Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

*🌚GANTALALLIYA🌚*

*WRITTEN📝*
*BY*
*DEEE*❤



*STANDARD WRITER'S ASSOCIATION*

True life story.


1-5

Wata zukek'iyar bakar mota kirar benz E350 na hango ta karyo kwana, wani dankareren gida ta tsaya, yana matsa horn mai gadi yataho da gudu ya bude gate, sannu da zuwa yakeyimas bai tsaya ya sauraresa ba ya wuce inda ake parking motoci.....


Maigadin yana rufe kofar yabi bayan motar da sauri, kan ya isa har mutumin dake cikin motar ya fito, gaishesa yayi tare da yimasa sannu da zuwa.....

"Yawwa sannu sabo, madam tana ciki ne ko tafita" yake tambayar mai gadin, daidai lokacin dayake bude kofar bayan motar yana dauko jakar sa.

"Ai ranka shi dade baka dade da fita ba wata mata tazo naga sun fita tare, kuma har yanzu basu dawo......." daga mishi hannu yayi rai abace yace "shikenan nagode zaka iya tafiya"


Yana shiga cikin gidan, tundaga bakin kofa yafara karo da shirgi kalakala, tsaki yayi ya wuce dakinsa, wanda yasameshi a yanda ya fita ya barshi, wani takaici ne ya rufeshi, kamar yayi kuka, ga yunwa daya kwaso.

Da kansa ya kyara dakin sannan ya fito kitchen domin yasamu abinda zaisa a bakinsa. Yana shiga idonsa ya kai kan gas cooker din, tayi dak'al dak'al, dagani tunda aka siyeta bata taba ganin ruwa ba, haka ya daure ya dauko wata yar karamar tukunya, itama seda yadaurayeta sannan ya dora ruwa, wanda baima san abinda zae dafa ba.


Fridge din ajiye kayan miya ya bude don yaga ko zae samu ragowar miya sai ya dafa farar shinkafa, yana budewa ya rufe da sauri, dan tsabar wani wari daya doshi hancinsa, nan take yaji amai ya taho mai, da gudu ya kashe wutar gas din yayi waje da sauri....


Tun a kofar kitchen din yafara sakin aman, ga wani jiri dayake dibarshi, haka yayi yagama, da kyar ya gyara wajen yayi dakinsa, toilet ya fada ya sakarwa kansa shower, sannan yasamu ya dan ji dadi.

Yana fitowa ya suri key din mota yayi waje, ba motar daya dawo da ita ya hauba yanzu, wata jar mota ya dauko an lullubeta da bakin tinted, yana fita bai tsaya a ko ina ba sai a chicken castle....

Anan yasamu yaci sakwara da miyar agushi, ci yake kawai amma zuciyarsa babu dadi. Yana gamawa ya koma gida, misalin karfe 6 na yamma, amma bata dawo gidan ba, sai yayi tunanin ya kirata a waya sai kuma ya fasa.

Kwance yake akan gadonsa kamar mai bacci, amma kuma ba baccin yakeyiba illa tunane tunane da suka shige mishi kai.

Ba ita tadawo gidan ba sai goma saura yan muntina....

Buzubuzu ta shigo gidan, daganin tafiyarta kasan babu nutsuwa atare da ita, gashi sai taunar chew gum take kai kace ba mace ba, bama wannan ba, shigar da tayi ma kadai ya isa kasan wacece *BINTU MATAR SADIQ.*

Dakinta ta wuce tayi wurgi da jakar hannunta tana "washhh!!! Nagaji wallahi" kayan jikinta ta cire ta wurgarsu a tsakiyar dakin,ta dauko wata doguwar rigar bacci,wacce inbanda tsami babu abinda takeyi, amma haka ta tafka abinta ko ajikinta...

Kan hargitsetsen gadonta ta hau ta kwanta abinta, wayarta ta dauko takira wata kawarta, saidai bata dauka ba, haka ta gaji ta ajiye ta ja bargo ta shige....

Shikuma tunda yaji shigowarta yakasa daurewa seda ya tashi ya biyota har dakin nata. A fusace ya shiga kamar wanda zai daketa sai dai yana zuwa yaji gabansa yayi wani irin mugun faduwa,a sanyaye ya karasa gabanta..


"Haba bintu! Ina kika tafi kika kai dare haka batare da kin sanar dani ba" shiru tayi kamar ba da ita yake ba, seda yasake magana ta dago a fusace "haba malam kafa takura min nidai wallahi, nadawo ma ko sannu da zuwa baka min ba sai tambayar daga ina nake, to unguwa naje koda magana ne? Girgiza mata kai kawai yayi kafin yace "Allah ya baki hakuri" tsaki taja "aikin banza kawai, nikatashi kafitar min adaki bacci nakeji" bata jira cewarsa ba taja bargon ta koma.

Salalo salalo yatashi yafita adakin, dakinsa yakoma ya kwanta yana tunanin, wai maiyasa bintu take mishi kwarjini ne? Meyasa idan yayi yunkurin yimata fada yake kasawa ne? Meyasa kuma yake masifar sonta? Da wannan tunanin har bacci ya kwashesa amma bai samu amsar tambayarsa ba....

To nima dai na matsu nasan wannan dalili😜

Written📝
By
*DEEE*❤
08177892239


*🌚GANTALALLIYA🌚*

*WRITTEN*📝
*BY*
*DEEE*💘

*OMG!!! FROM WHERE I AM GOING TO START SELF?😍 AM OUT OF WORDS😷 FAN'S I FEEL LIKE LAUGHING😃 AND CRYING😭 AT THESAME TIME❣ BABU ABINDA ZANCE DAKU SAI GODIYA, NAGODE ALLAH YA BAR ZUMUNCI YA BAR SODA KAUNA, KUMA INA MUKU FATAN ALKAIRI NANKIN BANINKI YANDA KUKE MIN*❤❤❤

*Maman Nawal! wannan page din na sadaukar miki da shi😘 nagode da kulawarki, so da kaunarki agareni, Allah ya barmana ke*❤


True life story.

5-10

Kirayekirayen sallar asuba ne ya tasheshi, toilet ya nufa ya doro alwala ya fito yazura farar jallabiyarsa ya nufi masallaci...

Ita ko gwanar ko motsawa batayi ba, tayi d'ai d'ai, sai sharar munshari takeyi. Seda yadawo ya biya dakin nata, a hankali ya bude kofar, a hankali ya soma kiran sunanta "bintu!bintu kitashi kiyi sallah, inyaso sai ki koma baccin" cikin masifa ta tashi "ohh ni bintu Allah ya hada ni da jarababben miji, kai kenan baka so kaga ina hutawa seka zo ka takuramin, ina ruwanka da sallah ta" daurewa yayi yace "haba bintu, kefa musulma ce, yakamata ki dinga kiyaye addininki, abinda kikeyi kwatakwata bai kamata ba" Allahu akhbar!! Kace yau yan wa'azin ne suka tashi, to idan wa'azi kakeji katafi kayiwa wayanda suke bukata, nikam bana so ehen" zaisake magana tace "kaga malam, kai bakayi taka sallar ba? Kwarai kuwa ninayi sallah" to kaje Allah ya bada lada, nikam sena tashi zanyi bacci bai isheni ba" tana gama fada tasake komawa ta kwanta.....

Cikin takaici yabar dakin, a zuciyarsa kuma yana fadin Allah ya shiryi bintu.


Bai dade da fita daga dakinba wayarta tayi kara, da sauri ta mike tana shewa ta dauka "uwar dakina ya akayi, nakiraki kafin na kwanta jiya baki dauka ba, lfy? Hmm kedai bari, wannan dan jarabar ne, ina dawowa ya tsareni wai senayi masa girki" da sauri bintu ta mike "wai kina nufin har yanzu baki fara juya shi ba" tabe baki saratu tayi, wato kawar bintu" bari kedai bintu, ai narasa wanna irin mutum ne, amma karki damu zamuyi maganinsa kwannan nan"

"Yazama dole ma muyi maganinsa, yau zanje wajen hajiyarmu, daga nan kuma zan leka gidan suna kinsan nafada miki yar wata makociyar mu ta haihu, idan nadawo zanzo har gida" to ba damuwa.... Sukayi sallama

Tashi tayi ta shiga kazamin toilet dinta, fuskarta kawai ta wanke da ruwa, sai bakinta data kuskure tafito, kitchen ta nufa, dan rabonta da abinci tun na rana, ruwan tea ta tafasa ta soya kwai na iya cikinta, tafito ta nufi kan dinning tana ci...

Shima sadiq daya koma dakinsa wanka yayi yayi shirin tafiya office.

A kan dinning yasameta baiyi niyyar cemata komai ba,dan yau tunda ya tashi yake jin haushinta, dan babu abinda yafi damunsa illa rashin sonyi sallarta, zai bude kofa kenan tace "sadiq ina son magana da kai" tsayawa yayi a inda yake batare da ya juyo ya kalleta ba yace "ina jinki sauri nake zan fita" seda ta kurbi ruwan tea tace "mukullin motar ka nakeso zaka bani, yau da ita nakeson fita"

Jiyayi kamar ta buga mishi guduma akansa,gaskiya bintu ta rainashi dayawa, yakamata yafara nuna jarumtakarsa akanta, ko zata shiga taitayinta, dakewa yayi yaci magani "ai ba daga gidanku kika zo da ita ba" da sauri ta mike ta kalleshi cike da mamaki "Sadiq nikake fadawa haka" juyowa yayi ya nunata da yatsa yace "angaya miki hakan, bintu bari kiji nafada miki, iskancinki yafara isata, bakida aiki sai gantali, babu ranar da zata fito ta koma ga ubangijinta baki fita ba, bamakidamu da tambayata ba, kuma sai sanda kika ga damar dawowa, to wallahi yau karna sake nadawo gidan nan naga bakya nan, k'azamar banza kawai shaaa shaaa shaaa" yafita ya barta a wajen, bintu kuwa mutuwar tsaye tayi, duk bala'in ta kasa cewa komai tayi, dan dama bokan ta yace duk sanda sadiq zaiyi mata irin wannan hargagin, karta sake ta tanka mishi, dan komai zai iya faruwa...

Takaici ne ya rufeta takasa karasa breakfast din da takeyi, seda ta tabbatar ya fita daga gidan tace "aiko kayi kadan ka hanani fita wallahi, kuma zanyi maganinka ne"

Dakinta ta wuce, cikin sauri tashiga wanka, nan da nan ta fito,komai bata shafa ba ta zura doguwar rigar atamfa, ko d'an kwali bata daura ba ta yafa kyale kawai, ta suri key din mota tayi waje...

Gudu kawai take zabgawa a titin kamar zata tashi sama, aiko batayi aune ba ta bugawa wani mai keke napep, amma cikin icon Allah baiyi komae ba, illa bomber motar ta daya sauka, aiko tsayawa tayi tafito tana ta dureduren ashar, shima mai napep din futowa yayi ya duba bayan kekensa yaga ba abinda tayi yace

"Allah ya taimakeki,wlh da sai kin biya ni" wani ashar din bintu tasake k'undumawa, tacire mayafin kanta taci dammara "wallahi baka isaba sai ka biyani motata, dan iskanci sai kuzo Ku shiga gaban mutum, wlh bazan dau asaraba. Mutane aka cika sai kallonta ake tana ta zagezage, hakuri ake bata amma sam tace bazata hakura ba,alhalin kuma itace mara gaskiya, reader's kuji karfin hali fa.😆

Wani mutumi ne yaga ana ta hayaniya, yayi parking aka bashi labarin abinda yake faruwa,yace mai napep din yatafi zai biya, yayi masa godiya yatafi.

Bakaniken sa yayiwa waya, cikin yan muntuna kuwa ya iso aka gyara mata motar, me makon tayi godiya secewa tayi "Allah ya taimakeku wlh da kunga bala 'i " tafigi mota tayi gaba. Mutane kuwa sai Allah waidai suke da irin su bintu.

Gidansu ta nufa, tabawa hajiyarta lbrn abinda Sadiq yayi mata yau da safe, da sauri hajiyan tace "shi Sadiq dinne yace haka" bintu ta gyada kai "to lallai gobe senayi miki hadin zuciyar kare, da kaina zan doka uban sammako naje barikin sojoji, idan sun yanka kare subani zuciyar, akwai wani hadi da wata aminiyata tafada min, indai akayisa, to sai yacce kikayi dashi, babu boka babu malam, kedai duk abinda zaice kiyi mishi shuru, gobe zanxo da kaina in kawo miki"

Rungumeta bintu tayi tace "yawwa hajiyata, shiyasa nakesonki, kina kawo wuta" suka kwashe da dariya, hira suka sha Sosai, sai yamma likis bintu tafara shirin tafiya

"Hajiya bari in tashi inje in shirya, zani gidan suna" Jakarta ta bude ta dauko dubu goma ta mikawa hajiya, ta amshe tana godiya, sukayi sallama...

Sadiq kuwa tunda yaje office kasa aikata komai yayi, tunani ne fal akansa, ga wata uwar rama dayayi, dayaga hakan bazai samu wata mafuta bane yasa ya tattara aikin ya ajiye ya nufi gidansu...

Yana shiga falon wani kamshin abinci mai dadi ya doshi hancinsa,da kyar ya hadiye yawun bakinsa, yayi sallama baki na rawa,jin shuru bawanda ya amsa mishi ne yasa yawuce kitchen kansa tsaye...

Khadija yatarar tana ta soya kayan miya da alama jolof zatayi, sallama yayi ta amsa da fara'arta "yaya Sadiq yau Kaine a gidan" murmushi yak'e yayi mata, dan gaba daya hankalinsa yana kan tukunyar dataketa faman juyawa "ehh nine nazo dije, tunda ke bazaki taba iya daukar kafa kizo inda muke ba"

"Yaya kasan halin ummana, sam bata son na matsa nan da cen, daga makaranta sai gida" tabe baki yayi"to yar umma, ina Umman taki take naketa sallama" yanzu ta shiga nan makota barka,amma tace bazata dade ba, kozaka zauna na kirawo maka ita? ah'ah ba sauri nake ba, bari na zauna a falo na jirata" ya fice, ita kuma ta cigaba da girkinta....

Zama yayi a falon yana kallo amma kamshin girkin khadija ya cika mishi ciki, jiyake kamar yaje yace tai sauri ta kawo mishi... Yana wannan tunanin kuwa sai gata dauke ta tere ta hado mishi, tunda ta shigo yake Allah Allah ta ajiye yafara ci....tun kafin ta gama ajiye masa ya karba ya ajiye agabansa, bude kulan yayi, jolof din couscous ne, yaji vegetables, da kaji..

Bai tsaya zubawa a plate ba yasa cokali yana ci,ciyake hannu baka hannu k'warya,dan yau ko tea din daya saba sha a office, bai samu yasha ba.

Khadija kuwa binsa take da kallo,sai a lokacin taga uwar ramar da yayi, tunani tafara yi a zuciyarta, meya ramar da shi haka? Kuma meyasa yake irin wannan cin abincin kamar wani dan kauye? Nan da nan taji tausayinsa yakamata "dagani akwai abinda yake damun yaya, koma meye Allah ka yaye masa" tafada a zuciyarta kafin tace "yaya sadiq kaci a hankali, idan bai isaba akwai wani" kunya ce ta kama shi,dan yama manta tana wajen, amma ya dake yace "cemiki akayi ina jin yunwa sosai ne? tashi ma kibani waje" dariya ce ta taho mata, ta tashi da gudu ta bar falon..

Seda ya cinye abincin tasss!!!! Yasha lemonsa mai sanyi, yakora da ruwan sanyi, wata nutsuwa ce ta saukar masa, take wani bacci mai dadi yayi awon gaba da shi.....

Bintu kuwa tana komawa gidan taga bai dawo ba,dadi ya kamata, batawani sakeyin wanka ba, kayan jikinta kawai ta sauya ta dau kwalliya tayi gidan suna....

*WRITTEN*📝
*BY*
*DEEE*💘
08177892239.


*🌚GANTALLIYA🌚*

*WRITTEN*📝
*BY*
*DEEE*💘


*⚜🇦rewa 🇼riters🇫orum⚜*


*• Follow us on facebook*~ _
www.facebook.com/Arewa-Writers-Forum-294302397727161/


*Dedicated to DEEE💘 NOVELS GROUP❤ THANK YOU FOR THE LOVE*😍



11-15

Baccinsa yakesha bilhaqqi, har aka fara kiran sallar magariba, bashida niyyar farkawa, khadija ce ta fito ta duba shi, tasameshi shameshame, rike baki tayi tana "ikon Allah, wannan ko lafiyarsa kuwa?

Sallamar ummansu ce ta dakatar da ita,bata amsa sallamar ba tace "yauwa Alhamdulillah! Umma zokiga abun mamaki" karasowa ummansu tayi tace "au wannan kuma yaushe yazo? Rike k'ugu tayi tabata labarin abinda yafaru tun zuwansa "umma nifa ina ganin akwai abinda yake damun yaya, kalla fa yanda ya rame, kamar wanda ya tashi daga cuta"

Umma batace komai ba, illa karewa sadiq kallo da tayi, tabbas itama ta hango akwai wani abu, amma batace komai ba, tashinsa tafarayi "sadiq! Sadiq! Tashi maza katafi masallaci gashi cen anata kiran sallah" da sauri ya mik'e " ah umma kin dawo, yaushe kika dawo bansani ba" yafada atare "kaje kayi sallah nace, inka dawo mayi magana" ta wuce dakinta khadija ma tabi bayanta...

Bayan yadawo daga masallacin ne, yasame su afalo,khadija ta dora kanta a cinyar umma sai zuba shagwaba takeyi, "yaya kadawo? sannu da zuwa, khadija tafada tana kallonshi, umma ma tunda ya shigo idonta akanshi yake "ehh dijen gala nadawo" kukan shagwaba tasaka "umma kinji yana cemin dijen gala koh" d'aga mishi dan yatsa tayi "au dama zuwa kayi kasamin y'a kuka kenan, batace maka bata son sunan nan bane" zama yayi yana fadin "tuba nake nadena"

Har k'asa ya tsugunna ya gaida mahaifiyarsa, bayan sungama gaisawa ne ya lura da irin kallon da umma kemasa, sunkuyar da kai ya dungayi yana jin kunya, dan yasan halin mahaifiyarsa akwai ta da lura, yanzu haka tagano akwai damuwa a tattare da shi.

Gyaran murya umma tayi tace "nikam sadiq rashin lafiya kayi ne haka" dammm! yaji gabanshi ya fadi "emmm aaamm mai kika gani umma?

"Gani nayi duk ka rame kamar wanda yatashi ajinya" sosa keya yayi yace "wallahi umma aiki ne yayi min yawa a office, ko abinci bana samun damar ci sosai, shiyasa na dan rame"

"Au kadan rame? Anya sadiq kana kallon madubi kuwa? Kaga uban dogon wuyan da ka ajiye kuwa, gawani uban gashin baki daka tara, abinda nasan kwata kwata da bakayi, to waima shin ita bintun tana ina take barinka kake futa baka ci abinci ba?

Yak'e yayi "umma ai bintu tana iya bakin k'okarinta taga naci abinci, nine dai bani da lokaci, har fada itama mukeyi da ita akan k'in cin abinci" tunda yake magana umma take harararsa, dan daga yanayinsa tasan karya yake mata "toh sannu shugaban k'asa sarkin aiki"

Sosa k'eya yayi yace "wallahi kuwa umma, amma zan dauki hutu,nasamu nadan huta nima" gyada kai umma tayi "Allah ya taimaka, yanzu ai seka tashi katafi gida kar bintun taga kayi dare ko? Ehh haka ne kam umma, nima yanzu nake niyya"

Amma a cikin ransa yace "wannan GANTALALLIYAR bama sai idan tana gidan ba" mikewa yayi zai tafi khadija tace "yaya ka tsaya kaci abincin dare mana" kamar yace zai zauna, amma sabida umma yace "ke madam na cen ta hada min favorite dina, intake jira nasani" *kuji karya k'iri k'iri*😆

Kallo kawai umma tabisu dashi yayi musu sallama yafita, yana dama karya koma gidansa, yazauna tare da mahaifiyarsa da kanwarsa...

Yana fita umma tace "Allah ya kyauta, amma nidai nasan akwai abinda sadiq ya boye min" karaf khadija tace "umma ko fada sukayi da anty bintu" atsawace umma tace "nidai banfada ba,kuma Karna sake jin kinfadi haka" kiyi hakuri umma" naji, d'agani ninaje nayi sallah...

Bangaren sadiq kuwa yana komawa gida dakinsa ya nufa, dan yasan kozai mutu bintu bazata zauna a gida bata futa ba, ruwa ya watsa yadawo yayi sallar isha'i, seda yadade a sujjadarsa ta karshe yana rok'on Allah ya shiryi matarsa, Allah yakawo ranar da bintu zata dena abinda takeyi su zauna lafiya, harga Allah babu wata mata dayakeson zaman aure da ita irin bintu, duk matan da suke binsa har office suna cewa suna sonsa gaba daya basa gabanshi, son da yakewa bintu Allah ne kadai yasani, gashi tana wahalar dashi,shiyasa kullum addu'arsa Allah ya shiryeta ya daidaita tsakaninsu... Da haka har bacci ya daukeshi baiji shigowarta ba.....

Ita ko bintu *GANTALALLIYA* ana cen gidan suna duniya tayi dadi,abincin da aka kawo mata na suna,tuwon shinkafa da miyar taushe, sai waina da sunasir,kadan taci, tafaki ido,ta bude Jakarta ta dauko wata katuwar bakar leda ta juye tuwon, waina da sinasir, ta zura su cikin jaka, tasake dauko wata ledar ta juye miyar taushen tayi fuska, sai yak'e takeyi....

Ashe duk abinda takeyi wasu mata biyu suna kallonta daga baya, d'aya ce tafara gani ta tabo d'ayar "laaaaa kinga wata mata, wanka iya wanka tayi, hada gwal ajikinta, amma tana juye abinci a leda, kodai irin matan nan ne masu aro kaya? Seda ta kare mata kallo tace "ai bintu GANTALALLIYA ce matar sadiq, mijinta abokin mijina ne, bakaramin mai kudi bane, amma bata da aiki sai yawo gida gida, biki kam ko ba,a gayyaceta ba setaje,tadebo abinci, dan bata girki a gidanta, ga k'azantar masifa,rowa kuwa ba'a cewa komai, da ta bayar da abu ta gwammaci ya lalaci. Shiyasa ma ni bana shiri da ita dan bata da kamun kai ko kadan" jinjinawa d'ayar tayi tace "Tabb gaskiya mijinta yana fama" jiyowa bintu tayi ta kallesu suka wayanci suka dau wata hirar... Ba ita ta baro gidan suna ba sai bayan sallar isha'i, daga nan tayi gidan aminiyarta hajiya turai.....

Afalo ta sameta ta dora kafa daya kan daya tana waya, ko sallama babu, tana ganinta suka kwashe da shewa "ahayyye chasss! Suka kwashe da dariya, hajiya turai ce tace "shegiyar ashe kina tafe" cire mayafi bintu take kokarin yi tace "ina tafe wallahi, daga gidan suna nake"

"Ya gogan naki kuwa" tabe baki tayi kafin tace "ehmm waya san mishi ne, ai baki san ma wani sabon salon iskanci ba? Gyara zama hajiya turai tayi tace bani nasha" wai yau ni sadiq zaicewa karna sake na fita daga gida, bama wannan ba, nace yabani makullin motarsa wai ai ba daga gidanmu nazo dashi ba" dariya hajiya turai ta kwashe da shi kafin tace "mena fada miki, ai seda nace kizo mukoma wajen lud'iya kika k'i, gashi nan, ai kadan kika gani a aikin namiji, saura yayi waje dake , koya auro wata matar yayi banza dake" wani uban ashar bintu ta zunduma tana "aiko bai isa ba wlh, nafi k'arfinshi.....ni wlh lud'iyan ne tsoro yake bani, shiyasa bana son komawa, gashi sai dare ake zuwa" wani kallo hajiya turai ta watsa mata "to ai sai ki zauna namiji yaita wahalar dake, kwanaki da mukaje, ke kanki baki ji dadi ba,ki juya shi yanda kike so, amma yanzu gashi asirin yafara karyewa ke zai fara juyaki, ke da bakinki kika fada mijinki baya wasa da addini, kuma kinsan irinwayannan idan ba tashi kikayi a tasayeba kezakiyi kuka da idonki" shuru bintu tayi,hudubar hajiya turai tana ratsata, tuni ta amince mata "to yanzu ya kike ganin za'ayi? Shawara ta rage taki, ni ko yanzu kikeso ashirye nake"

"Kibari dai sai gobe, akwai wata aminiyata ma da mijinta yake kawo mata matasala, inyaso sai muje tare" murmushin k'eta tayi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment