Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

FIRST RAMADAN WITH HABIBI.
  💔Heart touching story.💔




https://chat.whatsapp.com/LM4sMyc4lT5Jgnv9lw1vOS


FARIDAT HUSAIN MSHELIA (UMMU-JIDDA).

TSARABAR RAMADAN.
*Manzon Allah (SAW) Yace:*
*“Dukkan aikin da ɗan Adam yayi to nashi ne, Duk aikin lada yana da guda goma makamancin sa, har zuwa a ninka masa sau ɗari bakwai. Sai Allah maɗaukakin Sarki yace: Banda Azumi domin shi na wane, kuma ni ne zan saka akansa. Shi mai Azumi ya kame daga Sha’awarsa, da abinci, da abin sha saboda Ni.*

LAMBA NA ƊAYA .
Baccin kirki ya gagara ɗaukata saboda cike na ke da zakwaɗi da mararin shirya ma Habibina girke-girken alfarma wanda na cika wayata da su,wasu na samo su ne daga Tiktok wasu daga group ɗinmu na Whatsapp wasu kuma na cirosu ne daga shafin manyan chef da ke Facebook dan haka sam na gagara sukuni babban burina yamma ta yi in shige cikin kicin saboda wannan shine farkon azumi da zan yi a gidan HABIBI(FIRST RAMADAN WITH HABIBI).
Duk na ji zaman ya isheni minti-minti nake duba agogo amma sai in ga kamar an rage ma lokacin gudu dan haka na janyo wayata na shiga cikin group ɗin mu na sababbin Amaren da suka yi aure daf da Ramadan,nan take aka goge min hadda saboda hango bidiyon da takwarorina Amaren group ɗin suke turowa na yanke-yanken da suka fara gabatarwa dan haka na zabura na miƙe na shige kicin,dankwalin turawa na ɗibo cikin faranti na fara fera wanda ya ɗaukeni fin awa ɗaya,ina kammalawa na janyo kabeji,karas,koren wake,kokumba na goge na gogewa na yanka na yankawa na sashi a freezer,wake na ɗebo rabin Mudu na hau surfe na wanke shi tsaf na sa a firinji,kafin na fara kokawar haɗa jus,ina kammalawa na ɗebo gyaɗan da Momi ta niƙa min na zuba farar shinkafa akai na yi blending na shi,kafin na dawo gurin Naman sa da kifi na ciri kaza 4 na fara aikinta,duk aikin nan da nake yi Inna kammala guda 1 ina yin video in tura group ɗin mu na FIRST RAMADAN gudun kar a yi bani ko kuma a ga gazawata dan duk  yawancinmu classmate ne mun san juna.

Jin ana kiran Sallan azahar ya sa na tsagaita da aikin na je na sauke farali,ji na yi duk jikina ya yi sanyi kasala na shirin rufeni amma haka na yi ƙarfin hali na shiga cikin kicin na fara aikina,dafa wannan,sauke wancan,soya wannan sai da ya ɗauke Ni fin awa 5 ina aikin dan hatta gyaran gida sai da ana gab da ƙiran magrib sannan na kimtsa falona tare da jera kuloli bila adadin banda Flask da lemummukan da na yi ma HABIBI,turare na sa na wuta , a gaggauce na faɗa bayi na watsa ruwa na fito ban bi ta kan kicin ba dan ba zan iya gyara shi ba a wannan lokacin ga himilin wanke-wanken dana tara dan kusan rabin tukwane na na yi amfani da su bayan ribobi,blender da na yi aiki dasu ban wanke ba.

Riga kawai na zura da Hijab na fara rama Sallan la'asar wanda ban samu na yi ba saboda aiki,ina idarwa na gyagygyara jikina kafin na shiga cikin Ƙayataccen Falonmu wanda abokan mijina suka yi ma ƙawanya,gaisawa muka yi cikin raha da barkwanci bakin su fal murnan yau za su kwashi ganima,na kai dubina kan HABIBI wanda yake jin kan shi a kumbure irin shima Allah ya kawo shi lokaci ya zama magidanci,murmushi na sakar mi shi mai sanyi shima ya maido min da tashi kafin na shiga Serving na su cike da son burgewa,Kunun gyaɗa mai kwakwa na fara zuba musu tare da madara wanda na kusa juye gwangwani ɗaya,sai alalen da yaji hanta da ƙwai tare da source ɗin naman rago a gefe,irish ball tare da wainan ƙwai a gefe guda,sai irian rice wacce ta ji kayan lambu tuttura musu gabansu ƙamshi duk ya cika musu ciki har wani tanɗe baki suke yi dan girkin ya sha spices,dakatawa na yi da zuba farfesun kifin jin sannu da aikin da suke min ya yi yawa sai gasashshiyar kaza da na mata gashin tukunya ganin suna ta godiya sai na sa juice ɗin karas na ajiye ma kowa a gaban shi nima na janyo kujera na zauna tare da ɗiban kunun gyaɗan ɗan kaɗan na ƙarasa juye madarar gwangwani,ƙasa-ƙasa na ga HABIBI ya kalleni tare da aiko min da saƙon harara,a cikin zuciyarsa kuwa yana jin kamar ya jawoni ya lakaɗa min dukan tsiya dan shi sai yau ya tabbatar da mahaukaciya ya auro ba mai hankali ba banda haka ina mai hankali zai aikata irin abin da(DIYAN SHi)ta aikata,ta soye rabin kiret na ƙwan da ya siyo a ƙiyasin shi,ta juye gwangwanin madarar gari a rana guda wanda yana ganin zai kai musu rabin azumi tunda yanzu kowa ya san halin da ake ciki a ƙasar nan,kifi,kaji,namomi duk ta dafe shi a lokaci guda babban takaicin shi ko mutane goma ya ƙaro za su ci abincin har ya rage wai me ta aikata haka ne?ina hankalinta ya tafi ne har ta yi wannan ɗanyen aikin?


Ji ya yi abincin duk ya fice masa a rai dan HABIBI riƙaƙken Kwamared ne wanda ke da dokoki da ka'idodi a matsayin shi na cikakken ɗan boko mai degree har biyu amma har yanzu ba takamammen aiki,

Ashe da sauran rina a kaba dan yana kurɓan kunu ya yi saurin fito da shi jin wani irin TSAMI da ya ziyarci harshen shi da sauri ya ɗibi Irish balls ɗin nan ya kai bakin shi sai dai jin wani irin zaƙin maggi,da gafin kori da ya baƙunce shi yasa ya miƙe a guje ya fice daga Falon da sauri DIYAN HABIBI ta mara mi shi baya sai dai tana tunkaro shi ya yi saurin hankaɗeta ya yi waje da mugun sauri gudun kar abokanan shi su ci wannan kwaɓar dan ya san ya riga da ya gama kunyata a idonsu sai dai ko kafin ya isa aikin gama ya gama,ba bu abinda ba su ɗanɗana ba dan haka marasa hakurin cikinsu har sun miƙe a gaggauce tare da shigewa cikin motocinsu dan yunwa na ƙwaƙwularsu masu hakurin ne kawai su biyu suka rage da shan lemo da abarban da suka shigo da su,takaici tare da baƙin ciki yasa ya ji kamar ya kashe DIYAN SHi  yau dan ta yi matuƙar ja masa abin kunya a cikin abokai dan haka ya tasota a gaba a kan dole sai ta cinye duk abinda ta girka bayan ya sallami sauran, ganin yanda yake huci ya sa ta ranta ana kare sai gidansu dan bai da nisa a tsakani.
Regegeniyar tambayarta lafiya aka fara tsakanin Amminta da Abynta aka yi, kuka ta ke tana ƙarawa ta gagara furta uffan,ganin yanda take ƙiran sunan HABIBI a firgice ya sa Mahaifinta kama hannunta ya maidata cikin gidanta,jan hannunshi take har suka iso falonta nan ta tadda HABIBI yana kuka dafe da kumatun shi biyu, ganin asarar data tafka mi shi (Yo abin ku da kwamared iyayen tsumulmula da tsumi da tanadi),tun kafin Abynta ya ce uffan HABIBI ya miƙe yana nunota da hannu cikin rufewar ido dan ko ganin sirikin na shi ne yi ba ya ce"Ni kika kunyata DIYAH(DEAR)a gaban abokanaina?,ji yanda kika almubbazzarantar da kayan abinci dana maƙulashe fisabilillahi to na yanke hukunci ba zaki ƙara soya ko da dankwalin Hausa ba a gidannan har azumi ya ƙare,zan auno masara da kuka da kuɓewa shi ne abincin da zaki dinga ci har sai Ramadan ya wuce"



Kuka ta fashe da shi tana ce wa"Dan Allah Abi ka bashi haƙuri Ni ban san mena yi ba."

Nuna mata dinning Area Abyn ya yi ya ce"je ki ci abincin da kika dafa"dan tunda ya ga HABIBI na kuka a gaban manyan kololi ya san kwanan zancen,

Cike da ƙarfin gwiywa ta isa ta fara kai kofin kunun bakinta ta ji tsami ya buwayi bakinta dan haka ta furzo shi,ja da baya ta fara yi cikin tsare gida Abyn ya umurce ta ta buɗe kowanne kula ta ji, cikin ɓata fuska ta ke taɓa kowanne daga wanda tsami yayi yawa,sai wanda yaji ko suga ko barkono ya yi yawa nan da nan ta fashe da kuka dan tabbas da ace ta yi koyi da mahaifiyarta bata biye ma Ramadan time table na social media ba da bata shiga cikin chakwakiyar ba dan tabbas ita ɗin gwana ce gurin girki,

Ƙawayenta na group ɗin FIRST RAMADAN WITH HABIBI sun cuceta duniya da ƙiyama ko kafin ta ce uffan Abynta ya juya bayan ya jinjina ma sirikin shi akan hukuncin da ya ɗauka.



Labarin gajere ne na rubuta shi ne saboda faɗakarwa akan Amare masu biye kawayen social media idan kuna buƙatar cigaba in ga comments.





Ummu-jidda.

FIRST RAMADAN WITH HABIBI.
  💔Heart touching story.💔


https://chat.whatsapp.com/LM4sMyc4lT5Jgnv9lw1vOS



FARIDAT HUSAIN MSHELIA (UMMU-JIDDA).




TSARABAR RAMADAN.
  Manzon Allah (SAW)
Ya kasance yana yin buɗa baki da ɗanyen dabino kafin yayi Sallah, idan bai sami ɗanyen dabinon ba sai ya yi da busasshe, idan kuma bai sami busasshen ba sai ya ɗan kurɓi ruwa”.
[Tirmizi].




LAMBA NA BIYU.
A tunzure HABIBI ya mara ma sirikin shi  baya ya fice zuwa Masallaci domin gabatar da sallan Ishsha,ana idarwa aka kabbara sallan Asham jin yanda idon shi ke rufewa tsabar yunwa ya sa ya fice daga masallacin kai tsaye ya nufi wani madaidaicin gurin sai da abinci,

Layi ya bi har aka kawo kan shi sai dai yana miƙa Debit card ɗin shi domin a zari kuɗin abincin ba network, ƙoƙarin yin transfer ya yi ta cikin bankin shi na Opay da ke wayar shi nan ya nuna ya shiga amma mai gurin sam bata ga alert ba dan haka ta hana shi tafiya,abu ya haɗu ma shi goma da ishirin ganin ana niyyar karɓar abincin daga hannun shi yasa ya fizge a tsiyace ya samu gurin zama ya fara kwankwaɗar kunun tsamiyar da ya siya,sai da ya yi rabi sannan ya fara cin masan a yunwa ce ,wani irin mugun kallo ya wurga ma waiter ɗin da ke jiran alert ya ce"Matsa anan ko in barar da ke wallahi",

"Ba zan matsa ba,ka bani kuɗi dan ba mu ji alert ba."

"Sisi bana magani dan kin fi kowa sanin wuyar da cash yake yi kuma Bank ɗin ku ne ke da matsala dan Ni ya tafi."

Da wani bank ka yi Taransifar."ce War mai gurin,

"Opay"ya furta a daƙile dan ji yake yi kamar ya shaƙe su dan takaici banda shirmen da Diya ta aikata mi shi me zai sa ma har su gan shi a waje,

Shikenan ba damuwa ka tafi idan bai zo ba gobe za mu haɗu."ce War Hajiyar bayan ta ga receipt na transaction ɗin,

Wani dogon tsaki ya ja tare da ficewa sai dai me yana isa gida ya ƙara tadda wani kayan takaicin tun daga ƙofar falo in da ya hango throw pillows a zube a ƙofar shiga, tsallake su ya yi ya ƙarasa shiga falon in da ya tadda shi yanda ya bar shi sam Diyah bata kwashe kayan abincinta ba,tsaki ya yi ya shige cikin ɗakin shi domin ya watsa ruwa sam bai bi ta kan mashirmaciyan can ba a cewar shi.
  Diyah kuwa tsabar takaicin abinda ta aikata yasa ta ji yunwar cikin nata ma kan shi ya ɗauke dan haka ta rarrafa ta shige cikin group na FRWM(First Ramadan with HABIBI)janyo wayarta ta yi ganin takwas har ta gota ta san akwai labari daɗaɗa,buɗe datar ta ke da wuya ta ga akasin haka saboda dukkanin waɗanda suka aikata kalar haukarta ko mafiyin nata ma ba su ƙarke da mazajensu lafiya ba ,matsalar da ya fi jan hankalinta shi ne na aminiyarta wacce aka saketa sanadin Ramadan time-table na social media wanda ta rubuta shi a group ɗin SIRRIN YA MACE dake Facebook in da ta ce"Ina son mijina amma ya sakeni sanadiyyar na ɗauki kuɗin shi na yi siyayyar kayan ƙwalam da maƙulashe wanda na kwafo daga shafin sada zumunta,na tambaye shi kuɗin da safe ya ce bai da shi,yana fita na ɗauki Debit card ɗin shi na je na yi siyayya dan Allah ku bani shawarar yanda zan koma hide my id sister yau aurenmu ke cika sati biyu cif da aure."

Ai ban ƙara sa kai ƙarashen labarin ba na koma Facebook in da na shige SIRRIN YA MACE domin karanta comments kamar yanda na saba,

Cikin manyan baƙi na ga an rubuta"FIRST RAMADAN WITH HABIBI"sannan aka ɗauro post ɗin aminiyarta Laila wanda yawancin matan sirri Allah ya ƙara suke mata,sai masu kareta da sunan ƙaddara ne ai kuma mene amfanin bude gidan idan har ba za su ba ma juna shawara ba,dan haka sai ƴan abi yarima asha kiɗa suka fara bata shawara nan da nan na ji wani gamsuwa ya riskeni yayinda na haɗu da shawarwarin masu hankalin da suka ba da shawara dan haka nima na ce bari in gwada ko Allah zai sa HABIBI ya canza shawarar shi a kaina,

Ba tare da tunanin komai ba na yi post tare da tura ma mai girma admin domin ta yi hide ɗina,nan take kowa ta posta min dan na yi sara ne akan gaba tana online kuma ganin hukuncin da HABIBI ya ɗauka akaina  na cin tuwo ta san zai ja hankali dan haka ta yi min post aikuwa na sha zagi cin mutumci iri-iri kafin nagarin suka fara bani shawara,

Jin yanda idona ke min nauyi yasa na ajiye wayar a gefe sai dai ina rufe ido wani irin yunwa ya tasoni gaba dan haka dole na tashi a firgice tare da shigewa cikin kicin,

Haɗa shayi na yi tare da zabga Milo tunda madararmu ta ƙare,na sa sugar madaidaici tare da ɗaukan biredi da bota,sam yunwar ta rufe idona sam ban san da wanzuwar HABIBI a cikin madafar ba yana wanke kajin da na cika ma spices da yaji a gaban sink(Aikin Kwamared)

Har sai da naji ya ruƙo biredi da shayin cikin haɗe fuska ya ce"To be sencere ba zaki sha shayin nan ba almubazzara."

Ganin yanda ya yi maganan yasa na san he is serious dan haka cikin kuka na ce"Ni yunwa zata kasheni wayyo Ammina,ka bani ko in ƙirata Billah."

Wata muguwar harara ya doka min tare da komawa kan aikin shi na dirzan kaza da soson da yake yi duk kalar da na jibga mata ta fita,

Dariya ce ta so suɓuce min sai dai murɗawan da cikina ya yi yasa na fashe mi shi da kuka,cikin zafin nama ya damƙo hannuna tare da nuna min Iranian rice ɗin da na musu ya ce"Zo ki ci wannan in dai yunwa kike ji ko in maki bugun sakwara."

Ɗebowa na yi na kai bakina jin yanda shinkafar ta yi zaƙo-zaƙo tare da kayan haɗin na cabbage karas,green beans,da su gurjin yasa na haɗiyeshi da ƙyar nan da nan wani tari ya turniƙeni HABIBI ya yi saurin miƙo min ruwa a cewar "Bai gama fanshe kuɗin da ya kashe ba na aurena dan haka in na mutu na cuce shi."

Sai da tarin ya lafa sannan na ce"Ba zan iya cin wannan abincin ba mai kama dana ƴan fursin wallahi haba wannan wani irin gwale-gwale ne?."

"Mu ɗin bayin gidanku ne da za ki bamu abincin nan ko fursunonin ki ne?"

"Eh fursunonina ne"na faɗi hakan a cikin zuciyata sai dai a fili ce wa na yi"A'a HABIBI ka yi haƙuri Ni fa da niyar kyautatawa na yi maku wallahi amma ka ga alhairi na shirin zamar min sharri."

Harara ya banka mata ka fin ya ce"Wa ya koya miki wannan girkin mahaukatan?"Ya mata tambayar a harzuƙe dan ya san DIYAH ɗin sa ta iya girke-girken alfarma to mai yasa a wannan karon za ta kunyata shi.

A Tiktok na ga wata Chief ta ɗaura,sunan shi kawai ya ja hankalina na sauke shi a kan wayata kuma musamman na tanaje shi sai a farkon watan Ramadan dan in burgeka da shi HABIBINA.


Tiktok........




More comments
More Typing..




Ummu-jidda.

FIRST RAMADAN WITH HABIBI.
  💔Heart touching story.💔


https://chat.whatsapp.com/LM4sMyc4lT5Jgnv9lw1vOS


FARIDAT HUSAIN MSHELIA (UMMU-JIDDA).


TSARABAN RAMADAN.
*LADUBBAN HAWA KAFAR SADARWA A RAMADAN*
*Mu nisanci yaɗa musu, jayayya, da zage-zage ko ƙarya musamman kan Addinin Musulunci. Da masu zama su ƙirƙiri labarin ƙarya mara amfani.*

 

LAMBA TA UKU.
TIKTOK ki ka ce fa?

cike da mantuwa na furta "Eh wallahi ka san ai manhajar akwai ababe kala-kala na amfanin rayuwa na banzan ne kawai aka fi sani."

"Tabbas haka ne akwai tatattun mahaukata masu koya ma masu taɓin hankali irinki girki tunda kun raina na iyaye da kakanni da kuka gada."

"No no no HABIBI wallahi ba haka ba ne kasan fa mu ƴan zamani ne kuma dole mu yi amfani da hikimomin mu na masu jini a jika domin burge mazajenmu ta kowani fanni musamman fannin girki."


Harara ya banka mata cikin ƙofula ya ce"ɗauki abincin nan ki cinye, kuma This should be the last warning da zan miki magana a kan shiga TIKTOK da FACEBOOK in kunne ya ji gangan jiki ya tsira."

Ɓata rai na yi ina muy-muy da baki ba a zuciyata kuma na ce"Bai isa ba."

Ko duba yanayina bai yi ba ya cigaba da faɗan shi kamar zai aro baki"To banda hauka da shiririta ina naki  ni Ko a jerin girke-girken zamani da na ke haɗuwa da su a kafafen sada zumunta ban taɓa jin wani mai suna Iranian friend rice ba sai a gurinki,kuma ko da banga bidiyon ba na tabbatar da cewa daga kan green beans da duk wani abu mai tauri na tabbatar da sai sun tafasa shi sau ɗaya kafin a haɗa shi a cikin girkin amma saboda ke hauka na damunki haka kika cunkusa mana shi"jin ya yi shiru yasa na ɗago na kalle shi ganin ba alamun rahama a fuskar shi yasa na ajiye cokali gefe guda na tattara kayan lambun da suka sa shinkafar take gagara wucewa a maƙoshi na fara afawa ina yamutsa fuska,hannu baka hannu ƙwarya haka na cika cikina da fried rice ɗin mara daɗi,bayan na cire mata ingredients ɗin da yasa ta zama Irian fried rice,

Ruwa na kwankwaɗa sosai na yi gyatsa ganin yanda HABIBI ya zage yana gyara duk abinda zai iya gyaruwa a cikin girke-girkena yasa na sa hannu na fara tallafa masa,mun yi nasarar soye kajin nan bayan mun sulalata da su citta,kanumfari da albasa da sinadarin ɗanɗano sannan muka komo kan source ɗin naman rago wanda maggi ya masa yawa muka ƙara masa kayan miya dan haka ya dawo daidai muka sashi a fridge,sai kunun gyaɗar da na yi wanda tsami ya mi shi yawa nan da nan na ƙara dama wani muka gauraya shi da wancan mai tsamin ya dawo daidai dan haka ya zama mun cika wani ƙaton kula da shi babba,nan da nan HABIBI ya mance da laifin da na masa ya riƙoni bayan mun kammala aikin muka shige cikin ɗakin mu,

Ƙarfe huɗun asuba ya fita ya nufi masallaci mafi kusa da mu in da ya tarar da masu abinci duk sun fito dan haka ya damƙa amanar rabon abincin ga wani mai sai da rake akan a raba ma mabuƙata, ruwan addu'o'i ya sha a gurin ƴan ciranin da ke barin matansu a garuruwan su suna zuwa neman kuɗi garinmu,sun sha kunun gyaɗan nan kamar me tare da irish ball wanda na ƙara dafa wani na marmashe shi da wancan sai ƙwai dana ƙara soya shi da shi,Fried rice ɗin ma ruwa na ƙara mi shi ya dahu dan haka na zuba shi a ƙaton kula aka ba su suka hau rabo bayan sun yi layi daga ƙarshe har dambe aka kaure da shi dan wasu suna karɓar sau biyu.
Kajinmu kuwa da  farfesun kifi duka mun adanasu a firiji bayan mun yi sahur muka koma ramakon baccin da ba mu samu mun yi ba,

Sai guraren ɗayan rana muka farka in da muka tashi da wata sabuwar fitina daga HABIBI,neman ya sadu da Ni yake ta ƙarfi da yaji saboda yanda muka kwanta manne da juna dan haka daga farkawar sa Hajiyarsa ta fara haniniya tana wani zabura ita ala dole tana neman abincinta,a gigice na fara hankaɗe shi ina tuttura shi sanin muna cikin wata mai alfarma kuma duk jahilci na dai na san ba'a tarawa da miji in ana azumi,

Amma ina ɗan talikin nan ya fututtuke ido yana son jawo min hadisan ƙarya dana gaskiya dan haka na zabura na miƙe tare da shigewa cikin bayi na danna mi shi makulli a guje ya biyo NI yana bubbuga ƙofar ya na ce wa"in buɗe ko ya ɓalla ƙofar" ko mai ya tuna kuma sai na ji ya bar bakin ƙofar yana kwafa can kuma ya rufo ƙofar ɗakin a hassale nan na fara sauke ajiyar zuwa a jajjere kamar wacce ta sha gudun tsere, wanka na yi sannan na ɗauro alwalla na fito tare da rufe ƙofata gam.
  A can ɗakin Habibin Diyah kuwa istigfari ya fara tare da roƙon Allah yafiya akan abinda ya yi shirin aikatawa wanda cikin mafarki ya ga suna wasa da Amaryarsa DIYAH,farkawar sa yaji ta a jikinsa yasa ya ji sha'awar ta ƙara rufe shi sam ya manta da suna azumi kasancewar kuma tana gudun shi tunda ya amshi budurcinta yasa yake ganin kamar har yanzu tsoron ne shiyasa ya dage.

Nan take yaji wani nadama da takaicin auren gaf da Ramadan ya kama shi dan kan shi har ga Allah yana cikin wani hali yanzu,kuma da ace yana da hanyar da zai ɗaga sautin shi har iyayen yara su ji tabbas da ya ɗaga tare da gargaɗin su akan yi ma zalamammun matasan yanzu aure gab da azumi dan da yawansu suna karya azumin su dan biye ma sharrin zuciya,

Ya san dayawan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment