Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels





Compiled By Umar Dalha Funtua.



♦♦♦
*SANGARTATTCE*♦♦♦

Maman Abd Shakur

1...
Free page

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai.


"wayyo Allah na Baba mutuwa zanyi, wayyo Mama huramin cikin" mata biyune suka zagayeta akan tabarman dawasu yara mata guda biyu dake tsakar gidan dayasha simenti kal kal dashi duk sunyi zuru zuru, kana ganinsu kaga tashin hankali kwance akan fuskarsu, chan ta gefen tabarman kuma wajajen inda kafanta yake wani dan tsohone haka dake sanye da babbar riga dakuma yar hula daya zagayeta da rawani irin na malamai dinan ya rike kofin silver yakara abaki yanata addu'o'i aciki anatse, ihu takara yi ta dage rigarta sama tabude daidai cikinta dake nan kaman bata tabacin abinci ba, ta gefen haggun cikin ya dan kumbura idan kaga wajen saika rantse wani irin babban kurjine yafito ya kumbura haka yay ruwa zai fashe, ihu tasake yi tariko hannayen matan dake kanta tace "wayyo Allah Mamammu na shiga uku, azaba Mama wayyo, azaba yakemin" tasaki hanunsu tana ihu "Baba Baba baba kiranka nakefa, wayyyo Allah na ba banu ni" wani irin ihu take ta rirrike hannayansu gam tana nishi, wajen ciwon cikin kuwa sai balbal yake yanda kasan halita mai rai ne acikin wurin, duk ihun ta yacika gidan, tsabagen takaici ma daya daga cikin matayen wacce itace mahaifiyarta taja tsaki, hakan yasa dayar ta goge zufan datake yi agoshi, takamo fuskarta da hanunta tarike tace "haba Balkisu, iye mai gadon zinare, ki daure mana baga baban kinan namiki addu'a aruwaba, kefa mai dauriya ce, jaruma, kinga Layla da Raiyana zasuce ke raguwa cefa gashima sai kallonki suke" girgiza kai tayi tawani irin kece da kuka da ihu harda shesheka tace "ni kukiramin Baaba wlh, Baaba tazo, Baaba kizo ki taimakeni" tafara shure kafa idanun nan sunyi jajir tace "Baba, Baba, Muji, wayyo Allah na Mujittapa kuzo kutaimake ni, Shato kuzu dan Allah na shiga uku, wayyo Mama dubamin kiga kodai barkewa cikin yakeyi ne?" tawani irin buga ihu hakan yasa mahaifiyarta dake kanta ta buge bakinta da karfi tace "kewai baki iya kiran sunan Allah bane banziya kawai" daidai lokacin Baba ya cire cup daga bakinshi ya kalli Uwargidan yace "dagomin ita Zainaba" dagota tayi ahankali sai wani uban nishi take tana cije baki tace "tsaya tsaya uhmm" tsayawa tayi tana kallonta cike da tausayi, hannu budurwan tasa akan kafadar matar tareda runtse ido da karfi tana nishi tace "tona shirya" har Mama saida tasa hannu suka dagota zaune ahankali wani irin ihu tayi kaman zata mutu "ya isa, ya isa, yayi" suka jinginar da ita ajikin bango, kafamata kofin Baba yay abaki ta kurbi ruwan sosai tasha tana kara dage rigar atampan jikin ta sama, ragowan ruwan Baba ya debo yay addu'a zai shafamata akan kullutun da sauri tarike hanunshi tana ihu tana kuka tace "Baba wlh azaba yakemin, in kanama Allah karka tabamin, kaji dan yarasulullahi" hanunta Mama dake kanta ta buge tana wurga mata wani mugun kallo, hakan yasa Baba ya girgiza kai ya shafamata ruwan awajen tana wani irin shegen ihu da duk yacika musu kunne, tashi Baba yay ya kalli mahaifiyarta ya mika mata cup din yace "bayan awa daya kikara bata Amina, bari nakoma zaure wajen dalibai" jiki asanyaye ta karba tace "to malam" juyawa yayi yay hanyar zaure bude kofa yayi sanan ya daga asabari dazai sadashi da zauren yafita, almajirai ne cike a zauren sunata karatu da alo, ga wasu manya akansu dake rike da bulala suna lura dasu, bangon zauren duk jakunkunan almajiran ne dakuma taburmai dasuke kwana akai dan zauren nada girma sosai, daliban na ganinshi suka kara karfin karatun dasuke, fita yayi daga zauren zuwa kofar gida nan ma wasu almajiran ne akan simentin kofar gidan dayawa sunata karatu da alo, anyi babbar runfa daya kare kofar gidan sabida koda ana ruwan sama dan wasu almajiran anan waje suke kwana, ga robobin almajiran cike akan dankali dan dazaran karfe biyu tayi zasu tsaya sai ayi salla kowa yatafi bara, daga chan gefen kofar gidan kuma lungu ne dayasa suka gineshi dajar kasa aka zagaye suka maida bayi, anan almajiran suke wanka suke dai komi nasu sanan a kofar gidan akwai rijiya da guga dasuke diban ruwa, zama yayi akan tabarma da aka wareshi musamman tashi ce dan akwai yar dadduma mai taushi akai ya zauna tareda yin bismilla yanajan chasbaha, yana bin kowani dalibin dake wurin yana karatu da kallo, wani dalibi babba dan yana daga cikin wayanda ke kula da sauran almajiran ne yazo kusa da malam ya zauna tareda tankawshe kafa yadan dukar dakai yace "Allah taimaki Malam, Allah gafarta ma Malam, Allah kare mana Malam" ahankali Baba ya ijiye charbin ya kalli yaron yace "sun biya karatun da kyau Isyaka?" "i sunbiya Malam, na muhammadu ne kawai bai kawo da kyau ba amma nakara maimaita mai" murmushi Malam yayi tareda kishingida da bango yace "masha Allah to, daukomin Al Qur'ani na nabarshi a zaure saika biyamin naka inji" dan kallonshi matashin yayi saikuma ya sunkuyar da kai yace "Malam ya jikin Balkisun?" ajiyar zuciya Malam ya sauke yace "da sauki namata addu'a zata sami lpy nan bada jimawaba" cike da damuwa Isyaka yatashi yabar wajen zuwa zauren dan dauko abinda Malam ya aikeshi.

Gyangyadi tafara yi anan wajen a zaune, hakan yasa duk suka sauke ijiyar zuciya, Uwargidan dasuke kira da Umma tamike ta kalli Maman Bilkisun tace "sha biyu tayi bari na daura girki Amina" kallon yaran daduk sai kallon Bilkisu dake nan zaune tana gyangyadi suke tace "ai sai atashi aje ataya Umma aiki ko" hijabi Raiyana ta cire wacce ita kebin Bilkisu shekaran ta 15 tamikama Layla hijabin wacce take auta shekaran ta 8 tace "ungo kaimin daki" karba Layla tayi ta wuce dakin su ta ijiye tafito suka karasa kitchen din jajjage Umma tasa Raiyana itakuma Layla Umma tace "tahura mata wutar ta kama" tafice daga kitchen din zuwa tsakar gida dan tankaden tuwo.
Layla dake fifita wuta ne ta juyo ta kalli Raiyana dake jajjage, ajiye maficin tayi tazo kusa da Raiyana ta tsaya kaman zatai kuka tace "Anty Raiyana maisa Baba bazai kai Anty Baby asibiti ba, kinga ko koyau a makarantar mu anmana primary science fa, ance idan abu yafito acikin ka yay babba har yana motsi operation akeyi, Allah kuwa, Baba kuma yanata mata karatu tanasha da dafa mata ganye maisa bazaice aje asibiti ba" tunda take maganan Raiyana ta tsayar da jajjagen tana kallonta, Umma ne ta shigo kitchen din ta kallesu tace "surutun me kukeyi ba aiki nasaku ba?" baki Layla tabude zatai magana Raiyana ta girgiza mata kai hakan yasa tai shiru takoma gaban murhun tacigaba da fifita, abinda Umma ta shigo dauka ta dauka tafice daga kitchen din, hakan yasa Raiyana tadawo wajen murhun ta tsugunna tace "karki kara fadin maganan nan, Baba bai yarda da maganin asibiti ba kuma idan yajiki kinsan sauran, karki karayin maganan kinji" ahankali Layla ta gyada mata kai kowaccen su tacigaba da aikin da aka sakata.
Wuraren sha biyu da rabi ta farka azabure ta mike Mama dake zaune gefenta tana dama ma malam fura ta kalleta tace "ya cikin" hanyar dakinsu tayi ta daga labule ta kalli agogo sanan ta kalli Mama tace "Mama nakusa lattin makaranta shine baku tasheni ba" turo baki tayi tai gaban rijiya tadau botiki zataja ruwa, tabe baki Mama tayi tacigaba da dama furan ta, agurguje taje tayo wanka tafito daure da zani a kirji tashiga daki da gudu, uwar dakan su ta shiga dake nan agyare ko ina dan gado ne madaidaici sai ledan daki da aka shimfide, tsugunnawa tayi tajawo ganamasgo daga karkashin gado ta bude taciro kayan makarantar ta dake nan agoge, purple dogon wandon tafara sawa sanan tasaka rigar dayakai har gwuiwa fara tana dan bata fuska sabida yanda cikin ke mata ciwo kadan kadan yanzu ba kaman dazu ga, gaban madubi taje ta shafa farar hoda tasaka kwali, basilin ta lakato ta shafa akan pink and black lips dinta, dan lips dinta daga tsakiyar su pink ne sosai sai kasan kuma baki kaman ta shafa janbaki haka suke gashi sunwani irin tattare gwanin kyau and sexy, idan ka kalla kaman nama, komawa gadon tayi tasanya farin hijabin daya wuce gwuiwa, ta maida ganamasgo karkashin gadon tadau yar jakarta da litattafan ta keciki tafito ta zauna adakalin bakin kofa tana kokarin saka safa da takalmin makaranta Umma da fitowar ta daga kitchen kenan tace "Baby yaushe kika warke dahar zaki tafi makarantar allazi boko?" dan murmushi tayi daya bayyanar da beauty point dinta tace "Umma yafa dena fa wlh, kuma kinga nice monitor aji chalk natare dani dole nakai" baki Umma ta kama tace "su manito manya" dariya Balkisu tasaki harda fadawa jikin Mama dake kan tabarma tace "ana monito kina manito Umma" tacigaba da dariya kaman ba ita ke ihu dazuba, rankwashi Mama tasakin mata akai tace "tashi min akan jiki kafin na juye miki furan nan akan kayan makarantar nan" ahankali ta tashi kaman zatai kuka ta zauna kusa da ita Umma ta bude kullin zani taciro naira hamsin ta mikamata tace "gashi kihau mota, daga fillin mallawa zuwa dogon bauchi da shegen nisa keda baki da lpy" karba tayi cike da murna tace "nagode Umma na Allah barmin ke" komawa tayi kusa da Mama tana kallon furan, kaman zatai kuka tace "Mama dan sammin kinga ba'a gama abincin rana ba karnaje makaranta haka da yunwa" hararan ta Mama tayi tace "kwadayayya" dariya tayi tace "eh naji Mama kidan ban" da sauri ta shiga daki ta dauko karamin kofin roba Maman ta tsiya mata dan daidai ta shanye harda saka yatsa tana kakkale kofin ta lashe tass sanan ta ijiye kofin tana goge baki tace "nagode Mama natafi" da sauri tadau jakarta ta leka kitchen taga su Raiyana na kwasan tuwo tace "natafi" atare suka mata addu'a, Mama tace "salla fa?" "a school zanyi Mama" tabude kofa sanan ta daga asabari tafita.
[7/15, 12:17 PM] Ummi Tandama: ♦♦♦ *SANGARTATTCE*♦♦♦


Maman Abd Shakur

2 - 3
Free page

Zaure tawuce tana bin almajiran wajen da kallo kafin ta fita kofar gida tai wajen Baba da tunda tafito ita yake kallo, tsugunnawa tai agabanshi tawani kwaye fuska kaman zatai kuka ahankali tace "Baba natafi makaranta amma ni banci komiba ba'a gama abincin ranaba" girgiza kai kawai Malam yayi sanin halin yar tashi, hakan yasa ya saka hannu cikin aljihun babbar rigar dake jikinshi yaciro dari yabata da sauri ta karba tana murmushi tace "nagode Babana, Allah biyaka natafi" "ya cikin?" ya tambayeta anatse, tashi tayi tana kokarin saka kudin ajaka sanan tace "yadena Baba tundazu, natafi" "adawo lpy" tajuya ta fita tana waige waigen zauren, fitowa tayi tafara tafiya a layinsu daya yawaitu da bishiyoyin dogon yaro, dadan sauri take tafiya sabida takai bakin titi tahau boss dazai kaita school, wani gida dan madaidaici dake nan cikin layinsu ta shiga harda dan gudan ta dan sauri take wata matace yar dattijuwa haka, tana zaune tana tuyan waina anan tsakar gidan ahankali kaman wacce kwai ya fashewa aciki ta karasa kusa da matar wacce batama lura da itaba saidai kawai taji mutum akanta, fashewa tayi da kuka kaman wacce aka doka hakan yasa matar ta rike baki tace "mekuma aka miki iya shagwaba iya sonjiki Bilkisu" kara fashewa tai da kuka tana buga kafa akasa cikin kukan tace "tun safe banda lpy kokizo ki dubani kinata wainar saidawa abinki ko Baaba" arude matar tace "ni? Haba tagidana ai kema kinsan inda nasan bakida lpy tuni xan ijiye wainar nan nazo, dena kukan keko, halan cikin ne yatashi?" gyada kai tayi tana share hawayen Baaba tace "shiga daki ki dauko kular ki nasaka miki wainar ki kitafi kinga yau kinyi latti" da sauri tashiga dakin Baaba tana kokarin daukar kulan tace "Baaba ina Muji?" daga tachan waje Baaba tace "yafita da Keke napep waiko zai sami fasinja, saiyau ya daukota daga gareji" daidai nan tafito tamika ma Baaba kular, karba tayi tazuba mata wainar dayawa sanan ta baza mata kuli dayawa akai ta rufe kulan tabata tareda ciro hamsin tace "gashi adawo lpy" karba kulan tayi tace "kibar kudin Baba yabani, natafi Baaba saina dawo" "adawo lpy yar albarka banda wasa a aji kinji yar gidana" fita tayi tana murmushi tana mugun son Baaba, yayar mamanta ne haka suke kiranta, bayan tai aure data haifi Mujittapa (Mustapha) danta na farko shine Maman su lokacin kafin tai aure tazo tayata raino aiko malam yana ganin Maman su ya like mata ya nace yanaso, bayan wani dan lokaci fa suka tafi kauyen su dake chan hanyar gombe kauyen bojude lokacin tun kafin iyayensu su rasu akai bikin aka kawota gidan malam, Umma bata da matsala hakan yasa malam ya hade kansu suna zaman lpy, yayan malam 8, Umma yaranta 5 duka maza wanda duk malam yatura su nijar wajen wani babban abokin shi malami yin karatun addini awani babbar makarantar shi, yanzu ma watan su daya da tafiya kenan sai bayan shekara biyar zasu dawo dan makarantar har certificate ake badawa inka gama, sai kuma maman su data haifi su uku Balkisu, Raiyana da Layla, dukan su malam yasasu a government girls secondary school ne Raiyana da Layla na safe suke zuwa, itakuma dayake SS ne rana ne nata.

Karasowa bakin titi tayi ta tsaya tana jiran Bus wata makauniya tagani ita da yarta suna ta bara a shagunonin kan hanya wai tun safe basuci abinci ba, ba karamin tausayi suka bataba, tana kallonsu suka koma kan dakali suka zauna yarinyar nata kuka, jakarta ta laluba taciro naira darin da Baba yabata ta karasa kan dakalin dataga sun zauna, yarinyar nata kuka wai yunwa takeji maman na lallashin ta, ahankali ta duka darin ta mikama yarinyar tareda mata murmushi tace "dena kuka gashi" karba yarinyar tayi tana fadama maman ta bakaramin dadi matar tajiba tace "mungode yar nan, ubangiji Allah ya miki albarka ya raya miki yaranki" dariya Bilkisu tayi sosai tace "Ameen amma nibanyi aure ba mama" washe baki makauniyar tayi tace "to ubangiji Allah ya baki miji nagari wanda zai saki farin ciki sama da wanan dakika samu" ahankali tace "Ameen nagode" ta dagama karamar yarinyar hannu sanan tajuya ta tare bus din dake zuwa ta shiga har lokacin yarinyar nata dagamata hannu itama daga mata hannun tayi har bus yawuce ta daina hangosu.
Allah yasota koda ta shiga school ana gab dafara taran latti, da sauri tafara yin masallaci tai salla sanan tafito tai aji lokacin duk yan aji sun zauna ana ganinta akai tsit kowa nata kallonta hakan yasa tasha jinin jikinta, kujeran layi nabiyu ta wuce ta tsaya agaban sit din ganin duk su Aisha Shehu sun cike Walawa ta zauna awurinta, daure fuska tayi ta kalli Walawa tace "wlh kitashin min daga wuri ai chan ne sit dinki" tanuna kujeran bayan nasu, hararan ta Walawa tayi ta cigaba da zanen flower datake yi a paper, su Aisha Shehu dai sai dariya suke kasa kasa dan dama dagangan Walawa tazauna neman tsokana ne, ganin ko kulata Walawa batayi ba yasa taji abin ya mugun bata mata rai hakan yasa ta fizge byron hanun Walawa afadace tace "badake nake magana ba, kinga kitashi" kaman jira Walawa takeyi ta mike tsaye fuska a daure ta kalli su Fateema da Fa'za dake kusa da ita suma duk suna dariya kasa kasa tace "ku matsamin na fitan ma almasifatu daga wuri" gyaggyara kafa sukayi Walawa tafara tafiya hakan yasa Bilkisu tazo daidai bakin sit din tana jiran Walawa tafito itakuma ta shiga fuskar nan nata adaure fitowa Walawa tayi, saida tazo gab da Bilkisu tasa hannu ta taba mata nono, atsorace Bilkisu ta tsugunna a wurin tareda fasa ihu "wayyo Allah" ta kankame jikinta, aiko duka ajin sukahau ihu da dariya, su Aisha Shehu dasu Fa'iza harda buga benci suna dariya, Walawa ko hanyar kofa tayi ta tsugunna tana dariya harda rike ciki, gabaki daya ajin dariya ake Aisha Shehu tace "babu wacce ba'a tabama nono a ajinan ba, kece kullum kiki yarda yar malam, yaudai an taba dama gasu manya manya" aikuwa kowa dariya suna bubbuga benci irin abun yay musu mugun sugar dinan, saida ta goge hawayen datake yi sanan ta mike tazo gaban Aisha Shehu tace "eh aini kinsan ba yar iska bace irinku ba masu wasan taba nono a school" tana fadin haka tai hanyar kofa wurin Walawa, Aisha Shehu tabita da harara tace "to uban waye yan iskan, ba wasa bane kowa ajin nan an taba nashi saike, koba hakabane?" ta tambayi su Fa'iza da Fateema suma duk dariyan suke harda kama ciki danba karamin dadi abun yamusu ba yau yanda aka kama na Bilkisu yar malam yau, dan ita kadaice bata yarda amata wanan iskancin a aji gashi yau an shammaceta anyi kowa dadi yakeji. Kan Walawa Bilkisu tayi wacce tun kafin tazo kanta tahade hannu tana dariya tace "haba Billy yar malam, yakuri mana kawas ai bankama ba tabawa kawai nayifa dan nasan bakiso wlh bazan karaba, yakuri" kamota Bilkisu tayi ta durma mata duddu abaya daidai lokacin wata malamar english dinsu ta shigo aji hakan yasa duk suka koma wajen zamansu kowa ya natsu.
(oya name abunda kukayi zamanin secondary school?? Barinma wayanda sukayi girls school kadai😂)

Wuraren 4 suka fito break da salla, bayan sunyi salla duk tare suka tayata cin wainar dan dama sune kawayen nata Aisha Shehu Walawa da Fa'ixa saikuma Fateema, bayan sungama ciyeciyen su sanan suka koma class, sai wuraren biyar da rabi aka tashe su duk suka fito suna tafiya har suka gangaro bakin titi suka shiga bus kowacce tai gidansu.
Gidan Umma tafara biyawa ta ijiye kulan sanan tafito akofar gidansu tahadu da Isyaka yana alwalan sallan magriba, murmushi tamai hakan shima yamata murmushi da sauri ta shiga gida ta gaida Baba sanan tawuce cikin gida. Babu kowa a tsakar gidan duk sun shiga daki hakan yasa taja ruwa tazuba a buta tai bayin su bayan tafito ta tsugunna a makwarara tai alwala sanan ta shigo dakinsu, salla taga Mama dasu Raiyana nayi hakan yasa ta zauna akan kujera tana kokarin kunna fitila, kunnawa tayi ta ijiye daidai lokacin sun sallame Layla ce tafara tasowa Raiyana tabiyo ta abaya duk suka zauna kusa da ita Layla tace "me kika kawo mana daga school Anty Baby?" murmushi tayi ta bude jakarta gwaiba taciro da topi ta basu duk suka karba cikeda jin dadi Mama ta ballamata harara tace "aikin kenan" dariya tayi ta tashi tasaka hijabi tai sallan magriba tana idarwa ta daura kanta akan cinyar Mama ahankali tace "yunwa nakeji Mama sosai" mika hannu Mama tayi ta dauko kular tuwo dake gefenta tace "gashi nan zuba muku kuci keda kaninki to" tashi tayi ta dauko faranti ta zuba tuwon tasa miya asama ta kalli su Raiyana tace "ku sakko muci" sakkowa sukayi zasu sa hannu Mama ta harareta tace "bazaki je kicire kayan makaranta bawai" kaman zatai kuka ta tashi tawuce uwar daka tacire kayan ta fito daure da zani akirji ta zauna tana turo baki sanan suka saka hannu duka suka faraci.

Dr ne akan wani magidancin da akalla zaikai 75 years sa'an Baba buhari😂 acikin wani katafaran falo sai sumbatu yake yana "Dr Ayaan dina zaka kawomin, Ayaan" shiru yayi sabida alluran da likitan yamai daidai lokacin wani security dake sanye cikin uniform ya tsaya agaban falon yana sallama, izini matar dake falon cikin shiga ta alfarma tamai, hakan yasa ya shigo hanunshi rike da wata ipad, Karasowa yayi gefen Baba Sule wanda shine kanin magidancin dabaida lpy, cike da girmamawa yace "Alhaji wanan shine CCTV footage din natun ranan da Ayaan yafara rashin lpy abangaren shi, da lokacin daya fita daga gidan" ya kalli matar datai tagumi tana kallon fuskar mara lpy yace "Hajiya akwai bukatar kema kizo ki kalla dan wata da kayan yan aikin gidan nan ne tafara kawomai abinci lokacin yana garden tace kece kika aikota takawo mai, to ayanda dai CCTV footage din yanuna yanacin abincin yafara rashin lafiya saikuma..." yadanyi shiru cikeda damuwa yace "zodai ki kalla dakanki wata kila ki gane yarinyar dan munemo ta dole zatasan wani abu kan batar shi" tashi matar da aka kira da Hajiya tayi ta dawo gefen Baba sulen ta zauna jiki asanyaye tana kallo, tunda tafara kallo ta dafe zuciyar ta tana buga salati saikuma tafashe da kuka sosai ta kalli Baba Sule tace "Baba Sule ina dana yayi? Yanzu adai yanda yafitar nan a ina zamu ganshi, innalillahi wa innalillahi raji'un wanan wace irin musib.." shiru tayi ganin mara lafiyan yakara farkawa yarike hanun Dr dake kanshi yace "ina Ayaan dina? Eh Ina ka kaimin shi?".
[7/15, 12:17 PM] Ummi Tandama: ♦♦♦ *SANGARTATTCE* ♦♦♦


Maman Abd Shakur

5...
Free page

Iska da kiraye kirayen sallan magrib ne yashiga kunnenta yana ratsa har brain dinta, ahankali take bude ido ganin inda take yasa ta mike tsaye a firgice tana karanto ayatul kursiyu ko ina na jikinta na rawa, karan buga abu dataji shiya kara firgita ta hakan yasa mahaukacin kara juyowa ya kalleta, baya tafara komawa jikinshi ko ina rawa yake, juyar dakai mahaukacin yayi yacigaba da bubbuga kular nata abango yana dariya kafin yakamo bakin rigar shi ya cusa abaki yana ci, hannu tasa tarufe bakinta tacigaba da komawa baya sadaf sadaf, haushin kare taji abayan ta yasa ta buga wani irin mugun ihu ta shiga cikin gidan da gudun bala'i dan ta tsani kare, karan yazo ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment