Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


MIJIN BUZUWA complete
BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM MUNA GODIYA GA ALLAH DA YA BAMU DAMAN RUBUTAWA DA KARANTA WANAN LABARI UBAGIJI YADDA MUKA FARA LAFIYA MUKAI KARSHEN SHI LAFIYA .

KISHI DA BUZUWA SAI KA KWANTAR DA HANKALI KA KAI AIKI DA HIKIMAR KA WAYEWA DA ILIMI BAI FITAR DAKAI A GARESU, , , ,

GODIYA GARE KUMA KARANTA NOVEL DINA DA KUKE KOKARIN DAUREWA DA HAKKURI WURIN KARANTA LABARAINA WANDA ABUBUWAN DAKE YAWAN FARUWA A NAHIYAR MUCE MUKE TABOWA DON HASKA KAN YAN UWA DAMA MU DUKA.
NOVEL DINA NA KAUYAWA NE BABU YAWAN KARAYAN ARZIKI A CIKIN SHI SAI DAI ABINDA LABARIN YAZO DASHI BABU FAYYACE FITSA A FILI YADDA WASU KE SON IN SAUYA ZUWA HADI DA FITSARA NA KASANCEWAN MACE DA NA MIJI A GADO A HAKKAN KUMA NAKE DA DINBIN MASOYA MASU KARANTA SHI A HAKAN, GODIYA GARE KU HAR KULUN MASOYA DA MASU KAUNA NA.
GAMA SU SON NOVEL DIN ZAKU IYA KIRA NA DA WANAN LAYIN DON NEMAN KARIN BAYANI DARI UKU NE GA MAI SON BIYA TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK
09026931792 KO 08036959257


Hadari ne ya hade garin sosai baka ganin komai sai walkiya da kara kainan motoci a lokacin wanda suke haskawa don ganin gaban su.
A daidai wanan lokacin ne motoci guda uku da suka karyo titin a jera wanda ke nuna wani mai akwaine tafe a lokacin yadda mutane suke ta kaucewa a titin suna basu wuri.
Wasu daga bakin titi ke fadin yanzun haka ma ba maigidan bane tafe wanan fitsarariyar matan tashine haka da bata ganin kowa da mutunci a idon ta.
Wani gida motocin suka shiga a lokacin gini ne na zamani motan ne suka dan tsaya da alama magana akeyi da wani a cikin gidan.
Ba a dade ba suka wuce zuwa cikin gidan kai tsaye security ne suka fito don bude motar nan naga wata farar mata buzuwa ta fito tasha ado na fada da gani daga saman ta har kasanta kwaliya ne.
Doguwa ce sosai ga fari sai dai idan ka kura mata ido zaka iya gano farin ne kawai ke aki yake rudin mutane don kyau akwai kyau inda bamu matan mu na Nigeria masu kyan asali da dire bayan farin da gashi da kuma tsayi babu abin da suka dara matan Nigeria dashi na fannin kyauwo.
Tana wani tako ta shige ciki zuwa part din ta ta dan jima ciki ta fito tana kwala ma wata mata mai suna Labara kira da karfi .
Da saurin matar ta iso gareta tana dukawa tare da fadin hajiya barka da zuwa an dawo lafiya yaya han, , , ,
Dakata tace wa matar yaya naga witan part din can a kunne ko mara zuciyar nan ta dawo ne kuma ?
Matar ta dago kai a hankali tace wa hajiya babba kike nufi waye hajiya baba ina nufin fatima matar wancan shiyan ta fada a fusace jin an kira uwar gidan nata da hajiya babba taji haushi.
Eh ta dawo laraba tace ai tun ranan da kuka wuce washe gari ta dawo kutawa tayi tare da juyawa da karfi ta shige part din ta a hasale.
Anan tabar laraba da kallon mamaki ta nisa tana fadin ikon Allah mata da mijin ta kinzo kin hana zaman lafiya a tsakanin su haka ?
Ita kuma a daki sai faman huce takeyi ita daya nan ta dauki waya ta kira mijin nasu da suka rabu yau ya tafi waje yin wani aiki.
Duk da tasan dare ne a duk inda yake amma bai hanata kiran shi ba a wanan lokacin saboda tsananin kishin dake damun ta a lokacin.
Kiran farko ya tsunke bata hakkura ba ta sake kira a karo na biyu bai daga ba sai wayan na gap da katsewa ya dauka da alaman barci yake a lokacin .
Murya irin ta masu barci ya daga wayan tare da fadin Nafisa lafiya kira da dare haka yanzu fa kin san dare ne nan sosai a wanan lokacin.
Bata jira ya gama magana ba tace watau munafuntana zakayi ashe kasan matar ka ta dawo shine baka fada min ba tun muna tare sai kawai in dawo in samu ta dawo gidan.
Ajiyan zuciya ya sauke tare da fadin tadawo fa ni ban san ta dawo ba don basu fada min da cewa zata dawo ba ma kit ta kashe wayan.
Ta wurga a gefen gadon ta tana fadi a fili duk sai nayi maganin shegun tsofin don sai auren nan ya mutu inga ta bakin naci irin nasu.
A daidai lokacin ne kuma aka turo kofan side din nata wata matace cikin dogon riga ta dora hijjab a saman rigan nata.
Fuska da murmshi tace mutanen Abuja ashe kuna tafe yanzu ne an sauka lafiya yaya hanya fuska a daure ta juyo tana fadin eh muna tafe ko idan zan dawo sai na sanar da wani akace ko ma ?
Ke yanzu don baki da zuciya dawowa kikayi duk da maigidan ya nuna baiyi dake saboda rashin zuciya irin naki sai da kika dawo kamar ana zama dole ne.
Matar tadan sake murmushin dabai kai ciki ba tace nake ganin ke nan haka amma ni nasan yana yi dani har gobe ke ce dai ganin ki ke rudin ki ga hakan don ko na bar gidan shi bamu rabuba don ga diya ga zumunci a tsakanin mu.
Fati ke nan zakiko ga abinda ba daidai ba wallahi in dan kin nace sai kin zauna min da miji don sai na rami ya fiki shan iska a gidan nan tunda haka kika zaba wa kanki sannu sugar mai iyali ko tasbi sarkin zumunci shida bakajan da daya bai biyo ka ba .
Murmshi tayi Allah na tare da mai gaskiya dama jin kin dawo ne yasa nazo taron ki da dawowa ba wani abu ya kawo ni ba a huta lafiya bata tsanmanin ta amsa mata ta fice daga dakin .
Zuciyar ta yana ciki da mamakin fitsara irin na Nafisa wanda sam babu kunya a cikin shi ko kadan sai zallah cin fuska da fitsara filli.
Daki ta nufa a daidai lokacin da ruwa ya gauce sosai a garin na kaduna kamar da bakin kwarya da sauri ta isa ta rufe mirrow da sauran abinda baison walkiya a dakin saboda tsaro wanda ba kowa ke wanan ba a wanan lokacin sai masu sani da hakan a baya suka saura rufe irin wa yan nan abubuwan a daki yayin da ruwan sama ke zubuwa daga samaniya don kariya daga fitinan walkiya.
Falo ta dawo ta zauna tare da yaranta dake cin abinci a wanan lokacin ido ta tsurawa yaran biyu sai da ba wai don tana kallon su hankalin ta yana gare ta ba ne tunane takeyi a zuciyar ta na irin rayuwan da ta tsunci kanta a ciki yanzu.
Tun shigowan Nafisa cikin su komai na rayuwan ta da mijin nata ya sauya sallo a lokaci daya ba yadda suka saba gudanar da rayuwan su ba suda yaran su da sauran yan uwa.
Hatta yaran yanzu a matse suke da zama gidan mahaifin nasu sun fison zama a gidan kakanin su da zaman gidan nasu saboda matsin da suke ciki a yanzu.
Ita dai tasan aure ne a tsakanin ta da mijin ta na soyayya tun tana karama soyayyan su ta samu asali don gidajen su basu da nisa da juna shi din abokin yayan ta ne.
Kuma akwai zumunci na makwabtaka da ya koma kaman na jini daya a tsakanin gidajen su tun kakan su zumunci ya kulu a tsakanin gidajen biyu.
Wanda yakai bako ba zai iya banbanta tsakanin su ba sai wanda yasan tushen abin koda ta girma bai daina kulata ba cikin yan uwa haka ya kai har aure ya kullu a tsakanin su.
Tayi haihuwan farko lafiya ga cikin na biyune ya samu aiki kano suka koma can sun koma bada dadewa ba ya hadu da Nafisa yar mutan Niger da suka shigo Nigeria neman kudi da iyayyenta ta lake mai tun bai kula ta har ya soma kulata don suna sayar masu da abinci a bakin ma,iakatar su ne.
Yaron ta ne dayazo inda take zaune tana tunane ya katse da da fadin mama daddyn mu bai dawo bane naga anty ta dawo.
Shafa kan yaron tayi taja sauke ajiyan zuciya tace bai dawo ba Affan da kaga ya shigo nan ai anty ce ta dawo ita kadai.
Yaushe daddy zai dawo mama yaron ya kara jefa mata tambaya kuma tace Affan ban sani ba idan ya dawo ai zaku ganshi.
Bai barta ta huta ba ya sake jefo mata tambaya again yace mama ai anty ce bata bari mu ganshi ko munje wurin shi sai tace mu fito muna damun shi yana hutawa.
Murmushi tayi tace kai Affan ba yana zuwa nan ida muke kuna ganin shi ba to may kuma kake so shiru yaron yayi kamar yana tunane a zuciyar shi.
Sai kuma yace ni mama ban ma son ya dawo saboda may Affan uwar ta tambaye shi yace saboda idan ya dawo sai ki ta kuka mama su kuma suna dariya da anty kuma su fita tare.
Affan ban son yawan surutu fa ka faye surutu ina jin tsoron wanan bakin naka kullu naji ka kara fadawa wani matsalan mu sai na yanke ma kunne daya.
Shiru yaron yayi yana tunanen kada uwar ta yanke mai kune kamar yadda tace din kayan da sukaci abinci ta kawar ta gyara wurin suka shige dakin kwanan su.
Da safe bata fito ba sai da ta gyara part din nata ta nufi kitchen don dafa ma yara abincin zuwa school sai ta samu kitchen din a rufe.
Dakin kwanan laraba mai aiki ta nufa a nan ta samay ta tace yau laraba lafiya naga kitchen a rufe Labara tace aikin hajiya karama ne hakan.
Nima na fito zan gyara tace na barshi taja kofa ta rufe nayi tunanen zaki fito don saboda abincin yara gashi kuma ta kulle kitchen din.
Dan jimm tayi tana tunane a ranta wai may Nafisa take nufi da ita ne haka abinci dai na kowa ne a gidan amma haka take mata idan ta bushi iska sai tace wai ana barnan abinci da yawa gidan.
Bayan abinci ma da take ita daya sai ta ba wasu balle yanzu da ya samu karin girma sosai a wurin aikin shi basu da talaucin komai a rayuwan su.
Muryan Laraba ne ke fadin sai hakkuri hajiya idan mutum ya ci gaban ka sai dai bi wallahi gama tana ganin ta samu miji a hannu sai abinda tace a gidan.
Ba komai Laraba na gode badin tura su can cikin gida wurin hajiya su karba haka ta juya ta wuce zuwa part din ta tabar Laranba a wurin tana jin tausayin ta.
Daki ta koma ta shirya yaran ta fito dasu da kanta ta mika wa kanin mijin su dake zaune dasu a gidan ya kaisu cikin gida wurin hajiya a basu abinci.
Yace yau kun makara ne tace eh salis koda na tashi har gari ya haska sosai wallahi kaga idan nace zan tsaya dafa masu yanzu sai su makara.
Ta koma ciki ya kwashe yaran zuwa gidan su dasu don duk a unguwa daya suke zaune da iyayyen nasu gida uku ne a haka kuma Nafisa ke tsula tsiyar ta a gidan.
Don tafi son zaman kaduna saboda anan kawayen ta suka fi yawa da yan yaren su na buza da suke kara zugata tana iya shegen.
Salis na shiga gidan kafin ya isa part din mahaifiyar mijin nasu da yaran matan gidan suka fara magana a, a su Affan ne haka yau da safe nan.
Salis yace eh maman su ta makara ne yau bata tashi da wuri tayi masu abin karyawa ba shine zasu zo nan su dauka.
Murmushi hajiya kubura tayi tace Fatice zata makara da safe kawai dai yar bakin halin gidan su ta dawo jiya akwai da wata a kasa.
Ba an mayar da Fati bata san tadawo ba shine ta dawo ta samay su bakin halin nata na banza ya tashi yanzu ta soma ke nan har sai ta kure ta ta tanka mata.
Allah dai ya sauwa dayar matar gidan ta fada daga daki tace shi kuma da yazo sai ya biyewa iya shegen nata ba daga daki suke magana.
Sun shiga gun kakan su tana ganin su tace ai na sani ba yar iskan yarinyar nan ance ta dawo jiya ba nan yanzu tsiya zai tashi a gidan wanan karo ko ba zan saurara mata ba wallahi.
Salis yace cewa tayi makara tayi fa bata samu dafa masu abinci ba yau yaya maganan ku yazo daya da na mommy ne ?
Hajiya bata iyayin magana ba sai jan yaran datayi zuwa cikin part din ta ta zuba masu abincin da tayiwa yan marayun jikokin ta da suke hannun ta.
Bayan ta gama sallaman yaran ne ta dauki waya ta kira Fati din tace wai may ke faruwa ne yau a gidan naku cikin fara a ta fara gaida surukar nata da bata ko tsaya gaisawa da ita ba.
Amsawa tayi sama sama dakyat tare da maimaita tambayan ta a gare ta tace hajiya makara nayi tace jinan fati na san komai walahi nasan abinda yar banzan yarinyarin nan zata iya.
A sanyaye fati tace hajiya ba haka bane makara nayi yau din ban samu dafawa ba kashe wayan hajiya tayi badon ta yarda ba.
Kashe wayan nata yayi daidai da shigowan hajiya kubura wurin ta tace sai gasu Affan na ga sun zo karban abinci kuma ?
Bari hajiya Kubura duk da uwarsu ta boye min na san akwai wata a kasa wallahi bai yuyuwa haka kawai taki tanadarwa yara abin zuwa makaranta.
Nan suka zauna suna maganan hajiya kubura tace idan ita fatin bata iya magana mu ba kyalewa zamuyi ba ai ana horo da yuwa ne kuma ?
Kai hajiya ta dafe tace Allah ya kawo muna karshen wanan yarinyar a gidan nan hajiya kubura tace amin tana mikewa tare da fadin bari mu gani zuwa rana idan har sun dawo nan kin ga hasashen mu ya tabbata ke nan ta rufe kitchen din nasu ke nan.
Ta fice ta bar hajiya a cikin bacin rai tana tausaya ma wanan rayuwa da yayan nasu suka tsunci kan su a ciki na bamin auren buzuwa da ya dorawa rayuwan shi yana zaune kalau da matar shi ya jajibo masu wahala haka.
A gidan Fati kuma bata karya ba tun safe ba tunanen kanta takeyi ba a yanzu sai tunanen idan yaran sun dawo may zata basu idomie ne ya fado mata arai ta sayo ta dafa masu suci.
Damay zaki dafa wani zuciya yace mata tsaki taja tana tausaya masu a ransu take tunanen da can baya lokacin tana ita kaida ya fado mata a rai.
Abinci sai wanda ransu ke so zata dafa da ita da yaranta da maigidan ta har sai taba makwatab wani lokaci yau kuma gashi a sanadiyar kishi da buzuwa har horo yakai ga a rufe store da madafar abincin gidan baki daya.
Babu wanda zata kara kai kara gareshi tunda baji mijin nasu keyi ba ko ta fada karshe ma ya dawo ya hauta da masifa gashi ita ba son masifa take ba a rayuwan ta.
Haka ta taso da tsoro sam bata fada ko kadan saboda ruwan ciki irin na matan hausawa da ta taso a cikin shi wanda a cikin tarbiyan diyan hausa yake.
Kamun kaina a diyan hausawa rasgin hayani da fada da mutane barkatai wanda akasarin matan hausawa hake ne ke cutar su a gidan mazaje su da gun kishiyoyin su yan bana bakwai.
Tana tuna yadda Nafisa tazo gidan daga ita sai ghana most go din yan kayan ta a ciki amma yau ta koma kamar wata hamshikiya a gida.
Auren ta da aka dauro ba tare da sanin iyayyen su ba can bariki suka dauro auren su da ita inda ta tare a gidan da yake a lokacin a kano.
Sannu a hankali har ya samu iyayyen shi suka hakkura ta fara shiga cikin su inda take baiyana harin ta na zahiri a hankali.
Da farko ta yaudari mutane inda taja yan uwan miji a jikinta duk suka yarda da ita ta gama jin sirin su kaf kafin daga baya data bunkasa ta fara fitar da kalan ta ga mutane.
Inda yanzu kowa ya gama gane ta wasu masu zuciyar imani sun gujeta masu kwadai kuma har wanan lokacin suna tare da ita duk da abin hannun ta bai ban baruwa wasan dadi sai kayi mata bauta kafin kaci abu daga gare ta.
Don haka take kallon kowa a wullakance sai uan uwanta dakan zo jefi jefi cin arziki wurin ta wanda ba a wuce wata daya basu zo gidan ba.
Tazo da wata yarinya da take cewa wai kaunar tane sai da tafiya yai tafi aka gane cewa yar tace ta cikin ta yarinyar.
Nafisa zata girmay ma Fati ga shekaru haka yasa tafi fati wayo sosai har take jin tsoron ga fin karfi ga sihiri don bata shigo haka kai tsaye ba sai da ta shirya ta shigo gidan .
Shi kan shi maigidan ba a banza ta barshi ko yanzu kuma bawai ta fasa abinda takeyi din bane sai ma abinda yaci gaba a cikin halayen nata.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
Ina isa na fara bude kofana na lokacin yarinyar ta iso da kayan da Yusuf ya bata tana mika min kallon kayan nayi sai na karba ta karasa min da sauran a cikin daki na.
Godiya nayi mata tace babu komai ai ana tare bayan na aje kayan na fada saman katifa na wasu hawaye masu zafi ne suke silalo min a fuska na.
Idan na tunana da maganganun da ya fada min masu zafi duk da nima din nayi karfin halin ramawa a lokacin sai nake ganin ya kwaraini da yawa.
Na dade a wurin ina neman hanyan da zan rama abinda yayi mun din don yaji zafin da naji ban kai ga samun mafita ba wayana yayi kara a lokacin.
Yusuf ne ya kirani sai da ta kusa tsukewa na dauka na kara a kunne na ina sauraron shi yace har yanzu kina fushi ne yar mama.
Daurewa nayi nace ai ban fushi dakai don bakai min komai ba yaya na yace dakyau ina son ki saurare ni dakyau magana nake so muyi dake yanzu.
Ina jinka nace mai.
Khadija don Allah ina son ki bani hankalin ki ki fahinci abinda zan fada maki yanzu naji na kara furtawa.
Don Allah ina son in rokeki wata alfarma wani aiki zaki nake son ki min a kan aboki na amma aikin yana da wahala sosai sai dai indan kin daure ba wani wahala a cikin sa.
To ina jinka Allah yasa zan iya kuma Allah yasa dai aikin bai fi karfina ba, murmushi yayi yana fadin bai fi karfin ki ba ma insha Allahu don zaki iya.
Nace fada min inji aikin idan ba zai shafe karatuna ba da rayuwa na zan iya insha Allahu yace good girl dama na dade ina neman mace irin ki mai gaskiya da zan saka.
Ba wani abu zan saki ba sai taimako rayuwan abakina Samad nake son in danka a hannun ki don kice a yanzu kadai nake da ita da zatayi min wanan kokari.
Nace ni kuma yayana yace kwarai kuwa ke khadija don ko zaki iya idan munyi laakari da irin halin ki na san zaki iya shiyasa na zabo ki.
Tun ranan da muka shiga dakin hajiya mama na fara ganin ki da kuma abinda yafaru dake da Nafisa matar shi kika tsaya min a rai.
Ban kuma gaskanta hakan ba sai da naga kin iya biyu su a motar su zuwa nan Abuja kuma komai bai faru ba yasa na kara yarda da abinda nake shirin yi din .
Sai gashi kuma yanzu abubuwa suna wakana a yadda nake son su tafi a tsakanin ku cikin hukuncin Allah komai yana tafiya daidai.
Khadija ko kin san ba macen da ta isa ta tsaya kusa da Samad tun lokacin da ya auri Nafisa buzuwar matar shi kuwa.
Nasan kin san matar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment