Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

¹Aalimah*
SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI*

07030137870*

FREE PAGES 1


Jirgin ‘American Airways’ ya sauke AALIMAH MANSOUR a birnin Massachusetts na kasar Amurka a ranar ashirin da biyar ga watan Mayu, na shekara ta dubu biyu da goma sha shidda(2016). A sannu ta bi jerin gwanon masu saukowa daga jirgin rataye da matsakaiciyar jakar hannu ta mata. Sanye ta ke da doguwar riga da veil dinta kirarTahran (maroon colour) ta zagaye fuskarta da veil din rigar. Takalmin kafarta baki ne mahadin jakar hannunta marar tsayin dunduniya. Taku ta ke cikin nutsuwa har ta taka kwaltar filin jirgin (Boston Logan International Airport) ta shiga van din da sauran fasinjoji ke shigawadda za ta karasa da su zuwa ainahin ginin cikin filin jirgin, inda aka yi mata duk wasu immigration checks, daga karshe ta dauko jakar kayanta ta fito.
Hasken sassanyar ranar da ya soma ketowa ya dallare mata ido, ta sanya tafin hannunta ta kare saman idanunta daidai lokacin da masu taxi suka soma isowa gare ta.
Tambayarta suke inda za a kai ta. Ta diregajiyayyun dara-daran idanunta a kansu kamar mai kiyasi, kamar kuma mai tantance wanda ya kamata ta zaba,da ganinta ka ga bakoa kasar da bai taba zuwa ba, kafin ta tsaida idonta a kan wani dan tsamurmurin bature ta nuna mishi adireshin inda zai kai ta, wanda ke rubuce cikin jotter dinta, wadda ta fiddo daga jakar hannunta. Daukar jakar tata ya yi ya sanya a bayan motarsa ya bude mata kofar baya, ta shiga ta zauna. Ya zagaya ya shiga mazauninsa, ya tada motar.
Tafiya suke sannu kan hankali a kan kwaltar manyan titunan birnin Massachusetts tana karewa kyawawan titunan kallo.
Birnin Massachusetts na daya daga cikin manyan biranen da kasar Amurka ke tinkaho da su. Ya kuma kunshi al’ummatai daban-daban, daga yarekala-kala na duniya. An kiyasta population din birnin Massachusetts a shekarar (2017) da adadin (685, 094 population).

Yana kusa da Cambridge daga gabas, tana iyaka da Hampshire da Vermot daga Arewa, daga yamma zagaye yake da babban birniNew York, daga Kudu da birnin Connecticut da Rhode Island. Daga gabas kuma zagaye ta ke da Atlantic Ocean. Birni ne daga Arewa maso gabashin USA.

Mai taxi ya tsayar da motar a cikin estate din (Martha’s Vineyard) a kofar wani kyakkywan lodge cikin birnin BOSTON (Capital of Massachusetts).

Aalimah Mansour, ta yi ajiyar zuciya, ta lalubo adadin kudin da ya bukata ta ba shi, ya ba ta canjinta, ya kuma fitar mata da jakarta daga bayan motarsa. Sannu a hankali ta karasa kofar gidan tana nazarin kayatacciyar unguwar. Tana daga cikin manyan estate (kebantattun unguwanni) a birnin Boston. A saman kofar gidan an rubuta lambar gidan da kuma sunan mamallakin sa ‘ISHAQ RAAZEE’.
Kararrarwar kofar gidan ta shiga dannawa, sai da ta danna sau uku kafin ta jiyo muryar mace na fadin tana zuwa cikin harshen Nasara. Gabanta ya ci gaba da lugude kamar zuciyarta za ta fado daga cikin kirjinta. Ba ta da idea na irin karbar da za ta samu daga Kawun nata, haka ba ta da sanin irin karbar da za ta samu daga matarsa Mummy Zulaiha da ‘ya’yanta, matar da kowa a family dinsu ya kwana da sanin ba ta son kowa ya rabe ta, daga mijintasai ‘ya’yanta. Kada a rabi inuwar arzikin da suke ciki. Balle kuma su, da nata mahaifin duk cikin zuri’arsu shi ne mai karamin karfi. Banda Mamada ta dage ba za ta yi zaman hostel ba, alhalin ga Kawunta da iyalinsa a kasar da ba abin da zai kawo ta gidan Kawun nata.
Ta tabbata sai ta fi samun nutsuwa a zaman hostel din, amma ya ya za ta yi da umarnin iyayenta? Ta riga ta dora zuciyarta a kan son karatun nan, kamar yadda ta ke son rayuwarta. Sannan ba ta san kowa ba a kasar bayan su. Asstrict as her Mum is, (sabida tsantseni irin na mahaifiyarta) a kan tarbiyyah, ta tabbatar mata ko dai ta zauna gidan Kawunta ta yi karatun a gabansa, ta fuskanci kowannne irin kalubale na matarsa da ‘ya’yansa, ko ta hakura ta yi aure. Hankalinta zai fi kwantawa ita ta hakura da nata burin akan karatun nata.
Mahmoud, saurayi daya data ke da shi a rayuwarta, ko ta ce wanda ya taba cewa yana son ta da kalmar aure, dalibi ne shibai shirya ba, yanzu ne yake shekarar karshe a jami’a, sun kulla soyayyarsu ita da Mahmud Kaita ba tare da sanin iyayenta ba, karewa ma boye tarayyarta da Mahmud ta ke don muddin Mama ta san tana da tsayayye, duk sonta da karatun ga ‘yar tata, za ta hakura ne ta yi mata aure. Banda babban Yayanta Aboubacar (Abubakar)babu wanda ya san da maganagr Mahmud a gidansu, shi ma ya sani ne a dalilin Mahmud din abokinsa ne, kuma ta dalilinsa suka san juna.
Duk wannan tunanin Aalimah na yin shi ne a tsaye a kofar gidan Kawunta kafin a zo a bude mata kofar, cikin mintunan da ba su gaza biyar ba. A daidai lokacin ne kuma Easther (‘yar aikin) Mummy Zulaiha ta bude mata kofa. Kallon juna suka tsaya yi na rashin sani ita da Easther din na ‘yan sakanni, kafin ta ba ta hanya tare da yi mata alamun ta wuce ciki ba tareda ta tambayeta wanda ta zo nema ba. Ba kuma komai ya sanya Easther bai wa Aaalimah hanya babu tambaya ba, sai kamanninta da ta gani mai dimbin yawa da yaran gidan, musamman matan.
Aalimah ta wuce ciki tana jan jakarta cikin nutsuwa. Easther ta mayar da kofar ta rufe. Daidai lokacin da Mummy Zulaiha ta bullo daga upstairs a shirye tsaf, tana taku kwaf-kwaf akan tsanin takalmin ta irinna matan da duniya ke yi da su, suka kuma sameta dai-dai da ra’ayinsu, makale da jakar hannu da mukullin mota alamar fita za ta yi.
Sakin baki ta yi cikin madaukakin mamaki tana kallon ba’abziniyar budurwar da ke shigowa. Doguwa, sambaleliya, fara tas! Mai dogon hanci da manyan fararen idanu, labbanta sirara jazur da su, ma’abociyar yalwar sumar kai, wadda ta fallasa kasantuwarta daga ruwa biyu, wato kallo daya za ka yi mata ka fahimci ba cikakkiyar bahaushiya ba ce, jinin su maigidanta Ishaq Razee ce. Yarinya ta karshe da ta yi tsammanin gani a kasar America, kuma cikin gidanta, a dai cikin family din maigidanta.

Aalimah ta saki murmushin yake, wani lallausan murmushi mai ban sha’awa na nuna ladabi, ta russuna tana gaida matar Kawunta, wadda mamaki ya hana ta ce mata kanzil. Sai da ta gaishe ta har sau biyu, Zulaiha ba ta farfado daga suman mamakin wucin-gadin da ta yi ba, har sai da karamar ‘yarta Yasmin ta taba ta, tana fadin,
“Mummy ana gaishe kiâ€.
Firgigit ta yi, ta dubi Aalimah tana ayyana abubuwa da yawa a cikin ranta, me ya kawota? Wato Ishaq wuyansa ya yi kaurin da zai soma kwaso abzinawan danginsa yana kawo mata gida ba tare da shawara da ita ba? Abin da ba za ta taba dauka ba kenan. Amsa gaisuwar ta yi kadaran-kadahankafin cikin shaqaqqiyar murya ta ce,
“Ke da wa ku ka zo?â€
Aalimah ta sunkuyar da kai cikin muryarta mai sanyi, ta ce,
“Ni kadai ce Auntyâ€.
“Ke kadai tun daga Nigeria?â€
Ta daga mata kai alamar “Ehâ€.
Kamar za ta ce wani abu, sai kuma ta fasa ta ci gaba da saukowa daga stairs din. Ta dubi Easther cikin rashin walwala ta ce,
“Ki ba ta abinci ki nuna mata dakin kwana, ni fita zan yiâ€.
Easther ta amsa, “Yes, Ma!â€
Ta dubi Aalimah cikin hadiye fushi ta ce, “Ki wuce ku je. Sai na dawo. Zan kai Yasmin makaranta ne, daga can zan koma officeâ€.
Cike da ladabi Aalimah ta amsa, ta bi bayan Easther, Mummy Zulaiha da ‘yarta Yasmin suka fita.

Gidan Ishaq Raazee karamin ‘American lodge’ ne, ginin sama da kasa. A saman, dakin maigidan da na matar gidan har ma da na yaransu mata guda uku yake. A kasa kicin ne da babban English parlour wanda a cikinsa dakin manyan ‘ya’yansu maza yake. Mai aikin gidan, wato Easther ba ta kwana, zuwa ta ke da safe ta tafi da yamma in ta kare girkin dare. Don haka Easther ta rasa dakin da za ta kai bakuwa Aalimah, gidan ba a gina shi da niyyar karbar baki ba, tana ganin bai kamata ta kai ta sama ba, tunda maigidan a sama yake, bai kuma kamata ta ajiye ta a kasa ba babu kowa sai ita kadai. A falon kasan, akwai wani daki bayan na Yayansu dake makaranta, amma a rufe yake ba ta taba ganin an bude shi ba, balle tayi tunanin ajiye ta anan, don haka sai ta kai ta dakin su Yasmin kawai, wanda ke daura da na mahaifiyarsu. Cike da zullumin ko ta yi ba daidai ba. Ta koma kicin ta hado mata abinci a kan ‘tray’ ta ajiye mata a gefen gado. Ta yi mata sallama ta koma bakin aikinta.
Kafin Aalimah ta yi komai, wanka ta shiga don ji ta ke jikinta har wani danko-danko yake mata. Ga ta da son wanka dama kamar agwagwa komai sanyi, balle kuma a lokacin zafi. Hatta gashin kanta ji ta yi yana mata kaikayi – kaikayi, duk da yau kwananta uku da wanke shi. Ta sunce ta dauko kayan wankanta daga jakarta ta shiga toilet din da ke cikin dakin.
Ta tsaya na dan lokaci tana nazarin bandakin. Ba ta taba zuwa kasar waje ba, amma kuma hakan bai maida ita bakauyiya ba. Nazarin bandakin ta shiga yi wanda ke dauke da bathtube na jacuzzi, kalarsa light blue komai da ke cikin bandakin kalarsa kenan. Ta mika hannu ta zare ribbon din da ta daure tulin gashinta ya wargaje a kafadunta, baki sidik mai tsayi da salki, na abzinawan usli.
A cikin toilet din har da hand dryer makale a gefe. Ba karamin jin dadin hakan ta yi ba. Ga shampoos nan kala-kala masu tsada a jere, wannan na da nasaba da kasancewar su ma yaran gidan mata guda uku, gashin gare su kamar ita. A lokacin ta manta da komai ta tara ruwan dumi cikin jacuzzi ta shiga ta soma abin da ta fi so a rayuwarta, wato ‘wanka’. Ta jima tana kalkale sassalkar fatar jikinta kafin ta soma wanke sumar kanta tana cudawa da kumfar(head& shoulder). Ta gama ta busar da shi da hand dryer, ta dauro alwala ta fito. Doguwar rigar atamfa (fitted-gown) ta sanya ta dauko hijabin sallarta ta tada sallah.
Sai da ta rama sallolin da ake binta sannan ta samu nutsuwa tazauna ta soma cin abincin.
Faten dankalin Turawa ne da aka yi da Mushroom da zallar tsokar naman kaza. A gefe kuma gasasshiyar hanta ce a cikin bowl na tangaran ta sanya fork tana cin hantar a hankali bayan ta gama da faten dankalin. Da ta gama, ta kora da lemun kwali na Apple mai sanyi, sannan ta kishingida a sofa tana hutawa.

Mamanta, Daddynsu, kannenta da masoyinta Mahmud suka fado mata a rai. Ta san suna can suna sauraron kiran wayarta. Da sauri ta sauko daga gadon ta lalubo wayar a jakarta. Tana kunnawa ta tuno ba ta da internet connection, kuma ba ta da credit na kasar. A rashin saninta da cewa gidan (WiFi) suke amfani dashi. Ta maida wayar gefe ta ajiye ta dauki kayan da ta ci abinci da su ta sauko kasa.
Kofofin falon ta shiga nazari tana son gano wacce ce ta kicin?Sai ta jiyo karar kwanuka kamar ana wanke-wanke da karar zubar ruwa daga famfo. Nan ta gane kofar da ke can karshe ita ce kicin. Ta karasa ta tadda Easther suka yi wa juna murmushi na rashin sabo, Easther ta karbi ‘tray’ din ta hada da wadanda take wankewa, sai ta kasa komawa daki ta jingina da cabinet din kicin suka soma hira.
Aalimah ta ce tana so ta taimaka mata su ci gaba da aikin tare. Easther ta ce ta rufa mata asiri ta koma daki kada ta yi laifi wajen uwar dakinta, tunda ba ta ce ta sa ta aiki ba. Amma ta kasa komawar, sai ta samu daya daga kujerun karamin dining da ke cikin kicin din ta zauna, Easther na aikin suna hira jefi-jefi da turancinta mai rauni.
Easther ‘yar Africa ce, wato bakar fata wadda aka haifa ta kuma girma a kasar Amurka, wadanda ake kira black- American. Ta ke gaya wa Aalimah su ‘yan asalin kasar Ghana ne daga Kumasi, iyayenta da kakanninta duk a nan aka haife su sun rayu tsayin rayuwarsu suna yi wa Turawa bauta. Ta tambayi Aalimah amma ita ‘yar uwar Daddy ce ko? Don ta ga tana kama da shi da ‘ya’yansa. Aalimah ta gaya mata cewa; “Wan babanta ne Ishaq Razeeâ€.
Daidai lokacin da suka ji shigowar motoci har guda biyu, daya ta maigidan, daya ta Mummy. Yaransu ne suka fara shigowa daya bayan daya suna ta hayaniya, Aalimah ta dawo kofar kicin tana kallonsu. Basma ce a gaba, sai Khalisat sai auta Yasmin. Rabonta da su shekara shidda kenan zuwansu Nigeria na karshe. Lokacin Aunty Zulaiha na da cikin Yasmin. Duk sun yi wani irin girma mai ban mamaki da ban sha’awa, irin girman ‘ya’yan Turawa. Ba mai cewa Basma sa’arta ce domin ta yi biyunta a girman jiki. Mai bi mata Khalisat, Aalimah ta girme ta da shekaru biyu, shekarunta goma sha hudu. Ita da Basma za su yi sha shidda da ‘yan watanni. Bayan haihuwar Khalisat Mummy Zulaiha ta dade ba ta haihu ba,sai da Khalisat ta yi shekaru takwas,sannan ta haifi autarta Yasmin.
Haihuwarta ta farko da ta biyu ‘ya’ya maza ne. Su ma tsakaninsu ratar shekaru biyar ne, haihuwa irin ta turawa Mummy Zulaiha ke yi, haihuwar Khaleesat data yi shekaru biyu bayan ta Basma (unwanted pregnancy) ne wanda ba yadda zata yi da shi.Data haife tan kuma, sai tafi sonta fiye da dukkan ‘ya’yanta mata. Itama Khalisan bata aje Mummy kusa da kowa na gidan ba a kauna da shakuwa. Idan ka dubi Mummy Zulaiha ba za ka ce ta haifi wadannan zaratan ‘ya’yan ba saboda hutu da kula da jiki. Shekarunta sun kusa hamsin, amma tsammani za ka yi talatin da biyar gare ta.
Daga ita har maigidanta Ishaq sun yi auren wuri, aure na soyayya, irin makauniyar soyayyar da iyayenta suka gwammace su cire ta daga makaranta tun tana aji biyar na sakandire su aura wa Ishaq. A lokacin yana shekara ta uku a jami’ar Ahmadu Bello. Ko abin da zai rike ta ba shi da shi, ga hidimar karatu, don haka ya dauke ta ya tafi da ita kasarsu Niger Republic ya ajiye ta a family house dinsu, inda aka ba su daki a babban gidan na zuri’ar Mal. Ibrahim Raazi. Ya maida ita makarantar sakandire a nan garinsu, Yamai, duk da ba ta jin faransanci har a hankali ta koya, in ya samu hutun semester ne yake zuwa gida shi din ma ba kowanne ba.

Tun yana yaro yake son kasar Nigeria da son zama a cikinta, ko da ya gama sakandire ya ce da mahaifinsu Malam Ibrahim Razee shi a Nigeria zai yi jami’a yana sha’awar harshen turanci, bai hana shi ba, amma ya ce ya tafi tare da kaninsa ‘Mansour’ wanda ya samu double promotion sabida hazakarsa suka gama sakandire a shekara guda, shi ma ya yi karatun a can zai fi jinsa kamar a gida in suna tare.


3094856450
Sumayyah Kabara
Firstbank
Price 1&2 N400
6/28/21, 7:30 AM - Buhainat: **🌹 *Aalimah**🌹
*SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI*

07030137870

FREE PAGES 2

Ba su sha wahalar samun gurbi a jami’ar Ahmadu Bello ba, kasancewar a wancan lokacin neman masu yin karatun gwamnati ke yi ido rufe, ga kuma takardunsu sun yi kyau, wadanda aka yi wa fassarar takardun Nigeria, suka kuma shiga wani tsari na koyon harshen turanci da jami’ar ke yi a wancan lokacin, kasancewar sun yi karatunsu ne da harshen faransa. Komai tare suke yinsa a A.B.U kasantuwar baki da basu da kowa sai junansu, sannan kuma uwarsu daya ubansu daya.
A gida ba sa jituwa kasancewarsu sakonnin juna, kowanne kamar yana ganin hanjin dan uwansa. Amma da suka zo Nigeria ba su da kowa, dole suka rungume junansu. Wannan kuma wata hikima ce irin ta iyaye, mahaifinsu ya yi musu ba tare da saninsu ba.
Daga Mansour har Ishaq dukkansu gifted ne a karatu. Ba fanni daya suke karanta ba, Ishaq na nazarin International Relation, yayin da Mansour ke karantar Mass Communication. A hostel suke rayuwa, duk abin da suke bukata mahaifinsu na aiko musu ta banki.
Mahaifinsu babban malami ne ta daya bangaren kuma babban dan kasuwa a babban birni Yamai, yana sana’ar kasuwancin kayan abinci yana kuma taba kasuwancin rakuma da kiwonsu, wanda ya gada iyaye da kakanni. Matansa na aure guda biyu, wadanda ke haifa masa ‘ya’ya kusan a tare, don in wannan ta haihu yau, bayan sati daya ko wata daya za ka ji dayar ma ta haihu.

Inna Bintou da Inna Kasisi, sune matan Malam Raazee. Ishaq da Mansour ‘ya’yan Kasisi ne, wato uwargida. Haihuwa suke kusan duk shekara, don haka ‘ya’yan Malam Ibrahim ashirin da biyar a duniya kafin haihuwar ta tsaya wa matan nasa. Ishaq ba shi ne babba ba a ‘ya’yan Kasisi, yana da yayye har biyu, sannan shi, sai Mansour.
Ba duka ‘ya’yan Malam Razee ke son karatun boko ba, hasalima mazan duka ba sa so, sun fi son sana’ar mahaifinsu in ka cire Ishaq da Mansour, matan kuwa suna gama sakandire yake yi musu aure. Dalili kenan da sanda Ishaq ya zo masa da maganar ya samu matar aure a Nigeria yana so ya yi aure bai ja zancen da nisa ba, shi ya ma fi son hakan. Sai ya tuntubi Mansour ko shi ma yana da wadda yake so a hada? Ya ce shi kam ba yanzu ba, sai ya gama karatu.
Ishaq da Zulaiha sun hadu a jami’ar Ahmad Bello, kanwar wani course mate dinsa ce Ahmad Madobi, ‘yan asalin jihar Kano ne. Lokacin yana aji biyu a jami’,Zulaiha da ‘yan gidansu suka zo wajen Yayanta Ahmad, a lokacin yana tare da Ishaq Ba’abzine (kamar yadda suke kiransa). Abin nan da Turawa ke kira ‘love at first sight shi ya afku tsakanin Ishaq da Zulaiha.
Zulaiha baka ce (black beauty), yarinya danya sharaf ‘yar saandire. Iyayenta ba ‘yan boko ba ne, ‘yan kasuwa ne. Har Kano Ishaq ke zuwa daga Zaria wajen Zulaiha. Wata irin zazzafar soyayya ce ta shiga tsakaninsu, wadda ta sa iyayenta gwammacewa su cire ta daga makaranta su yi mata auren, don kuwa ta yi watsi da karatun ta kama Ishaq. Sai aka yi sa’a shi ma nashi iyayen ba masu tsattsauran ra’ayi ba ne a kan karatun, suka yi musu aure.

Hankalin iyayeyn Zulaiha bai tashi tashi ba sai da iyayen Ishaq suka ce Nijar za su tafi da ita can main house din su. Sun dauka tunda yana Nigeria bbai gama karatun ba haya zai kama su zauna. Daga karshe ba su da yadda za su yi, sun aminceAURE ba inda ba ya kai ‘ya mace, suka amince Ishaq ya tafi da matarsa kasarsa ta haihuwa, ya baro ta tare da iyayensa ya dawo makaranta ya ci gaba da karatunsa cikin kwanciyar hankali, tunda ya mallaki abin da zuciyarsa ke so.
A irin zaman amincin da ake yi tsakanin Inna Kasisi da Inna Bintou, ‘ya’yan wannan sune na waccan, sai ya zama cewa, Zulaiha surukar Bintou ce ba surukar Kasisi ba. Ita ke kula da al’amarinta tunda mijinta ba ya nan. Malam Razee bai ragi Zulaiha da komai ba ta fannin bukatunta tamkar mijinta na kusa da ita, makarantar da ta ke yi ma ta kudi ce, wadda shi ya sanya ta a can Yamai, har ta gama sakandire.
Sai dai sam Inna Bintou ba ta jin dadin surukuta da Zulaiha, sabida baudaddun halayenta;Yarinya ce mara godiyar Allah da fadin rai. Duk abin da suke mata a raine ta ke kallonsa ba ta godewa, ba ta jan jikokinsu a jiki, ba yaron da ya isa ya shigar mata daki. Ba ta taimaka musu da komai na hidimomin gida, ga ta da girman kai da raini ga kowa. Inna Kasisi kawai ta ke shakka a gidan, don ita kam ko kusa ba ta daukar raini, tana da zafi. Hatta ga ‘ya’yanta, mijinta ma lallaba ta yakeyi. Ita da kanta ta fahimci wasu daga halayen Zulaiha ba tare da Inna Bintou ta ankarar da ita ba. Don haka ta kara jan girmanta ta rike tamau a idanun Zulaiha. Ba ta shiga duk wata sabgarta, in taro suke yi a gidan na abin da ya shafi ‘ya’ya da jikokinsu, Zulaiha ba ta shiga sam, kullum tana killace kanta tana yi wa kowa kallon bai isa ba.
Malam Ibrahim bai san ko daya daga halayen Zulaiha ba, sosai yake kyautata mata iyakar iyawarsa, tunda yana ganin an rabo ta da iyayenta da kowa nata. Matan kuma babu wadda ta taba dosarsa da irin wannan zancen, don bai raine su da tsegumi da gutsiri tsoma ba.

Haka Inna Bintou ta yi ta hakuri da Zulaiha. A shekarar ne Ishaq da Mansour suka kammala karatunsu suka dawo gida. Kwarai Mansour ya ji dadin zaman Nigeria, ya ji yana son ci gaba da zama a can, musamman da yake ya yi nasa kamun shi ma a Nigeria. Don haka ya yi hidimar kasa a can kafin ya koma Nijar, yana
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

1 Comments On AALIMAH
avatar
nusaibah-2

3 months ago

Reply

I like dis book wllh

Please Login or Register in order to submit comment