Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

*_FARHATAL-QALB!!!*_
_(FARIN CIKIN ZUCIYA)_
💕

*NA*


*NANA_HAFSAT*
(MX)


WATTPAD: MISSXOXO00
AREWABOOKS:MSSXOXO

#ZAFAFABIYARWRITERS2022
#PAID NOVELS!!


بِسْمِ اللهِ الرَّحْمنِ الرَّحِيمِِ

×WANNAN LITTAFI KIRKIRARRE NE, SUNAYE, GARURUWAN CIKI DA DUK MA ABUBUWANDA LITTAFIN YA KUNSA MAFI YAWA KIRKIRARRU NE. WASU DAGA CIKI KUMA TA IYAYIWUWA ANYI HAKAN A GASKE. IDAN HAKAN YAYI KAMA DA RAYUWAR WANI KO WATA. INA NEMAN AFUWA. RASHIN SANI NE, IDAN NAYI KUSKURE INA NEMAN YAFIYA, SANNAN BAN YARDA A JUYAMUN LITTAFI NA TA WATA HANYA BA BATARE DA AN NEMI IZINI NA BA. YOUTUBE BLOGGERS, PRODUCERS. DA SAURAN MASU AMFANI DA RUBUTAN MARUBUTA. KADA A SO MA DAUKA MIN LITTAFI AYI AMFANI DASHI BA TARE DA AN NEMI YARJEWA TA BA. HAKKI NA NE, MALLAKATA CE. COPYRIGHT VERSION NE. KARKASHIN JAGORANCIN ZAFAFA BIYAR WRITERS💯♥️


××ו.
××ו.


*PAID BOOK*
*FREE PAGES: 1-5*


*FREE PG: 1*

×NEW G/R/A SHURAH××


*A* nutse take tafiya kanta a kasa, Sanye cikin uniform ruwan sararin samaniya. Yayin da hijabin da ke jikinta fari ne qal da shi. Kafafunta sanye cikin sandal takalmi daya gaji da dinkin zare. Yayinda kafafuwan ta ke cikin safa fara.

Sai yar jakar goyo ta buhu mai igiya. Idanuwanta na cikin gilashi da alama na kara gani ne wato medicated. Ita da kayan da ke sanye jikinta komai a tsaftace yake.

Uniform din sun sha ninkin guga ko ina tsaf tsaf da shi. Cikin sassarfa take tafiyar komawa gidah.

layin shiru. Tsit! Sai kukan karnuka da na kanari. Ko'ina jibga jibgan gate ne. Ya yinda masu gadi ke kofar gidajen da suke gaadi. Su na hira.

Manyan motoci na faffake a kofar gidajen. Dake dauke da shuka da dama. Iska mai ratsa jiki da bargo ce ke faman kaada bishiyu.

Manyan idanunta dake cikin gilashi ta sauke akan signboard/Tambarin da ke rubuce da: The Adams Family!!

Saurin wuce wa tayi har tana tuntube. Domin ba zata taba mantawa da gigitaccen marin da me gadin gidan yayi musu ba itada kawayenta ranar wata jumu'ah da sakaliya.

Gaban ta na tsananta bugawa ta fi ce daga cikin layin mai dauke da tankamemen gate mai nishi. Layi ne na masu hannu da shuni. Wato masu kudi.

Tana ficewa daga layin ta sauke nannauyar ajiyar zuciya. Kana ta cigaba da tafiya zuwa layin gidan su. Kallo daya zaka yiwa unguwar tasu kasan ta marasa hali ce. Tulin shara mai tsananin tashin hankula ce a gefen wani bingi da suka mayar wajen zubar da shara.

Ya yinda yan jari bola ke kan bolar suna tsince tsincen su. Wanda baki daya yaran unguwar ne ta:


××UNGUWAR SHURAH××


Jerin wasu mata tsofaffi ne ke gefen wani tsauni. Sanye cikin riga da zani da dankwali kowanne daban daban. Sunyi butu butu da su suna shiqar masara, Maiwa, Dawa, Gero da kuma masara.

"Ke zo nan wahidin. " Cewar wata tsohuwa take cikin tsofaffin da ke shiqa.

Da sauri ta karasa duk kuwa da kasan zuciyaar ta bata kaunar sunan da Marka kakar su ke kiran ta dashi. Sarai tasan yadda sunanta yake. Amman taki ta kirata da ainihin sunan. Sai ta boye shi cikin wata manufa dake kasan zuciyar ta.

"Ina wunin ku. Ya aiki?" Ta tsugunna har kasa tana gayshe da su baki daya.

"Lapia kalau Waheedah. An taso ku ne kika dawo da wuri haka?" Cewar lawuri aminiyar kakar su Marka.

Girgiza kai kawai tayi. Ahankali tace,

"Kudin makaranta ne ban biya ba."

"Ungo rike ki karasa. Idan kin gama kije ki wajen Na'Ateeku ki ce ya baki sakon."

"Tohm Marka.." Ta amsa, Tare da matsa wa suka ketare ta suka wuce. Har takalmin Marka kasan ya gogi hijabin jikin ta.

Yayinda ta dauki kwaryoyin ta shiga dagawa sama daya kasa daya. Iska na dauke dattin....

Haka ta jima tana shiqar kowanne. Ta kammala tukun sannan ta dure kowanne a buhu bayan ta a'aauna.

Uniform dinta ya rine da kura. Hakama gilashin idanunta da kurar ta dabaibaye shi.

Wajen shagon Na'Ateeku ta nufa. Tana zuwa ta tsaya daga gefen shagon bayan ta gayshe shi.

"Marka ce ta aiko ni..."

"Eh na shi na . " Yana magana yana jan kasan leben sa. Ya dakko leda baka ya saka taliyar kakkaryawa guda daya da tumatirin gwangwani.

"Gashi ki bata."

Ta miqa hannu biyu zata karbi ledar yayi azamar riko tafun hannunta. Take jikinta ya dauki rawa ta saki ledar a kasa gabanta na tsananta bugawa.

"Haka fatar ki ta ke lallausa. ?Tamkar kedin ba yar yankin awaki ba na unguwar shura? Wabillahil lazi wani sai yace a GRA din kike..." Ya karasa, Hadi da daukar ledar ya sake mika mata.

Waheedah dai a firgice ta ke da shi. Taja baya tana girgiza kai.

"Ungo matsoraciya... Ki cewa kakar taki komai yayi, Na wane darajar kaya.? Ki ce harda la'ada za'a. Don na yaba kwarai. "

Sam bata gane zancen sa ba. Ta dai matsa da sauri ta dauke ledar. Ta fuce daga cikin shagon tamkar zata tashi sama dan sauri.

"Waheedah Umman ku na gidah?" Cewar Najan Isubu kawar Umman mu.

"Eh to .Da ke ban koma gidan ba. Ina wuni?"

"Lapia kalau. Idan tana nan kya…Koda yake basshi ma zan biyo da kai na idan na shigaa gidan Furera nayo mata barkar Aina'u. "

"Tohm ..."

Kai tsaye ta kama hanyar shiga gidan su. Gaban ta na tsananta bugawa da mamakin Na'Ateeku mai shago. Dan iska ne ashe?

Ta sauke nannauyar ajiyar zuciya kana ta shige cikin gidan su bakin ta dauke da sallama...!!!


#FARHATAL-QALB
#ZAFAFA2022


_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

_BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_

_4 BOOKS 4500_
_3 BOOKS : 3500_
_2 BOOKS : 2500_
_1 BOOK: 1500_

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
*FARHATAL-QALB*
_(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_
💗


×NA×

×NANA HAFSATU×
(MX)

×ZAFAFA BIYAR2022×
#PAID NOVELS!!


×FREE PAGE: 2×


××××××

Kukan Yaya Kamal ta jiyo tun daga soro kafin ma ta karasa shigaa cikin gidah.

"Wayyo Allah na .., Wayyo Allah na Umma..."

Daga can kurya ta jiyo muryar umman ta su tana lallashin sa.

"Kayi hakuri Kamal. Allah zai baku lapia da yardar sa , Da dukkanin masu rashin lapia na gidah dana asibiti."

"Kafa ta Umma.. kafa ta"

"Dena kuka Najeeb. Zaku samu lpy idan Allah ya yarda."

Kifa kanta tayi a jikin bangon soron. Yayinda ziraren hawaye suka shigaa reto a kyakkyawar fuskarta.

Marka taja dogon tsaki tana mai cigaba da sakatar hakoran ta .Ta zauna a saman turmi kafa daya na kan daya.

"Garin aure auren ka. Gashinan ka auro jalli jogam. Da yara shanyayyu ko wata biyu basa yi da lapia. Kash Assh. Allah wadaran na ka ya lalace. Wohoho."

Duk maganganun da Marka kakar su takeyi. Waheedah na jiyo ta daga soro. Ta share hawayen da ke cigaba da kwarara da kasan hijabin jikinta. Kana ta shigaa cikin gidan kan ta a kasa.

"Gashi marka.."

Da sauri marka ta wafce ledar tana mai leka cikin ta

"Taliyar kakkaryawa da tumatirin gwangwani. Lallai yau ta ke sallah. Wannan yaro Na'Ateeku yasan abun arziki. Bai gayan ki sako ki sanarmun ba?"

"Au yace komai yayi zai bada har da la'ada. "

" A hayye sama mata...!!"
Cewar marka. Hade da dora hannunta akan katon hancin ta ta saki gud'a ... Ta kuma fara taka rawa tana shilla hannuwa .

Ita dai Waheedah wucewar ta kawai tayi cikin dakin su tana dafe kwankwason ta.

"Ke wahidin .. " Marka ta sake kirawo ta.

"Na'am "

"Kin gama shiqar ne da zaki shige 'daka?"

"Na kammala Marka."

Marka dake bin taliyar hannunta da kallo taja dogon tsaki.

Ita dai Waheedah bata sake cewa komai ba. Ta cire kayanta ta daura zani hadi da zura hijabi. Sauran omon wankinta ta dauka ta hade shi da kayan makarantar ta acikin bokiti. Tayi hanyar dakin su Yaya Kamal

Bakinta dauke da sallama ta shigaa ciki. Umman su na tsakure daga gefe ta zabga tagumi. Ta gayshe da Umman su da ya Kamal yayanta. Kafin ta bisu da ya jikin su? Ta hada da adduar Allah ya basu lapia.

Gwanin ban tausayi haka ta tsaya tana bin yan uwan nata da kallo. Hakika suna jin jiki shekara da shekaru. Ga shi su ba hali ne da su ba da zasu yita sintirin asibiti.

Ta sake sauke numfashi a karo na ba adadi tana mai zabga tagumi

"Ya akai ..Ki ka dawo da wuri Waheedah?"

"Bakomai ummah. "

Umman ta danyi yaqe kafin ta girgiza kai kawai

"Kawai dai ki ce saboda baa biya kudin wata bane ko?"

Waheedah ta daga kai alamun eh.

"Allah ya kyauta .. Ina su Zainab su suna makarantar ko?"

"Eh.... Marka ce ta je ta biya musu." Ta karasa fada tana mai lankwasa yan yatsunta

"Abincin ki na daki wajen randa. Tashi kije ki ci. Ko wanka zaki?"

"Uniform dina zan wanke tukun. Shiqar su dawa Marka ta sa ni." Tana gama fada ta miqe tayi waje.

Tuqa tuqa ta je da ke ta gidan su ta baya ta taro ruwa. Nan da nan ta durje kayan ta 'dauraye ta shanya. Ta sake debo wani tayo wanka taci abinci. Tayi sallah.

Ko da ta karasa cin abincin tayi sallah, Ruwa ta shiga jidowa tana zubawa a inda suke adana ruwan su. Ta cika ko'ina tsaf sannan ta koma dakin da su Ya Kamal suke.

"Kije ki sallah umma. Kici abinci" Tace da Umman su da ta hada kai da gwiwa.

Batayi musu ba ta tashi ta fice daga dakin. Waheedah ta matsa kusa da yan uwan nata tana jera musu sannu.

Baa jima ba sai ga Sa'adatu nan ta dawo. Daya matar Malam Nalado mahaifin su Waheedah. Itace ta biyu,/ Amaria.

Da waqa ta shigo gidan tana jujjuya kai.

" A hayye wata tafi wata... A sa'a wata tafi wata. A hayye ko ni na fi. Uhm uhm kamshin menene wannan marka?"

"Taliyar kakkaryawa ce dan arziki irin albarka Na'Ateeku ya aikon harda tumatirin gwangwani "

"Lallai yau zamu ci dabge....."

"An dade ba a hadu ba kam." Cewar marka da ke gaban murhu tana gyara karairakin ciki.

Hadiza (mahaifiyar su Waheedah) Ta fito daga cikin daaki ta nufi wajen Marka ta sunkuya da ladabi,

"Marka kawo na karasa."

"Ki karasa me? Matsa kafin na kai miki bugu.."

Da sauri hadiza ta miqe ta shige dakin su Kamal jikinta a sanyaye. Yaran suka bita da kallo cikeda tausayi. Dukkanin su su biyun suna kwance akan katifu kanana irinta yan boarding dinnan . Kana kallon su kasan majinyata ne dake bukatar kulawa. Yayinda Waheedah ke gaban su tana musu sannu. Ita kadai ce mai lapia acikin yan uwan nata.

Cikin haka sai ga Najan Isubu ta shigaa gidan bakinta dauke da sallama. Sa'adatu ta dubeta ta watsar. Najan ma ta mayar mata da kallo sheqeqe tana mai tura daurin dankwalin ta gaban goshi.

"Marka ina wuni?"

"An kwan kalau? Ya iyali ?"

"Alhamdulillah! Ya fama da mu? Ya jikin su Najeebu?"

"Da godia. Ya wajen su Isubu. Yana tashi ko?"

"Eh suna can. Shi da su gurare."

"Allah sarki..."

Sallama tayi ta shige dakin su Kamal. Nan da nan kowannen su ya shigaa gaisheta. Tayi musu ya jiki tana duban su cikin tausayawa.

"Ungo nan Waheedah." Ta zuge dan tofi ta janyo jaka daya (dari biyu) ta miqawa Waheedah.

"Me zan siyo.?" Cewar Waheedah,

"Ba abunda zaki sayo. Kudin makaranta na baki. Kije ki biya idan Allah ya kai mu gobe. Kinji ko?"

Nan da nan fuskar Waheedah ta kyakkyabe da farin ciki. Hawaye daya na bin daya suka shigaa reto a fuskar ta. Ta tsugunna har kasa tana godia

"Nagode. Ubangiji Allah ya saka miki da mafificin alkhairin sa. Allah ya biya miki bukatun ki na duniya da lahira . Allah ya..."

"Godiar me ake ne. ?"

"Godiar kudin wata ce marka. "

"Aiho to..."

"E.. Ina ce wani bayani ne... Na karya miki dankwali Markatu." Najan Isubu ta sake daga murya tana mai sakin shewa. Abunda ya sake rura wutar zuciar marka. Taja tsaki tana mita.

Hadiza tayita yiwa najan Isubu godia .

"Bakya gajiya. Allah ya saka miki da mafificin alkhairi. Allah ya yaye miki dukkanin kuncin da ke damun ki ya wanye miki da burukan ki.. Mungode, Mungode "

"Kaiya bar godia hakanan hadiza ai mun zama daya. Menene amfamin amintar idan har babu taimakekeniyar juna aciki? Kada kuma ki manta kafin nayi miki kece kika yiyyi mun. Don haka abar zancen. Ni magana ce muhimmiya ta kawo ni...."

"Toh... Ina sauraron ki Najaatu."

"Magana ce akan aikatau. Ko ince wankau."

"Toh Alhamdulillahi. Aina ne?"

"Acan GRA dinnan. Yan kananan kayyayaki zaa dinga wanke musu. Domin inji ne ke musu na manyan sannan kuma mota ce ke zuwa ta dauki wankin su ta kai kamfanin wanki ayi ta dawo musu da shi. Sai yan tsince tsincen gyara da ba za'a rasa ba."

"Tohm Najaatu. Allah ya saka miki da mafificin alkhairi..."

"Kai wannan godia. Yauwa gidan da zaki dinga yi din gidan dogaye ne. Inkiyar ahalin gidan ce. Wai ahalin dogaye, idan kaga gajere to baqo ne. Kinsan da ba a kasar nan ma sike ba, daga baya suka dawo. Wadda ta samamun aikin tace na fara zuwa gobe. Nace mata zan kawo wadda zata musanye ni. Ni cin ruwa nake a hannaye na. Na dena wankau. Amman tace da albashi me tsoka wallahi. Kuma ba yunwa. .."

"Ahh Masha Allahu. Allah ya biya ki Najaatu."

"Aamin. Kinji sunan gidan da turanci. Adams menene.?" Ta daga kai tana tunani.

Waheedah dake gefe ta dan jujjuya kai tana tunowa kafin cikin daga murya tace.

"The Adams family.........


_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

_BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_

_4 BOOKS  4500_
_3 BOOKS : 3500_
_2 BOOKS : 2500_
_1 BOOK: 1500_

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
*FARHATAL-QALB*
_(FARIN CIKIN ZUCIYA)_
💕


*NA×


×NANA HAFSATU×
(MX)


×ZAFAFA BIYAR2022×
#PAID NOVELS!!


×FREE PAGE: 3×


××××××

"Kwaret Waheedah haka sunan yake. Gidan nan idan kuka shiga zaku dauka a wata kasar kuke. Wani irin gidah ne wohoho aljannar duniya. Allah ka yi mana arziki. Wato wasu basusan ana talauci a duniya ba. Allah Hadiza zan iya jefa matashin kai na kwanta bacci a shirgegen wajen adana motocin gidan. AC sai sanyaya wajen take hadiza. Hmm Allah ka iya mana..." Najaatu ta karasa fada tana kada kai

"Ai Najaatu Allah ya kara mana wadatar zuci kawai. Idan kana kallon na sama da kai ba zaka taba sanyawa zuciyar ka salama ba. Wallahi damuwa ba zata sararawa zuciyar ka ba."

"Wallahi hadiza. Alhamdulillah kam. Allah ya aurar da yayanmu ga inda zasu ji dadi. Su dama nera su ture nera su hau nera."

"Toh Najaatu Amin. Amman kar ma su sanyawa zuciar su hangen mazan da suka yi musu nisa. ...."

"Eh ai addua ce muke yi. Tunda ba wanda yasan abunda gobe zata haifar."

"Hakane. Toh Allah ya amsa, Aamin."

"Aamin Aamin. Wato Waheedah kin gane gidan ko?"

"Eh.. Ai kinsan gate din layin yana kallon tsallaken titin dake kallon makarantar mu. To yafi sauki kabi ta layin a zuwa makaranta da dawowa. Wata rana mu da su Fanna mun dawo daga makaranta mun biyo ta layin. Akwai bishiyar fruit acikin gidan. Tun lokacin kafin ma kamar a tare gidan ."

"Kwarai don daga baya suka dawo. A kasar waje suke..."

"Eh tohm. Sai su fannah suka shigaa , Daman kofar gidan a bude muka ganta. Sai suka hango bishiyar. Shine suka daddauki karare da zasu karkado bishiyar don fruits din su fado. Suka shigaa ciki. Ni da Basira muna leken su. To mai gadin ashe yana ta waje. Saboda haka mu ya hango muna lekawa, Shine ya faffalla mana mari. Su kuma suna ganin yana marin mu suka shige da gudu..." Waheedah ta karasa fada tana runtse idanun ta. Tuno marin da suka sha.

"Maganin ku kenan. Gobe ma ai kwa kwara. " Cewar Umman su.

"Ah kiji ki hadiza da wata baudaddiyar magana. Yo ko ina ai ana dandalar arzikin wasu. Wani yaci a jikin me shi haka rayuwar ta gada. .. 'Dan gaba da iska da alama bai san darajar ya mace ba.da zai dora hannu ya mare su ...."

Ita dai Waheedah shiru tayi tana daga zaune . Yayinda mahaifiyar tata da najan Isubu suka cigaba da hirar su.

"Dan Allah ki daure ki kammala komai da wuri. Kinga tana zuwa kawai rakiya za'ayo miki zuwa can din. Idan kika gama aiyukan ki sai ki dawo gidah. "

"Insha Allahu Naja'atu. Allah ya kai mu ya bamu iko."

"Aamin. Ita wadda ta yo mun hanyar ta jaddadamun kan tsafta nan kuwa kinga bana jinki. Idan tsafta tana yawa ma taki tayi. Sai abu na biyu sunasan mai gaskia da amana. Nace mata kaf unguwar nan babu mai rikon amana irin ki.. Kinada gaskia kowa zai shaida. Tace sunason mai ladabi da biyayya. Nace mata sun samu. Bantaba sanin ki da munanan halaye ba Hadiza. Don haka na bada shedar gaskia akan ki. Na kuma san zasu same ki fiye da yadda suke zaton samu. Sai dai fatan Allah yasa ki fara a sa'a. Allah kuma ya hada zuciyoyin ku Amin. Allah kuma yasa su so ki su kauna ce ki. Ku zauna lapia har kawowar karshen zamantakewar ku."

"Allahumma Aamin Najaatu. Allah ya saka miki da mafificin alkhairin sa. Allah yabiya miki dukkanin bukatun ki. Ya yaye miki dukkanin kuncin ki. Nagode, Nagode, nagode ."


Nan suka cigaba da maganganun su. Waheedah na mamnatsawa Yaya Kamal kafafun sa dake ciwo tamkar zasu ballo daga jikin sa saboda tsabar wahalar ciwo.

Hamisu autan Inna Sa'adatu ne ya shigaa dakin dauke da faranti da curin taliyar da bata fi cokali daya ba. Yanata lasar hannun sa daya.

"Ga shi Waheedah. Inji Marka. Taliya mai yanka yanka."

Dake tanada madaukakin kyankyami nan da nan ta shigaa girgiza kanta . Dubada yadda kudaje ke bin taliyar.

"Na koshi. ."

"Kai dawomun da abinci na." Cewar marka cikin daga murya.

Nan da nan jikin Umma na bari ta yi hanzarin karbe farantin hannun hamisu . Hadi da lekawa ta kofa tana kakaro murmushi

"Wasa take masa Marka . Zaa ci ai abar marmati ce. "

"Uwar yan kanzagi sarkin fadi ba a tambeya ka ba. Bashi ya dawo mun da taliya ta. Dan ubanta ko ina take cin irinta da zata ce ta koshi? "

"Kiyi hakuri marka."

"Kar ki sake bani hakuri. Ki bashi ya dawo da ita. Ko kunci ban yafe ba "

Jin jaka yasa Umma hadiza ta mikawa hamisu farantin, jikinta a sanyaye ta koma gefe ta tsakure tana mai aikawa Waheedah kallon kin kyauta da abinda kikayi.

Najaatu ta miqe zata tafi. Yayinda umma hadiza tabiye mata zata mata rakiya.

"Su marka ni ba'a rabon da ni?"

"Ah haba Najaatu. Zo ga wannan ki danqa kici ai abar marmari ce."

"Wasa nake wallahi. Bari na tafi, Mu kwan lapia "

"Toh Najaatu. "

Zasu saka kai su fuce sai ga shigar malam na lado cikin gidan. Kunnen sa daya ya nana speaker din rediyo ajiki yana sauraro.

Najaatu na ganin sa ta tsaya da fitar don su gaysa.

"Sannu da zuwa Malam." Cewar umma hadiza

"Yauwa .. Ah Malama Naja."

"Na'am malam Na lado. Ina wuni?"

"Lapia kalau Najaatu. Ai rannan mun gaysa da isubu ta wayar gurere."

"Allah sarki. Suna can "

"Wallahi.. toh ya iyali. Komai qalau.?"

"Kalau. Mungode Allah." Cewar Najaatu. Suka tsaya daga soro suna sake zantawa da Hadiza.

"Ahh. Marka yau taliyar kakkaryawa ce abincin rana? Ahh yau zaa sha dabge. Bismillah." Ya shiga nannade hannu riga zai tsoma hannun sa acikin farantin gabanta da take ci. Da sauri marka ta janye farantin tana afka masa harara,

"Matsa. Sahorami mijin sahorama. Da bakasan hakkin iyalin ka ba akan ka. Kazo fankan fankan zaka tsoma hannu aciki tamkar kai ne ka bada kudin abincin. "

"Kiyi hakuri marka. Najajje wurare da dama na rasa aikin yi. Tun safe Ina kofar dakalin gidan mati "

"Shi Matin ba zuciya yayi ba ya fantsama ya nemi na kansa har ya zama abunda ya zama ba yanzu. ? Ammaa saboda mutuwar zuciya kake binsa "

"Ki gafarce ni Markaa "

Tsakanin uwa da da sai Allah. Ta janyo farantin ta saka shi agaban sa. Fuskarta a yamitse tace,

"Sirikin ka ne ya bayar aka kawo."

"Sirikina kuma marka?. Bangane ba "

"Eh miji na samawa yarinyar nan wahidin. Don ba zamu zauna da zagada zagadan yammata ba bayan sun isa auren. Jikokin lawure baki daya ta aurar su "

Shiru malam na lado yayi. Ya ciko hannun sa ya zura taliyar a baka. Sai daya hadiye tukun yace,

"Wanene sirikin ?"

"Na'Ateeku dai. Kuma kasan kaf unguwar nan idan ka tsame gidan mati ba wanda yakai Na'Ateeku samu da zuciyar nema. .”

Naja'atun Isubu dake tsaye a zaure da umma hadiza sai gata a tsakiyar su marka

"Aure fa kikace Marka.? Auren ma kira sa da wanda zaki bawa sai na ateeku . Mutumin da ya haifeta. ? Haba marka..…..


_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

_BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_

_4 BOOKS  4500_
_3 BOOKS : 3500_
_2 BOOKS : 2500_
_1 BOOK: 1500_

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
_*FARHATAL-QALB*_
_(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_
                     💞
_NA_


_NANA HAFSATU_
_(MX)_


_AREWABOOKS:MISSXOXO_
_WATTPAD: MISSXOXO00_


_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_


_FREE PG:4_
××××××


Marka ta 'daga kai sheqeqe ta dubi Najan isubu hade da jan tsaki ta kaikaice kanta gefe.

Domin Marka tana cikin jerin tsofaffin nan masifaffu wanda basa ganin kowa da gashi.

Don kaf cikin sansanin su na manya tsofaffin unguwar shurah ta kere su a rashin mutunci da rashin ganin daraja. Haka takan taka duk wanda ya nemi ya kawo mata
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2

Please Login or Register in order to submit comment