Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[6/3, 4:12 pm] Takori: ZUMUNTAR KENAN 1
Da ka doso garin Giwa gidan za ka fara hanga daga gabas masu kudu na garin, tangamemen gida da aka yiwa jan rufi na zamani mai zagaye da girgijejen gate na bakin karfe da aka fi kira da Mahdi-ka-ture. Dauke yake da (estate) guda wanda ya hadiye gidaje na zamani (flat) guda goma sha biyar.
Idan ka daga kanka sama, rubutu ne da aka yi da ruwan gwal mai sheki an rubuta ABUBAKAR BAMALLI GIWA ESTATE. Gidaje ne reras (dispersed) masu sanyin gani a ido da fenti ruwan gwaiduwar kwai. Gida daya ne ya bambanta da wadannan gidaje guda goma sha hudu wato gida na farko.
Gida na farko ya fi duka gidajen girma, kuma shi kadai ne mai hawan bene. Mamallakiyar wannan babban gida tsohuwa ce ‘yar kimanin shekaru saba’in da biyar mai amsa sunan HAJIYA HADIZA GIWA, wadda ‘ya’ya da jikokinta ke kira da HAJJAH.
Za ka yi mamaki idan ka ji cewa, duk girman gidan nan ita kadai ta yi rayuwa a cikinsa a matsayin matar gida, haka duka ‘ya’yayen nan goma sha biyar ita ta haife abinta daya bayan daya, babu dan miji babu dan kishiya a ciki.
Wannan ya faru ne a cewar al’ummar garin Giwa a sabili da kaunar da marigayin mijinta Abubakar Bamalli Giwa ke mata, da kuma kyawawan halayenta da kyakkyawar mu’amala da kowa.
Don haka ne bayan rasuwar A.B Giwa ‘ya’yansa ba suyi maraici mai yawa ba. Hajja ta zamo bango abar jinginarsu, wannan kuma baya nufin cewa sakar musu take yi, a’a, akwai tarbiyyar sannan akwai (discipline) ga duk wani da ko jikan Hajjah.
Babu wanda za ta sakawa kara ya tsallake, babu wanda za ta cewa eh, ya ce mata a’ah. Babu wanda zai zartar da wani hukunci a kan gaban kansa ko iyalinsa ba tare da izininta ba.
Mace ce mai kyakkyawan tunani tare da kaifin basira, ta yadda duk wani motsi da ‘ya’yanta ko jikokinta suka yi ta san me suke nufi. Mutum ce kaifi daya ba ta zance ta canza.
Haka duk kaunar da take gwadawa ‘yan jikokinta ba za ta taba yarda karami ya kawowa babba raini ba. Jikokinta suna kaunarta sosai fiye da iyayen da suka haife su. Yawanci da daya da daya suka zame kayansu suka dawo nan (Babban gida kamar yadda suke cewa) wurin Hajja. Don a cewarsu, sun fi jin dadi gidan Hajja, abinci kala-kala kala-kala sai wanda suka zaba, tana kuma basu labaran hikaya da tatsuniyoyi na dabarun zaman duniya, tana rungume su komai girmansu ta rarrashe su ta ji abin da ya dame su idan iyayensu sun bata musu rai. Amma hakan ba ya nufin idan ka yi laifi ta sanya Baban Giwa ya hukunta ka, don dai ita dai ba ta iya dukan jikokinta in ba da mahuci ko rankwashi ba.
Haka nan bayan ran A.B Hajiya Hadiza ta tsaya tsayin daka wajen tarbiyyar zuriyarsa, tare da kiyaye auratayya tsakanin jininshi. Har yau, har gobe Haj. Hadiza na bisa kudurin mijinta A.B Giwa na gama auratayya tsakanin jininshi, suna so ko basa so, in yaso daga baya su suke sanin yadda suke yi su shirya su so juna a bisa dole har su zo suna gode mata.
Hakan ne ya haifar da yaduwa da fadada hadi da watsuwar zuri’ar A.B Giwa cikin garin Giwa da wajenta, inda kuma duk suka shiga dole a gane su, saboda kamanninsu da tsagin Mallancinsu dake gefe da gefen fuskar kowannensu, wanda wanzamin gidansu ke yiwa kowane yaro da kowacce yarinya ranar radin sunansa. Duk da cewa sun kebe kansu cikin Estate dinsu, sana’ar neman abinci ko aikin gwamnati na fiddasu cikin garin Kaduna ko Zaria
A cikin gidan A.B Giwa, bayan jikokinta akwai dangin mijinta mai rasuwa, ‘ya’yan ‘yan’uwanta Kaltume da Kubra, dukkansu zawara ne. Kuma da yake sun manyanta sai suka zamo masu jibantar ayyukan gyaran gidan da harkar dahuwar abinci, duk da akwai wadatar masu aiki a gidan.
Bangaren ‘ya’ya maza (Boys quaters) shi Hajja ta ware daga farkon gidan wadanda ga gidajen iyayensu amma sun gudo sun tare mata har girmansu. Sauran jikokinta ‘yammata da suka tasa duk ta aurar dasu a nan cikin Giwa ko Zaria da jininsu, mafi yawa na cikin Zaria, ‘ya’yan Hajja goma sha hudu ne, maza goma mata hudu.
Abubakar Bamalli Giwa hamshakin mai arziki ne na da can-can shekaru aru-aru da suka wuce. Asalinshi Bamalle ne na garin Giwa, iyaye da kakanni, sana’arshi noma ne na kayan abinci (crops production) su masara, gero, achcha, dawa, alkama, shinkafa, dankali, doya da kayan miya, su yake nomawa duk shekara a loda a Daf-Daf zuwa kasuwannin garuruwa masu bukata.
Ya mallaki tafka-tafkan gonaki sama da goma a cikin garin Giwa, wadanda shima gadarsu ya yi. Gidajen haya bila adadin a cikin Giwa da Kaduna, har ma da Zaria.
A duk shekara ya kan nome amfanin gona mai yawan gaske, a nan ake loda su a buhunhuna zuwa kasuwannin garuruwa daban-daban.
Zai yi tsayi in fayyace ko in lissafo sunayen zuri’ar Abubakar Giwa daya bayan daya, amma babban su shine Alh. Mukhtar Abubakar Bamalli wanda ke jagorantar reshen BAMALLI FOOD CROPS AND CASH CROPS PRODUCTION na Kaduna, wato wakilin kasuwancin kayan gonarsu na reshen jihar Kaduna baki daya, don haka zaman shi da iyalinshi ya fi yawa cikin kaduna, duk da gidansa na nan cikin A.B Bamalli Estate, in sun zo sallah ko biki budewa kawai suke yi su share su shiga.
Sai Ahmadu A.B Proffesor ne a jami’ar Ahmadu Bello a tsangayar harkokin noma da kiwo, gidansa na nan cikin jerin gidajen malamai na A.B.U Zaria, kamar Baban Kaduna (Alh. Mukhtar) shima gidansa ne na biyu a A.B Bamalli Estate. Yadda Alh. Mukhtar ke zuwa da iyalinshi suyi kwanaki ko sha’ani, haka yake zuwa da nashi.
Alh. Na’ibi Abubakar Bamalli ke bi mashi, gidanshi na nan cikin Estate shi ke kula da gonakinsu. Sai Ibrahim A.B, mai kula da gidajen hayarsu na cikin Kaduna. Barau A.B shine ke kula da Distribution (rarraba) amfanin gonakinsu zuwa garuruwa, shima cikin Estate yake shi da iyalinsa. Sani A.B, Sadi A.B da Salisu A.B, kowanne da bangaren da yake jagoranta cikin hanyar neman abincinsu.
Sai Aunty Hauwa wadda ke auren dan aminin marigayi A.B wai shi Alh. Sabi’u Kwangila da ‘ya’yanta biyar, suna nan cikin Kaduna a unguwar Malali. Yaya Ladidi ke bi mata, ita kuma Zaria take aure unguwar Tudun Wada. Sai Yaya Hafsatu dake aure nan cikin Giwa. Aunty Rabi (autar Hajjah) ita ce kadai mai karancin shekaru a cikinsu. ‘Yar kimanin shekaru ashirin da bakwai, shekarar baya ne aka yi auren ta da Yaya Muftahu dan kanin A.B wanda aiki ya hulla shi Kano, yana aiki da gidan wayar Zain.
Kwari irin na Hajiya Hadiza wannan ba zai rasa nasaba da jin dadin da take samu wurin ‘ya’yanta ba, domin a kulli yaumin kamar ana kara mata kwari da kuruciya ne, ba za ka yarda da tarin shekarun da take dasu ba a fuska da yanayin jiki. Ita kanta ba dukiya kadan ta mallaka wurin marigayin mijinta ba, iyayenta da kakanninta ‘yan asalin Zaria ne tushen unguwar Tukur-Tukur.
Marigayin mijinta Alh. A.B Giwa shine dan garin Giwa ba ita ba, ita aure ya kawo ta. Haka bayan ranshi ba ta tsallake ta bar wannan muhallin da suke ciki ba ita da ‘ya’yanta. Tana kokarin hada kansu ba tare da sun yiwa mahaifinsu nisa ba, don kara killace zumuncin su. Basu aure mace ko namiji sai cikin zuri’ar su (jinin su).
Wannan ne ya sanya suke kama da juna, inda duk ka gansu in ka san daya daga cikinsu za ka gane su. Farare tas-tas masu dogon hanci da yalwar idanu da garin jiki (girma da tsayi). Da an gansu an san su, in ba ta tsagin ba ta kamannin, in ba ta kamannin ba ta jin kai da yanga, daga matansu har mazansu.
Mutane da yawa kan ce zuri’ar A.B sun fiya girman kai da dagawa, amma a zahiri nutsuwa ce kawai da Allah ya haliccesu da ita da tsabar sanin ciwon kansu, domin dukkaninsu ilimi na Muhammadiyya da na zamani ya wadaci kwanyar su. Har kullum arzikin A.B karuwa yake, domin basa wasa da hakkin Allah cikin dukiyoyinsu (Zakkah).
Har zuwa inda yau ke motsi tun bayan ran marigayi A.B, ba a ko taba kwatanta auren bare cikin zuriyar sa ba, don a ganinsu auren bare zai bata musu family, zai jawo rarrabuwar kamanni, ya rarraba musu kan ‘ya’ya, kuma ya haifar da sauyin kamanni cikinsu.
Hajjah duk da kasancewar mace ce mai fada a yawancin lokuta, amma fa in ka iyawa halinta ka fahimci likes and dislikes dinta, to ta fi ruwan sha saukin sha. To haka gaba daya ‘ya’yanta suke lallaba ta, suke faranta mata, ba ta da ciwuwwukan da tsofaffi ke fama da shi ko daya irin su sukari, ciwon kafa, hawan jini ko rikicewar girma. Musamman babban danta Alh. Mukhtar ya fi kowa iya zama da ita da tattalinta da yi mata biyayya a bisa dukkan umarninta.
A cikin Estate din akwai babban masallacin da suke haduwa suyi dukkan salloli biyar a kan lokaci, bangaren maza daban, an sanya labule tsakaninsa da bangaren mata. Yaransu da manyansu da wuya ka ga suna sallah a cikin gida in ba da wata babbar lalura ba.
An hore su da sallah da kula da lokacin yin ta. Da zarar Baba Barau (Limamin A.B Mosque) ya yi kiran sallah kowa zai aje abin da yake yi ya je ya daura alwala ya tafi masallaci ya bi jam’i, maza da mata, yara da manya, ‘yammata da samari.
A gefen masallacin karamin clinic dinsu ne (dakin shan magani ne wanda suke biyan likita guda duk wata da Nurse suke kula da lafiyarsu da ta yaransu akai-akai). Haka main market Giwa bangaren kayan abinci duka rabi shagunan Bamalli ne, suna hada-hadar tafiyar da harkokin kasuwancinsu rai kwance, hankali kwance.
Dukkan mazan fannin aikin noma suke karanta (Agricultural Engineering ko Agriculture Science) a jami’ar Ahmadu Bello. Matan ne kowacce da bangaren da ta karanta, Aunty Hawwa ta karanci Quantity Surveying ne, Ladidi Education, malamar makaranta ce. Yaya Hafsatu Home Economician ce, Aunty Rabi kuma aikin jarida ta karanta. Da yake Musbahu mijinta a Kano yake aiki ya samar mata aiki a Kano da gidan rediyon Freedom, ko haihuwar fari ba ta yi ba.
Allah ya albarkaci wannan family da nutsuwa da biyayya ga mahaifiyar su Hajjah, babu mai zartar da hukunci a gidansa ko a kan iyalinsa face da sanin ta, da amincewarta. Haka igiyoyin auren da take kukkullawa a tsakaninsu basa ganin bekenta, domin duk wanda ya bi ko ba da son ransa ba, daga baya sai ya ga amfaninsa. Don haka duk cikin samarin da ‘yammatan da suka tasa babu mai tunanin yin budurwa ko nuna ga wanda yake so, sai wanda Hajjah ta ga ya yi mata dai-dai ta hada su.
A halin yanzu dai yara uku ne mata a gabanta da basu haura shekaru bakwai zuwa takwas ba, duka jikoki ne, Ummi, Zanirah da Fa’iza. Samarin maza ‘yan sakandire da na jami’a sune Allah ya yi yawa dasu a gidan. Duk sun baro gidajen iyayensu sun tare a baskwata din Hajjah.
Ba ta nuna damuwa sam, kamar yadda ba ta takura da zaman su, ita dadi ma take ji duk inda ta juya ta gansu, tana bari-bari ko suna hirarsu ta jika da kaka cike da kauna da fahimtar juna.
Dadi take ji ta ga jikokin nan nata sun zagayeta, wannan ya tsokani wannan, wancan ya tsokani wancan, ta yi ta shari’a, ta yi ta bari-bari ko ta kai musu duka da mafici.
Sai dai Hajjah ta raini jikokinta da kyakkyawar tarbiyya ta yadda babu yadda za ayi ka ga karami ya kawowa babba raini, ko ka ga da wuya macen da ta tasa ta zauna kusa da mazan ko kokaye-kokaye, haka nan duk motsin da dayansu zai yi, to a kan idonta ne.
Yanzu kam hankalinta duka yana kan ‘yan matasan jikokin nan nata mata guda uku da suka saura a gabanta ta dage wurin tarbiyyar damu. Wato ni, Ummi (Khadija) da Zanirah.
FA’IZ, Da ne ga babban dan Hajja Alh. Mukhtar, kuma rayuwarshi ta dawo gidan Hajja ne tun daga shekarun yaye ba kamar mu ba. Kaunar Hajjah da Fa’iz daban ce da duk sauran jikokinta, saboda shi kadai ne me sunan marigayi A.B wato (Abubakar), kuma a cewar ta kullum Yaya Fa’iz shine photocopy na A.B Giwa, daga kamanni har halayya.
Fa’iz ya shiga ran Hajja fiye da duk ‘ya’ya da jikokinta. A cewar Hajjah, Fa’iz yaro ne mai shiga rai, kuma mai nuna mata kulawa fiye da kowa a zuri’ar. Komi Fa’iz ya samu na Hajjah ne, baya kyashin kadar da komai nasa wajen faranta mata, musamman kasancewarta ma’abociyar cin farin goro da mu’amala da man zaitun, habbatus-sauda da turaren miski a jiki da tufafinta.
Tun yana karami ya san yadda yake samar dasu gare ta baya bari ta neme su bayan sun kare sai dai wani ya tadda wani, daga Abubakar-Fa’iz da take kira (Hafizi), kasancewar shi mahaddacin Alkur’ani a shekaru na goma sha biyar. Zai kuma iya karya harshe ya karanta shi tiryan-tiryan da dukkan kira’ar Hafizan da muke dasu a Saudiyyah, irin su Abdur-Rahaman Sudaith, Jabir da Abdur-Rahaman Bn Marwan Al-Juhainy da Khusairi.
Fa’iz ne kadai ya yi karatun sakandire a birnin Madinah Al-Munawwarah, daga aljihun Gwamnati. Yana da shekara goma ya yi musabakar izfi talatin daga jihar Kaduna ya samu sponsorship zuwa wata sakandire a Madinah.
Ya dawo gida yana da shekaru goma sha bakwai, ya kuma zabi gidan Hajjah a matsayin gidan zamansa maimakon gidan mahaifinsa Alh. Mukhtar a cikin Kaduna. Daki guda Hajjah ta ware ma mijinta Fa’iz a Boys Quaters da duk abin da zai bukata, sannan in ta ji shi shiru kullum kafarta na hanyar dakinsa don ganin “ko lafiya Hafizi baka shigo ba?”
Sai ya ce, “Akwai abin da nake yi ne Hajja, zan shigo anjima kadan”. Haka suke a kullum.
Zanirah kanwa ce ga Fa’iz, wato ita ma diyar Baba Mukhtari ce, zamanta gidan Hajjah ya samo asali ne tun wata tafiya da mahaifiyarta Mama ta yi aikin Hajji tana shekara hudu ta kawowa Hajja ita. Bayan dawowar Mama kiri-kiri Zanirah ta ki gidansu. Ita da Jabi Road sai hutu, shi din ma ba kowanne ba, sai wanda ta ga dama.
Babban Yayansu shine Bashir wanda ke karatu a matakin farko na jami’ar Ahmadu Bello, sai Fa’iz wanda a bana ne ya kammala sakandire, Abdulhakim ke bin Fa’iz, sannan Shu’aib, Yahaya, sai Zanirah da autansu Abbas da muke kira (Junior).
Khadija (Ummi) ita kadai ta fara cin sunan Hajja a cikin mu. Diya ce ga Aunty Hauwa dake Kaduna. Ummi tun tana shekara biyar Aunty Hauwa ke kawo ta hutu wajen Hajja su hadu ita da Zanirah suyi ta wasa, zuwan ta ya zama akai-akai duk hutun makarantar boko. Da dai Ummie ta gane irin dabdalar da yara sa’o’inta ke yi a gidan Hajja sai ta yiwa uwarta tawaye ta shiga ihu da tirjiya duk lokacin da aka zo tafiya da ita gidansu.
In kuma aka takura mata tafiyar, to a ranar duk gidansu ba mai barci da shesshekar kakanta har da shidewa. Dole iyayenta suka hakura da kulafucinta suka bar ma Hajja.
Ni FA’IZAH AHMAD ABUBAKAR GIWA, ina daya daga cikin jikokin A.B Family, kamar yadda na fada a baya, mahaifina shine da na biyu a ‘ya’yan Hajjah wato Professor Ahmadu Bamalli na jami’ar Ahmadu Bello. Auren zumuncin Bamalli shi ke tsakaninshi da Mamana Maimunatu da muke kira Momin ABU, shi kuma Baban ABU. Nice ta fari, sai Abdallah, Walida ke bin Abdallah. Yayin da Kausar ta kasance autarmu.
Momi ma’aikaciyar jinya ce ita a asibitin koyarwa na Zaria (ABUTH). Tsananin rashin kulawarta gareni wai don nice diyar fari, kunya da kawaici mai sawa a hantari yaro ya sanya Babanmu ya dauke ni daga gabanta tun ina shekaru biyar ya bai ma Hajjah.
Nima dama na fi son gidan Hajja, ko don su Zanirah. Sai muka dunkule mu ukun nan muka bude rayuwar da ta caza kwakwalen iyayenmu a gaba da kakarmu Hajjah. Ta yadda babu ranar Allah da za ta fito ta fadi bamu bar abin fadi ba, domin dukkaninmun nan kowacce da halinta, muka kuma hadu da maganinmu Ya Fa’iz ta yadda babu ranar Allah da ba zamu barta ba tare da Hajjah ta yi shari’a ko rabon fada a cikin ta ba.
Ba zan manta ba, a ranar da zan koma Giwa ban iya na yi barci ba saboda doki da murna, da asubar fari kuwa na shiga bubbugawa Babanmu kofa ya fito mu tafi Giwa kafin su Zanirah su tafi makaranta.
Don haushi Momi fitowa ta yi ta mammake ni ta kuma ce ba za a tafin ba sai sha biyun rana. Haka na wuni ina duba agogo ina zumburar baki, domin dai har sai da Baban ABU ya shiga cikin makaranta ya fito sannan muka taho Giwa (makyankyasarmu).
Muna zuwa kuwa na gayawa Hajja abin da Momi ta yi min, ta ce (ya yin da ta rungume ni) “Ki barta daga yau ganinki ma sai ta cike form, tunda ba ta sonki ni ina sonki. Da kafarta za ta zo neman ki, ki zuba ido”. Ni kam na san abin da ba zai taba yiwuwa bane Momin ABU ta wanko kafa ta zo Giwa domin ni, sai in tata ce ta kawo ta.
Na ce, “Hajja ina su Zanirah ne? Tunda na zo ban ji duriyarsu ba”. Ta ce, “Suna Islamiyya yanzu za ki gansu, kema in Allah ya kaimu gobe Babanku na Giwa (Baba Barau) zai amso miki form daga boko har Islamiyyar ku dinga tafiyar ku tare”. Na shiga tsalle ina murna.
Daga nan na shiga kitchen din Hajja na soma bude kuloli da kwanuka ina tsame namomin dake kan abincin ina cinyewa, Hajjah na falo ba ta sani ba. Ni Allah ya halicce ni da shegen son nama kamar mage, Momin ABU kan ce kamar mayya. Don haka ko da nake Zaria Hajja kan sa ayi mani dambun nama mai yawa ta aike mani cikin samira duk sadda Babanmu ya zo gaishe ta.
Dai-dai sanda na bude wani madaidaicin (food flask) ruwan kasa Hajja ta shigo. Na kai hannu zan dauke cinyar kazar dake kai Hajjah ta rike hannuna tana murmushi, ta ce, “A’a, an cinye na kowa to ban da na Hafizina, haba Fa’iza? Don ya ga naman nan tun kafin a dafa shi ba zai zama haramiyarsa ba, dole ne ya ci cinyar kazar nan”.
Na dube ta rike da murfin flask a hannu daya, daya rike da cinyar kaza cikin mamaki na ce, “Hajja waye kuma Hafizi da ya fi kowa da za a sawa kowa abinci a kwanon samira shi a zuba mishi food flask?”
Hajja ta ce, “Fa’izu mana, dole ne a girmama Hafizin Qur’ani. Balle Fa’iz da duk ya fiku sona, ku baku yi min sai dai in muku, Fa’iz fa? Naman nan ko idan kika sake kika ci in dai Fa’iz ne sai kin amayo shi”.
Na soma yagar cinya ina ci abuna, na ce, “Hajjah ai dama ke kike daure masa yake cin zalin mutane, don bakya ganin laifinsa, kina fifita shi a kan kowa”.
Hajja ta ce, “Ba na gani din, na fifita din”.
Na cinye nama na bi lafiyar gado, ba jimawa barci ya kwashe ni, Hajja ta shiga harkokinta.
Hayaniyar su Ummi da Zanirah ce ta tada ni.... “Ehu! Fa’iza? Don Allah Hajja da gaske? Da gaske kike Hajjah ta dawo nan da zama?”
Ban ji amsar da Hajja ta basu ba, Zanirah ta fyallo a guje ta daka min duka a baya, na tashi wurgigi a firgice, sai kuma muka dafe juna muna kyalkyatar dariya.
Bayan sallar isha kowacce ta bude kwanonta za ta ci abinci, Ummi ta ce, “Shegiya Fa’izah dama tunda na ga kwanukan nan lami na san kin zo garin”.
Zanirah ta ce, “To meye don ta ci namanmu bayan kin samu ma ta zo? Da kafin ta zo ba cewa kike dama Fa’iza ta zo hutun nan muje muyi shi gidan Baban Kaduna ba? Wai inda ita tafiyar tafi daxi? Amma yanzu daga zuwan ta kin fara yi mata korafin cin nama?”
Ummi ta harare ta, ta ce, “Ka ji ta kamar gaske sai wani kakkare ta kike, dama ban san halin bane, gobe ne zuwa jibi za a fara rabon dambe tsakaninku”.
Dai-dai lokacin Fa’iz ya shigo yana sanye da ruwan madarar jallabiya da carbi a hannunsa, farin yaro tas kamar haifaffen Da’ifah, matashi mai garin jiki irin na zuri’ar A.B Giwa. Hancin nan mikakke har baka, kanshi akwai tarin suma. Gefe da gefen fuskarshi tsagin mallancinshi ya fito radau, dogo mai tsayi da kafadu tun a wancan kananan shekarun.
Da gani daga masallaci yake rike da tasbaha a hannunshi na dama. Shigowar shi ta katse Ummi da Zanira daga musun su, ya wuce ko kallon mu bai yi ba kai tsaye zuwa kitchen ya dauki filas dinshi ya fita.
[6/3, 4:12 pm] Takori: Jim kadan sai ga shi ya dawo a fusace, ya dangwara min ma’adanar abincin a cinya yana zazzare fararen idanusan wadanda tun a wancan lokacin suke da wata irin baiwa ta kwantaccen ruwa kamar hawayen da bai kai ga zubowa ba a cikinsu, da babbar murya ya ce, “Ke kwalamammiya amayo naman da kika ci ko billahillazee in yi kuli-kulin kubra dake yanzu a gidan nan, in lallasa ki dukan da uwarki ba ta taba yi miki ba”.
Na ma rasa me zan ce don mamaki da takaicin ambaton uwata da ya yi, haka Ummi da Zanira sunyi wuri-wuri. Ya ci gaba da magana cikin bala’i.
“Kazamar banza mai kashi a wando, wa ya ce ki sa min kazamin hannunki cikin abincina? Tunda ma kika saka wannan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On ZUMUNTAR KENAN
avatar
umm

7 months ago

Reply

Why is it not complete

Please Login or Register in order to submit comment