Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

***★BAKIN ARTABU**cigaban
**JARUMA*YAZILA★***
Littafi Na Daya {1}
Na Abdul Aziz Sani Madakin gini..
TYPE Suleiman zidane kd...
Whatsapp 09064179602
*****
Marubucin ya fara da cewa:
====================================
Lokacin da aka kacame da azabebban yaki tsakanin jaruma dabira da jaruma yazila acikin keji sai suka wanzu suna masu kaiwa juna sara da suka cikin tsananin zafin nama. Juriya da jarumtaka tamkar jikinsu bana jini da tsokabane. Sai da suka shafe sa a uku cur suna wannan gumurzu amma dayansu bai sami nasarar koda lakuyar jikin abokin gwaminsa ba. ' Yan kallo kuwa da sarki raihan hankalinsu ya dugunzuma ainun bisa ganin yadda ako yaushe yakin nasu dabira kekara tsamari. Tashin hankalinsu sarki raihan shi ne. Idan jaruma yazila ta sami nasarar hallaka dabira sunyi asarar sarkin yakinsu wacce babu kamarta aduk fadin mayakan birnin. Lokacin da sa a uku ta cika sai dabira da yazila suka tsaya da yakin suka jada baya suka yi cirko cirko suna haki da kallon juna kamar zakaru saboda gajiya.
A sannan ne dabira ta fara tunanin hanyar dazatabi ta sami nasarar akan yazila amma kuma bisa mamaki sai taji zuciyarta na bugawa da karfi a duk sa adda ta kalli fuskar yazila.
Abu na biyu daya fado mata arai shi ne batun wannan laya dake wuyan yazila anya kuwa wannan laya dake wuyan yazila ba ita ce tasa nakasa samun nasara akantaba ? Yazama wajibi agareni na cire wannan laya daga wuyan yazila tunda dai tace daga hannun musulmi take.
Koda gama aiyana haka acikin zuciyarta sai tayi jifa da takobinta gefe daya ta dubi yazila tace , ” tunda dai munkasa yiwa junanmu illa da makami saimu gwada yar kashi domin mu kawo karshen wannan gabatamu ”.
Koda jin haka sai jaruma yazila ta bushe da dariyar mugunta irinta ma abota shirka sannan ta murkushe fuska kuma itama tayi wurgi da takobin tace. ” Ai dama haka nakeso. Domin ta haka ne kadai zamu iya bambancewa tsakanin aya da tsakuwa ” ™Nasiru Muhammad™
Nan take duk su biyun suka dunkule hannayensu suka gyara tsayawa sannan suka fara zagaya juna. Kwatsam ! Sai suka kacame da azababban fada suka rinka kaiwa juna naushi da bugu. Hannu da kafa.
Babu abinda zai baiwa mutane mamaki face yadda suke bugun jikinsu tamkar suna bugun buhun hatsi. Ma ana ko gezau basayi. Sai dai kaga sun shanye dukan sun maida martani.
Aikuwa kafin an juma sun hadawa junansu jini da majina. Ana cikin haka ne suka jada baya alokacin guda suka bayar da tazarar taku shida shida sannan suka rugo da gudu kowacce ta daka tsalle sama. Suna haduwa sai kowacce ta gabzawa yar uwar mummunan naushi a kumatu tun a saman feshin jini yai fitsar burgu daga cikin yanayi mai kama da suma
Suma.
Al amarin daya sa gaba dayan mutanen dake fadar suka mike tsaye zumbur cikin firgici domin a zatonsu jaruman biyu sunyi ragas babu wanda hankalinsa yatafi na kowa dugunzuma face sarki raihan domin yana mikewa tsaye a dimauce bai san sa adda maya ruga da gudu izuwa bakin kejin dasu jaruma dabira keciba. Al amarin humaira kuwa dama bata fito ba zata iya kallon wannan gumurzu da za ayi ba tsakanin yazila da dabira.
Lokacin da gari ya waye taji gaba dayan gidan sarautar tayi tsit tamkar babu mai rai acikinsa sai ta gane cewa lallai kowa na can fada ana kallon wannan fada daza ayi. Dama tun a daren jiya tsakanin yarta dabira da tsohuwar abokiyar gabarta tazila wanda tazo musu a siffar tsoho kasim. Bayan humaira ta gama dan kintse kintsenta saita mike tsam ta fito daga cikin turakarta ta kamaa tafiya acikin harabar gidan sarauta inda ta rinka arba da dai daikun dakaru masu tsaro da bayi masu kai kawokai tsaye humaira tawuce izuwa dakin da aka sayki bako ™Nasiru Muhammad™kasim duk inda ta wuce sai aka ga dakaru da bayi suna rissinawa suna gaisheta har ta isa kofar dakin da zuwa ta iske kofar dakin a bude batayi mamaki ganin hakan ba saboda dama tasan yanzu ankama yazila an tafi da ita.
Duk da cewa humaira taga fuskar jaruma yazila ajiya da daddare amma har ayanzu zuciyarta na wasi wasi akan anya kuwa yazila yarta ce?
Zuciyar humaira na bugawa da karfi ta kunna kai izuwa cikin dakin ai kuwa tana shiga tayi arba da jakar guzurin yazila wacce ke rataye ajikin bango. Kawai sai ta dauko jakar ta sauketa akas ta bude.
Nan take idanunta suka yi arba da wadansu surutu wadanda dabira tanada irin su sak. Sannan kuma taga rigar da aka sawa yazila a ranar da aka haifeta wacce dabira ma tanada irinta.
Koda ganin wadnnan tufafi sai humaira ta dubesu ta rungumeshi a kirjinta sannan ta fashe da matsanancin kuka domin a yanzu ta tabbata da cewa lallai yazila yarta ce kuma yar uwar dabira. Tana cikin wani hali ne ta tuno da cewa yanzu haka fa yazila da dabira na can fada suna yaki kuma za su iya kashe junansu.
A firgice humaira ta mike tsaye ta juya da baya a guje ta rungume da wannan tufafi ta nufi filin fada. * * *
Lokacin da yazila da dabira suka baje akas cikin mawuyacin hali. Sarki raihan ya rugo da gudu izuwa bakin kejin yana isowa sai yai turjiya bisa ganin abin daya faru.
Bawani abu bane yafaru ba face tashin yazila da dabira atare lokaci guda kamar wadanda suka farfado daga dogon suma.
A tare yazila da dabira suka mike tsaye. Kowacce ta sake dunkule hannayenta kuma suka goge jinin dake yoyo abakinsu. Kawai sai yazila ta kurawa hular karfen dake kan dabira idanu. Itakuma ta kurawa layar wuyanta ido take suka sake rugowa da gudu batare da sunyi ™Nasiru Muhammad™ yunkuri daka tsalle samaba.
Cikin bakin zafin nama dabira ta kaiwa layar yazila cafka tayi saar damketa kuwa itama yazila saitayi sa'ar damkar hular karfen dabira
. Alokaci guda kowacce ta cire abinda ta damka. Wato yazila tasami nasarar cire hular karfen dake kan dabira. Sai ga kyakkyawar fuskarta ta baiyana a fili dogon gashin kanta mai haske da kyalkyali ya zuba har kasan kwankwasonta.
Dabira kuwa sai tasami nasarar cire layar dake wuyan yazila tayi wurgi da ita. Atare duk su biyun suka naushi juna da kafa a kirji kowacce tayi baya taga taga kamar zasu fadi kasa. Amma sai suka cije.
Adai dai wannan lokaci ne sarki raihan da sauran gaba dayan jama'ar dake fadar suka kame kamar gumaka saboda tsananin mamaki bisa ganin yadda kamannin yazila da dabira suka zo iri daya sak tamkar an tsaga kara yazila da dabira suka kurawa juna idanu kowacce jikinta na tsuma cikin mamaki.
Bisa mamaki kuma sai kowacce ta sunkuya ta dauki takobi suka ruga ga juna suna ihu irin na manyan sadaukai domin su sake kaurewa da sabon yaki. Lokaci guda suka sake tsayawa suka waigo baya sakamakon jiyo muryar humaira wacce ta taho da gudu tana daka musu tsawa bisa umarnin su dakata da wannan yaki. Ai kuwa sai suka kame suka kura mata ido. Da isowar humaira sai tayi sauri ta bude kofar kejin dasu yazila ke ciki ta kamo yazila da dabira ta rungumesu atare ta fashe da matsanancin kuka
Gaba dayan jama ar dake wajen sai suka rude da kabbara ™Nasiru Muhammad™
Cikin yanayin rashin fahinta dabira ta janye jikinta daga cikin na humaira ta dubeta tace. ” Yake ummina yanzu kina nufin kice yazila ce yar uwatace da nadade ina son na gani ? ” Humaira ta gyada kai tace. ” Kwarai kuma ga cikkakkiyar shaida ”. Nan take humaira ta tunawa dabira wannan riga ta tarihi tace, "kin shaida wannan riga kuwa ? Irin taki ce da kike ta ajiyarta.
Ki gafarceni yake 'yata hakiki na boye miki wani babban sirri na dangane da asalinki da kuma tarihin tawa rayuwar. "
Koda humaira ta zo nan azancenta sai hawaye ya zubowa dabira ta dubi yazila tace, "ke kuwa me yasa kika boye kamanninki agareni ? Yanzu ashe ke jini nace amma ban saniba, yanzu inda da tsautsayi da shikenan sai dayammu ya kashe daya".
Yayinda yazila taji wannan batu sai itama zuciyarta ta karaya, hawaye ya zubo mata. Kawai sai ta bude hannayenta biyu tana mai fuskantar Dabira.
Nan take Dabira ta fada kan kirjinta suka rungume juna kuma suka fashe da kuka a lokaci guda suna dada kankame junansu.
A wannan lokaci gaba dayan jama'ar dake fadar suka cika da tsananin mamaki bisa ganin yadda Jaruma Dabira ta rungume babbar abokiyar gabarta.
Bayan dabira da yazila sun dan jima a rungume da juna kuma fadar tayi tsit kamar babu mai rai acikinta, sai yazila ta janye jikinta daga jikin Dabira ta dubeta cikin murmushi tace, "yake 'yar uwata kiyi sani cewa tun daga ranar da nazo garin nan naku naga irin yanayin rayuwarku naga ya banbanta da irin tamu ainun akan adalci,karamci da zaman lafiya, sai naji nakamu da sha'awar wannan addini naku Ina son yanzu take ki shigar dani wannan addininaku. Ina son yanzu take kishigar dani cikin addinin".
Koda jin haka sai Dabira ta cika da tsananin farin ciki batare da bata lokaci ba Dabira ta biyawa yazila kalmar shahada ta maimaita.
Koda sauran jama'a suka ji YaZILA tayi kalmar SHAHADA, sai suka rude da kabbara. Shi kansa sarki Raihan bai san sa'adda yakama murmushi ba saboda farin ciki.
Nan take sarki RAIHAN maya shiga cikin kejin ya kamo hannun DABIRA da YAZILA yajasu suka tafi izuwa cikin gidan sarauta, HUMAIRA nabiye dasu.
A sannanne fadar ta watse kowa ya kama gabansa kai tsaye sarki raihan, humaira, yazila da dabira suka wuce har izuwa turakar sarki raihan suka zauna.
Zamansu keda wuya sai wadansu likitoci mata guda biyu suka hau duba Yazila da Dabira suka samusu magani a fuskokinsu inda jini yafito. ™Nasiru Muhammad™
Bayan sun kammala aikinsu na likitoci sun fita sai Sarki Raihan ya dubi Yazila da Dabira cikin murmushi yace, "ya ku wadannan zaratan jarumai kusani yau ni da mahaifiyarku muna cikin matukar farin ciki bisa ganin yadda allah ya hadaku har kuka gane juna.
Tabbas shigowar yazila izuwa cikin addinin allah cigaba ne babba a garemu. Yanzu dai kafin na yiwa yazila bayanin halin da muke ciki ke humaira sai ki basu tarihin rayuwarki da yadda yazila da Dabira suka rabu tun suna jarirai, har izuwa lokacin da kika gudo izuwa nan kofar birninmu tare da mijinki aka kashe shi a gaban idanunki".
Batare da bata lokaciba Humaira ta kwashe dukkan labarinta ta zaiyane wasu yazila.
Ai kuwa tana gama bayar da labarin, Yazila da Dabira suka fashe da matsanaicin kuka saboda bakin ciki kuma suka harzuka ainun.
Cikin tsananin fusata Yazila ta mike tsaye ta dubi Dabira tace , "yake 'yar uwata kizo mu tafi izuwa birnin kisra yanzu domin mu dauki fansa akan sarkin kisra da sarkin yakinsa. "
Koda jin wannan batu sai dabira ta kama kafadun yazila tace, "yake 'yar uwata kiyi sani cewa zuwa da shiri yafi zuwa da wuri.
Ina tabbatar miki da cewa ahalin yanzu wadannan abokan gabar tamu ba a zaune suke ba, harma sunyi gagarumin shirin yaki sun taho nan garin domin su baje wannan birnin namu. Labari ya riskemu....."
Kafin dabira ta gama fadin abinda ke bakinta sai sarki Raihan ya tari numfashinta yace, "yake Dabira ai wannan jawabi bana bane, nawane".
Dabira tayi murmushi tace, "ka gafarceni yakai abbana hakika na wuce gona da iri".
Shima sarki Raihan sai yayi murmushi sannan ya dubi yazila yace, "yake 'yar uwar Dabira kiyi sani cewa a halin yanzu a ko yaushe abokan gaba zasu iya baiyana a kofar birninmu kuma labari ya riskemu cewa sun zo da mayaka masu tsananin yawa da ya wuce misali domin har gudummawar mayaka suka samu daga sauran kasashen makwabtaka.
Tabbas yanzu bamu da wani zabi wanda yafi mufita mutari abokan gabar nan tun gabannin su iso".
Koda sarki raihan yazo nan azancensa sai yazila ta dubi Dabira tace, "yake 'yar uwata kisani cewa nice sarkin yakin birninmu kamar yadda kike sarkin yakin nan birnin, saboda haka nasan dukkan sirrin mayakanmu da irin yanayin yakinsa, lallai zan bayar da gagarumar gudummawa a wannan yaki daza ayi kuma na tabbatar da cewa ba karamar barna zan yiwa su sarki Daksur ba.
Babban burina shine, na kashe sarkin yaki da sarki Daksur da hannuna".
Koda jin haka sai Dabira tayi murmushi tace, "ni kaina burina kenan domin dole ne mu dauki fansa akansu bisa bakin cikin da suka jefa mahaifiyarmu a ciki.
Ya ke 'yar uwata tunda dai yanzu allah yasa kin karbi addinin musulunci na san cewa zuciyarki zata sake kekashewa ga barin tsoro kuma zaki sami kwarin gwuiwa fiye da da can, saboda haka ina ganin idan muka hada karfi da karfe ni dake a wannan yaki zamu iya samun nasara akan abokan gaba ".
Kafin yazila ta budi baki tace wani abu sai sarki Raihan ya tari numfashin Dabira yace, "ba haka bane yake 'yata,ke dai kawai munemi taimakon allah, amma ai karfinmu ko dabarar mu baza su sa musami nasara ba akan makiya ba domin na tabbatar da cewa suma baza su fito ba kai tsaye sai da kyakykyawan shiri irin wanda basu taba yin kamar saba.
Yanzu abin da nake so dake yake Dabira ki tafi tare da 'yan uwarki yazila ki tara dukkan mayakan kasar nan ku fara shirye shiryen dabaru na yaki wanda yakamata kuyi, nima yanzu zan je na tara dukkan 'yan majalisata domin mutattauna akan wannan yaki, amma dai kusani nine wanda zan jagoranci wannan yaki inyaso kubiyu kurufa min baya idan allah yasa narayu abayan wannan yaki ™Nasiru Muhammad™ kuma nasami nasara za a daura aurena da mahaifiyarku domin mun daidaita junanmu".
Sa'adda sarki raihan yazo nan a jawabinsa sai yazila da dabira suka kamu da tsananin farin ciki basu san sa'adda suka rungume sarki ba a tare lokaci guda suka sumbaci goshinsa.
Batare da bata lokaci ba Yazila da Dabira suka fice daga cikin dakin da sauri suka nufi wani bangare daban na gidan sarauta inda suka iske wani barde a tsaye cikin shigar yaki.
Dabira ta dubi Barden tace, "ma za ka busa kahon tara mayaka domin yanzu nake son mu shirya yadda zamu bullowa wannan yaki". Koda jin haka sai barden yacika Umarni.
Ai kuwa nan take dakaru suka dinga tuttudowa daga wajen gidan sarauta suna rugawa izuwa filin fada suna taruwa da jeruwa a sahu-sahu.
Wannan shine abin yafaru abirnin misra bayan jaruma yazila taga mahaifiyarta da 'yar uwarta Dabira kuma ta karbi addinin musulunci.
*** ***
A can birnin kisra, bayan sarkin yaki da sarki Daksur sun yi bincike a cikin halwar tsafi sun ga duk abinda ya faru ga jaruma yazila wadda ta bijire musu kuma tazama babbar abokiyar gabarsu sai hankalinsu ya duguntsuma ainun domin sun tabbatar da cewa aikin dake gabansu ba kadan bane.
Bisa wannan dalili ne sarki daksur yasa aka shiga sauran kasashen kafirai dake makwabtaka don neman gudummawar Dakarun yaki. Duk sarkin da wasikar ta iskeshi sai yaba da hadin kai ya aiko da dakarun masu yawa da makamai da kuma isasshen guzuri.
A yamma da birnin kisra akwai wata babbar kasa mai suna tashwar.
Birnin tashwar na karkashin mulkin wani sadaukin saurayi ne, kyakykyawan gaske mai tarin arziki da karfin mulki.
Wani iko na allah shi dai wannan sarki baya tsafi kuma ™Nasiru Muhammad™tsafi baya tasiri akansa. Bisa wannan daliline gaba dayan sarakunan dake mulki a nahiyar suke shakkarsa domin ba a taba kai masa hari ba ko wargi.
Shi dai wannan sarki ana kiransa da suna Uhaisu bn kairuf. Sarki uhaisu yana da matukar karfin damtse na allah ya isa, domin komai girman giwa idan yayi mata naushi daya sai ta fadi kasa idan zai jarraba karfinsa ya kansa karti dari su rufar masa shi kadai, sai dai kaga ya bazarda su gaba dayansu sun baje a kasa suna yoyon jini a hanci da baki. Idan kuwa ya naushi mutun iya karfinsa tofa ko kashin karfe gareshi sai ya karye.
Sarki uhaisu bashi da wani addini don haka bai matsawa kowa ba a kasarsa duk addinin da mutun yaga dama yana da ikon yinsa. Wannan ya samo asali ne tun daga iyayensa da kakanninsa, haka ya taso ya samesu, basa addini kuma basa hanawa ayi.
Akwai wata rana sa'adda mahaifin sarki uhaisu ke kan gangarar mutuwa wato yana kwance acikin jinyar cutar ajali awannan yammaci da suka ka daita su biyu kacal a cikin turakar sarki sai uhaisu ya dubi sarki yayin da hawaye ya zubo masa yace, "ya kai abbana ina son nayi maka wadansu tambayoyi guda biyu wadanda suka dade suna yawo acikin zuciyata"
Koda jin wannan batu sai mahaifin nasa ya kamo hannunsa ya dorasu akan kirjinsa kuma ya kura masa idanu alokacin da shima idanunsa suka ciko da kwalla sannan ya budi baki da kyar yace, "ya kai dana na san tambayoyinka dake ranka kuma na dade ina jiran ranar dazaka gabatar dasu agareni.
Tabbas yanzu ne lokacin daya dace kayi mini wadannan tambayoyi domin tun kana karami na boye amsarsu, kuma gashi harka girma kakai munzalin dazaka gajeni amma baka san amsar tambayoyin ba wadannan suke faman damunka acikin zuciya.
TAMBAYARKA TA FARKO AKAN ADDINI CE. Kana so kasan dalilin dayasa bamu da addini? Tambayarka ta biyu kuwa itace kana so ka san dalilin da yasa naki yin aure, kuma kaima ban taba nuna maka ina da ra'ayin kayi aure ba? Kasaurara da kyau kaji amsar wadannan tambayoyi naka kuma kayi amfani da basirarka wajen amfani dasu domin idan baka nutsuba har abada bazaka sami daraja da daukaka ba irin wadanda na samu a rayuwata.
Dalilin dayasa bamu da addini shine, mahaifina kafin yarasu nayi masa irin wannan tambaya, domin yadda ka taso babu addini. Kuma babu aure haka nataso amsar da yabani itace.
"Ya kai dana kayi tunani yanzu addinai sun yi yawa a cikin wannan duniya, akwai masu bautar rana, wata, ruwa, wuta, gumaka, dabbobi da sauransu. Kai wasu ma aljanu suke bautawa. Mahaifina yaga yamin cewa addini guda daya ne, kuma ubangiji daya ne wanda shine na gaskiya mai ikon komai da kowa.
A wannan zamani babu wannan addini kuma kaima zaka riski wannan addininne a karshen rayuwarka, abu ne mawuyaci kasan wannan addini amma wata kila in ka sami haihuwa danka yasan wannan addini.
To ka gaya masa cewa duk ranar da wani gagarumin yaki ya taso ya halarceshi domin a wannan tafarki ne zai san wannan addini na gaskiya har ya fahimceshi kuma ya aminta da shi "
Sa'adda mahaifina yazo nan azancensa sai na cika da mamaki na dubeshi nace, "ya kai abbana ashe baka gaya min cewa yaki ba zai taba zuwa birnin tashwar ba? Ya kuma yanzu kake mini batun yaki ?"™Nasiru Muhammad™
Koda jin haka sai mahaifina yaja numfashi tamkar ransa zai fita, a sannan yace, "bana nufin yaki zai zo har nan ya riskeka, ina nufin za'a aikomaka da sakon gayyata. Lallai ka amsa gayyatar, amma kafita yakin kai kadai, kada ka kuskura ta tafi da kowa idan har kana son kasan addinin gaskiya.
Dangane da tambaya ta biyu dake ranka kuwa ba wani abubane face batun aure. Tun da mahaifiyarka ta rasu ban sake yunkurin aureba.
Haka mahaifina ya kasance, shima mahaifina haka rayuwarrsa ta wanzu har izuwa kan kakanmu na arba'in da daya.
Abinda nake nufi anan shine duk wanda yai aure acikinmu haihuwa daya yake samu kuma sai matarsa ta mutu, shima sai yamutu yabar abinda ya haifa.
Lokacinda aka haifeka sai naji babu abinda nake so a duniya sama da kai, kuma naji ina son kayi nisan kwana a duniya.
A cikin gidan sarautar nan akwai wani daki guda daya wanda ba'a shigarshi kuma kai ma baka taba ganin an shigeshi ba, haka ne?"
Kodajin wannan tambaya sai na jinjina kaina nace, tabbas na san da wannan daki kuma na dade ina mamaki da tunani akansa."
Mahaifina ya sake ajiyar zuciya yace, "Akwai wani aljani bawanmu a cikin wannan daki wanda bama bauta masa shima kuma baya bauta mana, amma zaman amana ne da kauna tsakanin zuri'armu da tasa. Duk abinda zai samemu a rayuwa shi wannan aljani ne ke sanar damu.
Zidane kd.
Marubucin ya cigaba da cewa:
==============================
=============================
A iya tsawon rayuwata ta duniya sau daya na taba. Ganawa da wannan aljani kuma shine ya gaya mini cewa kada na kuskura na kara yin aure a rayuwata. Idan kuwa nayi sai an kawo harin yaki izuwa kasata an kawar dani. Yakai dana kaima kayi amfani da wannan nasiha wacce wannan aljani yayi mini kuma kada ka kuskura ka shiga dakin da wannan aljani yake domin ku gana sai ranar daza ka fita wannan gagarumin yaki da aka gaiyaceka. "
Har kullum sarki Uhaisu baya mancewa da wannan jawabi na mahaifinsa don haka sai ya hakura da batun aure gaba daya a rayuwarsa saboda yana son yayi nisan kwana a cikin daular mulki daya tsinci kansa a ciki.
A ranar da wasikar gaiyata izuwa yaki ta riski sarki Uhaisu daga birnin kisra sai yacika da tsananin farin ciki domin yasan cewa lokacine yazo da zai cika babban burinsa na duniya domin yasan mahaifinsa ya gaya masa cewa bayan anyi wannan gagarumin yakinne zai iyayin aure har ya sami magaji kuma lallai zai yi tsawon rai a duniya.
Lokacin da maga-takarda ya gama karanta wasikar gayyata a fadar sarki Uhaisu fadawansa suka ga ya cika da farin ciki sai mamaki ya kamasu domin su a saninsu babu sarki ya tsana sama da yaki kuma babu abinda yafi so sama da zaman lafiya. ™Nasiru Muhammad™
Sarki Uhaisu ya kasance mutum mai adalci, tausayi da jin kai, gashi da karrama mutane, wato bai iya wulakanci ba bashi da izza da jin kai irin na sarakai, duk da cewa allah ya bashi karfi, kyawu da dukiya mai yawan gaske.
Bisa wannan baiwa da allah ya baiwa sarki Uhaisune ya zama cewa 'yan mata, 'ya'yan sarakai, attajirai da manyann matsafa suka kamu da tsananin kaunarsa, wasu da yawansu a dalilin kamuwa da sonsa ne ma
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2

Please Login or Register in order to submit comment