Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


: *MR BELLO..!*
_(The young Teacher)_

*NA*

*JANAFTY*💕
*Wattpad:Janafnancy13*


_*Bismillahir Rahamanir Rahim in the Name of ALLAH the most  Beneficient the most mercerfull praise be to Allah lord of the words.....*_

_Assalamu Alaikum my Follow fans,am starting my new Book i ask ALLAH subhanahu wata"ala to guide me throught and make me it sussufull till End Ameen ya Allah_

*Copycats are not allowed to transform this book by any means without the prior written permission of the writer.Immediate action will be taken if caught?*

? _DEDICATED TO: *Bashir Sufyan Sardauna* and *Nazifi yarima*❤️ Sakallahu fil jannah Dudes..For ur all Support,care and Concern..Allah yabar zumunci Ameen_

*....SHIMFIDA....*

        *🅿?1*

*GGUSS KWATAR-KWASHI*

A haraban Babbar Makarantar ta GGUSS, Goverment Girls Unity Secondry School Kwatar-kwashi Dake Tsakanin Dajin kwatar-kwashi Zuwa Gusau, Da Misalin ƙarfe 10:30am na Safe.

Daga Cikin Babban Filin Haraban Makarantan Na Hangi ɗalibai Birjit ba Adadi mata ne Zallah Ta Ko"ina Suna Yawo Wasu Suna Tsaye da Tarin Akwatunsu da Jakunkunansu Wasu kuma Suna ta Tururuwan Shiga Doguwar Mota Fara mai Ɗauke da Tambarin GGUSS KWATAR-KWASHI, gefe ɗaya kuma Kowaccensu Tana Sanye da Uniform ne Ajikinta wasu Nasu Wando light green ne Both Riga da Wando da Ɗan kwali sai Farin Hijabi A yayinda Wasu kuma ke Sanye da Dark green d'in Wando sai Both Farin Riga da Da'n kwali da Hijabi.

A yadda Haraban Makarantan ta Rikice da Hayaniya da Murna da Iface ifacen Ɗalibai zaka Fahimci Hutu ne Ɗaliban Suka Samu Tun ma Ba Daga yadda Wasu Iyayen Ɗaliban keta Zuwa Ɗaukan yaransu Wanda basu yi Register da Motar Makaranta ba, Ayayinda Wasu ke Ta Fitowa Bakin Get d'in Mkrantar ga masu Mashi nan suna ta Ɗaukansa Zuwa inda zasu Hau Mota Zuwa Gida.

Daga chan ɓangaren Na Hangi Wasu 'Yan mata su Uku Tsaye A bakin Wata Bishiyar Dalbejiya Dukkansu Gabansu Akwai Tarin jakunkuna, da Sauran Tarkacensu masu yawa, sakamakon Wannan Hutun Third term ne ƙarshen Zangon karatunsu na Jss 3 sai Shiga SS1 Kenan, Suna Sanye da Uniform ɗinsu na Junior, light green both Riga da Wando da Ɗankwali sai Hijabi Fari, Dukkansu Ukun Tsawonsu Ɗaya Sai dai kuma Biyu Daga Ciki Farare ne Tas, Sai Ta Ukun Wacce ke Tsakiyansu Ɓaka ce Sulub ammh Bak'inta bamai Duhu bane mai haske ne, Wanda Ke Shining, Doguwa ce Mai K'arancin Girman Jiki, Fuskarta tana da Faɗi Ammh ba Sosai ba, Tana da Manyan Idanuwa Masu Ɗauke da Gashin Ido Zarara sai Ƙaramin bakinta Wanda Yake Baƙi baki, A shekaru Dukkansu bazasu gaza Shekaru goma Sha Shidda ba Daga Kallon Farko Zaka Fahimci Zallar Ƙuruciyarsu A lokacin.

Daga bayansu sukaji Ance " *ANEESA...*" atare Suka Waiga dukkansu suna Kallon Ɗaya Daga Cikin Senoirs ɗinsu Jidda Madaki Waɗanda Suke Kan Zana Jarabawarsu ta Fita Ma'ana WAEC, Saboda Haka Su Suna Makaranta basu Azuwa Hutu sai Sun kammallah Neco wanda kuma bazai yi ba Sai ya Tattara ya koma gida.

Itama ɗin Sanye Take da Uniform ɗinsu na Senior, Dark green da Farar riga da Hijabi, Kyakkyawar Gaske ce Gata Fara gata Doguwa mai Ɗauke Da Daran Daran Idanuwa masu Haske Cikin Siririyar Muryanta tace "Aneesa Plz D'an zo na ganki..." Ta faɗa Cikin Yanga Wanda ya Zame mata Halitta.

Jin Abunda tace yasa Aneesa Ta ƙara Haɗe Ran Kamar Wacce Aka Aikoma da Saƙon Mutuwa Saɓanin Sauran ƙawayenta da Fuskarsu ke Washe na Farin cikin Zasu koma gida yau, Cikin Sanyi Jiki da Takun Ɓacin Rai Aneesa Ta Nufi Jidda tana Faɗin " *S. JIBIYA, B. KAITA* Ku jirani bari na Dawo.." Jin Haka yasa S. Jibiya tace "Ok *A. BUKAR BULAMA*..." Ta faɗa Tana bin Aneesan Da Kallo kafin Ta Maida Kallonta kan B. Kaita Suka haɗa ido Suna Ƙunshe Dariya.

Aneesa kamar bazata Taka ƙasa ba Haka ta Rinƙa jan ƙafa Zuwa Wajen Jidda Dake Tsaye tana Jiranta Tana ƙarisowa ta Riƙo Duka Hannayeta Cikin Salon Muryanta tace "Aneesa Don Allah karki manta da Alƙawarin mu Kinji.." Ta faɗa Tana Sakar mata Fararen Idanuwanta.

Gyara Tsayuwa Aneesa Tayi Tana Jifan Jiddan Da Wani Banza Kallo A fakaice, kafin tace "Wani Alƙawari kenan...?" Ta faɗa Da Sigar Rainin Wayau Lokaci Ɗaya Itama tana Sakar mata Manyan baƙaƙen Idanuwanta masu Ɗauke da Zara zaran Gashinta baƙaƙe masu ƙara Fito da Salon Kamaninta da *KANURI*, Jidda Ta Saki Ajiyar Zuciya kafin Ta ƙara Riƙe Hannun Aneesa Tana bin Haraban Mkrantan da Kallo Yadda Taga Kowa na Haraman Tafiya sai D'ai d'ai Irinsu ne Suke Hidimar gabansu.

Cikin ƙara Kwantar da Murya Tana faɗin "Haba My Anee, har kin manta da mganarmu na Kiyi ƙoƙarin Saka yayanki Ya Soni koda bai kai Kwatankwacin Irin Son Da Nike mai ba, plz Anee Ki Taimake ni Don Allah Wlh bazan iya Rayuwa ba Matuƙar babu *MR BELLO JIƘAMSHI*...." Ta faɗa idanuwanta Sun ciko da Ƙwallah Suna Ƙoƙarin Zubowa.

Cikin Wani Baƙin ciki da Takaichi, Aneesa ke Bin Jidda da Kallo kafin Tace "Oh..! Na Manta ammh Tunda kin Tuna min zanyi k'ok'ari sosai Anty Jidda.." Ta faɗa tana Zare Hannunta Cikin na Jidda Wace ke Share Ƙaramar Kwallar data Ziraro mata, Murmushi ta sakarma Aneesa kafin tace "Yauwa ko kefa Anee, Ammh zaki Dawo ki Ɗora SS1 Ɗinki Anan ko Aneesa..?"

Ɓata Rai Aneesa Tayi kafin tace "A"a bazan Dawo ba Nifa Na gama Wannan karatun Har Abada Tunda bana Shiga Aljanna bane.." Ta faɗa Cikin Nuna yadda Ta Tsani Karatun Gaba ɗaya, Dariya Jidda Tasaki Cikin Aji da Wayewa Tace "Oh Anee Wai ke bazaki Chanza ba Shiyasa bakwa Shiiri da Mr Bello sam, Kuna gida Ɗaya Ammh Ra"ayinku ya bambanta Shida baya son Zama da Wanda baya son Karatu.." Tura baki Aneesa Tayi kafin Tace "Aiko da Muke gida Ɗaya ba Uwarmu Ɗaya ba Kuma ba Ubanmu Ɗaya ba, Ba Abunda Na Haɗa Dashi Hanyar jirgi Daban na Mota Daban.." Dariya Jidda Ta ƙara Sakawa Tana kallon Aneesa Wacce ke Kallonta Tana ƙara Haɗe Rai Fuskar nan na ƙyalli baki da kuma Uban man Vaseline d'in Da Aneesa ta Shafama Fuskarta.

Haushin Dariyan Jidda yasa ta Juya Zata Tafi Da Hanzari Ta Riƙo Hannunta tana 'yar Dariya tace "Sorry my Anee, na daina Dariyan Kinji ko? Na yarda baku Haɗa komai ba Ammh dai gidanku Ɗaya, zaki min Abunda na Sakaki ko..?" Aneesa Data Waigo Tana Ƙara Tamke Fuska tace "Nifa bana Shiga Harkanshi Sai dai nama Anty Rahila mgana Tayi mishi Tunda Ita Naga Suna Shiri Sosai.."

Da Sauri Jidda Tace "Yauwa Ki Gaya mata Kinji ko, Ga Nombar Wayata In kin koma gida ki kirani ko da wayar Anty Rahilan ne Kinji ko my Anee.." Ta faɗa Da Sigar Lallashi Lokaci Ɗaya Tana Saka mata Takardan Data Rubuta mata Lambarta Karɓa Aneesa Tayi Cikin Ƙosawa Tace "Naji Anty Jidda bari na Tafi Su B. Kaita na Jirana.." Fuskarta Jidda Ta Shafa tana Faɗin "Ok Aneesa nagode sai naji kiranki.." Da Sauri Aneesa Ta Ƙwace Hannunta ta Wuce Tana Sakin Tsaki Acikin Ranta Take Faɗin "Ai sai kiyi Tayi Iska na Wahalar da mai kayan kara Uban Waye zai kiraki kan Wannan Mugun.." Ta faɗa Harda Tsirtar da yawu kafin tace "Allah ya Tsareni da Haɗa Shirgina Da Mara Imani."

Ta faɗa Tana Ƙarisowa Wajen Dasu S. Jibiya Suke Suna Jiranta Tun kafin Ta Ƙariso ta Dunƙule Takardan Da Jidda Ta bata ta Wurgar Da Ita gefe Tana Waigon Jidda Wacce ta Juya ta Nufi Hostels ɗinsu na DAURAMA part 2, Da kallon Mamaki B. Kaita tace mata "A. Bukar me aka baki kika yaga Haka..?" Tsaki Aneesa Taja Tana Gyara Tsayuwa kafin tace "Nombar Wayar yar Wahalar ce wai na Kirata in na Koma gida.."

S. Jibiya tasaki Dariya kafin tace "Ikon Allah Toh kan mene..?" Aneesa Tace "Kan Wannan Mugun mara Imanin Wanda ya baroni da gidanmu ya kawoni Cikin Wannan Dajin yana Cin Zalina mana.." A tare S. Jibiya da B. Kaita Suka Haɗa baki Suka ce "Wai *MR BELLO MUHAMMED JIƘAMSHI*....?" Aneesa Ta Ƙara Jan Tsaki tace "Bello dai kam Don ni bazan ce mai Mr Bello ba Wlh..."

B. Kaita tace "Gaskiya Aneesa bakya kyautama kanki ina Laifin Mr bello Da Kika bi kika Tsaneshi, taimakon ki fa yayi Daya kawoki mkranta kikayi karatu kika zama 'ya kamar Kowa.." Da Mamaki Aneesa Ta kalleta kafin tace "Nace ne ya Taimakeni ko Kinji nace miki ina Buƙatar Taimako ne, King B. Kaita Ki kama bakinki karki gaya min mganar banza nace Baƙin Mugu Wanda ya Kawoni Wannan Dajin Allah Yana Cin Zalina ko Zaki Rama mai Ne Domin Naga Alamar Kema Cikin Layin Su Jidda ne na Son Wanda bai Dace daku ba.." Ta faɗa Cikin Fushi.

B. Kaita ta Harzuƙo ma Aneesa Tana Faɗin "Eh ɗin Faɗi ki ƙara Ina Son Mallam Bello kuma so na Aure Aneesa Zuciyata Kullum Tana Zafi da Takaichi Duk Sanda Naji Kina Aibatan Mr Bello, Haba Shikenan kuma don Jininku bai Haɗu ba, baki Sonshi sai ki Hanamu mu Masu Sonshi mu Soshi ko mu nuna muna Sonshi, Tsakaninki dashi Daban muma tsakaninmu Daban, Saboda Haka Muma Kibar mu Mu nuna Muna Sonshi Domin Babu Abunda yayi mana Kuma yayi Dai-dai Da Ra"ayinmu.." B. Kaita ta Faɗa Cikin Nuna Masifarta Harda Ɗaga Murya.

Aneesa da Wata Zuciya ta Ciyota ta Tsallake S. Jibiya ta Dira gaban B. Kaita taci Kwalan Hijabinta tana Faɗin "Ina Ruwana da Son da Kuke mai Nidai sai na Faɗa ba Kuma Zan Fasa Faɗan Bello mugu ne mara Imani ba, Ko zaki iya Rama mai ne...? sai naga Ƙarewar Son da Kike mai Banza Kawai mara Aikin yi.." Ta faɗa Indanuwanta Sun Kaɗa Sunyi Jajir.

B. Kaita da Abun na Aneesa Ya kaita Wuya sai kawai ta cakumo Aneesa Suka Fara Dambe Tana Faɗin"Ni ba banza bace kece babbar Banza butulu mai Raina Alheri.." Tuni Faɗa ya kacame, S. Jibiya ce ke ƙoƙarin Rabasu da Sauran Student d'in da basu gama Tafiya ba, suka ƙariso Suna Raba Kawayen Juna Faɗa, S. Jibiya ce ke Faɗin "Haba Aneesa, Billy meye Haka Wannan ba girmanku bane Aganku kuna Faɗa da Junanku..." Aneesa Data Shaƙe Wuyan B. Kaita da Hijabi Take Faɗin "Aganmu munayin Mana Uban Waya ja In ba Ita ba Dama Tuni Billy Take Shigan Hanci Da Ƙudundune Wlh yau kafin mu bar Mkrantan nan Sai mun Goge Raini Tsakanina Da Ita.." Take Faɗa Tana Haki tana ƙara Tamke Wuyan B. Kaita Wacce ke Ƙoƙarin Ƙwace kanta.

Daga bayansu Sukaji Ance "Are u Stupid Aneesa Bukar Bulama....?"

Sukaji An Faɗa Daga bayansu Cikin Kakkausan Murya, gaba ɗayansu Suka Waiga Suna Kallon Uncle Aminu da Mr Bello Suna Tahowa, Hannunsu Sarke da Juna, Kamar Wasu Tagwaye Dama Duk Sch d'in ba Wanda baisan Abota Da Shaƙuwa Irinta Uncle Aminu da Mr Bello ba, Uncle Aminu Yana Sanye da Riga da Wando black And White, Sai Wani Rufaffan baƙin Takalminsa na Fatar Damisa Sai Mr Bello yana Sanye da Riga da Wando Rigar Dark Blue mai Dogon Hannu sai Wandonshi mai Ruwan Blue mai Haske, Ƙafarsa sanye da Takalmi Baƙi booth sai kansa Dake Sanye da p cap, wanda ya Rufe Rabin Fuskarsa Dukkansu Dogaye ne masu Surar Jiki Ƙirar Maza Cikakku Masu Zati da Haiba.

Uncle Aminu Fari ne Mai Faɗin Fuska da Dogon Hanci yana da Gemun Shi ɗan Dai-dai Wanda yake Ƙara mai kyau mai Haɗe da Zagayayyen Bakin shi mai faɗi Kaɗan, Mr Bello Fuskarsa bata bayyana ba Sosai Sai dai Daga yanayin Fatar Hannunshi Inda Rantsantsen Agogo na Kamfanin Rado ke Ɗaure A tsinsiyan Hannunshi na kallah na Fahimci Fari Ne Sosai Saboda Yadda Fararan yatsunshi ke Kwance da Gashi Sun Kwanta Zara zara Gwanin Ban Sha"awa, Yana da Faɗi Kaɗan Daga Sama Saboda In yana Tafiya Zaka ga yana Buɗewa, a kallon yanayin Tafiyarshi kaɗai ya Isa Zatinsa da Jarumtarsa Su Dakeka Tun kafin kaga Fuskarsa ma.

Duka Ɗaliban Dake Wajen Suka Fara Matswa Jikinsu na Rawa Suna Tsoron Kada A haɗa dasu Uncle Aminu da Mr Bello A lokaci Ɗaya ai Fire ne, babu Wanda Baisan yadda Suke cin Ƙaniyar Ɗalibai ba Acikin Mkrantan Musamman 'yan Taurin kai Irinsu Aneesa, Aneesa Ko Ajikinta Sai ma Ƙoƙarin Ƙara Riƙe Wuyan Hijabin Billy Kaita Da takeyi Itako Tuni Ta Saki Wuyan Aneesa Tana Ƙoƙarin Ƙwace Kanta Salamatu Jibiya Kuwa Baya ta Matsa Tana Zare Ido Aranta Tana Addu"ar Allah yasa yanzu Motar gidansu tazo Ɗaukanta.

A gabansu Suka ja Burki Uncle Aminu ne ya kalli Aneesa Dake Wani Hura Hanci ga Bakinta na Ƙara Ɗaukan Ido Cikin Tsawa Yace "Leave her Hijab Now Don Ubanki..." Ya Faɗa yana Sakin hannun Mr Bello Wanda kanshi ke ƙasa yana Danne Danne Cikin Wayarsa, Kamar baima san Abunda Ke Faruwa Awajen ba, Aneesa na Ƙunƙuni Harda Ƙwallarta ta Saki Wuyan Hijabin Billy Kaita tana Faɗi ƙasa ƙasa "Nidai ba Ubana ba Wlh.." Ta faɗa Tana Share Hanci ba Zato ba Tsammani Taji Gam!! An Buge mata baki, da Hanzari Ta Dafe Wajen Tana bin Hannun Wanda ya Maketa da Kallo Mr Bello ne Cikin Muryan Sanyi Ammh Cike da Faɗa yace "Ba Ubanki ba sai Ubanwa..?" Ya faɗa ammh Still kanshi na Kan Wayarsa Dake Hannunsa.

Uncle Aminu ne ya Riƙe Kugu yace "Au haka tace Bello? ƙanwar nan Taka fa Zan ci Ubanta, Duk da Mun Riga mun basu Hutu.." Mr Bello Dake Danna Wayarsa yace "As u wish..." Ya faɗa yana Ɗago da kansa Lokaci Ɗaya Ɗaliban Wajen kowani ya fara kama gabansu Wasu ma Jakunkunansu Suka Ɗauka Suna Nufar bakin Get, Jikinsu na Rawa Kada Laifin Aneesa ya Shafesu Domin kaf Mkrantan Kwarta-kwashi ba Wanda baisan Waye Uncle Aminu da Uncle Bello ba wajen iya cin ƙaniyar Ɗalibai Kuma ba Wanda bai san Wacece Aneesa Bukar Bulama ba wajen Rashin kunya da Rashin Tsoro.

Jin Abunda Mr
Bello yace ne ya sa S. Jibiya ta Marairaice Fuska tana Kallon Aneesa Tana mata alamun Ta bada Haƙuri Ita kanta Billy Kaita Tsoro ya Shigeta ganin Uncle Aminu ya isa Bishiyar Dalbejiya yayi Tsalle ya Katso Reshe Ɗaya ya Tsinketa Wata Doguwar Bulala Ta bayyana Kafin ma ya Ƙariso B. Kaita da S. Jibiya Suka Matsa Gefe Suna Rawan Jiki Shiko Mr Bello Baya ya Juya Bayan ya Ɗaga Wayarsa ya Ɗaura a Kunni ya fara Tafiya kamar Zai Fita bakin Get.

Cikin Tsawa Uncle Aminu yace "Kneel Down..." Aneesa Ta kalleshi tana Ɗaga Idonta sama Irin Banji me kace ba Sanin Raininta yasa bai Jirata ba ya Fara Zuba mata Bulalar Dake Hannunshi Cikin Ƙwarewa da Mugunta Tun Aneesa na Tsaye tana Cijewa karta yi Kuka sai da Hawaye Suka Fara Fita Daga Idanuwanta ta Duƙe Ƙasa Tana Kuka bai barta ba sai da Bulalar Ta gama Karairayewa A jikinta kana ya ƙyaleta ya kalleta yana Faɗin "Wannan na Bye bye Kwatar-kwashi ne In kika Dawo First Time SS1 akwai Welcome to GGUSS SS1 kwatar-kwashi Tunda Ke Har yanzu bazaki yi Hankali ba Bush girl kawai wato ba Ubanki ba sai dai nawa ko..?"

Ya fada yana Saka ƙafa ya Shureta Dai-dai Lokacin da Wata Arniyar Motar Buggati baƙa ta Shigo Cikin Mktanta Kallon Farko Kowa yayi ma motar Suka san Motar da Zata Ɗauki Mr Bello da Aneesa Ce Domin duk Faɗin Mkrantar babu Wanda Ake Zuwa Ɗauka da Motocin Alfarma sai Su, Aneesa Dake Duƙe tana Kuka Ko Ɗagowa batayi ba nan Uncle Aminu ya Juya ya Nufi inda Mr Bello ke Tsaye yana gaisawa da Direbansu Mallam Inuwa, Tuni Ɗaliban Mkrantan Masu Tafiya Sun Watse Su kuma 'yan SS3 sun Shiga Jarabawa.

Lokacin da Mr Bello ke gaisawa Da Mallam Inuwa yaja p.cap Ɗinsa Sama kyakkyawan Fuskarsa Ta Bayyana Wow.. Haƙiƙa Allah yayi Halitta Domin Wata kamilalliyar Fuska na Hanga mai Cike da Kyau da Haiba Farin Namiji ne mai Ɗauke da Dogon Hancinsa Har Baka A kallon Farko In kayi mai Zaka Fahimci ya haɗa Nasaba da Fulani Zagayeyyen Baƙin Sajensa ne ke Ƙara mai kyau Wanda yayi ma ƙaramin Bakinshi Kwanya matsakaitan Idanuwanshi masu Ɗauke da Wasu Fararen Idanuwa Masu Kyau da Narkan da Zuciyan 'yan Mata, Sai zara zara gashin Idanuwansa Masu Tsawo da baƙi Da Gashin Girarsa Baƙi Siɗik Haɗe da Wani Kwantaccen Gashin Kansa Irin na Fulani Mr Bello baya barin Gashi Ya Taru Akanshi ko A yanzu Ma Babu Cikar Gashi Sosai

*MUHAMMED BELLO MUHAMEED JIƘAMSHI* Kenan wanda Ɗalibai da Malamai kema Laƙabi da _MR BELLO_  kuma Ƙani ga Cheif Army of Staff na ƙasa Gaba ɗaya Wato *LT. GEN. MUKTAR MUHAMMED JIƘAMSHI* Cikkaken Namiji ne mai Aji da Zati Wanda Kaf 'yan Matan Dake GGUSS kwatar- kwashi ke Rubibi Akanshi, Tun daga Kan Malamai da Ɗalibai, Kan 'yan Junior ne da Senior, Kaf Ɗinsu ba Yarinya Da Zatace bata Crushing Ɗinsa, Mkrantar Tana ji Dashi Domin Tunda Ƙasa Zuwa Sama Shine kaɗai Malami ƙwara Ɗaya Tak da yake Ɗaukan Su Mathematics Sakamakon yana da Master Digree Akansa Wanda ya Haɗosa a babban Birnin America Wato U.S.

Da Sauri Billy Kaita da Salamatu S Jibiya Suka ƙariso ga Aneesa Suka Riƙota Billy na Faɗin "Aneesa Don Allah ki daina Wannan Taurin kan Wahala kawai zaki Dinga Sha.." Aneesa Na Miƙewa Ta Fizge Jikinta Tana Share Kwalla tace "Bazan bari ba Ki Rabu Dani Munafuka Ai Burinki ya cika Tunda Yau ɗin ma Ina Murnan zan Bar Uƙuba sai da Aka ƙara Zalunta ta, In kika ƙara Nuna Kin ma Sanni Billy Allah ya Isa Tsakanina Dake Domin Duk Masoyina bazai so Wanchan Mutumin ba.." Tana gama Faɗin Haka ta Ɗauki Trolley ɗinta da ƙaramar Jakarta Da Wata Jaka Ta Rataya abaya kafin ta kalli Salamatu Jibiya tana Faɗin

"S. Jibiya Sai munyi Waya Ga Mallam Inuwa chan yazo zan Tafi kada yasa atafi Abarni irin na Wanchan Term din.." S. Jibiya bata samu Zarafin mgana ba Aneesa Ta Wuce Ruƙu Ruƙu da Kaya Billy da Salamatu Jibiya Suka Bita da kallo Suna Kaɗa kai Sanin Halin Aneesa na Masifa da Saurin Fushi Ammh Akwai Saurin Sauka Nan da Gobe zata manta komai don Duk Faɗin Kwatar -kwashi bata da kamar Billy Kaita da Salamatu Jibiya.

Tana ƙarisowa Mallam Inuwa Ya Tareta da Fara"a yana Faɗin "A"a ga Ɗiyata 'yan Makranta, Kai Masha Allah Hajiya tace Kin kammallah zangon karatu na Farko.." Ya faɗa Cike da Murna Cikin ɓata Rai Aneesa Tace "Wlh na gama Dawowa wannan Mkrantan Baba kama ji gaskiya Haba na gaji da Wannan karatun Mkrantar Ta Isheni Baba Wahalar Tayi yawa Tunda bana Shiga Aljannah bane.." Ta faɗa Tana Sakar mai Akwatunanta Guda Biyu Ɗauka yayi yana Dariya gefenshi ya kallah yaga Basu Bello Sun gangara Zuwa Quarters d'in Malamai Mr Bello zai Ɗauko Jakarsa.

Booth ya Buɗe yana Zuba mata Akwatunan, Hannu ya Miƙa yana Faɗin "Au hakane fa Kin gama Toh kawo Jakar itama asaka A ciki Karatu kam Kin gama Tunda bana Shiga Aljannah bace Wanda Kika samu Allah samai albarka.." Washe baki Tayi Tana Faɗin "Yauwa Baba Allah sa Yadda ka Fahimta Haka *YAYA MUKTAR DA ANTY RAHILA* Suma su Fahimta ko da yake Ko Sun barni nasan Wannan Mugun bazai barni ba ammh Wlh Wannan karon ko Guduwa ne Sai na Gudu Borno Wajensu Yaya Ali In dai Aka matsamin sai na Dawo Mkrantar nan..." Ta faɗa Harda Sharɓe Ƙwallah..

Kallonta yake bayan Sun gama Saka kayan ya Rufe Booth d'in Motar yana Faɗin "A"a 'yata mai yayi Zafi basai kin gudu ba, Insha Allahu Shima Zai Fahimceki.." Ya faɗa Yana Danne Dariyansa Ganin Tana Wani Taɓe baki gidan baya ya Buɗe mata yana Faɗin "Ɗiyata kinbar ƙawayenki gasu chan.." Jin Haka yasa Ta Juya Tana kallon Salamatu Jibiya da Billy Kaita Suna Tsaye Suna kallonta, Harara ta Makama Billy Harda Murguɗa mata baki Tana Faɗin "Sai Wata rana na bar Muku Mkrantar.." Ta faɗa kai Tsaye Tana Shigewa Mota, Dariya Suka saka Aran S. Jibiya Tana Jaddada Dawowar Aneesa SS1 Dole kamar yadda Yake Awajensu.

Basu Daɗe ba sai ga Uncle Aminu da Mr Bello Sun Ƙariso Yana Ɗauke da Wata bak'ar jakar Baya, Musabaha Sukayi da Aminu Suka Ɗanyi Mgana kafin Suyi Sallama don Uncle Aminu sai Next Week zai Tafi Sakamakon Ɗaliban SS3 Dasuke WAEC basuyi Darasinshi na Na Turanci ba shikuwa Mr Bello Da yake Malamin Lissafi Kuma Jiya Sukayi Paper, d'in Dat Why Shi Zai Wuce Gida Shima Kuma Uncle Aminu Dake Kano sai Sati na Sama Zai Tafi.

Shi ya Buɗema Mr Bello Ƙofar gaban Motan ya Shiga Suna Ƙara Sallama, kafin ya Rufo ƙofar Motar Mallam Inuwa ya Tada Motar Suka Fice Daga Mkrantan Uncle Aminu na Ɗaga musu Hannu Aneesa na Cikin Mota tana Makamai Harara Aranta tana Faɗin "Mugu sai Abi Wani Sarkin Ba Aneesa ba.." Ta faɗa Harda Yar Dariyanta Karaf Ko Suka Haɗa Ido da Mr Bello Yako Makamata Harara yana Faɗin "Don Ubanki Ɗauke waɗannan baƙaƙen Idanuwan naki Akaina ko nasa Mallam Inuwa ya Faka Motar nan na Wurgaki Dajin nan." Ya faɗa Cikin Tabbatar da mganarsa.

Jin Haka yasa Tayi Saurin Sadda Kanta Cikin Rawan Jiki Saboda Tasan Zai aikata Don Wanchan Term d'in ma Tafiya yayi ya barta sai da tabi Direban gidansu Salamatu Jibiya ta tafi gidansu ta Kwana Washegari Akazo Aka Ɗauketa, Haɗe Rai Tayi kanta ta maida Gefe Tana Ƙunƙuni Acikin Ranta Shiko Gyara Zama yayi yafito da Wayarsa yana latsawa Mallam Inuwa na gefe yana Tuƙi yana kanne Dariyarsa ganin Yadda Aneesa Take Tura Baki kamar Zai Tinko Ya Faɗi Saboda Ƙunƙuni.

Suko su Billy, su Aneesa Suna Tafiya ba Daɗewa Kusan Tare Motocin Gidanasu S. Jibiya da Billy Kaita Suka zo nan da nan Kowacce Ta Ɗauki Kayanta Suka Loda Amota Sukama Juna Sallamar sai sunyi Waya Kafin Su Dawo mkranta.


*How to pay....?300 0552179550 JAMILA UMAR GTB, VIPS..?600...or MTN card aturo ta wannan Nombar 09069067488 hade da Hoton Tracsation*


_akwai garabasanmu Na Sanyaya biyu,👭 Matar Naseer Da Mr Belll

Please Login or Register in order to submit comment