Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ο»Ώ*_maman Al-ameen CE_* πŸ‘ŒπŸ‘ŒπŸ‘Œ
*INDO BALA'I*

πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€



_bismillahirrahmanirraheem,ina rokon Allah yabani ikon farawa cikin sa'a nakuma gama cikin sa'a,ameen_





Page 1/2

*_Na Maman Al-ameen momcy_*



Tafe take tana tsalle tana waka tana cilla ledar dake hanunta,wani gida ne ginin laka naga tashiga ko sallama babu tahau kwala kira


Inna! inna!! inna!!!


Wata yar dattijuwace tafuto daga wani daki tana kai indo kekam bansan sanda zakiyi hankaliba ko sallama babu sai kwalamun kira kk to ina aikan danamiki


Turo baki tayi tace gashichan

Inna tace to maza sai kitashi kije kidibo ruwa ko,kai inna dan Allah daga dawowa ta daga kasuwa ko hutawafa banyiba,

Inna tace to ahikenan inbaki dibo ruwanba naga da abunda za'a dafa abincin kici

Tana turo baki tadauki bokiti tafuta

Wasu yarane su biyo suna tafiya da alama aika suka futo da kwano akansu,amma ban hango meye acikiba,

Daya daga cikin yaranne yace laaa hasan kaga INDO bala'i tafuto ,dayan yace laa wlhy itace kai mutsokaneta mu gudu,
Aikuwa sukabi ta suna sanda itakuwa tafiya takeyi sam bata lura dasuba saiji tayi sunce INDO bala'i suka ruga aguje ai aje bokitin tayi tabisu dagudu tayi nasarar kama daya Wanda shine me kwano akansa kyawawan Marika tabashi tareda buga masa naushi abakinsa tsabar azaba saida yasake kwanon dake kansa yafadi kasa ananne nayi nasarar ganin abunda ke ciki garine ciki da alama nika suka karbo aikuwa yakife acikin lallausan kasar garin ga baki yafashe sai jini yake ,

Dukda haka batasakeshi cewa take ayo nisa arkace ko yau sai kasan uwar datasa ka tsokaneni ehee Dada wanka masa mari tayi yafara bata hakuri dakyar muryarsa take futa tsabar azaba


Wani mutumine yazo wucewa yaga yadda INDO ke sanbadan yaro yanufota dakyar yakwace yaron ahanun INDO tareda tambayar meyamata ,cikin huci INDO tace katambayeshi mnh,kallon yaron yayi yace mekamata cikin kuka yaron yace wai dan muncemata INDO bala'i

Hantsilowa INDO tayi zata kara kai masa duka mutumin ya tareta tana cewa oh sake maimaitawa kayi ko,

Hakuri mutumin yadinga bata dakyar tahakura tadauki bokitinta tayi gaba,

Dazumar d'ayan ma sai tabishi ta dakashi

>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *tushen labari*




Mallam bala shine asalin mahaifin INDO Wanda suke zaune akauyen tsamiya su biyo mahaifinsu yahaifesu,shida kaninsa suntashi cikin gata dukda bawani hali sukedashiba sai rufib asiri babansu dankasuwane yana zuwa birni yasaro yazo kauye yasayar ahaka har ciwon ajali takamashi yarasu ,bala da kaninsa aminu mahaifiyarsu na kula dasu sosai dukansu suna makaranta arabi da boko dake kauyen bala shiya rike kasuwancin babansu suna samun naci Dana makaranta kasancewar yakai matsayin samartaka, shi kuma aminu baya zuwa kasuwar ,lokacinda aminu yagama secondary yanemi yayanshi yaturashi birni yakaro karatu shi kuma dama tunda yagama becigababa yamaida ahankali kan kasuwancinsa,haka kuwa akayi yatura kaninsa aminu birni dan karatun jami'a

Bayan tafiyar aminu birni yayansa bala yahadu da harira suka kulla soyayya ba jumawa sukayi aure amma tinda suka yi aure harira ba labarin haihuwa ko bari bata tabayiba


Shikuma aminu yana chan birni sai karatu yake harya kammala degree na daya yashiga tabiyu




Harira tana kulada gwoggwo wato surukarta mahaifiyarsu bala


Bayan aminu yagama degree dinshi ta biyu yadawo gida kafun aiki ya samu ,sosai matar wansa ke kula dashi shima kuma yana darajata sosai,

********************
Bayan shekara biyu aminu yadibi takardunsa yatafi birni Neman aiki ,cikin ikon Allah yasamu aiki awani company ,yakanje gida duk weekend ahaka yana samun kudi yana ajiyewa haryatara na fili yasaya yayi gida, bayan anbashi manager a companyn,yahadu da dawa ta yar babban mutum acikin garin kano,sukayi aure ,bayan auren su dashekara daya ta haihu namiji akasamasa sultan ,

Bayan aihuwar sultan da shekara daya matar bala wan aminu tarasu,bayan rasuwarta da kamar bazai sake aureba daga baya yahaduda hadiza ya aura ,itama saida tayi shekara shida Allah yabata aihuwa ta haifi diya mace akasamata Aisha taci sunan mahaifiyarsu suke kiranta da INDO


Ba yanda aminu beyiba kan yayansa yayarda yakoma kano kasancewar gdnsa babbane kuma part biyu ne aciki manya manya ga boys quarters dayayi abangare dabn ,Sam bala yaki yarda yakoma kano, acewarsa yafison mahaifarsa da kasuwancinsa akauyensu,



Lokacin sultan na yaro yakanje kauye amma tinda yagama primary yakoma waje da karatu,achan yakammala karatunsa tindaga secondary har degree dinshi,



Lokacin kuma INDO anshiga primary ,tanada shekara goma sha biyu tana primary 4,kasancewar ba asata da wuriba,


Amakaranta INDO batabarin kowai indai aka tsokaneta zata rama bata barin ta kwana gashi Allah yayita da karfi,harda maza buguwa take,saidai kuma Allah ya zuba mata kwakwalwa ,mallam ai sunaji da ita saboda kokarinta amma akan fadarta suke batawa,


Mahaifiyar sultan Wanda yakekiranta da mami tasake aihuwa ta haifi shukhra Wanda kusan sa oi ne da INDO


*******************cigaban labarin....

_Kubiyoni_



*INDO BALA'I*
πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€


Page3⃣~~4⃣



_na maman Al-ameen momcy_





Indoce zaune tanashan kunu da kosai nakaryawa inna tafuto daga daki tace yanzu INDO har yanzu baki gama shan kokonnanba so kike ki makara ko,turo baki tayi tace to inna ba yanzu zangamaba,

Wucewa inna tayi tacigaba da aikinta dantasan da takara magana yanzu gwoggwo daga daki zata amsa antaba mata mesunanta ,

Zainabce kawar INDO Wanda ake kiranta da *Abu* tashigo itama da shirinta na namakaranta ,chab INDO bakima gama shiryawaba kinsanfa muna jarabawar chanja ajinefa gskya ki aje kokonnan mutafi karmu makara,

INDO tace toke banda abunki akwai mallamin da ya isa yahanani shiga jarabawa ne inda kijirani nakarasa kijirani ,zama Abu tayi tace to kiyi sauri,saida tashanye kafun tatashi suka tafi asoron gidan suka hadu da baba ,yace ah uwata har anfuto ,INDO tace eh baba Abu tagaida baba,baba yaciro kudi yace toga muttala ayi tara,INDO takarba da murnanta tana yiwa baba godiya suka futa,ai kuwa suna isa makaranta suka samu har anshiga jarabawa,da confidence dinta tawuce aji Abu nabinta abaya itadai tana dan tsoron,saboda tasan sunyi latti,

Mallam idine yace ke INDO daga ina kuke sai yanzu kuke zuwa makaranta bacin kunsan kuna jarabawa,hawayen karya INDO ta kirkiro tana matse ido ,wlhy innatace ba lafiya shine natsaya nayi aiki kumama.....kwai sai tafashe da kuka kamar dagaske ,mallam idi yaji tausayinta yace kiyi shiru Allah yabata lpy sai kuyi sauri kurubuta dan ankusa abuga,


Ai dasauri INDO tayi cikin aji Abu tabi bayanta suka fara jarabawar ba wuya suka gama sukayi submitting suka futa dayake daya zasuyi kowa yagama gida zaitafi ,

Suna futowa INDO tace Abu muje gonar mallam lado musaci masara,

Abu tace kai INDO bakyajin tsoro kinsan fa sai yakai kararmu wurin megari ,INDO tace da Allah ja ke kinada matsala towaye me tsoron megari da Allah mallam indaki kizo muje,haka Abu tabuta sai gonar mallam lado,masarar da tayi da wacce batayiba haka sukayita balla insun bude sukaga batayiba sai su jefar ,aikuwa sun acikin haka saiga lado yanufo gonarsa suna ganin haka suka aune dagudu damasararsu ahanu kowa ta rike nata ,binsu yayi amma yakasa cinmisu kasancewar ya dan tsufa bashida karfin binsu ,haka yadawo cikin gonarsa yaga irin barnan dasukamishi,

Ai mallam lado beyi wata wataba yabi bayan su dan yagane yaran dama bayau suka fara masa barnaba ,inyakai kara iyayensu suce ayi hakuri,

Gidan megari yanufa yaje yakora masa bayanin abunda su INDO yar mallam bala suka masa

Megari yatura akirawo iyayensu ,mallam balane zaune da buta ahanunshi yana alwala gwaggwo kuma nagefen dakinta ta shinfida taburma tanadan shan hantsi,

Sallama akayi baba ya amsa yakara sa alwalarshi kafun yafuta ,tinda yaga dan aiken megari yasan INDO tayi wani abunne,dan aike yace dama megari yace anasan ganinka,
Mallam bala yace to bari tashiga nafuto sai muje ko,

Yana shigowa gwoggwo taga fuskarsa ta chanja tace uhmm ai nasan ba kalauba yauma sharrin aka kumayi wa jikata ko,ai tana ganin baba yafuta itama tadauki mayafinta tayi hanyar waje ,dan Aiken takalla tace tofa daga ina? baba bece komaiba ,dan aike yace megari ne yace akirashi ,tace injidai lapiya ?yace aa dama mallam ladone yakai karar yar gidannan INDO sunyimasa barna agon.....ai kafun yakarasa gwoggwo ta haushi da masifa oh mukam munshiga uku eh jikata ita kadai ke laifi agarinnan ko to bazai yiwuba muje wajen megarin tama rigasu baba yin gaba sai surutai takeyi ita ala anyiwa yar jikanta INDO sharri,



Suna isa megari yakora musu bayani akan laifin da yarsu tayi,baba yana kokarin bawa mallam lado hakuri gwoggwo tace ai ba maganar bada hakuri ni banyarda INDO tashiga masa gonaba ,to mema zatayi da masararsa yarinyar data tafi makaranta mezai kaita gona tatashi tatafi tanata masifa ita antaba jikanta,baba kam hakuri yabawa mallam lado tare da bashi wani Abu yarage asara,



Su INDO kam gidansu Abu sukayi suka gasa masararsu suka Nada acikin su kasancewar innar Abu bata gida,




Saida suka cinye sukasha ruwa suka futo ,aikuwa suna futowa INDO taga yaron daya tsokaneta ranan aiwuf ta chafke yaro tahau tilansa ,saida damasa na jaki tabarsa suna shigowa gidansu baba yana tsakar gida inna kuwa tana kicin tana aikinta duk bonbomin gwoggwo batacemata kalaba ,

Suna shigowa baba yace zonan ,yanda taga baba ya bata rai tasan cewa lado yakawo kararsu gida,dukawa sukayi kusa da baba ,yace daga ina kuke yanzu INDO tace baba daga makaranta muke bata auneba taji saukar mari baba yadaka mata sawa daga ina kuke tatsala uban ihu saida gwoggwo taji daga daki aikuwa tafuto,

Tana masifar wayataba INDO, dasauri taje taja INDO agaban baba tana masifa me tayi masa baba bece komaiba yatashi yayi waje,


*********

Sultan ne zaune a falon sa shukrah tashigo yaya wai kazo inji dady,juyowa yayi ya harareta ke baki iya sallama bako,

Tace yi hakuri yaya,yace to wuce kice ina zuwa,

Bayan shukhrah tafuta yadauki wayarsa yazo kiran da dady ,dadyne da Mani zaune afalon sai shukhrah ,

Sultan yace gani dady ,dady yace eh dama sonake tinda baka fara zuwa aikinba kuma ga shukhrah tasamu Hutu to sonake muje kauye muyi ziyara gobe saboda haka sai ka shirya ,yace to dady Allah yakaimu ,

Shukhrah kam sai murna takeyi zataje kauye ,mami tace kekuma irin wannan murna haka in dady yace yafasa bandakefa,dariya tayi tafada jikin dady dady yace ai autana kinsan dole aje dake ai ,


Bangaren sultan kuwa haka kwai yaji bayason zuwa kauyennan ,kwai dai bazai iya cewa dady bazeje bane,kuma ga asobitinsa ba akarasa aikinba kuma zasu tafi ,haushin zuwa kauyen yadanji amma sayya daure yahada kayansa ,




******INDO kam ranan batafuto adakin gwoggwo ba dantasan in tafuto kuwa zata jibgu agun baba,

Hardare tana dakin bata ko lekoba har bacci yadauketa ,



Washegari da tingoma su sultan suka iso tsamiya driver yakawo su dan sultan ba gwanin yin driving bane,saboda besababa inyayi tuki waje kadan saiyaji yagaji,


Adai dai kofar gidan sukayi parking suka suka shiga cikin gidan driver kuma yanata futo da kayan da suka Zo dashi a but
.
Da murna inna takarbesu tashinfidamusu tabarma sannan takawo musu ruwa,

Bayan angaggaisa ,inna tace kedai banwayekiba baki taba Zuwa kauyen ba ,shukhrah tayi murmushi dady yace ai makaranta ne yake riketa yanzu sunyi hutune nace to bari na kawosu ita da yayanta suyi Hutu ,kafun agama masa aikin asibitinsa,inna tace ayya ace likitane fa ,mami tace eh Shikuma abunda yazaba knn





Baba yace gashi kunzo kakar naku kuma tafuta tashiga makota

Berufe bakiba gwoggwo yashigo ,tana fadin to yau mutanen birni ne akauye tafada tana dariya irinta zolaya


Sultan yace eh mune mnh ko ba aso zuwanmubane,gwoggwo datakaraso kan tabarman tana shirin zama tace wuuuu wane ni ince banason ganin jikokina ,

Da gudu ta shigo cikin gidan da Abu ahanunta ,KO lura dasu batayiba takutsa ta tsakaninsu ta yi dakin gwoggwo....

*Maman Al-ameen ce*πŸ‘Œ



*INDO BALA'I*
πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€



5⃣&6⃣




_Na maman Al-ameen momcy_,




Ai kuwa gwoggwo na ganin INDO tayi daki aguje tasan da wani Abu ai sai ta Mike tabi bayanta dakin

Shikam baba da takaici yagama isarsa ko kallon inda take beyiba, dadyne yace Aishace haka


Inna tace itace
Momy tace to meye kuma tashigo gida aguje haka kamar wacce akabiyo


Baba yace yawuci wani abun taje tayi,yarinya kullum cikin nema wa mutane magana take daga taje gonar wane tamasa barna sai kaji ance tafasawa dan gidan wane kai ko baki ko kaji ta gurda wani haka kullum muke fama da ita kuma ko a makaranta ma haka ake kawo kararta,ni wallahi nama rasa yanda zanyi da yarinyar nan,
Sultan lokaci daya maganganun baba suka bata masa rai wai anrasa yaya zasuyi da ita bata bugu bane ai ambartane wani haushi aransa yace inama atare suke ai da tayaba wa aya zakinta daduk wannan iya shegen bazatayiba


Dady yace to meyasa baza Ku dinga daukar mataki akantaba karfa wataran daje tajawo wa mutane abunda yafi karfin bada hakuri fa

Baba yace ai bakasaniba kaga ko uwarta bata isa tayi magana ba sai gwoggwo tataso akan mutane koni ban isa dukar INDO ba sai gwoggwo tahau masifa wataran ma harda kuka wai ana zalinta mata jikanta


Momy tayi ajiyar zuciya tace amma bekamata kuwa abarta akan wannan tarbiyyarba dan kokadan hakan bashida fa ida tinda ya macece kuma girma takeyi yakamata ace ana girmane ana hankali kuma duk rintsifa gidan wani zataje to ahaka....momy bata gama maganaba saiga gwoggwo da INDO sunfi to ,


Gwoggwo tayi murmushi tace cha nayi tafuto tagaida iyayenta da yayanta

Zama sukayi INDO najikin gwoggwo ,tace ina wuninku,dady da momy suka amsa ,gwoggwo tace to baki gaida wannakiba,

Sai asannan taluradashi bakaramin kwarjini yayi mataba ,yanda taga yawani murtuke fuska yasa tawano turo baki,taki gaidashi,


Gwoggwo tace iy bazaki gaidashi ba,INDO tace to mutun yana wani bata fuska ne Zan gaidashi yaseen bazan gaidashi ba ,

Wani irin curin takaici da haushin tane ya wurgu a zuciyar sultan ,aransa yanacewa zanyi maganinki kuwa kafun inbar garinnan,


Gwoggwo tace toga kanwarki sai kuje kudanyi hira kallon kallon shukhrah da INDO keyiwa juna ,INDO tayi murmushi tace to kanwata tashi muje yawo ,gidansu kawata nan makota ,shukhrah tamike suka futa ,tin asoron gidan INDO kecewa shukhrah ke wai hala haka wannan yayannaki yake baya dariya yawani murtuke kamar Wanda akayiwa mutuwa,

Shukhrah tace ke niba ruwana bakisan yaya bane baya wasa da yara kuma inkikayi masa laifi suka yakeyi,


INDO tace wa yake duka ,shukhrah tace to innayi laifi ko agaban mamyne yana dukana wallahi,
INDO tace lallai ai wallahi nikam yabigeni sai na rama dan bazan barshi yaci zalina abagas ba kam ehe,



Shukhrah tace ke yaya fa yanada karfi wallahi bazaki iya ramawaba, adai dai nan sukashigo gidansu Abu


INDO tagaida innar Abu dake tsakar gida tace inna Abu fa ,inna tace tace tana daki baban ta yamata duka wato indo awarar yaro kuka diba kuka guduko,ai kema dakije kihadu da babanki dannasan daga gidannan gidanku suka nufa,indo tace ai ni banmaci awararba kuma rashin kunya yaro yamana muka daki banza kuma muka dibi na banza tana maganar tana shigewa dakin Abu


Shukhrah kam binta tayi itama cikin dakin,inna kuwa addu'ar shiriya kawai tayi mata,



Agida kuwa INDO na futa aka kawo karanta tabigi yaro kuma ta dibarmasa awara,baba be iya yace komaiba sai tashi dayayi yafuta waje,gwoggwo tace oh nikam naga takaina ace yarinya duk garinnan ta tsole musu ido kodan sunga yafisu kyau ne yarinya kamar yar larabawa suke mata hassada,sai asannan sultan yayi magana OK kaka keso kike kibata yarinya ko to bazeyiwuba bari baba yashigo da mingama Hutu tare zamu wuce da ita kano


Gwoggwo tace eye Mara kunya wato nine banmata tarbiyyaba sai Kaine ka iya ko ,oh Ku yan birni akwai wata tarbiyyanema daku



Momy tace yi hakuri gwoggwo, bama inda zata wasa yake miki ,tace ai damainanankan bawanda zai tafi mun da jika kalan kije chanma kuyita zalintarta ahakama inasa ido ake mata balle abayan idona
.
Mikewa sultan yayi yakoma mota yasauke sit yakishingida yana ganin yaran kauyen yanda suketa wasa cikin kasa da dauda ,aransa yace ba doleba cututtuka yadinga shigar yara,

Indo da shukhrah yahango duna dawowa, futowa yayi yajingina jikin moto yanajirar karasowarsu danso yake yafara takawa INDO burki akan shashancin datakeyi ,

Shukhrah indo tataba tace ke kalli wannan yayanki Wanda baya dariyarnan yanda yadada murtukewa ko annuri babu afuskarsa shukhrah tace ke haka yayafa yake ko agida baya dariya amma wataran yakanyi murmushi wa mamy ,suna isowa daida jikin motar yace ke kuzonan ,shukhrah ya kalla yace yawo ko,zatayi magana amata wani kallo dayasa tasha jinin jikinta,
Kallon shukhrah yayi yace wuce zamu hadu a gida ,

INDO dabece tawuceba zata wuce yace ke zonan ,juyowa tayi tagallamasa harara ta murguda masa baki tashige gida da gudu.... ..


*INDO BALA'I*
πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€



9⃣&πŸ”Ÿ




_Na maman Al-ameen momcy_






Cikin masifa gwoggwo tace fadamun wayadake nace ko,INDO cikin kuka tace bawannan bane mekama da mayuΓ±nan Wanda baya dariyarnan yayan wanchan shukhrah nibanmasan sunansaba,

Gwoggwo tace shegen yaro meya miki Shikuma daga zuwarsa?
INDO tace ba innace tabani tuwon su baba nakai mishiba dakiba to shine inazuwa dakin yafara dukana wai harda cewa sai yakashenima,


Gwoggwo ai sai tafara salati la ilaha illallahu yanzu kaikuma yaronnan ahaka birnin taku take daga ganin mutun kace zaka kasheshi yau naji dan iskan yaro tana magana tana tafiya ,duk wajen daga inna har mamy ba Wanda yakalli inda suke balle yayi magana dan zuwa yanzu momy tagano halin gwoggwo akan INDO

Sultan da dama duk yanajin abunda sukeyi yayiwa dakin key yayi kwanciyarsa,haka gwoggwo taje tagama masifarta da zage zagenta tahakura tatafi,dan tasan ai yana cikin dakin yanajinta


Su dady da baba suna dawowa sultan yasamu baba akan maganar tafiya da INDO, aikuwa baba ya amince dama shima yana tinanin hakan aransa,




Da asuba indo najin tafiyarsu baba masallaci ta futo ta lallaba sai dakin baba,dan daukar mataki akan abunda sultan yamata,

Aikuwa tana shiga taga system dinshi a kunne da alama yana amfani dashinema yaje sallar aikuwa tazauna tadinga shige shige batamasan inda take shigaba saida tayi nasarar gogemasa komai na laptop dinshi kafun tatashi lafuta adakin ,



Sultan yana dawowa daga masallaci yadauki laptop dinshi da niyyar cigaba da abuda yakeyi ,kwae sai yaga laptop arufe yabude yaduba komai babu aciki ,gashi duk tsare tsarenshi na asibinda zaibude aciki suke kuma akan abunda yakeyi knn yabari yatafi sallah ,duk kololuwar bacin rai yakai kuma yatabbata INDO ce ba kowa ba tataba masa
Kwafa yayi ransa yayi matukar baci
*INDO BALA'I*
πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€


Page 1⃣1⃣&1⃣2⃣




_Na maman Al-ameen momcy_




Su mamy duk kayansu driver yakaimusu mota ,futowarsu kawai yake jira su tafi,


Gabadaya sunyi sallama ,gwoggwo harda yar kwallarta wai Aminu yaki zaman kauye,


Dady da mamy duk sunshiga mota ,INDO da shukrane tsaye ajikin mota suna sallama da Abu,

Baba yafito dakaya ahanunshi dama lokacin gwoggwo takoma cikin gida ,

Mikawa indo yayi yace toga kayanki maza kushiga manah jiranku zasu yi tayi,
.damamaki indo takalli babanta tace baba kayan meye kuma"

Yace kayanki mnh tare zaku tafi ai kije chan kiyi rashin ji kiga kosu yan birnin zasu barki"

Fashewa da kuka tayi tafada jikin Abu dukansu sai sukasa kuka,

Baba yace shukhrah shiga mnh ,shiga motar shukhrah tayi itama jikinta duk yayi sanyi,

Mamyma sake cikin mota sai tadanji tausayinsu,

Babane yamatso yabude motar yaja indo ajikin Abu yasata amota yarufe ,aikuwa indo sai takara kaimin kukanta sosai tajeyi baba kan gida yakoma dan sauri yakeyi yatafi kasuwa,

.bakaramin kuka Abu tayiba musamman dataga tashin motar su indo ai saurayi gida tacigaba da kukanta ba kakkautawa,

Ahanya indo tin mamy da dady na kokarin bata hakuri har suka hakura duka rabu da ita ,daga karshe bacci menauyi yayi awun gaba da ita,




***sai misalin karfe daya suka iso garin kano daidainan kuna indo tafarka idonta ya sauka cikun garin kano,

Kallo taketayi duk inda akawuce saitakalla amma bata magana saboda haushin kowa takeji,


Saida suka iso gate din gidan taga anbude musu tankamenen gate din gidan ,tahangi cikin gidan mamaki yakamata sosai ganin irin girman gidan da haduwarsa,

Ai saitaji tasake ranta lokaci guda ganin harda kayan wasa ga bishiyoyi harda na mangoro ai sai tasaki murmushi ita kadanta,

Bata karasayin mamaki ba ma said a suka shiga tsantsarerren falon gidan ,ai tuni INDO tasaki baki tana karewa falon kallo yanda yahadu ga wani kamshi natashi afalon ,dama INDO akwai San kamshi da tsafta ai saitaji gidan yaburgeta sosai,

Mamy dake tsaye tana kallon yadda indo ke murmushi tana kallan gidan abun yabata mamaki sosai,mamy tace wa shukhrah datazube akujera ta dibo gajiya kuhaura sama manah keda momy(INDO) kuyi wanka ,

Shukhrah tamike indo tabi bayanta suka haura sama ,mamy ma bayansu tabi tashiga bedroom dinta,


Bedroom din shukhrah yaburge INDO sosai ,musamman cikin toilet dinta ga ruwa ga komai ka kayan kamshi ai haka indo tadage tayi wanka sosai tawanke gashinta da baya kitsiwa tsananin yaukinsa da tsayinsa kullum saida ta daureshi,



Tana futowa tashafa mayukan shukhrah masu tsada da kyau, sannan tagoge kanta,shukhrah dale cire kaya zata shiga wanka tace INDO aida kinbari munje wanke Kai saloon dabaki jika kankiba"
INDO takalleta kawai tacigaba da abunda takeyi ,powder kawai tashafa sai ruwan tirare datayi ajikinta ,tasaka wani riga da skrt na atamfa acikin kayanta,sai tayi kyau sosai,dama tayi alola kwai sai tayi sallarta,itama shukhrah tana futowa tashirya cikin Riga da skt amma na kanti,tayi sallah kafun takalli INDO databaje agado tanasonyin bacci tace sister tashi muje muci abinci mnh kobakyajin yunwane ,tashi tayi suka futo falon,daidai Shikuma yanashigowa falon ,

Ido 4sukayi da indo amma sai yakauda kansa kamar begantaba ,shukhrah CE tace yaya sannu da dawowa,be kalletaba yace kuma sannunku dadawowa,


INDO kuwa ko kallanshi batayiba balle yasa ran zata gaidashi,wucewa yayi dakin mamy basujima suka futo tare ,


Mamy tace shukhrah yayato bakuci abincinba ,shukhrah tace mamy jiran ki mukeyi,to ai gani sai muci ko,tayi maganar tana karasowa dinning din,
Shima karasowa yayi yaja kujera yazauna sukafara cin abincin,har cikin ranasa yaji dadin ganinta a gidan dan tabbas zai gyara mata zama kam,



Suna gamacin abincin indo tace ita bacci tajeji tahaura sama,itama shukhrah haka tayi ,tunda suka kwanta basu tashiba sai kusan magrib ,



***washegari dukansu ne zaune agaban dady harda sultan,dady yakalli INDO yace mamana ni a wani class kkne a skull"

Tace dady iam going to primary 5"
Dady yace to ashema class dinku dayada shukhrah sai Ku cigaba dayi tare ,kuma mindayma hutunku zai kare saikifara. zuwa,

Dady yakalli sultan dabayace komai yace sai kuje skull din ranar Monday din kayima regtration,sultan yace to dady yabar falon,sukuma suka cigaba da hirarsu da dady dan mamy tana
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment