Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ya wurgeta dashi ,kana ya daka mata wani irin mugun tsawa "leave my room ,dirty girl" da gudu ta fita har tana tuntuɓe da ƙafar umma

Tana fita kuma yayi kwaɓa² da fuska kamar zai saka kuka ,ba wannan rude person ɗin ba "Ummy plzzzzz...ki daina barin yaran nan na shigo mun ɗaki Allah kallona suke nikuma banaso gaskiya"
Murmushi tayi cike da jin daɗi a kullum tana godewa Allah daya bata yaro kamili wanda ruɗin duniya da kuɗi da ƙarfin sha'awa baisa ya zame ba .
"Kana gautsi ne Habiby ina laifinta don ta kawo abinci?"
"Ummy shiyasa nakkeso ki barmun if I'm starve ,zan nema da Kaina"
Shiru ta masa ta fara serving ɗin sa tana ƙoƙarin saƙo masa zancen yarinyar sister ɗin ta da takeson ta haɗa su ,amma wani ɗaci yayi yina shan magani yina hura hanci ,sam yaƙi barin suyi maganar,dole ta ƙyalesa ta fice

3.30
Ina kwance ina barcin Asara,zee tazo ta ɗaka mun duka a ɗuwawu da littafin hannunta ,a furgice na farka gamida ɗaurawa da masifa "wani baƙar dagar ce kuma ?"
"Malama sai ki tashi ki sallah mu wuce tutorial " Jan tsaki nayi na juyar dakai na maka a pillow na miƙa hannuna zan sake jan bargo ,hannu tasa ta funcike

"Kitashi mana kina ɓatamun lokaci"
"Waii meye haka tare aka kawo mu makaranta ne dake? To bazani ba "

Jijjigani ta cigaba dayi ,don dole na tashi ina ƙunƙuni saboda ta gama wartsakar dani ya rigada ya gudu ,ji nayi kamar in shaƙeta ,haka na ɗauki buta nayi tap Ina jan mata Allah ya isa.

Ina idar da sallah muka tafi cikin asibiti ,inda ya fi zama quite muka nema gaban office ɗin doctor jabeer ,nan muka sama wata dogon benci muka zauna muka ar ajiye littafanmu zamu fara karatu

Kamar an mintsineni. Na kalli zee "roomy nan ne office ɗin da ake bada labarin en ajinmu na zuwa ko?" Ɗaga mun kai tayi alamar "Eh"

"Wai me sukeyi a ciki?"
Kallon windown tayi don ta tabbatar ko ba kowa a ciki kafin tace "kin fi kowa sanin me zasuyi a ciki mana en iska ne fa "

Caɓe fuska nayi cikin alamun rashin fahimta "wallahi ban ganeba me sukeyi ,wai iskanci sukeyi da wainnan zaftara zaftaran mazan ,musamman akwai wani acikin su naji ana kiransa doctor jabeer duk a cikin likitocin asibitin nan rankatakaf nafi tsanansa shege mai gemun fir'auna kiga gemu tsuiii kamar na bunsuru ba gemun Allah bane na Iskancine"

Duddulo ido waje tayi "Ke nadiya gaban office ɗin su ne fa in suna ciki fa ?"

"To Ni ina ruwana iya gaskiya na na faɗa Ubangiji ya haɗa su da cutar...." Ɗifff na ɗauke wuta ,bakina a buɗe na kasa rufewa saboda Turo ƙofar da akayi aka fito ,Zuwa yayi ya wuce mu yina babbanka muna harara aikuwa muka haɗe kai muka kwashe da dariya maimakon muyi laasar ,sannan ba kunya muka buɗe littafanmu muka fara karatu ,kamar karatun jarida nike karatuna daganan sai in Mana bayani ammafa in yazama bayanin zee yaci karo da nawa haka zan kafe alankatafir nike kan daidai ,sai ta sauke murya ta ce "Nadiya baki zuwa aji nifa malam yace mana haka ke kuma ra'ayinki kika fada ,nawa zan ɗauka naki ko na professor?" Sai ince "shikenan kowa ya riƙe fahimtar sa" sai mu je na gaba

Adams dake office Amma Gardama na ya hana masa sukuni ne ya leƙo da nufin yaroƙemu mu rage murya ,saidai daƙyar ya haɗiye miyaun bakinsa ,tunowa da fuskata ce wacce ta bubbuga masa bamban mota tana tsiya securitai sun taso mu ,jinjina lamarin yayi a ransa "wannan ne Nurse ? Gata ƙazama ,ga bala'i ga gardama? Ga gulma (saboda ya ɗauki muryarta ita ne yanzu ta gama munafurcin Dr jabeer) Gaskiya in tanajin haushinka ,wannan wannan dai ma zata iya kasheka wannan dai?"

Tun sanda ya fito na ankare da fitowarsa a raina nace to ga wasu masu ɓata yaran jama'an nan

Zee nacan na karatunta nikuwa na shuga gyara baki zanyi tsiya saida na hararesa tukum na murguɗa masa baki kana na daura da masifa "maye nadai fi ƙarfin mutum namana ɗaci garai in mutum ya tauna mutuwa zaiyi ,bar ganinmu anan ba ƴan iskan bane da kuka saba kawowa aha" ɗagowa zee tayi ,cikin mamaki

"Au Dama nadiya dakikayi shiru ba saurarana kikeyi ba neman tsiwa kikeyi?...sorry sir ba...ta..." Bakinta ne ya kama rawa saboda ganin wani haɗaɗɗen handsome guy ya kafeta da ido ƙwaran cikin idonsa har yina mata zaiba zaiban shining blue
Gaba ɗaya birkicewa tayi shikuma gabaɗayansu kallon hadarin kaji ya bisu dashi lokaci ɗaya yaji a duniya ba halittar da ya tsana sama da watannan lutuwar yarinyar da yaji an kirata da Nadiya ,wucewa office ɗin yayi ya sama waje ya zauna kansa tuni ya fara masa ciwo saboda hayaniyarta
Ƙunƙunai ya shigayi a ransa "gata wargajejiya ,maimakon ki tattalin ƙibanki ki zama calm ko Allah yasa maza su tausaya maki su aureki badon muninki ba ,don ina kai ɗan ƙwalisa ina auran ƙatuwa,ta shige gaban mota a gurin taro ta sattar maka da tayoyin mota ?

Nikuwa nace zuƙiiii ,na gaisheka da ƙarya malam Adams ,saikace Nadiyar giwace ? Kodai duk tsanar ce?

Nadiya kam bushewa da dariya tayi ta ɗakawa cinyar zee duka "wayyo Allah zee tayi gamo da ɗan Aljani,ke don Allah bai baki tsoro ba ,anya bazamu guduba,wannan dai badai mutum ba ji kyau don Allah? Tsiya nike masa amma zuciyana sai bugu yike abum..bum..bum,gashi mayen baice komai ba "

Zee lumshe Ido tayi a hankali saboda yanda yayi mata narai² zai zubo da ƙwalla ,a sanyaye tace "nadiya ba maye bane madaran kyaune ,wannan su ake kira da ɗaya a cikin birni,kawai tashi mu tafi don ƙila muka sake haɗe ido dashi suma zanyi"

Tsaki nadiya tayi "kinji sokuwa duk kin zama kalar tausayi ,to Ni Ko ifritun minan jinnine nafi ƙarfin ka ɗan larabawa " na buɗe murya da ƙarfi yanda zaisan dashi nikeyi musamman da na kirasa da ɗan larabawa ,don tunanina ya gama bani in ba Aljani bane to balarabe ne yayi shigan hausawa

Koni takaina batayiba ta shiga haɗa kan littafanmu ta rungumesu ta miƙe ,sakin baki nayi ina kallonta "Ina kuma zaki"

"Jikina ya mutu Nadiya ,wallahi basirata ya cushe billahi ko na zauna ba abunda zan ringa fahimta"

" kai amma ko irin mazan nan masifa ne,maganinsu a nemi gidan yari a kullesu ji kallo ɗaya ya birkita maki lissafi ? Kai ashhshato muje ,dama cikina ya fara salati yunwa nikeji"

Ji yayi kamar ya fashe da ihu bayan ya gama jiyo hiransu ,wai shi duk ajin da wainnan banzayen yaran da surutu kamar sun haɗiye aku zasu na admiring?? Tagumi ya rafka a haka Doctor Jabir yashigo ya tardashi


The payment is on going #500 mtn card,special 1000 via this 7782217014 , Mohammad Hassana, Fcmb or contact me direct 09065990265
[6/20, 11:25] 😘😘😘: *GIDAN DAƊI*
_(Duniya🌏)_


Oum Aphnan✍️

Free page
005


_Manyan mata azo ayi gyaran Aure ta hanyar Amfani da zafafan magungunan matan Hajja mai gyaran Aure ,indai gyara ne na ciki da waje bakida matsala ,zaki cike zaki tsamtsam ,zaki ta zuba kamar maliya ,miji na santi ,kar kuce na cikaku da surutu Hmm kayane humhum tested and guarantee 💯 Dm kya bada labari da kanki 08069946904 ,sai kunzo 💃_


_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._

I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 08066268951


Sunana Nadiya Mohammad Mu biyune a wajen Iyayenmu Ni da yayata Anty Nusaiba ,Babana Alhaji Mohammed Ahmed ɗan kwangilane kuma delegate ne na en siyasa a jam'iyya maici, a don haka Munada kuɗin rufin asiri a gidanmu , Mahaifiyata Nurse ce tanada asibitoci na kanta guda biyu ,mu en asalin garin gombene amma yanayin aiki ya kawo iyayena garin Abuja da zama ,Yayata ta girmeni da shekaru Huɗu amma ita ba mace bane mai ƙiba a taƙaicedai tabiyo jikin Babana na real fillo ,mahaifiyata kuwa ƙatotuwa ce kundai san Nurses' da manyan Ass,to Ni ita na biyo da ƙiban da komai ,gaskiya family enmu kyawawan gaskene dukkanmu ba mummuni ,saidai tsiyata da tonon tsiwa yasa ba'a ganin kyawuna a kullum tsinata akeyi ana cemun mummuna yaya Nusaiba ta fini kyau ,haka dai muka taso makaranta ɗaya mukeyi da Antyna ,nasha janyo faɗa ta shiganmun ai mata dukan tsiya ta dawo gida tana kuka ta tarar dani ina zaune a falo ina kallo ko cin abinci ,yaya Nusaiba tana wahala dani Ni nan shaidace amma bata taɓa ƙosawa daniba ,yarinyace mai tsananin haƙuri hakan yasa Iyayenmu suke sonta sosai ,wannan abu kuwa na ɓata mun rai .....Mun girma cikin kulawan Iyayenmu haka har yaya Nusaiba ta gama makarantar secondary ɗin ta,Babana ya neman mata medicine a sudan,sam yaya Nusaiba bata son hanyar likitanci ita tace Microbiology takeso Amma Babana ya hana wai mazan yanzu sai kana da abunyi ake kaika ɗakin miji ku zauna lafiya ,bata ja da tsayiba tabi umurnin iyayenmu ta tafi ta Barni,naci kuka na ƙoshi na rungumi rayuwa ta Ni kadai tun daga sannan rashin jina ya ƙara gaba bana karatu dama ada Anty Nusaiba ke matsamun yanzuko bata ,don haka wata zubin bana karatu sai night to exam,Babana shine ya sangartani yana kirana da mamana ... Uwata ,mamana kuwa ko nayi laifi bata mun dogon faɗa saboda Ni autace na gaban goshi ,kundai san Nurses' da azaban son yaransu tun Bama basu aihu da yawa ba .
Allah kaɗai yike cetona inada ƙwaƙwalwa inna burbura karatuna Inyi barci abunda na karanta ko tas suna kaina ina shiga exam na watsa masu na fito na manta ,a haka dai na kasance ƙinji tamkar namiji ,rashin Anty Nusaiba ,rashin zaman mamana a gida yasa na zama kasa Sarkin barci kullum ina barcin asara,sai cin abinci kamar jakka ,gashi duk masu aikin da aka kawo sai baƙin halina ya koresu don haka gidanmu ba mai aiki sai masu gadi ƙarfafan sojoji guda biyu,gidanmu akwai enci wannan dalilin yasa bansan meye kwaɓo ko tauna magana ba yanzu zan faɗa maka maganar da babban zai rike kai kamar yayi ihu ,a haka dai na gama secondary school ɗin a saidai naci waec na faɗi jamb ,nan kuwa na dawo gida na rashe na cigaba da tsula rashin m . Ban iya girka komai ba sai indomie


Lokacin da na zana jamb ɗina a shekaran Anty Nusaiba ta dawo 9ja da shaidar kammala degree ɗin ta a medicine ta fara inten ɗin ta anan Abuja
Sosai taga rashin jina yayi gaba don haka ta fara jana a jiki saidai Nikam ina nayi nesa

Anty Nusaiba tunda ta gama degree dinta ta fara tunanin yin aure saidai kowani saurayinta yazo nice nan mai kora mata su da baƙin halina ,abun yina damun Antyna amma ya zatayi dani.....?
Ni Nadiya ƙazamace Ni kaina na sani don akan wanka kullum sai munyi faɗa da Anty Nusaiba ,akan ɗakin kwana kullum sai munyi dambe don takance mai warin maza bazata kwana a ɗaki da itaba sai nayi wanka ,in tsiyan ya ishi Iyayenmu sai su roƙeni inje in wanka to sananne zanyi ,Abu ɗaya Anty Nusaiba ta mora girki, subhanallh duk cin abinci saita take table da abinci munci naci a fitar da ragowa, wannan yasa na liƙe mata tanayi inaci tun a wuta ,hakan yasa nasan yanda ake sarrafa abinci amma yiɗinne dai banayi kuma ko an sakani haka zanta kuka wai ai ga Anty Nusaiba nan

Don't think Ni yarinyace shekaruna Sha bakwai a duniya ,amma childhood characters suna wulwuli da rayuwata

Akwai wataranan Asabar ba aiki kowa yina gida tun safe yaya Nusaiba ta gama mana abinci ta shiga wanka ,ta fito tana ta en gayunta a gaban dressing mirror ,juyi nayi na wuce dinning na lafto chips da farfesun kaza ba brush nahau cusawa saida naci na ƙoshi nayi gyatsa sannan na haɗa tea mai kauri cikin cup ɗin who send you ,tamkar dai gejin cin abincin wani gardin shima haka na ɗaura da bread da butter ,warwas nayi akan kafet ɗin bedroom ɗin mu sanyin fanka na hurani saboda yanda zufa ke tsatsafo mun a duk gaɓɓan jikina to Ni abu ba kaɗanba ƙatuwa.

Anty Nusaiba raɓeni tazoyi gamida liƙe hanci ta ɗauko riga da wandon fakistan milk da maroon ta saka ɗauko mayafin kayan ta taho gaban mirror tana rolling ,pillow nayi da hannuna ina kallonta har ta gama shiryawa kana nace "To sai ina isashiyar kanta ,fita zakiyi da sassafen nan iyayenki na barci? To kina saka ƙafa kika fita a kunnen dady dama kin riƙa kin zama riƙaƙƙiyar kuɓewa anje an kaiki Sudan kin iskance " ɗaga hannu tayi ta make bakina

"Ke nice kike zagi nifa yanki ne" wani ihu na ƙwalla da ya tsorata Iyayenmu aiko sai gasu a guje "Lafiya ?"
"Mum...dady Anty Nusaiba Bata sona nace zan bita inda zata wai bazata daniba wai Ni ƙazamace bla...bla"

Juyowa mamana tayi ta kalli Nusaiba "wai ke me yasa bakida hali keda yar uwan taki ma ?" Shiru kawai ya Nusaiba tayi ta girgiza kai batace komai ba inaji anata mata faɗa haka kuma duk sai naji ta bani tausayi ,ƙarshe akace in shirya in bita sai sannan tace "Dady plz kace tayi wanka da brush to ,don wallahi a haka zatace zata bini kuma wari takeyi "

Harara na banka mata "Kin haɗiya reza a gicciye nice zanyi wanka a sanyin nan ? Bazata saɓuba"

"To mumy kinjiko ,nikuma in har da ƙazanta zata bini ina likita gwara in haƙura na fasa siyan cosmetics ɗin"

Yafitoni Dadyna yayi ,nakuwa shagwargwaɓe naje na haye cinyarsa ,shafa kalbar kitsona da tsagon suka haɗe saboda daɗewa ba kitso yayi yina mun magana cikin rarrashi

"Mamana ai kinajin yawo ko?" Ɗaga masa kai nayi da sauri
"To maza nadyn dady aje ayi wanka kar Anty ta fasa fitan"
"Kambu to sai kuma dady ka ƙyaleta ? Ai dole taje ko?" Murmushi yayi "ƙwarai kuwa tunda kema wankan zakiyi "
"Eh nadaiji " hakana dai na tafi naje na rage datti wankan 2mns badon na fita ba ,ina fitowa naga iyayen namu sun fita sai ita dake zaune akan stool ta ɗaura jakarta dazata fita dashi akan cinya tana chart da wayarta ,tsaki naja naje na ɗauko Vaseline ɗina na shashafa fuskana caɗai kamar ɗanwake ,itadai sai bina da ido take ,saida naje na hangame kwabana ina lalubo wasu cukurkuɗaɗɗun kaya marasa guga kafin ta maza tace "Ga kayan na ciro maki my love"

Kallon banza na wulla mata "Anty banason saka wandon jeans ƙaiƙayi yikemun baki ganina ƙatuwace ?"

"Amma inkinsa yina maki kyau don kina fina kyau Ni bakiga kayan larabawa na sakaba,Ni basamun kyau" caɓe baki nayi "Kumafa haka ne kece ya Nusaiba akwai rama ga muni,to zuciya ba hali,Ni ban insa " itadai murmushi tayi wai itace nadiya take kiranta da mummuna yarinyar da a Sudan sajewa takeyi da en ƙasan har kalan skin ɗinsu ɗaya wai itace mummuna? Wayo tai mun ta lallaɓani nasan marasa squeezing tamun rolling nan kuwa cikina yayi tuiii a waje ga manyan ass ,inda zaka gane ba wata babba bace shine Banda cikan ƙirji kuma fuskata kwaɓa² yike irin na shafwaɓaɓɓun yara ,ipad ɗina na ɗauka mara sim don Banda mai kirana na saka cambas irin na zuwa ball na fito na wuce car na tsaya ina jiranta

Ɗakin mumy ta shiga amsar makullin mota,suna liƙe suna hira kamar wasu Romeo ba masu manyan en mata ba,A sannan ne take bata haƙuri tana ƙara nuna mata niɗin dai eruwarta ne tana haƙuri dani

"Shikenan mumy amma dai in kun sama lokaci a kaita Psychiatric hospital taga likitan ƙwalwa ke likitane kinsan alamomin hauka ,kuma Nady ta ɗebi kaso da dama " babanmu dake gefene ya kwashe da dariya "Lallai Nusaiba kin tsorata da lamarin er uwarki "

*****
A mota ƙira'ar sudais tasa har suka isa Suhash shopping mall ,nan tayi parking suka fito ,tana tafe tana mata nasiha kar tayi tsiya da kowa ,aiko bata rufe bakiba wata mata tazo wucewa da ɗan ta riƙe da ice cream yaron bai wuce 7 years ba ,cikin rashin kula irin na yaro ya bangaji cikinta ya kuwa sheƙa mata ice cream a takalmi ,wayyo Ji kake ɗauuuuuuuu ta yanka ma yaron mari mai tsananin zafi a take yaron ya gigice ,ya fasa ihu ,aiko uwarsa ta juyo da sauri ta rungume ɗan ta tana kallon nadiya dake hura hanci tana masifa ya ɓata mata takalmi

"Haba en mata bakisan yaro ba"

"Yaci kazan ubansa shi yaron ,nima ai yarinyar ce ,kece dai baki bawa ɗanki tarbiyya ba"

"Shikenan keda iyayenki suka baki tarbiyya cigaba da faɗa da ƙaramin yaro ..." Da sauri ta katse ta

"Ahhhh karki zageni wallahi Ni pepper ne yanzu zan kwaɓe muyi dambe in kinfi ƙarfina shikenan sai in kuka ina share hawaye"

Nusaiba takai ta dawo ta rasa yanda zatayi haƙuri take ba matar in matar nikuma tana mun faɗa,kawai sai na fashe mata da kuka wai tafison bare a kaina .

Wani Chubby guy ne ya tako a hankali cikin ƙwalisarsa ya matso inda muke so yike ya janyeni ta baya amma ina na aza anty Nusaiba ce ba zato ba sakan masa one blow a baki da sauri ya riƙe bakinsa yina nanata "Ah....ah....ah" ruɗewa Nusaiba ta ƙarayi ,dasauri takai gwuiwonta ƙasa "Man Plz sorry she's young " zare hannunsa yayi a saman bakinsa

Ya sa hannu ya ɗago ta ,maye gurbin mamakinsa yayi da wani irin lafiyayyen murmushi mai tsadan gaske "Karki damu ƙuruciya ke damunta jiba da ta nausheni ma ta gudu" waigawa tayi nankuwa taga na ɓace ,can ta hangoni wajen kayan chocolate na maƙale Ina leƙe

Girgiza kai tayi cikin takaici ,shikuwa sai dariya yike yi "kayi haƙuri kaji "

"Ƙanwatace ain't vex? Muje ki zaɓi abinda zaki siya joooor "

Ɗan murmushine ya ƙwace ma Nusaiba ,lallai guy ɗin is so friendly tasata yayi suka wuce wajen turaruka

Nikuwa taune yatsa nayi "shegiya Anty Nusaiba anga kyakyawar namiji sai rawar kai akeyi ,to baidaice yina sonta ba kuma bari inje masu"

09065990265
Wxp only plz🙏🏻
[6/20, 11:26] 😘😘😘: *GIDAN DAƊI*
_(Duniya)_

Oum Aphnan✍️

Free page
007


Tun daga parking lot nake ƙwalla mata kira har cikin gida ,da ƙarfi na hankaɗa ƙofar na shiga tana kwance ta ƙanƙame pillow tana shan love ,a tsorace ta miƙe zaune tana maida gashin kanta daya wargaje saboda kwanciya
"Nadiya why are you banging the door like that,are you mad "
Dafe kaina nayi na koma na jingina a jikin ƙofa ina lalubo video ɗin da na ma ya Hisham "Come and see ,come nowww?!" Ƙur ta mun da ido bata da niyyar miƙewa
"Come on ! Kizo ki gani mana"
"Hello!" Ta ɗan kira attention ɗina ɗagowa nayi na kalleta "Who is your senior sister,who age who?" Turo baki nayi ,da har nayi zuciya zan tafi ganin interest ɗina ne yasa na dawo nabita kan gadon na miƙa mata "watch your naked evil" a tsorace ta karɓa Saidai wani ƙara ta fashe dashi da sauri na rufe mata baki da hannuna "Malamansu momy is around ,she may definitely need to dig the true ,to shawara ya rage naki me kike gani zaki fasa auransa ne ko zaki auri mayaudari ɗan iska mai rungume mata a titi"

Kwantawa tayi akan pillow wasu kyawawan hawaye suna layi a kuncinta "Dole zan fasa auren Hisham ,Nagode ƙanwata"
Rungumeta nayi "Da kyau" na bata amsa na wuce bathroom Ina bouncing kamar wacce tayi abun arziƙi

****
32hours Later

Muna zaune a ɗakinmu Ni ina game a laptop ɗina Anty Nusaiba tana chating a wayarta fuskarta a murtuke ,Hisham ya kira wayarta yafi sau ba Adadi taƙi ɗagawa,a hankali momy ta Turo ƙofar ɗakin ,da sallamata saidai ba wanda ya amsa ta
Kewayowa gefen bed ɗin tayi daidai an sake kiran wayarta ,direct Anty Nusaiba ta nufa ta miƙa ma wayar "Amshi Hisham yace yina kiran wayarki bako ɗagawa"
Da muryarta adashe kamar wacce tayi kuka tace "ok mom kije zan kira shi da wayana"
"Oh no pick up" a hankali ta ɗauki wayar ,batayi magana ba na ɗan lokaci Saida yace salamu Alaikum ,kafin tace "hello"
Ta bangaren Hisham ya zarce da cewa "Sweetheart how are you I've been wondering what happen to my blossom..." Da sauri ta katsesa da
"Oh sorry I will call you later" kafin yayi wani magana ta datse kiran ta mika ma momyn wayan

Karɓa tayi tana jujjuyawa tana saka abubuwa a ranta "me ke damunki?" A takaice ta amsa da ba komai
"Ok me ya hanaki magana da Hisham"
"Haba momy ki ƙyaleta mana may be she is not in the mood tayi magana ne" na karɓe maganar da sauri ina wani tattare gira

"Yi mun shiru dake nake magana ehen,ko kece mouthpiece ɗin ta"
Danna wayar nayi na nuna mata wayana "to kalli nan" wani shock tayi amma da sauri tayi maintaining kanta
"Oh really? Nusaiba zo muje" ta faɗa tana kamo hannunta
"Momy go where now,kuyi maganar anan mana "
Kallona tayi ta bankaɗa mun harara "kece big informant banso kiji,na gaji da rabata da masoyanta da kikeyi wannan bazaki yi nasara ba..." Shiru tayi saboda Dady da ya Turo ƙofar
"Ohoo haɗe mun kai zakuyi? So kuke ku nuna mun nine kaɗai namiji a gidan ,zan ƙaro wata ,gaskiya zan ƙaro mai tayani hira"
Dukda momy tasan wasa yike bai hanata tankawa ba "Come on,daga naxo ganin lafiyarsu ...kawai ma dai muje" ta tasa ƙeyarsa suka fice ,Ni kam dariya na saki abuna rai fes ,itakuwa Anty Nusaiba taɓe fuska tayi ta juya ta kwanta ,ta rarumo wayarta ,a hankali na miƙe tsaye ,ina nanata mata "karki yarda ki ɗauki wayarsa kinji ,You guys should break up!"

*****
Muna zaune a dinning muna lunch mu ukune ,still Kiran wayar Anty Nusaiba ya damemu ,duk dauriyar momy saida ta magantu
"Haba pick nah" na saka fork Ina ƙaƙarin gutsuran kaza kenan nayi saurin cewa "momy its ya Hisham fa,Anty karki ɗauka"
Muzurai momy ta mun kana ta sanyaya muryarta "Nusaiba ɗauki wayar mana" a zafafe na cusa naman a bakina na soma magana yagau yagau "Yawwa ɗauka ki ci masa You locked the relationship with him ,ya aiko a amsan masa kayan baikonsa...."
Harara momy ta kwasa mun
"Nadiya Inaso inga young man ɗin da zai zo auranki" caɓe baki nayi na magantu ciki ² "Aiko ba rana bare wata"
"Me kika ce?" Da ƙarfi nai magana ina ɗan bubbuga kai "Ahhh bance komai ba " kallon banza tayi mun "ohooo bakomai ?" Gyada mata kai nayi "gwara ya zama bakoman "ta faɗa ranta a ɗan ɓace ,saboda taji zafin mugun alkaba'in da nikewa kaina "momy sorry it joke"
"Gwara ya zama ba'an Nadiya "
Daidai nan ya sake Kiran wayar
"Oya ɗauka in ga gari"
Dakan dinning table ɗin nayi a zafafe nace "yawwa ɗauka ki faɗa masa bazaki iya ba kuma, wedding is cancelled ,baki yi kawai period"
"Kinajina bazan ce maki lallae ki auresa dole ba ,kawai abunda nikeso shine ki ɗauki
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On GIDAN DADI
avatar
surayya-5

9 months ago

Reply

I love ur novels sis

avatar
khadija-3-1

6 months ago

Reply

Mash Allah yayi

Please Login or Register in order to submit comment