Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

13/12/2019 à 20:33 - Les messages envoyés dans ce groupe sont désormais protégés avec le chiffrement de bout en bout. Appuyez pour plus d'informations.
13/12/2019 à 20:33 - Vous avez créé le groupe “💑KALLON KITSE💑”
13/12/2019 à 20:34 - Vous avez retiré Sis Meerah
13/12/2019 à 20:35 - Vous avez changé l'icône de ce groupe
21/12/2019 à 15:34 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑



_SAMIRA HAROUNA_


*Littatafan marubuciyar*


*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._


*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAREN GIDA)*


🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛


_Na karb'i uzurin uwaren gida wannan karan, na kuma fahimci kukan su, sun ce kullum in dai labari ya biyo tsakanin miji da matan shi biyu, to sai marubuta sun yi k'ok'ari sun nuna uwar gida ce marar kirki, a k'arshe sai amarya ta mallake mijin, alhalin kuma a zamanin nan yanzu ba haka bane, dan haka dan Allah mu gyara, zaiyi wuya ace kullum uwar gida ce marar mutunci, duba da dayawa daga cikin maza sai sun k'ara auren ma su ka gane kirkin matan su na farko, ba ma miji kad'ai ba har da dangin shi, dan haka ku share hawayen ku, *Samira* za ta cika mu ku zuciyar ku da farin ciki, a matsayin ta na uwar gida ita ma uwar katarere😉, su momyn Dady *d'ogalawa* ne😂, ku biyo ni muji wa ake wa kallon kitse ne._


```Fatan alkairi masoya```


_Bismillahir rahamanir rahim_


*1*



Cikin kuka ta cire glishin (glass) idon ta ta kalle shi tace " Abban *Bilal* me na yi ma ka? Wane laifi na aikata da har za ka hukunta ni ta hanyar yi min kishiya? Abban Bilal ka dai na so na ne ko me? Me na rage ka da shi da har za ka k'ara aure a wannan lokacin? *Shekara goma sha uku* mu na tare da kai, ba ka k'ara aure ba sai yanzu, sai yanzu da na fi buk'atar ka a kusa da ni? Me ya sa? Me ya sa za ka k'ara aure? Ka gaji da zama da ni ne? Ko kuma dangin ka ne su ka saka ka k'ara aure, saboda har yanzu ban k'ara..."

Yasan me za ta fad'a, dan haka ya yi saurin rufe mata baki, manna kan ta ya yi a k'irjin shi ya na shafa bayan ta ya na fad'in "Haba Momyn Bilal, me ya sa za ki bari har shed'an ya shiga zuciyar ki ya rik'a raya mi ki wannan tunanin? Ni na fad'a mi ki kin min laifi? Ko kuma na fad'a mi ki zan k'ara aure ne saboda na dai na son ki? Haba dan Allah, ki nutsu mana, sannan ki saurare ni, ta hakane kad'ai za ki fahimce ni."

Da k'arfi ta d'ago daga jikin shi tace "Fahimta? Na fahimce kama ka ke cewa? Ai ni da k'ara fahimtar ka kuma har abada, ka riga da ka ruguza yarda da fahimtar da na ke ma ka a baya, Abban Bilal, wallahi ba zan sake sauraren ka ba, ka cuceni, ka zalunce ni, tsawon shekaru na d'auka ina rayuwa a k'ark'ashin yaudarar ka, kullum ka na fad'a min ni kad'ai ka ke so, ba ka da sha'awar k'ara aure a rayuwar ka, ba ka da wani dalilin da zai sa ka k'ara aure, amma shine yanzu za ka zo min da wai za ka k'ara aure, lallai, sai yau na yarda da ake cewa namiji ba d'an goyo bane, kuma duk macen da ta rik'e namiji uba, to tabbas za ta mutu marainiya, gashi na ga zahiri."

Ganin yanda take kallon shi ya san ba ta ganin shi da kyau saboda lalurar ta, dan haka ya d'auki glishin da ke gefe ya fara k'ok'arin saka mata, buge hannun shi ta yi ta zauna kan kujera ta na fad'in "Rabu da ni, macuci kawai."

Da tsantsar mamaki ya kalle ta har ya zauna kusa da ita, ba tare da ya daina kallon ta ba yace "Dan Allah Momyn Bilal ki daina kukan nan, kinfi kowa sanin matsalar ki, dama ya lafiyar idon ki, bare kuma ki na irin wannan kukan, ki daina dan Allah, kinsan kukan ki ya na matuk'ar tab'a zuciya ta, wallahi ba na son ganin zubar hawayen ki ko da na farin ciki ne, da kinsan irin rad'ad'in da na ke jin a game da zubar hawayen nan na ki, to hak'ik'a da kin tausaya min kin share hawayen ki, sannan ki saurari mijin ki."

Cikin share hawaye tace "Ai da kan ka ka je ka ciro min tikitin (ticket) kuka, sannan da hannun ka kama nawa hannun ka d'ora ni a motar tashin hankali, *Usman* wallahi ban yi tsammanin haka daga gare ka ba, ama shine har ka ke wani cewa wai na daina kuka, humm."

Jingina bayan shi ya yi ga makekiyar kujerar cikr da nuna damuwa yace "Assha, ban zaci haka daga gare ki ba, gaba d'aya na ji na rasa k'arfin gwiwar da na shigo da shi gidan nan, gaba d'aya na ji na tsani kai na, na ji ina ma mutuwa ta d'auke ni kafin wannan ranar, ni *Usman*, ni ne yau na yi silar zubar hawayen mata ta, abar alfahari na, farin ciki na, kwanciyar hankali da nutsuwa ta, kuma uwar d'ana mafi soyuwa a zuciya ta, tabbas yau d'in nan na ji kamar rayuwa ta ba ta da anfani, macen da na ke matuk'ar so fiye da komai, wai yau ita ce ta ke kira na da macuci, macen da na ke d'aukar farin cikin ta da mahimmanci, yau ita ce ta ke kira na da azzalumi, macen da bayan mahaifiya ta, ita kad'ai ce na fi d'auka da mahimmanci, amma ita ce ta ke kira na da mayaudari, macen da na ke d'aukar addu'ar ta gare ni tamkar addu'ar mahaifiya ta, amma ita ce ke cewa na yankar mata tikitin kuka, matar da na ke da yak'inin rayuwa ta ba za ta tab'a moruwa ba idan babu ita a tare da ni, ita ce ke k'ok'arin ruguza farin cikin gida na."

D'agowa ya yi daga jinginar ya na kallon ta yace " *Nana Khadija* ta da na sani, ta na da hak'uri, ta na yakana, ta na da fahimta, sannan ta na da uzuri wa mutane, haka ma ta na son duk abin da na ke so, da zan ce wannan abun bak'i ne alhalin fari ne, to ba musu Khadija za tace tabbas bak'i ne, ko da kuwa za'a yanka ta ba za ta sauya maganar ta ba, dan haka ni ba zan bar wannan hawayen na ki su ci gaba da zuba ba, ni mai son ki ne har kullum, k'auna kuma ba k'arya ba ce, dan haka Nana Khadija ta na fara *auren nan*, in dai har auren da zan yi shine silar fara shiga damuwar ki, to na fasa har abada."

Tun da ya fara magana ta ji jikin ta ya yi sanyi, maganganun shi sun tab'a zuciyar ta sosai, amma sai ta kasa kallon shi saboda kunyar da ta rufe ta, a hankali ya dafa kafad'ar ta ya kwantar da ita a kan k'irjin shi ya na ci gaba da shafa ta ya na fad'in "Abu d'aya da banji dad'in shi ba, shine rashin samun yardar ki, na yi mamaki da takaici da ki ka kasa fahimta ta, ban ji dad'in yanda ki ka rufe idon ki ba ki ka k'i saurara ta, na so ace kinfi kowa sanin mijin ki, na so ace kin fahimci zan k'ara aure ne ba dan na gaji da ke ba ko dan na wulak'anta ki ba, kamar yanda na sha fad'a mi ki kuma yanzu ma zan sake jaddada mi ki, Khadija ba na da burin had'a ki da wata mace a duniyar nan, kin gama min komai a rayuwa ta, kin mayar da ni cikakken namiji, kin bani farin cikin da duk na ke buk'ata, hankali na ya na kwanciya idan har ina tare da ke, idan har ki ka ga na yi aure to Allah ne ya tsare haka, kuma kinsan duka abin da Allah ya hukunta babu mahalukin da ya isa ya tsallake shi ko ya canza shi, amma tun da na ga kin kasa fahimtar hakan, maganar aure na rushe ta saboda farin cikinki, dan dama ba wai zanyi bane dan ina son haka d'ari bisa d'ari, zanyi ne saboda sunna ne, kuma ina sha'awar samun ladar da ake samu ta ciyarwa."


_Me ku ka ce masoya, ta yi farin ciki? Ko kuma ta hak'uri ayi kawai?._


*Sai mun had'u a shafi na gaba.*
26/12/2019 à 11:32 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑



_SAMIRA HAROUNA_


*Littatafan marubuciyar*


*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._


*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*


🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛


```Fatan alkairi masoya```


_Bismillahir rahamanir rahim_


*2*



D'agowa ta yi daga jikin shi ta na kallon shi a dishi-dishi, karb'ar gilashin ta ta yi da har yanzu ya ke hannun shi ta mak'ala a idon ta, tarau ta gan shi ta ciki dan haka ta kamo hannun shi ta na murzawa tace "Ka sa na ji kunyar kai na, Abban Bilal na hak'ura, ba zan so ka fasa aure ba a kai na, idan na yi haka na zama azzaluma kuma mai son kan ta dayawa, sannan fasa auren na ka zai iya janyo matsaloli da dama, daga ciki kuwa har da dangin ka, dan za su zarge ni, ni kuma ba zan so haka ba, dan haka na amince ka k'ara aure, na san ba za ka wulak'anta ni ba, duk da dai ina d'an jin tsoron yan matan yanzu, amma ina fatan ka mana zab'i na gari, ba zab'en tumun dare ba."

Murmushin gefen labb'a ya yi yace "Na riga da na yanke hukunci, na san kin amince ne saboda kawai ki faranta min rai, ni kuma ba na son tursasaki a kan abin da ba kya so, dan haka ya wuce kawai."

Da sauri ta gyara zama ta na fuskantar shi tace "Haba aljanna ta, ni fa na ce na amince, wallahi babu takura a ciki, wani k'aramin rashin fahimta ne, kuma sai ga shi cikin ikon Allah fasihi kuma nagartattacen miji na ya fahimtar da ni, dan haka in ba so ka ke na maka kuka ba kawai ka amince."

Yanda ta k'arashe maganar cikin shagwab'a ya birge shi, dan haka ya rumgumo ta jikin shi ya na dariya, cikin so da k'auna ya ci gaba da rarrashin ta tare da saka mata albarka, tambayar ta ya yi "To yanzu ina so ki fad'a min duk abin da ki ke buk'ata, ni kuma insha Allah zanyi mi ki shi a matsayin tukuici da kuma fad'an kishiya."

Kasancewar ta mace mai yawan shagwab'a da son jiki ya sa ta turo baki gaba ta kwanta a kafad'ar shi tace "Kaji ka da wata magana, ai ni yanzu ba kai ne za ka min hidima ba, ni ce ma zan bayar da tawa gudunmuwar."

"Ban yarda ba, sai kin fad'a, in ba haka ba kuma zan kama ki ne."

Yanda ya yi maganar cikin sigar rausaya ya sa ta tashi ta nufi d'akin ta ta na fad'in "Na k'i wayon, ka kamani d'in."

Ya na jin haka ya tashi da gudu ya nufe ta, ita ma a guje ta k'arasa shiga d'akin, kasancewar Bilal na wajen kakannin shi (iyayen Khadija) ya sa su ka saki jiki sosai su ka more rayuwar su, dan dama kusan kullum haka su ke.

*Washe gari* kamar kullum misalin *09:30* su ka gama shirin fita, har farfajiyar gida su ka isa tare, ita ma kuma cikin shirin fita ta ke, sai da ya shafi lallausan kumatun ta tare da sumbatar ta kafin yace "Ni zan wuce, ki kula min da kan ki, sannan ki gaishe min da su Mama, tun da ba za ki bani damar da zan kai ki da kai na ba bare na gaishe su."

Masha Allah, duk da cikin gilashi ne ta waina idon ta, amma bai hana su d'aukar hankalin Usman ba, saboda girman idon da kuma farin su tamkar madara, cikin wasa da idon ta ne tace "Na shiga uku, da alama sai an shekara d'ari ka na min gorin wannan maganar."

"Ai dole ne, dan na lura kamar ba kya so na je na kwaso albarka wajen Mama, sannan na sake mata godiya da ta bani ke."

"Gashi kuma ba kya gajiya da godiya kullum."

"Ni kam ina zan gaji da godiya, duk wanda ya baka yar sa ka aura ai ya gama ma ka komai, bare kuma mata irin ki Khadija, ai har duniya ta nad'e ba zan daina mu su godiya ba wallahi, dan na san sun fini sanin ki, amma kuma hakan bai hana su ka rabu da ke ba su ka bani ke, duk da kuwa sun san ba zan tab'a rabuwa da ke ba in ba mutuwa ce ta raba mu ba."

Ajiyar zuciya ta sauke tace "Idan har na biye ma ka, to hak'ik'a zan tabbata anan ban tafi in da zan je ba, dan haka sai an jima, nima ka gaishe min da Mama na da Abba na, tun da ka k'i bani damar bin ka bare na gaishe su."

Ta na fad'a ta juya ta na dariya shi kuma ya na fad'in "Au! Ramawa ki ka yi? Shikenan ai zan kama ki."

Gwalo ta masa tace "Ka kamani d'in, kafin nan na san in da na kai."

Wata tsandareriyar mota ta shiga bla (bleue) shi ma haka, sai dai ta shi bak'a ce, kowa hanyar da za ta sada shi da na shi iyayen ya nufa, dan su dama a *zarya* su ke, bayan masallacin *sahaba*, Khadija gaba ta yi saboda gidan su na gaban sabon gidan mota na *Rimbo*, shi kuma Usman gidan iyayen shi ya na nan *sabon gari* a 'yan *banana* (🤸‍♂aradu unguwar mu).


Ko da ya isa mahaifiyar shi kad'ai ya samu a gidan, dan haka su na gaisawa ya d'auko maganar auren shi, tambayar da ta fara mi shi ita ce "Khadija ta sani?"

"Eh Mama, ta sani, kuma ta bada goyon bayan ta d'ari bisa d'ari, yanzu amincewar ku na ke buk'ata."

Cike da kamala tsohuwar tace "Ba ka da matsala da amincewar mu *Fodio* (sunan mahaifin ta ne, dan haka ta ke ma sa inkiya da Fodio), tun da dai har ka shirya, kuma ka na ganin ba wata matsala, sannan matar ka ma ta amince ba tare da tashin hankali ba, ai ka ga Alhamdulillah, sai dai kawai mu bika da addu'a da kuma fatan alkairi."

"Nagode sosai Mama, Allah ya k'ara lafiya da girma, yanzu kenan idan Abba ya shigo za ku iya magana da su, duk yanda ku ka yi zuwa dare idan na dawo na ji insha Allah."

Kasantuwar shi d'an fari ya sa ko ido ba ta son had'awa da shi kamar ta na jin kunyar shi, ba tare da ta kalle shi ba tace "Shikenan ba damuwa, insha Allah zan fad'a ma sa."

D'an gyara zama ya yi alamar zai tashi yace "Mama babu wata matsala ko wani abun da ku ke buk'ata?"

"Ah, Fodio kai ne za ka bar gidan nan da wata matsala? Ai sai dai in ba ka raye, Alhamdulillah wallahi babu komai, Allah dai ya yi albarka, Allah ya sa ka gama da duniya lafiya."

Sai da ya durk'usa k'asa ya amsa da "Ameen Ameen Mama, nagode sosai da addu'ar ki gare ni, ni zan wuce sai anjima idan na dawo."

"To Allah ya yarda, Allah ya tsare, ka gaishe min da waccen mutumin."

Dariya ya yi yace "Watak'ila fa gobe ku gan shi gidan nan, dan mahaifiyar shi ta tafi d'auko shi."

Cikin wasa irin ta kaka da jika tace "Ka ce mi shi ma kar ya kuskura ya zo in har ya san ba zai taho da k'atuwar bak'ar leda ba."

"Zai zo da ita Mama, ai kin san shi da k'ok'arin cefanai."

"Ko dai k'ok'arin jefawa a ciki ba."

Da wannan wasan ya bar gidan zuciyar shi sakayau da ita kamar kullum, dan har abada babu abin da ke dagula mi shi lissafi, b'angaren mace, Allah ya wadata shi da mata kamar Khadija, babu abin da ya nema a gurin ta ya rasa, haka ma iyaye, Allah ya bashi iyayen da su ke son abin da ya ke so, sannan su ke nusar da shi tare da kora shi da addu'a a kullum, hakan na sa shi farin ciki , kuma shima ya na k'ok'ari sosai wajen sauke hakk'ok'in duka b'angarorin, haka ne m'a sanadiyar da ta sa kullum ci gaba ya ke gani babu komawa baya ko rashin nasara, dan Allah ba ya kunyatar ko tab'ar da wanda ya kiyaye hakk'ok'in wannan mutanen a duniya.

Khadija ma a gidan su farin ciki ta ke kamar ba ta farin ciki a gidan ta, hakan kuma ya samo asali ne sakamakon samun kan ta da ta yi a tsakiyar mahaifiyar ta da kuma d'an ta, sai sauran matan yayyun ta da kuma 'ya'yan su, bayan sun ci abincin rana yan uwan ta maza su uku su ka shigo gidan, anan ta tara su kuma ta fad'a mu su auren da mijin ta zaiyi, ta gaggauta fad'a mu su hakane saboda ta san sune za su iya bata shawara mai kyau wacce ta dace, kuma kamar yanda ta yi tsammani hakane ya faru, sosai su ka kwantar mata da hankali tare ja mata kunne da nasihohi ma su shiga rai, tare da kafa mata misali da matar babban yayan ta wanda da zai k'ara aure ta tashi hankalin kowa, a k'arshe dai sai da ta bar gidan, yanzu gashi nan sai amaryar ke rayuwar ta a b'angaren na su, abin da ba ta son ganin shi ke faruwa a bayan idon ta kuma ba yanda za ta yi, ga yayan ta ma su na hannun uban su sai yaga dama ya ke barin su su je wajen uwar, saboda hure mu su kunne da ta ke, hakan ya k'ara saka jikin Khadija yin sanyi, kuma ta yi niyyar yin aiki da shawarwarin da su ka bata, a haka ita ma ta yi yammacin ta tare da maman ta abar k'aunar ta, zuwa *5:30* na yamma kuma Bilal ya d'auki kayan shi su ka wuce tare da maman shi a motar ta.

Su na isa gida Bilal ya wuce da yan kayan shi d'akin shi tare da canza na jikin shi, ita ma kaya ta sauya ta wuce madafa dan sarrafa abin da za su ci da dare, tare da Bilal su ka shiga ya na kama mata duk aikin da ta ke yi, sai da aka gama sallah magrib ta gama lokacin Bilal ya wuce masallacin da ke had'e da gidan su, ta na gama ajewa a mazaunin cin abinci ta yi wanka ta shirya cikin riga da zane wanda su ka d'auke jikin ta sosai, kasancewar babu wata tazara mai tsayi tsakanin sallah magrib da isha'i ya sa ta yi sallahn ta, ta na kammalawa ta fito falon ya yi daidai da shigowar Bilal daga masallaci tare da baban shi.

Ta na ganin shi ta tashi tsaye ta turo baki tace "Sai yanzu za ka dawo min gida? Ina ka shige haka?"

Kallon Bilal ya yi yace "Yau salon gaisuwar maman ka kenan? To ka fad'a mata ba zan amsa ba."

Ita ma Bilal ta kalla tace "To ka fad'awa Abban ka ya juya ya koma in da ya fito, dan ba ya da muhalli a gidan nan yau."

Dariya ya yi ya kalli Bilal yace "Ka tambayar min ita kaji, wai dama ana korar mutum da gidan sa?"

Da shu'umin murmushi a fuskar ta tace "Ka fad'a ma sa sau nawa aka yi, idan kuma bai tab'a gani ba to yau zai faru a kan shi."

Bilal da ya saki baki ya na kallon su dukan su ne ya matso kusan maman shi ya rik'e hannun ta yace "Momy dan Allah ni dai muje ki zuba min abinci na ci yunwa na ke ji."

Dafa kanshi ta yi tace "Muje ka ji yaro na, kai da gidan ku."

Sun juya za su wuce ta ji ya rik'o hannun ta, juyowa ta yi su ka kalli juna, murmushi ta masa tace "Ina so na rumgume ka, zuciya ta bugawa ta ke da k'arfi."

Jan hannun ta ya yi su ka nufi d'akin shi, Bilal na ganin haka ya k'arasa shi kad'ai ya zuba abincin ya fara ci, dan ba zai iya jiran su ba, su na shiga d'aki su ka k'wak'wume juna kamar sun shekara ba su had'u ba, sumbatar ta ya ke tare da fad'in "Na yi kewar ki sosai, wuni d'aya ba mu had'u ba alhalin ina cikin garin nan, gaskiya ba zan k'ara nesanta kai na da ke ba."

Da k'yar dai su ka rabu ta taimaka mi shi ta cire ma sa kayan ta mi shi wanka kafin su ka fito, zaune ya yi ta zuba mu su abinci a faranti d'aya, amma
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment