Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

***★BAKIN ARTABU**cigaban
**JARUMA*YAZILA★***
Littafi Na Biyu {2}
TYPE A
***Nasiru**Muhammad**Tijjani***
Marubucin ya cigaba da cewa:
==============================
=============================
KOFAR birnin misra ta cika ta batse da dakarun yaki, babu masakar tsinke. Amma gaba dayan mayakan adadinsu bai wuce dubu dari uku da ashirinba.
Tsaye a gaban rundunar masu jagorantarsu mutun ukune. Na farko shine sarki Raihan, na biyu kuwa JARUMA YAZILA, sai kuma JARuMA DABIRA.
Yazila da dabira sun yi shigar yaki ne iri daya kuma duk sun sanya kayan karfe, kowannensu ya rufe jikinsa ruf! Baka isa ka gane cewa sun kasance mata ba saboda sun rufe kansu da hular karfe sun boye gashin kansu.
Shikuwa sarki raihan shigar bakin sulke yayi, kuma takalminsa ma bakine na kafa. Hatta kufen takobinsa da garkuwarsa duk bakake ne.
Kwatsam! Sai aka jiyo bugun tambura da ganguna yana tashi daga sama. Nan da nan sautin ya cika dodon kunne, kai kace makadan duniya ne suka taru suke buduri.
Lokacin da tawagar mayakan ta matso kusa kuwa aka ga yawansu sai kowa ya firgice, aka razana ainun, saboda yawansu ya ninka na mayakan birnin misra sau dubu.
Kura ta tshi ta turnuke sama, karar kofatun dawakai da haniniyarsu ta cika dodon kunne.
Kai! Komai jarumtakar mutun idan ya hango wannan runduna ta susarki DAKSUR dole ne ya firgita ya yi zaton ma yakin duniya ne ya barke.
Bisa mamaki sai rumdunar su sarki daksur suka ga kokadan abokan fadan nasu basu razana da ganinsu ba. Maimakon masu firgice ko su dimauce sai suka kara nutsuwa kuma kowa ya tsaya a inda yake, jira kawai yake yaji umarnin daza a bashi.
Bawani abubane yasa basu razanaba face addu'ar da suke ta. Faman karan tawa acikin zukatansu gami da neman taimakon allah.
Lokacin da su sarki Daksur suka hango abokan gamansu suka gansu 'yan kadan a gabansu tamkar a ajiye dan tsako a gaban shirwa. Kuma suka ga kokadan basu firgitaba, sai al'amarin yayi matukar basu mamaki, ya zamana cewa allah ya juya tsoro da shakku a zukatansu.
In ka dauke mutum uku da suke dasuke jagoran tarsu, gaba daya sauran mayakan duk sai tsoro ya darsu a cikin zuciyarsu harma suka sauka fara nokewa abaya kadan-kadan kawai jira suke yi suga yadda zata fara wakana ga manyan jarumansu a baban dogaronsu.
Sarki Uhaisu ne akan gaba, yana tafiya kai tsaye ba tare da shakkar komaiba , har maji yake kamar ya sauka daga kan dokinsa ya ruga da gudu izuwa cikin abokan gaba ya hausu da sara da suka saboda zakuwa da dakewar zuciya irin ta JARUMAN KWARAI.
A hannun daman sarki Uhaisu, sarki Daksurne. A hagunsa kuma sarkin yakine.
Lokacin da ya rage saura baifi taku arba'inba tsakanin rundunadunonin biyu sai rundunar su sarki daksur suka yi tirjiya aka fara kallon-kallo.
Sai da kura ta lafa sannan aka fara ganin juna sosai. Sarki daksur da sarki Raihan suka kurawa juna ido jaruma dabira da sarki uhaisu ma suka zubawa juna idanu. Ita kuwa yazila ta kurawa sarkin yaki idanu.
Jaruman shida suka kama tsuma ya zamana cewa kowannensu ji yake kamar ya zabura ya afkawa abokan gabarsa.
Da yake rundunar tazo kusa sai yazamana cewa babu bangaren da yake tunanin yayi amfani da mayakansa masa kibiya. Nan take sarkin yaki ya fara baiwa 'yan kasansa masu mashi da garkuwa umarnin su fara kai hari.
Ai kuwa sai suka hau kan sawun gaba, kowannensu ya saita mashinsa yana mai fuskantar a bokan gaba koda ganin haka sai shama sarki raihan ya baiwa nasa mayakan kasan umarnin su fito gaban filin daga wadanda adadinsu ai wuce su dubu arba in ba. Su kuwa dakarun arnan. Yan kasa adadinsu ya kai kusan dubu dari biyu da hamsim lokacin guda aka baiwa kowanne bangare umarnin su afkawa juna aikuwa sai kowanne banagare suka rugo da gudu suna kartar kasa kafirai suna ihu. Musulmi suna kabbara. Ahaka aka kacame da mummuna azababen yaki aka fara sokaiya da bugegeniya sai aka ga masu na fasa kirazan maza. Jini na tsartuwa da fallatsi. Mazaje na zubewa kasa suna zama gawa kai kace sassabe ake yi a gona. Sai da aka shafe sa a daya da rabi ana wannan bakin artabu sai gashi gaba dayan dakarun sun zama gawa. Dayansu bai tsira da raiba. Al amarin dai ya matukar dugunzuma hankalin kafirai ke nan suka cika da tsananin mamakin yadda aka yi wadannan kalilan din musulmin suka yi ragas da dakarunsu na kafirai wadanda suka nin kasu sau biyar a yawa? Koda sarki uhairu yaga wannan abu daya faru sai ransa ya baci zuciyarsa tafara tafarfasa kamar zata kone nan take ya zare takobinsa ya dagata sama ai kuwa sai sarki daksur da sarkin yaki ma suka zare nasu takobin. Koda ganin haka sai sarki raihan dabira da yazila ma suka zare nasu takubban. Kamar hadin baki sai kowanne runduna ta zabura ta durfafi abokiyar gabarta. Wohoho! Masifa idan ta zo babu makawa saita afku. Saboda tsananin karfin takun sawun mutane da dawakai sai da suka haddasa girgiza kasa a wannan wuri tamkar zata ta rufta. Kururuwar maza kuwa da haniniyar dawakai ta yawaita ainun har kai cewa da yawan mayakan sun firgice tun gabannin a hadu a fara gumurzu. Ai kuwa ana haduwa aka kacema da azabebban bakin artabu mai tsanani firgitawa daban tsoro nan fa aka bude kasuwar daukar rayuka. Sai gashi sassan jikin bil adama na shawagi asama tamkar ruwan samansu akeyi ji kuwa ya rinka fantsama yana malala akas kai kace teku ce ta balle. Babu abin da zai baiwa mutun mamaki face yadda arna ke ihu aya yin da suke mutuwa. Sannan kuma babu abin da zai baiwa mutun sha awa yajefashi cikin farin ciki face yadda musulmai suke kabbabra aya yin da mutuwarsu tazo duk sa adda sarki uhaisu sarki daksur dasu sarkin yaki suka kutsa cikin dakarun musulmai sai dai ka ga mazaje na zubewa kasa suna yin shahada. Haka ma a bangaren musulmai duk sa adda yazila dabira da sarki raihan ma suka kutsa cikin arna saidai kaga kamar sassabe sukeyi agona.
Komai lurar mutun bai isa ya gane bangaren da kke samun nasara ba. Wani babban abin mamaki shine babu yadda su sarki Daksur basu yi ba don su hadu da su sarki raihan ba amma ya gagara saboda yawan turmutsutsu da cakudewa gami da rudewar mazaje.
Sai da aka shafe sa'a uku da rabi ana wannan masifaffen yaki a sannan ne kowanne kowanne bangare ya gane kurensa domin an gane cewa babu bangaren daya samu rinjaye don gawarwakin kowanne bangare sun yawaita a kas.
Koda sarki Uhaisu ya lura da cewa ya kasa gane abin da ke faruwa a filin yakin sai ya fisge wani kaho da ke hannun wani badakare nasu ya busashi.
Nan take yaki ya tsaya kowanne bangare suka ja da baya. A sannan ne aka tsaya ana kallon-kallo. Nan take su sarki Daksur suka cika da tsananin mamaki bisa yadda kalilan mutane suka yi Ragas da mutanensu. Al'amarin daya matukar kona zukatansu ke nan aka sake yin cirko-cirko ana kallon juna. Nan take sarki Uhaisu ya nuna yazila da tsinin takobinsa yana mai nuni da cewar da ita yake son karawa yanzu.
Sarki daksur yai nuni izuwa ga sarki Raihan. Shi kuwa sarkin yaki yai nuni izuwa Dabira. Ba tare da sanin ko da wa zai gwabza ba.
Abinda suka sani kawai shine wadannan mayaka guda biyu wadanda suka saanya kayan yaki iri daya kuma suka rufe fuskokinsu da hular karfe, ba wasu bane face JARUMA YAZILA da DABIRA.
Da gudu. Aikuwa suna a tsakiya suka rufe junansu da sara da suka cikin tsananin zafin nama juriya da bajinta.
Tun kafin yazila ta fara gumurzu da sarki uhaisu tayi ta karanta wata addu a ta musamman a cikin zuciyarta. Bisa mamaki kuwa sai taji ta sami wani irin gagarumin karfi ya shiga jikinta irin wanda bata taba jinsa ba gami da azababban zafin nama na gaban kwatance. Aikuwa sai gashi ta zamewa sarki uhaisu alakakai ya rasa yadda zai yi da ita ya zamana cewa karfi yazo daya. Al amarin daya matukar baiwa sarki uhaisu mamaki ke nan. Domin shi a saninsa bai taba haduwa da jarumin dazo daya ba sai wannan karon.
Babban abin bakin ciki ma shine. Sarki daksur yayi masa bayanin cewa lallai da mace yake yaki. Kuma ba zai wuce jaruma yazila ko dabira ba.
Lokacin da sarki uhaisu yaga ya mace na neman bashi kunya sai zuciyarsa ta kufulo ta kama tafarfasa kamar zata kone don haka sai ya kara zage dantse iya karfinsa yaci gaba da kai mata wawan sara da suka cikin sauya salo al amarin da janyo ta rude kenan ta daina cigaba da karanta addu ar dake bakinta. Aikuwa damar da uahisu ya samu ke nan ya yai mata wani wawan duka da hannunsa cikin shammata a fuska saboda karfin dukan saida jini ya fetso daga cikin bakinta tamkar an yi wurgi da takarda haka ta fado daga kan dokin ta baje a kasa cikin matukar galabaice koda ganin haka sai sarki uhaisu ya dako tsalle daga inda yake tsinin takobinsa na kallon kas da nufin ya tsire cikin yazila. Duk da cewa yazila tana cikin wani mugun hali idanunta na gani dishi dishi. Koda ta hango sarki uhaisu yana shirin tsire mata ciki sai kwallah kabbara da karfi ta kaucewa harin nasa cikin matukar zafin nama. Take tsinin takobin tasa ta chaki kasa ta lume cikin kasar kafin yazare takobin tayi wuf ta mike tsaye zumbur kamar sifirin kawai sai ta daka tsalle sama ta doki kirjinsa sau uku. Yayi taga taga da baya kamar zai kife kasa amma sai ya cije saboda jarumta da juriya irin tasa ya tsaya cak yana kallon cikin tsananin mamaki domin itace bil adama ta farko wacce ta sami nasarar iya taba jikinsa haka.
A dai-dai wannan lokacinne abokan gaba suka yanyame jaruma yazila zasu hallakata. Ai kuwa sai ta tarwatsasu duk inda takai sara ko suka sai dai kaga ana zubewa kasa tana samarwa kanta hanya da karfin tsiya tana durfafar inda sarki Uhaisu ke tsaye.
A haka ta samu ta karaso inda yake suka sake ruguntsumewa da sabon masifaffen yaki.
Koda Uhaisu yaga cewa lallai karfi yazo daya shi da abokiyar gwaminsa sai ya sake shammatarta ya doki hannunta mai rike da takobin. Takobin tayi tsalle sama sai yazila ta daka tsalle sama domin ta cafo takobinsa shima sai ya daka tsalle saman ya doki kafafunta da kafarsa guda.
Nan take yazila ta rikito kasa arude kuma a hargitse, kanta na buguwa da kasa sai hular karfen ta ta cire, kyakkyawar fuskarta ta baiyana a fili karara.
Har sarki uhaisu yaji ya kamu da tsananin son jaruma yazila, don haka sai ya mike tsaye daga durkushen da yake yaja da baya a lokacin da suka fara kallon-kallo tsakaninta da shi tana mamakin abinda yasa ya fasa kasheta. Itama a lokacin ne ta lura da irin tsananin kyawunsa da kyawun surar halittarsa. Bisa mamaki sai itama taji ta kasa afka masa suci gaba da yaki.
A can bangaren jaruma dabira da sarkin yaki kuwa, labari ya shabanban domin kwarmazuwa suke yi har ta kai cewa kowannensu ya yiwa dan uwansa rauni sau biyu. Ita ta yankeshi a damtsensa na hannun dama da kuma gefen kirjinsa jini na zuba amma ko gezau bai yiba. Shikuma ya yanketa a gadon bayanta da cinyarta ta hagu gashi itama jini na diga amma bata sare ba sai dada fafatawa suke.
A bangaren sarki raihan da sarki daksur kuwa al'amarin ba kyangani domin nema suke yi su yi RAGAS saboda kowannensu ya yiwa dan uwansa rauni sama da guda biyar, duk jikinsu yai fata-fata da jini, har ta kai cewa suna layi, jiri na dibansu, suna layi kamar za su bingire kasa.
A na cikin wannan hali ne kawai aka ji an busa kahon tsayar da yaki. Faruwar hakan keda wuya sai sarki Uhaisu yaruga izuwa inda dokinsa yake yai tsalle ya haye kansa sannan ya zabureshi da gudu ya nufi can baya inda sansanin su na yaki yake amma yana juyowa yana waigen jaruma yazila alokacin da itama ta bishi da kallo kawai.
Sarki raihan da sarki Daksur kuwa, sai suka yanke jiki suka fadi kasa sumammu.
Dabira da sarkin yaki kuwa, suka ja da baya suna kallon juna cikin cizan yatsa da tsananin ta kaici domin ba haka suka soba.
A binda suka so shine a barsu su fidda raini ya zamana cewa daya ya kar daya. A guje kowanne bangare suka rugo suka dauke sarkinsu.
Nan take kafirai suka kwashe gawarwakin mutanensu da marasa lafiyarsu suka koma da baya izuwa can sansanin nasu sukuwa musulmi sai suka kwashe jama'arsu da dukkan kayayyakin nasu suka koma cikin birnin misra aka mayar da kofar birnin aka rufe.
A guje aka tafi da sarki raihan a cikin keken doki izuwa gidan sarauta. Jaruma yazila da dabira na biye da shi hankalinsu a dugunzume bisa ganin halin da yake ciki ko kadan ma basu damu da raunikan dake jikinsuba.
Cikin hanzari aka shigar da sarki cikin turakarsa aka kwantar da shi akan gado. Nan da nan aka kirawo likitan sarki yashiga aikinsa. Ai kuwa ba a dadeba sai sarki ya farfado ya dawo cikin haiyacinsa.
Yana bude idanuwansa yayi arba da Humaira tsaye akansa tana zubar da hawaye, dabira mana tsaye kusa da ita tana kuka, sai kuma Yazila a can gefe daya ta kura musu idanu cike da kwalla.
Bisa mamaki sai suka ga sarki raihan ya dubesu cikin matukar mamaki, kawai sai ya yunkura ya mike zaune yana mai cewa, "mu yiwa allah godiya daya bamu nasara akan makiya".
Koda jin haka sai mamaki ya dada kamasu. Dabira ta matso dab da shi ta zauna akan gefen gadon ta dubeshi tace, "haba ya abbana saboda me zaka ce mun sami nasara alhalin bamu kashe manyan shugabannin abokan gababa , kuma bamu kai tutarsu kasba? Ai burina shine mu ragargazasu kuma mu cafkesu a matsayin bayi sannan mu kwashe dukiyoyinsu a matsayin ganima kuma muje har can birninsu mu kafa tutar musulunci".
Lokacin da Dabira tazo nan a zancenta sai sarki Raihan ya sake yin murmushi a karo na biyu yace, "ai abinda da nake nufi da mun sami nasara shine, basu cimu da yaki ba. Duk da cewa sun ninkamu ninkin-ba-ninkin a yawa kuma mun yi matukar basu mamaki da tsoro domin basu taba tsammanin cewa hakan yakin zai kasance ba. Kuna ganin dai da kansu suka busa kahon tsayar da yakin suka ja da baya. Babban abin daya kara faranta min rai shine, wannan bakon jarumin da suka zo da shi bawani bane face sarki Uhaisu sadaukin da babu wani mayaki da ya kaishi jarumtaka da sa'ar yaki kamarsa, amma sai gashi ya kasa karar damu kuma a karshe ma sai na ga jikinsa yayi sanyi, haka kawai ya janye yakin ya ruga da gudu ya hau dokinsa ya bar filin dagar.
Ko shakka bana yi addu'ace ta kwacemu a wannan yaki, amma ba dabarar muba ko iya yakinmu ko jarumtakarmu. Yanzu abinda nake so daku shine, kuje ku yiwa jikinku magani sannan kowa ya huta. Idan allah ya kaimu yammaci sai mu zauna mu tattauna akan yadda zamu bullowa wannan yaki saboda tabbas sharar fage muka yi yanzu ne za a fara yakin. Suma abokan gabar tamu sun koma masaukinsu ne domin suyi sabon shiri da tsananin dabarar daza su yi su sami nasarar mallakar wannan birni namu mai albarka.
Ba tare da wata gardama ba su jaruma dabira suka yiwa sarki raihan sallama suka fice daga cikin turakar tasa suka barshi tare da likitansa da Humaira.
Lokacin da jaruma Yazila da 'yar uwarta Dabira suka isa turakarsu sai suka zauna suka shiga yiwa kansu magani. Da yake ita yazila bata da rauni sosai a jikinta sai ta fara sawa dabira maganin.
Duk da juriya irin ta dabira da jarumtakarta sai da ta rinka runtse idanu saboda tsananin zafi da zogin da take ji, har yazila taji ta kamu da dan tausayinta.
Yazila tayi ajiyar zuciya sannan tace, "yake 'yar uwata kiyi sani cewa na so ace nice na kafsa yaki da sarkin yaki domin bani da burin dayafi mu dauki fansa akansu shi da sarki Daksur. "
Dabira ta numfasa tace, "ni kaina nayi matukar mamaki bisa yadda aka yi na kasa samun nasarar hallakashi farat daya. "
Yazila tace, 'Ai ban yi mamaki ba domin kinsan cewa shi makiyi ko yaushe a cikin neman sa'a yake da sauya dabaru na yaki. Kinga wannan bakon jarumin sarkin da suka zo da shi wanda muka fafata da shi ba karamin tai maka musu yayiba, in ba don shi ba ma da farat daya zamu yi musu, hatta salon yakin da naga sarkin yaki keyi irin nasa ne. "
Koda jin haka sai dabira ta waigo ta dubi yazila ta ce, "tabbas biri yayi kama da mutum, domin yadda kika bani labarin yadda kuka fafata yaki da shi a wancan karon karfinsa da jarumtakar sa sun karu yanzu, in ba don haka ba lallai da sai na samu nasarar hallakashi. Wai shin dama ina son nayi miki wata tambaya. Lokacin da kuke bakin artabuke da wannan jarumin sarkin, duk da cewar ina cikin yaki na lura da lokacin da ya sami nasarar dukan kafafunki kika fado kasa a matukar galabaice. Harya daga takobinsa zai dankara miki sara ya hallakaki a dai-dai lokacin da hular kanki ta cire ta fadi can gefe daya sai kuma na gaya fasa. Shin ko kin san dalilin daya sa ya fasa hallakaki?".
Sa'adda yazila taji wannan tambaya sai tayi murmushi tace, "ya za a yi nasan dalilin da yasa ya fasa kasheni? Nidai kawai naga jikin sa yayi sanyi a sa'adda yayi arba da fuskata babu mamaki nayi masa kamane da wata 'yar uwarsa".dabira tace haba yazila ya a a yi a sami wata mai kama dake in ba niba ? Ai a gaba daya nahiyar nan nida ke mun fita daban domin ke ma kin san cewa ba karamin kyau allah ya bamu ba ni dai kawai abinda na fahimta shine nan allah ya jarrabi wannan sarki da kamu da sonki. Wannan shine kadai dalilin daya sa ya fasa hallakaki sa adda yayi arba dake ” yazila tace haba ganin sarkin fawa sai miya tayi zaki? In ban da abinki yau ne fa kadai ya fara ganina ” dabira tayi yar karamar dariya sannan tace ai shi so farar daya yake shigar mutun ba sai an shaku ba kiji tsoron allah ki gaya mini gaskiya ke kanki baki ji kin kamu da sonsa ba ? Rantse da girman iyayenna ban taba ganin kyakkyawan da namiji ba kamarsa gashi da kyan sura. Gashi sarki kuma gawurtaccen jarumi. “ Yazila ta maidawa dabira murmushi sanna tace. “ Ai koda ina sonsa kuwa daga yanzu da na daina sonsa tun har kika yi masa irin wannan yabo. Domin alama ce cewar kin kyasa kema kina so idan har zai karbi addinin allah nan gaba zan tsaya tsayin daka naga kin aureshi “.
Koda jin wannan batu sai hankalin dabira ya dugunzuma ainun tace, "Ai koda nima ina sonsa ba zan yarda na bashi soyayyata ba tonda ke ya gani yace yana SO ba niba. Ina nufin ke ya fara gani, don haka lallai keya kamata ki mallakeshi".
Abu kamar wasa sai gardama ta karde tsakanin jaruma yazila da jaruma dabira. Daga karshe bayan itama Yazila ta sawa Dabira magani sai ta mike tsaye ta fice daga cikin dakin nasu domin kawai ta katse wannan muhawara dake tsakaninsu.
*** *** ***
A can sansanin su sarki Daksur kuwa, lokacin da sarki Uhaisu ya iso bakin tantinsa sai ya sauko daga kan dokin nasa ya daure dokin. Har yayi nufin shiga cikin tantin nasa sai ya fasa ya taka da kafafunsa ya shige izuwa cikin daji ya shige duhuwar wadansu dogayen bishiyoyi ya sami karkashin inuwa mai sanyi kusa da wata korama mai ruwa garai-garai.
Koda ganin wannan korama sai farin ciki ya lullubeshi tun sa'adda yake fafata yaki. Nan take ya tsugunna a gaban wannan korama ya zuba hannayensa guda biyu ya kwarfo ruwan domin ya kai bakinsa ya sha.
Kawai sai yaga hoton fuskar jaruma Yazila a cikin ruwan tana yi masa murmushi.
Nan fa ya kasa shan ruwan ya zubar ya sake debo wani ruwan, aikuwa sai ya sake ganin yazila a ciki, sai da ya yi hakan sau uku sannan ya rintse idanunsa ya sha ruwan. Koda ya bar bakin koramar ya koma karkashin bishiya ya jingina bayansa a jikin bishiyar yaci gaba da ganin yazila a wuri daban-daban tana masa gizo.
Koda ya fashinci cewar idanunsa ne suke yaudarar sa han kalinsa ya duguntsuma ainun don yagane cewa ya fada cikin tekun SOYAYYA kuma tekun da bai san iyakar zurfinsa ba.
Nan fa yaji babu abinda yake so a duniyar gabadaya sama da sake ganin JARUMA YAZILA a zahiri.
Ta yaya zan sake ganinta har ya nuna mata abinda ke zuciyarsa ko ya furta da bakinsa alhalin ta kasance abokiyar gabarsa suna kokarin hallaka juna ? Yanzu haka ma ai yazila tana can cikin birnin misra kuma an kule kofar garin.
Koda ba a rufe ba ai baza a barshi ya shiga ba domin ana ganinsa maza a afka masa don hallakashi.
Nan fa sarki Uhaisu ya fara tunanin zuci yana mai cewa, Ai kuwa idan sarautata da jarumtakata basu sana mallaki wannan kyakykyawar budurwa ba, to kuwa basu da wani amfani a gareni".
Nan take sarki Uhaisu ya kudurce a cikin zuciyarsa cewar ta kowanne hali sai ya tabbatar da cewa ya mallaki Jaruma yazila.
Al'amarin sarki daksur kuwa, lokacin da suka dawo sansanin su inda suka kafa tantinsu sai suka ga dokin sarki Uhaisu a daure a kofar tantinsa sai suka yi tsammanin ko yana ciki dan haka sai sarki ya tura aje akirawoshi a gaya masa cewa
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2

Please Login or Register in order to submit comment