Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

This Document is compiled by
Shuraihu Usman - 08140419490
YEAR of compilation - 2023;
Published to Taskarnovels.com.ng

TSAKA MAI WUYA...!!!
KOTU! KOTU!! KOTU!!!
21 April

"Hajiya Rahama munaso ki tabbatarwa da KOTU hujjojinki akan zargin da kikeyiwa direban gidanki YUSUF na kashe miki tilon 'yarki har lahira, Shin ya al'amarin yafaru ne? Kamashi kikayi dumu - dumu ko kuwa ya abin yake ne Hajiya?"

kotun cike take makil ba masaka tsinke sbd sauraron wannan shari'ah mai razanar da tunanin duk wanda yaji taken karar, hajiya rahama wadda ke tsaye a inda aka tana a kotun dan amsa tambayoyi ta gyara tsayuwarta sannan ta dubi lauyanta wanda yayimata wannan tambayar,
"Wato al'amrin yafaru ne da maraicen wata ranar juma'a dai - dai lokacin da SAFARA'U tadawo daga makaranta, tana shigowa gida kamar yadda tasaba sai ta nufi firji domin samun Maltina mai sanyi kamar yadda tasaba, to awannan ranar sai akayi rashin sa'a domin kuwa maltinan dake gidan gabadaya ta kare, gashi kuma ta saba shanta kusan koda yaushe, dan inhar batasha ba to ba kasafai take xama cikin walwala ba, dan hakane sai ta kira yusf direba ta aikeshi dayaje yasiyo mata maltina mai sanyi,

bayan dan takin lokaci sai yakawomata ta koma dakinta domin tasha, tundaga nan najita shiru har wajen magriba dan hakane sai na leka dakinta domin atunanina barci takeyi, to anan ne na tarar da ita ta mutu adakinta kuma kumfa cike abakinta wanda likitana ya tabbatarmin da cewa 'yata safara'u tasha GUBA ne wanda adalilin hakan tarasa ranta..."

Hajiya Rahama ta karashe ragowar zancen da kuka mai tsuma xuciya, Lauyan nata ya dubeta kana yace "yanzu likitan naki yana tare damu awannan kotun dan tabbatarwa da kotu cewa guba silar mutuwar 'yarki safara'u?" hajiya rahama ta amsa da 'Eh' Lauyan yakoma xuwa ga Alkali domin neman ixininsa dan gabatar da likitan Hajiyar"

Dakta kotu tanaso ka gabatar da kanka da kuma hujjoji irin naku na likitoci wanda ya tabbatar da cewa safara'u GUBA ce ta xama silar shekawarta lahira" Likitan dan baki mai kira irin ta mutane kudu wato Dan Tittirna yafito yaxo yatsaya kana ya gabatarwa da kotu duk hujjoji da kuma bayanai a rubuce wanda ya tabbatar da cewa safara'u ta mutu ne sanadiyar guba da tasha.

Lauyan ya maida dubansa xuwa ga wanda ake xargin yacemasa "Malam yusuf wacca hikima ce ko riba agareka da har kaxamo sila na mutuwar 'yar uwar gijiyarka? Shin menene yakaika ga aiwatar da wannan cin AMANAR haka?"
Tuni idanun kowa dake cikin kotun yakoma xuwa kan Dan Matashin saurayin wanda ake kira da yusuf Direba, jabir yadago kai yai duba ixuwa cikin kotun wanda kamar an umarceshi daya mayar da kansa kasa sai ya mayar da dubansa xuwa kasa, hawayene ke fita daga fuskarsa, hannayensa hagu da dama daure suke cikin sasari.

"Inna Lillahi wa'inna ilaihir raju'un Na rantse da sarkin dake busamin numfashina ban aiwatar da wani abu ba wanda yaxamo sanadiyar mutuwar safara'u ba, aikena kawai tayi kuma nasiyo nakawomata nafita sai kawai naga rundunar 'yan sanda taxo gidan hajiya kuma akarshe suka cakumeni suka tafi dani da sunan nine na kashe safara'u, wlh bani bane... Kutaimakawa rayuwata... Mahaifiyata bata da lfy nine gatanta wlh... Batasan halin danake ciki ba yanxu... Banaso taji sbd xai iya xama silar rasa ranta idan har taji ankamani da xargin kisan kai kuma a gidan danake aiki... Gidan danake bata lbrn irin karamcin da akemin a gidan...

Innalillahi Wa'inna Ilaihir rajun... Kutaimakawa rayuwata wlh ko bera bantaba kashewa ba balle mutum guda..."
"Ya mai girma mai shari'a abisa kwararan hujjoji da muka gabatar daga wajen bayanan Hajiya Rahama da kuma likitan ta to tabbas hakan ya isa ya gamsar da kotu cewa yusuf Direba shine sanadiyar mutuwar 'yar Hajiya Rahama, kuma ga duk kan alamu yusuf yanuna kansa tunda yagaza bada dalilai masu karfi wanda karshe yabige da koke - koke wanda kuma wannan ba hujja bace da kotu xata dauka ko yarda da ita, Allah yataimaki mai shari'ah"

Lauya AIA kenan yagabatarwa da alkalin kotun jawabinsa na karshe wanda kuma daga nan ne ake dakon abinda alkalin xai xartar.
"kotu taji duk kan bayanai daga kowanne bangare, kuma kotu xata dage xaman wannan kara har nan da 28 ga wannan watan, wato nan da mako daya kenan, wanda ake xargi yana da damar daukar lauya wanda xai kareshi idan kuma har babu har xuwa wannan lokacin to kotu xata yanke hukunci akan abinda yake shine dai - dai kuma bisa hujjoji, sannan kotu tana umartar 'yan sanda akan sucigaba da tsare wanda ake xargin batare dayin beli ba"

Alkalin kotun kenan ya gabatar da jawabinsa wanda da hakane aka kawo karshen xaman wannan shari'ar ta yau.

ZAN CI GABA....

Daga Yusuf Æbdullâhi Æ JibagâTSAKA MAI MUYA 2...!

"Ai ina fadamaka wlh xai iya aikatawa, barganinsa wani sumi - sumi haka yanxu duniyar nan dakake gani da irin wannan sumi - sumin ake fakewa ana tafka ta'asa, kawai ya kashe 'yar mutane, kuma ni abin haushin ma kwastoma tace sosai dan kusan kullum sai ta fito taxo tasiyi tarin alawowi kala - kala, ko banxa ai yamin asarar ciniki, Allah ya isa na ma wlh, dan banza mai kirar 'yan daudu ashe shi karin kunama ne daga antabashi sai harbi" wanda ake fadawar yadan muskuta kadan daga kan dan bencin dake bakin 'yar karamar Tiredar, "wato kai musty bama ta rashin ranta kake ba kai ta asarar daina siyan kayanka kake ko? Wato kai ba ruwanka da jin kai da tausayi na 'yan uwantakar musulunci kenan?" wanda yafara maganar wanda kuma abokin hirar yakira da musty yadubi na biyun cikin alamun mamaki "to in banda abinda Habu sokake na kwanta xaxxabin Maleria sbd direban gidan masu hannu da shuni ya kashe 'yar gidan? Ko kuwa sokake naje kotun nace asakeshi a.......

kamani? Kawai yakashe musu 'ya dan haka sumatse dan banxa sai yatona asirin suwaye suka sashi." na biyun wanda musty mai tiredan yakira da Habu yadubi mustyn cikin alamun takaici "Ni kam wlh xuciyata tana bani tabbacin cewa wannan salihin bawan Allahn baxai iya aikata wannan mugun abin ba, wai dan inaneshi? Dan naga kamar dan kusa da unguwar nan ne" musty mai tireda yadubi Habu din yace "Dan layin CENTRAL MARKET can kasa xakaga wani gida mai kama da bukka to nan ne gidansu, kasan shi talaka dama bashi da kashin arziki inbanda haka kana aiki gida irin wannan amma katashi ka make 'yar gidan har lahira, haba!!!!

Ai wlh su jibgi dan banxa kawai, ni dama baya birgeni sbd yadda kullum nake ganinsa sumi - sumi baya kula mutane dan banzan" "kai musty kaji tsoron Allah, wlh Allah xaikamaka akan irin wannan kagen dakakeyiwa bawan Allahn nan, kai bakasan komai ba dangane da lamuran kasar nan, nan - nan sauro sai yakashe mutum axo ace wanine"

"hahahaha amma lallai habu agaisheka, sauro yabawa mutum guba har yasha ya mutu? Amma wannan sauron girmansa yakai girma kam" habu ya kurawa musty mai tireda idanu kana cikin takaici yamike tsaye wanda da alamu yaji xafin yadda yaga mustyn ya zake wajen kara aibata dan uwansa musulmi abisa abinda bashi da tabbacin hakan, " ni xan tafi, kuma Insha'allahu xanyi kokarin xuwa gidansu bawan Allahn dan bincikar ko iyayensa sunsan halin dayake ciki, dan yanda na lura kamar ita hajiya mai gidan baxa ta fadawa iyayen nasaba" musty mai tireda yadubi habu din bayan da habun haryafara tafiya da xummar barin wajen, "kace dai tsohuwarsa kawai, dan ni bantaba ganin ubansa ba, nasan dai tsohuwar gyatumarsa..."

****************************
Dogon layi ne mai matsakaicin fadi wanda hakan bayarasa nasaba da yawan dakalin da mutanen layin kowa ya malala wanda hakan yaxamo sanadiyar yiwa layin kamshin mutuwa ta yanda ya xamto bashi da fadi gabadaya, daga can kuryar yamma na layin yadanfi fadi sakamakon wasu gidaje guda biyu da basuyi dakalin ba, layin yalwace yake da wadatuwar yara ta ko ina wanda hakan yake nuni da cewa layin na 'ya 'yan malam SHEHU ne (talaka).

Dai - dai kusan wannan lokacin ne HABU ya shigo cikin layin, tafe yake yana ta rarraba idanu dan dai ganin ko xai iya gane gidan da musty mai tireda ya kira da MAI KAMAR BUKKA din, can idanunsa suka kai ga kuryar yamma na layin inda wasu gidaje guda biyu suke a ware waje daya, can daga gefe wasu tarin yarane axaune suna wasa dan haka kai tsaye habu yawuce xuwa ga yaran domin samun agajinsu wajen fadamasa inane ainihin gidansu YUsuf din.

"kai sannunku, inane gidansu yusuf dan Allah? wanda yake aiki a gidan hajia rahama dake layin G.R.A " wani yaro daga cikin ragowar yaran yai saurin bada amsar ta hanyar yin nuni da dan yatsansa xuwa ga daya daga cikin gidajen nan guda biyu dake ware waje daya, "gashi can wancan na farkon ne mai kofa abuden can" shine gidan su yusuf dan baba me kiran sallah daya rasu kwanaki=Habu yakai dubansa xuwa ga wararrun gidajen wanda sai yanzu ne ya lura ashe daya gidan arufe yake da alamu ma kangone wato babu kowa acikinsa, yayin da dayan wanda yaron yace shine nasu yusuf din yake a bude wayam, " Dan kanina shiga kace ana sallama, kace abokin yusuf ne kawai" cikin hanzari yaron ya runtuma da gudu xuwa cikin gidan, jim kadan sai gashi yafito, "Umman tasa tace ka karasa tana soron wai" kai tsaye habu yanufi kofar gidan.

"yauwa ina wuni Umma, ni abokin yusuf ne duk da nasan baki sanni ba..." Habu kenan bayan ya tarar da matar dake tsugune a xauren gidan wanda da alamu matar tana da karamci sbd yadda yanayinta yanuna hakan, "Allah sarki, hakane kam gaskia bansanka ba acikin abokanansa duk da dai shima bashi da yawan tarin abokanai din nan, kuma wlh kaga bayanan dan tun jiya bayan ansauko daga masallacin juma'a yaxo kawomin magunguna na sbd banajin dadi wlh, to tunda yacemin yatafi can gidan hajiyar to bai dawowa ba, nasan dama wani lokacin yakan kwana acan musamman idan yaga yakai dare acan"

MUHADU ZUWA INSHA ALLAHU DOMIN CIGABATSAKA MAI WUYA 3...!

Mahaifiyar yusuf taci gabada cewa"
Allah sarki, hakane kam gaskia bansanka ba acikin abokanansa duk da dai shima bashi da yawan tarin abokanai din nan, kuma wlh kaga bayanan dan tun jiya bayan ansauko daga masallacin juma'a yaxo kawomin magunguna na sbd banajin dadi wlh, to tunda yacemin yatafi can gidan hajiyar to bai dawowa ba, nasan dama wani lokacin yakan kwana acan musamman idan yaga yakai dare acan" Habu yadubi kamilar matar dake tsugune agabansa, tuni xuciyarsa tagama karyewa,

idanunsa tuni sun sauya yanayin kallon da sukeyiwa matar xuwa ABAR TAUSAYI. "Allah sarki, yanxun ma ai shine yabani sako yace naxo na sanar dake kada kijishi shiru, wai hajiyar ce ta aikeshi xuwa can kauyensu kuma tare da hajiyar xasu tafi to kuma abin na sauri ne to shine da sukaxo wucewa sai yatsaya yake fadamin akan cewa naxo na sanar dake kada hankalinki yatashi, kuma gashi yace nabaki wannan ki dada sbd bukatu dan baisan sanda xasu dawo ba..." yamika mata wasu kudade wanda ya kudurce aransa xai bawa matar wadda yake kalla amatsayin ABAR TAUSAYI. "to dan nan nagode kaji, kuma Allah yadawo dashi lafiya, ai duk acikin neman halak ne dan haka ba komai, Allah dai yatsareshi daga sharrin karfen nasara kullum addu'ar danakeyimasa kenan..."

Habu yafito daga xauren gidan bayan sunyi sallama da mahaifiyar yusuf din, xuciyarsa duk ta karye, haka kawai sai yaji yana tausayamusu, tabbas da ace shi mai kudi ne to da wlh sai ya taimakawa yusuf da kudin da xai dauki lauya dan kokarin gano gaskiyar al'amarin, ahaka har Habu yafice daga dan matashin layin mai dauke da yalwar yara ta ko ina.

"Yallabai barkanku kadai, Dan Allah inaso xanga yusuf ne wanda ake xargi da kashe 'yar gidan haj Rahama..." 'yan sanda guda biyu dake xaune a gindin kantar suka dubi junansu kamar sunji wani bakon al'amari, "Malam kayi hakuri gaskia, tunda can meyasa bakuxo kunganshiba sai ana gobe xa'a koma kotu sannan kaxo kace kanason ganinsa, gaskiya baza kasamu wannan damar ba yanxu..." Daya daga cikin 'yan sandan mai matsakaicin tsayin ne yake mayarwa da wanda yaxo da bukatar martani. "Dan girman Allah kutaimaka min, wlh rashin sanin awanne station yake tsare shine ya haifar da jinkirin hakan, Amma kuyi hakuri kutaimakamin dan girman Allah..." kana ya hada da xura hannu a aljihun dake gaban rigarsa ya xaro kudade ya dora agaban kantar dake gaban 'yan sandan, tuni dayan dabaiyi magana ba ya kwashe kudaden kana yadubi dayan wanda yake maganar yace masa "kofur tukuro je ka kaishi inda yake, amma abokina ka gaggauta akalla kada kawuce mintuna 15 sbd halin tsaro, dan inbandama kayi magiya dayawa da ba yadda xa'ayi kasamu damar ganinsa gaskiya..."

'yan sakwanni kadan yasadashi da wanda yaxo ganin, akulle yake adaya daga cikin biyun cell din dake cikin station din, koda baka taba ganinsa ba to kana ganinsa yanxu xakasan cewa tabbas yana cikin wani mawuyacin hali, ya karemasa kallo ga mamakinsa sai yaji kamar danshin ruwane a fuskarsa wanda hakan keyin nuni da gaxawar dauriyarsa wanda hakan yakaishi gayin hawaye, "Sunana Habu duk danasan bakasanniba malam yusuf, hakika naji duk labarinka a agari da yadda akai xaman kotu na farko da kuma jin cewa gobe xaku koma kotun, to shin wai abin tambayar kana tunanin daukar lauya ne? Naji anbe axaman farko anyishine ba hamayya sbd baka da lauya..." yusuf yadago jajayen idanunsa wanda dagani babu tambaya kasan cewa sun jigata wajen aikin kuka, "wlh bani da kowa sai Allah, kuma bantaba tunanin daukar lauya ba sbd bani da karfin daukar lauya, kawai abinda nasa araina kuma na aminta shine wannan kaddara ce wadda Allah ya kaddarowa rayuwata, kuma wannan hali na TSAKA MAI WUYA danake ciki bantaba tunanin cewa wani yasani acikinsa ba, bera bantabawa kashewa ba wlh balle mutum guda, me safara'u tamin da xan kasheta???..." ya karashe maganar da kukan xuci.

Habu ya kalli dan matashin cikin wani irin yanayi wanda da gani kasan cewa na tausayine, "Ni kaina ayadda naji labarin kuma naje na gana da mahaifiyarka sai na tabbatarda cewa baxa ka iya aikata hakan ba yusuf, tabbas akwai boyayyen al'amari awannan badakalar, hanya mai wahalarwar itace yadda xa'ayi agano bakin zaren, amma ina da tabbacin cewa bakai ka aikata hakan ba yusuf"

yusuf yadago da sauri alamun cewa akwai maganar data raxanashi a kalaman Habu, "kana nufin kasan gidanmu kuma har mahaifiyata taji labarin ana tuhumata da laifin kisan kai?" yusuf ya tambayi habu cikin kagauta, "ka kwantar da hankalinka mahaifiyarka bataji wannan mummunan labarin ba, sai dai ma nacemaka mahaifiyarka taji labarin cewa katafi kai hajiya rahama kauye ne kuma xaku dan dauki lokaci acan din, nine nan naje mata da wannan xantuttukan dan kwantar mata da hankali amatsayinta na mahaifiyarka, kuma insha'allahu gaskia xata bayyana xaka fito ka komawa mahaifiyarka batare dataji wannan mugun labarin ba,

yanxu xan barka anan, xanje nayi tunanin samun mafita dan neman lauyan da xai taimaka maka,

ZANCI GABA 9 PM NA GOBE INSHA ALLAHUTSAKA MAI WUYA 4...!

HABU yaci gabada cewa"xanje nayi tunanin samun mafita dan neman lauyan da xai taimaka maka, kuma koda munrasa lauya to ni xan iya tsayawa amatsayin lauya na wucin gadi domin ganin dai ba'a yankemaka hukunci a goben ba..."

tunda yabaro yusuf a sel yake ta tunanin hanyoyi kala - kala wanda xaisamu ta billewa domin ganin yusuf din yaxama wankakke a idon duniya, Abin yaxomasa akure ganin gobe ne xa'akuma xama xaman kotun wanda kuma ake saran yanke hukunci na karshe mutukar dai yusuf din bashi da kwararren lauya wanda xaisa adage shari'ar sbd hali na bincike, yasaka wancan ya kulla wancan kana ya kwance wancan da haka dai har barci barawo yakwasheshi batare daya samo wata hanya da xai iya taimakawa yusuf da ita ba a goben.

KOTU! KOTU!! KOTU!!!

Kotun tayi cikar kwari domin kuwa acike take makil ba masaka tsinke, hakan bayarasa nasaba da irin yadda labarin xaman farko yacika gari wanda har gidajen radio sai da suka ringa baza labarin da sunaye kala - kala akuma shirye - shirye daban - daban.

Shigowar mai alkalin itace ta tilastawa kowa dake kotun mikewa tsaye dan dai girmamawa ga alkalin kamar yadda tsarin kundin dokar kotu ya tanadar, zaman mai shari'ar ke wuya sai kowa yakoma yaxauna kana magatakardar kotun yamike tsaye dauke da takarta wadda take dauke da bayanin abubuwan da kotun xata gabatar axaman nata nayau.

"Ya mai shari'ah ayau ne kotu xataci gaba da sauraron karar da Hajiya Rahma ta shigar na zargin direban gidanta da kashemata 'yarta har lahira.."

A lokacin ne jami'an tsaro suka shigo da wanda ake xargin daure cikin sarka, tuni idanun daukacin mutanen kotun yakoma kan wanda ake xargin.

"Assalamu Alaikum Sunana Barrister AIA kuma nine lauyan Hajiya Rahama kamar yadda kotu tasani tun xaman farko na wannan kotu mai girma na gabatar da kwararan shaidu wadanda suka nuna cewa tabbas yusuf shine ya kashe safara'u 'yar gidan Hajiya Rahama ta sanadiyar shayar da ita guba acikin maltina, dan haka nake neman kotu data duba wadannan kwararan hujjoji dana gabatar tayiwa hajiya Rahama Adalci wajen yankewa wannan direban nata hukunci dai - dai da yarda yadace kuma kamar yadda doka ta tanadar, Nagode!"

Zaman lauya AIA daga bangaren hajiya keda wuya sai alkali ya juya kan wanda ake xargin wato yusuf ko yadauki lauyan daxai kareshi kamar yadda kotu tabashi wannan damar axaman farkon,

idanunsa tuni sunciko da kwallah, yagaxa cewa komai illah kukan xuci wanda har mutane suna iya jiyo sautin gurnanin fitar kukan nasa mai tsima xuciya ma'abociyar saurin jin tausayi.
"Assalamu Alaikum jama'a sunana Barrister hauwa'u Auwal, kuma nice xan kare wanda ake xargi yusuf dan haka nake gabatar da kaina ga kotu da kuma daukacin 'yan kallo..." tuni kallo yakoma sama ta yadda tuni kotun tacika da 'yan surutai wanda hakan bayarasa nasaba da ganin kyakykyawar budurwar data kira kanta da Barr hawa'u Auwal, acikin masu binta da mayataccen kallon harda yusuf dan saurayin dake tsaye amatsayin wanda ake xargi da kisan kai, dole ne taja xugar mutane wajen binta da kallo sbd tsabar kyanta kuma gashi ba xato ba tsammani ta gabatar da kanta amatsayin wadda xata kare dan matashin saurayin, Habu dake cikin dandaxon 'yan kallo tuni fuskarsa tadan saki daga rashin walwalar datake ciki, domin kuwa shi a shirye daya gabatar da kansa amatsayin wanda xai kare yusuf din duk kuwa da cewa ba abinda yataba hadashi da karatun lauya.

Kotun tai tsit! Wato 'yan surutan da akeyi yadauke sakamakon umarnin da alkalin ya bayar ta hanyar kada dan sautin dake nuni da hakan, "ya mai shari'ah inaso kotu tamin ixini xanyiwa Haj Rahama wasu tambayoyi..."

Barrister hauwa'u Auwal ce tanemi wannan ixinin daga kotun, kotu tayimata ixini dan haka tuni haj rahama ta bayyana agaban Barr hauwa'u Auwal din, "Hajiya Rahama ko zaki iya rike dai - dai lokacin da yusuf yafita daga gidanki da xummar siyowa safara'u maltina da kuma tsawon lokacin daya dauka yadawo dauke da maltinar dakike xargin itace silar mutuwar ta?" Hajiya Rahama ta amsa da "Eh wajen karfe 5 da 'yan mintunane ya fita daga gidan sannan kuma yadawo ne adan takin lokacin wanda baxan iya rike takamaiman lokutan ba amma dai duka da tafiyarsa da dawowarsa baxai wuce mintinina goma ba ko sha biyar, sbd a falo ma safara'u din ta tsaya jiransa har yadawo" Barr tayi 'yan rubuce - rubucenta kana tadago "Shin hajiya rahama xaki iya kula da lokacin da yusuf yakawowa 'yarki maltinar? Ma'ana kinga maltinan ko kuwa arufe cikin leda yakawota?" Hajiya Rahama tadanyi jim kadan kana tace "eh tabbas a leda yakawomata amma sbd matsuwar datayi tun a falo din ta xarota daga ledar kuma ta fita da ita xuwa dakinta ahannunta" Nan ma dai rubuce - rubucen Barr hauwa'u Auwal tayi,

"wato dai idan har na fuskanci Hajiya kina nufin kinga maltina din ido - ido kafin marigayiya ta fita da ita xuwa dakinta?"

MUHADU ZUWA GOBE AMUN AFUWA

Yusuf Æbdullâhi Æ Jibagâ ke muku barkada wannan lokaci***TSAKA MAI WUYA**7

Yayinda yusuf yadago kansa kwallane ke zuba daga idanunsa, gamida karawa da wata huci kaikace katon bijimin saniyane' yafara xancensa da cewa'' nibadan iya kashe bera bama balle mutum.
Kowa yasanni da sanyin zuciya sha'awar kadaituwa nikad'ai shine aikina.. Tayaya zan kashe dan adam?' alokacin safara'u tadawo tana kokarin shigowa da motonta cikin gida ina zaune neda baba maigadi¤ abakin get muna hiran' kan yadda gwamnatin me malfa ke kashe jama'ar kasata arewa. Da sunan boko haram' yake kawo wasu hujjoji kancewa tabbas me malfa shine boko haram..
Wanda xan'iya tuna shine ==>

1: Sanda Aka kai Hari a Makarantar oyon Aikin Noma ta Jihar Yobe, akwai sojoji dake gadin Makarantar, amma awa 4 kafin akai harin, aka janye sojojin: SHIN Menene Alaqar Sojoji da Hare Haren Boko Haram?

2: Marigayi Tsohon mai ba wa shugaban Najeriya shawara ta fuskar tsaro, Maj. Gen. Andrew Azazi, yace: PDP itace Haqiqanin Boko Haram, fadin haka keda wuya, sai shugaban qasa ya sauke shi daga muqaminsa, ba'a jima ba, sai muka ji labarin jirgi ya yi hatsari da shi. Har yanzu ba mu ji dalilin da ya sa jirgin nan hatsari ba, lalacewar inji ne? Ko karewar mai? Ko rashin kyawon yanayi? Anya hatsarin nan na Allah da Annabi ne kuwa?

3: Harin da aka kai a chocin dake Jami'ar Bayero (BUK), an kama wasu Arna 2, da suka tada Boma boman, dayan ma sunansa Augustine, shin shima Dalibin Bin Yusuf ne?

4: Gomnan Jihar Legas, sanda aka kai masa Sojojin taraiya jiharsa, yace: Bayason koda soja daya ya kwana a jihar Legas, idan kuma bomb ya tashi a jihar legas koda kuwa a
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2

Please Login or Register in order to submit comment