Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[8/19, 10:54 AM] Zarahh: 👮🏻 *COLONEL UBAIDULLAH*👮🏻
( _the story about a young gentle man_)



*ᏚᎢᎾᎡY ᏔᎡᏆᎢᎢᎬN ᏴY*✍🏻


*Z͢A͢H͢R͢A͢ A͢B͢D͢U͢L͢* (ᴹᴼᴹᵞᴺ ᴬᴴᴸᴬᴺ)


( *y̾a̾r̾ s̾a̾r̾a̾r̾i̾n̾ k̾a̾i̾n̾u̾w̾a̾*)
👸🏻 *SAHIBAR KAINUWA*👸🏻

_dedicated to my brother_

*U̶B̶A̶I̶D̶U̶L̶L̶A̶H̶I̶*

_my wattpab_@Fateemah0

_QAUNAR KU DABAN YAKE_
*ANTY HAUWA MMN USWAD*
*&*
*ANTY FAUZAN YAR AMANAR KAINUWA*
_ALLAH YA RAYA ZURIA MY ANTY'S_💘
____________________
_Alhamdulillah ina qara godewa Allah a ko da yaushe salati da daukaka da tsira da aminci su qara tabbata ga shugabanmu Annabi muhammad S,A,W da iyalan gidansa da sahabban sa da ma goya baya har izuwa ranar sakamako_🤲🏻
__________________
Ya Allah kabani ikon farawa lpy na kuma gama lpy🤲🏻

*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*


*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*____________________________________*

*page°°°1&2*



*9JA,BARRACKS ABUJA*

Tsaye yake daga shi sai 3quarter mai ratsin tambarin sojoji a jiki, sai farar T-shart and p-cap shi ma na sojoji.

Dogo ne amma baza kace masa dogo sosai ba ,yana da ɗan fadin fuska daidai wa daida ,sannan baza kace masa fari ba, za dai ka iya saka shi a layin chocolate color
Yana da gashin baki wanda ya kewaye masa baki wanda hakan ba ƙaramin kyau ya qara masa ba, duk da idonsa sanye yake da black shadow,but yana da ƙananan ido kmr na yan'chinese , yana da faɗaɗɗan ƙirji irin na gwarazan maza jarumai saɗaukai.

Duk ya zuba hannayen sa a aljihu, yana tsaye fuskar sa babu alamun fara'a domin shi ko da smiling ne bai cika yiba infact baya ma yi balle kuma dariya bcox baya daukar raini a *barracks*, bama iyakar barracks ba ,a koma ina ne baya daukar raini, duk da sojoji ne amma da yawan ana shakkar sa.

Iska ne ke ƙadawa awajan domin a garden din barracks din yake tsaye.

Bakin sa ne ke moving ahankali saika Lura da kyau kafin ka fahimce ashe waya yakeyi but da airpieces a kunnan sa.

Bisa alama kuma da mahaifiyarsa yake wayar domin yadda yake wayar cike da natsuwa.

Mama tace.

"*UBAIDULLAH* ina fatan dai komai lafiya?"

Sai da ya numfasa ya hura iska kafin ya ce

" eh mama lafiya lau fatan kuma kuna nan lafiya? Ina su sister's ?"

Mama tace.

" lafiyarmu lau hafiza ta je gidan yayarku ummu,na aiketa ,ita kuma na'ila wai taje karban aron littafi agidan su kawarta."

"Mtsww!!! wlh mama na'ila bata jin magana at oll,na hanata zuwa yawo amma bataji, wani irin littafi da rana haka?"

Mama tace.

" indai na'ila ce sai dai mu dinga taya ta da adduah Allah ubangiji ya shiryeta."

Ya amsa da ameen
Hira suke dan tabawa na tsakanin uwa da ɗanta.

mama tace.

"Ubaidullah yaushe zaka zo ka gan mu ne kam munyi, kewarka sosai wlh."

" Karki damu mama zanzo a next week weekend In sha Allah."

mama tace.

" Allah ya kaimu" suka ci gaba da hira,
Ji yayi anyi hugging dinsa ta baya azafafe ya juyo domin yaji kamshin turarenta
Kashe wayar yayi yana cewa I will call u back mama luv you!!

Sa ke fuskantar ta yayi yana tamke fuska , ita kuma tana murmushi sanye take da kakin sojoji itama sai murmushi take masa, tasa hannu zata shafi fuskarsa ya buge hannun, sannan ahankali ya bude mouth dinsa lyk mai koyan mgn yace.

"waike *RUMAISA* how many times zan fada miki ki dai na haɗa jikin ki da nawa?"

Smiling tayi tace.

" first lieutenant Ubaidullah I will never tried to say I love u duk fadin barracks din nan oll ladies din DA suke rububin suna sonka karya su keyi! ni ce masoyiyar ka Wanda nake maka true love, plss I beg u Ubaidullah ka so ni ko da kaɗan ne "

ta ƙarasa tana so ta shige jikinsa ya bankaɗe ta ya wuce yana jan dogon tsaki ,rumaisa kuma tayi kwafa ta juya domin indai wannan wulaƙancin Ubaidullah din nan ta saba shan sa.

Ahanya kafin ya isa dakinsa ya hadu da close friend dinsa infact garinsu daya tare suka taso burinsu ɗaya arean su ma ɗaya.

*ZAIDU* yace.

" Ubaidullah tun dazu nake neman ka ban ganka ba ina ka shiga?"

A kasalance yace.

" ina garden barrack ne menene?.

" No dama stall sergeant David ne yazo neman ka akan mgnr meeting din da za a gudanar anjima a babbar filin taro na *murtala barracks* shine lieutenant general yace. A fada maka kai da commander Ku shirya domin taron ma yana da nasaba da mu dan gsky naji ƙishin ƙishin akan cewa zabe za ayi domin tura jama'ai izuwa bordern Niger domin kama yan'ta'adda."

"To kai Zaidu a bakin wa kaji ?"

"Na dai fara ji a bakin sergeant first class A,M kasan halinsa maybe shima ji yayi."

Ubaidullah yace .

"ok amma K,B yasan da mgnr ?.

Zaidu yace.

" eh dazu ma mun hadu dashi na fada masa kaine kawai baka sani ba."

Ba tare yayi mgn ba ya jinjina kai kawai.

Duk inda ya gitta sai an kallesa amma ya tsare gida dan Ubaidullahi akwai tsare gida, su na tafiya suna dan taba hira har suka isa part dinsu.

Suna shiga parlour suka sa mu Raihana kwance a 3seter sanye take da wandon sojoji da black T-shart kanta ko p-cap din ma babu, balle kuma dan kwalli ko veil"

Ubaidullah yayi tsaki yace.

" ke kuma fa? oya tashi ki fita kafin raina yabaci ya fada yana mata nuni da kofar waje."

ahankali Raihana ta miƙe tana taku harta zo daf dashi domin numfashin su har yana sarkewa waje daya tace.

" i will,but ina so kasani wlh wlh bazan taba barin ka ba Ubaidullah, ta juya ta fice."

Zaidu ya kwashe da dry yace.

" wlh ladies din yanzu duk sun gama kwarkwancewa kalli fa yadda suke rushing akan ka?"

Tsaki Ubaidullah yayi ya shige bathroom domin yayi fresh'up.


Bayan ya fito ya shirya, ya ɗauki doguwar jallabiyya ya saka,
yadan kwanta.

Ya lumshe ido yana tuno rayuwar baya , haƙiƙa yanzu komai yana so ya zamo masa tarihi,sai kuma babban burin sa, na gaba.

Bacci ma yake ji amma bazai iyaba dan haka ya tashi zaune.

Kallon sa.

" Zaidu yayi,lafiya kuwa Ubaidullah?.

"Mtsww wlh Zaidu ina yawan tuno baya ne."

"Bai kamata ka dinga tuna baya ba Ubaidullah,ka fuskanci gaba kawai,a rayuwar ka komai ya wuce, tunda a karshe Allah ya cika maka burin ka na zama jami'in soja, wanda kuma ake alfahari dashi."

Numfasawa yayi.

" Zaidu kasan ina da buri sosai a rayuwa ta, but bana so na dawo dasu mama barracks din nan,cox ka kalli abinda ladies ke min mama ba za ta ji dadi ba, ba ma zata jure ba."

"Haka ne kuma ,to amma ya zakayi?"

"Abinda nima ban gama yanke shawara ba kenan."

Tattaunawa suka cigaba dayi.

K,B ne yayi sallama ya shigo da sauri har yana tuntube,
Zaidu yace lafiya kuwa K,B?

"Ina kuwa lafiya, ga Raihana da Zeey can su na dambe wlh ina tausayawa Raihana dan babu abun da zata ɗauka, a jikin Zeey, yarinyar da ko wasu mazan tsoronta sukeyi, balle kuma Raihana."

Dryn mugunta Zaidu ya hauyi, yace.

"Ubaidullah tashi muje mu gani,kai Zeey bata da hakuri,am sure Raihana ce bata da gaskiya, cewar Zaidu."

Duba agogon sa Ubaidullah yayi,yaga har to 4, yace.

" i don't have time for this stupid ladies, Ku shirya mu tafi meeting."

Shiryawa sukayi cikin kakin su na sojoji ,suka fito su na taku a hankali, wanda na Ubaidullah ya sha banban da nasu.

Commander suka sa mu sannan suka ɗun guma *murtala barracks*.


•••••••••••••••••••


Duk inda ka wulla idon ka baza ka iya banbance waye da waye awajan ba.

Sojoji ne birjik ta ko ina da ina.

Nan aka nemi da a buɗe, taro da adduah ,major usman shine wanda ya buɗewa musulmai nasu,sai major jonh shine ya buɗewa christian nasu,
Kafin, aka fara gabatar da meeting.

yayin da major general yake jawabi cikin harshen turanci, akan jaruman da barracks ke ji dasu za a tura ,amma kafin nan za,ayi ƙarin girma ga wa'inda suka je yaƙin maiduguri,
Lieutenant general ne ya karbi jawabin daga hannun major general ya ɗora,da nasa akai.

Mutum na farko daya lashe takwabin girma mai tambari shine...!!ehem ehem! *first lieutenant Ubaidullah* wanda a yanzu zai karbi matsayin, *CAPTAIN UBAIDULLAH*,nan jami'ai, aka hau tafa masa ji kake rab! rab! bayan anyi wa Ubaidullah ƙarin girma, shima Zaidu matsayin captain aka bashi, K,B kuma a tym din aka basa ,matsayin first lieutenant ,daga nan aka cigaba da rabon muƙamai.

Ba a watse ba kuwa, sai da aka kira sallar magriba tukunna musulmai sukayi masallaci sai da suka idar, yan'9ja barracks suka koma.

A gajiye suka shiga part dinsu.

" Zaidu yace oh Allah ƙarin girma babu gayyata sai dai kawai gayyar sojoji? ai da an bari iyayen mu da yan uwanmu sunzo kafin ayi mana ko dan bamu da mata ne? Ko kuma,mu bamu kawo iyalan mu barracks ba?"

K,B ya kwashe da dry yace "Zaidu kenan yanzu kai a tunanin ka, ka kai aure ?"
" ai abun ne yazo ba shiri shiyasa kuma kaga nan da wata daya ne zamu tafi border gashi naji major general yace gobe zamu fara sabon training,amma kusan Allah commander victor bai so wannan ƙarin girma da a kayi ba, daka kalli kwayar idonsa zaka hango baƙin ciki da hassada ƙarara."

"Wlh K,B ka kiyaye ni! Cewar Zaidu, ni zaka kalla kace ban isa aure ba?" Wani dry Ubaidullah ya kwashe dashi,sai da suka dan tsorata su na kallon sa.

"Ubaidullah wannan dry haka?" cewar Zaidu.

K,B yace "ina kuwa lafiya mutum sai kace mai iskokai."

"No wlh hirar taku ce ta ban dry ,kunsan ai ni dry bata cikin manner dina "

Zaidu yace "dama kai kam dryr ka ,sai dai kana gida,ko kuma kana tare damu."

"But nifa wlh hassadar commander victor bai dame ni ba,tunda hassada a barracks ba yau farau ba,and bazai zama karshe ba, so just 4get about this matter,mu fuskanci yin gaban kanmu dan yanzu mun sake zama manya, captain ai ba wasa ba,muna tafiya yaran mu su na bin mu a baya."


Ubaidullah yace "b4 mu tafi i need to go home,I want to see my momma and my lovely sister's."

Zaidu yace " ok when are u going?"
A takaice Ubaidullah yace, "next week In'sha Allah."

"When did u come back?"
Sai da ya ɗauki som minute kafin yace "5days."

Zaidu yace " zan bika mu tafi tare sai mu dawo, but kasan fa, sai mun samu permission daga wajan, *GENERAL OF THE ARMY*."


Ubaidullah yace

"eh nasani."

K,B ne yace.

" kenan ni kadai zaku barni?"

"Hahaha my guy kaima ka shirya kawai kaje ganin gida,amma seriously da mun dawo aure nake so wlh."

Girgiza kai Ubaidullah yayi, yace mayan aure kawai,ku tashi muje sallah, tashi sukayi suka fito atare,sukayi hanyar ma sallaci



*WANENE UBAIDULLAH*?
×××××××××××××



Sharhin ku ne zai sa mu cigaba ko mu dakata......!!!! Domin fahimtar littafin ya muku ko bai muku ba



COMMENTS
&
SHARE


BY MOMYN AHLAN✍🏻
[8/19, 10:56 AM] Zarahh: *COLONEL UBAIDULLAH*
( _the story about a young gentle man_)



*ᏚᎢᎾᎡY ᏔᎡᏆᎢᎢᎬN ᏴY*✍🏻


*Z͢A͢H͢R͢A͢ A͢B͢D͢U͢L͢* (ᴹᴼᴹᵞᴺ ᴬᴴᴸᴬᴺ)


( *y̾a̾r̾ s̾a̾r̾a̾r̾i̾n̾ k̾a̾i̾n̾u̾w̾a̾*)
👸🏻 *SAHIBAR KAINUWA*👸🏻

_dedicated to my brother_

*U̶B̶A̶I̶D̶U̶L̶L̶A̶H̶I̶*

_my wattpab_@Fateemah0

_QAUNAR KU DABAN YAKE_
*ANTY HAUWA MMN USWAD*
*&*
*ANTY FAUZAN YAR AMANAR KAINUWA*
_ALLAH YA RAYA ZURIA MY ANTY'S_💘
____________________
_Alhamdulillah! ina qara godewa Allah a ko da yaushe, salati da daukaka da tsira da aminci su qara tabbata ga shugabanmu Annabi muhammad S,A,W, da iyalan gidansa da sahabban sa, da ma goya baya har izuwa ranar sakamako._🤲🏻
__________________
Ya Allah kabani ikon gamawa lpy.🤲🏻

*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*


*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*____________________________________*

*page°°°°3&4*


*UBAIDULLAH ABDULLAHI GALADIMA.*
Shine asalin cikakken sunansa, haifaffen garin Bauchi ne, ya kasance maraya Mahaifinsa tsohon Soja ne."

Ubaidullah tun yana yaro yake sha'awan aikin soja, sakamakon ganin yanda mahaifinsa yake ɗebi ba ɗaɗi da yan ta'adda.


Su hudu ne rak awajan Mama mahaifiyarsu, Ubaidullah shi ka
ɗai ne namiji, shi ne na biyu, Anty Ummu ita ce babba, sai ,Ubaidullah,Hafiza,Na'ila.

"Tun Ubaidullah yana da shekara goma a duniya Allah yayiwa mahaifinsu rasuwa, a wani yaƙin garin jos da a kayi, aka kashe mahaifinsu, sunyi kukan rashi a lokacin da aka shigo musu da gawar Baba, wanda a lokacin yake riƙe da matsayin commander na sojoji, Baba ya taka muƙamai da dama a aikin soja, bayan rasuwar Baba komai ya dagule musu, domin a lokacin sun ga jarabawan rayuwa.


Abinci ma gagararsu yake yi, Mama tayi kuka harta godewa Allah, a lokacin kuma su hafiza su na yara, dan Hafiza shekararta biyar Na'ila kuma tana da shekara hudu, Ummu kuma tana da shekara goma sha takwas. Dan tsakanin Ubaidullah da Ummu ratan shekara takwas ne, Ubaidullah kuma yana bawa Hafiza shekara biyar harda rabi,
tsakanin Hafiza da Na'ila kuma ratan shekara daya ne, shiyasa suka taso kansu daya.


Sun sha matukar wahala kafin Mama data ga zaman ba zai yuwu ba, ta koma toya kosai a bakin kofar gida, domin a cikin dangin Ubansu Ubaidullah babu mai taimaka musu, a lokacin da Baba yake raye kuma kullum zaka gansu sunzo suna bin su, su na jan su a jiki kamar da gaske, amma tun da ƙasa ya rufewa baba ido shikenan suka ɗauke kafarsu, babu wanda ya sake tako kafarsa izuwa cikin gidan balle ya kawo musu ko da ƙwayar marasa ce.


Mama tasha wuya ba ka ɗan ba wajan kula da yaranta, Ubaidullah ganin burinsa bazai cika bane ya sa shi zuwa wajan ƙanin mahaifinsa domin ya taimaka masa, amma abun mamaki sai ya koreshi, Ubaidullah yana da matuƙar zuciya tun a lokacin yaci Alwashi akan burinsa, sannan ko zasu mutu bazai sake taka kafarsa ba izuwa wajan dangin mahaifinsa ba.


Da wannan Alwashin Ubaidullah ya ba zama neman aiki, yana ɗan shekara goma a lokacin amma ba labari, dan haka ya fara aikin cire yashi sai ya siyar, da haka ya koma makaranta, a wajen ne kuma suka hadu da amininsa Zaidu.


Ya na da shekara goma shabiyu ya koma aikin karfi wato buga block, tun Ubaidullah yana ƙarami amma ɗamtsensa duk sun fito sakamakon aikin karfin da yake yi.


Rayuwa kenan har Ubaidullah ya zo ya hana Mama toya Kosai, har ya fara biyawa ƙannansa kudin makaranta, ya biya nasa ya biya nasu.


A lokacin da aka tashi bikin Anty Ummu, Mama tayi kuka kamar ranta zai fita, saboda ba kudin da zata yiwa 'yarta kayan ɗaki, inda a karshe Mama taci bashin kudi har dubu ishirin awajan wata mata, ashe kudin nan zai zama tashin hankali.


Bayan biki mata ta dinga rashin kirki wa Mama tana gaya mata baƙaƙen maganganu, ran Ubaidullah ya baci dan ya tsani abun da zai batawa mahaifiyarsa rai, dan tun bayan rayuwar Baba Mama ta kamu da cutar hawan jini.


Kudinsa daya tara zai biya kudin makaranta ya ɗauka ya bayar,dan bazai jure ganin hakan ba.


"Ubaidullah yana da shekara sha biyar a lokacin kuma yana ɗan zuwa training jikinsa duk ya murɗe, wata ranar laraba suka buga ma wani babban mutum block sannan suka masa aiki, nan ya mai dasu kamar yaransa, sosai kuma yake jindadin aiki dasu.


Kamar a wasa yake tambayarsu aikin da suke sha'awa domin aikin karfi bazai kaisu ko ina ba.

Ubaidullah ya ce ," *Aikin Soja.*"


Alhaji Adamu ya ce.
"Da gaske aikin soja ku ke so?"

Suka jinjina kai gami da cewa "eh"

Alhaji Adamu da yake babban mutum ne ya ce, "ai kuwa major Hamza aboki na ne yana garin Abuja, sannan da ma naji wani sanarwa akan cewa yara matasa masu jarumtaza'ayi zabe wanda suke sha'awar aikin soja, za'a turasu ƙasar libya domin su samu ingantacciyar training, ina da aboki ma a ƙasar libyan wanda shine mataimakin mai bada horo, idan kuna so sai na tsaya muku na nema muku takarda ku tafi, shekara uku kacal za kuyi ku dawo da cikakkun tambarin ku na sojoji."


Abun nema ya samu, nan Ubaidullah da Zaidu sukayi na'am

Ko da Ubaidullah yake fadawa Mama fatan Alkhairi tayi masa, sannan ta saka masa albarka.

Abu kamar wasa, bayan su Ubaidullah sunyi wannan maganar da Alhaji Adamu da sati biyu ya kira su yake shaida musu akan cewa sun samu shiga, murna kamar miye, suka dinga zuba godiya tare da yima Alhaji Adamu adduar gamawa da duniya lafiya.


Alhaji Adamu ya ce,"kun zama tamkar yarana saboda ni ban da ƴaƴa maza, mata ne su biyu kuma duka duka shekararsu goma sha biyu ne, babbar sha uku, ai kun san su ko?" suka ce "eh" ,Alhaji Adamu ya ce "ina jinku tamƙar yarana, dan haka ku daina min godiya, nan da wata daya zaku tafi kuje ku fara shiri."


Ai kuwa nan da wata daya su Ubaidullah sukayi sallama da gida, Mama,Anty Ummu,su Hafiza ,sunyi kuka dan gani suke idan ya tafi bazai dawo ba, shekara uku ba wata uku bane ba sati uku bane, ba kuma kwana uku bane.


Sai da suka fara zuwa Abuja tukunna aka ajiye su a *Abacha barracks,* nan suka karbi wani horo na sati daya, kuma jirginsu ya ɗaga izuwa libya.


Sosai Ubaidullah yake nuna jarumtarsa da baiwarsa a fagen training, a cikin wata shidda Ubaidullah ya iya riƙe bindiga tare da kwarewa a wajan saiti, shi a karan kansa mai koyar dasu sai da ya sallamawa Ubaidullah.


Su na waya dasu Mama lokaci zuwa lokaci su na jin lafiyarsa shi ma yana jin nasu.


A cikin shekara biyu Ubaidullah ya zama kwararre, idan ka kalleshi sai ka rantse ya kai shekara ashirin amma bai kai ba, shekarunsa sha bakwai ne, kawai jikin ne ya horu da horo ya saka shi zama babba, fuskarsa dama tun asalinsa ba mai ƙaunar dariya bane, sai dai idan yana tare da yan uwansa ko abokansa.


Lokacin da su Ubaidullah suka yi shekara uku a kasar libya sai da aka tura su yaƙi a maƙotar ƙasar ,inda suka yi nasaran lashe yaƙin.

Kafin Ubaidullah su dawo Nigeria sai da ya karbi matsayin *master sergeant.*"


Ranar da suka dawo kuma aka shirya musu liyafa agarin Abuja na taya su murna.

Alhaji Adamu yaji dadi sosai ganin su Ubaidullah basu watsa masa ƙasa a ido ba, su ma sosai suke basa girma tamƙar mahaifinsu, dan sun mai dashi Babansu.

Ranar da Ubaidullah ya sauka agarin Bauchi wayyo zo kuga murna awajan yan uwansa, inda suka rungumesa sannan suka saka kukan farinciki sakamakon ganinsa da sukayi da kakin sojoji, tare da nasarori tun da ga takardansa wanda zai fara aiki a *MURTALA BARRACKS ABUJA.*

Tun daga wannan lokacin Rayuwa ta canza ga ahalin margayi tsohon Soja Abdullahi galadima.

"Hakan ne ya sa Ubaidullah ya fiye zama a garin Abuja, sai dai ya zo weekend 2days ya koma Abuja bakin aikinsa, dan basu son Ubaidullah yana nesa dasu.

Duk yaƙi ,ko kuma kama yan' ta'adda su Ubaidullah ake turawa.

Shekararsu daya da dawowa daga libya suka sake komawa wani yaƙin, inda aka dinga ɗauki ba'daɗi, da kyar su ka sha kamar ba zasuyi rai ba, amma da ikon Allah suka ci yaƙin, yayin da Ubaidullah shi da Zaidu suka ƙarasa wannan yaƙi a ƙasar. Bayan sun dawo aka gayyatoAlhaji Adamu, inda ya tsaya amatsayin Uba,
aka musu ƙarin girma, inda suka lashe muƙaman *first lieutenant* sannan suka samu kudi.


Ubaidullah ya kawo shawara suka haɗa kudi suka canzawa Alhaji Adamu mota.


Ya ce "a'a yarana kun fini bukatar kudi ,dan haka wallahi na yafe."

Su ka ce "ai ba dan yana da bukata bane kawai dan su faranta masa ne amatsayinsu na 'ya'yansa, dan haka ya karba ya saka musu albarka."

A lokacin ne kuma aka mai dasu *9JA BARRACKS* bayan sun dawo nigeria kenan.

Nan suka hadu da KB kuma suka zama abokai.

Tun da Ubaidullah ya tako kafarsa izuwa 9ja barracks to'fa nan ladies suka sakosa a gaba, amma ko kadan baya ɗaga ido ya kallesu balle yasan dasu.


Gida Ubaidullah ya gina wa mahaifiyarsa mai kyan gaske, inda yanzu a nan suke rayuwa, dan yanzu kudi yana shigo masa, dan first lieutenant ba wasa ba, da ma ance bayan wuya sai dad i,babu wanda yake fata ya mutu a wuya ko a talauci.


Wannan kenan shi ne taƙaicaccan tarihin *First Lieutenant Ubaidullah* wanda a yanzu akayi
masa ƙarin girma ya koma *CAPTAIN UBAIDULLAH*saboda yaƙin da sukaje agarin maiguduri, yayin da da yawan Sojoji sun gudu wasu kuma an kashe su, hatta su Ubaidullah sai da suka sha harbi kafin suka tsira.
Dawowar su da wata biyu shine aka musu ƙarin girma, sannan za'a sake tura su border nan da wata daya, wannan kenan."




___________ *Wasa farin girki*



Gaskiya ba kullum zaku dinga samun littafin nan ba,
Ina barar adduar ku
Ngd ngd ina ƙaunar ku masoya a duk inda ku ke.💖




COMMENTS
&
SHARE

BY MOMYN AHLAN✍🏻🤗
[8/19, 10:56 AM] Zarahh: *COLONEL UBAIDULLAH*
( _the story about a young gentle man_)



*ᏚᎢᎾᎡY ᏔᎡᏆᎢᎢᎬN ᏴY*✍🏻


*Z͢A͢H͢R͢A͢ A͢B͢D͢U͢L͢* (ᴹᴼᴹᵞᴺ ᴬᴴᴸᴬᴺ)


( *y̾a̾r̾ s̾a̾r̾a̾r̾i̾n̾ k̾a̾i̾n̾u̾w̾a̾*)
👸🏻 *SAHIBAR KAINUWA*👸🏻

_dedicated to my brother_

*U̶B̶A̶I̶D̶U̶L̶L̶A̶H̶I̶*

_my wattpab_@Fateemah0

_QAUNAR KU DABAN YAKE_
*ANTY HAUWA MMN USWAD*
*&*
*ANTY FAUZAH YAR AMANAR KAINUWA*
_ALLAH YA RAYA ZURIA MY ANTY'S_💘
____________________
_Alhamdulillah ina qara godewa Allah a ko da yaushe salati da daukaka da tsira da aminci su qara tabbata ga shugabanmu Annabi muhammad S,A,W da iyalan gidansa da sahabban sa da ma goya baya har izuwa ranar sakamako_🤲🏻
__________________
Ya Allah kabani ikon gamawa lpy🤲🏻


_dedicated to my *Fans*_


*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*


*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*____________________________________*

*page°°°°5&6*



Da washe gari suka fara fita ƙarin training a wajan commander Victor.


A cikin 2weeks Ubaidullah ya sauke nashi, dan shi baya wasa barin ma a wajan aikinsa na soja.


Ya fito zaije office dinsa suka hadu da Zeey.

sanye take da 3quarter na sojoji da black t-shart tana ganinsa ta taho da gudu tayi tsalle ta ɗaga kafarta,ta kai masa naushi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On COLONEL UBAIDULLAH
avatar
zainab-hassan

5 months ago

Reply

????

Please Login or Register in order to submit comment