Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[ 🧣🧣 *DAURIN BOYE* 🧣🧣


*NA*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*


HASKE WRITERS ASSO

(home of expert and perfect writers)✍


*_Dandano daga littafin DAURIN BOYE_*



0⃣1⃣


Sake gyara tsaiwarshi yayi jikin machine din nasa samfurin lifan kirar MOTO B,agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa ya kalla yana sake qiyasta mintocin daya kashe tsaye a qofar gidan,tabbas banda wani babban dalili babu abinda zaya sanyashi zaman jira har kamar haka,babu abinda ya tsana a rayuwarshi kaman jira,mutum ne shi mai kiyaye qa'ida wanda bai yarda da samfurin wannan maganar da hausawa ke bawa lokaci ba na african time.


Sauke hannun nashi yayi ya maida dubansa ga madaidaicin get din dake maqale da katangar gaban gidan wanda ya kasance shine kofar da zai sadaka da ainihin cikin gidan,kaman jiran hakan kuwa ake qofar ta soma yunkurin budewa,cikin sakannin kadan matashiyar dake yunqurin bude qofar ta bayyana.


A hankali take takowa zuwa inda yake,sanye cikin dinkin atamfa riga fitted da skert wanda ya zaunawa jikinta das,ta lullube jikinta da mayafi wanda baikai matsayin medium ba,a hankali yayi kokarin mamaye fuskarshi da murmushi duk da yadda fuskarta take kadaran kadaham hakan bai dameshi ba duk da yana ankare,ba fara'a sannan ba kuma a daure take can ba,kallo take kare masa tun daga nesa kaman yadda ta saba masa duk sa'ilin da ya ziyarceta,shirt ce jikinsa ruwan makuba da bakin wando jeans mai matsakaicin kudi,kafafunsa saye da takalmi budadde dinkin hannu na kasuwar kofar wambai,fes yake hakanan kayan sun masa kyau babu laifi,sumarshi kanshi zuwa sajensa a gyare a taje wanda hakan ya sake bayyana sirrin kyan da Allah ya bashi,ba shakka banda wani abu guda tak muhammad ya cika mijin aure wanda za'a iya nuna shi a ko ina,saidai wannan abun daya rasa din ya sanya ta cireshi daga tsarin mutumin daya cancanci aurenta.


"Barka da fitowa gimbiya zulaiha" ya fada cikin sassanyar muryarsa wadda na daya daga cikin abinda ke burge zulaihan tare da shi,duk da bata jin zata iya bashi damar kasancewa cikin rayuwarta,yana ci gaba da nazarin yanayin fuskarta a fakaice sanda ta amsa masa
"Barkan ka" ta fada cikin wani salon shan qamshi da basarwa
"Har na fidda rai ai,na tsammaci yau bazan samu ganinki ba"
"Kusan da hakan ce ta kusa faruwa,saboda zamu fita ne da maama,sannan ma kuma bansan zaka zo din ba,yanzun ma zuwa nayi na gaya maka.....don Allah ya kamata ace duk sanda zaka zo ka fara sanarmin tukunna kafin kazo din"ta fada kanta tsaye tana yamutsa fuska murmushi ya saki gami da dan duqar da kanshi qasa yana wasa da duwatsun dake shimfide a qofar gidan,baice komai ba sai murmushin da yaci gaba da fitarwa yana tattaunawa shi da zuciyarsa,tabbas yasan wannan rana na nan tafe,fiye da haka kuma na nan zuwa nan gaba kadan,wannan ba baqon lamari bane a gareshi,zulaiha ba itace mace ta farko da makamancin hakan ta faru tsakaninsu ba,saidai bazai yanke mata hanzari ba,zai jirata har zuwa ranar da zai zata furta kota yanke alaqar dake tsakaninsu da bakinta,sai bayan daya kammala wannan tunanin sannan ya dago ya dubeta
"Shikenan....babu damuwa...kiyi hakuri" ba tare data tanka ba ta juya tana niyyar komawa cikin gidan nasu
"Ki gaida maaman idan kin shiga"
"Zata ji" ta fada gami da jan qaramin tsaki can qasa ta shige gidan gami da rufe qofar gidan garam.


Kai ya girgiza bayan shigewarta cikin gidan yana sakin murmushi tare da cije lebansa na qasa,cikin qwarewa ya haye saman babur din bayan ya tadashi ya figeshi cikin gudu ya fice daga layin,zuciyarsa cike fal da tunani da mamaki,mamakin da har yau yaqi barinsa,tsahon shekaru kenan wannan abu na daure masa kai,da gaske haka rayuwa ta koma?,ya gode Allah da baiyi gaggawar yiwa hukunci wa rayuwarsa ba.


Titi ya hau ba tare da yayi wata doguwar tafiya ba ya soma sauka daga kan kwaltar zuwa gangaren titin,daf da wasu jeran baqaqen motoci da farare a qalla guda biyar ya soma qoqarin tsaiwa,wanda tun kafin ya kai ga tsaiwar wasu matasa kimanin su bakwai sanye da coat baqi da fari suka doso shi,kowanne fuskarshi manne da baqin gilashi wanda hakan ya sanya baka iya ganin qwayar idanunsa,ya kuma qara musu kwarjini qwarai,daya daga cikinsu shi ya riqe babur din sanda ya sauka,yayin da dayan ya matso kusa da shi yana bude masa qofar daya daga cikin motocin wadda duka ta fisu kyau da girma,sai da yaga ya shiga sannan ya rufe masa qofar,sauran suka zagaya suka shige ragowar motocin nasu,yayin da daya daga cikinsu shi kuma ya haye babur din ya bisu a baya.


"Ya dai,akwai wani sauyi ko ci gaba kuwa yau?" Wani kyakkyawan matashi wanda aqalla zaiyi shekara talatin da hudu dake zaune daga corner motar riqe da magazine ya fada yana dubanshi,fuskarshi na nuna alamun dariya yakeson yi,takalman qafarsa ya soma yunkurin cirewa gami da agogon hannunshi ba tare daya dubeshi ko ya amsa masa ba,ya dannan wani madanni dake gaban sit dinshi,wani qaramin akwati ne ya fito ya zuba agogon takalmin harda wayar dake hannunshi qirar VIVO bayan ya kasheta,ya maida akwakwun muhallinsa ya jingina da makarin kujerar sannan ya waiwaya ya dubeshi
"Me kake tunani mahmoud?,ita dinma kaman sauran,abun ma kamar yana sake lalacewa ne" ya qarashe maganar yana lumshe idanunsa tare da sauke numfashi


"Duk inda xaka je ka dawo dai shawarata ce kan hanya,na sha gaya maka ka sauqaqewa kanka walaha,ka laluba cikin familynka,akwai gomayyar 'yammatan dake sonka ka zabi daya cikinsu ka huta,kaga wannan babu wani fargaba tattare da kai,duka ana tare". Kansa yaci gaba da girgizawa ba tare daya bude ido ya kalli mahmoud ba,tsahon sakanni tamkar bazai amsa mishi ba sannan ya ware idanunsa yana duban sit din dake gabansa
"kana tunanin qaramin abu ne ya sanya na guje musu dukkaninsu na xabi inbiyo ta wannan hanyar?,su dinma kusan duka abu guda ne,babu wani banbanci,halayyar daya ce dai kaman yadda sunansu yake daya,abu guda dukkaninsu suke wa,manufarsu guda ce......" Maganar tashi ta katse sakamakon shigowar kira wayar tasa,ya maida qwayar idanunsa ahankali kan wayoyin dake zube a gefansa,kusan lokaci guda idanunsu shida mahmoud suka sauka kan wayar RAMLA sunan dake yawo kenan bisa screen din,murmushi mahmoud ya saki ganin ya kau da kanshi tamkar ba cikin wayarshi kiran ya shigo ba
"Yallabai ka daga mana?"
"Qyaleta kawai" ya bashi amsa kai tsaye gami da danna wani madanni,wani dan qaramin abu mai kama da fridge ya bayyana,cikinsa nau'ikan abubuwan sha ne masu sanyi da duka duka basu wuce gwangwanaye da kwalba goma sha biyu ba,daya a ciki ya dauka hadi da cup ya maida abun muhallinsa ya koma ya jingina da kujera ya tsiyaya yana kaiwa bakinsa ba tare da yabi ta kan qorafin daga waya da mahmoud ke masa ba,a maimakon hakan ma sai ya maye gurbin qorafin nasa da tambaya
"Jirgin qarfe nawa zamu bi ne?" Tunda ya masa hakan yasan bai bukatar xancan,saboda haka shima ya tayashi
"Yanzun airphort din muka nufa ai,tunda duka duka awa guda da 'yan mintuna ya rage lokacin tashin jirgin ya cika"
"Ok,kafin nan mu biya na sauya kayan jikina"
"Ba matsala" ya fadi yana gayawa driver inda zasu fara zuwa kafin su isa airphort din.


🧣🧣🧣🧣


A nutse ta miqe daga saman abun sallar tana sakin 'yar qaramar hamma tare da furta "a'uzu billahi minash shaidanir rajim" gami da ninke daddumar ta mata ma'ajiya a muhallinta,zare hijabin jikinta tayi tanayi tana duba agogon dake maqale a bango saboda gudun makara,qarfe shida na safiya ya nuna mata,hakan ya mata dadi ta tabbatar kafin lokacin tafiyarsu makaranta ta kammala dukkan abinda zata yi din,gyara dankwalin kanta tayi wanda ke niyyar zamewa saboda santsinsa da kuma santsin sumar kanta,sannan ta zura slippers ta bude qofar dakin nata ta fita a hankali.


Makekan falon nasu shiru yake tamkar babu halittar kowa cikin gidan,bugu da qari mamaye yake da dan sauran duhun asuba da bai gama yayewa ba,babu motsin kowa,don hatta da masu aikin gidan basu tashi ba,kunna qwayayen falon tayi take haske ya game ko ina ya kuma bayyana asirin kyan da falon ke da shi,sannan taci gaba da takawa a hankali ta doshi wani corridor wanda a nan kitchen dinsu yake.


Kitchen ne na alfarma wanda ya mallaki dukkan wani nau'in kayan amfani da kitchen ka iya buqata,kai tsaye ta nufi jikin wani dan qaramin Allo wanda ke dauke da timetable na abincin da gimbiyar gidan ke buqata kowacce rana,alhamis ce saboda haka ta sauke idanunta kan THURSDAY dake rubuce baro baro,ta kuma karanta abincin dake qarqashin ranar,kanta ta jinjina saboda yau aikin nata kaman mai yawa ne,gashi a jiya bata samu ta duba me zata girka ba yau sakamakon bacci fa yayi nasarar saceta tana tsaka da karatun test da zasuyi a safiyar yau,cikin hanzari ta bude freezer ta fiddo dukkan abinda zata buqata,sannan ta wuce store dake cikin kitchen din ta fiddo kayan amfani,sannan ta soma aikinta cikin hanzari da qwarewa.


A qalla ta shafe kusan mintina talatin sannan ta jiyo motsi alamun ana niyyar shigowa kitchen din,fuskarta qunshe da murmushi wanda ya sanya dimple dinta dake dukka kumatunta lonawa,tunkan ta qaraso tasan wacece,ita kadai ke tashi ta kama mata aiki,ita daya ce matar da hakanan Allah ya hada jininsu take qaunarta,ita daya ce take ganin qauna daga idanunta,irin qaunar data rasa,irin qaunar da take buri da fata ta ganta daga wajen wadda tayi silar kawota duniya saidai har yau abu yaci tura,a wajenta ne kawai take ganin kulawa qauna da kuma sassauci.


Ita dince kuwa,daya daga cikin masu aikin gidan ce inna laraba,fuskarta fadade da fara'a tace
"Yanzu inna laraba yau dinma ba zaki kwanta ki huta ba?,ina cewa jiya da qyar kika samu ciwon qafar nan ya barki?" Itama fuskarta qunshe da fara'ar tace
"Banda abinki shatu ai kema kinsan ban saba da wannan baccin bayan sallar asubar ba,kuma na tabbatar kina nan ke daya kina fama da kacaniya" ta fada tana qarasowa kusa da ita,murmushi ta saki sannan cike da girmamawa ta gaida innar kaman yadda take kiranta tare da tambayarta ya qafar tata,amsa mata tayi itama cikin kulawa kafin ta matso da niyyar kama mata aikin,duk yadda taso hanata amma innan sam taqi,haka ta sakar mata suka ci gaba da aikin tare suna hira.


Bata ankara ba taga lokaci ya ja,har qarfe tara saura na safiya,idanu ta zaro don tun jiyan da daddare anty asma'u ta ja mata kunne cewar qarfe tara zata fita,kuma driver ba tsayawa jiranta zaiyi ba,ruwanta ta shirya da wuri ruwanta karta shirya ta samu mai ajjiyeta makaranta"hakan ya sanya ta tattare komai a gurguje ta soma shiryawa saman qawataccen teburin cin abincin dake sashe na musamman dake cikin falon.


Plates da spoons suka rage suta dauko ta dawo da niyyar ajewa daga nan ta shiga ciki ta shirya itama,duk da cewa ita sai goma zata fita,amma dole ta shirya tabi asma'un koda qarfe bakwai asma'un zata fita,tsaye ta tadda ta shirya tsaf cikin wata doguwar rigar material,ta zuba makeup sosai,hannunta maqale da 'yar madaidaiciyar hand bag mai azabar kyau,kafadarta rataye da mayafinta wanda wanda haka qa'idar saka mayafinta yake,qwayar idanunta saye da tafkeken sun glasses wanda ya kusan cinye rabin fuskarta,table din take qarewa kallo har sanda aysha ta qaraso wajen tana dora plates din saman teburin gami da gaida asma'un.


Bata damu da amsa gaisuwar da take mata ba saima tambayar data jefo mata
"Waima baki shirya ba?" Ta fada cikin bacin rai tana zare glass din fuskarta kasancewarta mace wadda qanqanin abu sai ya bata mata rai ko ya tunzurata
"Yanzun zan shirya in sha Allahu" ta fada a tausashe,cikin hasala asma'un tace
"Kada ma ki shirya wannan ya rage naki,ni dama na soma gajiya da tafiya dake gaskiya,ya kamata daddy ya barni haka nan ya raba mana tafiya tunda babu dole.....ina cewa tun jiya na sanarmiki lokacin da zan fita,amma saboda tsabar raini da salon ki jawa mutum fada baki tashi kin gama komai a kan lokaci ba"
"Kai...kai me yake faruwa haka da sassafen nan kuma lafiya?" Cikin bacin rai asma'u ta juya tana kallon mahaifiyarta dake saukowa daga stairs,shirye cikin tsadajjen lace na alfarma,hannayenta da wuyanya duka sanye da jewels da banguls masu tsada
"Mommy nida yarinyar nan ne mana,wai ki duba fa jiya gabanki na gaya mata when zan fita shine wai har yanzu bata shirya ba"
"Garin yaya ke ayshatu?...." Jin tambayar tayi banbarakwai,tunda dukkaninsu sunsan me ya tsaidata,hidimar abincin safen asma'un ne,wanda dukkansu sun kwana da sanin cewa don ta itama a soke abincin safe,totally ma ba damuwarta bane abinci
"Ya kuma kika tsaya,jeki ki shirya,idan kuma har ta gama baki fito ba sai ki samu napep ya kaiki" ta fada itama tana jan daya daga cikin kujerun dining din da alama karyawa zatayi akwai muhimmiyar fita kenan.


Juyawa tayi a hankali ta doshi corridor din da dakunansu suke,sam batayi mamaki ba tunda ba yau bane farau,hajiya sa'adatu irin matan nan ne da basu cika ganin aibu ko laifin dansu ba,bugu da qari tana da attitude na idont care kan lamuran da ba nata ba,tayi ma rawar gani yau data tanka,idan da taso Allah ya kyauta kawai zata ce tayi zamanta ta hau hidimar gabanta ya tasu koma ya zasu qarke ohon mata,indai hakan bazai shafi shalelen tata ba ko kuma ita bazai kawo mata wani cikas ba.


Duk da cewa a gurguje ta shirya amma hakan bai sata ta samu nasarar tadda asma'un ba,saima hajiya sa'adatu data samu tana yunqurin bude murfin mota zasu fita ita da drivanta,kallo daya tayi mata tace
"Gashi har asma'un ta wuce tun dazun,saidai ki qarasa titi kibi ta haya" ta qarashe maganar tana shigewa motar tare da yunqurin rufewa
"Ba komai zan qarasa din mommy,a dawo lafiya"
"Allah yasa" ta masa sanda drivern ya fara jan motar suna niyyar ficewa daga gidan ba tare data damu da yadda ayshan zata kai kanta makarantar ba.


Tana nan tsaye har motar mommy ta fice sa'annan ta soma takawa a hankali cike da nutsuwar data zama tambarinta tabi bayan qurar motar ta fice daga gidan ta 'yar qaramar qofar dake maqale jikin get din.


Duk da yake akwai 'yar tazara kadan tsakanin gidan nasu da bakin titi amma sam bata ji tafiyar ba,hakan ya faru ne sakamakon yadda qwaqwalwa da zuciyarta baki daya sukayi zurfin tare da nisan kiwo wajen tunani,tunani qwaya daya da ko yaushe bata gajiya da shi,hakanan batasan randa babin tarihin rayuwarta zai rufe ba,hakan batasan meye qarshen nasa ba,yaya qarshen nasa zai kasance?,wata iriyar cukurkudaddiyar rayuwa da tayi take kuma kanyi ita ke mata kai kawo cikin qwaqwalwarta.


Sam ta sha'afa sai data tsaida mai napep sukayi cinikin nawa zai kaita sannan ta laluba jakarta cikin fargabar ta fito da kudi?,Allah ya taimaketa jakar a ciki ta sanya kudaden da daddy ya bata sanda zaiyi tafiya,ta sauke ajiyar zuciya a hankali tana hamdala cikin zuciyarta.


Kusan babu wanda ta tarar cikin ajin,sakamakon akwai tazarar awa guda daga lokacin da za'a shiga lacture din da sanda tazo,guri ta samu na musamman inda tafi sha'awar zama ta zauna,sa'an nan ta zaro handout dinta taci gaba da dubawa kafin lokacin da zasu zana test din ya cika.


*mrs muhammad ce*👑
[09/01, 4:17 PM] +234 803 238 4602: 🧣🧣 *DAURIN BOYE* 🧣🧣


*NA*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*


HASKE WRITERS ASSO

(home of expert and perfect writers)✍



0⃣2⃣





Kusan rabi da rabi take karatun,fiye da rabin hankalinta ya ta'allaqa ne akan wayarta,wadda ba komai take kalla ba sai wasu numbers wanda ke rubuce da sunan MAMA NA,ta kallesu yafi sau shurin masaki,ta kwatanta kira fiye da irgen yatsun hannunta saidai ta kasa hakan,ba wani abu bane ya jawo haka ba illa tsoro da fargabar abinda kiran zai biyo baya,taji ance bata ji dadi ba,tana so ta kirata ta mata sannu da jiki,saidai bata da wannan damar,ba qaramin qunar baqin wake take ba duk sanda tayi jarumtar kiranta,wanda hakan daga qarshe baya haifar mata da d'a mai idanu.


"Qawata sarkin sammako" taji an ambata ta gefanta,wayar ta rufe ya dago kai fuskarta qunshe da murmushi tana duban Aliya dake sauke jakarta daga kafada kana ta yiwa kanta mazauni kusa da ayshan itama tana murmushi
"To ya za'ayi" ayshan ta maida mata amsa tana gyara zamanta
"Hala yauma uwar masu gidan zata fito da wuri ne kika kwaso qafa kika biyota?" A maimakon ta bata masa murmushi ayshan ta saki,tasan halin rigima sarai irin na Aliya.

'Yar tsama suke qwarai da asma'u,basa hada hanya da ita,saboda banbancin halaye qwarai dake tsakaninsu,bugu da qari tana jin haushin yadda take mu'amalantar ayshan wadda ta zame mata qawa kuma aminiya a dui fadin makarantar,sosai Aliya keson aysha sabo managartan halayenta,nutsuwa haquri gami da kunya,uwa uba ayshan na daya daga cikin daliban da sukayi fice a duk fadin department dinsu,kai bama iya tsangayar tasu kadai ba a duka makarantar ma.

Kai Aliya ta kada cikin takaici,saidai ayshan bata bata damar cewa komai ba ta tareta
"Kinso yau ki makara qawata,ya akai haka?"
"Hmmm,wlh yau mama ta tsaidani sai dana hadawa ya khalil breakfast,Allah ne ya soni na masa sharp sharp na fece,da Allah ne kadai ya san makarar da zanyi" duka tana zancan ne sanda take ciro handout dinta daga jaka,kafin su sake cewa komai lacturer din ya shigo ajin.


Qarfe uku na rana ta kammala duk abinda zatayi cikin makarantar,hakan ya sanya ta tattara komai nata ta fito don ta qarasa inda zata samu asma'u,saidai koda taje wayam taga wurin babu alamun motarta,hakan ke nuna bata cikin makarantar,bata wani damu ba ta soma takawa da qafa don zuwa bakin get din makarantar don ta sami abun hawa,don yau Aliya ta rigata tafiya gida,ita ta tsaya ta dudduba wasu karatuttuka.


Jin qarar mota a bayanta ya sanyata sake rabewa don bawa motar damar wucewa,a sannan idonsu ya hadu da drivern,asma'u ce,ita da wasu mutum biyu a motar,da alama qawayenta ne,dauke kai asma'un tayi tamkar bata ganta ba,sai tama qarawa motar wuta tayi hanzarin wuce ayshan,sam hakan bai dameta ba,saboda ba yau farau ba,babu abinda asma'un ta tsana nan gidan duniya irin alaqar da zata bayyanar da cewa ayshan jininta ce,gida daya suka fito ko suna da dangantaka,tunda ayshan ta fahimci hakan sai itama take baya baya da duk wata alaqa da zata hadata da asma'u cikin bainar jama'a.


Kai ta jinjina kawai taci gaba da takawa zuwa qofar makaranta,wannan abun na asma'u zata iya cewa bai bata ranta ko kadan,idan ma ya bata din bai wuce digo daya cikin dari ba,a yanzu qyamatar da take fuskanta take kuma bata mamaki ta shafe ko wacce iriyar qyama da qiyayya da dukkan wata halitta zata nuna mata a doron duniya,dukkan wata tsana saidai ta biyo bayan waccar,da wannan tunanin ta tsaida wani dan sahu dake niyyar gifatata ta masa kwatance inda zata ta fada ciki.


Kamar kullum yauma a qalla ya kusa shafe mintuna ashirin yana tsaye yana jiranta,har sai data kaishi ga qosawa ya haye saman babur din da yazo da shi ya zauna,saboda rashin sabo saura kadan babur din ya tuntsira da shi Allah ya taimaka cikin zafin nama yayo gaba ya dawo ya zauna dai dai,mahmoud dake zaune cikin motarsu dake fake a wani layi ya tuntsire da dariya harda duqawa,ba don ba dabanba da ya fito ya masa vedio ya ajjiye saboda tarihi,saidai yana tsoron tashin balli tilas ya zauna cikin motar kamar yadda yayi masa umarni.

Sake duba agogonsa yayi yana qissimawa ranshi mintinan da zai qara wanda matuqar bata fito ba zai qara gaba,a gajiye yake,daga airphort yake ko gida bai isa ba ya sauya kaya ya canza akalar tafiyar tasa zuwa gidansu,bayan ya yiwa daya daga cikin yaranshi waya ya kawo masa babur din,kwanaki goma ya kwashe a qasar da yaje,bai kuma samu damar kiranta ba tunda ya tafi saboda gudun tonuwar asiri,don kada ta tsammaci ya janye hakan ne ya sanyashi tahowa kai tsaye gidansu.


Kamar ko yaushe yauma haka fuskarta take,ta qaraso inda yake saidai a yau waya take amsawa,ganin ta iso gareshi yasa ta bada uzurin zata sake kira ta kashe wayar ta lanqwasheta a hannunta yauma tana sake qare masa kallo a kaikaice
"Allah ya baka kyau na nunawa sa'a,saidai hakan ba zaiyi tasiri a raina ba saboda kana da babban naqasu na rashin hatimin nasara" duka take wannan maganar a ranta,sama sama suka gaisa tamkar baqin juna,shi kansa yana jin wani irin cikin ranshi,duk yadda yaso kawo sabo da shaquwa tsakaninsu zulaihat taqi bashi dama.


Shiru ya ratsa tsakaninsu bayan ya gama iya maganganun da yaga sun kamata,saidai rashin samun gamsashshiyar amsa yasa maganganun nashi basuyu tsaho ba
"Ammm...dama akwai abinda nakeson gaya maka"
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment