Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

🌻 *THE WORLD MAN*
(NAMIJIN DUNIYA)

*MALLAKIN*
*REAL EESHOW*

HOME OF QUALITIES WRITERS ASSOCI…

*BOOK 1*

*PAGES* 0️⃣1️⃣➡️0️⃣2️⃣

Tafiya sukeyi cikin nutsuwa suna hira su biyu Hauwa'u ta kalli Inteesar tare da cewa"Inteesar gaskiya ina ganin musamu wani gurin mu fake saboda naga hadari na niyyar tasowa ke sarkin mura".
"toh yanzu a ina zamu fake anan gurin".
"kinga wata rumfa can muje muɗan fake in ruwan ya ɗauke semu wuce gida".
"toh".
nan suka ƙarasa rumfar wani me shayi suka zauna zamansu keda wuya ruwan sama ya kece aka shiga ruwa kamar da bakin kwarya.

Andaɗe ana ruwan sannan ya ɗauke suka tashi suka cigaba da tafiya sunyi nisa sukaga wasu motoci ƙirar Land cruser baƙaƙe se ta tsakiyar data ƙasance roice-roice fara tas me baƙin tintac motar itace ta cikon ta bakwai wato dai ma'ana a tsakiya danno kai sukayi sunzo wuce daidai su Inteesar bazato sukaji ruwan taɓo da kwatami ya watsomusu a jikinsu sakamakon motar fallatsamusu da tayi cikin sauri da zafin zuciya Inteesar ta wawuri wani dutse dake kusa dasu ta jefi ɗaya daga cikin motar dutsen be tsaya akan kowacce motaba se a glass ɗin farar motar nan ta tsakiya tass kakejin ƙarar fashewar glass ɗin a razane Hauwah ta kalli Inteesar tare da kallon motocin tace"nashiga uku Inteesar kinsanko motar wa kika fasawa glass kuwa?".
cikin masifa wadda ita kanta batasan tanada itaba tace"ko motar waye ina ruwana meyasa su masu kuɗi basusan darajar ɗan Adam ko cemusu akayi muba mutane bane ke bakiga abinda sukayimana ba ruwan kwatamifa suka fallatsamana kina kallo kuma ko niyyar tsayawa basu da ita amma ke saboda rashin kishin kai yasa ki cemun wai nasan motarwa na fasawa glass ina ruwana ko wayemana ai tare suke".

Jin ƙarar glass yasashi ɗagowa daga karatun daily thrust ɗin da yikeyi tare da zubawa gaban motar da yike ido wow na furta sakamakon ganin haɗaɗen matashin guy ɗin yagaji da haɗuwa komai nashi abun burgewane saurin fita drivern yayi bejimaba ya dawo cikin girmamawa yace"Oga wasu yarane kan amfallatsamusu ruwan taɓo shine ɗaya daga cikinsu tayi jifan amma gashi can su Muhd sun zagayeta".
cikin muryarsa da kamar ammasa dole yace"buɗemun mota".
"angama ranka shidaɗe".
nan drivern ya buɗemasa a hankali ya zura ƙafarsa waje yafita cikin takun zaratan maza masuji da class yaƙarasa gurin wanda hakan yayi daidai da ɗaga hannun Muh'd ze wankawa Inteesar mari.
a ɗan daƙile NAMIJIN DUNIYA yace" Dakata Muh'd".
yaƙarasa maganarsa tamkar wanda aka tilastawa
Wani ƙasƙantaccen kallo me cike da zallan ƙyama da wulaƙanci yake jifanta da shi Cikin lion voice ɗinsa yace" ke Waye Ubanki da me kike gadara da har zaki fasamin glass ɗin motana ubanki waye a ƙasarnan".
Lokaci ɗaya Idanunta suka rine saboda tsananin ɓacin rai saboda dukda suke talakawa batason a wulaƙantamata iyaye a zuciye tace "Da Uban da kake gadara dashi nake gadara mutumce kamarka".
Azuciye ya ɗaga hannunsa da niyyar yarfa Mata mari yaji an riƙe Murmushi ta saki me cike da takaici da ƙunan rai tace" daka mareni tabbas da ka aikata kuskure mafi muni atarihin Rayuwar ka idan har ka yadda wannan wulaƙantaccen hannunka ya taɓa tsaftacciyar fuskata ta".
ta faɗa tare da yin wurgi da hannunsa Bata jira Jin abinda zeceba ta finciki Hannun Hauwa da jikinta keta rawa suka bar wajen.

Hannu yasa ya hargitsa tulin sumar dake kansa kana ya furzar da iska me zafi daga bakinsa wani irin tsuma jikinsa keyi yayinda jijiyoyin kansa suka tashi ruɗu-ruɗu dasu tabbas tunda yake babu wani mahalukin daya taɓa muzantashi irin wannan bagidajiyar yarinyar tamkar ze tashi sama ya juya yashi ɗaya daga cikin motocin guard ɗinsa kafin yaƙarasa sun buɗemasa ƙofa shiga yayi tare da lumshe sexy eyes ɗinsa yayi da sukayi ja dasu tare da furta "senayi maganinki ko ƴar waye harni NAMIJIN DUNIYA za'ah samu wata dirty girl zata gaggayamun magana nayi alƙawari sekinyi regreting ɗin abunda kikayi ".
yana wannan zancen zucin har suka isa wani tanƙamemen building dogo kallo ɗaya zakayiwa haɗaɗɗen building ɗin ka fuskanci ma'aikatace saboda mutane daketa hada-hada a gurin suna gama parker motocin Muh'd yace"Oga mun iso".
buɗe lumsassun idanunsa yayi da sukayi ja ya kalli handle ɗin ƙofa alamar a buɗemasa buɗemasa Muh'd cikin takun ƙasaita haɗe da jiji dakai ya fito ma'aikatan dake gurinne gabaki ɗayansu suka shiga gaidashi ba tare daya amsaba yashiga tafiya saboda tsananin ɓacin ran da yike ciki be zame ko inaba se gurin elavatorn da shikaɗai yike hawa ya danna yashiga ya rife a hawa na goma elavatorn ya tsaya tare da wangale ƙofar fita yayi tare da nufar wata haɗaɗɗiyar ƙofa yashiga nan take wani haɗaɗɗen guri ya bayyana se wata mata datasha atarch akanta yare-yare fuska tasha mai ga heavy make up data cika fuskarta dashi tana danna waya ta bayyana tana ganinshi ta ƙara gyarawa cikin ƙissa tace"Oga sannu da zuwa".
be amsamataba hakan yasa tagane yau yana cikin ɓacin rai dan haka takama kanta tare buɗemasa ƙofa yashiga tanƙamemen office ɗinsa daya gaji da haɗuwa kallo ɗaya zakayiwa office ɗin kasancewa kuɗi sun zauna domin komai na more rayuwa akwaishi zama yayi sakatariyarsa daketa kwarkwasa tashiga zayyanemasa shadul ɗin ranar jingina yayi da kujerarsa tare da lumshe ido fita sakatariya Zeezee tayi bata jimaba se gata da wani haɗaɗɗen cup a hannunta taƙarasa gaban table ɗin da Namijin duniya ke zaune tace"sir your copee is ready".
ba tare daya buɗe idoba yayimata da nuni data bashi miƙamasa tayi ta juya a hankali yashiga shan copee lokaci ɗaya yaji wata nutsuwa tazomasa ya aje cup ɗin tare da danna wayarsa yayi dialing wata number bugu ɗaya aka ɗauka daga ɗaya ɓangaren wancan yace"Oga ɗiyar massenger ɗin Sir Ahmad ce".
wani murmushin gefan baki Abdallah Namijin duniya yayi ba tare da yayi maganaba ya kashe wayar tare da tura text ya jingina da kujerarsa yana tinano irin abubuwan daya tanazarwa Inteesar.

Ɓangaren Inteesar ko suna barin gurin Hauwa'uh ta kalli Inteesar tace"nifa tsoro nikeji saboda nasan NAMIJIN DUNIYA baze taɓa barinkiba Inteesar meye danya watsamana ruwa".
"gaskiya duniya ba gaskiya wato shi bakiga abinda yayimanaba saboda yanada kuɗi seni nawa kika gani ba wani tsoronsa da zanji ai mutum ne shina kamar kowa kodon kina sonsa shiyasa kike kareshi".
"ba haka bane ƙawata kawaidai……".
saurin dakatar da ita Inteesar tayi tare da cewa"dame kikeso naji da baƙincikin gidanmu koko dana irin wa'innan watsatstsun mutanen da basusan darajar ɗan Adam ba".
"ya haƙuri ƙawata".
suna wannan zancen suka iso gidansu shiga gida tayi itama ta shige gidansu.

Kamar kullum Inteesar nashiga gida ta tadda su Uwar Gwarama da maƙarrabanta a tsakar gida tanata zuzzubs tsumi a roba wanda ta zabga uban flavour a ciki seka ɗauka tsumin arziƙine bakinta ɗauke da sallama tashiga ba wanda ya amsamata Inteesar tayi gurin Innah Uwar Gwarama ta duƙa cikin ladabi tace"Innah sannu da hutawa".
taɓe baki Uwar Gwarama tayi tare da cigaba da zuba tsuminta ba tare dataji haushiba ta miƙe tafara tafiya bazato taji su Ruƙayya da Bilki sun tintsire da dariya Bilki tace"dolema mutum ya rasa mashinshini tunda an riga angama badakai a waje".
"kema dai banda abinki waye zeje ya auri ragowar ƙarti yanaji yana gani da kuɗinsa".
"wallahi sede a ƙare abinsu waje ba'ah wannan hotel ba'ah wancan yawon karuwanci da sunan makaranta".
wata matashiyar yarinya ce tafito me tsananin kama da Inteesar tace"badai yayata ke yawon karuwanciba sede waccan".
ta nuna Uwar Gwarama dake zuzzuba tsumi nanfa Uwar Gwarama tashiga bala'i tana cewa"ƙarya akemata ai gaskiya suka faɗa inbanda ta tsaya yawon barikinta aida tini tasamu miji saboda kowa yasan metake aikatawa mijin aurema ya gagareta ba'ah taɓa zuwa nan gidan da koda sau ɗayane gurin Inteesar ba".
"hakane Iyah muma nan gida zamu barta danba mesonta".
suna cikin wannan maganar Abbansu ya shigo fashewa Uwar Gwarama tayi da kuka tashiga zayyanemasa ƙarya da gaskiya aiko yashiga jibgar Inteesar da Khadija seda yayi me isarshi sannan ya kyalesu.

AFTER ONE DAY

Sanye Abbah yike da Uniform ɗin masu shara sega wani me irin kayansa gaisawa sukayi yace"a'ah Ahmadu se yanzu kazo".
"a'ah na daɗe da zuwa ina bayane yanzu gashi inji Oga tin ɗazu yabayar yace abaka inkazo".
ansa Abbah yayi yana dubawa yaga takardar sallamace daga aikice sosai hankalinshi ya tashi yana ƙoƙarin tafiya office ɗin Ahmad Malam Ahmadu ya dakatar dashi tare da cewa"yace kar abarka ka shiga gurinsa".
sosai hankalin Abbah yaƙara tashi a wannan ranar duk yadda yaso dayaga Ahmad abu ya faskara dole haka ya tafi gida.

Jiki ba kwari haka Abbah yashiga gida tare da zama kusa da Uwar Gwarama jiki a sanyaye kallonshi Uwar Gwarama tayi tare da cewa"lafiya kashigo hannu na dukan cinya Malam".
"Ladidi an koreni a aiki".
Khadijat dake zagayowa dake zagayowa daka backyard ɗin gidan ce wani farinciki duk ya lulluɓeta da murnarta ta shiga ɗakinsu tana ƴan waƙe-waƙenta ɗago kai Inteesar tayi daga karatun Alqur'anin da takeyi tare da cewa"meyafaru naga kina murna".
"Abbah aka kora a gurin aikinsu".
"shine kuma kike murna".
"eyi ai gwarama da aka koresa daga aikin koba komai a dena banbantamu da ƴaƴan so shima yaji yadda mukeji a zuciyarmu na abinda yikemana kamar ba ƴaƴansa ba duk ya tsanemu ni wani lokacin har tinani nike anyako Abbah ne babanmu".
"Khadija meyasa kike irin wannan ne koba komai ai mahaifinmune kidena irin wannan inkuma ba hakaba zamu ɓata".
"yi haƙuri Aunty".!!!!!!

Votes and Comments
Plz share fisabilillah

*Dan Allah a tayani share*

_*Daga Alƙalamun ƴar Mutanen Gwarzo.*_
🌻 *THE WORLD MAN*
(NAMIJIN DUNIYA)



*MALLAKIN*
*REAL EESHOW*


HOME OF QUALITIES WRITERS ASSOCI…


*BOOK 1*


*PAGES* 0️⃣3️⃣➡️0️⃣4️⃣


Jiki ba kwari Abbah yamiƙe yaɗauki buta ya zagaya be wani jimaba segashi yafito yaƙara zama kusa da Uwar Gwarama baki buɗe Uwar Gwarama ke kallon Abbah sannan tace"amma dai gaskiya Malam se yanzu na yarda da zancen Uwani na cewa zuciyarka a mace take murus yo inbanda haka meyasa bazaka nace gurin wannan yaro arziƙinba kaji ba'asin abinda yasa ya korekaba se kawai ka yayo jiki ka tawo gida to wlh Malam ahir ɗinka dan tashi zakayi ka koma bazan riƙa ci dakai da wata ƙatuwa da ƴaƴanta ba akan wanne dalilin kamar kai nikeyiwa neman imma zaka tashi kaje kaji meke faruwa kaje danni bama zan iya cida me ƙashin tsiyaba wallahi wani yahana uwarsu yin sana'ah tace se ƴaƴanta sunyi karatun boko yanzu aisaci boko a wuta aikaga ko maga abinda bokon nasu ze tsinanamasu dukda bamma yadda bokon akeyiba ba babban bokoba wanda harka mutu baza'ah dena yimaka gori ba danni bame ɓatani ƴaƴana basu jawomun abun kunyaba na wata su jawomun haka kurum a'ah ba dani za'ayi wannan sa lallen kazarba atoh".
har Uwar Gwarama ta gama zazzage Abbah becemata ƙalaba yashafa sumar kansa tare da cewa"to a temakeni da abinci konaji sanyi a zuciyata".
wani banzan kallo da Uwar Gwarama ta makawa Abbah da sauri ya miƙe tare da washe baki yace"ya haƙuri bara inje ɗin".
"yadaifimaka ".
nan Abbah yafara tafiya daidai nan Wata matashiyar mata tayi sallama wadda bazata wuce shekaru42 ba jin Uwar Gwarama bata ansamata ba haka Abbah shima ta nufi ɗakinta.


Tana shiga Khadijana yiwa Inteesar kitso ta saki da sauri ta rungumeta tare da cewa"sannu da dawowa Ummah".
murmushi Umma tayi itama Inteesar ta rungumeta rungumesu tayi gabaki ɗayansu sannan tace"ko ni Aishatu zaku karyani ku sakeni inzauna".
murmushi sukayi gabaki ɗayansu suka zauna cikin farinciki Inteesar tace"ya aka baro su Halima".
"suna gaidaku".
cikin zumuɗi Khadija tace"Ummah kinsan wani abun farin ciki ko daya samemu kuwa".
cikin farim ciki Ummah tace"Auta meya samemu haka naga kina farin ciki haka".
kallonta Inteesar take da mamaki dan ita batasan meya samesu na farinciki da Khadija keta farin ciki hakaba tana wannan tinanin ta tsinkayi muryar Khadija na cewa"Ummah anfa kori Abbah daka gurin aikinsa kinji daɗin danaji kuwa ".
haɗe rai Ummah tayi tare da cewa"Khadija meke damunki ne haka da har kike farinciki dan an kori mahaifinki daga aiki ashe duk huɗubar danakemuku ke bata shiga kunnenki Khadija mahaifinku nefa kome yike yimana bekamata kiyi farin cikiba Khadija ".
"ai Ummah……".
saurin katseta Ummah tayi ta hanyar cewa"ya isheki haka a rayuwa duk wanda bashi da haƙuri baze kai labari ba kuma komai na duniya ɗan haƙurine watarana se labari komai kaga yasamu bawa da sanin Allah kuma komai muƙaddarine daga Allah ba'ah taɓa dawwama a abu ɗaya shiyasa kullum bani da abinda zancemuku sede kuyi haƙuri kunji shi haƙuri riba garesa".
Ummah na cikin yimusu magana Uwar Gwarama ta buɗe ƙofa cikin masifa tace"ga kayana can kije ki wanken".
ta wuce fuu Ummah takalli Inteesar tare da cewa"tashi kije kiyimata".
"toh".
zumɓurar baki Khadija tayi tare da cewa"saboda Allah Ummah duk gasu Bilki da Ruƙayya bazasuyiba se Aunty saboda itace karkatacciyar kukar gidannan me daɗin hawa haba".
"au bakiji nasihar dana gama yumuku ba kenan ko saboda kinada kunnen ƙashi ko".
Inteesar ta fita tsakar gida Khadija ma tabita tashiga tayata cikin kayan harda nasu Bilki da Ruƙayya hattana pant ɗinsu da suka gama period seda suka haɗa nan Inteesar tashiga wankemusu.


Kwance yike akan sofa ya lumshe idanunsa kamar me bacci a hankali ya buɗe idanunsa da suka yimasa nauyi yayi kana ganin fuskarsa zaka gane yanada damuwa tashi yayi ya nufi tanƙamemeb wardrobe ɗinsa ya buɗe ya zari wasu haɗaɗɗun ƴan kanti yasaka ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗi kanshi sannan ya ɗauki phones ɗinsa ya fita.


A hankali yike sakkowa daga stairs yana ɗaura gucci watch a hannunsa tunda ta ɗaura idanunta akansa ko ƙiftawa batayi harya ƙarasa sakkowa cikin takunsa kamar yana tausayin ƙasa yaƙarasa sauka ya nufi falon Haneefa ce zaune ita kaɗai cikin wasu english wears riga da wando rigar kusan rabin ƙirjinta a waje fuska tasha heavy make-up kamar ga atarch yare-yare da murmushi tace"morning sweetheart".
Abdallah(Namijin duniya) kallo ɗaya yayimata ya ɗauke kansa gefe yaƙara haɗe rai kamar wanda aka aikomasa da mutuwa yace"lfy what of you".
"lafiya ƙlau".
ya miƙe ya nufi ƙofa ɓangaren granny ɗinsa ya nufa yana shiga ya tadda Abbih ɗinsa da Mummy zaune ƙarasawa yayi bakinsa ɗauke da sallama ƙasa-ƙasa taɓe baki Innah tayi tare da cewa"yaudai ban dafa abincina dakaiba dunkum dangin tsaka atoh inma zakaci abinci da Mamanka tayi kaci dan bazan bakaba".
dariya Mummy tayi tare da cewa"rabu da ita Son ai se inbaka nawa".
murmushin gefan baki yayi ya zauna tare da cewa"ina kwananku ".
"lafiya ƙlau Son yaka tashi".
"lafiya ƙlau Abbih".
"masha Allah".
miƙewa Abbih yayi tare da cewa"Ammi ni zan wuce inada wani meeting".
"to Allah ya tsare".
"Ameen ya Allah Son seka fito".
"toh Abbih".
nanya fita Mummy ta miƙe tace"Ammi se anjima Son seka dawo ".
"toh"
yafaɗa a daƙile Mummy washe baki Ammi tayi tare da cewa"toh Fatimah Allah yayimiki albarka".
"Ameen".
nanta tafi murmushi Abdallah yayi ganin Ammi ta kauda kanta gefe yaƙarasa gurinta tare da cewa"Ammi an tashi lafiya".
"da ban kwanaba ka ganni zaune kamar duniya ne".
murmushi yayi yace"Ammi tuba nike ayi haƙuri".
"aini tunda kaƙi jin maganata nabarka da halinka ace yaro kamar wanda akayiwa mugun abu bakason yin aure anjuma nan zan shirya inje gidan aminiyata inma wani abun akayimaka naji dan bazan bari a cuci jikana kwalli ɗaya ba a duniya atoh bara in zubomaka abinci inshirya ku ajeni gidan Ta Annabi ina dalili ina ɗan mafari a sabautamun jikana ga abokinka har zeyi aure nanda sati biyu amma kai shiru akeji ".
bece komaiba a ta wuce a zuciyarsa yace"hmm Ammi bazaki gane abinda ke damuna ba a duniya ba macen da zata yarda ta aureni matsawar tasan meke damuna".
yana wannan zancen Ammi ta fito ta ajemasa plate ɗin irish kaɗan yaci ya miƙe tare da kallon agogon hannunsa yace"Ammi sena dawo bara se su Muhd su kaiki ni kuma na wuce inada meeting".
"toh seka dawo".
nanya fice ta taɓe baki tare da cewa"imma wanine yasamun hannu agun jikana zanji koma meye".
nanta tafi ɗaki ta shirya ta fita suka tafi.


Yana fita ya shiga mota suka fara tafiya har sun ɗauki hanyar gurin aikinsu ba tare daya buɗe idoba yace"Hospital zamu".
"toh Oga".
nan suka canza akalar motar suka nufi wani katafaren asibiti suna isa ya zagaya ya buɗemasa nanya fita cikin takunsa na isa harya isa ciki ya nufi office ɗin doctor Muhseen murya can ƙasa yayi sallama ya shiga murmushi ɗauke a fuskar doctor Muhseen yace"sannu da shigowa".
"yauwa".
Namijin duniya yafaɗa tare da zama kan kujerar dake kusa table ɗin Muhseen ya miƙamasa hannu suka gaisa bayan sun gaisa Doctor Muhseen ya ɗakko wata farar leda tare da miƙawa Namijin duniya ya ansa cikeda kulawa Doctor Muhseen yace"bara inɗakko maka water seka sha".
"ohk".
nanya ɗakko mishi ya buɗe drugs ya buɗe bottle yasha sannan ya miƙe yace"se anjuma".
nan ya fita be jira amsar doctor Muhseen ba wani irin tausayin Namijin duniya ne yakama doctor Muhseen a hankali ya furta "Allah na sane dakai Abdallah insha Allahu Allah ze baka lafiya kamar ko wanne mutum".
nanya nutsatsa yana tinanin Allah yabawa Namijin duniya komai amma Allah ya rageshi da wata babbar ƙaddara megirma yace"insha Allahu Abdallah zaka cinye wannan jarabawar".
jiki a sanyaye ya cigaba da cike files ɗin dake gabansa.


5:00pm

Zaune Abdallah yike yana danna phone ɗinsa kallo ɗaya zakayimasa kasan tinani kawai yikeyi a guest house ɗinsa Ahmad ya buɗe ƙofar falo har ya ƙaraso inda yike Namijin duniya kasan cewa yayi zurfi a cikin tinani domin ko sallamar da Ahmad yayi be amsaba taɓashi Ahmad yayi da sauri ya ɗago ya kalli Ahmad dafashi Ahmad yayi tare da cewa"Abdallah meyasa koda yaushe kakeson ɓoyemana damuwarka ne tin muna yara baka da abokan da suka fimu inbaka faɗamana damuwarkaba wazaka faɗawa".
sauke numfashi Namijin duniya yayi tare da cewa"bakomai Ahmad inda dashi dana faɗamaka".
"ohk to meyasa kasa na kori mutum haka kurum ba dalili dafa wannan aikin sukecin abincifa shida iyalansa".
sauke numfashi Namijin duniya yayi tare da labartawa Ahmad komai da Inteesar tayi masa murmushi Ahmad yayi tare da cewa "haba My Man aiba haka yakamata kayiba ai kan yarinyar yakamata ka huce ".
kallonsa namijin duniya yayi alamun yana san sanin mezaiyi mata murmushi Ahmad yayi tare dakai bakinsa saitin kunnensa yayimasa raɗa wata magana wadda nima kaina Real eeshow bansan meya faɗamasa ba lokaci ɗaya namijin duniya yasaki wani murmushin gefan baki tare da furta "amma Ahmad kana ganin ba raini a wannan shawarar taka kuwa ?".
"wanne irin raini My Man ai wannance kawai hanyar da zaka rama kenan a ganina".
shiru Namijin duniya yayi kafin daga bisani ya saki wani ƙayataccen murmushi saboda se yanzu yagane abinda Ahmad yike nufi cikin jindaɗin shawarar Ahmad ya furta "shiyasa nike
ƙara ƙaunarka saboda kai akwai kawo light".
dariya su dukansu sukayi sai a sannan namijin duniya yaɗanji ranshi yayi sanyi nan suka koma hirar bikin Adam daga bisani Ahmad ya ɗaga waya yayi sai kuma ya aje naga yayi murmushi
Babu ɓata loƙaci sakataren Ahmad yashigo shida wani ɗan dattijon mutum abayansa.



Zama sukayi a ƙasan carpet cikin girnamawa sakataren Ahmad yace"ranka yadaɗe gashinan".
"ohk we can go".
nan yafice yabarsu da Abbah daketa ƴan kalle-kalle saboda tinda yike bai taɓa ganin tsararren guri ba kamar wannanba saboda falon yagaji da haɗuwa komai na more rayuwa akwaisa a falon gefe guda kuma tanƙama-tanƙaman photunan Namijin duniyane a kowanne bango na falon
dakyar ya ɗauke idanunsa daga kalle kalle yamaida ƙasa cikin rawar jiki ya gaishesu Ahmad ne kawai ya amsa namijin duniya kuwa kallo ɗaya yayi masa yakauda kai ya taɓe baki a zuciyarsa yace"dama wannan ne mahaifin dirty girl ɗinnan yarinyar nan mara tarbiyya dubeshi wani iri".
yana cikin wannan zancen zucin yaji Ahmad yace "dama abinda yasa kaga
na sallameka agurin aiki babu laifin dakayi dama wata sabuwar dokace tafito mun dena ɗaukar tsofaffi da wa'inda basuda kwalin degree amma idan kana da wanda zaka kawo mai kwalin degree tom ka kawo sai yamaye gurbinka ko mace ko namiji amma bada Comphany ɗina za ai aikiba na Namijin duniya ne zasu ɗaukesa".

Cikin farin ciki yaɗago ya kallesa yana washe baki Abbah yayi tare da cewa"to ranka yadaɗe Allah yasaka da alkhairi nagode Allah yaƙara arziƙi amma banida wani namiji dayayi wannan karatun sai dai mace zan iya kawota?"
Murmushi Ahmad yayi tare da cewa "ai babu komai Baba kakawota inhar tana da degree".
shiru Abbah yayi daga bisani yace"ammafa wani hanzari ba guduba ita da ƙawarta suke komai Alhaji Zannah ne yayiwa yarinyar tawa komai be kamata na samarwa tawaba itakuma tashi nayi musu hakaba koba komai be taɓa ware tawaba abawa tashin kawai se a kyale Inteesar ɗin".
damm ƙirjin Namijin duniya yabayar daketa shan ƙanshi jiyayi kamar yasamusu baki amma saboda tsabar girman kai da izza bazaka gane yaji wani abuba yacigaba da operating ɗin phone ɗinsa jiyayi Ahmad yace"a'ah Babah ka kawosu kawai gabaki ɗayansu a kawosu sesuyi interview in Allah yakaimu gobe".
Wani farincikine ya lulluɓe Abbah nan yadungi zabga godiya yatafi yana tafe yana murna ganin aikinsa yadawo bai suɓucemasa ba.


Murmushi namijin duniya yayi wanda shikaɗai yasan ma'anarsa yabawa Ahmad hannu suka kashe Ahmad yace"to tazo hannu saura plan ɗinmu na biyu ita harta isa taja da ɗaya daga cikin ɗan cliff ɗinmu Tripple A saura shawarar Adam shima aji tabakinsa daganan semuyi tsare-tsaren biki".
"toh tashi muje".
nansuka tafi yayinda ran Namijin duniya yayi fess ji yike kamar yajawo gobe tayi.



Washe gari
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment