Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[5/6, 3:32 PM] ❣️DANGI DAYA❣️: 🌱DANA SANI🌱

Writing by Amnah el yaqoub


1


Aguje na shigo gida, koda wasa bana kallan gabana, ko ina sa kafata nakeyi ,mama na tarar a tsakar gida tana tankadan garin tuwo, da saurinta ta daga kai ta kalleni kawai ta girgiza kai tare da fadin "Allah ya shiryeki,
" kafin taci gaba da abinda take anty na husna ta shigo Aguje itama, tanata faman haki, kasan cewarta me Dan jiki, mama tace" husna menene?" Kafin ta Koro Mata bayani saida ta wankeni da mari, aikuwa atake nasa kuka tare da bibbiga kafafuna,
" mama kin ganta ko" harara mama ta watsamin, husna tace" mama tsokanata tayi, har yaushe zanci gaba da fada Mata cewa niba sa'arta bace, Amma taqi ji"
mama tace "ubangiji Allah ya shiryeku"
Ta dubeni tasake cewa "ke kuma jiki magayi,"
ta maida hankalinta Zuwa ga husna, "ina Aiken dana muka?"
Sai asannan husna ta kalli ledar hannunta sannan tabawa mama tattasanta, nide cike da haushi nayi cikin daki ina harare harare.


Ma'u kenan koda wasa batasan raini, akwaita da San girma inde kana so ku shirya toka girmamata, wnda nikuma bazan yi wannan ba, inde Fannin tsokana ne to bada ga nanba, kasan cewarta me jiki shiyasa nake tsokanarta da suna lakekiya, kokuma Ma'u, ita kuma abnda bata so kenan, tafisan husna, nikuma inde inasan wani Abu awajanta to anan zakaga ruwan biyayya, anty husna kamr abakina aka radata


Asalin labari
Garin zaria gari ne me cike da dunbin albarka, mahaifinmu malam mu'az (principal) Dan Garin ne, unguwar kofar doka jikin gidan firzin, iyayensa sun Dade da rasuwa, su biyu suka bari shida kaninsa hassan suma su biyu ne yayinda hussainin yarasu awajan haihuwar su, Ammu hassan baida aure yanade karatu ne ynxu, muna kiransa da Ammu ne kasan cewarsa qani awajan mahaifinmu

Mama kuma sun hadu da Abba ne amakaranta inda aka turashi teaching practice daga zaria Zuwa kano anan suka qulla soyaiya harta kaisu ga aure har aka samemu, ita din haifaffiyar kano ce, kuma bafulatanar asali, haihuwar mama ta farko ta haifi yan biyunta Mata hassana da hussaina, hassana ta rasu awajan qyanda saikuma hussaina ayanxu wadda nake kira da anty husna, saikuma ni danaci sunan kakata ta wajan uba Nafeesa, Amma Ana kirana da FEENAH







Mrs usman ce🖊
[5/6, 3:32 PM] ❣️DANGI DAYA❣️: 🌱DANA SANI 🌱

Writing by Amnah el yaqoub




3


Anty maimuna ita tayimin komai muka shiga hostel ina ganin mutane da robobinsu Amma kala ta banbanta suna tafiya Hall na amsar abinci, lebira yana binmu da kayana akansa, har mukaje wani hostel inda naga ansa P.T.A HOUSE, wata yar tsohuwa muka gani fara da ita, ashe itace me kula damu, naji anty maimuna tace mama yar yalwa ina wuni nima na gaida ta, anbani kwana da komai nashirya kayana wasu kuma nasaka su cikin loka, daga nanfa nafada tunanin gida, Allah sarki mama kome take yi yanzu? Dumin danaji a fuskata shiya tabbatar min dacewa kuka nake, ga wani Abu danakeji a maqogarona, "sannu" naji anfada, wata matashiya ce medan jiki na kalleta tacemin "kema new Comer ce? Nace" eh tace sunana Rabi'atu idan bazaki damuba zanso mu zama qawaye ni nazo ne daga Hadejia, kefa?"

Uhm nayi ajiyar zuciya nace Mata" daga Zaria nake, "

😳Ido ta zaro tace" gaskiya daga nesa kike," ta sake cewa" kiyi hakuri kidena kuka ahankali zaki saba muma da haka muka saba, kinga ni tun daga js 1nafara", Ido na zaro cike da mamaki, nace "bazan iyaba," tacemin "dande ba'a kawokin bane, wanne bangare zakiyi karatun"?

" Arabic"

murmushi tayimin tace" gaskiya ni ina S.T.Q ne (Senior Tahfizul Qur'an) ss1,amma kirki damu akwai qawata Zainab da take S.A.S (Senior Arabic School) zan hadaki da ita, batada matsala, saiku dinga tafiya tare harkisan kan school din,"

godia nayi Mata, tace" ga gadona nan Opposite din naki idan kina buqatar wani Abu,"

nace Mata" to. "

Ta Mike Zata tafi sannan tacemin" baki fadamin sunanki ba,"

NAFEESA MU'AZ Amma FEENAH ake kirana, tayi murmushi "nice name"


" shukhran" nafada Mata,

Tace " iyeeee gaskiya ne kaji yan Arabic,"

murmushi na maida Mata, ni shaf na manta da larabci nafada Mata, kuma hakan yasamo asali ne da musun da mukeyi nida husna agida, tayimin turanci in maida Mata da larabci, duk wanda baijiba munyiwa kanmu, 😃😃hawaye ne suka zubomin Allah sarki anty husna qawata yayata abokiyar fadana


** *** **


"Wai bazakici abincin nanba tun dazu kinsa kwano agaba Babu abinda kike sai tunani"

husna tace "mama wallahi nafisa nake tunani Allah sarki ko yaya take yanzu"
mama tace "toya za'ai husna, jinake jiya jiyan nan kika Gama cewa garama ta tattara yanata yanata tatafi," husna tace "to ai mama itace take tsokanata,"

"haka de kuka iya, inji mama, yi sauri ni kici kizo ki doramin kunun gyada babanku yakusa dawowa, banaso ya tadda ba'ayiba yafara fada, daga kai husna tayi, tana goge qwallar idonta, kallanta mama tayi, ita kanta daurewa kawai take Dan wani Abu takeji aranta kamar ta fashe da kuka, toya za'ayi, nafeesa kwata kwata bataji, tafiyarta school din shine kwanciyar hankalinsu.

** *** **
Cikin wata daya na goge, nasaba da mkrnta, saide kewar su mama danake kwana da ita nake tashi, kwanciyar hankali na shine ina tare da Zainab da kuma Rabi'atu, kokari na da kuma yawan surutu danake dashi shiyasa nayi jama'ah duk inda nabi zakaji Ana Feenah Feenah ba junior ba, ba senior ba, anty maimuna tunda na bata dubu dayan nan nace inji Ammu shikkenan kullum saita yabeshi, babanku yanada kirki Feenah gashi Dan kyakykyawa, nide kawai jinta nake ina Mata dariyar yaqe, to wanne kirki mutumin dayayi sanadin rabani dasu mama.

** *** **
Nayi suna sosai amakaranta har club nashiga na larabci wato Arabic Club, kuma hakan yaqara temakamin wajan sanin larabci na, haka kuma suna ji Dani da suka fahinci inajin larabci sosai yawan fitar da za'ayi kokuma wata drama to Dani aciki.
Ranar wata jama'ah muna dakinsu Zainab sani, nida Rabi'atu kaina Akan acinyar Zainab tanamin tsifa,tace" Feenah kanki badai gashi ba, infada miki wani sirri?"
Nace Mata" fadi,"

tace" wallahi har darura nake kicemin inyi miki kitso sbd kan naki yayi tsawo", kallanta nayi nace" lalle bakisan me tsawon gashi ba, tacemin "kamar ya" , nace wlh da kinga na husna bazakice inada gashi ba, tafini gashi, Ido ta zaro tacemin "a hakan" nace" yes, "tace" kai Feenah kinga fa gashinki"

nace" baby bazaki yarda ba sai kin ganta tukunta," haka sukai ta mamaki, muna firar club dinmu ne Atu tace "nifa Feenah wlh idan kina larabci har birgeni kike, bari kiji inde kikasa abaya kikai Rolling ko hmm kede kawai qawata "mafi kalam" (ba magana)" daria mukayi Gaba dayanmu" wlh Atu Allah ya shiryeki,"
daga karshe muka tafi yawonmu kasancewar juma'ah ce Babu abinda ake, saida muka tsaya awani bohol dayake gaban Dakin su Zeey wato Gumel house muka qaraci wasan ruwanmu sannan muka tafi, mune Arewa house, su Hadejia house da kano house, kasan cewar duk muna da friends acan sai wajan magrib muka tafi dakinmu nida Atu.


Mrs Usman ce 🖊
[5/6, 3:32 PM] ❣️DANGI DAYA❣️: 🌱DANA SANI 🌱

Writing by Amnah el yaqoub




2


Babu abnda nabari daga kamannin mama tamkar photo copy, yayinda anty husna tayi kama da abbanmu, ayanda mama take bamu labari itama hassanar anty husna suna kama da juna Sam bazaka gane suba.
Nikam kamar maman nadauko Hali nede ya banbanta fara ce ni tas da dogon hancina, inada yalwar gashin gira tare dana ido, ayayinda Dan qaramin bakina yake da taushi me launin ja, inada gashi dede misali Amma na anty husna yafi nawa yawa
Gaba daya na fitini yaran unguwa banda wasu qawaye na kirki sai marasa ji irina, ni kenan kullum cikin yawo tare dasu, qawata ta arziqi daya ce Amina yarinyar maqocinmu.
Shekara ta goma sha hadu matakin karatuna ynxu ne magana junior, ayayinda anty husna take 17years yanxu ne take shirin yin candy, ganin yanda na fitini yaran unguwa da jawa iyayena magana hakan yasa Ammu yace akaini boarding school ko suma sa huta da wannan abin fadar danake rabawa.
Hakan ce ta kasance da'aka tashi sai aka rabani dama jihar Gaba daya akai nesa Dani izuwa jigawa, bording school ta BABURA, kasan cewar tun muna yara nafi karfi ta bangaren Arabic, husna boko shiyasa tayi science nikuma nake Arabic school, inada kokari dede misali musanman ta Fannin larabci, kokadan bana maida hankali sosai Akan boko kawai nide larabcin Nan nasa agaba, ayayinda husna kuma ko ta'al bata saniba saide ta tambayeni itama tafisan bokonta.
Bamusha wahalaba Akan hanya kasancewar Ammu yasan jigawa kadan, hakan yasa muna Zuwa babura muka dau hanyar dazata sadamu da school din, mun danyi tafiya kadan sannan muka je gate din makarantar, dayake Ana kawowa dalibai shiyasa muma muna Zuwa aka Bude mana gate din muka shiga, akwai tafiya medan nisa kafin muka shigo cikin makarantar, muna Zuwa Aria class nafara gani sai kuma bishiyoyi dayawa, wadanda basuda cikar ganye, ina juyawa hannun hagu na na hango wani gate din na daban, wasu yanmata nagani guda biyu suna dosowa inda muke sukazo zasu wuce ta gabanmu, daya daga cikinsu ce take magana da yar'uwarta, muyi sauri muje hostel kar abusa karbar lunch mu makara adakemu, anan nagane kenan gate din hostel ne, Ammu ne yamusu tambaya su nuna mana office din da ake karbar sababbin dalibai, Babu musu suka nuna mana wani office, Nan muka nufa, tagaban wani class muka wuce naga ansa J.A.S 3B muka wuce mukaje office aka gamamin komai, hatta roba da kofi sun bani sbd karbar abinci, anan malamin yahadani da wata prifet sbd ta nunamin inda zan zauna da class dinmu, sunanta maimuna, Ammu yabani kudi yace indinga amfani dashi kafin suzomin visit, yabani 1k yace inbawa maimuna ,yaqara da cewar bazai min fadaba idan na musu laifi zasuci ubanane yaqara Gaba, daga nanfa idona yarena fata, ba uwa ba uba Babu yar'uwata mai sona husna.









Mrs Usman ce🖊
[5/6, 3:32 PM] ❣️DANGI DAYA❣️: 🌱DANA SANI 🌱

Writing by Amnah el yaqoub

Dedicated to Mrs Abdallah

4
Watana biyu mama Abba husna da Ammu sukazo ganina, nayi murna kamar ba gobe, kowa sai nan nan yake Dani, Ammu kuwa fuskar nan ahade "ke baki iya gaisuwa bane" nace" sannu Ammu ina wuni?" Bai amsaba

naje nakira musu qawayena harda anty maimuna suka gaisa, ina kallanta tana satar kallansa shima haka, nan kuwa basusan uwar yan sa'ido tana hankalce dasuba,🤣 husna ta taboni tace" autar mama nakusa candy fa,"
fari nayi da idona nace" wlh fadi ki qara nice farko nice qarshe," hararata tayi tace" a a kece qarshen de yarinya", nace" ina lissafawa fa tare zakuyi candy da anty na," tace
" wace antynki bayan ni," nace "aike ta dabance, anty maimuna nake nufi,"

"Ok" tace,kallan su mama tayi taga hankalinsu baya kanmu tace" ke wannan boss dinfa naga suna kallan kallo shida ita, koda wata aqasa ne? "
Nace" nima haka nagani," dariya tayi tace" intayi tsami maji," dariya mukasa harda tafawa, kallanmu mama tayi, aranta tace" me Hali baya fasa abinsa. "
Dazasu tafi kuka nasa musu, ina kallan Ammu tagefen idona yana harara ta, niko ko ajikina, Abba yayimin fadan karatu da fatan alkhairi, yayinda mama tayimin fada Akan cin abinci, tace" nafeesa gashinan baki rasa komai ba, Amma duk kinbi kin rame saikace yar gidan kamaye awun igiya, kinyi firit dake sai wani uban kwankwaso", dukanmu maganar mama tabamu dariya bnda Abba da Ammu da hankalinsu baya kanmu, haka suka tafi inaji ina gani, sai kuma kewarsu tadawomin sabuwa fil, Amma dana tuna saura befi wata dayaba muyi hutu sai naji sauqi.
Haka muka Gama term din bayan munyi jarabawa nazo ta biyar, cike da murna nadawo gida, kowa yayi farin ciki da dawowa ta, haka kuma su mama sunga canji atare Dani, mun baje afalo ina tabawa husna labarin bording, Ammu yayi sallama take muka shiga taitayinmu, muna gaisawa nabashi report dina, murmushi yayi yace yayi kyau saiki qara dagewa, "insha Allah" nace, yasakai zai fita mama tace "ga abinci fa,"
yace "yana dawowa."
Allah sarki sai gashi ya dawo da leda ahannunsa ya miqo min, nakarba tare da fadin "nagode,"

"gashinan kyaci duk kin rame sai uban qashin wuya" mama tace" kaima de kafada nafeesa batasan cin abinci. "

Araina nace" ai kaine ka ziga akaini school din," shide ya dauki abincinsa yayi waje, yana fita muka Bude ledar, kaza ce babba sai maiqo take, kai nida husna munyi party ranar mama tace" kamar Baku taba cin kazaba," husna a kace ai mama kazar Ammu daban take," tace "wato kun raina babanku hmm zaku hadu dashi ai, jiki magayi."

Dazai fitane bayan yagama cin abinci yacemin "ya gajiyar hanya ya qawayen naki?" Nace "suna nan kalau anty maimuna ma tace na gaida ka,"
be cemin komai ba yafice, aikuwa mukasa daria, nace" anaso Ana kaiwa kasuwa, "husna tace" hmm damafa ita yakesan tambaya, shine aka wayance "ya qawayen naki" tafada tana kwaikwayon maganar sa, dariya muka qara sawa.
Haka naci Gaba da karatuna a jigawa cikin kwanciyar hankali, Dan nalura da jihar akwai zaman lafiya, a term dinmu na karshe su anty maimuna sukayi candy, nayi kuka harna godewa Allah, tabani address dinta hade da number waya, nima nabata nawa, nayi kuka na rashin ta, danma da qawayena yan Amana zeey da atu





Mrs usman ce 🖊
[5/6, 3:32 PM] ❣️DANGI DAYA❣️: 🌱DANA SANI 🌱

Writing by Amnah el yaqoub

Dedicated to Mrs Abdallah



5...
Rayuwa na tafia lokaci na sauyawa, harna shiga ss 3,yayinda husna tasamu gurbin karatu a A. B. U zaria,tana karan tar "lab" a wannan lokacin kam, komai nawa yasake futowa, nazama yanmata boobs dina dede misali yayinda hips dina suke acike, naqara haske nutsuwa tazomin nikaina idan nayi kwalliya tsayawa nake ina kallan fuskata musamman idan naga nayi murmushi kumatuna sun lotsa, (dimple), nida husna bazaka ce yaya da qanwa bane danna tarota komai, nan kuwa tabani shekaru masu yawa kafin a haifeni shiyasa batasan raini.

"Zeey wai kukan nan be isabane, tun dazufa kike ta faman yi,"
"feenah Dan Allah kudena kuka,"
tafada tana goge kwalla itama, rabuwa kenan Babu dadi, anhadu daga gari mabanbanta gashi ynxu za'a rabu, munyi alkawarin ko bayan mun rabu zamu dinga zumunci, haka muka rabu kowa rai Babu dadi, munyi exchange din numbers tare da address, daga karshe akazo daukar kowa muka rabu cikeda kewa
Ammu ne yazo daukana shida wani abokinsa banma sanshi ba acikin abokan Ammu, muna tafiya suna firarsu, munzo wani gari suka tmbyeni nafeesa inane nan, nace musu STK ne (sule tankarkar) haka sukai ta tambayata garuruwa ina fada musu su Gumel dasu layin dazaka shiga Dan zomo,, su gagarawa, munzo round na wani gari gujungu anan bacci yafara fizgata, bansan kuma me suke tattaunawaba.

** *** ***

Kwance yake Akan bed dinsa qirar Italy, Dakin na kalla komai pink and blue ne, banga fuskar wanda yake kwancen ba kasan cewar yarufe duka har fuskarsa da wani farin tattausan blanket,yaya! Yaya!! Yaya!!! Tafada da karfi, dakyar ya Bude Zara zaran gashin idonsa, yasaukesu Akan ta, "Saudat yaushe zaki bar mutum ya huta ne,"

Dan turo baki tayi, tace" yaya momy tace infadama break fast is ready"
"naji" shine kawai abinda yace yajuya yaci Gaba da baccinsa, sai wajan eleven yatashi, dama haka yake, kasan cewar Babu abinda yake yi, bayan yayi wanka saida yagama shafe shafensa kamar wani mace sannan yafuto, iyayansa yasamu a main falo bayan ya gaida su ne momy tafara fadan data saba wato Akan rashin cin abinci da wuri, shafa kansa yayi cike da shagwaba yace "momy zan dinga cifa"
, yan biyu ne sukasa daria Muslim yace "yaya na shagwaba kamar mu" , bukhari yace "ai shima namiji ne shiyasa yake yi, dama maza ne sukeyi ko momy," harararsa tayi tace" ai sakarci ne yasa sukeyi din ba komai ba, "
Muslim yace" yaya wai hakane? ", dalla kuyiwa mutane shiru kamar dasu ake magana," momy bari inyi sauri inci abinci akwai inda zanje, abincin sa yakeci cike da nutsuwa dady yafuto da shirin office bayan ya tsugunna ya gaida shine, yace " my son idan kagama abinda kakeyi kuje ka raka saudat Zata duba exam dinta jiya tayimin magana nace tabari Zuwa Yau mugani, kadaure kakaita banaso tana driving da kanta ne" , amsawa yayi cike da ladabi, bayan yagama ne saudat ta futo sanye da atamfa Riga da sket, dinkin ya karbi jikin ta kasancewar ta fara, suka yiwa momy sallama suka tafi.
Iyalan sanata muhd marzuq kenan, matansa biyu yana zaune a unguwar sharada, marzuq farid Dan kasar masar ne balarabe ne na asali yana kasuwancin saida motoci daga masar Zuwa Nigeria, kuma sosai harkar ta karbeshi, yana yawan zama a Nigeria da matarsa saudat balarabiyar masar suna Nigeria Allah yabasu ciki suka reneshi a Nigeria har lkcin haihuwarsa yayi suka samu muhd, bayan haihuwarsa da shekara ashirin ta rasu, haka marzuq yayi ta renon muhd haryakai minzalin aure, bayan yaga hankalin dansa ya kwanta shine ya sake aure ya auri wata balarabiyar mai suna bara'ah, Amma ita tafisan zaman masar tace bazata iya nesa da iyayenta ba, shiyasa shima marzuq din zamansa yafi yawa a masar, shikuma muhd yace yafi San Nigeria inda yagama karatunsa yafada harkar siyasa har yakai matsayin sanata, saide suje masar ziyara shida iyalansa, matarsa ta farko hajiya hafsat tanada yara hudu Ahmad shine babba sai saudat dataci sunan kakarta wadda ta rasu, sai kuma yan biyu bukhari da Muslim, sai mamy hakima, tanada yara biyu mabaruka da maryam, gidan Ana shimfida zaman lpy Babu tashin hankali, haka kuma basa nuna banbanci Akan yaransu saide Akan Ahmad, mahaifinsa yana mutukar sansa, ya shagwaba shi duk abinda yake so yi masa yake, kodan shine babban dansa oho.
Yana wadaqa da kudi San ransa, haka iyayensa agaban kowa nuna masa kauna suke, Yau shine wannan mota gobe waccan, saide baya neman Mata haka kuma Babu ruwansa dasu shaye shaye na zamani kamili ne na gske haka kuma yatsaya Akan qannansa Babu wasa sosai yake kula dasu.
Ahmad yahadu qarshe ne wajan kyau Gaba daya shiya dauke kamar kakansa marzuq saide kawai launin fatarsa ne yadau na momy wankan tarwada ne, yanada doguwar fuska gashin idonsa gazar gazar masu tsawo tare da dogon hanci idan yayi murmushi gefen kumatunsa daya yana lotsawa yayinda yake Dan karamin lips masu laushi, ba shida jiki sosai, haka kuma Shiba ramamme bane, yanada tsawo daidai misali, Ahmad yahadu karshen haduwa gashida gayu, kuma sai gayun nasa yahadu da kudi, Dan haka yake facakarsa San ransa, duk kannansa farare ne bnda maryam shida itane kawai fatarsu take da Dan duhu Amma daka gansu kasan hutu yazauna musu, baya shiga sabgar yanmata shiyasa har Yau baida wata budurwa, shekarar sa 27 yanzu, yagama degree dinsa a masar wajan kakansa, yakaranci bangaren kasuwanci (business administration)

** *** **

Kinsan Allah feenah idan bakiyi sauri ba zamu tafi mu barki, turo bakina nayi nace kai sister ynxu fa zan Gama, tsaki tayi "haba mutum kullum baya gajiya da shafe shafe" wayarta ce tayi ringing ta amsa tace" hello sister aysha gamu nan fa ahanya", husna ce ta zare wayar tace" karyata ke aysha kinganta nan tana abinda ta iya, shiru tayi sannan naji tace karki damu ai Yau sai kwanan kano insha Allah, OK bye sai mun zo. "






Mrs Usman ce 🖊
[5/6, 3:32 PM] ❣️DANGI DAYA❣️: 🌱DANA SANI 🌱

Writing by Amnah el yaqoub

Dedicated to Mrs Abdallah


7


"Sister Dan shirya ki rakani gidan su khadijaty mana, tun shekaran jiya take ta damuna awaya inje, naqi Zuwa, shine Yau nace Mata gani nan ahanya tare da autar mama" ,nace
"khadijatyn ki qawarki ta Amana,"
tace "yes kinsan ni banasan kwashe kwashen qawayen nan kamar ki"
, dariya nayi nace "Allah sarki ni, aina kusa denawa insha Allah nima ina shiga babbar makaranta shikenan,"

tace "nikuwa ina qawayen ki su Zeey,"

"dazu ma munyi waya kalau suke"

"OK,"

Munje gidan su khadijaty yarinya me hankali tayi mana tarba ta mutunci, Babu ruwan ta, saida suka Gama firar rakinsu sannan mukadau hanyar gida.
Munzo daidai layin gidanmu mukaji Ana mana horn abayanmu, Babu wadda tajuya acikin mu, "haba yanmata inata muku magana kamar bakwa jina" juya manyan idanuna nayi nace "ayya ai kasan dayake ba jinsinmu daya da motor ba shiyasa mukayi tunanin da yar'uwarta kake,"
murmushi yayi yaga alama tanada zafin kai, husna ya kalla yace" to kuyi hakuri, nayi laifi nide sunana auwal kuma ina zaunane a kaduna, naga sister dinki kuma tayimin wlh ina kaunar ta Dan Allah ko zaku bani dama nasaukeku agida ta yanda zanga gidan namu?"
Husna lkci daya tayaba da hankalinsa Babu ruwansa da tarkacan nan irinsu tara suma na samarin zamani, tace" karka damu, acan baya kadan muke ai munkusa qarasawa, "
Yace" a a anty kode bakwasan shiga ne, Baku yarda daniba, "

tace" masa shknn, sis mushiga",

muna hanya yake tmbya ta number ta, nace masa" bnda waya," yacewa husna" wai haka ne anty, "murmushi tayi tace" karka damu zan baka"

, inajinsu yana tambayarta tanata bashi amsa akaina, daga karshe ta bashi Number ta, muna Zuwa kofar gidan, gabana yabada damm ganin Abba da Ammu atsaye, sum sum muka futo daga motor mukayi gida.
Juya motar yayi, shima ya futo su Abba suna tsaye suna kallan ikon Allah,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment