Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

This Document is compiled by
Shuraihu Usman - 08140419490
YEAR of compilation - 2023;
Published to Taskarnovels.com.ng

TSAUTSAYI KO GANGANCI? 1¶

Suhairat kyakyawa
tagani tafada tana zaune agarin maiduguri
shuwa arabce fara doguwa iyayenta sunada
rufin asirinsu amma duk idonsu ya rufe basu
gani kwadayi yasa kullum burin maihaifinta
yaga yarsa ta samu hamshakin mai kudi.

kuma bawai da burin aureba kawai ta
yaudaresa ta yashe kudinsa tayi gaba
abunta ya zaunar da suhairat yayimata
mummunar hudubarsa tun bata dauka ada
kafin hudubarsa suhairat macece mai son
jama'a gata dama kyakyawa ko acikin
maiduguri saikayi dagaske zakasamu mai
kyauta dan haka take da masoya dayawa
amma ana tsoron yimata magana saboda
wulakancin babanta idan yaga kai bakowa
bane kuma kai ba mai kudi bane kai koda ace
kai mai kudine sai yayi bincike yaga yawan
dukiyarka dayaga batada yawa sai yarabaka
da ita sannan mahaifinta yanada m:asifar fada
indai akan kudi ne shiyasa abokanansa suka
samasa kasko. Mahaifinta baidamuba suhairat
tabar gida harnawani kwanaki tareda wani
hamshakin mai kudi wannan yasa suhairat
gaba daya ta chanza itama burinta harka da
mai kudi suhairat ta karbi kyautar motoci yafi
sau akirga daga haduwarku ta farko dolene
kayimata kyauta ta musamman suhairat har
aure takeyi idan taga akwai kudi masu
yawwa agunka saita aureka idan tagama
tatsaraka saita nemi ka saketa idan kuma
kaki saita kaika kotu tabawa alkalin cin hanci
ya kashe auren idanma haka baiyiba. Saita
kasheka ta hanyar sama guba a abinci
wannan yasa suhairat ta shahara tsakanin
attajiraiiii
Ko wane attajiri da masu kudi da kuma
manyan jami'an gwamnati suyi tarraya da
suhailat yarinya mai haskawa kenan a harkar
bariki yawan daddewa warka da ita shine
yawan kudinka da hidimar da kakeyimata
suhailat tanayin bariki da uba kuma takoma
tayi da dansa kai harma gwamnoni suna
mu'amala da suhailat. Mahaifinta yasamu
duk abunda yakeso domin yanzu yasamu
abunda yake nema domin yanzu ana iya
sakasa acikin sahun matasan attajirai na
garin maiduguri sakamakon yanzu yanada
motoci sunkai goma sha biyar gidaje da
filaye kuma basusan addadin suba amma
kullum ya gifta ta gaban jama'a ana
zundansa ana zaginsa shida yar tasa ana
cikin haka Al amarin tashin hankali yafara.

Faruwa a maiduguri haka yasa kowa yaje
zaman gida ba harka mutum saidai yaci
abunda yatara harkar tsaro tayi karanci a
garin yau bomb gobe harbe harbe abunma
yafi taba farar hula dan haka talakawa suke
kauracewa gun neman abincinsu titina kuma
babu zirga zirga saboda jami'an tsarone
akan titina idan kafita zasu cima zarafi idan
kafada hannu wadanda ba nagariba.
Acikin garin bauchi da misalin karfe hudu
nayamma yusuf yana zaune a gida
sakamakon yajin aiki da hukumar jami'oi
sukatafi wannan shiya yusuf zaman majalisa
da tuni ya dauki littafi yana nazari yusuf
dalibine a jami'ar AtBU ta BAUCHI yana
nazarin tatalin arizikin kasa wato economic
yana shekara ta uku saura daya yagama
yanata mafarikin zama hamshakin mai kudi yusuf kyakyawan amma iyayensa talakawane
yanason rayuwar fantamawa suna zaune a
unguwar hotoro mahaifinsa yanada kokari
wajen farantawa iyalinsa kuma gashi dattijon
arziki anagani girmansa da jin maganarsa
Yusuf bashida wani buri nagani yafarantawa
iyayensa sakamakon ganin yadda suke
dawainiya da ruyawrsa yusuf yana dan taba
sana'ar hannu amma bawai don ya riketa
amatsayin madogaraba yanayi kafinta da
sauran aiyuka wadanda yaga zai iya kuma ta
inda yashafawa kansa ruwa wajen rashin
kula yan mata zamani na yanzu masu
wayyon tsiya da son kudin jaraba shiyasa
bayada tunani komai sai na karatunsa
dalibine mai hazaka yajan ajin farko a jami'a
wato 1st class wanda hakan ba karamin.......

temaka masayayiba wajen rage kashe kudi a
makaranta komai abokanansa ne keyimasa
mata kuwa wannan ba'a magana sunsha kai
masa farmaki amma basuyi nasaraba mace
daya kawai taciri tuta amma bawai a sunan
budurwaba sai dai wace yafi kulawa acikinsu
yakejin maganartaaa
Wasu suna zargin soyayyace a tsakaninsu
amma idan ka tambayi daya daga cikinsu
zaicema a'a bawata alaka tsakaninsu
maryam ce yar gidan kwamishinan yada
labarai na jahar bauchi itace take kaisa har
gida a motarta tanason yusuf amma takasa
gayamasa kuma ita taga alamun baison yin
soyayya saboda sau dayawa idan suna hira
tana dan tsokanarsa akan soyayya sai yace.

aishi bayayi bayanzuba wannan shike bata
tsoro gayamasa abunda ke ranta gudun
alakarsu tasamu matsala amma tanajindadi
saboda tasan baya kula wata yau ranar
asabar itace ranar ta tafara chanza yusuf
wajen misalin karfe hudu na yamma yayi
wanka yafito wata majalisarsu ta matasa ya
zauna amma yau yayi rashin sa'a shikade ne
tunda yaga haka yayi zargin akawai wasan
kwallon kafa tunda yaga abokanansa
basunan yana zama yafito da wayarsa kirar
nokia 2700 domin ta tayasa hira abunka da
samarin zamanin na yanzu ba'arasasu dayin
yan chating dinan nazamani wato su 2go da
kuma facebook dandalin sada zumunci haka
kuwa akayi yusuf yashiga application ya bude
2go chat ....

TSAUTSAYI KENAN dayasan meye zai tarar yau a 2go dai beso rike wayaba arayuwarsa ..abokanansa goma sha biyar
dukansu abokanansa ne wanda yasansu na
makaranta da na majalisa sai mata biyu
daya yar uwarsa daya kuma maryam ce
kawarsa ta makaranta yana budewa yaga
babu kowa akai sai yayi niyar sauka kawai
sai ya chanza shawara yaje yashiga room na
nageria da kuma ATBU na ATBU yaga basu
tatatauna wani abu mai mahimmanci dan
haka sai yafita yakoma na nageria anan ne
yaga anata takadama akan suwaye sukafi
shirya yaudara da karya a soyayya to
abunka da wanda ba harkasaba amma sai
yaji jayayya tana burgesa sai yatsaya yake
kalla na dariya yayimusu dariya to acikin
wanda sukafi rinjaye wajen musun watace
suhailat da wani namiji usman sai suhailat
takecemasa kaikuma sarkin dariya baka
magana ne sai yace ai ba hirata akeba kawai
kallo nake tace hmm to meyasa kace haka
sai yacemata aishi bayayya soyayya sai
tayimai dariya tace lailama ka rainaman
hankali ace wai saurayi baya soyayya haka
dai sukaita hira basu ankaraba kawai YUsuf
yaji kiran sallah yayimusu salama yace yatafi
sallah yana fita yaga friend request din
suhailat yayi murmushi yayi accepting

GOBE ZAN DAURA
wannan labari yazo mukune daga tasakar¶¶¶YUSUF A JIBAGA,T$AUT$AYI KO GANGANCI.? 2

tayimai dariya tace lailama ka rainaman
hankali ace wai saurayi baya soyayya haka
dai sukaita hira basu ankaraba kawai Ashir
yaji kiran sallah yayimusu salama yace yatafi
sallah yana fita yaga friend request din
suhailat yayi murmushi yayi accepting
Bayan sallar isha'I wajen karfe tara nadare yusuf ya dauko wayarsa yafara dane dane sai
ya ziyarci shafin dandalin sada zumunci na
facebook yana shiga ya bude inbox dinsa
yaga babu wani sabo sako sai comment da
akayi akan status dinsa yayi replay ya sauka.

yashiga 2go hana hawa yaga sakon suhairat
ce tace kai matsoracin mata tayimai wink
yayi mata murmushi yace to kinga laifin
nane? Tace eh kuma a'a saboda kowa ai
yakamata yana jaraba sa'arsa yusuf yace
sa'ar kawai itace kudi nikuma banida kudi
kinga nasan wahala zansha tace haba ai
akwai so tsakani da Allah yace eh hakane
amma ai yana karanci a irin wannan lokacin
yace kuma koke nace inasonki bazaki soniba
saboda banida kudi ko mota ko babur saida...

taji wani abu acikin zuciyarta tabbas gaskiya
ya fada amma yakai yasani amma kuma sai
taji kawai ai tadamu tasansa ko wane shi
saitace a'a aini bana cikinsu nan fa sukaita
chat har saida batirin wayarsu yakare sannan
suka hakura yusuf ya kwanata cike da r:ashin
jindadi tunda yake bai taba jindadi din 2go
irin wannan ba amma gashi batir yayi mai
tsiya itama haka suhailat takasan ce taji.

kawai tadamu da abunda bata tabayiba taji
tadamu da wani wanda ba wai wani karuwa
take dashiba kuma wai dama haka rayuwar
duniya take domin ita a tunaninta yaza'ayi
ace ta social network ayi irin wannan
shakuwa da kuma damuwa haka taita tunani
har bacci yasaceta
Akwana atashi shakuwa takuma shiga.

tsakaninsu marar musalatuwa wanda daya
daga cikinsu bayajindadin hawa 2go batare
dayaba kuma sunyi musayar lambar waya
ajunansu amma kuma babu wanda ya furtar
kalamar soyayya a tsakaninsu amma kuma
yanayinsu yayi kama da na masoya kuma
babu wanda yataba ganin wani kuma babu
wanda yataba nunawa wani hotonsa yanzu
Haka yusuf baya kula kowa ko abokanansa
na 2go da sunyi salama suka gaisa shikenan.

ba hira sai yayi appear away abunda bayayi
da kuma baya dadewa online amma yanzu
sai yayi awa biyu uku akai maryam tana mai
magana amma bayamata replay da wuri sai
abun yafara damunta anya kuwa bawata
Yusuf yasamuba yakemata haka nan da nan
kishi ya motsa tarasa abunda yake mata dadi
yau dai tayi shawarar zuwa gidansu yusuf da..

yamma domin jin meke faruwa haka saboda
abokansa ma sunga chanji harsuna tunani ko
maryam ce ta ciri tuta agunsa suke soyewa
yadena kula mutane haka amma sai sukaji
sabanin haka itama kanta maryam din abun
nadamunta kuma shareta yake.
Yammaci mai dadi wanda yake dauke da

tatausar iska mai dadi wace kekadawa daga
arewa zuwa kudu wannan yasa zakaga kowa
na cikin nishadi a fuskarsa iskace mai yaye
damuwa musamman gwaraye marasa aure
ance sunfi yawan matsaloli wannan iskar
tana temakawa wajen zurfafa tunani da
neman mafita akan matsala wannan yasa
kowane yafito dibar rabonsa a dai dai lokacin
motar kirar 406 takaryo kwana shikuma
yafito daga gida sai gyara kwalar riga yake yusuf ne yayi wankan yamma yana sauri
zuwa wani waje hakan yafito a fuskarsa ne
kallo daya zakaimai kakaranci haka a tare
dashi baima kula da motarba horn yaji
anyimasa ya juya hankalinsa yakai kan motar
sannan yaganeta yaje bakin motar yayi turus
domin saurinsa yaje ya karbo wayarsa agun
charge domin jiya kwana sukai suna chat
kuma ba'a kawo wuta ba sunyi kuma
alkawari da suhailat zasuyi chat karfe hudu
danhaka yamanta ma da maganar zuwan.

maryama amma gashi yanzu hudu da minti
biyar yasan suhailat tanan tana jiransa
yashiga gaban motar suka gaisa tayimai
salama ya amsa da yar fara'a a fuskarsa
tace wai meke damunka ne shine yasa nazo
naji yayi wani murmushi yace haba babu
abunda yake damuna mekikagani tace naga
changi ne awajen chat da kuma waya idan
nakiraka Allah Allah kake mugama idan kuma
muna chat sai naga kana delay idan nayi
magana kace ka aiki kake akasin da bahaka
kakeba idan kana wani abunma sauka kake
amma yanzu sai na sauka nabarka online
nadawo natarar dakai yusuf idan akwai wani.

abu kagayamin domin yau nakeson gayama
wata magana mai mahimmanci idonta duk
yacika da kwalla gata dama bata iya fadaba
ko rashin mutunci nan da nan idonta yafara
kadawa wanda suke kamar madara don
haske amma dan lokaci kadan sun chanza yusuf yakasa hada ido da ita kuma yakasa
magana dagowar da zaiyi yaga hawaye fala..

idontaaaaaa
Mahaifin maryam hamshakin dan kasuwane
kafin ya rike mukammin kwamishina yatara
dumbin dukiya kuma maryam kade Allah
yabasa dan haka ya dauki son duniya ya
duramata shiyasa maza sukayimata cha
akanta kowa da kokan barar tasosa domin.

samun soyayyarta amma duk tayi watsi dasu
saboda tasan yawancinsu don dukiyar
babbanta suke sonta dan haka take gani
ashir shine wanda take nema kuma takeso
domin tasan dukiyarsu bata gabansa don
haka take tunanin tasamu wanda yaddace
daita wannan yasa take neman soyayyarsa
Abun yayi mutukar taddawa yusuf hankali
ganin hawaye a idonta wannan yayi mutukar
girgizasa to wai meyasama take kuka haka.

shima ya tsinci kansa acikin tausayamata
yace haba maryam mai yayi zafi haka kike
zubada hawaye haka karkisan kukamana
kukanki ba karamin taddamin hankali yakeba
kuma kwana biyu ina busy ne shiyasa kikaga
haka amma yanzu komai ya lafa aiki nake
tayya babba wannan shine karo nafarko da
yayimata karya dan haka yasa ta yarda da
maganarsa ta danyi murmushi tareda sakin
fuska sannan shima yayi mata shima hade..

da yar dariya itama tayimasa sannan tace to
ai nazata kasamu watane kamanta dani yayi
murmushi habawa ai bana soyayya kinsan
tace to ina wayarka sai gabansa yayi daras
tana gun charge dazu na kaita tace shikenan
sai tace ma inzaka ne yanzu yace bako ina
nafito ne yusuf ya duba agogo yaga 4:15
acikin ransa yace tanacen tanajirana sai
maryam tace to bari natafi yace to sukayi
sallam cikin jindadi akan zasuyi magana a
2go anjima.
Tana tafiya yaje yakarbo wayarsa yatarar da.

20 missed call nan da nan yakira suhairat ce
amma shiru bata daukaba ya hau 2go
yaganta online yayimayta magana amma
shiru duk komai yayimai zafi yarasa abunda
kemasa dadi yayita kiranta aMma taki dauka
yarasa abunda kemasa dadi yayi niyar sauka
kenan sai ga maryam online sai yayi sauri..

yayimata magana tajidadin haka sai
sukatayin hira har takesasa dariya tanamai
zancen aure sukai ta dariya sai wajen
magariba zasu rabu sai yaga replay na
suhairat take cemasa bana kusa da wayar
nakiraka shiru sai kawai nashiga wanka ina
fitowa kuma barci ya daukeni sai yaji sanyi
aransa yace ai nazata fushi kikayi saboda
ban amsa kirankiba

yusuf A jibaga shiya shirya muku wannan muhadu gobe...

add me on whatsapp
08071051138T$AUT$AYI KO GANGANCI? 3

yusuf yace nazata fushi kikayi saboda
ban amsa kirankiba tace a'a kasan bazanki amsa kiranka bana kusa da wayarne
nakiraka shiru sai kawai nashiga wanka ina
fitowa kuma barci ya daukeni sai yaji sanyi , Azuciyarsa.

iyaba burina naga nakasance dakai akoda
yaushe suhailat ce tayi wannan furicisukayi hira sai yacemata sai anjima
suka sauka tace toya alkawarina yace yanan
anjima zan nunamiki dafatan kema kinyimin

nawa tace ehmana yayiwa maryam salama
ya sauka.
Soyayya mai karfi ta kulu tsakanin yusuf da
suhairat da kuma maryam amma yafison
suhairat ranan suna chat sai suhairat take
gayamasa kwana biyu fa batajindadi amma
batason zuwa asibiti tai tayimasa shagwaba
amma yadage sai taje asibiti suka bar
magana akan gobe zataje sai takece masa
naso nabaka mamaki kwanaki kawai da
saidai kajini a bauchi, yace a haba aiko walahi
danafi kowa farin ciki yace wakikasani a bauchi,?
tace kai nasani gunka zanzo ya zare ido. Na
suprise ya turamata yace a ina zan ajiyeki
rufamin asiri tace hmm matsoraci to gun yar
uwata zanzo dad ne ya yahanani yace koda
naji dama kinada yar uwa? Tace eh kasan
Shekal? Yace eh nasani amma gidan wasu
nasani dan ajinmu tace to yayata tana aure
a commisioner road nan zatazo yace eyyyah
banjidadiba tace ai baka kainiba sukaidai
cigaba da hirarsu ta soyayya sunyi bala'in
shakuwa ta yadda kowa ke shaukin ganin
dan uwansa wannan tasa Akafara ganin.

change agun yusuf yanzu kullun yana dane
dane da waya yanzu ma baya fitowa ko
yaushe yana gida idan kagansa yafito sai
sallah kokuma kai charge haka yakoma
ranan suna chat sai suhailat take cemasa My
dear kazomana garinmu yace ai garinku
bazan iya zuwa nadawoba shiyasa amma
walahi da tuni nazo tace eh hakane amma ai
zaka iya kwana daya kadawo yace aikuma.

bazan iya zuwa nayi kwana daya
nahakuraba dole sai nakara kuma gashi
kudin motar wani zaibani tace haba indai
wannan karkadamu idan ma a mota kakeso
akawoka walahi zansa a kawominkai kawai
ni anhanani zuwane amma da kawai saidai
kagani yace to kibani kwana biyu zanyi
nazari akai tace to my dear.
Washe gari suhailat da yusuf suna hira sai
take cemasa honey namatsu naganka yace
me too dear amma ina tunanin iyayenane
amma babu damuwa zanyi zuwa na kwana
daya amma kuma ba wannanne matsalaba,
rashin kudi tace hmm wannan ba matsala
bane kanada account a bank yace a'a tace
to kaje ka bude gobe zanturoma da kudi
tacemasa sai yace to amma ya dauki
maganar wasa gari nawayewa sai yaje gun
abokinsa yace ya rakasa zai bude account
abokinsa yace ba'afa bude account a bank
saida kudi yusuf yace nawa yace kowane..

bank da kaidar bude account a bank banking
farko sai mutum yanada 2000 wato first bank
sauran kuma 5000 da sauransu yusuf yace to
muje 1st bank din sukaje gun customer care
aka basu bayani akan asusun da zasu iya
budewa da ka idojinsu yusuf, yace zai bude
asusun ajiyene tace to suka karbi form suka
cike sukai komai yabude account akabasa
account number da yamma yabawata tace to.

gobe zaiji alert yaushe zaizo yacemata
zasuyi magana gobe tace to aikuwa gari na
waye da misalin karfe goma na safe yaji
wayarsa tayi kara yazata message ne amma
yana budewa yaga akasain haka baisan
sanda ya mike tsayeba domin kudin sunbasa
mamaki naira dubu dari yagani nan take ya
rikice yarasa samun nutsu ya shiga sake
saken zuci
Yusuf ne yaketa fama gyaran daki yana share
dakin mahaifiyarsa tace baki zamuyine ake.

wannan tsaftar sai yayi murmushi yace a'a
amma yaji zuciyarsa ta buga domin niyarsa
kawai yayi tafiyarsa batare da yagayamusu
ba tunda kwana daya zaiyi idan yadawo sai
yayimusu wata karyar amma sai gashi ana
neman kamasa tun kafin abun yakan kama
amma sai ya chanza shawara zaibiya ne
kawai yasiyi kayan sawarsa a wani shagon
wanda zaisa basai yadauki nasaba domin
kar'agane. Daddare wajen misalin karfe 9:00
suna hira sai yakecemata gobe zanzo
suhailat tayi murna dahaka sosai tace pls
kataho da wuri kaji kaga harkahuta koh sai
yace ai wajen 10 zai taho tace haba yayi..

rana kataho 8 yace ai kuma yayi wuri aguna
haka dai suka tsaida lokaci zai bara bauchi 9
washe gari da sassafe ya shirya yayi wanka
wajen misalin karfe 8:00 ya dauki duk abunda
zai dauka wanda yasan zaiyimasa
mahimmanci a tafiyar yafito bai zame ko
inaba sai shago. Saida kanan kaya yafitar da
dubu 20000 a bank yasiye kanan kaya masu
masifar kyau kuma masu tsada kala biyu
20000 baizame koinaba sai bauchi line yaje ya
nemi motar maiduguri kuma yayi sa'a saura.

mutum biyu yana zuwa ya shiga ba'afi minti
biyarba wata budurwa tazo tahau suka tashi
9:15 dai dai sunbar cikin garin bauchi suka
kama hanya sai gudu motar kirar computer
ce toyota yusuf ya toshe kunnasa da abun
kunne yakuna waka ya jingina da kujera ya.

shiga kogin tunani yadda acikin kwanaki 14
yashiga cikin kogin soyayya gashi yau shine
yayi tafiya mai nisa har zuwa garin maiduguri

YUSUF A JIBAGA KE MUKU BARKA DA DARENYAU.

MUHADU GOBET$AUT$AYI KO GANGANCI ? 4

sunbar cikin ga bauchi suka
kama hanya sai gudu motar kirar computer
ce toyota yusuf ya toshe kunnasa da abun
kunne yakuna waka ya jingina da kujera ya
shiga kogin tunani yadda acikin kwanaki 14
yashiga cikin kogin soyayya gashi yau shine
yayi tafiya mai nisa har zuwa garin maiduguri
akan mace yabar iyayensa da yan uwansa
baisantaba basu taba haduwaba amma
gashi yau yana kan hanya anya kuwa yayiwa
kansa adalci yana cikin wannan tunanin yaji
ance malam mekaki tunani ne wata murya
mai zakice tacemai haka tareda taba.

cinyarsa yayi firgigit yace mefa wannan
budurwarce takemasa magana tace kabada
kudin motarka. Yace yi hakuri namanta ne
yamika nasa to dama budurwanan so take
tasamu damar yimasa magana dan haka sai
tacemasa kaiko mekake tunani yace uhm
bakomai tayi murmushi tace anya kuwa wani
tunanin naka yawuce kace haka yace eh
hakane ina tunanin tafiyar ne bantaba zuwa
maiduguriba shiyasa tace eyyah to gun
wazaka nanfa ta chanzamasa tunani yakama
kokwanto anya kuwa yagayamata kokuma.

yayimata karya sai tace yanaji kayi shiru sai
ya wayance yace mekikace tace gun wazaka
a maid din yace gun yayana zani tace oh
awace unguwa yayi shiru sai yacemata idan
mukaje tasha zankirasa sai yazo ya daukeni
tace ok suna cikin tafiya sai suka hango.

motoci sunyi tsaya sai direbansu yayi sauri
yayi tsaya ashe yan fashi ne suka tare hanya
dan haka ya koma baya basu gansaba
sukayi baya sosai suka tsaya duk wanda zai
wuce suka hanasa wucewa suka jira anan
babu wanda suka yazo ya wuce wato
maidawowa gashi ko nisa basuyi a suka.

tsaya nan yusuf suna hira da budurwanan
anan ne yake tambayarta yace ke gashi baki
gayammin sunankiba sai tace sunana hauw,a jiddah mahaifina shine commisioner yan
sanda na maiduguri amma ina karatu bauchi

jami'ar bayero university kano yace ok yayi
kyau wato ana yajin aikin malaman jami'a
yasa zaki koma gida to meyasa kikahau
motar haya eh motarmuce taci karan shaf
shine nikuma banbari a gyaraba walahi
nadamu nagani a gida shiyasa yace hakane
to amma ai lafiyarki tafi komai kinsan
yanayin rashin tsaro musaMman ma yanzu
garin naku dazamu shiga tace hakane todai.

Allah yakaimu lafiya yace ameen yacemata ai
nima a jami'ar nake taku tace haba da
zumudinta yace Allah ina karanta economic
kefa tace turanci nake karantawa yace wow
inason course din MSC dina a english zanyi
tace nima inason econs sosai amma tafison
account nan fa sukaita hirar makaranta har
wajen karfe hudu sai wajen biyar saura
sannan yan fashinan suka saki hanya tunda
suka dauki hanya gudu kawai saboda basu
dare yayimusu cikin ikon Allah basu kusa da.

maiduguriba sai ga hadari baki kirin ya
turunke sama wajen karfe 7:45 suka shiga
garin amma saboda hadari saikace karfe
12:00 dare ne kowa yatafi gida dama ga
dokar tabaci da akasa sakammakon rashin
zaman lafiya suna cikin tafiya sunkusa zuwa
tasha direban na sauri ya saukesu yasamu
makwanci kawai akafara ruwa suna shanyo
wata kwana akafara harbe harbe direban na.

kokarin sake hanya amma ina yamakara yan
boko haram ne da kuma yan sanda da sojoji
suke musayar wuta tun an harbe direban
motar ta nufi ramin kwalbati tafada kuma ga..

ruwa ya tsunke nima birona anan yafadi ina
lalubE domin kawomuku makomar yusuf da
Hauwa,u shikuma yusuf yaga suhairat aran
kuma yana mafarkin komawa gida washe
gari
Rai ajali cikin wannan harbe harben mutane
da yawa suka mutu acikin motar nan dakyar
Yusuf yasamu yafito daga ciki gashi anamaka
ruwan sama yana fitowa itama hauwa,u.

tafito sai suka runtuma da gudu sukabi wani
layi tsautsayi da baya wuce rana da kuma
taka sawun barawo ashe acikin motar nan
ansami murjanatu saboda rudewa
batasaniba suna cikin gudu kawai yaga tafadi..

tana nishi sama sama sakamakon yawan
jinin da ta zubar jiri ya debeta tafadi yusuf
yayi kamar ya gudu amma yakasa saboda
tausayi kuma tanata wani kakari tana salati..

Yusuf yaje kanta yace ya akayi tanunamasa
cikinta yataba yaji wani dumi yayi salati
inalillahi wa'ina ilaihi raji'un kafin yayi wani
abu sai yaga ankewayesa da bindugogi tana
cewa yusuf idan nayima laifi kayafemin yace.

a'a nan takeyi tayi shahada yan sanda nan
suka bugamasa ankwa suka dauketa sai
asibiti shikuma yana musu bayani amma.

basu kulashiba wani daga cikinsu yasa kan
bindiga yabugesa yafadi sumame. Hankalin
suhairat yagama tashi shiru yusuf bai
kirataba kuma wayarsa akashe tunda
hadarin yataso take nemanmsa amma shiru
yasa tafito yawwo bawai dan tasan inda.

zataba amma daniyar neman yusuf. Amma
shiru haka ta hakura takoma gida cike da
bakin ciki takuma zulumi. Bai farkaba sai
wajen karfe 9 nasafe tun suman da yayi inda.

yagansa aciki shine ya dugunzuma
hankalinsa da tunanin meyake faruwa
dashine haka yana zamansa lafiya yajawowa
kansa masifa yana cikin wannan tunani yaga
wasu sunzo kansa basucemasa komaiba
suka ajiye wasu abubuwa akan tebir sai wani
dogo yashigo sirri ya zauna yana kallon yusuf
yace dan samari inaso kabamu hadin kai.

akan yan tambayoyin da zanyima yusuf baice
komaiba yaci gaba yace idan kuma
kayimman taurin kai to bazakiji dadiba domin
munada hanyoyin dazasu sakaka kayimana.

bayani amma naganka kyakyawa dakai
shiyasa banso mubatamaka kyaunka shine
nake baka shawara sai yace gaka kamar mai
hankalin amma meyasaka shiga boko haram?
sannan menene hadinka da yar kwamishina
yan sanda gashi kajawomata ankasheta

AJIBAGQ KE MUKU BARKA WANNAN LOKACI.√

afuwan yau labarin nwa yazoda abun tausayi

AMMA GOBE XANCI GABA INSHA ALLAHUT$AUT$AYI KO GANGANCI ? 5

sai wani dogo yashigo sirri ya zauna yana
kallon yusuf yace dan samari inaso kabamu
hadin kai akan yan tambayoyin da zanyima
yusuf baice komaiba yaci gaba yace idan
kuma kayimman taurin kai to bazakiji dadiba
domin munada hanyoyin dazasu sakaka
kayimana bayani amma naganka kyakyawa
dakai shiyasa banso mubatamaka kyaunka
shine nake baka shawara sai yace gaka
kamar mai hankalin amma meyasaka shiga
boko haram sannan menene hadinka da yar
kwamishina yan sanda? gashi kajawomata
ankasheta

kuma mungano cewa kai bakone
ba dan garinan bane kai gunwa kazo?
Wadanan tambayoyi sun mutukar bashi tsoro
dakuma rashin samun amsarsu yayi shiru na
wani lokaci kawai sai hawaye suka kama
zibomasa tunani iyayensa yafadomasa sai
yanzu ya tuna abunda ya rabosa da gida sai
kawai sajin din yace kofur muje anjiMa
mundawo suka fita suka barsa...

Hankalin iyayen yusuf ba karamin tashi yayiba
na rashin ganin dansu kwana daya wannan
abune da yusuf baitabayiba hankalin
mahaifiyarsa yafi tashi akan mahaifinsa shi
baidamuba sosai saboda yasan da namiji ne
duk inda yake zaiyi kokari wajen ganin yakare
kansa kawai addu'a yakeyi akan duk inda
yake Allah yadawomusu dashi lafiya hakama
maryam duk tashiga wani yanayi na rashinsa
itace zirga zirga zuwa gidansu yusuf. Faman
kiran wayarsa amma akashe, mahaifiyarsa ta
sheda mata cewa" sudai tundasafiyar,
rananda zai bata haryau kwana biyu kenan
bata ganshi ba..
Wannan dalilin yasa maryma duk tabi ta rame
abun ba karamin daure mata kaiyayiba
saboda ba halinsa bane wannan
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment