Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:Jamilaumar351*

*DEDICATED TO:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi...!*

_Bismillahir rahmanir Rahim in the Name of Allah,The Most  Beneficent The Most mercefull Praise be to Allah Lord of The Words..._

*001*

*ZARIA..*
Area:Tukur-Tukur...

'"Hafsah!...Hafsah...!Hafsah...! sunan danaji Megidana Abdullahi na Tsagamin shi da Asuban fari,wanda hatta mazan da suke wucewa ta kofar gidanmu in sun dawo Daga masallaci suna iya Jiyo kwakwazon Kiran Sunana da Abdullahi keyi muryansa Kakkausa kamar zata tsaga gidan.

Kaina na Dafe ina Daga Durkushe acikin karamin Kichen dinmu Dake tsakar Gida Ina Faman kunna Risho sai na kunna Lagwanin sai ya mutu da kanshi Tun Wajen 6 da wani abu na safe na Fito ina idar da sallar Asuba ban ma yi Tunanin komawa ba Saboda yau din Litini ne farkon Sati Su Amira nada Makaranta kada su makara Abdullahi ya Dora Laifin akaina Tunda tare yake Wucewa dasu in zai tafi aiki Bisa Mashin Dinsa mai Suna Wayyo Kudina.

Saurin Mikewa nayi Jin kiran yafara Kusantoni kada na Kular Dashi dogon Sikat din Jikina na gyara Lokaci daya da Hijabin danayi sallah wanda ban cire ba Jin garin yau din an Tashi da sanyi sanyin Damuna dayake Jiya an kwana Tsala ruwa,ina kokarin Shiga Dakin muka ci karo Dashi zai Fito,Da Sauri nayi baya ina Raba Ido Cikin Kulufuwa da Takaichi yake Jifanta da wani kallo kafin ya Daga Murya yana Fadin"Wani sabon Iskanci kuma kika samo Hafsah..!?

Muryanta cikin Sanyi nace"Name fa Abban Amira..? Harara ya wurgamin yana Fadin''Bansani ba..Nace bansani ba bandama Salon iskanci kira nawa nayi miki Tun ina Daga cikin Daki baki amsa ba sai da na Fito..? Yafada yana wani karkace tsayuwa Cikin Jin Haushinta,Ajiyar Zuciya ta sauke kafin ta kada kai kawai ta wuce shi Zuwa Cikin Dakin bayanta yabi yana Fadin"Hafsah ina mgana kina Tafiya..? Yafada cikin Mamakinsa.

Atsakiyar Falon Taja ta tsaya tana Fadin"A"a kayi Hakuri ba Tafiya nayi ba na Shigo Daki ne kada makota su jiyo Fadanka,mganar kuma Kira banji bane Lokacin danaji na amsa kenan zan taho Dakin sai ga ka kayi Hakuri.."Tafada Cikin Sanyin Murya Kawai Tsayawa yayi yana Kallonta cikin Fada,sai yanzu na karemai kallo Dogon Namiji ne mai Cikar zati da kamala mai Fadin Kirji da cikar Cikakken Da Namiji mai iko Ba fari bane ammh Wankan Tarwada ne,Fuskarsa bata da Tsawo sosai sai dai tana da Fadi kadan Hancinsa Dogo ne Turbarkallah Masha Allah Sajensa daya zagaye bakinsa shi yake karamai kyau da Kwarjini.

Abdullahi Usman Direba kenan Dan Misalin Shekaran Haihuwan 32 da biyu Aduniya Mai iko ne kuma mafadacin Namiji ne ga iyalansa bai da sauki ko kadan Ballatana Ragowa a kallan Farko in kayi mai bazaka taba Zaton Abdullahi ya iya Fada ba ammh Ranar dakayi katarin zuwa gidansa nan zaka ga Abunda ake Kira Tijara da kudinka Sai kayi Mamakin Dama Abdullahi na iya Dogon Mgana ne..?haka yake baka iya yankema Abdullahi Hukunci ga Dabi"unsa matarsa Hafsah ce kadai Zata iya Fadar Wanene Abdullahi 90%Cikin Halayyarsa wanda Mutane basu sani ba,sai yan"uwansa makusantansa.

Numfashi ya Sauke Lokaci Daya yana Fadin"Eh Lalle wato kada makota Sujiyo Fada na ko Hafsah..? Wato ga mafadaci ko..? Yo in gaskiya kikeso Uban wa ke sani Fadan in bake ba.Kullum kwakwalwarki bata Daukan Mgana Koda yaushe sai dai adinga nanata miki Mgana Daya,ko karatu ya isa ki gama Haddaceshi acikin kwakwalwarki ammh Ina baki da Buri illah Kiga Ina Mgana Shine Burinki sai anyi Mgana kiwani Langwabe kai kamar Wata marainiya kina Sharan kwallar karya.."Yafada yana kallonta tana goge kwallarta da gefen Hijabinta,Bata dagoba ta kara kwantar da Murya tana Fadin"Allah ya baka Hakuri.."

Tsaki yaja yana Fadin"Ameen...Sai ana mgana ki wani fama ma mutane kuka kina wani Allah baka hakuri"yafada yana kwaikwayan Muryanta cike da Haushi ita dai bata Dago ba kanta na kasa tana kallon Center Capet din Dake tsakiyar Dan madaidacin Falon nata wanda yaci Kujeru saiti Daya mai Dauke da Karama Mai zaman mutum biyu Guda biyu da kuma Mai zaman mutun uku guda daya na kuma mai zaman mutum biyu,Babu komai daga kujerun sai Tibin Bango Plasma dake kafe a bangon Dakin,wanda ya samu mahadin Dish din da suke kallo Dashi..

Hannu ya yarfa yana Kallonta yace"Kinga Malama ni ba Hayaniya na Fito nayi dake ba ina Takarduna wanda na Dawo dasu gida Daga wajen aiki Ranar Jumma"a saman Madubinki na ijiye kuma yanzu nazo zan Dauka bangani ba.."Cikin Sanyin Murya ta wuce Cikin Bedroom din tana Fadin"Suna cikin Dorowan gado ni na Dauke da zan gyara Dakin Jiya.."Binta yayi abaya Cikin Fada yake Fadin"Kinji ko..?kai Hafsah wai ke Wata irin macece..? Sau nawa zan gaya miki kidaina Tabamim kayana ko wani abu nawa in na ijiye da Hannuna Ehe..?

Yafada yana Tsareta da manyan Idanuwansa kamar ya maketa Baki ta saki kafin ta Bude tana Fadin"Haba Abban Amira ina Laifina anan?,na dauke maka ne saboda kada Amira ko Amir su dauka su bannata maka.."Tafada Cikin karya Murya Wani Dogon tsaki yaja yana fadin"Na sakaki..? Ki barsu su bannata mana bani na ijiye ba..? ko kinfini sanin akwai su Amiran ne..? Nifa wannan Sanaben naki sam baya Burgeni Hafsah in ma zaki chanza Ki chanza Tunkafin dare yayi miki,Dillah Malama daukomin Takarduna zan Fita dasu ne..!

Yafada yana Yarfa mata Hannu batayi musu ba ta Juya Ta Bude Drower din gadon ta Daukomai Takardun ta mikamai bayan ta Ramkwafa Fizgewa yayi cikin Fada yana Dubawa Zuwa chan yace"Allah ya Soki Wlh da wata Takarda ta bace sai kin Raina kanki..Daga yau sai yau karki kara Tabamin kayana Daga inda na ijiye am i Clear..? Yafada yana Taba kunnansa Numfashi ta Fesar tana Fadin"Naji insha Allahu haka bazata kara Faruwa ba.."Bai kalleta ba yawuce gefen gadon yana zama ita kuma ta Fice tana kada kai.

Kichen ta koma Sai lokacin ta Duba taga ba Kalanzir ne Da Sauri Ta Daga glan din kalanzir din nasu taji ba komai sai da gabanta yafadi sanin Halin Abdullahi yanzu kan mganar ba Kalanzir sai Ranta ya kara baci tayi Kokarin samun wata Dubara ammh Ashana taki kama Lagwanin Dole dai uwar naki Dakin ta koma tana Sunne kai yana Saka Takardun Cikin karamar bakar Jakarsa ta Briefcase ta Shigo yana ganinta ya Daga kai yana kallonta,Tunda yaga tana wani Sunne kai yasan akwai matsala Baki ya Tsuke yana kallonta yace"Da wani abu ne..?

Yafada kai tsaye Cikin Sanyinta tace"Eh...Eh...Dama da..."Dama mene in zaki yi mgana kiyi malama..! Ya katseta cikin Dauriya tace"Eh dama Kalanzir ne na duba naga babu wanda zan kunna Rishon dashi.."Tafada tana Sosa kanta Wani irin kallo ya sakarmata kafin kawai ya kada kai yana Fadin"Bazaki taba Chanzawa ba Hafsah narasa Wata iriyar macece ke..? Sau nawa zan gayamiki duk Abunda babu ki dinga Fadamin tun kofa da Nisa..? Yanzu ki duba agogo 7am  ake nema kuma kina sane da cewa 7:30am nake fita na Biya na kaisu Amira makaranta kana na wuce wajen aiki, baki ma sa mana Ruwan wanka ba ballatana akai ga Abun karyawa.."yafada cikin bayyana Takaichin dake cin Ransa.

Kasa tasakeyi da kai kafin tace"Kayi hakuri Wlh Allah bansan babu sai ya..."Wannan ya Rage naki ga Naira Dari ki Dauka ki Siya gawayi kiyi amfani dashi Domin yanzu babu inda zan samu kalanzir sai dai in na tashi Daga Office na Taho dashi.."yafada yana Jefamata Naira Darin daya Dauko Daga Cikin Walet dinsa bata tsaya wata mgana ba ta Duka ta Dauka ta Fita zuwa Falo karamin Dakin dake kallon nasu ta Shiga inda suke ijiye kayan abinci sai kuma wata karamar katifa Inda Amir da Amira ke kwana Mirmishi ta saki kafin ta karisa ta zauna gefen gadon tana Dukan Kafar Amira Lokaci daya tana Fadin"Amira...ke Amira Tashi maza.."

Ido Amira yar Shekara Shida ta Bude tana kallon mamanta Cikin Sauri ta mike tana Fadin"Mommy ."Mirmishi Hafsah ta sakarmata tana shafa kumatunta tace"Tashi kiyi sallah kiyi Sauri kizo ki shiga gidan Asiya ki Siyomin gawayi yau mun Tashi kalanzir din mu ya kare sai Abbanku yatashi aiki zai taho mana Dashi.."Amira bata koma ba Tatashi tana Fadin"Mommy ina Abba...? Hafsah tana kokarin Tada Amir tace"Yana daki kije ki gaisheshi Dagachan sai ki shiga bayi kiyi awala kiyi sallah kizo ki siyomin ina Jiranki kinji ko..? Dakai ta ansa mata kafin ta Ruga ta Fita da Gudu Amir ta Tada daga Barci waje ta Fita dashi ta sakashi Bisa Foo yayi Fitsari,kana ta wanke mai Fuska ta mai alwala ta turashi Daki tace yaje yayi sallah ya wuce yana Dan Gudunsa na yara wanda shima Ashekaru iyakarsa Shekara uku da wani abu.

Kichen din ta koma tana Tunanin me zata yi musu na karyawa Sharp sharp,ganin Lokaci ya tafi ya sa ta Fito da Murhun gawayin nata tsakar gida saboda yasha Iska Duk da Tsakar gidan bai da girma ammh kana gani zaka Fahimci komai na gidan Muhallin mace Daya ne,Buhun gawayinta ta Zazzage duk da ya kare ammh ta samu Kadan tayi Sauri zubashi Cikin Murhun gawayi ta kwafkwafi Sauran kalanzir din glan ta kunna wuta dayafara kamawa Da mafici ta tada gawayin da Sauri ta Dora yar madaidaiciyar Tukunyarta Ta cika da Ruwa,Dayake suna da Rijiya Tun Jiya almajiranta yunusa ya cikamata babban Robanta da Ruwa.

Kwai ta fasa,lokaci daya tana yanka Albasa ta gama kenan tana Jajjaga kayan miya da kayan kamshi Wanda zatayi amfani Dashi Wajen Soya kwai da Dahuwar indomie,Sai ga Amira ta Fito tana sanye da karamin Hijabi bayanta ta Rumgume tana Fadin"Gud mrning mommy.."Tana Dariya ta Dakata da Abunda takeyi tana Fadin"Ehe Amirata ta zama baturiya kin gaida Abbanku toh yaji kin iya Turanci..?

cikin Farinciki Amira ta gyada kai tana kallon Mahaifiyarta Kumatunta Hafsah ta ja tana fadin"Gud girl...Maza muje na Bude miki gida ki siyomin gawayin kafin wannan ya mutu.."Tafada tana mikewa Daga kan kujeran Tsugunee,Taja Hannun Amira suka nufi hanyar waje ita ta cire sakatar kofar gidan kana ta Damkama Amira Naira Darin,Fita tayi da gudu itama kuma Hafsah ta tsaya nan tana Lekenta dayake gidan yana kallon Gidansu ne,ko minti goma Amira batayi ba sai gata ta Fito Dauke da kullin bakaken leda Guda Biyu masu Dauke da gawayi Da Sauri Hafsah ta tarbeta suka Dawo cikin Gida,cikin Sauri ta Dauki Wata Karamar Roba acikin kichen dinta ta Juye Ruwan zafi har ya fara Tafasa,ta shiga daki dashi Cikin Bedroom dinsu ta shiga inda Ta Iske Abdullahi na wasa da Amir cikin bayin takai Ruwan ta zubamai Rabi Cikin Botikin karfen dake bayi wanda yafi kama dana gargaji ko Tiolet dinsu na Tsuggune ne ammh mai Floshing din nan,ammh kuma bayin Shinfide da Siminti sai Tashin kamshin Detol yake yi Domin Hafsah akwai Tsafta kwata kwata bata da Kazanta.

Akwai Wata katuwar Bombi mai Cike da Ruwa,cikinta ta Debi Ruwa ta surkamai Ruwan wankan Daidai Misalin sanin Komai tama Abdallah bata iyamai,Sauran ruwan kuma ta kauda dashi gefe Ta Fito tana yarfa Hannunta Lokaci Daya take fadin"Abban Amira ga ruwan wankan chan.."Bai amsa mata ba ita kuma bata damu ba ta Fice sanin yajita Sarai,koda ta Fito Tsakar gidan Amira ta karisa jajjaga mata kayan kamshi da Hanzari ta Bude Ledan gawayin ta kara Ta Fifita yatashi taDauko wata karama Cikin Tukwananta ta Dora ta zuba Ruwa Daidai,Daki takoma ta Dauko Indomei guda Biyar wanda zasu ci da kuma wanda su Amira zasu tafi Dashi Makaranta.

Agurguje take komai sai da ta Zuba Indomie ta tura Amira ta Dubo mata ko Abbansu ya Fito Daga wanka ta Dawo tace bai Fito ba, bata damu ba ta cigaba da aikin gabanta Cikin Sauri ta Sauke Indomie ta Dahu ta maida kaskon Ta Zubo mangyada Cikin wata karamar Roba da Cokali ta fara So kwan sai da Tagama tas kana tatashi ta Shiga Kichen ta dauki basket din su Amira ta zuba musu harda kwan,ta mikama Amira ta kai Daki Sauran kuma ta Zuba cikin kula,Ruwan zafi ta maida Saboda Sauri bata saka Cittan da ta saba Dafawa dashi ba Sauri take ta kamallah komai kafin ta Shiga Daki,kawai suma su Amira wanka ya Rage Ruwan yana zafi ta Juye cikin Flaks kana ta maida Wani Ruwan wanka.

Tattarra komai tayi zuwa Cikin Daki saman capet din dake Tsakar dakin ta Jera komai Ta Zura da Gudu ta Dauko Pure water guda biyu ta fasa ta Durama su Amira cikin goransu na Cikin basket dinsu,ta koma kichen ta kwaso kanann kofuna ta Dawo daki ta jera kusa da Falks din Ruwan zafi Dayan dakin ta koma ta kwaso kayan tea dinsu tazo ta jera duka cikin Sauri kafin ta Nufi Cikin dakinsu nan ta Iske Abdullahi ya Fito wanka yar yayi ma Amir wanka ma,Da Hanzari tatura Amira cikin bayi ta Tubeta ta mata wanka ta Fito Amir ta fara Shafa ma mai Abdullahi kuma yana tsaye yana saka maballin Rigarsa,Amira ita ta shafama kanta mai Hafsah ta Fito musu da Uniform,Amira ta saka ma kanta ita kuma ta sakama Amir harda safa da Takalmi ta Dauko musu Jakunkunansu ta jasu zuwa Falo ta zaunar dasu ta hada musu Tea ta zuba musu Indomie da kwan ta Turama kowanne gabansa tana Fadin"Oya kowa yayi Bismillah kuma kuyi Sauri in ba Haka ba Abbanku yatafi ya barku.."Jin haka yasa suka Fara cin Abinci bayan sunyi Bismillah.

Tea din Amir ta Dauka tana Fifitamai sanin baya iya shan Abu da Zafi sai ga Abdullahi ya Fito Cikin Shigar Riga da wando kalan Navy blue,sunyi matukar mai kyau Ta kallesa tana Mirmishi ammh shi ko kusa Fuskarsa ba Walwala kusa da Amira ya zauna Jikinta na Rawa ta Shiga Kiciniyar Zubamai Indomie din Hannu ya Dagamata yana Fadin'Barshi..Bani Tea din kawai.."Jikinta a sanyaye ta Tsiyayamai Ruwan Tea din ta Tura gabanshi da wata Harara ya Rakata kafin yace",Oh ni kike so na hada Tea din kenan yau..?

Da sauri Hafsah tace""A"a ba nufina ba kenan naso ka Hada da kanka ne kada kace ina cika maka Siga.."Hararanta yakarayi kafin yace"Toh bazan hada ba..Kuma ki cika sigan ki gani.."Numfashi ta sauke kafin taja Kofin gabanta Madara ta farama Zubamai Cokali Biyu Zata Rufe kenan yace mata,"Kina Nufin Iya madarar da zansha kenan..? Wai ni Hafsah ke ki ke siyan kayan Shayin ne da kike min Ididdiga..?

Saurin Taran Numfashinsa,tayi da cewa'Bafa haka bane..Gudun nayi na Saka maka da yawa kace na Cika maka madara.."Wani kallon kasa kasa yayi mata kafin yace"Commom malama Karamin madara kina batamin Lokaci.."Numfashi ta Sauke Aranta tana fadin komai akayi maka koda na Gudun karkayi mgana ne sai ka Tanka,Madara da Bonviter din da yawa ta Zubamai Siga kuma ta sakamai kadan ammh duk da haka sai da yayi korafin ta bashi Tea ba siga Kai ta dafe kawai tana kallonsa Sigan ta Turamai gabansa Lokaci daya tana mikewa kallonta yayi yana Fadin"Ina zaki..? Ke bazaki karya bane..? Tana kokarin Shiga Uwar dakin tace"sai anjuma."Baki ya tabe kafin yace"Kanki.."yafada yana Zakuda kafada irin ko ajikinsa dinan.

Takwas daidai suka gama karyawa Shi ya fara mikewa yana kwalama Hafsah kira sanin Kiran yasa ta Fito da Sauri Lokaci daya tana Dauke da Jakarsa Karama baka da makullin mashin dinsa ta ramkwafa ta mikamai ya amsa Lokaci Daya yana ficewa,Ita kuma ta kama Hannun Amir yana Rike da basket dinsa Hakama Amira suka Fito Nan suka iske Har Abdullahi ya Fito da farar Lifansa dake Cikin wani Daki kwara daya dake gidan wanda ba"a gyara ba sai dai yana da kofa Siminti kasa ne kadai bai Dashi da Silin nan yake ijiye mashin dinsa in ya Dawo har Kofar Gida ta rakasu Daganan ya karbi Jakarsa yace ta koma bata Rufe gidan ba sai da taga Tashinsu Amir na gaba Amira kuma na baya Rike da kwandonsu ya tada mashin dinsu suka tafi tana musu Fatan Dawowa Lafiya.

Ajiyar Zuciya ta sauke kafin ta maida kofar gidan Ta Rufe,ta koma Daki ta zauna itama ta karya Saura kuma ta ijiyema Alamjiranta in yazo ta bashi,Kwashe komai tayi ta maida Muhallinsa Sauran kayan da aka bata kuma ta maida Kichen ta koma ta gyaro Dakunanta,Kayan su Amira kuma ta kaisu dayan daki ta Zuba cikin kwandom kayan wankinsu na Abdullahi kuwa ta Ninkemai ta Saka cikin Wardrope batayi wanka ba sai da ta wanke bayi kana ta Juyo Ruwan wankanta ta kashe gawayin ta maida kichen ta kulle kana ta koma Daki tayi wanka ta Shirya Cikin Riga da Sikat na wata atamfa mai kalan ja,Da baki Karamin Azkar dinta da wayarta ta Dauka tazo falo ta Zauna Bisa Kujera,tana kallon agogo har 9am tayi ammh Shuru Nepa basu kawo Wuta ba gashi tana son Tayi Blanding din kayan miya kishingida tayi kan kujera tana Tunanin in basu kawo ba in Yunusa yazo sai ya mikamata Nika Wayarta ta maida gefenta tafara Karanta azkar dinta hankalinta kwance.

_Hmmm ya kuka ji Salon..? Zai kayatar da ku..? Kuna so...? Kuna Bukata..? Cike Tagging dinki da kayattacen Sharhi..Ni kuma bazan yi kasa agwiwa ba wajen Baku Update akai akai da yardan Allah...Karku manta Kuyi Following dina ta sabon Account dina ta Wattpad@Jamilaumar351,Kana ku cike sa da Like da Vote Domin karfin gwiwana Son so Fisabilillah masoyan kwarai..._


*SHAKIRA...*💞
*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated to: My Habibaty💞Aisha Idris Abdullahi*

*002*

   "Tana cikin karatun azkar din ne Wayarta Dake gefenta ta Dauki Tsuwa ta Dakata ta Dauki Wayar sunan wanda Taga yana Kiranta ne yasa ta Saki Mirmishi Cikin Jin Dadi da wani Farinciki Ta Daga tana Fadin"Qawata.."

Dagachan Bangaren Subai"a tace"Ba wani kawarki Allah Hafsah Daga ke har yaya Abdullahi baku da kirki ace Har yau kwana na goma da Haihuwa ammh Daga ke harshi ba wanda ya Leko..? Haka ake Rayuwa..?Har Anty Zannira Dake kaduna tazo Ita da Mijinta ammh ke ban ganki ba,Ballatana Shi yaya Abdullahin..?

Hafsat ta Saki Mirmishi kafin Tace"Toh uwar korafi kin gama.
? Domin bana so na katse miki Hanzari ne Tunda kika Dauko Wannan Dogon Korafin naki sai kin idashi zakiji Dadi.."Subai"atu tace"Ba wani Sarkin korafi ko Gaskiya.."Hafsah tace"Ai bance ba gaskiya bane ammh sai ki Tsaya ki Saurari nawa uzurin ko.? Kinsan dai Haka kurum Tunda Kika Haihu Banaki Leko ki ba ko...?

Subai"atu Tace"Umh...Ina Sauraranki.."Hafsah tace"Wlh Tunda Kika Haihu nace ma Abban Amira zani Barka ammh baicemin komai ba Har suna yazo,Ranar suna kuma Wlh naso zuwa sai na Tashi bana jin Dadi,ga Amir nata Zazzabi Da Amai Shiyasa kika ga Baki ganni ba Ammh Insha Allahu Cikin Satinan ina Tafe karki Damu kawata.."

Subai"atu tace"Haka dai kikace Don ki Kare kanki da Mijinki bakomai..Sai na ganki.."Hafsah tace"Lah..Baki yarda ba...? Share zencen Subai"atu Tayi kafin tace"Jiya Ammi tazomin Barka Harda Abun arziki ki Tayani Godiya Qawata Allah ya saka da Alheri ya kara Tsawon Rai.."

Hafsah tace"Kajiki da wata mgana..?Don Uwa tama yarta wani abu sai ya zama Abun Godiya.."Subai"atu tace"Hakane kuma..ammh ai Godiya Abu ne mai kyau ko..? Ni ba wannan ba Ina Jiranki Allah kuwa Har Danki yayi Fushi Dake ya kwana Goma Aduniya baki zo kin ganshi ba ballatana Shi Yaya Abdullahin...." Hafsah tace"Kiyi Hakuri Insha Allahu Zamu zo.."

Subai"atu Tace"Toh Allah yasa."Daganan sukayi Sallama kowa ya Ijiye wayarsa Hafsah ta Gyara zama tana Sauke Numfashi Abun yazomata Cikin Ranta na Rashin kyautawarta ga Kawartata Subai"atu wanda kuma Ba Laifin Kowa bane sai na Abdullahi Domin Tunda akayi Haihuwar take mai nacin Tambayar ya barta Taje tama Subai"atu Barka ammh ya ki Kula Mganarta Har Suna yazo,Ranar sunan kuma Har yace ta Shirya ya kaita Ita da yara sai kuma yan Masifarsa suka Tashi Daga kawai Ta bata Lokaci wajen Shiryawa Shikenan yace ya Fasa kaita kuma Bai lamunta ta Fita ba Takaichi kamar ya kasheta,Tana ji Tana gani ya kwashi su Amira Zuwa Gidan Mama suka barta agida saboda Takachi Sai da tasha kuka,Ranta ya baci yasaa bata karamai mganar Zuwa Gidan Subai"an ba ta barshi ai Shima kanwarsa ne In Ya barta Taje Domin kanshi in ya Hanata Shima kanshi yayi mawa Ita miye nata aciki.

Gashi Abunda ke bata mamaki da Abdullahi yana da kyakyawan Mu"amala da kowa banda ita Shiyasa ko zata Shekara Fadin Aibun Abdullahi babu mai yarda,Ko Wajen iyayenta bata Isa ta Kushe Abdullahi ba,baya kwana Biyu baije Tudun wada ya Gaishesu ba,weekend kuwa Shi da yara a Cikin Zaria suke yinshi da Tudun Wada,Shiyasa komai zai mata Take Shanyewa sanin ko Zata Shekara Fada bamai yarda da Ita Saboda in ka Ganshi Bazaka Taba Zaton yana iya Doguwar Mgana ba ballatana Har ya iya wannan Hayagaggar,Abunda ke Daurema Hafsah game da Abdullahi Shine,Komai tayi mai Bata Burgeshi kuma komai tayi ba Daidai bane Duk ko iya Kokarinta na ganin ta zama mai Daidai acikin Idanuwansa ammh Abu ya Gagara Shekara Biyar da Auransu ammh ba wani Abunda ya Chanza Suna nan Jiya yau.

Ajiyar Zuciya ta Sauke jin Sallaman almajirinta yunusa,mikewa tayi ta Fito suka Gaisa,Rijiya ya Nufa ya Fara Zuba mata Ruwa Cikin Babban Roban Dake wajen,Ganin haka yasa ta Bude Kitchen ta Shiga ta Dauko kayan Miya ta Fara gyarawa Ta Tagama sai ta Saka Cikin Wata Robarta mai murfi tana cema Yunusa in ya Gama Zuba Ruwan ya mata Wanke wanke ya Dauki Nikan nan ya mika mata Gidan Nene mai nika yace mata Toh Daganan Ta koma Daki,Tana nan kwance Bayan Fitan Yunusa Zuwa Nika sai ga Nepa sun kawo Wuta ta Mike tana Fadin"Kash Nepa baku kyauta ba sai da yunusa ya tafi kai min nika kana kuka maido Wuta..?

Sai Lokacin kuma Abun yayi mata Shar cikin Ranta Da Sauri ta Mike tana Salati Cikin Ranta Tuna Abdullahi baya som Miyar Nika yafison kuma na Jajjage,ita kuma Abunda yaasa bata Jajjaga ba Taga kayan Miyan yana da yawa ne Bata iya zaman Jajjagasa Shiyasa takai Nika ajiyar rai ta Sauke afili ta Furta.."Fada ne da korafi yau zan Shashi Acikin Gidan nan Har sai na Godema Allah.."

Yunusa na
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment