Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[07/07, 11:23 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍

        *RUƊIN DUNIYA!*

🌍🌍🌍🌍🌍🌍


*NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL*
_UMMUDAHIRAH_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

                  *P.W.A✍️*





*Romantic Book ne, kuyi haƙuri sabida salon labarin ne ya zo a haka; babu yadda na iya.*










_________________________

*BABI NA ƊAYA*
_______________ *KADUNA ZARIA*
            A garin Kaduna ƙaramar hukumar Zaria; anguwan tudun wada. Malam Iro me kifi, sana'ar sa kenan siyar da kifi. Gado ne da yayi wajen mahaifinsa marigayi, tun yana saurayi yake sana'ar wadda ta kai yanzu har Aure yayi a cikin sana'ar, kuma alhamdulillah yana samu dai-dai gwargwado kuma har ya rufawa kansa Asiri. Mahaifiyar sa tana raye kuma shi yake kula da ita tunda shi kaɗai ne ɗa namiji da suka haifa, sai ƙannin sa biyu mata waɗanda yanzu haka sun yi aure da jimawa, sai dai Allah ya yiwa ɗaya rasuwa a lokacin da zata yi haihuwar fari. Shi ya ci gaba da kula da matafiyarsu tare da nasa iyalan, wanda a lokaci ɗaya jinyan mutuwa ta tarar da mahaifiyar tace ga garin ku nan.

              Shekaru da dama sun shuɗe, wanda har ga shi girma ya soma tarar da Malam Iro; amma har yanzu cikin sana'arsa ta gado yake. Yanzu haka Allah ya albarkace sa da Yara huɗu Mata; wacce matarsa Harira ta haifa masa. A cikin rayuwar Malam Iro akwai dogaro ga Allah da tsantsan tawali'u, duk abun da Allah ya ba shi yana ƙoƙarin karɓa da hannu bibbiyu sannan kuma ya yi mishi godiya. Sai dai kuma matsala guda ɗaya ce a rayuwar sa da yake samu, wanda kuma a yanzu ta zame mishi babbar matsala da yayi sanadin soma gurɓata rayuwar ƴaƴan shi

Harira Mace ce mai tsananin son abun duniya, haƙiƙa duniya tana matuƙar ruɗanta wanda ta kai har ba ta iya bambance abu mai kyau da mara kyau a rayuwarta, ita burin ta kawai tayi kuɗi, me zata taɓa ya zama kuɗi? Sannan aina zata samo hanyar da zai kawo mata kuɗi? Shi ne tunanin ta a koda yaushe. Tun farko Harira irin matan nan ne kyawawa da Allah ya zuba musu kyau; kasancewar ta bafulatanan nan cikin Zaria cikin anguwan Fulani, tallen fura da nono take kawo wa nan cikin kasuwan tudun Wada, wanda har Malam Iro ya ganta kuma tayi masa a zuciya, babu ɓata lokaci ya bayyana mata irin ƙaunar da yake mata, to, itama bata ja zancen ba ta amince domin a lokacin kaf cikin samarin ta shi ne wanda take ganin yana da ɗan kyan gani da sura me kyau, duk da a rayuwarta ta taso da burin auren shahararren me kuɗi; kasancewar yanda ake ce mata tana da kyau, irin su masu kuɗi suko so, domin irin su ne ake ajiyewa a gaban mota, to, ga shi kuma har ta kai wannan lokacin babu wani me kuɗi da ya taɓa cewa yana sonta, tun tana saka ran zata same su domin ta ƙi aure tana jiran irin su, amma kuma shiru kake ji sai irin ƴan iskan samarin nan da suke kawo mata hari ko yaushe. Haƙiƙa ta ji daɗin shigowar Iro cikin rayuwarta, wanda babu ɓata lokaci ta ba shi dama ya tura gidan su, aka yi komai na al'ada aka sanya musu ranan aure.

             Bayan lokaci yayi aka ɗaura musu aure ta tare a gidan su, tana zaune tare da mahaifiyar sa. Sai dai tunda aka yi auren ɗabi'un Harira waɗanda be san su ba suka soma bayyana, Mace ce fitinanniya ga shegen rowa, ko abinci tayi ba ta ba wa mahaifiyarsa, sai dai idan shi ya dawo ya nema mata abun da zata ci, sosai mahaifiyarsa take kuka da irin halin Harira saboda kasancewar ta Mace mai haƙuri, haƙiƙa tana ƙunsan baƙin ciki a wajen ta, ga shi ko kaɗan ba ta ganin girman ta har zagin ta take yi tayi ta gaya mata maganganu mara sa daɗi, shi kansa Iro haƙuri yake yi da ita sabida shima irin mahaifiyarsa ne, tun yana tanka mata yana tsawatar mata har ta zo ta fi ƙarfin sa yanzu, domin a yanzu ta sake kilewa rashin mutunci sai wanda ya daɗu a gunta, bare yanzu tayi ƙawaye matan masu kuɗi masu hannu da shuni, a wurin su take koyo duk wasu abubuwa da bata san su ba a baya, ita rayuwarta kawai tana hangen waɗanda suka fi ta ne shiyasa kullum fitina ba ya ƙarewa a gidan su, kullum da abun faɗan da zata yiwa Iro, ya gaji dai ya ƙyale ta ya fita harkan ta.

             A haka rayuwa ta ci gaba da tafiya har Harira ta haifi ɗiyarta Mace ta fari, aka sanya mata sunan Ƙanwar Malam Iro da Allah ya karɓi abun sa, Nana Firdausi. A lokacin da Harira take da cikin ƙanwar Firdausi har ta kusa haihuwa, sai kuma mahaifiyar Iro ta rasu, sanadin da aka maida wa yarinyar sunan ta, Ummu Kulsum, suna kiranta da Ummu, ita dai Harira da sunan ta gatsau take kiran ta babu ko kunya. Bayan kamar shekaru huɗu sai ta ƙara haihuwar Mace, itama aka saka sunan uwar Harira, Fatimah suna kiranta da Zahra, sai kuma Auta da aka haifa bayan shekaru uku da haihuwar Zahra, sai dai fa tunda aka haifi yarinyar nan Harira ta ɗaura buri na duniya a kanta sabida ganin yadda yarinyar ta fita daban da sauran ƴaƴan ta, tsananin kyawun ta da kaf ƴaƴan ta basu biyo ta ba, duk kyawun Harira ta ninka ta a kyau nesa ba kusa ba, shiyasa tunda aka saka mata suna A'isha Humaira, sai ita Hariran take kiranta da suna Arab sabida tsantsan kyawun ta, kuma sunan ta ji shi ne a wajen wasu masu kuɗi da suka sanya wa ɗiyar su, shiyasa itama take ce mata Arab, shiyasa sunan ya bi ta har girman ta, wanda daga ita ne kuma bata sake haihuwa ba. A wannan lokacin Harira wacce yaranta suke kiran ta da Inna; babu irin sana'ar da ba ta yi don kawai ta farfaɗo da rayuwar ƴaƴan ta, kuma ta sanya su a inda zasu yi gogayya da yaran masu kuɗi, shiyasa tun suna yara makarantar kuɗi suke yi, ita take biya musu kuɗi da komai bata damu da sai Malam Iro ya bayar ba, wanda a yanzu shi kuma yaran suke kiran shi da Baba, sai dai idan ya samu kuɗi yana taimaka musu sosai tunda zuciyarsa bata mutu ba, bazai iya gani yaran sa suna rayuwa be da amfani a tare da su ba, sai dai bai da wani iko dasu tunda sai abun da Harira tace a gidan ake yi, tuni ta mallake shi domin har biye-biyen Malamai take yi yanzu.

            Tunda yaranta suka girma bata da wani buri a yanzu sama da su samo mata masu kuɗi, kowanne iri ne idan yana da kuɗi; to, tana son yaranta su samu, shiyasa bayan sun gama secondary school; Ummu da Zahra, sai ta saka su a nan F.C.E Zaria, duk sanda suka je makaranta suka dawo zata ɗaura musu tallan shinkafa su shiga cikin kasuwa suyi talla, ita a ganin ta idan suna yawo kwararo-kwararo hakan ne zai sa masu kuɗi su gansu har su zo gare su

Yayinda ita kuma Firdausi tana zaune a gida ta ƙi makaranta, sabida ita bata da buri sama da tayi aure, kasancewar rayuwar gidan su yana mugun ɓata mata rai, kwata-kwata ta tsani halayyar da Innarsu take shirin jefa su a ciki, shiyasa ita kaɗai ce ta fita zakka a gidan su, wadda ita ta biyo halayen Mahaifin su ne sak, shiyasa yake tsananin ƙaunarta saboda tana bin maganar sa, yayinda ita kuma Inna Harira ta tsane ta kuma ta fita harkan ta, dalilin da yasa tace, "baza ta biya mata kuɗin makaranta ta ci gaba ba tunda ba ta mata biyayya." Ita kuma dama bai dame ta ba bare ta saka hakan a ranta, duk da Babansu yayi mata alƙawarin, "idan har ya samu kuɗi a wannan shekaran zai saka ta sai ta riƙa bin ƴan uwanta". Amma ita furr tace, "ba ta so." Tace mishi, "ita aure take so yanzu, kuɗin da zai saka ta makarantar gwara ya siyan mata kayan ɗaki." Kasancewar tana da saurayin da yake neman ta tun tana secondary school, sun shaƙu da shi sosai. Ɗan Kaduna ne amma yana zaune da Kakarsa a nan

To hakan ya yiwa Baba daɗi, shiyasa ya samu Nafi'u saurayinta yace mishi, "ya turo magabatan shi."

Abu kamar wasa har aka sanya ranan aure kusan shekara biyu, a haka Baba yayi kurɗa-kurɗan shi har ya samu ya yi mata komai da uba yake yiwa ɗiyarsa

Ba tare da ko sisin Inna ba, tunda ita tace, "ta ƙi bin umarnin ta sai abun da take so zata yi, to ta je tayi auren idan hakan shi ne zai fishshe ta."

Haka kuwa aka yi auren lokaci yana cika. Aka kai Amarya gidan ta da ke can Kaduna, alhamdulillah Nafi'u yana da rufin asiri dai-dai gwargwado tunda yana aikin sa kala-kala. Haka dai ya fi ma Firdausi tunda tayi aurenta ta baro gidan su, su ma ƙannin ta tana fatan ace wata rana sun gane gaskiya su gane cewa Inna tana saka su ne a cikin *RUƊIN DUNIYA!* wanda hakan babu inda zai kai su sai dana-sani.

        Ƙaramar ƙanwar su wato Arab, wacce a yanzu tana S.S 2 ne, ita kuma Inna Harira tana mata awara ne da yamma tana siyarwa a can bakin layin su. Gaba ɗaya yaranta ban da Firdausi ta ɗaura su a tirban da take buƙata, kuma su kansu sun tashi idanunsu a buɗe basu da buri sama da su cikawa uwar su burin ta, su kansu suna jin haushi musamman ganin su a gidan ƙasa gidan talakawa, ga ƙawayen su duk yaran masu kuɗi, shiyasa basu da aiki sai ƙarya, idan ka gansu baza kace yaran talaka bane sabida suturun da suke saka wa, kamar baza su taka ƙasa ba don yanga da iyayi. A duk cikin su ukun; Arab ta fi su fitsara da rashin kunya, domin ita halin mahaifiyarta ta ɗauka har ta zarta ta a son kuɗi, dalilin da yasa kenan ta soma ba wa maza kanta tun a wannan lokacin don kawai ta samu abun duniya, ga ta da samari ko ta ina, duk inda ta gibta sai ta samu saurayi, sai dai ita babu aure a tsarin ta a cewar ta, "sai nan gaba, sai ta gama karatu sannan zata yi aure". Dalilin da yasa take gara kan samari kenan, ga shegen wayon; sai ta ci kuɗin saurayi kuma ta hana shi abun da yake so sai ta gama jan mishi rai ko kuma ta gama wulaƙanta shi. Arab kenan yarinya mai zamani wacce take cin duniyar ta da tsinke a yanzu, a duk faɗin tudun Wada da kewaye babu wanda bai santa ba, har kirari ake mata da sunan, 'Arab Matar manya, kin fi ƙarfin Yaro'.








✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️

          

         Yau ma kamar kullum yanda Inna Harira ta saba yiwa Arab awara domin ta fita mata dashi; hakan ne yau tayi mata, sai dai na yau ya fi na kullum yawa saboda ganin yanda ake ciniki sosai, ba ta daɗewa yake ƙarewa idan ta fita dashi, shiyasa tace wa Arab ɗin, "Autana yau da yawa zan yi miki tunda naga kina dawowa da wuri yana ƙarewa."

Arab tace, "ai kuwa Inna dama ina so in yi miki magana ki ƙara yawan shi don naga ba ya isan su suna son awara na wlh."

Baki Inna Harira ta washe ita kuma tana cewa, "ai dole ne su so awaran ki sabida daɗi, Ni na san na iya ai, ko kayan da nake kashe wa wannan awaran dole su riƙa santin shi."

Dariya daga Arab har Ummu da take jin su suke yi

Ummu tace, "Inna ai Ni ina ganin hannun ki ne mai albarka, ko abincin nan da muke fita dashi ba ki ga yanda ake wawa ba wlh, mu ma idan za ki sake yin mana sai ki ƙara yawan shi, ki haɗa ma har da kunun aya don shima ana yawan tambayar mu."

"To shikenan Allah ya kaimu goben za'a ƙara, dama ina ta tunanin siyan fridge wlh, to yanzu tunda kin ce haka kinga ban ga ta zama ba, yanzu ki taso ki shiga kasuwa sai ki siyo min abun kunun mu fara mu gani; Allah ya bamu sa'a."

"Amin AMin." Duk suka amsa daga Ummun har Arab

Sai Inna Harira ta kuma cewa, "yi sauri Auta ki shirya yanzu zan yanka miki ki wuce."

"To Inna." Arab ta amsa tana tashi daga bakin ƙofan da take zaune tana yankan ƙumba, ta wuce cikin ɗakin su, kayan jikinta ta cire ta ɗaura zani daga iya ƙirjin ta, kana ta fito kanta babu ɗankwali ta kamfaci ruwa a rijiya ta shiga wanka. Ta jima kafin ta fito tunda dama haka ta saba yin wankan ta, bayan ta shiga ɗaki ta gama shiryawa ta fito wajen

Ummu ta soma koɗata tana cewa, "iyen ba Ƙanwar mu, kin ga yanda kika tsatso kyau kuwa? Anya wannan baza ki haɗa gosilo a titi ba? Tirƙashi."

Dariya kawai Arab ɗin take yi tana duba jikinta

Yayinda itama Inna Harira sai washe baki take yi tana koɗa ta tana cewa, "ƴan matana ta fi na kowa kyau, iyee! Kin yi kyau sosai Auta na, na san yau akwai kasuwa kenan."

Fari tayi da manyan idanuwan ta tana taunan chewing gum ɗin bakin ta, yayinda ta furta, "sosai ma Inna, sai mun dawo kawai kiyi min addu'a."

"To Allah ya tsare Allah Ubangiji ya bada Sa'a, Allah yasa a samo mana rusheshen me kuɗi wanda zai kai Ni Makka bana."

"Amin AMin innarmu." Duk suka amsa suna dariya

"Ke ma tashi ki shirya ki wuce kasuwan nan kinga yamma tana yi." Tayi maganar tana kallon Ummu

Ita kuma Arab ƙaton farantin da aka jera mata komai, kama daga kan; icce, matsama, ashana, kalanzir, kafi-tankiya da Robbern zuba awaran idan ta tsame, duk suna kan farantin saboda ƙato ne, sai ta riƙe Robbern awaran a hannu tunda shi mai hannu ne, irin bokitin nan ne fari amma ƙato sosai, ta yiwa Innan sallama ta fice a gidan tana ci gaba da taunan chewing gum ɗinta, ƙararas-ƙararas kawai ake ji tana tafiya kamar zata karye tsaban yanga. Sai da ta ɗan yi nisa da gida sannan ta hangi Zahran su a cikin wata ƙatuwar jib ita da saurayin ta, shiyasa ta nufi wajen don ta ƙi wucewa sai ta kwashi rabon ta, tunda ta hangi wannan motan to akwai maiƙo a wajen, shu'umin murmushinta ta saki har da cije laɓɓa; tana wani gyara tafiyar ta cikin tsananin yanga ta nufe su tare da rangaɗa musu sallama

Gaba ɗayan su suka kalle ta suna amsa mata sallaman,
Yayinda Zahran tace, "Ah har kin fito Auta?"

Yatsina fuska tayi tana kallon ta tace, "eh wlh na fito, shi ne na hango ki nace bari in zo, dama Inna ce tace idan na ganki in amshi Naira ɗari biyu zan ƙara icce dashi, sannan kuma in siya yaji da sauran."

Zahra tace, "to ai Ni bani da kuɗi, ban fito da kuɗi ba, sai dai ki koma..."

Tun kafin ta ƙarisa zancen saurayin nata yace, "a'a Baby bari in bata." Sai ya sanya hannu a cikin Aljanu cikin sauri ya zaro kuɗi daga ciki, ƙirgawa ya soma yi

Yayinda Arab sai zuba murmushi take yi har tana ƙara leƙawa tana lanɗe baki, idanunta suna ware a waje tana ganin yanda yake sarrafa hannayen nasa wajen ƙirga kuɗin, a zuciya kuma tana taya shi ƙirga

Sai da ya ƙirga dubu goma cif kafin ya miƙo mata yana mata murmushi yace, "yauwa ƙanwata ga shi."

Ta miƙa hannu cike da yanga ta amsa still tana murmusawa tace, "na gode."

Murmushin ya kuma yi ko ƙyafta idanu ba ya yi a kanta yace, "babu komai ƴan mata yiwa kai ne, amma Baby ƙanwar ki ne da gaske?" Ya ƙare maganar yana mayar da idanun sa a kan Zahra

"Eh ƙanwata CE love, ita ce take bina kuma ita ce ƙaramar mu."

"Masha Allah gaskiya kyakykyawa ce, ga kama nan ma na gani sabida duk kuna yanayi ai."

Dariya kawai Zahran tayi,
Inda ita kuma Arab ta lanƙwashe murya tana sake mishi godiya

Yace, "babu komai ki je kawai."

Da haka ta wuce ta tafi; Zahra na mata, "sai ta dawo".

         Tana wucewa saurayin yace, "Baby gaskiya duk ta fi ku kyau wannan ƙanwar taku, wow! Allah yayi halitta a nan."

Haɗe fuska ita kuma tayi tana cewa, "to me kake nufi ne wai kake ta koɗata a gaba na?"

Murmushi yayi yace, "Baby Sarkin kishi, ai saboda tana ƙanwar ki ce nake koɗata a gaban ki, amma babu wani abu a raina, yanzu mu je shan icce cream ɗin ko mu fasa?"

Murmushi tayi tare da cewa, "mu je idan har baza a jima ba."

"No Baby baza mu jima ba wlh, just thirty minutes ma ya isa."

"Ok mu je."

Daga haka suka rufo ƙofofin motan sannan ya ja suka tafi.
     







_In ana comments za a iya ganin posting koyaushe, so ku ba da haɗin kai please, idan kuma babu wani comments ba na bukatar ƙorafi don Allah, duk sanda ku ka ga sabon update shikenan._
[07/07, 11:26 pm] OumƊahirah نفيسة: 🌍🌍🌍🌍🌍🌍

       *RUƊIN DUNIYA!*

🌍🌍🌍🌍🌍🌍


*NA_NAFISAT ISMA'IL LAWAL*
_UMMUDAHIRAH_

*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT 🧝*



*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞

```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

                  *P.W.A✍️*










_________________________

*BABI NA BIYU*
______________Wayanta ne ta soma Ring, sai ta ɗan dakata daga tafiyar yauƙin da take yi, tare da ajiye Robbern awaranta ta soka hannun ta a cikin Aljihun doguwar riganta; tare da zaro wayanta tana kallon me kiran. Sunan Besty ne ya fito ɓaro-ɓaro a kai, ba tare da jan lokaci ba tayi peacking tana karawa a kunne da cewa, "ya dai Besty?"

"Lafiya, ke nake jira tun ɗazu gani a wajen suyan ki, ko dai yau baza kiyi bane don naga time yana wucewa?"

Yamutsa kyakkyawar fuskarta tayi cike da yanga irin nata tace, "No gani nan a hanya ai, ina zuwa."

"Ok kiyi sauri da Allah, akwai labari wlh."

"Haba nawan?" Tayi maganar tana ɗan sakin fuskarta kaɗan

"You just have to come and see for yourself. "

"Ok. I'm coming" Sai ta zare wayan a kunnenta tare da zura ta a cikin Aljihun, sannan ta ɗauki Robbern awaran ta ci gaba da tafiya. A haka tana yi kamar baza ta taka ƙasar ba har ta fita layin gidan su, duk inda ta wuce gungun maza kallon ta suke yi, majority wasu gulman ta suke yi, ƙalilan kuma suna mata magana kasancewar mutanen ta ne. Sai dai ta gaisa dasu kawai ta wuce har sanda ta kai babban titi inda take yin tuyan awara

Da sauri Ibrahim her friend; ya taso daga saman wani benci da ke gaban shago a wajen; ya sauke mata farantin saman kanta yana dariya tare da cewa, "Oyoyo my Besty, I've seen you before everyone."

Murmushi tayi tana ajiye Robbern tace, "uhm Ni ban ga alama ba, bayan yau kwata-kwata ban ganka ba sai yanzu, ina ka shige ne?" Ta ƙare maganar tana narkar da manyan idanuwanta a cikin nashi, tare da sauke mishi wani kallo da ke rikitar da duk wanda ta yiwa shi

Shima ɗin kafe ta yayi da idanun yana cije leɓe cike da tsantsan sha'awar ta da ƙaunarta yace, "oh my Besty! Me kike ci na baka na zuba? Ai abun da yasa na kira ki kenan ki ƙariso don in shafa miki labarin abun da yake faruwa... Amma tukunna dai bari in soma hura miki wutan nan don naga time na gudu." Sai yayi saurin ɗaukar kafi-tankiyan ya ajiye sannan ya soma jera itacen a ciki, a haka ya gama ya hura wutan

Ita kuma har ta saka kujera ta zauna suna magana a tsakanin su. Wani almajiri ta kira ta kalli Ibrahim ɗin tare da cewa, "Besty ba shi kuɗi ya ƙaro min icce, don wannan bazai ishe Ni ba."

"Ok nawa kike buƙata?" Yayi maganar yana ɗago kai tare da kallon ta

"Two hundred is ok." Sai ta kalli Yaron tace, "ka siyo min iccen ne na ɗari, sai yajin hamsin."

"To." Yace yana amsar kuɗin a wajen shi

Komai Ibrahim yayi mata hatta da ɗaura mai a wuta, sai da yayi zafi sannan ita ta soma jefa waran tana cewa, "My Besty bani labarin in sha na ƙosa."

Dariya yayi yace, "Arab Sarauniyar son labari! Yanzu kuwa." Sai ya gyara zama a saman bencin da ya ɗauko

Har zai soma maganar kuma sai wani saurayi ya iso wajen yana kiran sunan shi, tare da ba shi hannu suka gaisa, sai ya zauna a kan bencin shima yana kallon Arab tare da cewa, "Ƙin fi ƙarfin Yaro ya ne?"

"Dai-dai Sa'id." Ta amsa shi batare da ta kalle shi ba tana ci gaba da saka awaran

Shi kuma yace, "but yau ba ki fara suya da wuri bane? I think zan zo inga wuri ya cika sai na iske babu kowa, yanzu ma kika fara ai."

Yatsina fuska tayi da cewa, "wlh kuwa. I did not start early."

"Ok. tunda na zo da wuri yau dai na taki Sa'a, za'a ajiye min na ɗari uku ina dawowa, don Allah yanzu ba jimawa zan yi ba kar in dawo inga an cika wurin sai na jira layi."

"Ba ka da matsala, kawo kuɗin sai in
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment