Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

YAYA DA DUKIYA BA A KETAR SU

Na Rasheedah A kardam

Ebook creat by Shuraih Usman

Ebook publish by www.hausaebooks.cf

Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.cf

Kuna ziyarci shafinmu don samun sababbin littatafai



Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com

YAYA DA DUKIYA BA’A

K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. ﻦﻤﺣ ﺮﻟﺍ ﻟﻠﻪﺍ ﻢﺴﺒﻟﺍ

ﻩﺮﺳﻭ ﻪﺘﻴﻧﻼﻋﻭ ﻩﺮﺧﺁﻭ ﻪﻟﻭﺃﻭ ،ﻪﻠﺟﻭ ﻪﻗﺩ ،ﻪﻠﻛ ﻲﺒﻧﺫ ﻲﻟ ﺮﻔﻏﺍ ﻢﻬﻠﻟﺍ . ﻢﻴﺣ ﺮﻟﺍ.

ﻢﻴﻫﺮﺑﺇ ﻝﺁ ﻰﻠﻋ ﺖﻴﻠﺻ ﺎﻤﻛ ﻪﺘﻳﺭﺫﻭ ﻪﺟﻭﺯﺃ ﻰﻠﻋ ﻭ ﺪﻤﺤﻣ ﻰﻠﻋ ﻞﺻ ﻢﻬﻠﻟﺍ .

ﻚﻧﺇ ،ﻢﻫﺮﺑﺇ ﻝﺁ ﻰﻠﻋ ﺖﻛﺮﺑ ﺎﻤﻛ ﻪﺘﻳﺭﺯﻭ ﻪﺟﺍﻭﺯﺃ ﻰﻠﻋﻭ ﺪﻤﺤﻣ ﻰﻠﻋ ﺖﻛﺭﺎﺑﻭ

ﺪﻴﺠﻣ ﺪﻴﻤﺣ . GATARWA Dukkan yabo ya tabbata ga Allah.

Ina godiya a gare sh’i, ina neman taimakonsa, ina neman

gafaransa, kuma ina neman tsarinsa daga sharrace-

sharracen rayukanmu da mitagyn ayyuka. Wanda Allah

ya sh’irye sh’i babu mai b’atar da sh’i, wanda kuma ya

b’atar ba mai sh’iryar da sh’i. Ina shaidawa babu abin

bautawa da gsky sai Allah, shi kad’ai, babu abokin

tarayya gare sh’i. Ina shaidawa cewa Muhammadu

bawansa ne kuma manzonsa ne. Ya Allah kayi tsira ga

wad’anda suka bish’i da ky’aky’awan kw’aikw’ayo har

zuwa ranar kiyama. Kuma ka musu aminci, aminci mai

yawa Ameen. SADAUKARWA Na sa daukar da wannan

littafi mai sun YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU, ga

Mummy’s d’ina Khadija’s. GODIYA godiya mai d’imbin

yawa gareku, da bazarku nake taka rawa a duniyar

Rubutu, Allah ya barmu tare. Maryam .S. Bello Maryam

Alkali Mamu(Mrs Jabo). Page-1~5. Tari wanki ne a

gabanta, sai faman wanke su takeyi, kalo d’aya zaka mata

ga gane ta gala baita sosai, har k’arfin har bata jin karfin

jikinta. Gwaggo ne ta taho da wasu kayan wankin ta kara

mata, tace “Khadi maza- maza kiyi sauri ki wanke ma

Beeba kaya, zata gidan Innarku. A wahale na d’ago nace

“Inna ga wasu sabbin kayanta can na wanke su, sun

bushe tasa su, kuma suna da ky’au, gash’i nayi wankin da

yawa na gaji. Gwaggo wani uwar ashar ta narko, wanda

ni Rash bansan lokacin da nayi baya da sauri ba. Shako

ta Inna tayi tace”dan jakar ubanki ni zaki fad’a ma kin

wanke wasu, kuma har kina iya cewa kin gaji. Eh!

Lallekam yau zaki gwadan ke yar Zamani ce, ban isa dake

ba ko?. Khadi cikin muryan kuka tasoma cewa”dan Allah!

Gwaggo kiyi hak’uri wlh ba da wara manufa na fad’i

hakan ba. Gwaggo kara shaketa tayi tace”ko uwar ki ma

bazata mayar min da martani ba. Kafin Khadi tayi

magana ji kake tass tass tass ta wanke ta da mari har sau

uku, dukanta tafarayi ta kota ina. Wayyo ni kaina Rash na

tausaya ma Khadi, don ga alama fuskan gwaggo nan bata

da tausayi ko kad’an Taku a kullum mai k’aunar ku ﺪﻴﺷﺍﺭ

9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA

DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-6~10. Gwaggo sai da tayi likis ma Khadi kafin ta

ky’aleta, tace”wlh sai kin gama wankin nan yau ko na

miki dan banza duka, sha-sha kawai, mts tayi tsaki ta nufi

cikin d’akinta. Khadi kam kuka tasha ga wani yunwan da

ke murd’amata ciki. Kama cikin tayi ta tamke da d’an

kwali abunka da Khadija maganin Maza cikin dakiyar

zuciya ta fara wankin , da ikon Allah kafin akira Sallah

la’asar ta gama. Gwaggo ta fito da abinci a d’an k’aramin

kwano wanda ko d’an yaro bazai ish’esh’i ba. Ta turo

mata kwanon ta juya tayi d’akinta ko tausayin Yarinyan

nan bata ji ba. Ga uban aikin da ta mata a cikin gidan

kamar jaka. Malam Ahmadu ne ya sh’igo da Sallamansa,

in donsa ne ya sauk’a kan Khadi dake kwance tamkar

wanda aka d’aura ma dutsin dala da gauron dutsi aka. Da

sauri ya k’arasa gurinta cike da tausaya wa, ya tallabo ta

yace “Mama na ya dai? Mai ya same ki na ganki haka? .

Gwaggo ta fito cike da masifa tace”komai ne ya same ta

ko zaka karb’a mata ne, sai in sani. Cike da b’acin rai

Malam Ahmad ya nufo ta, yace”kee Hauwa wlh ki kiyaye

ni zan sas-saba miki akan Khadija sam ba kya tausayin

yarinyan nan. Gwaggo tace “ina ko zan tausaya mata ba

sanin zafinta nayi ba bare na san miye tausayi. Malam

yace”duk aikin da take yi a gidan baky’a gani ko?. Kuma

ba ky’a sanya yar cikinki. Wannan yarinya Yata ke a gun

mu, duk irin rikon da muka mata Allah zai tambaye mu,

Hauwa kiji tsoron Allah. Gwaggo tace”ehehe wa’azi

zakamin ai tsoron Allah kulum cikinta muke, yar wani ba

yata bace nawa kawai na san, fuuu tayi d’aki in ka gama

sai ka sanar min. Taku a kulum mai k’aunar ku ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺪﻴﺷﺍﺭ

9:12] ﻡﺩﺮﻛ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA

DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-11~15. Cikin ta kaici yazo ya tallabi Khadi ya d’agata

sai a lokacin ya kalli d’an abinci da gwaggo ta bata.

Taburma ya d’auko a d’akinsa ya sh’in fid’a mata, ya

zaunar da ita. Kular abincinsa ya kawo mata tare da juye

ruwa mai zafi ya had’a mata Lipton ya bata da kyar ta iya

sha. Abicinsa ya kara mata, sai da ya tabbatar ta kosh’i

kafin ya ci sh’ima. Khadi ta mik’e jiki ba kwari ta nufi

rijiya ta d’ebo ruwa ta nufi bayi, wanka tayi ta fito, ta sha

fa mai kayanta masu d’an kyau ta saka ta dawo waje gun

Malam don gudun bala’in Gwaggo. Malam yace”Mama

nah bazan fasa miki nasiha ba, inaso ko kasance mai

yawan hak’uri kinga halin Gwaggon ku kullum Addu’a

nake mata Allah yasa ta gane gsky. Khadiya duk halin da

kika samu kanki, ki kasance mai hak’uri zakici riban

rayuwanki. Kai ta d’aga masa alamae Eh!. Heeba ce ta

sh’igo da Sallaman ta, cikin fara’a ta k’araso gun su,

sannu da gida ta musu kafin tace”Addah ina ta sauri inzo

in tayaki aiki, da aka tash’i a makaranta, ban samu abun

hawa ba, Gash’i har kin gama. Khadi tayi murmushi

tace”ba komai k’anwata, ya makaranta?. Alhamdulilah! Ki

d’auko abinciki kici to Adda. Malam yana jin dad’in

yanda yaransa suka had’a kai, baran Beeba da sam bata

gado halin uwarta ba, heeba ya rinya ce mai hankali

kamar Khadi. Sabanin Rabi da ke ji da taken rash’in

kunya, halinta sak na uwarta hatta kama da Gwaggo take

kama. Gwaggo tafito tsawa ta daka ma Beeba kee mai

kikeyi a gunsu, kin dawo ko sanar ni bazakiyi ba, ni bana

son kina taraya da mai fiska kaman na muciya. Oh! Ni

Rash nace”wannan Gwaggon wata irin macece ta fiye

son kanta, anya ma idonta na gani kuwa?. Duk irin kyan

Khadi tana zaginta. Ko beeba ma bazata gwada mata

kyau ba don ta d’aran mata nesa ba kusa ba. Taku a

kullum mai k’aumarku . 9:12] ﻡﺩﺔﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺪﻴﺷﺍﺭ PM,

9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A

K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-16~20. Jiki

ba kwari Beeba ta nufi d’akin, don sam ita bata son irin

yadda mahaifiyarta ke nuna tsana ma Khadi. Gash’i ko

kad’an Khadi bata nuna damuwarta kuma hakan ba sh’i

zai hanata biyayya ba.Allah yasa Gwaggo ta gane. Ya

sh’irya mana ita Ameen. ‘Dakin su tash’iga Gwaggo ta

balbaleta da masifa, Gwaggo tace”Beeba bana son ganin

ki da wancan mai fuskan mujiyan, kema kuma sai niman

kai kike da su. Ni har Malam da ke biye mata ba kyalesh’i

zanyi ba, ko kad’an bana k’aunar in bud’e ido imganta a

gidan nan. Beeba tace”haba Gwaggo ba kyau fad’an haka

fa, kuma ae Addah tana iya k’ok’arinta gurin kyautata

miki. Ita ne kulum cikin aiki bata hutawa ko ni bana miki

aikin da take, nikam ina son Addah na tana da halaye

mai… Bakinta Gwaggo ta make tare da wata harara

tace”kee a kul d’inki kar na kara jin cewa kina had’a kanki

da wannan yarinya, Ko kema ta shanye miki Zuciyan ne?,

kama yanda ta shanye na Malam baya ganin laifita baya

son amata fad’a. Beeba tace”ko d’aya Gwaggo gsky kenan

Khadi tana da halaye mai kyau. Mts Gwaggo ta ja tsaki ga

abinki can maza ki ci don zaki gidan Innan ku, zaki anso

min aika a gunta. Beeba ta d’auko abinci zatafita gunsu

Malam Gwaggo ta dakatar da ita, ba yanda ta iya dole

yasa taci a d’aki badan taso ba, don ta fi jin dad’in

kasancewa da yar’uwanta. Gwaggo tace”Beeba yi sauri ki

sh’irya kije min gidan Inna ku. To ta amsa ta kammala

cin abinci tayi wanka ta d’auko kayanta masu kyau ta

sanya su, ra fes da ita. Gwaggo “nagama sh’irin ke nake

jira kizo fad’an sakon, don inje kar dare ta min a hanya.

Sai da Gwaggo ta d’auko sakon da zata kai ma Inna kafin

ta bata kud’in mash’in tace”kice ta had’a miki duka aikan

harda kayan da na saya d’in, to ta amsa ta fito sai da tayi

sallama wasu Malam kafin ta tafi. Taku a kullum mai

k’aunarku 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺪﻴﺷﺍﺭ PM, 9/14/2016] Rash

Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM. Notice Masu karatu na zansa

sunan littafina daga KHADEEJATUL-KUBRAH zuwa YA’YA

DA DUKIYA BA’A K’ETARSU, cos Daman YAR’RIKO ne suna

Da na fara sawa, sai aka samu wacce tayi. So yanzu

namar dashi YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU. Yafi

ma’ana kuma sakon littafin akan haka zai tafi. Pg-26~30.

Ana kiran sallah tayi d’akin su ta kwanta, kasanewan

garin da sanyi lokacin hunturu ne. Addu’a tayi ta kwanta

ga yunwar da ke addabarta. Haka har bacci b’arawo yayi

awon gaba da ita. Dukun-kune take a yar ta barmata gefe

kuma katifar Beeba ne yar k’arama wanda mutum d’aya

zai d’auka. Bacci take amma sanyi ya dameta. Kiran

Sallah asuba ya farkar da ita da kyar ta mik’e ta d’ibo

ruwa a randa sai d’ari take yi. Alwala tayi ta koma d’aki

tayi sallah bayan ta idar ta fara azkar d’in safiya wani

bacci ne ya d’auketa kamar daga sama taji an shek’a

mata ruwa mai sanyi nan take ta fara d’ari-d’ari, duk da

haka Gwaggo bata kyaleta ba wani ruwan ta k’ara kwara

mata. Barin da takeyi ya tsananta, Gwaggo tace”ke har

kimsami daman da zaki kwanta bacin safe, uban wa ya

baki dama?. Malam yana karatun Al-qur’ani mai girma

sai yaji kamar ana hayaniya jin maganan yayi yawa ya

fito, yaji d’akin su Khadi ne da sauri ya sa kai cikin d’akin

ganin Khadi ta fi luuuu zata fad’i yaje da sauri yana”Salati

ya tare ta fad’a a hannunsa cikin k’unan rai ya d’ago ya

kalli Gwaggo yace” in kin kasheta ae kin huta, kin san

yarinya tana fama da Pneumonia kuma yayi mata yawa

zaki kwara mata ruwan sanyi, haba hauwa anya kina

tsoron Allah kuwa ae d’a ko ba kai ka haifeshi ba, bai

kamata kina wula kanta ta ba.( Yan uwa mata kira

gareku, kune jigon gida duk lokacin da gida yayi kyau

kune, kusani Ya’ya da Dukiya, da Dabba ba’a mugun tar

su. A rauwa ba kasan wanda zai taimake ba, sai kaga d’an

da ka haifa da cikin ka wani lokacin bai jik’anka ba,

wanda baka san zafin sa ba ya taimake ka kuma Ya’ya

Rahmane dan Allah kuna kyautata ma yara ba sai naka

ba ku d’auka duk d’aya suke a gunku). Gwaggo ko a

jikinta tayi waje tana cewa”ni dai dole ta fito ta min aiki

yau ko ta ji a jikinta. Malam ya kali Khadi ta idanunta

suka kafe a sama da sauri ya d’auketa ya fita waje da ita.

Beba da ta fito daga d’aki ganin halinda Adda ta ke ciki

yasa tayi gun Malam da hanzari suka fita dake garin da

sanyi da kyar suka samu mai Napep yace”Yaro Asibitin

Murtala zaka kai mu, Malam da Beeba suka shigar da ita

ciki suka d’au hanyar Asibitñ, sun d’anyi tafiya kafin suka

iso asibitin, kud’in mai napep ya basa kafin ya d’auki

Khadi suka shiga cikin Asibitin nurse suna hango su, suka

tahoda sauri suka karb’eta. Emergency aka nufa da ita,

Dr Abdul ke bakin aiki, da sauri “nurse suka sanar masa

an kawo patient. Yace “ok! I’m coming now”. Bata dad’e

da isa gun su Malam sai ga Dr Abdul nan ya iso. Dubata

ya soma yi yaga tana wani yanayi numfashinta na shirin

d’aukewa, tai makon gaggawa aka bata cikin ikon Allah

suka samu numfashinta ya dai-daita. Magunguna ya

rubuta ya mika wa Malam yace”Baba gashi kaje

Pharmacy ka sayo, in ka dawo ka bawa nurse sai ka

same ni a office d’ina. Malam ya amsa da rawar jiki ya

nufi pharmacy. Taku a kulum mai k’aunar ku . ﺓﺪﻴﺷﺍﺭ

9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA

DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-21~25. Malam suna hira da Khadi Gwaggo ta fito

wani sak’on kalon da Gwaggo ta aika ma Khadi, yasa ta

mike ba sh’iri ta nufi kitchen ta d’aura girkin dare, sai da

ta magama aiki Gwaggo tazo ta d’auke tukunyan d’akinta

ta sh’iga dash’i duk abun da suke Malam na kalon su bai

ce mata komai ba. A zuciyansa ya na mai jin-jina bak’in

hali irin na Gwaggo, Malam ya mike ya fita waje zuwa

gurin da suke d’aukan karatu. Rabi ce ta sh’igo tayi

d’akinsu ta nufa ta dau naira goman Gwaggo tasa a

wando ta fita waje, alawa ta siya sai da ta shanye kafin ta

dawo gida. Gwaggo tazo d’aukan raina gomanta don a

siyo mata sikari ta saka a surki, taga babu kud’i cike da

masifa tazo ta danki Khadi tace”ke barauniya bani kud’i

na da kika d’aukar min wato satan ma gadonsa kikayi a

gun uwar ki. Khadi tace”Gwaggo ko d’akin ma ban sh’iga

ba ina zaune a nan gurin fa. Gwaggo tace”oh! Sharri zan

miki ko?. Ni a ya’ya na babu b’arawo ba mu gaji sata ba

sai dai ko gun uwarki ne zuri’an barayi. Nan take Khadi ta

soma hawaye jin takaicin yanda ake kiran iyayenta da

suke kasa. Eyeh lalle kin samu gu dan ban dakaki ba

shine kike kuka ko?. Gwaggo ta d’auko dorina tazane

Khadi sai da taji hannu ta ya gaji tace”naira goman da

kika d’auka a madadin abinciki na yau da kuma karin

safiya. Gwaggo ta juya zata tafi sai ta dawo ta rike kunne

Khadi tace”saura in Malam ya baki abunci ki karb’a ki

gani ni dake yau a gidan nan. Ina son ana kiran Sallah ki

sh’iga d’aki ban yarda ki leko waje ba, ina ga munanan

kafarki a guri kin san sauran ta nufi d’aki. Taku a kullum

mai k’aunar ku 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash

Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-31~35. Malam ya sayi

maganin dubu buyu da d’ari biyar ya nufo k’ofan

Emergency ya mika ma nurse “Malam ya tambayi office

d’in Dr Abdul nurse ce ta gwada masa, godiya ya mata

nufi office d’in, da Sallaman sa ya tura k’ofar aka bashi

izinin shigowa, Dr ya nuna masa gun zama Malam ya

zauna. Sai da Dr ya gama yan rubuce-rubucen sa tukun

ya d’ago da fuskansa tare da zare yar faran glass d’in da

ke manne a kyakyawan fuskansa. Malam ya msa sannu

da aiki,Cikin girmamawa ya amsa, kali Malam yace”Baba

jikin Khadeeja yayi tsanani sosai, mai yasa kuke barinta

tana aiki da ruwan sanyi?, kuma tana zama a inda ke da

sanyi, mai ya kawo hakan bacin na sha fad’a muku illar

hakan amma kun kasa koyayewa. Malam da jikinsa yayi

sanyi yace”Dr in Allah ya yarda wanan karon zamu

kiyaye fatan mu kawai yanzu ta samu lfy. Dr Abdul ya

kallesa sosai tabbas ya gano damuwa a cikin idonsa ga

alamar magana a bakinsa, amma tunda bai fad’a ba “ni

dai zanyi iya kokarina ganin na taimaka mata, ya Allah

kabata lfy ameen. Ya kalli Malam yace”shikenan zaka iya

tafiya amma akula mata da shan magani. Kai Malam ya

d’aga masa alamar eh!. ‘Dakin da aka kwantar ta ya

yashiga Beeba ya gani a bakin gadon ta zuba mata ido ga

alamar tayi kuka sosai. Da Sallama ya shigo Beeba ta

masa sannu ya amsa tare da zama a d’aya daga cikin

plastic chairs d’in dake d’akin. Yace”Beeba ya jikin Addah

ki?. tace” da sauki amma har yanzu bata tashi ba, bacci

take ya kalli Khadi yace”Allah ya baki lfy, cikin zuciyar shi

kuwa cewa yake” ya zama dole in d’auki mata ki akan

Gwaggo bazai yiwu Khadi taci gaba da wahala haka ba.

Ya mike ya nufi k’ofar Asibiti ya sayo musu abinci ya

dawo ya kawo musu nan Beeba ta karya, shima sama-

sama yaci abincin. Gwaggo ne tafito daga bayi ta na

zuwa d’aki taga ba Beeba ta duba d’akin su Khadi taga

bata nan d’akin Malam ma baya nan, Rabi ta tambaya

tace”kee ina Beebalo?. Rabi ta kalli ina tace” ba sun fita

da Malam ba naga ya riko Adda Khadi, tsaki tayi ta leko

titi basa nan, nan takama bala’i yau zaizo ya sameta akan

me zai fita mata da yarta don wata marar galihu, ita

yarta na galihu, cikin gida ta koma sai surutu take ita

d’aya. WACECE KHADIJA?. khadijatu~Kubrah shine asalin

sunan Khadi ya d’aya tilo ga Malam Adam. Malam Adam

haifafen garin kano cikin unguwan Dakata gurin fire

service. Yayan Malam Ahmad ne Ubansu d’aya ne. Tun

Malam Ahmad na karami Allah yayi rasuwa Mahaifiyar

sa, ya koma hannun Maman Adam wato Kakan Khadi

kenan, ta yi musu rikon tsakani da Allah har suka girma.

Adam shiya fara yin Aure kasan cewan shine babba sun

shekara da yawa da matar sa Balkisu Allah bai basu

haihuwa ba, sai daga baya ta samu ciki ya zo mata da

laulayi haka tayi ta fama har tazo haihuwa, ta kwana biyi

tana na kuda, kafin rannan ukun har ana shirin shiga da

ita operation ta haihu ko juyawa batayi ba Allah ya karbi

abunsa. Malam Adam yayi kukan rashin matarsa mai

hankali da kirki, watan ta shida da rasuwa Baba Ahmad

yayi Aure, ya auri matar sa Hauwa amma auren dangi

sukayi yar kwan war Maman sa ne,(danganta karsu ta

gun uwa kenan da haiwa). Hauwa macece mai masifa

tun tana budurwa ta ki jinin Balkisu Maman Khadi ganin

yanda Ahmad ke zama a d’akinta hakan yana bata haushi

sosai. Cikin ikon Allah Khadi ta samu kulawa in ka ganta

bazaka ce bata sha nono ba madara take sha bul-bul da

ita ga ta da gashi ga kyau sosai, gwanin burgewa. Hauwa

shekaranta 3 da Aure ta haifi yarta Beeba kar kuso kuga

murna gunta, ta d’au son duniya ta d’aura ma Beeba, ta

taso cikin kulawa ga hankali, in ka ganta sak Malam

Ahmad kamar kakinta yayi, yarinya mai hankali da

nutsuwa, jinin su ya had’u da Khadi tun Beeba na

karama Khadi ke mata wasa komai ta samu zata kawo

mata, amma in Gwaggo ta gani ta kwace ta yar ta daki

Khadi, ana cikin haka wata ranan talata Malam Adam ya

tashi da ciwon Ajali kwanasa biyar Allah ya karbi abunsa

tun daga wannan rana Khadi ta dawo hannun Malam

Ahmad da zama, nan Gwaggo ta samu daman galla za

mata, sam bata kaunar ganin Khadi da Beeba sun zauna

gu d’aya. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺍﺭ PM, 9/14/2016] Rash

Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-36~40. Sam Gwaggo bata

‘kaunar ganin Khadik, da Beeba sun zauna gu d’aya. A

kwai wani rana, da Khadi na wasa ma Beeba, Gwaggo na

zuwa ta saka k’afarta ta shure Khadi, ta fad’i akan hannu

ta, sai da ta gurd’e. Ranan ran Malam ba ‘karamin b’aci

yayi ba, har sai da ya mari Gwaggo. Tun daga lokacin ta

‘kara tsanar Khadi, har zuwa girmanta, sam bata tausaya

mata, duk aikin gidan Khadi keyi, Beeba kuwa bata son

ganin Khadi cikin damuwa, in Gwaggo ta bata ma Khadi

aiki, sai ta faki idon Gwaggo ta zo ta tayata su gama. Haka

rayuwansu ya kasance dad’i da ba dad’i, Malam ya sanya

su a Makaranta Khadi da Beeba suna ‘ko’kari, amma

Rabee kam in ban da niman tsokana ba abunda take. A

hakan har Khadi ta kammala Secondary school d’inta, ta

barsu Beeba yanzu ke karatu har islamiya an yaye ta.

Matsalar ta d’aya ne sam bata kula saurayi, ko sunzo

Gwaggo koran kare take musu, wai baa su nimi mayya

ba. Tana lashe zuciyar mutane, har ta lashe na Malam da

yarta Beeba. Hakan sam bai damun Khadi,ita kulum da

Malam addu’a su, Allah ya shiryi Gwaggo yasa ta gane.

Wankin Gwaggo dana Ya’yanta Khadi ke yi, in tafara sai ta

gama, bata isa tace”ta gaji ba Gwaggo zata fara mata

bala’i, wani lokacin, abimci ma hana ta take. Back to lbr.

Khadi bata farka ba, sai kusan k’arfe sha biyu, sai da

Malam ya ga tasamu ta ci abinci, kafin ya musu sallama,

akan zaije shi gd ya dawo, Beeba ta mishi adawo lfy, ya

fita. Yana isa gd, Gwaggo ta taso cikin masifa, tana

tambayar sa ina ya kai mata yarta?. Ko dun bai damu da

ita ba ne, yana son wannan mayyar ta lashe mata kurwa,

kamar yarda uwarta ta lashe zuciyan mutane. Sai da ta

gama sababinta Malam bai bi ta kanta ba, abincin sa ya

d’auka, ya fita tare da tabarma da pillow. Gwaggo na

ganin ya fita, gyale ta d’auko ta fara binsa a baya, har

taga ya nufi Asibitin Murtala, itama tace”ma me Napep

su bi Malam, haka ko akayi, har ya shiga cikin asibitin, ta

bisa a baya, har ‘kofan Ward d’in da aka kwantar da

Khadi. Ta na labe taga ya shiga d’akin bai dad’e ba ya fito,

ya nufi wani guri a cikin asibitin. ta na shiga, gadajen ta

rink’a bi, har ta iso na su Khadi, wani mugun kalo ta

sakar ma Khadi,da ke jin gine da pillow, tace”mayya kin

lashe zuciyar mijina da yata, to bakiyi sa’a ba, tana zuwa

kusa da ita, ta wanke ta da kyakyawan mari, nan take yan

d’akin suka yi mata caaa. Kafin ka ce me, guri ya d’auka

da hayaniya. Dr Abdul ne ya fito daga Ward d’in dake,

kusa da na su Khadi, hannunsa rike da waya, da alamar

waya yakeyi. A hankali ya ke tafiya, tun daga nesa ya ke

jin hayaniya, yace”Dr Umar ina zuwa, naga kamar female

ward na lfy, bai karasa ba ya iso gun hayaniya, yayi yawa,

da kyar ya kutsa zuwa cikin gun, sam ya manta bai kashe

wayar ba. Dr Umar shima bai kashe ba, dai-dai lokacin

Malam ya iso gurin, ganin abunda ke faruwa ya soma jan

Gwaggo da ta rufe Khadi da duka, sai zuba bala’in take.

Dr Abdul ya iso yana “tan bayan lfy?. Gwaggo sai wani fin

cikewa take, Malam ya d’auke ta da mari. Ta d’ago tana

kalon Malam tace”ka mare ni a kan wannan banzan,

mayyan mai kod’ade’en fuska. Ba zan yarda ba, sai na

rama ta sake yin kan Khadi, itakam in banda kuka ita da

Beeba sun rike juna. Dr Umar da ke jin duk abunda ya

faro, duk da baya gurin amma ransa ya baci sosai, cikin

zuciyarsa yace”duk da bansan maike faruwa ba amma

wata irin macece haka?. Malam ya ransa ya baci mari ya

sake wanke Gwaggo da shi, zafin yasa ta nutsu sosai, sai

ta dawo ta fara jan Beeba, ita ko gadon ta rike, security

aka kira suka fita da ita. Sai da guri ya lafa, Dr Abdul

yace”Baba ka sameni a office d’ina ya fita, Malam ya nufi

office d’in sa. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash

Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA

©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-41~45. Sai
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment