Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Najwah ki kwantar
da hankalinki kiyimun bayani". Kasacewa komai
tayi.
***********
Kawai saita samu kanta da yimasa 'karya" dama
kiranka nai inbaka ha'kurin abinda Inna tayiwa
wakilanka" "dakata Najwa Innafa mahaifiyatace
menene abin bada ha'kuri a ciki? Kar insake ji
kinji ko". Kawai saita fashe da kuka "yanzu
Mustapha kanji kana gani zata rabamu? Kasanfa
munasan juna, gaskiya kai wani abu". Cikin
dauriya yace "me zanyi Najwa?". "Mustapha
kawai mugudu". " subhanallah haba Najwa idan
rai ya 'baci hankali baya gushewa, Inna ta isa
damu ta isa komai a kanmu bazanso ki gujewa
mahaifiyarki sabida niba, kisani idan ubangiji ya
nufa muna da raban kasancewa babu wani
mahalukin dazai hana idan kuma 'KADDARARMU
CE a haka bamu isa hanawa ba. Abinda fa
ha'kuri baibamuba rashinsa bazai bamu ba".
Jikinta yai sanyi cikin shagwa'ba tace to ani
banasan auran dole kuma ba kyau ko a addinan
ce kodai ka daina sonane?".
Cikin sautin jan hankali yace "Najwaty! Ajiyar
zuciya tai ya cigaba Najwa True lovers
are like upper & lower eyelids!.They often meet
because they miss each other
and
when they meet, they don't see the world
around". Najwa tai shiru kalamansa nai mata
dad'i cikin jan hankali yace "Najwah say me
something please"( Najwa kice mun wani abu
can Allah).
Cikin so shau'ki 'kauna tace " Mustapha!! MY
HEART IS LOCKED KEYS ARE WITH U OPEN
AND SEE HOW MUCH I LOVE YOU".
Kawai saita katse layin tana tsananin jin nauyi
tamkar yana kallonta.
Cikin hanzari ta shiga band'aki ta gyara jikinta
tayo alwala lokacin har biyar tayi.
Kubiyoni
A daran Zainab ta kira sauran 'yan'uwanta
Fiddausi Maryam Saudaht tace su had'u gida da
safe sabida tattauna matsalar Najwa. Ta kira
Husnah tace ta gayawa Inna Najwa na gunta kar
hankali ya tashi. Haka Najwa ta kwana sukuku
da'ita, washegari drivern Zainab ya d'aukosu
zuwa gida. Tun a hanya gaban Najwa ya dinga
mugun fad'uwa tana jin kururruwa a
kunnuwanta kamar ana kiranta wasu lokutan har
rufe idonta takeyi. Suna shiga layinsu taga taron
mutane, abin ya tsoratata ya kuma bata mamaki
gabanta ya cigaba da fad'uwa har suka wuce
taran mutanan da makara zasu ma'kabarta. Ta
dinga biybiyarsu da kallo har sukai parking suka
fito. Gab da zasu shiga gida taji ankira sunanta,
sai taji kamar muryar Mustapha cikin azama ta
juya amma ga mamakinta ASHIQ ne cikin
murmushi yake nuna mata takobinsa duk jini
jikinta a hankali yaimata nuni da hannunsa
saitaga MUS'AB kwance cikin jini. Wata
giggitaciyar 'kara ta saki daga nan bata sake
motsiba cikin sauri Zainab ta shiga gida da'ita.
Abin mamaki tana shiga duk 'yan'uwanta na
zaune cikin damuwa Inna har sharce hawaye
takeyi, ganin sun shigo da Najwa ranga- ranga
yasa sukai kanta suna tambayar lafiya. Cikin
jimami tace " nidai muntaho lafiya 'kalau kawai
sai ganin nai ta zube". Ruwa mai sanyi aka zuba
mata ta saki ajiyar zuciya a hankali ta soma
motsi can cikin 'karaji ta furta MUS'AB. Gaba
d'aya wajan suka bita da kallon tausayawa
banda Zainab data bita da kalon mamaki. Inna
ta share hawaye "Najwa Mus'ab kuma saidai
wani bashi ba ya tafi ya barmiki duniyar saiki
zuba ruwa kisha". Cikin rud'ewa tace "Inna ya
mutu? Dama mafarki na zama gaskiya? Allah
kasa in farka daga wannan mummunan
mafarki". Cikin jin haushi Maryam takai mata
duka dama cike take da haushin anbawa Abdul
auran Farida. Da sauri Zainab ta tare tana
tambayar abinda yake faruwa.
Inna ta share hawaye tace" Zainab tunda na
kori mayen yaron nan da danginsa Najwa ta
gudo gidanki jiya, a daran na aikawa iyayan
Mus'ab sukace yau zasu aiko ai maganar
auransu, yau muka wayi gari da mummunan
labari wai Mus'ab ya mutu". Cikin tashin hankali
Zainab tace "ya mutu?". Maryam tace "tabbas
ya mutu ni walahi badan ance ya shiga dakinsa
ya rufeba akajiyo ihunsaba kuma yasa sakata
walahi tsaf zance Mustaphs ne ya kasheshi don
gadon marasa imanine". Cikin sauri Saudaht ta
doke mata baki " garin shegen kishinki saikin
d'aukowa kanki masifa".
Inna ce tai musu tsawa suka bari. Najwa kuwa
jin ana neman la'kabawa Mustapha yasa ta
had'e fuska tanasan furtawa amma tsoro ya
hanata. Take idonunta suka sauya launi daga
fararre tas zuwa jajjaye tamkar gauta. Wata
muguwar sha'ka taiwa Maryam ta soma
dukkanta tun sunaiwa lamarin kallon wasa saiya
zama babba. Sunyi sunyi su 'kwaceta sun kasa
bata saketaba saida ta 'bala mata hannu 'baras.
Sunyi jigum suna kallonta zuciyoyinsu fal tashin
hankali Maryam sai 'burarri takeyi Zainab ta
dinga kallon Najwa cike da zargin wani al'amari
amma tana tsoran furtawa.
Bata tankawa kowa ba ta shiga dakinta tai
kwanciyarta dukkansu suka kasa yimata
magana tamkar an d'aure musu bakuna. Suka
d'auki Maryam suka kaita wajan me gyara.
Bayan sun dawo sukaje sukaiwa iyayan Mus'ab
gaisuw.
Najwa sai laasar ta farka lokacin duk yayyenta
sun tafi gidajansu, bata ko kali inda Inna take ba
ta shige bayi tayi wanka ta fito ta tada sallah
azahar da la'alar ta had'a tana idarwa idonta
yakai kan wata leda a d'akinta sai 'kyali take da
sauri ta d'auka abin mamaki take a way ne ciki.
Batai tunanin waye ya ajiyeba kawai ta bud',a ta
hau ci. Husnah ta shigo kamar anjehota cikin
masifa tace " Besty baki da imani Mus'ab ya
mutu ko ajikinki ko?". "To dan ya mutu sai me?
Nina kasheshi?". Yake jikin Husnah yai sanyi ta
dinga yiwa Najwa kallon mamaki takai idonta
kan abincin gabatanta "waya baki?" "Hmmmm!
Sabida kinmaidani matsiyaciya banda kudin siya
ko?". Husnah sai taji wani bambarakwai duk
Najwa ta sauya mata. Jiki a sanyaye tai mata
gaisuwa ta wuce.Tun daga ranar babu jituwa tsakanin Najwa da
Inna, hakama Husnah ta kasa gano kanta.
Najwa duk ta rame tayi ba'ki ga wasu 'kuraje a
fuskarta da suka haddasa mata muni na bagaira
babu dalili, hakan yasa duk ta tsangwami kanta
ko fita batayi. Chat ta bud'e a wayarta wanda
hakan ya taka muhimmiyar rawa wajan
d'aukemata hankali ga yin adu'a ko sallah tayi
tana idarwa zata d'auki waya babu batun adu'a
hakama bacci da ita take kwana a hannu.
Mutuwar Mus'ab tana nu'kur'kusarta a zuciya
hakan yasa mata yawan fargaba mai tsanani.
Gani babu sarki sai Allah Inna ta soma janta a
jiki tanai mata nasiha zatanta tunanin Mus'ab
ne, cikin 'kan'kanin lokaci suka koma dai-dai.
Maryam tasha jinya sossai hannu ya warke,
saidai bikin Abdul da Farida babu abinda aka
fasa. Tayi mitar tayi masifar a banza.
A hankali fuskar Najwa ta washe ta dawo
normal, suna waya da Mustapha lokaci lokaci
yaso ya zo yaiwa Inna gaisuwa saidai tsoro ya
hanashi. Yana shakar Inna matu'ka.
Bacci yake jinsa yake kamar a farke a hankali
'kadangaran ya mi'ke a tsaye tamkar mutum
yana murmushi yace "Mustapha ka cika taurin
rai, nace kafita gonata kana neman yimun wasa
da hankali sau biyu ina kawoma farmaki kana
kufcemin, tabbas zaka tafi ma'kabarta tamkar
yadda d'an'uwanka ya tafi cikin rashin tsoro
yace " kai ma'kiyin Allah inshaa Allahu nafi
'karfinka, bazakai nasara a kainaba, wai kai
waye? Kana neman takuramun fa".
Take ya zabga masa wata bulala take Mustapha
ya saki 'kara ya farka daga mafarkin abin
mamaki da tsoro shatin bulallar rad'au a
hannayansa harda kwailewa. Kansa ya d'aure
yanasan sanin ainihin abinda ke bibiyarsa amma
bayasan sanya kansa cikin hallaka.
Adu'a yayi ya mi'ke yai wanka ya fita duk jikinsa
a sanyaye. Mahaifiyarsa taitai masa nasiha daya
shiga gaisheta zatanta ko batunsa da Najwa ne.
Kai tsaye gurin Malamin Islamiyyarsu ya nufa
Ustaz Yusuf, bayan sun gaisa yai masa bayyani,
yai jim daga 'karshe yace ya bashi gobe zaiyi
istihara. Washegari cike da azama ya koma
saidai kalaman Malaminsu ya bashi tsoro da
mamaki, bayan sun gaisa yace "gaskiyar magana
Mustapha lamarinka 'boyyayan sirrine, domin
nayi istihara jiya amma bana ganin komai sai
wani wani duhu da 'bur'bushin wani 'karamin
haske wanda ya rufeka, inaga mubarwa Allah
komai mu durfafi adu'a domin ubangiji baya
bacci".
Haka suka rabu jiki a sanyayye.
Ku dakace ni........
Cikin kwanciyar hankali soyyayarsu ta cigaba da
bun'kasa a 'boye batare da sanin Inna ba, sukan
had'u a gidansu Husnah ko inzata makaranta ko
intaje weak end gidan Zainab.
Ina na kula da takunta kwata - kwata ta daina
maganar Mustapha ammafa kowaye zaizo
nemanta bata fita, tayi hancinin tayi dukan harta
gaji.
Zama ba d'ankwali kuwa sai abunda ya cigaba,
musamman yanzu da ake turomata style
(samfir) na gyaran gashi da kitso a chat, wani
abun birgewa har gashi ake d'auka bayan anyi
parking ai disple picture dashi wato (Dp) ba tare
da la'akari da wa kake chat ba. In tunaninki
kinsan bakya bada numberki ga maza akwai
masu had'a number haka kawai. Wata kuma duk
sanda takai caji budewa suke su kwashi
numbobi kawai dan san zuciya.
A duk lokacin da Najwa tai Dpy na parking zakiji
freind d'inta na yabawa itoko tanajin dadin haka.
Har so take azo exfection a sch dan kawai a
yaba gashinta. Kwanci tashi suka zana
jarrabawar shiga aji shida ita da Husnah duk
sunyi nasara.
A hankali Mustapha ya soma zuwa gidansu
Najwa, sabida bayasan ke'bewarsu wani waje
daban gudun fad'awa TARKON SHAI'DAN gara a
gidansu komai zai faru ya faru. Tun yana zuwa
ana hanata fitowa harta soma satar jiki tana
fitowa.
Hankalin Inna ya tashi matu'ka ganinta
Mustapha asiri yaiwa Najwa taki kowa saishi. Ta
tara yaranta kaf tana kuka kan itafa tagaji susan
matakin d'auka. Aunty Zainab cikin lallashi tace
"Inna kidaina zubarwa Najwa hawaye, hawayan
mahaifa masifane ga yaransu, musamman
Najwa da take mace, kamata yai mui mata
adu'a. Kuma idan mun duba ai Mustapha baida
wani hali da za'a gujewa auransa. Nagartacan
mutum ne da kowa yake yabansa". Cikin masifa
Maryam tace " inji ubanwa? 'Dan iskane". A
zafaffe Zainab ta wanka mata mari " Maryam na
fahimci kece jagorar wargaza tafiyar nan sabida
mijinki zai auri 'kanwarsa, shi aure ai nufin Allah
ne kuma MATAR MUTUM kabarinsa ke baki isa
hana abinda ubangiji ya tsaraba. Harkike neman
zagina kan rashin gaskiya. To ainayi bincike kan
lamarinsa 'karshema yanzu shiyakewa yarana
lesson kuma nayiwa Abban yara magana yace
yayi bincike Mustapha ko abokin fad'a bashi
dashi".
Cikin borin kunya Maryam tace " Inna kinji ko
wallahi Najwa 'KADDARARMU CE kina kallo
yadda Yaya ta mareni akanta kuma ai bashari
duk wanda zaifadi halinsu baya nane tunda ni
munfi kusa dasu......kallon da Najwa taimata
yasata gum dan yanzu mugun tsoranta takeji
tunda tasha duka. Cikin tausassawa Saudaht
tace "shiyasa yayan 'kurfi take birgeni da tana
kusa da tuni ta sasanta mtssss! Auran nesama
baiyiba". Fiddausi tai murmushi tace "Inna
gaskiya ubangiji ya haramta auran dole miyasa
zakiyiwa Najwa bayan mu bakiyi mana ba?
Kuma ma yanzu aibata da saurayi inba
Mustapha ba mafi a'ala kibarta ta aureshi karta
jawo mana magana. Ma'aikifa ya hara ta hakan
da kansa ya raba auren dole har sau biyu.
Ma'aiki (S A W) yana cewa:- Zuciyoyi rundunane
daban- daban, idan wad'anda suka dace da juna
suka had'u sai suyi 'kawance. Idan basu dace
da juna ba sai suyi baram-baram.
Wata rana wata mata mai suna Asmah'u Bint
Khidam taje wajan Manzon Allah (s.a.w). Tana
mai cewa. 'Babanta ya aura mata wani d'an
'kaninsa dan ya kare matsayinsa a wajansa sai
ma'aiki (s.a.w)yace mata:" idan kinso na raba
tsakaninku idan kin ha'kura shikenan ki zauna da
mijinki".
Haka Ma'aiki (s.a.w) ya raba aura tsakanin
Usman bin Muz'um da iyalanka. Kamar yadda ya
raba na Abdullahi d'an Umar da matarsa".
Zamani ya sauya Inna yanzu yara a tsaye suke
ko kana tarbiyarsu sai kana adu'a domin duk
tsarewarka sai ubangiji ya tsare maka". Jikin
Inna yai sanyi nan da nan ta sako. Sun daidaita
magana akan Najwa zata kira Mustapha ya turo
magabatansa. Aunty Zainab ce ta hana tace
zatai masa magana. Da haka taro ya watse
saidai tunda aka ajiye magana Najwa ta kasa
walwala da farin ciki gaba d'aya ta sauya daga
Najwarta zuwa

Yaya Zainab hargida tai kiran Mustapha kan
maganar inda gaske yake ya fito, yaimata
al'kawarin zai sanarwa mahaifiyarsa. Da farko
Mama taso tirjewa sabida abinda Inna tai musu,
amma yaitai mata nasiha yana bata ha'kuri.
Mama tai musu fatan alkhairi akasoma shirye-
shiryen kai kud'i naira dubu talatin yakai sai
dubu ashirin nasa rana. Mijin Yaya Zainab shiya
amshi kud'in anyi komai a mutunce.
Gaba d'aya Najwa ta sauya, miskilancinta ya
'karu fiye dana da. Al'amarin mafarkinta ya
cigaba da faruwa saima abunda yai gaba.
***********
Mustapha kansa ya kasa gane kanta a haka
suka cigaba da tafiya. Ko hira yazo ta dinga
d'aure fuska tana 'kun'kune daga uhmm sai
uhmmm tun baya damuwa har yakai ga nunawa
Husnah. Saidai itama bata samun sakin fuska
daga gareta. Ko makarantar boko ta daina
tsayata saidai abinda ya d'aure mata kai kullum
inta dawo makaranta a wajan kukar nan ta
layinsu take samunta sannan su jera kamar
basuba su tafi makaranta.
Inkuwa akaje makaranta itace tsokani wancan
yima wancan ba'a. Ga wani 'karfin masifa da
take dashi ko malamai sai sunyi da gaske suke
tan'kwarata, dukan makara kuwa tuni aka daina
yimata sabida duk Malamin daya daketa to
kuwa zaikwana yana jinyar hanunsa.
Kwanci yashi har suka zana jarrabawar gama
makaranta, lokacin Najwa ta 'kara wani kyau na
fizgar hankali, abinda basu saniba duk daran
duniya ASHIQ ke zuwa ya d'auketa a mafarki ya
kaita aimata gyaran jiki irin nasu. Nan da nan ta
soma had'uwa da manyan alhazawa saidai bubu
wanda taken a fuska, Mustapha kad'aine
taurarranta. Saidai zuciyarta najin haushinsa
idan bata 'bata masa raiba bata jin dad'i. Gaba
d'aya Mustapha damuwa da fargaba ta sashi
gaba duk ya zabge yayi ba'ki adu'ace kawai
take ri'ke dashi.
Kullum ASHIQ cikin tsora tashi yake tare da
barazanar d'aukar ransa. A haka har aka tsaida
lokacin biki.
Najwa zaune a dokin 'kofa Inna tana d'akin girki
cikin fad'a tace " waike Najwa wace irin
hallitace da bakya jin magana?". Cikin so'baro
baki tace "menayi kuma Innarmu?". Cikin takaici
tace " Najwa duba fa jikinki kali shigar da kikai
kida acikin gida kike kinsan wazaya shigo? Kai
babu kalabi ga kuma kin zauna dokin 'kofa
mattatarar shaid'anu, anya Najwa wannan
rayuwa ce?".
"Kefa Inna kinsoma matsa mana , haka ake
rayuwa? Kawai ki barmu muji dad'i haba". A
zafaffe tace "kee! Najwa saurara ni zaki gayawa
maganar banza?". Itama cikin zafi ta waigo take
muryarta ta bud'e ta koma muryar babban
mutum idonta yai shud'i da ja ta nuna Inna da
yatsa take ta soma lan'kwashewa bakinta da
hannunta suka soma juyewa cikin minti uku
kacal ta koma tamkar mai cutar shan Inna. Ba
kowa yai hakanba face ASHIQ, domin lokacin ita
Najwa ma tana gefene tana chat jira take Inna
ta gama fad'anta ta tambayeta wace Najwar?
Najwa tana kallonsa sai hawaye babu bakin
magana. Takuma kasa tunanin yin adu'a sai
bayan fitarsa ta samu damar mi'kewa tai waje
tana kururuwa.
Ku biyoni.......
'KADDARMU CE!
SANAH S MATAZU
16-17
Da taimakon Maman Husnah Najwa ta fito da
Innah daga dakin girki saidai babu hannu babu
'kafa. Hankalin yaranta ya tashi sossai. Aka
dirfafi neman magani amma ina, wani ikon Allah
da sukayi suka gaza saisuka watsar da lamarin
tamkar ankauda tunaninsu da hankalinsu a kanta
kullum cikin zaryar kulawa da'ita suke amma
basa yun'kurin nema mata magani. Mustapha
inya takura Najwa da batun har rigima sukeyi
dan haka kowa ya tattarasu ya zuba musu na
mujiya.
Jikin Inna yasa aka 'kara bikin su Najwa zuwa
wata guda, saidai babu wani cigaba tilas aka
ha'kura Yaya Zainab ta d'aukowa Inna mai kula
da'ita aka soma shirye- shirye. Hankalin Najwa
yai mugun tashi zuwa lokacin duk tafita
hayyacinta, ko gidansu Husna ta daina zuwa,
lokuta da dama kasancewar layinsu shirune in
muguntar ASHIQ ta motsa saiya tunkud'ota
wajan kukar nan ya kawo yara ya zube yana
gefe yana kula da'ita suita shirme. Husna kad'ai
ke kula da zamanta a gun amma ta kasa
fad'awa kowa.
Kullum ASHIQ cikin wasa da hankulan
makusanta Najwa yake babu wanda ya ke lura
da lamuranta, dana cutar Inna dama-dama
Fiddausi tafisu tsayuwa wajan du'a'i.
Biki ya 'karato ankawo lefe an tsaida lokacin
biki, sati biyu duk wani shige da fice Husnah
keyi, dan wayarsma yanzu saita gadama take
d'agawa, Mustapha ya gyara 'bangare guda a
gidansu babban parlour yayi cikinsa da toilet da
kitchen da stor sai bed room da 'bangaran ba'ki
d'aki guda. Anyi fenti anyi siminti da komai .
Ansoma hidimar biki Inna na kwance, sai gani
da'ito duk wanda ta kalla saidai aga tana zubda
hawaye hankula sun tashi sossai gidan biki sai
koke-koke. Amarya dai gata nan sukukku kawai
sha'ani ake amma bata da nutsuwa duk ta
zabure. Tunanin kowa cutar Innarta ke damunta.
Babban tashin hankalin Najwa matsawar da
ASHIQ yai mata kan ta kori Mustapha ta'ki
sabida ya kasa nasara a kansa. Babban tashin
Najwa duk lokacin datai yun'kurin yimasa rashin
mutunci wuyarta su had'a ido ko taji sautin
muryarsa take yanke jikinta yakeyin sanyi. A
haka aka d'aura aure ka soma shirin kai amarya.
Yaya Zainab da sauran 'yan'uwanta sunyi rawar
gani sossai. Sun 'kawata dakin Najwa ko mai
uba sai haka. Najwa dai gata a gidan masoyinta
datafi 'kauna, saidai tsantsar tsanarsa da takeji
kamar ta kashe kanta. Amma da zarar taji
muryarsa angama tsiya. Da farko zaman nasu ya
soma dad'i amma daga bisani sai Najwa ta
koma zam Najwan ASHIQ sabida tasoma nasarar
hana Mustapha gudanar da wasu ibadunsa,
kamar azumin littinin da alhamis. Tsayuwar dare
kau daya soma ASHIQ zai soma tsoratata ta
dnga iface- iface tilas zai katse ya saurareta.
Mijin yayarsu ta 'kurfi tunda yazo yaga jikin Inna
yace zai turo mai magani daga can a dan yana
komawa ASHIQ ya gama dashi bai kwanaba.
Tilas washegari ta koma 'kurfi domin yin takaba.
Saidai zuciyarta cike da zargi sabida yadda aka
bada labarin mutuwarsa domin kwatankwacin
rasuwar Mus'ab ne.



Da taimakon Maman Husnah Najwa ta fito da
Innah daga dakin girki saidai babu hannu babu
'kafa. Hankalin yaranta ya tashi sossai. Aka
dirfafi neman magani amma ina, wani ikon Allah
da sukayi suka gaza saisuka watsar da lamarin
tamkar ankauda tunaninsu da hankalinsu a kanta
kullum cikin zaryar kulawa da'ita suke amma
basa yun'kurin nema mata magani. Mustapha
inya takura Najwa da batun har rigima sukeyi
dan haka kowa ya tattarasu ya zuba musu na
mujiya.
Jikin Inna yasa aka 'kara bikin su Najwa zuwa
wata guda, saidai babu wani cigaba tilas aka
ha'kura Yaya Zainab ta d'aukowa Inna mai kula
da'ita aka soma shirye- shirye. Hankalin Najwa
yai mugun tashi zuwa lokacin duk tafita
hayyacinta, ko gidansu Husna ta daina zuwa,
lokuta da dama kasancewar layinsu shirune in
muguntar ASHIQ ta motsa saiya tunkud'ota
wajan kukar nan ya kawo yara ya zube yana
gefe yana kula da'ita suita shirme. Husna kad'ai
ke kula da zamanta a gun amma ta kasa
fad'awa kowa.
Kullum ASHIQ cikin wasa da hankulan
makusanta Najwa yake babu wanda ya ke lura
da lamuranta, dana cutar Inna dama-dama
Fiddausi tafisu tsayuwa wajan du'a'i.
Biki ya 'karato ankawo lefe an tsaida lokacin
biki, sati biyu duk wani shige da fice Husnah
keyi, dan wayarsma yanzu saita gadama take
d'agawa, Mustapha ya gyara 'bangare guda a
gidansu babban parlour yayi cikinsa da toilet da
kitchen da stor sai bed room da 'bangaran ba'ki
d'aki guda. Anyi fenti anyi siminti da komai .
Ansoma hidimar biki Inna na kwance, sai gani
da'ito duk wanda ta kalla saidai aga tana zubda
hawaye hankula sun tashi sossai gidan biki sai
koke-koke. Amarya dai gata nan sukukku kawai
sha'ani ake amma bata da nutsuwa duk ta
zabure. Tunanin kowa cutar Innarta ke damunta.
Babban tashin hankalin Najwa matsawar da
ASHIQ yai mata kan ta kori Mustapha ta'ki
sabida ya kasa nasara a kansa. Babban tashin
Najwa duk lokacin datai yun'kurin yimasa rashin
mutunci wuyarta su had'a ido ko taji sautin
muryarsa take yanke jikinta yakeyin sanyi. A
haka aka d'aura aure ka soma shirin kai amarya.
Yaya Zainab da sauran 'yan'uwanta sunyi rawar
gani sossai. Sun 'kawata dakin Najwa ko mai
uba sai haka. Najwa dai gata a gidan masoyinta
datafi 'kauna, saidai tsantsar tsanarsa da takeji
kamar ta kashe kanta. Amma da zarar taji
muryarsa angama tsiya. Da farko zaman nasu ya
soma dad'i amma daga bisani sai Najwa ta
koma zam Najwan ASHIQ sabida tasoma nasarar
hana Mustapha gudanar da wasu ibadunsa,
kamar azumin littinin da alhamis. Tsayuwar dare
kau daya soma ASHIQ zai soma tsoratata ta
dnga iface- iface tilas zai katse ya saurareta.
Mijin yayarsu ta 'kurfi tunda yazo yaga jikin Inna
yace zai turo mai magani daga can a dan yana
komawa ASHIQ ya gama dashi bai kwanaba.
Tilas washegari ta koma 'kurfi domin yin takaba.
Saidai zuciyarta cike da zargi sabida yadda aka
bada labarin mutuwarsa domin kwatankwacin
rasuwar Mus'ab ne.
'KADDARARMU CE!.
SANAH S MATAZU.
17-18.
Tunda yayarsu ta gama takaba ta dawo gida
d'ungurun gum ta soma kulawa da mahaifiyarsu.
Kullum takan tofa Ayyatul kursiyu da fala'ki da
nasi ta shafa mata cikin sati guda 'kaffafunta
da bakinta suka dawo dai-dai saidai bata
magana sai nuni da hannu.
Tunda ta soma yiwa Inna adu'o'i sai ASHIQ
yasoma tsoratata, saitaji ana kiran sunanta ko
kuma ana dariya mai 'karfi. Ko taga Najwa na
binta da wu'ka. Kanta ya kulle ta tab star
matsalar Innarsu daga Najwa ne. Dan haka taje
gurin limamin unguwarsu saidai amsar da ustaz
Usman ya bawa Mustapha itama haka abata.
Saidai ya bata adu'o'i sossai tare da yimata
bayani kan kodai Najwa ba jinsusu bace ko
kuma ala'ka ta tsakanin MUTUM DA ALJAN.
*************
Husnah ta soma ja tanai mata tambayoyi akan
Najwa saidai babu wata satar amsa, abu d'aya
ta tsinta game da Najwar zuwa biyu 'kiyyayar
Mus'ab da zaman bakin kuka. Hankalinta ya
karkata da batun kukar dan dama takan yawaita
jin tsigar jikinta na harbawa intazo wucewa.
Koma menene zata cigaba da adu'a.
*******
'Ya'yanta sunji dad'i sossai saidai sunyi
mamakin sauyin da aka samu. Musamman
Najwa da tun a gun fuskarta ta sauya idonta yai
jajir. Bata wani tsaya dogon bayani ba. Tai
murmushi tace "kudai kudinga adu'ar nemawa
kanku da yaranku tsari a koda yaushe" duk sai
jikinsu yai sanyi. Nan da nan Najwa ta azalzali
Mustapha kan sai sun tafi gida basu wani jimaba
suka wuce. A hanya yake mata 'korafi kan
meyasa tace su taho?. Cikin 'kun'kuni tace "
yayar nan zanyi maganinta tana yimana
shisshigi" da sauri ya dubeta saita wayance tace
" nufina tafimu kusa da Inna sossai". Dariya yai
amma 'Kazan zuciyarsa yana auna kalamant.
Haka zaman nasu ya kasance, matsalar yau
daban ta gobe daban, yanzu abinda ta tsira
shine xuwa taiwa Mama rashin kunya wanda
hakan kan tunzura Farida su hau dambe.
'Karshe kuma Faridan ake cuta. Dama wazai
had'a 'karfin MUTUM DA ALJAN (Munayshst).
Kullum cikin kawo 'kararta suke ya rasa yadda
zai 'bulowa lamarin. Matsalar da tafi damunsa
tun auransu 'barinta uku kenan, yana lura da
sakacinta wajan yin sallah kan lokaci inyai
magana sai ta hau fushi da 'kun'kuni. Sai ya
ha'kura ya 'kyaleta amma da zarar da kwanta ya
kan lalla'ba yai mata adu'a.
**********
Mustapha na zaune a 'kofar makarantarsu bayan
antashi yara 'yan tahafiz sun soma zuwa. Kamar
daga sama wata sumammiyar mota ba'ka tai
parking a bakin TEEMAH COOL SHOPPING,
katafaran kanti saida kayan 'kwalam da
ma'kulashe. Bai damu da lura da irin wannanba
amma haka nan ya samu zuciyarsa da san ganin
na cikin motar. Gabansa ya tsananta fad'uwa
yana jin wani irin abu mai nauyi a 'kirjinsa. Cikin
dog on wando jeans ta fito yai matu'kar kamata
sai wata half best fara tas kanta yasha 'karin
gashi. Cikin jin tsanarta yake Allah wadarai
da'it. Saidai me ? Hantar cikinsa tai mugun
kad'awa lokacin da ya had'a ido da'ita. Ya
murza idanuwansa sossai, tabbas itace meya
kawota nan? Kayan jikintama zahiri dasu ya
barota gida. Karaf idonsa yakai kan na kusa
da'ita fuskar tamkar ya santa amma tunani yake
ina ya santa?.kafin ya gama d'ibar tashin
hankalin daya kwasa har sungama sun fito
sunzo giftashi ta sakar masa murmushi ta d'aga
masa hannu.
Cikin tsananin tashin hankali ya nufi gidan da
yake tazararsu babu yawa nan da nan ya isa
gida. Gab da zai shiga gida wani yaro yai masa
salama ya basji takarda kan yai magana yaron
ya gudu. Da sauri zuciyarsa ke azalzalarsa ya
bude takardar yana bud'ewa gabansa yai mugun
fad'uwa.
"MATARKA TA ZUBDA CIKINTA" wasu 'kwalan
tashin hankaline suka zobo masa.
Yana shiga Farida ya samu cikin rad'a yace
mata "yau Auntynki ta fita?" Kai ta girgiza ,"a'a
tunsafe tana kwance wai cikinta ke ciwo". Da
azama ya 'karasa turus yai lokacin dayai arba da
manyan ledojin TEEMAH COOL SHOP. Cikin
masifa ya 'kwalawa Farida kira jiki na rawa ta
taho cikin hargowa yace "kikace bata fita ba
wannan fa?". A tsorace takaiwa kayan kallo
tabbas kayan shopping ne to waya kawo cikin
tsoro tace " walahi bata fitaba yaya "A zafaffe
yace "jeki". Jikinta na rawa ta koma ta cigaba
da aikinta.
Dai-dai lokacin Najwa ta farka cikin wata
giggitaciyar 'kara tana dafe kanta. Ga
mamakinsa jini ke bin 'kafaffunta cikin kallon
tsana Mustapha ya soma kallonta yana zagaye
zagaye d'akin Najwa a tsorace ta soma ja da
baya tana mamakin sauyawar Mustapha.
Ku dakaceni ya tabbata Najwa ce a mota?
Shin menene makomar auransu? Shin cikin ya
zubene? Ya batun Inna? Shin ina Auran Farida
da Abdul? Mustapha na sakin Najwa?.
'KADDARARMU CE!
SANAH S MATAZU.
18-19.
Cikin tsananin zafin rai ya soma nunata da
yatsa" Najwa kin cutar dani kin zalunceni, bazan
yafe miki ba". Kuka ya ci 'karfinsu su duka cikin
rauni murya tace "Mustapha menai maka? Meye
laifina? Kaimun bayani yadda zangane ka
sanyani cikin duhu". Takaici ya kashe Mustapha
abu guda ya fad'o masa bayan yawace-yawace
tana kora 'kwayoyi banda haka kanmi zata raina
mashi wayau. Kawai sakai yai ya bargidan
bayan ya gargadi Farida karta fadawa Mama.
Cikin sanyin jiki Najwa ta tashi ta gyara jikinta.
Shayi me kauri taso had'awa idonta yakai kan
TEEMAH COOL SHOP cikin hanzari ta bud'esu
ta d'auki kaza guda da nono ta hau ci duk
zatanta Mustapha ya ajiyesu.
Haka zamansu ya sauya salo kwata - kwata
babu jituwa makwancin kowa daban amma basu
bari a fuskanta ko a magana bale a fuska sai
isu-isu.
**********
Jikin Inna saisan barka,kullum samun cigaba
akeyi. Cikin 'kan'kanin lokaci Mustapha ya rame
yayi duhu, kullum yanayin da zaiga Najwa
daban. Najwa zamansu baya damunta koda
wasa tamafi sakewa a ganinta takurata yake.
Koda Husnah tazo ta kawo mata ankon bikinta
bata wani fuskanci akwai matsalaba hakama
Yaya Zainab da su Saudaht da sukazo. Ganin
babu sarki sai Allah Mustapha ya nemi shiri
suka dawo normal. Saidai kuma me? A duk
lokacin da yau Yuan',kurin kusantar Najwa wani
zafi ke fitowa ajikinta kamar tururin oven na
bread. Hankalinsa yai matu'kar tashi sossai
yanaji yana gani saidai yaita fama da ciwan ciki.
Yauma kamar kullum kwaliya tai cikin dogon
wando three quarter jeans yai mata kyau blue.
Rigarta pink kanta yasha gyara sai kamshi
takeyi abin sha'awa. Cike da kulawa suke hira
harya fita taimasa rakiya. Tana dawowa ta
ma'kala eirpiece tanaji a haka tai bacci kai
abud'e. Tana kwanciya ASHIQ yai muguwar
dariya ya soma zagayata.
**********
Mustapha yana isa makaranta principle ta bashi
takarda shaidar neman aiki da wata makaranta
ta nemi yaiwa d'alibanta horo na wata uku. Can
zoo road zaije yakai sa'kon, dan haka yad'auki
machine d'in abokinsa ya tafi. 'Karfe d'aya da
rabi dai-dai yazo kan hanyar titin gyad'i gyad'i
zai biya wajan wani abokinsa kamar ance kali
can gabasan yai mugun fad'uwa. Najwa ya
hango tana tuka mota sabuwa dal 'kirar korolla.
Gefanta wani kyakkyawan saurayine suna had'a
ido ta kashe masa ido ta 'kara wuta.
Mustapha a million ya rufa mata baya amma bai
risketa ba 'karshema fad'uwa yai har yai
targad'e. Ko gurin mai gyara baijeba ya nufo
gida a zafaffe ya shigo gida abin mamaki tana
kwance tana bacci. Ko kayan karinsu bata
kwasheba ga eirpiace a kunnuwanta. Take
jikinsa ya mutu

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment