Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

HANKAKA MAI DA DAN WANI NAKA
littafin Maryama Abdul
Ebook created by Shuraih Usman
Published at www.hausaebooks.com.ng






HANKAKA MAI DA D'AN WANI NAKA

NA MaryamerhAbdul

01. Rayuwarta

Assalamu alaikum, Maryam is saying hy to you nd your love ones. Yes am back, but this time with a true life story, ni da kaina labarin ya jijjigani da naji that's why I decide to share it with you all and ofcourse da yaddan meshi, I just pray nd hope abunda zan rubuta ya anfane mu kuma masu hali irin wannan su daina ko ince Allah ya shiryesu ya kuma kare mana zuri'a.

***

Na canja abubuwa da yawa cikin labarin saboda wasu dalilai, kamar sunan mutane da garuruwa. Labarin nan ba ni na k'irk'ireshi ba, in yazo iri d'aya da rayuwar wani/wata yanayin rayuwa ne yazo d'aya kuma ban rubuta shi dan cin zarafi ba sai don gyara, kuma ku sani da yaddar mai labarin na d'aura alk'alamina.

***

Yakamata d'an Adam ya sani (mace/namiji) cewa 'ya'ya amana ne a garemu kuma tabbas zai tambayemu game dasu, in ma ya kasance ke/kai ka haifa ko kuma rik'o kakeyi, muddin ka karb'a kaci amana ko ka biyewa son zuciya tabbas zaka ga sakamako.

***

Labarin nan ya k'unshi cin amana, son zuciya, soyayya, ha'inci, rayuwar aure da tab'arb'arewar tarbiyya. Ku biyo ni dan jin abinda labarin ya k'unsa.....

************************************

      "A ganinka ba soyayya nake nuna maka ba da har na baka abunda mutane da yawa suka gagara samu daga wurina Fu'ad? Ka daina fushi dani akan laifi k'ank'ani irin wannan, mun wuce wannan stage d'in na fad'awa juna tsantsar soyayya da lab'b'a. Action speaks louder than voice"

Kallonta ya tsaya yi yana mai tantance maganan da ta fad'a. Tab'e baki yayi ya d'auke kai kamar bazai amsata ba

"A ganinki zan yadda da cewa sona yasa kika bani abunda ni nasan ba nawa bane kuma ba mallakina bane..."

Dafe kansa yayi yana kad'awa a hankali, bata iya furta komai ba dan tasan bazai shiga kansa ba a wannan lokacin, musamman in tayi la'akari da cewa ta sha maimaita masa iya gaskiyarta amma yak'i amince mata.

"Babu ma anfanin fad'a miki hakan Surayya, ke kinsan yanda na sameki kuma bazan yadda kina sona ba tunda bakya iya kawo min abunda nake buk'ata a lokacin da na nema"

Hannunshi ta damk'e cikin nata, idanunta na kansa tana lumshesu a hankali cikin salonta. Bata barshi ya k'ara ko da kalma d'aya ba dan a nata ganin furuci bazai iya daidaita mata shi yanda take buk'ata ba.

"Am here for you now, am sorry"

Wannan kad'ai ta iya furtawa ta cigaba da yi masa abinda tafi k'warewa. Bai iya hanata ba dan dama shine burinsa.

Ba dan komai yake nuna mata b'acin ransa a duk lokacin da ya nemeta bai sameta ba sai don susuce masa da takeyi da kuma biyewa duk wani tarko nasa, shi shaida ne tana matuk'ar sonsa amma hakan ba shi zai sa ya bata yadda d'ari-bisa-d'ari ba.

*****

A hankali yake bugun k'afanta tare da k'iran sunanta.
"Surayya! Tashi mana"

Bargon da ke jikinta ta gyara tana mai juyi ahankali, can ciki ta iya furta "umm"

"Kinsan k'arfe nawa? Ko bazaki je gida bane yau? Maghrib fa ya gabato, ana ta k'iranki a wayarki na tabbata daga gida ne"

Mik'ewa tayi tana mai janyo rigarta da ke gefenta tana k'ok'arin sawa.

"Wankan ma bazaki yi ba yau?"
"Nayi latti, meh yasa baka tasheni tun wuri ba Fu'ad? Yanzu wani k'aryar zanyi?"

Tab'e baki yayi ya d'auko mataji ya fara taje sumar kansa yana k'are mata kallo ta jikin madubin da ke gabansa.

Cikin mintuna biyar ta gama sa kayanta, ta gyara fuskarta had'e da sa hijabinta mai hannu. Jakarta ta d'auko ta isa inda yake tana mai sake masa murmushi, hannunsa ya mik'a mata alamar ta bashi nata hannun. Janyota jikinsa yayi yana mai sanya hannunsa cikin hijabin nata

"Ohh Fu'ad i have to go now, duk abunda na maka bai isheka ba?"

Tayi maganar ne da alamar tsokana, hakan yasa yak'i kulata ya cigaba da abunda ya fara. Cikin kunnenta ya furta
"i will surely miss you"

Murmushi tayi mai d'an k'aramin sauti, ta rik'e hannunsa tana mai yi masa fari da idanunta.

"Zan zo zance anjima"

Ya riga ta furtawa. Sallama sukayi irin tasu tana mai tabbatar masa cewa zata jirasa sannan ta fice fuskarta cike da annashuwa.

*****

"Salamu alaikum" ta furta cikin sanyin muryarta tana mai shigowa cikin falon. Daga kitchen taji an amsa ta, hakan yasa ta ajiye jakarta da hijabinta da ta cire a d'aya daga kujerun falon ta isa wurinta.

"Sai yanzu Surayya? Ina kika tsaya haka? Baki ga missed calls na Zayyan ba? Ai yazo yana nemanki baki dawo ba, yanzu ya fice inaga masallaci yaje"

Sosa kanta ta d'an yi tana mai murmushin da bai kai ga zuciyarta ba.

"Ai Aunty nasa wayan a silent ne, kuma da naje makarantan sai na biya gidan k'awata, a can ne na d'an b'ata lokaci bansan yamma yayi haka ba"

Anty Hajara bata waigo ta kalleta ba bare ta amsa ta cigaba da yankan kayan miyanta, tasan za'ayi haka, shiyasa bata d'aga hankalinta ba ma dan rashin dawowanta da wuri.

"Barin shiga ciki in d'an watsa ruwa, na gaji sosai wallahi"

"Toh, in kin gama ki d'an zo nan ki taya ni miyar nan, Alhaji na hanya kuma kinga har yanzu ban gama yi masa abincinsa ba, ko sallah banyi ba, ki d'an hanzarta kizo ki karb'eni kinji. Yauwa 'yar albarka"

Murmushi suka sakarwa juna sannan ta fice daga kitchen ta wuce d'akinta bayan ta d'auki jakarta da mayafinta.

*****

Cikin bacci taji ana lalumarta, bud'e ido tayi ahankali tana mai son gano wanda ke k'ok'arin sanya hannunsa cikin wani gurbi a jikinta, rashin wadataccen hasken d'akin ya hanata tantance ko waye. Cikin muryarta mai nuni da ta kamu da abinda yake mata ta furta

"Ka daina"
Tana k'ok'arin rik'e hannunsa yana turewa.

"Ya zan daina bayan kema kina son abunda nake miki?"
Ahankali yake maganar, hakan bai hanata gane ko shi waye ba. Jin wanda bazata iya hana shi bane yasa ta hak'ura ta zubawa sarautar Allah ido ya gama wasa da ita ya fice daga d'akin.

Ahankali ta k'ira sunanshi, waigowa yayi daga bakin k'ofan yana sauraronta
"Yaya Zayyan ka fara kai ni mak'ura, ka guji ranan da zan maka abunda bazaka so ba, mugu azzalumi".

Kwafa yayi ya fice daga d'akin ya barta tana mai zubar da hawaye.

"Wannan wani irin gida ne Allah ya kawo ni? Na gaji"

Kuka mai sauti takeyi cike da rashin sanin abun yi. Kafin ta kwanta sai da ta had'u da uban gayyar ya dawo, bai ji kunyarta ba ya furta mata "na dawo fa" ita kad'ai tasan meh hakan yake nufi, ga matansa har uku amma babu wacce ta gano manufarsa sai tsirarrun 'yan matan da suke wurin wanda sunsan halinsa kuma sun san ma'anar hakan a garesu da kuma ita.

Wayarta ta janyo ta tsarawa Fu'ad text, wanda tsantsar kewarsa da kuma kod'a zuwansa na d'azu da abunda yayi mata ne a ciki. Bata fi mintuna biyar da turawa ba ya k'irata, nan ta mance da Zayyan da sauran matsalolinta ta cigaba da soyewa da masoyinta.


Wattpad:- @MaryamerhAbdul
HANKAKA MAI DA D'AN WANI NAKA

NA MaryamerhAbdul

NAGARTA WRITERS ASSOCIATION

02. Mafarin komai

Idanunta da ke kan Zaituna ta d'auke had'e da tab'e baki. Meh zata ji a wurinta matsayin shawara bayan ita kanta na neman shawarar madafar rayuwa? Tana mamakin k'arfin hali da nuna isan 'yan matan gidan nan, tare suke rayuwa sunsan duk abunda ke rayuwar d'aya daga cikinsu amma har wani yana da k'arfin gwiwar tunkarar wani yayi masa magana.

"Dallah malama ki k'yaleni, kin isheni da shawararki. Ki gyara naki rayuwar mana? Ni meh nakeyi?"

Ta fad'i hakan cike da b'acin rai, idanunta tsantsar haushi ke yawo a cikinsu.

"Dan ina fad'a miki gaskiya shine zaki gaya min magana Surayya? Ni fa nasan irin rayuwar da mukayi a gidan nan, shiyasa nake baki shawarar da ta fisheki tun kafin wani yaci galaba akanki rayuwarki ta tsiyace yanda na sauranmu ya zama".

Kanta ta girgiza tana mai mamakin irin taurin kan Surayya, meh zatayi mata da zai sa ta gane manufarta?

"Ina fad'a miki saboda naga duk cikinmu babu mai nutsuwarki da k'in kula samari, ina gudun miki lokacin da zaki kasa saita kanki ki fad'a rayuwar halaka wanda na tabbata tsantsar nadama ne zai biyo baya".

Idanunta ta juya alamar maganan ya fara isarta, bata furta komai ba Zaituna ta cigaba da cewa

"Kinga rayuwar gidan nan babu mai fad'a maka gaskiya, mu shida tunda na taso ban ga an kwab'i wani ba ke shaida ce, kuma cikinmu ke ce k'arama. Daga kan Suwaiba har ke babu wanda Allah ya kawowa miji kuma duk kinsan dalili, kamar dai yanda nace miki ke d'in dai ke ce d'aya wacce muke sa ran aurar dake hannu meh kyau nan kusa tun kafin lokaci ya k'ure ki zama cikin sahunmu, a shekaru yanzu nasan zaki kai ashirin da biyu..."

Bayani ta cigaba da yi mata tana nusar da ita amma Surayya tunaninta ya tafi maganar da sukayi da mahaifiyarta kwanaki uku da suka wuce.

"Kinga ni bana tare dake Surayya, Antynki ita ce uwa da Uba a gareki, lokaci yayi da zaki fidda miji kiyi aure"

Maganar da mahaifiyarta ta fad'a mata kenan, bata iya mata musu ba a lokacin a ganinta zata manta da maganar, toh gashi yau d'aya daga cikin yayyun nata ke bata shawarar aure saboda kamewarta.

*****

"Surayya!" "Surayya!!" "Tashi ki gani Surayyata 'yar kyakkyawata"

Hannunta yake shafawa ahankali yake maganar, cikin baccinta mai dad'i take jin maganar tasa. A hankali yake shafa sassan jikin yarinyar da bazata wuce shekaru goma-sha-d'aya ba a duniya.

Kuka ta sake masa kamar yanda ta saba a duk lokacin da ya shigo d'akinta. Hakan bai hanasa ida manufarsa ba, sai da ya biyawa kansa buk'ata ya fice daga d'akin ba tare da wani ya gansa ba.

Kuka takeyi mai shiga rai, har yau ta kasa sabawa da halin mai gidan na wasa da ita. K'aramin kwakwalwarta ya kasa tantance mata abinda yake yi, bata isa ta furtawa kowa abunda yake faruwa a kusan kowani dare ba saboda tsoro dan kakkausar shaidar da yayi mata zai illatata muddin yaji maganar a bakin wani.

Abun takaicin ba ita d'aya yake yiwa hakan ba, sauran yaran ruk'on da suke tare takan ji suna zancen tsakaninsu, mamakinta d'aya, shin su basu tsoron ya illata su dan sunyi maganar ko dai bai musu kashedi kamar yanda yayi mata ba?

A shekaru sun girme mata, yawancin maganarsu akan halin mai gidan baya wuce

"D'an iska ni ai da yazo min jiya bugesa nayi nace kada ya kuskura ya tab'a ni, sai yayi ta wasa da mutum bai iya komai ba bayan wannan"

Wasu daga cikinsu kuwa k'yamar abun sukeyi dan basu san meh manufarsa da anfaninsa ba, gani suke nuna isa da girma ne dan an kawosu gidanshi su zauna kasancewarsa mai rufin asiri.

Tun bayan rasuwar mahaifin Surayya mahaifiyarta ta k'ara aure, Anty Hajara ta d'aukota ta kawo ta gidan mijinta kasancewar Allah bai tab'a bata haihuwa ba.

Ta had'ata da sauran yaran rik'on gidan ana kula dasu, cinsu shan su da duk wani abu da yaro zai buk'ata ana yi musu dai-dai gwargwado, matsalarsu bai wuce Alhajin gidan ba. Ya kasance mai bin yaran da dare bayan kowa ya runtsa, wasu daga cikinsu tun suna tirjewa har suka fara biye masa duk da bai tab'a wuce wasa ba.

Surayya kad'ai ke mugun tsoronsa, duk lokacin da yazo mata bata iya hana shi ko cewa uffan sai dai zubar da hawaye, ko dan k'arancin shekaru irin nata shiyasa bata iya hana shi kaman sauran 'yan matan, ko jan kunnenta da yayi mata yasa take tsoronsa.

*****

Surayya bafulatana ce ta usul, fara kyakkyawa mai tarin nutsuwa da girmama na gaba. A shekarunta sha-uku sassak'en budurci ya fara bayyana a jikinta, kyawunta ya k'ara fitowa.

"Alhaji jiya fa kazo nan, yau ma ka sake zuwa"

"Shhhh!"

"Gaskiya ba wani inyi shiru, ni na gaji in baka barni ba Allah zan maka ihu, kaje wurin wasu mana sai ni ne?"

Ta k'arashe maganar cikin muryar kuka tana turesa daga jikinta, hasken da ya gauraye ilahirin d'akin yasa ta gwale ido dan bugun zuciyarta da ya tsananta.

"Alhaji ma na lafewa anan kenan?"

Zayyan ya fad'a cike da b'acin rai yana huci

"Ke kuma da ke jaka ce mara hankali kike barinsa ya tab'a ki? Ke kinsan irin hak'urin da nayi a kanki ina jiran ki k'ara girma ashe shima mutumin nan idonshi na kanki? Ni na rasa baban nan wani irin jaraba ne dashi, d'anshi yaga abu meh kyau ashe nashi idon da maitarsa har yafi nawa".

Janyota yayi yana mai kallon yanda take a tsorace da mamakin ganinsa a d'akinta, hannunsa ya d'aura akan lab'b'anta yana yi mata wani shu'umin murmushi.

"Surayya ina sonki, dan Allah ki fad'a min gaskiya, baba ya tab'a shiganki?"

A tsorace ta kad'a kai alamar a'a duk da bata san ma'anar maganan nasa ba, tunaninta d'aya in Alhaji yaji zai yi gunduwa-gunduwa da ita.

Murmushin murna yayi ya janyo ta jikinsa

"kada ki bashi kanki Surayya, ke tawa ce, na dad'e ina rainon soyayyarki a zuciyata, ki min alk'awarin kare min kanki daga kowa, ni kad'ai ne naki kinji, in kina son wani abu ki nemeni ni kad'ai ne zan iya baki"
HANKAKA MAI DA D'AN WANI NAKA

NA MaryamerhAbdul

NAGARTA WRITERS ASSOCIATION

03. Zayyan

"Surayya yanzu ke in nace miki zanyi aure ma zaki yadda? Duk shekarun nawa in kin had'e nawa ne? Makarantar ma ban gama ba taya zaki kawo min maganar aure?"

"Haba Fu'ad, ya zaka ce min haka? Abunda ake yi a auren wanne ne baka yi? Abunda ake yin auren dominsa ko kuma ciyar dani da bani kud'in kashewa? Duk kana yi min, gani nayi ya dace mu suturta abunda muke yi mu tsaftace shi, amma sai tirjewa kakeyi kana nuna min ba sona kakeyi ba"

Hawaye ke rige-rigen sauk'a daga idanunta, bata yi tsammanin jin haka daga wurinsa ba, a tunaninta zai yi farincikin shawarar da ta yanke tsakaninsu amma sai ya watsa mata k'asa a ido.

"Surayya please understand"

Dakatar dashi tayi ta hanyar matsawa gefe dan hannunshi da ya kawo zai rik'eta.

"Babu abunda zaka ce min Fu'ad, ba sona kakeyi ba shiyasa baka son muyi aure"

Kuka ta fashe dashi iya k'arfinta. Miyau ya had'iye mai d'acin gaske yana mai runtse idanunsa had'e da damk'e hannunsa, bai d'auka wannan lokacin zai zo da wuri haka ba.

Jin kukan nata ba mai tsayawa bane yasa shi matsowa daf ita, bai yi k'ok'arin rik'e ta ba sai da ya tattaro duk wani zancen da yasan zai nusar da zuciyarta.

"Babyn Fu'ad na sha sanar dake bana son ganin hawayenki, k'ona min rai yake matuk'a, ki tausaya min ki daina kukan sai muyi magana a tsanake mu san abun yi, ke kinsan ina sonki kuma zan miki duk abinda kikeso"

Bayanta yake shafawa ahankali had'e da janyota zuwa jikinsa, kalamai masu dad'i yake yi mata sai da ya tabbatar sun shigeta sannan ya d'ago da ita.

"Kalleni kiji abunda zance miki"

Bakinta a zumb'ure ta d'ago rinannun idanunta tana k'are masa kallo wasu hawayen na dad'a taruwa a kurmin idanunta.

"Zanyi maganan da iyayena in naje gida next week, duk yanda mukayi zan sanar dake. Ya miki?"

Murmushi ne ya sub'uce mata, k'ank'ameshi tayi iya k'arfinta tana mai nuna masa tsantsar murnarta. Bata iya tantance yanayin fuskarsa ba amma murnar da take ciki ya wadatar da ita a wannan lokaci.

*****

"Malam, kaga ka fita min daga d'akin nan, Allah a yau sai in yi maka ihu ko in had'aka da Anty Hajara, kai ko kunya baka ji kana zuwa wurin 'yar matarka, ni ko ka manta ni wacece a wurin Anty Hajara? 'Yar yayanta fa? Haba, na gaji wallahi"

Janyota yayi da iya k'arfinsa ya toshe bakinta

"Kaji banzan yarinya, yaushe kika girma da zaki hana min abunda na raineki dashi? Ni ke da iko dake ko ke kike da iko dani? A gidana fa kike zaune kike cin arziki, kuma yau rana tsaka zaki taso min da shegantaka"

Duk iya k'ok'arinta na k'watar kanta ta kasa, da hannu d'aya ya danneta yana k'ok'arin cire tufafin jikinta.

Lokaci d'aya ta gallara masa cizo had'e da bugesa da gwiwarta, k'ofa ta bi zata gudu ya kamo k'afarta, bakinsa ya kasa mutuwa

"Ai baki isa ba wallahi, sai da kika girma zaki hana ni lasar zumarki, sai lokacin da zan kwashi gara zaki raina min hankali?"

Cikin kuka take basa hak'uri dan ya k'yaleta amma janyota yayi jikinsa

"Yi min shiru, yau sai kin rainawa aya zak'inta, ni kikeson tonawa asiri tun ban miki komai ba?

"Baba wallahi in baka saketa ba ni da kaina zan sanar da kowa abunda kakeyi"

Daga sama yaji muryar ya doke sa, tsayawa yayi kallonsa yana mamakin ta yanda ya shigo d'akin har yasan abunda yake faruwa.

"Zayyan, meh ka shigo yi nan cikin talatainil laili haka? Lafiyanka?

"Nazo wurin masoyiyata mana Baba, haba dan Allah, yarinyar nan ni take so ka hak'ura da ita mana baba, tun tana maka shiru har ta fara rainaka, ka bar min ita kawai da ni tafi dacewa"

"Kai Zayyanu ni kake fad'awa haka? Ka fice min daga nan"

Ya nuna masa k'ofa da hannunsa. Surayya da ke durk'ushe gefe sai ajiyar zuciya take tana kallon ikon Allah, tun shekaru biyu da suka wuce uba da d'a ke rige-rigen zuwa wurinta, yau dai sun had'u kicib'is kaman yanda take addu'ar hakan ya faru.

Tun ranar da Zayyan ya fara yi mata kalamu da biyewa duk k'orafi nata tafi sakewa dashi akan mahaifinsa, baya tab'a yi mata wani abu in tak'i aminta sab'anin Alhaji da duk kukan duniyan da zatayi sai ya gama abunda ya kawo sa zai tsallake ta ya wuce.

"Da gaske fa nake Baba, in baka daina takurawa Surayya ba ni da kaina zan kawo matanka su ga abunda kakeyi, nagode Allah mama bata raye bata ga abun takaicin nan ba"

Zufa ke keto masa duk da iska mai sanyin da ke shigowa ta tagar d'akin.

Jiki ba laka yaja k'afansa yabi gefen d'an nasa zai fice

"Kuma baba ba wai yau ne kawai nake nufin ka barta ba, in ka sake zuwa wurinta Allah komai na iya faruwa, kuma kai kasan abunda ya dace kayi dan rufin asirinka"

Bai tanka sa ba ya fice ya bar musu d'akin.

Da gudu ta isa wurinsa ta shige jikinsa tana mai sake wahalallen kuka.

"Shhh! Yi shiru, komai ya wuce daga yau"

Gashin kanta yake mayarwa baya had'e da shafa bayanta. Ahankali ya had'e bakinsu wuri guda, dan kanshi ya k'yaleta ya tsurawa fuskarta da yayi ja ya d'an kumbura dan kukan da ta sha.

Ita ma shi d'in take kallo tana mai sake masa murmushi.

"Happy birthday, abunda nazo fad'a miki kenan na tarar da mutumin nan. Yau kin cika shekara goma sha shida, nazo tuna miki alk'awarin da kika min ne"

Murmushin bai gushe daga fuskarta ba ta sauk'e k'wayar idonta. Murmushi mai sauti yayi ya gyara mata gashin da ya kwanto mata bisa fuskarta.

"Ko za'a bani alk'awarina yau?"

Narai-narai tayi da idanunta, a hankali ta gyad'a kanta alamar a'a cike da shagwab'a tace

"Ni fa dama ban maka alk'awari ba ya Zayyan, na fad'a maka ina tsoro"

Alamun tafiya suka ji daga bakin k'ofar, tuni ya kashe wutar d'akin ya lafe bayan k'ofa.

Kwankwasa k'ofar akayi Surayya ta isa duk ta daburce ta tsorata. Can ciki ta furta "waye?"

"Nice"

Muryar da taji ya k'ara tsurar da ita. Da hannu yayi mata nuni da ta bud'e k'ofar sannan ta murd'a ta bud'e tana mitsike ido da bayan hannunta.

"Anty Hajara lafiya?"
Ta furta tana mai yin hamma tare da toshe bakinta da d'aya hannunta d'ayar kuma na idonta tana murzawa.

•.•.•.•.•.•.•.•.•.•.•.•

Follow me on Wattpad dan samun complete littafin da ma sauran littafaina
Kwaiseh Maryamah
BADAK'ALA
Soyayya ce
Jarabtarmu kenan
Hankaka mai da d'an wani naka
Wattpad:- @MaryamerhAbdul
Thank you
HANKAKA MAI DA D'AN WANI NAKA

NA MaryamerhAbdul

NAGARTA WRITERS ASSOCIATION

04. Hak'urina ya k'are

"Lafiya... meh ya same ki?"
Ta tambaya tana kallon fuskarta daga bakin k'ofar.

Murmushin yak'e Surayya tayi
"Babu komai, meh kika gani? Meh ya fito dake da dare haka?"

"Alhaji ne..."

"Alhaji kuma? Meh ya same sa? Meh ya faru?
Ta tare ta tun kafin ta ida maganarta, cike da mamakin rud'ewarta Anty Hajara ke kallonta, can tace

"Lafiyanki Surayya? Ko zazzab'i kike?"

Fuskarta ta shafa tana mai sauk'e ajiyar zuciya
"Lafiyana k'alau Anty, baki gama maganarki ba"

"Ohh, dama Alhaji ne ya tashe ni wai inzo in duba ki, toh na d'auka baki da lafiya ne ko wani abu"

Murmushi ta sakar mata tace "lafiyana lau Anty, nagode. Barin koma bacci nakeji sosai"

Ta k'are maganar tana mai yin doguwar hamma.

"Sai da safe"
Ta juya tayi hanyar waje, ware ido tayi ganin zata fita daga cikin falon.

"Ina zaki je kuma Anty?"
Cikin d'aga murya ta tambaya.

"Shhh! So kike kowa ya tashi, zanje in duba Zayyan ne, shima ance in duba sa, bansan meh ya same ku ba dukka kuna neman b'ata min baccin yau"

Cikin muryar da ba kowa zai
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment