Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ya dame ni game da shi ba, ba zan taba
karya 'yancina na kasancewata halitta mai daraja
da Ubangiji ya karramata da kunya ba, wato
halittar da aka yi min na zamowata 'mace
Haba, mace ta rasa kunya? Ai kuwa dai tayi
rashi mai girma, kalaman Yaya Dijah ke nan
kunya ai adon 'ya mace ne, a bakin Umma na saba
jin hakan, don haka na kara kudurawa raina babu
wani abin da zai sa in nuna mishi wani abu in dai
yaga ci gaba da yin shirun nashi yafi mishi to yaje
yayi tayin shiru.

78

Aka wayi gari a gidanmu da ma sauran gidajen
Musulmi na garuruwa daban-daban, hidimar sallah
a ke yi, Jama'a sai kaiwa da kawowa suke yi cikin
walwala da farin ciki ga dukkan alamu kuma an yi
sallar ne cikin walwala da wadata.
Tasa kayan sallar tawa nayi a gabana gaba
dayansu ina binsu da kallo daya bayan daya, kafin
zuwan sallar niyyata in sanya kayan da Yakumbo
Halima tayi min ne ranar sallah don girmamawa a
gareta, amma a yau da aka wayi gari ana hidimar
sallar ga kuma kayan sallar tawa a gabana sai naji
bazan iya kaucewa sanya daya daga cikin kayan
sallar da Mubarak yayi min ba duk kuwa da niyyar
da nake da ita ta daina mu'amalla da kayanshi.
Duk da hakan sai na ce to tunda yanzu hidimar
sallah a ke yi bari in bari bayan sallah na dauki
wannan matakin amma yanzu bari in yi adon
sallah kawai.
Bakin yadin na sanya wanda jikinshi yafi kama
da voil ko silk tasha ado irin na barnina a gaban
rigar dan madaidaicin ado da yayi matukar kawata
rigar ta zamo gwanin sha'awa, na sanya takalmi da
gyale tare da Jaka da suka dace da kayan.
Sannan na dauko 'yar sarkar da 'yan kunnena
tana sanya ga kuma warwarai da agogo, in tsaya
cewa nayi kyau ma bata baki ne kawai, na tsaya

79
gaban dogon yaron Innata da Babah Lantana ta
fitar a dalilin hanata saida gadon da nayi na dauko
shi na kawo dakin.
Kallon kaina nake yi a cikin shi cikin zuciyata
na tabbatar ban taba yin kyau irin na yau din ba,
ko ba a gaya min ba kuwa dama nasan ni din mai
kyau ce, don kuwa kowa ya ce da Innata nake
kama Innata kuwa mata ce da ta rayu mutanen da
suka santa suna ba da labarinta.
Yau kam duk mishikilancin shi da taurin kanshi
in ya ganni ba zai iya kame bakinshi yayi shiru ba,
sai ya yabi kyan kwalliyata sai ya furta wata kalma
da zata zamo mai karfi a tsakanina da shi.
Ina tsaye a wurin ina kara feshe jikina da turare
tare da kara kallon kaina a madubin Asabe ta shigo
dakin tana zage-zage nayi kamar in tanka mata
tunda nasan da ni take yi sai nayi maza na baiwa
kaina shawarar kame bakina tare da hanzarta barın
gidan don ba zai zamo mata komai ba ta rufe ni da
dukan da zai yi dalilin da zata tumurmusa ni ta
lalata min kwallioyar sallar tawa ba.
Don haka nayi maza na yafa gyalena na kuma
shuri takalmana nayi waje, gidan Umma na nufa
zanje in yi mata barka da sallah daga nan taga
kwalliyata.

80
Nayi maza na yamutsa fuska na ce, a'a Umma
ni fa ba don kowa nake yi ba, tayi murmushi, au
haka ne Maryamu kai wannan kayan sallah naki da
kyau suke kai ji wata sarka kai kai kai, wa ya saya
miki wannan sarka Mero?
Na shiga dibi-dibi cikin sa'a ta sake tambayata,
Dijah ce ko? Nayi maza na ce mata ch, lokacin ne
na kara sanin darajar sarkar.
Nabi umarnin Umma na shiga nayi wa Baba
barka da sallah a falonshi na fito daidai Mubarak
yana shigowa gidan ban daga ido na kalle shi ba
balle in gane irin kwalliyar da yayi na dai san
kawai na shaki kamshin turarenshi.
Baba ya bani goron sallah, nayi maganar ina
nuna mata kudin da ya banin, tayi godiya. Kai
wannan kwalliya taki tayi kyau, bani plate guda
biyu Umma zan ba wasu, zuciyata ta soma yin
nauyi da na soma tunanin har uwarshi ta gane don
shi nake yin abubuwa masu yawa amma shi bai
gane ba, ko kuma ya gane ya ki nunawa saboda
bai da bukatata.
Babu wanda ya ganni bai yabi kwalliyata ba sai
shi sai kokarin karbar waina yake yi wai wasu
bakin sun kara zuwa mishi.

82
Iko sai Ubangiji, girman 'ya mace babu wuya
ai duk in da budurwa takai kin kai Maryamu, kin
kuma yi kyau irin wanda ba a zaton miki ba.
Nayi murmushi na ce Umma kenan, na juya
tare da cewa na tafi, da sauri ya biyo ni wata kila
yayi zaton zan tsaya mishi ganin ban nuna alamar
hakan ba ya sa shi fara yin magana ina za ki ne
haka?
Ban tanka mishi ba, da ke fa nake magana, na
sake yin kamar ban ji shi ba, tafiyata kawai nake yi
to tsaya mana ki ji maganar da zan gaya miki, cak
naja na tsaya saboda abinda zuciyata ke raya min,
ya biyo ki ne ya gaya miki wata muhimmiyar
magana, zai yabi kwalliyarki ne wata kila ma yayi
abin da zai fi hakan dadi a gare ki.
Naja na tsaya ya iso ya same ni, maimakon in ji
ya kama hanyar gaya min wata magana mai dadi
sai naji ya fara jero min tambayoyi ina za ki ne
haka? A hankali na ce mishi gida, to me za ki je
kiyi a gidan da ki ke irin wannan saurin? Nayi
shiru saboda ban ga kamar zan iya amsa irin
wadannan tambayoyin ba.
Muje in kai ki kiyi hoto, ban kalle shi ba na ce
na daina yin hoto a daidai lokacin kuma na kama
tafiyata cikin zuciyata ina tunanin bai iya komai ba
sai sayayyan kaya mai kyau amma bai san yaga

83

kayan jikin wanda ya sayawa ya yaba kwalliyar da
aka yi da su din ba, to ko meye amfanin sanya
kayan nashi?
Ina dosar kofar gidanmu na hango Mansur shi
kuma yana fitowa daga zauren gidan namu ga
alama nemana yaje yi daga in da ya hango ni ya
saita kyamararshi ya soma daukana a hoto, kan mu
gamu yayi min hotuna da dama.
Muna gamuwa da shi ya soma furta min
dadadan kalamanshi masu sanyaya zuciya da
sanyata cikin wani hali na natsuwa da farin ciki.
Alfarmarki nazo nema, ta me fa? Ya sake
kallona cikin wani yanayi tanfar dai tsoro yake kar
ya nemi alfarmar bai samu ba. Cikin natsuwa ya ce
min gaishe-gaishen yan uwa da abokan arziki
nake so in roke ki muje tare.
Ba wani tsaya yin wani tunani ba na ce mishi
muje, dadi ya kama shi don in kara mishi jin dadin
kumá na sake ce mishi, jira ni ina zuwa, na wuce
na nufi gidanmu da nufin in canza kayan jikina in
sanya wanda yayi min.
Cak! Naja na tsaya a cikin zaure ina sauraron
maganar da nake ji tana fitowa daga bakin
mutumin da zuwanshi gidan namu ya zama ka'ida
in bai zo ba wannan satin to sati mai zuwa za ka

84
ganshi ya zo, a yanzu kuma har da tsaraba ya ke
zuwa mata da shi
Ba dai kin ce kin ba shi wadannan kajin yaci
ba, ta ce eh, to ki gaya mishi kawai ba zai yi
jayaiya da ke ba, cikin zuciyata na ce oh'oh shi
kam Babana ko me a ke nema a wurinshi kumna
yanzu oho? Sanin da nayi Mansur yana jirana shi
ne abinda ya hana ni tsayawa in ji zancen nasu
sOsai, na shiga gida kawai na wuce su na shiga
dakina na canza kwalliyata cikin kayan da Mansur
yayi min wanda suma suka yi matukar karbata.
Na fito na same shi yana tsaye ni yake jira yana
ganina ya saki wani lallausan murmushi, kin san
kuwa al'amarinki yana bani mamaki, da sauri na
tambaye shi mamakin, sai ya kalle ni ya ce min, to
komai ki ka yi kyau ki ke yi Maryamu, komai ki
ka sa yayi miki kyau ko kin taba sanin ke din
daban ce da duk wata budurwa da ki ke gani?
Ai ni a wurina da za ki bar ni da na yi wa kaina
alfarma na daina kiranki da suna Maryamu in
koma kiranki da sunan (Ta fi su) saboda ke din
daban ce a cikin 'yanmata duka.
Murmushi kawai nayi naje na shiga bayan
motar da Mansur ya tanada don zuwa gaishe-
gaishen yayin da shi da Isiyaku suke gaba.

85

Babu inda ba mu je ba har gidan Yaya Dijah da
Jumare da Yakumbo Halima, shima ta bangarenshi
mun je mun gaida tsohuwar Kakarshi ba mu dawo
ba sai bayan La'asar.
Ina fitowa daga cikin motar na hangi Mubarak
a kofar gidansu ta wajen gidanmu yake
fuskantowa abinda na tabbatar shi ne dawowana
yake son gani.
Yana hango nin kuwa na ganshi ya dunfaro
gidanmu yana tahowa nayi maza na shige cikin
zaure don kar ya same ni a waje. Ina shiga sai
gashi ya shigo, sannu da zuwa nayi mishi gaisuwar
duk da ba dabi'ata ba ce yinta bai 6ata lokacinshi
wajen amsata ba.
Me ke tsakaninki da Mansur? Abinda kawai ya
bukaci sani kenan, na dan yi shiru saboda
nauyinshi da nake ji, sai naji ya ce min kiyi
magana mana, gaya min kawai ai gara in sani, me
ke tsakaninki da shi?
Cikin karfin hali da jarumtaka na bude bakina
a hankali cikin natsuwa na ce mishi, saurayina ne,
to da kyau! Abinda kawai ya fadi kenan ya juya ya
fita. Ya bar ni tsaye a cikin zauren sai dai
maimakon in wuce in shiga gida nima kasa
motsawa nayi a wurin ban san dalili ba har kusan
minti uku da fitan shi ina tsaye a inda ya bar ni.

86

Sunkuyar da kaina kasa nayi ina kallon faratun
yatsuna can cikin zuciyata dai ba zan iya cewa ga
takamaiman abinda nake tunani ba.
Motsin da naji ne ya sani dagowa cikin sauri,
Mubarak ne ya sake dawowa gabana yayi
mummunan faduwa saboda yanayin da na gani a
tare da shi, tsoro ya kama ni nan take naji jikina ya
dauki rawa, dukana zai yi ko me?
Bacin rai da ke fuskarshi ba mai tsanani ba ne,
sai dai da ganin yanayin da ke tare da shi ka san ya
shanye wani abu saboda yanda idanuwanshi suka
canza launi.
Me ki ka ce min yana tsakaninki da Mansur?
Shiru nayi ban iya ce mishi komai ba, kiyi magana
magana ki sake gaya min irin maganar da ki ka
gaya min dazu. Wani shirun na sake yi ban tanka
mishi ba.
Ai ban san kin iya rashin kunya ba sai yau, kina
nufin don kin koyi rashin kunya sai ya zama za ki
ya cin fuskata kici mutuncina ki bata min, to ai
ban san saurayinki ba ne shi yasa na bar ki kina
hidimominki, to anma tunda ke da bakinki ki ka
gaya min to ina so in sake ganinki da shi ki ga
abinda zai faru.
Ina so in sake ganinki da Mansur ko in ji
labarin an ganku tare ki ga yanda zamu kare ni da

87

ke, mara kunya kawai, wacce ko wayo bata da shi,
yana fadin hakan yayi shiru sai dai bai juya ya fita
ba.
Sake tsare ni yayi yana kallona wani irin kallo
da ba zan iya tantance irinshi ba, saboda kainaa a
sunkuye yake hawaye suna ta zubo min, yana
kuma kallonsu amma bai sa shi tafiya ya kyale ni
ba.
Tun kwanaki ki ke nema kiyi min wulakanci
me nayi miki? Me nayi miki da ki ke so sai kin
bata min rai? Ki gaya min in laifi ne in baki hakuri
in kuskure ne in gyara, amma ba zan lamunci,
rainin hankali ba daga wurinki.
Ya juya ya fita nima na lallaba na shiga gida
na hau gadona na kwanta, kuka sosai na kama yi.
Asabe tana kallona tun tana shiru har ta soma
magana ita kadai, in dai namiji ne matsalarki ai
kuwa ba ki yi kukan ba tukuna musamman ma
wannan dan iskan da ki ka likewa mai kwashe-
kwashen tsiya, ban dai tanka mata bá.
Ban sani ba ko kashedin da Mubarak ya yi min
ne ya tsorata ni na kasa sake fita tare da Mansur,
ban iya sake zuwa ko ina ba sai dai kawai in yi
kwalliyata in zauna a gida.
A 'yan kwanakin da na zauna a gidan nan ne na
gane Babana da Babah Lantana ba karamin

88
dasawa suke yi ba, ji da shi Babah Lantana take yi
ba kadan ba, ko abinci zai ci sai ta zauna ta tasa
shi a gaba yana ci tana kara mishi tana yi mishi
wata hira mai dadi da zata sa shi ya ji natsuwa
cikin zuciyarshi.
A zuciyata na ce wato itama dai matar nan ta
iya komai na kyautatawa raini ne kawai da
wulakanci yasa bata yi, ko wanene ta samu yayi
mata wa'azin da ta gyara halinta? Oho, tunda ko
nima dai wannan sallar sau biyu tana zuba abinci a
kwano tana bani, ban karba ba ta sake kawo min
soyayyun kaji nan ma naki saboda zuciyata bata
kwanta min kan in ci ba, amma duk da haka hakan
da tayi yasa al'amura sun dan yi sanyi fiye da da.
Kwana bakwai a ka yi Babana ya fara fita,
Babah Lantanan ce kuwa ta ce babu in da za shi
sai an kwana bakwai, ya zauna shima ya huta a
cikin iyalinshi.
Rannan ya fita ya dawo naji shi yana ce mata
yau dai kasuwar ta dan yi nauyi ga abinda a ka
samu, na kasa kunne in ji abinda zata ce mishi
tunda kullum ya dawo ya ce mata babu kasuwa
fada take kamawa tayi ta sababi tana fadin ya dai
6oye kudinne kawai amma wane irin rashin
kasuwa bayan dazu ta wuce ta wurin taga yara sun
kewaye shi suna sayen abubuwa?

89

Abin mamaki sai naji yau ta ce inishi to ai yau
da gobe kenan, Mallam a ka ce wai kayan
Ubangiji in babu kasuwa ai sai ka dawo gidanka
ka hau sabon gadonka kayi kwanciyarka ka
wataya.
Ta soma zuba mishi abinci yana ci yayinda ni
kuma can cikin zuciyata nake fadin to da haka ki
ke yi mishi wa zai damu da rashin kirkinki balle
har aje ana yi miki rashin kunya.
Suna cikin hirarsu nima ina sha'anina a daki
sai na jiwota tana tambayarshi, to in kirata ne ka
gaya mata? Yayi shiru bai amsa ba, in ban da
uh'uh din da na ji ya fada, don haka na kara kasa
kunne wajen sauraron magana tasa sosai don na
gane da ni a cikin zancen nata.
To amma ai yau ne kayi alkawarin gaya mata,
da safe ka ce a'a yanzu da yamma ka sake cewa
uh'uh to me ka ke nufi? Ko za ka saba alkawari
ne? Dattijo da saba alkawari? Ya sake yin shiru.
Ai fa aikinka ke nan in ana magana da kai kayi
gum da baki kamar wani mai cin najasa, taja wani
mummunan tsaki alamar dai ranta ya soma 6aci,
ko ma ya riga ya bacin, ai dama nasan karya ka ke
yi ba za ka iya gaya mata ba ka ce za ka iya, abin
bakin ciki wai uba yana tsoron 'yarshi.

90

To in ba za ka iya gaya mata ba ni in gaya mata
tunda ni kam ai ba tsoronta nake ji ba yayi maza
ya ce mata uh'uh to in kira maka ita? Yayi shiru ba
ga ta can a daki ba? Kai Mallam kai kam ba ka da
dattaku, kai tir!.
Kalaman nata suka sanya ni naji wani iri, ga
bakaken maganganun da take ta gayawa Babana
ina ji, ban da haka kuma na tabbata ko wace irin
magana Babah Lantana take son ya gaya min to ba
mai sauki ba ce, kan haka sai naji maganganun
nata sun sanya tsigar jikina yana tashi.
Ban iya ci gaba da zaman da nake yi ba,
mikewa nayi na fito nazo na durkusa a gabanshi
cikin natsuwa da girmamawa na ce mish1 gaya min
maganar da ta matsu in ji Baba, ko menene gaya
min kawai zan iya dauka.
Ai kai Mahaifina ne, kai ka rene ni ka kuma yi
min duk alherin da uba ke yiwa da, na kuma
godewa Ubangiji kana sona ba ka yarda ka bayar
da rikona ga kowa ba, don haka babu wani dalili
da zai sa ka rinka sa ranar gaya min wata magana
kana dagawa tunda dai kasan dole ne zan ji ta to
gaya min kawai zan fi jin sauki in na ji ta a
bakinka maimakon a ce wani ne zai gaya min.
A hankali ya dago ido ya kalle ni cikin natsuwa
ya ce min aure zan yi miki Yaacuwuna, na daga

91
ido na kalle shi, damuwa ce karara a fuskarshi ko
ni da ya ce zai aurar ba tare da nasan mijin da yake
nufin banin ba babu irin wannan damuwar a tare
dani, tunda dai nasan a tsakanin biyu ne za a yi
daya, ko a baiwa Mubarak ni ko Mansur, wanda
duk aka yi da shi zan zauna tunda su dukansu ina
da dalilan da za su sa ni zama da su.
Na kawar da wannan tunanin daga zuciyata na
daga ido na kalli Babana cikin natsuwa na ce
mishi Baba wa ka ke nufin baiwa ni? Na dan
sunkuyar da kaina kasa don kunya da girmamawa.
Auren ai na zumunci ne, cikin hanzari na dago
na kalle shi a zuciyata kuwa dadi ne ya kama ni,
wato dama Baba yana sa ne da zumuncinshi da
kullum ake yi mishi gori a kai, wato dama yayi
niyya a kaina ne zai gyara zumuncin nashi ta
hanyar bada aurena gare su?
Ai kuwa dai duk wanda ya baiwa ni zan zauna
da shi da zuciya daya in kuma yi mishi ladabi da
biyayya irin na aure. Amma don in kara samun
natsuwa cikin zuciyar tawa sai na tambaye shi
cikin 'ya' yan wanka ne ko na kannenka za ka
baiwa ni Baba?
Sai da yayi gyaran murya saboda yanda ta
make take nema kuma tayi rawa kafin ya iya ce
min a'a wannan dan uwan uwar taki Lantana ma

92

zuwa gidan nan Mahammadu Nalami shi zan
baiwa ke, don kara karfafa musu zumnuncinsu ai
kin san abokin wasanta ne?
Kadan ya rage in suma a tsugune saboda
tsananin kaduwar da nayi. Nalami fa kace Baba?
Ya gyada kai tare da cewa eh shi nace, ban san
yanda a ka yi ba sai tsintar kaina nayi ina yiwa
Babana tambayoyi.
Zumuncin Babah Lantana yasa ka baiwa
wannan mutumin ni naka zumuncin fa Baba?
Shiru yayi yana kallona bakina ya sake yin subuta
ya ce mishi, ba zan auri Nalami ba Baba, domin
babu abinda ya hada ni da Babah Lantana balle
zumuncinsu da har zan je ina auren danginta.
Tuni na soma kuka ina fadin me nayi maka
Baba? Me nayi maka da ka ke taimakon masu son
ganin nayi bakin ciki a kaina? A gabana kayiwa
Innata alkawarin ba za ka bada rikona ba ne
saboda ba za ka iya rabuwa da ni ba to me yasa za
ka bada aurena a inda kasan zan yi bakin ciki.
Nan da nan kawai sai naji zuciyata tana raya
min babu abinda yasa a ke yi min irin wannan
musgunawar illa don uwata ta rasu, Yaya Dijah da
aka yi aurenta Innarmu tana raye ai bata irin
wannan tozartawar ba nan take na soma kuka da
iyakacin karfina.

93

Kan ka ce meye wannan sai ga makwabta suna
shigowa tambayar me ya faru? Babah Lantana ta
tsaya tana yi musu bayani ai ba komai a ka yi mata
ba tunda ga uban nata nan a zaune wai daga yace
zai bada aurenta ga wani dan uwana shi ne take
wannan borin kar ku dada kar ku rage.
Maimakon a gamsu da bayariin nata sai kuma a
hau salati dan uwanki? In ta ce eh sai a gyada kai
a'a tayi ihu, to wane dadinki taji balle aje ana
baiwa wani dan uwanki ita? Wannan ya gayawa
wannan mutane sai shigowa suke yi yayinda ni
kuma nake kwance a kasa ina ta faman kurma ihu.
Gaba daya a wannan lokacin fatana bai wuce
dayan biyu ya faru da ni ba, in ma dai Babana ya
tausayawa kukan da nake yi ya fasa bada ni ga
Nalami ko kuma azabar kukan yayi dalilin da nima
zan bi bayan Innata in huta da bakin cikin zama da
Babah Lantana.
Ban san yanda aka yi ba har Umma taji tazo ba
sai jinta nayi ta katse Babah Lantana tana mnai
cewa, In ban da 'ya'yan yau ba su san biyayyar
yaye ba yaushe za a ce ka tarawa ubanka irin
wannan Jama'ar mu da yaushe? Umma tayi maza
ta ce mata ke dai kam Lantana ba ki san biyayyar
yaye ba da kin santa kuwa da ba haka ba, da ba ki
a1kata ma irin abubuwan da ki ka aikata ba.

94
Ke wannan sharrin ma da ba ki kulla shi ba, me
yasa baki ba shi tsohuwar yarki da ki ke tashe da
ita shekara da shekaru ta rasa mijin aure ba?
Wannan ai ba huruminki ba ne ki ka shiga don
kuwa ba ki yi mata rikon da za ki zartar mata da
irin wannan hukuncin ba.
Da sauri Babah Lantana ta shiga fadin ai ni ce
ma ni ce na hada? In ke ce in ma ba ke ce ba ce dai
duk daya, yi kokari kiyi hakan a kan "yarki da ki
ka bari tana tanbada kina kallo in ba nema ki ke
sai taja miki irin abinda kema ki ka jawa iyayenki
ba.
Mero kam ai tayi sa'a tana da uban da za a sa
shi yayi mata aure da mijin da aka san ba nata ba
ne don a cutar da rayuwarta, sai dai ba tanan take
wai an danne buduri a ka yace ai ba nan take ba.
In kin yi ne don kin ga duk abinda ki ka yi
mata a zaman da ki ka yi da ita bai ishe ki ba
ruwanki kema kina da 'ya'ya abinda ka shuka
kuma shi ka ke girba, mai rabon ganin badi kumna
ko ana dakawa a turmi sai ya gani, haka ana
muzuru ana shaho zakaran da Ubangiji ya nufa da
cara sai yayi.
Don haka tashi mu tafi Mero, ta sunkuyá ta
kama hannuna na mike na tashi tsaye tana fadin ke
ai kin yi arziki da Ubangiji ya ce yayi miki miji

95

wasu ba gasu nan ba sun tsufa a titi da suna da
iyayen na gaske ai da ba su zuba musu ido ba.
Ki tafi da ita ina za ki kaita? Ko za kije ne ki
kara bijirar da ita? Umma ta waiwayo ta kalleta
cikin nutsuwa tace mata ai mu ba mu bijirewa
iyayenmu ba balle mu haifi masu bajirewa, ba zan
bar miki ita ba ne balle kiji dadin cusa mata wani
bakin cikin tunda ke ba Imani ne da ke ba.
Babu wata za dai ki kai mishi ita ne yayi
abinda ya saba, ta ce eh zan kai mishi ita biyo ni
ke kuma ki hana ni ko ki kwace ta.
A kofar gida muka samu Mubarak yana tsaye,
ganina tare da Umma ya sa shi wucewa gaba ya
fara tafiya muna shiga gidan yaja ya tsaya, wacce
irin musiba ce wannan Umma? Ta ce, Eh ai
rayuwa ta gaji ganin al'amura da dama sai addu'a
kawai don haka ba' yana nufin komai ya kare ba
ne.
To me ya saura Umma? Tayi murmushi tare da
fadin da yawa. Ni kam in ban da kuka babu abinda
nake yi, duk bayanan da Umma ke yi na zai wuce
watarana kuma sai labari jinta kawai nake yi
kullum abinda a ke gaya min ke nan wata rana sai
labari, har yanzu kuma ban ga alamar abubuwan
za su wuce ba tunda kullumn wasu muna nan
abubuwan sai kara samuna suke yi, duk wata fitina

96
ko tashin hankali da na gani a rayuwata ban taba
ganin abinda ya kai cewan da Babana yayi wai zai
ba da aurena ga Nalami ba, in dai ba tashin
hankalin rasa uwata da nayi ba ne.
Ana cikin haka sai ga Baban Mubarak Albaji
Muhammadu ya shigo, menene ne haka a ke ta
kuka ke kuma kin tasa ta a gaba kina kallonta?
Umma ta shiga rattaba mishi bayanin abinda ya
faru.
Hankalinshi a kwance ya ce to ba shi kenan ba
ina ce yarshi ce? Kowa yayi shiru har da ni din
saboda ba zan iya ci gaba da yin kukan a gabanshi
ba, jimawa kadan sai kuma yayi tsaki kafin ya
sake cewa amma bai kyautawa kanshi ba da ya
bari a ka maida shi abinda a ke cewa an maida shi
din, bari in je wurin Mallam Sule mu tafi wurin
nashi tare muji yanda za a yi.
Umma ta ce, To Ubangiji yasa muji alheri, ya
ce amin. Nayi kukan bakin ciki a wannan lokacin
har sai da na rasa hawayen a idona, na rinka jin
tanfar ni din komai nawa ya kare ciki kuwa har da
farin cikin rayuwata.
A duk lokacin da Mubarak ya zaunar da ni da
Dufin rarrashina ko ba ni hakuri kan balin da nake
Ciki bana sauraronshi, saboda ni kam can cikin
Zuciyata bana jin haushin Babana da mutane ke ta

97

fadin maganganu marasa dadi a kanshi, nafi iin
Ciwon Mubarak gani nake tanfar inda yayi wani
abu mai karfi da wuri tun lokacin da nayi ta fata da
burin yayin watakila da wannan abinda ya farun
bai faru ba.
To wai sai a yanzu da Babana ya riga ya furta
wannan maganar shi ne suke ta faman zirga-zirga
aje wurin wannan aje wurin wancan ana kamun
kafa wanda bana zaton zai yi wani tasiri don
magana daya kawai Babah Lantana zata yi ta
birkita komai shi ne kai din ba Dattijo ba ne tunda
ga shi kayi alkawari za ka canza.
Daga ranar da Alhaji iuhammadu yace bari ya
kira Mallam Sule suje wurir Babana zuwa cikar
kwana bakwai ya tura wa Bapaia mutane daban
daban har sau biyar daga ciki akwai tawagar da
Liman ya jagoranta ta Malamai wadanda suka yi
mishi nasihohi a kan muhimmancin bayar da aire
a inda ya dace wato bin kufu'i don a samu zimatu
lafiya fahimtar juna da girmamawar da a ke bukata
tsakanin miji da matarshi.
Haka nan mai unguwa ya jagoranci mayan
unguwa bayanshi Alhaji Muhammadu abokanshi
Sun je har sau biyu.
Yanda na samu kaina cikin kunci da bak ciki
haka Mubarak ba zan ce ya fini ba ne, kawai don

98

ni kadai nasan abinda zuciyata ke ciki, amma ko
daga jin irin aiken da Babanshi ke yi daya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment