
"Ok tom bye bye" tabashi amsa bayan ta lumshe
idanuwanta, katse wayar tayi lokacin da taji
yace "bye bye good night and have a nice sweet
dream"
Addu'ar kwanciya bacci tayi ta shafe jikinta, da
tunanin kabeer bacci yayi awon gaba da ita.
Washe gari da misalin karfe biyu nadiya ta
dawo daga makaranta dama ba makarantarsu
daya dasu amir ba su akusa da gida suke ita
kuma nadiya makarantarsu da dan tazara da
unguwarsu, a gaggauce ta shiga gida tana shiga
tasan cewar yaya kabeer yana gidan saboda taji
kamshin turarensa sannan ta hango takalmanshi
a kofar falon mama dan haka bata bari kowa
yaji dawowarta ba ta wuce dakinsu ta ajiye
school bag dinta ta fito ta shiga kitchen,
Abinci ta zuba ta zauna tana ci kamar ance kalli
window tana kallon wurin tayi ido biyu dashi
tsaye yana kallonta yana yi mata murmushi,
Sunkuyar da kanta tayi tadaina cin abincin,
murmushi kabeer yayi ya saki karfen dake jikin
window din,
"Kici abincinki dama kawai nazo ganinki ne, bari
natafi inyaso sai nadawo da yamma lokacin kin
gama laumar.."
Bai jira abinda zatace ba ya juya yawuce,
murmushi tayi ta tashi ta leka sai da ta
tabbatar da cewar yatafi baya gidan sannan ta
koma ta dauki abincinta ta nufi dakin mama
tana tafe tana cin abincin,
A falo tasamu mama tana shirya husna da
alama wanka tayi mata,
"A'a kekuma yaushe kika shigo? Jibeki kina
tafiya kina cin abinci, keda zaki yiwa wani fada
amma kece meyi"
Zama nadiya tayi saboda mama kamar yayarta
take sam batayi kamada mahaifiyarta ba kai
idanma ba sani kayiba zaka zaci ya da kanwa
ne domin kamar yadda abba yake jansu ajiki
haka itama maman ke jansu ajikinta musamman
ma nadiya domin kowanne abune yake damunta
to ita take fadawa sannan idan shawarane ma
da ita take yi,
"Hajiya mama kenan wallahi wata yunwa na
debo kuma ina zuwa sai na iske yaya kabeer
agidan shine nagudu kitchen na buya acan
nazuba abincin nafara ci, yanzu kuma da ya tafi
shine nadawo nan dan kisan nadawo.."
Tsayawa da shafa man da take yiwa husna
mama tayi tana kallon nadiya,
"Nadiya wai menene tsakaninki da kabeer ne?"
Nadiya jin maganar tayi tazo mata a bazata dan
haka tayi shiru tagagara bawa mama amsa
wanda har sai da mama ta maimaita mata
tambayar sannan tayi gaggawar zakulo amsa ta
bawa Maman,
"Mama babu komai kawai zumunci muke yi
tunda ni yar uwarsa ce shi dan uwanane"
"Nasani nadiya, amma bayaga wannan bana son
wani abu ya hadaku muddin ba zumunci bane"
"Amma mama saboda..."
Katseta mama tayi bata barta ta karasa abinda
take son tambaya ba,
"Ya isa haka bana son tambaya, ki maida
hankalinki kawai kici abincin da yake gabanki"
Shiru nadiya tayi taja abincin taci gaba da ci
tana ta sakar zuci saboda bata san dalilin mama
na rashin son wani abu ya hadata da yaya
kabeer ba amma
Koma dai menene sannu ahankali zata tambayi
Maman....
*_Ummi Shatu_*
[7/8, 6:42 AM] Humaira Khaleel: ® *HASKE
WRITERS ASSO*
*MIJINA SIRRINA...!*🌹
_(Labarin K'auna)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*5*
aishaummi.blogspot.com
~~~Bata kara bi takan maganar ba suka cigaba
da hirarsu ita da maman har ta kammala cin
abincin da takeyi ta tashi tabar falon ta koma
dakinta tana rikeda wayar mama, lafewa tayi
akan gadonta suna yin waya da yaya kabeer,
sun dauki lokaci mai tsawo kafin suyi sallama
nadiya ta tashi ta shiga wanka ta fito ta shirya
tasaka uniform din islamiyyarta domin karfe uku
suke tafiya su dawo karfe shida na yamma,
Hannen kannenta ta kama suka yiwa mama
sallama suka tafi, sai da misalin karfe shida da
yan mintuna suka dawo, dawowarsu tayi daidai
da zuwan yaya kabeer shi da wani abokinsa,
Nadiya bata bari sunga fuskarta ba tafara
gaidasu,
"Baiwar Allah ya kiketa boye kaine kamar marar
gaskiya,kodai bakida gaskiya?" Abokin yaya
kabeer din yace da ita,
"Kabarta kawai musty domin yar kauye ce" yaya
kabeer yafada cikin barkwanci da tsokana, ita
dai nadiya shiru tayi musu tana jinsu sai dai ta
lura wannan abokin na yaya kabeer wanda aka
kira da musty sai faman binta da kallo yake, duk
inda ta waiga sai taga yanata kare mata kallo,
Ganin haka yasa ta takura ta shige gida yayinda
yaya kabeer ya mara mata baya,
A soron gidan suka tsaya kowannensu fuskarsa
dauke da murmushin kauna,
"Yaya kabeer ina ka samo wannan abokin mai
shegen kallon tsiya?"
Dariya maganarta ta bashi dan haka ya fara
darawa yana kallonta,
"Wai musty? Abokinane unguwarmu daya
sannan tare muka yi karatu dashi"
Dan karamin tsaki taja, "Allah na tsani mutum
ya tisani agaba yayita kallona"
"To yanzu dai nayi laifi tunda har na kawo
wanda yayi miki abinda bakya so, ayi min
afuwa..."
Murmushi tayi, "ni ai ba laifi nace maka kayi
minba amma dai wannan abokin naka gaskiya
ya fiya kallo da yawa"
"To ai nabaki hakuri"
"Nahakura"
"To zan iya tafiya?" Yace da ita cikin tsokana,
"Zaka iya mana yaya kabeer..."
"To fara shiga gida nagani"
Wucewa tayi tana murmushi ta shige cikin gida
sannan shima kabeer din ya juya yafita.
Fuskarta dauke da fara'a ta shiga cikin gidan,
zaune ta tarar da mama da kannenta tana
yimusu shari'a wanda kusan kullum aikin kenan
amir da amira kamar zasuga hanjin cikin
junansu,
"Ke kuma a ina kika tsaya su Amira suka rigaki
shigowa?" Mama ta tambayeta idanuwanta
akanta,
"Mama yaya kabeer ne ya tsayar ni wallahi.."
Shiru Maman tayi ta mayar da hankalinta gasu
amir taci gaba da yimusu sulhu, yayinda ita
kuma nadiya ta ajiye jakar islamiyyarta ta shiga
kitchen domin ta jiyo tuwon da mama keyi ya
fara kauri alamun ya kama,
Itace ta karasa girkin sannan ta fito daidai
lokacin abbansu ya dawo nan kuma dukkaninsu
suka dunguma zuwa falonsa kamar yadda suka
saba.
Tunda musty abokin kabeer yaga nadiya yaji
ta kwanta masa arai domin yarinya ce mai
hankali sannan kuma mai nutsuwa gata da
kunya da ganin girman nagaba, gani daya da
yayi mata yasashi kamuwa da sonta dan haka
batare da ya shawarci abokinsa kabeer ba ya
samu mahaifinsa yayi masa maganar nadiya
domin shi dagaske yake sonta bada wasa ba
sannan son aure yake yimata ba na yaudara ba
shiyasa ma yake son mahaifinsa yaje ya
tambayo masa aurenta,
Aranar da ya sanar da mahaifinsa aranar yaje
ya samu baban nadiya daf da lokacin sallar
magrib, kasancewar abba mutum ne mai
karrama bako sai da ya karrama baban musty
sosai ya fito musu da ruwa sukayi salla kamar
dama sun san juna sannan baban musty
yafadawa abba abinda ke tafe dashi,
Shiru abba yayi kafin ya cewa baban musty zai
tambayi nadiyan ko tasan musty din inyaso duk
yadda sukayi da ita zai kirashi a waya ya fada
masa, anan suka yi exchanging din phone
numbers dinsu abba ya shiga gida,
Lokacin da yashiga falonsa nadiyan ya samu ita
da mama suna cin tuwo tare, su kuma yaran an
zuba musu taliya suna ci,
Sai da abba ya bari sun gama cin abincin
sannan yayi gyaran murya yace,
"Nadiya zo nan"
Kusa dashi ta koma ta zauna, "gani abba"
"Bakon da nayi dazu saboda ke yazo.."
Ras,ras gaban nadiya ya fadi saboda bata san
abinda tayiba,
"Abba laifi yace nayi masa?"
Murmushi abba yayi,
"Ba laifi kikayi masa ba nadiya, yazo nemawa
dansa aurenki ne, sunan yaron wai Mustapha
abokin kabeeru ne yayanki"
Ba karamin faduwa gaban nadiya ya sake yiba,
nan fuskar musty ta bayyana acikin zuciyarta
lokacin da ya kafeta da ido yana yi mata
wannan kallon kurullar....
*_Ummi Shatu_*
[7/11, 7:58 AM] Ummi A'isha *MIJINA
SIRRINAH...!*🌹
_(Labarin K'auna)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
® *HASKE WRITERS ASSO.*
*6*
aishaummi.blogspot.com
~~~Shiru nadiya tayi saboda bazata iya fadawa
abba cewar yaya kabeer take so ba,
"Nadiya ya naji kinyi shiru ne?"
Muryar abba ta dawo da ita cikin hayyacinta,
"Abba babu komai.."
"To Mustapha dai ya turo mahaifinsa tunda
babu wata matsala zan sanar dasu inyaso
yafara zuwa har kusamu ku daidaita"
"To abba" ta fada kanta akasa, ita dai mama
tana zaune tana jinsu amma har akayi aka
gama batace ko uffan ba,
Mikewa nadiya tayi ta fita zuwa dakinta gaba
daya tama rasa abinda yake yimata dadi acikin
zuciyarta, gashi bata son fadawa yaya kabeer
domin gudun sakashi cikin damuwa,please call
me ta tura masa nan take ya kirata,
"Yaya kabeer yau ban ganka ba"
"Nidinma yau ban samu ganin fuskar gimbiya
nadiya ba amma nasan dalili.."
"Wanne daliline?" Ta tambayeshi cikin dokin jin
abinda zai fada,
"Yau naje unguwa ne sai dazunnan nadawo
shiyasa ban shigoba, amma gobe sammako zan
dako da sassafe inyi karin kumallo da
kyakkyawar fuskarki"
Dariya abinda yafada ya bata dan haka tafara
dariya,
"Kaji yaya kabeer da abin dariya sai kace wani
abinci da zakace zakayi karin kumallo da
fuskata"
"Ni ai kinfi abinci, da ace za a ajiye min ke inyita
kallonki to da na tabbata bazanji yunwa ba.."
Wata dariyar ta sake yi har tana kokarin fadowa
daga kan gadonta,
"Yaya kabeer zaka sa cikina ya fashe dan dariya
gashi dama naci tuwo na koshi dayawa.."
"Wai wai, wai, overfeeding kikayi ai? Oya tashi ki
fara exercise ina jiyoki daga nan"
Tashi tayi tana dan murmushi,
"Allah yaya KB jina nakeyi nagaji nidai ban son
exercise dinnan.."
"To yi tsalle guda goma ina kirga miki, oya fara"
Tsalle tafara tanayi yana kirga mata har sai da
tayi guda ishirin sannan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment